Shu'umin Namiji Complete Hausa Novel
SHU'UMIN NAMIJI !!!*
*(Wannan labarin ƙirƙirarren labari ne, wanda na ƙirƙira, bakuma naso ajuya min shi tako wani siga....)*
*WRITTEN BY*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*DEDICATED TO MY LOVELY BROTHER KHABEER*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Вisмiιιαhirra hamanirrahiм*
*Chapter 1*
Wani irin gudu black colour car ƙirar RANGE ROVER ke falfalawa akan babban titin dake cikin garin *ABUJA* ...
Gaban wani irin makeken gate motar ta tsaya, minti kaɗan kuma ta soma wani irin ƙara kamar zata cire kunnen maisaurare, cikin mintuna ƙalilan maigadi da jikinsa ke rawa ya wangale makeken gate ɗin, da gudun bala'i ya cinna hancin motar tasa ciki, daga yanayin yanda yayi parking kaɗai ya'isa nusar dakai cewa wanda ke cikin motar, cike yake da iskanci haɗi da zallan taɓara... Duk yanda naƙosa wanda ke cikin motar yabayyana nasamu damar ɗauko muku hoton fuska da surarsa amma abun yaci tura, domin dai shegen ƙin fitowa yayi bare nasamu ganinsa.......
15 minutes ya kwashe cas batare daya sanyo kansa waje ba, a hankali yasako ƙafarsa waje wacce ke ɗauke da tsadadden black canvas mai ɗauke da fararen igiyoyi a samanta, a hankali yagama fito da duka jikinsa daga cikin motar, Masha Allah !! shine abun dana furta lokacin dana gama sauke idanuna akan shi, kyakkyawa ne ajin farko, haɗaɗɗen matashi maiji da kyau haɗi da zallan kuɗi uwa uba hutu, fari ne tas banda sajensa dakuma tulin gashin kansa babu abun dayake baƙi ajikinsa,, saurayi ne mai cikar zati da kuma haiba, yana da cikar sura dakuma ƙaƙƙarfan jiki, kallo ɗaya zakai masa kafahimci cewa mutum ne ma'abocin yin gym, kyakkyawar fuskarsa tana ɗauke da yalwatattun idanu masu ɗauke da brown eye balls acikin su, sannan kuma yana da dogon hanci gwanin burgewa, bakinsa kuwa ɗan ƙarami ne, mai ɗauke da ƴan saffa saffan laɓɓa light pink colour, gashin girarsa dana idanunsa a yalwace suke tamkar dai wanda yayi ƙari, wani irin haɗaɗɗen sajene yayi mawa fuskarsa ƙawanya, wanda kuma haddashi yaƙara wa fuskar tasa kyau, jikinsa kuwa gaba ɗaya a murɗe yake, sanye yake da White t-shirt fara ƙal ƙal da'ita, yayinda wandon jikinsa yakasance black pencil jeans wanda ya kamasa sosai, sai ƙafarsa dake sanye da black canvas, kunnensa kuwa saƙale yake da earpiece, da'alam dai ƙiɗan sa yake sha,, yayi matuƙar kyau sosai, fuskarsa tana ɗauke da wani asirtaccen murmushi mai ƙayatarwa da burgeqewa,, hanunsa riƙe da car key ɗinsa yadoshi wani haɗaɗɗen gini, dake cikin harabar babban gidan nasu, da'alama dai nanne babban falon gidan.....
Wata haɗaɗɗiyar Farar Mata wacce bazata wuce 47 years ba ke zaune akan ɗaya daga cikin haɗaɗɗun kujerun falon, tasha ado cikin wani irin danƙareren lace mai kyau da tsadar gaske, a zahiri idan kaganta zakai zaton batawuce 35 years ba, bakomai yasanya hakan ba fa ce tsananin hutu dakuma tsantsar jindaɗi da yabayyana ajikinta wanda hakan ya ɓoye asalin shekarunta,, iya gwala gwalan dake sanye a wuyanta haɗi da kunnenta, kaɗai ya'isa ya tabbatar maka dacewa itaɗin baƙaramar mai tarin dukiya bace.... Da wani irin fito yashigo cikin falon yanayi yana kaɗa makullin motarsa dake saƙale cikin yatsarsa manuniya,,
"Hello Mom "
saurayin yafaɗa cikin unigue voice ɗinsa...
Murmushi wacce aka ƙira da suna Mom tayi haɗe da cewa " Your Well Come My Son"
Bai amsa mata ba saima zama yayi akan kujeran dake kusa da'ita yana mai yunƙurin cire takalman dake ƙafansa......
*((Wannan salon na dabanne My Fans kubiyoni domin jin wanene *SHU'UMIN NAMIJI !!* *wayeshi ? menene halinsa ? wace gwagwarmaya za'a tafka ? Saikun biyoni zakusan komai, takunce dai Mrs Sardauna, kada kumanta wannan labarin yasha banban da sauran.... ))*
*(I'm sorry my fans Insha Allah zakujini da cigaban MENENE MATSAYINA ? a bubuwane suka shamin kaina shiasa kukajini shiru....)*
*10/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Lovely Brother Khabeer*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*Chapter 2*
"Inakaje ne wai *ΖAID* tunsafe rabon dana saka acikin idanuna ?" Mom tatambayeshi,
ɗan taɓe bakinsa yayi haɗe da cewa "aiki ne yaimin yawa a office, Labisat takawomin abinci.. " yanakaiwa nan a zancensa yasakai yafice daga cikin falon.... Murmushi kawai Mom tayi domin tafahimci cewa Shu'umanci'n Zaid ɗinne yatashi....
Wani irin haɗaɗɗen gini naga Zaid yanufa, wanda yake can gefe da makeken lambun gidan, key yasanya haɗi da buɗe wata ƙofa, wani irin haɗaɗɗen falo mai masifar kyau Zaid yashiga wanda nake tunanin nanne mallakinsa, Masha Allah, falo ne daya amsa sunan sa falo, cike yake da abubuwan more rayuwa, kujerune irin leather sit ɗinnan farare ƙal ƙal zube a tsakiyar falon, yanda kujerun suke da haske kaikace ba'ataɓa hawansu ba,, tsakiyarsu kuwa wani haɗaɗɗen brown chanies carpet ne shumfuɗe mai taushin gaske, wasu irin ƙawatattun curtains brouwn colour ne suka taimaka wajen sake bayyana kyawun falon, duk da cewa bawani tarkacen kayan ƙyale ƙyale bane a falon, amma hakan bai hana falon yin kyauba, kallo ɗaya zakamawa cikin falon katabbatar cewa mamallakin wannan katafaren falo, baƙaramin ɗan gayu bane,, tundaga falo Zaid yasoma cire rigarsa yawurga kan kujera, yana tafiya yana cire wandon jikinsa ahaka ya isa cikin haɗaɗɗen bedroom ɗinsa, saida yacire duk wani kayan jikinsa, kafun ya shige cikin bathroom ɗinsa, koda na leƙa cikin bathroom ɗinnasa saida nayi tsananin mamaki, wai ace banɗaki aka kashemawa kuɗi haka tamkar wani fadan shugaban ƙasa ? hmmm ALLAH yakyauta....
Fitowa yayi ɗaure da towel a ƙugunsa, yayinda jikinsa ke jiƙe da ruwa, gaban makeken dressing mirror ɗinsa dake cike da mayukan shafa haɗi da turaruka kala kala yanufa, saida yatsane ruwan jikinsa, kafun yasoma murza tsadadden lotion ɗinsa akan haɗaɗɗiyar fatan jikinsa,, komai dai cikin tsanaki yakeyi harya kammala,, riga da wando yakuma sawa, saidai wannan karon Blue colour garesu, sun kuwa matuƙar amsar jikinsa,, Wayarsa ƙirar iphone 11 pro max ne tasoma ruri alamar shigowar ƙira,, harta katse Zaid bai ɗauka ba, wani ƙiranne kuma yasake shigowa,, ɗan ƙaramin tsuka yaja haɗi da nufar inda wayar take,, Zee shine sunan dake yawo akan screen ɗin wayar, picking call ɗin yayi haɗi da kara wayar akan kunnensa batare da yace komaiba, "Hello Baby !! zee tafaɗa cikin wata irin shaiɗaniyar muryarta, ɗan ƙaramin murmushi yayi haɗe dacewa "Ya'akayi ne Zee ?" jin abun dayace yasanya Zee sake gyara zama haɗe da ƙara kashe murya tace " Ina guest house ɗinka pls Baby kazo... " Okay " yafaɗa a taƙaice haɗe da kashe wayar yacusa cikin aljihun wandonsa,, knocking ƙofar ɗakinnasa akashiga yi, cikin muryan faɗa faɗa yace "Uban waye ke bugamin ƙofa kamar yasamu falon Ubansa ?" Labisat dake tsaye riƙe da tire ɗin abinci ahanunta, taturo baki gaba haɗe da cewa "Bro nice fa, abincinka nakawo ma ka" tsaki yakuma ja haɗe da cewa "Oya maidashi fita zanyi, innadawo nazo naci " sumi sumi haka Labisat tajuya da abincin.....
Wata haɗaɗɗiyar Blue car yashiga haɗe da bata wuta yafice daga cikin gidan.....
Kaitsaye G.R.A yanufa inda acan guest house ɗinshi yake, yana zuwa maigadi ya wangale masa gate yacusa motar tasa ciki......
Jin tsayuwar motar shi yasanya Zee tashi da sauri tanufi hanyar fita daga falon, da sassarfa taje tafaɗa jikinsa haɗe da goga masa breast ɗinta, cikin kirsa tace " sannu da zuwa babyna,, wannan munafukin murmushin nasa yayi mata haɗe da cewa "Ƴan Mata yakike ?" "lafiya ƙalau " tabashi amsa daidai lokacin dasuka ƙaraso cikin katafaren falon,, janyeta yayi daga jikinsa haɗe da zama akan ɗaya daga cikin kujerun falon " Kawomin ruwa " yafaɗa daidai lokacin daya cire rigar jikinsa,, cike da kwarkwasa Zee tamiƙe haɗe da ɗauko masa goran ruwan faro acikin friedge,, karɓa yayi yakafa bakin gorar abakinsa, tas yashanye ruwan haɗi da cilli da goran ruwan hanu yamiƙa ma Zee akan tataho gareshi, aikuwa dama jira take dan haka taɓalle duka aninayen gaban rigarta, take manya manyan breast ɗinta suka bayyana,, kansa yanutsa acikin breast ɗinta, bayan yayi mata masauƙi akan cinyarsa, cikin salo yacire mata gaba ɗaya rigar dake jikinta, hatta breziya bai barmata ba, bakinsa yaɗaura akan nipples ɗinta, yashiga yi musu wani irin kalan tsotso yayinda hanunsa, ke kan bayanta yana shafawa ahankali, tuni Zee taƙara rikitasa da salonta, ɗaukarta yayi caɗak suka nufi bedroom, kwantar da ita yayi flat akan gado, bayan yacire komai najikinta, yanda yake wasa da'ita kaɗai yasanya Zee ficewa acikin hayyacinta, domin Zaid ƙwararrene awajen iya sarrafa mace,, cikin mintuna ƙalilan Zaid da Zee suka faɗa duniyar ashsha duniyar Mazinata, (Ya Allah kakaremu daga aikata Zina Ameen).......
*****
*ZARAH ! ZARAH !!* wata mata dake zaune kan tabarma keta kwaɗa gira,, "Na'am" wacce aka ƙira da suna Zarah ta amsa tana mai fitowa daga cikin wani ɗaki,, wata kyakkyawa matashiyar budurwa wacce bazata wuce 20 year ba tabayyana gaban wannan matar da ke aikin ƙwaɗa ƙira, cike da girmamawa tace Inna gani,, "Au dama tunɗazu kinajina iskancine yahanaki amsa ƙirannawa kome ?" matar tafaɗa tana mai gallamawa yarinyar dake duƙe a gabanta harara,, cikin tausasa murya Zarah tace "Kiyi haƙuri Inna wallahi, banjiki bane inacan ciki ina shirin makaranta, yau muna da lecture'n safe banso na makara " "Uwar Lecture kuke dashi da ubansa, inkinga kinfita agidannan to wallahi kinga mamin aiki nane " Inna tafaɗi haka tanamai tsakace haƙoranta da tsinken dake riƙe a hanunta,,,, cikin sigar lallami Zahra tace "Dan Allah Inna kiyi haƙuri idan nadawo sainayimiki duk abun dakike so " "Zaki tashi kisoma aikin dana saki ko kuwa saina mangareki banza mai kama da aljanu " Inna tafaɗa cikin faɗa , cikin sanyin jiki Zahra tatashi daga gaban Inna.... Wanke Wanke tafarayi sannan tayi sharan tsakar gida dana ɗaki,, saikuma hurawa Innar wuta, koda takammala aikin nata har 9 tayi, sam bataso ace yau tayi latti ba domin kuwa suna da lecture 8:00am, shikenan yauma lecture'n Sir Adam yasake wuceta kamar dai yanda yawuce ta wancan satin..... hijab ɗinta mai launin ruwan ƙasa tasanya, haɗe da saɓa jakarta a ƙafaɗanta, fitowa tayi tasamu Inna nazaune, bakin murhu tana ɗumamen tuwo, "Inna nizan wuce makaranta " Zahra tafaɗa,, "To uwar ƴan boko saikin dawo, aikin kenan bacas ba as saidai zuwa makaranta, da Mijin aure kika fito dashi, kikayi aure aida nahuta da wannan wahalar taki " Inna tafaɗa cike da bala'i.. Itadai Zahra batasake ce da'ita ƙalaba, tasakai tafice daga cikin gidan, tana fitowa ƙofar gida, zazzafan hawaye suka gangaro daga cikin idanunta, dasauri tasanya hanu tashare hawayenta, kana tacigaba da tafiyarta.........
((Wanene Zaid ? Wacece Zahra ? saigaba zakuji kosu ɗin suwayene, Wace alaƙace ke tsakanin Zaid da Zee ? mata da mijine kokuwa, iskancinsu kawai suke ? kubiyoni don sanin gaskiar al'amari... ))
*11/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Lovely Brother Khabeer*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*Chapter 3*
(sorry a chapter 2 nayi mistake nasa guest house ɗin Zaid na G.R.A, to ba G.R.A zansaba mistake ne, guest house ɗin Zaid na Maitama ne ba G.R.A )
Har takawo bakin titi bata samu abun hawa ba, gashi yau antashi da wani irin zafin rana, duk da cewa taran safe ne amma hakan baihana ranan bayyana zafin taba, tsaye tayi abakin titi tanamai ƙaremawa motoci da mashunan dake wucewa akan titin kallo, har izuwa yanzu mai adaidaita sahu ko ɗaya baizo yagil ma akan titin ba, takusan minti 12 tsaye a wajen kafun tasamu wani mai adaidai ta yaɗauke ta, kaitsaye babban jami'an da take karatu suka nufa.... Kamar koda yaushe abakin titi tace mai adaidaita ya sauƙeta domin dokace ba a shiga jami'an da motar haya, saidai idan motar kanka kokuma machine, nanma saidai in mallakin mutum ne... Ɗalibai ne iri da kala ke gudanar da harkokinsu acikin makaranta, wasu na hira da samari wasu kuwa na karatu, kamar dai yanda kukasan ƴan jami'a keyi,, kaitsaye tanufi gindin wata ƙatuwar bishiya wanda anan ƴan course ɗinsu ke tare, da'alama dai fitowarsu kenan daga lecture.... Da sallama ɗauke a bakinta taƙarasa garesu, bako wanne daga cikinsu bane suka amsa sallaman nata ba sai ƴan tsiraru, wasu ko da kallon banza suka rakata,, musamman ma ƴan matan dake wajen, koka ɗan hakan bai dameta ba domin dai hakan ba sabon abu bane a wajenta, musamman ma idan tayi la'akari cewa ita da su ɗin akwai banbanci, domin dukansu ƴaƴan manya ne itakuwa ƴar talaka ce futuk, shiyasa ma koda wasa bata yunƙurin haɗa kanta dasu,, zama tayi a gefen Aminiyarta Husna... " Yauma saida kikasakeyin missing lecture, anya kuwa Zahrah wanan exam ɗin da zamuyi baza'a samu matsala ba ?" Husnah tayi maganar fuskarta ɗauke da damuwa,,
ajiyar zuciya Zarah ta sauƙe, haɗe da cewa " Bansan yazan yi ba Husnah wallahi dole ce take sawa nayi latti gashi unguwarmu a kwai ƙarancin abun hawa " Zahrah ta ƙare maganar daidai lokacin da take ciro wani hand out a jakanta, "shikenan mukoma gefe saina koyar dake abun dana gane, domin ni wallahi lecture ɗin Mr Adam sam bana ganesa " Husnah tafaɗa tana mai yunƙurin miƙewa tsaye.... Duk da cewa tazo latti amma tafahimci darasin da Husnah takoyar da'ita, tamkar ma tananan akayi.......
Basu suka kammala lectures ɗin dasuke da shiba harsai 5 pm, a gajiye take liƙis uwa uba ga yunwa dake ƙwaƙulan cikinta, rabonta da abinci tun 10 am nan ma Husnah ce tasaya musu snacks da drinks a Cafeteria, ɓatare da ta tsaya wani abu ba tashiga Adai dai ta sahu tayi yo gida...
*MAITAMA*
Zaid da Zee kuwa ayar su suka sheƙe sosai, domin Zee har kuka saida tayi mawa Zaid, wanda hakan kuma ba baƙon al'amari bane wajensa, domin sau da dama idan yayi sex da Zee tofa saitayi masa kuka, na azaba ko na daɗi wannan ne kuma baisani ba,, tsaye yake agaban dressing mirror dagashi sai towel ɗaure a ƙugunsa, hankalinsa gaba ɗaya yana kan busar da gashinsa da yakeyi da hand dryer, Zee dake kwance akan makeken gadon ɗakin shame shame, kuwa ƙura masa idanu tayi, itakam Allah yasani, Zaid yana matuƙar burgeta, tanajin son gayen har cikin zuciyarta, saidai tasan cewa ko sama da ƙasa zasu haɗe, Zaid bazaitaɓa auren ta ba, saidai tana godemawa Allah ahakan ma daya bata daman raɓansa, domin raɓan Zaid ma sai mai sa'a, kuma sai macen da ta amsa sunanta mace ƴar gayu da aji....
Tsab yagama shiryawa haɗe dayi mawa kansa feshin turare mai daɗin ƙamshi,, Car key ɗinsa ya ɗauka haɗe da wayarsa, hanu yasa acikin aljihun wandonsa, kuɗi ya ciro bandir ɗin ƴan dubu dubu, ya cillamawa Zee akan cinyarta, batare da ya kalleta ba yace " Kada ki tafi sai kin kimtsamin gado na " yanakaiwa nan azancensa, yasakai yafice daga cikin ɗakin bakinsa ɗauke da fito,,, a maimakon Zee taji haushin yanda yamata, saima murmushin da tayi haɗe da lumshe munafukan idanunta, afili ta furta cewa "Allah kamallakamin Zaid amatsayin mijina".....
Tundaga Zauren gidan nasu ta ke jiyo tashin muryan Inna dana Baffa da'alama dai sana'artasu ta kullum sukeyi wato faɗa,, shahada kawai tayi tadoshi cikin gidan, domin dai tasan tana shiga tofa kanta faɗan zai dawo... Aikuwa a rubuce yake tana sawo kai cikin gidan, Inna ta ce "Kekuma uwar gantali saiyanzu aka tashi daga makarantar ?" cike da ladabi Zahrah ta rusuna haɗe da cewa " Baffa ina wuni "...."Daban wuni ba zaki ganni ? nace daban wuni ba zaki ganni ?? Baffa yakuma faɗa cikin tsawa, kai kawai zarah ta girgiza haɗe da nufar ɗakinta,, kwanciya tayi luf akan ƴar katifanta, zuciyarta cike da tunanin halin rayuwa dakuma yau da kullum....
Koda Zaid yabaro guest house ɗinsa bai zarce ko'ina ba sai wani babban Club ɗin dake cikin garin abuja, makeken Club ne mai kyau da tsaruwar gaske, irin Club ɗin nan ne daba kowa ke zuwanshi ba sai wane da kuma ɗan wane, Club ne na manyan guys, da kuma manyan ƴan mata, kamar ƴaƴan shugaban ƙasa da sauransu, amma idan dai har kai ba wani bane kuma ubanka ba kowa bane to fa baka isa shiga wannan haɗɗɗen Club ɗin ba, Zaid kuw yamaida wannan Club ɗin kamar ɗakin baccinsa, domin kuwa zaiyi wuya ace ya kwana ɗaya baijeba...
Zama yayi akan ɗaya daga cikin kujerun da aka ƙawata tsakiyar Club ɗin dasu, yana zama wata ma aikaciyar Club ɗin tanufu inda yake hanunta ɗauke da tire na glass wanda samansa ke ɗauke da glass cup guda biyu, da kuma zungureren tsadaddiyar kwalban giya, kasancewa duk wani ma'aikaci dake cikin hotel ɗin yasan, abun da Zaid ɗin ke sha idan yazo wajen... Duk yanda ma aikaciyar Club ɗin nan ke kwarkwasa Zaid baiko ɗaga idanunsa ya kalleta ba, domin shi baimaga macen dazai kula ba kaf cikin Club ɗin, balle kuma ita banza mai aiki.... Cike da nutsawa Zaid yakafa kansa ya kwankwaɗi giya son ransa, saida yayi tatul tukun yabar cikin club ɗin, bayan yayi waya da Asmee ƴar wani minister dake cikin Naija, cewa tazo ta samesa a guest house ɗinsa......
*WAYE ZAID ?*
Zaid tantirin Mazinaci ne kuma ɗan giya, uwa uba baida mutumci ko ƙaɗan, sannan kuma komai kayi masa baka burgesa, Zaid yana da Munanan halayya, Zina shine babban ciwon daya riga yayi mawa jiki da zuciyarsa ƙawanya, Zaid Mazinaci ne na ƙarshe, iskancin sa yake zubawa babu mai hanasa, domin dai iyayensa sunriga da sungama shagwaɓasa, bayajin maganan uban kowa, duk wata haɗɗɗiyar mace wayayya dake cikin garin Abuja babu wacce batasan Zaid ba, domin iskancinsa ya shahara yayi ƙarfi, kasan cewarsa kyakkyawan saurayi mai wanka da naira, yasanya wasu ƴan mata ke matuƙar ƙaunarsa, sannan kuma suke burin mallakansa, amma saidai sama yayiwa yaro nisa babban ma saidai kallo....
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Lovely Brother Khabeer*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*Chapter 4*
*Alhaji Ma'aruf Chanji* shine sunan maihafin Zaid, Babban mutum ne da ake da mawa dashi acikin Nigeria, yana da kuɗi sosai, sannan mutum ne mai kyautatawa na ƙasa dashi, bashi da rowa ko kaɗan, matarsa ɗaya *Hajiya Safara'u* kuma itace ma haifiyar Zaid, daga Alhaji Ma'aruf har Hajiya Safara'u shuwa arab ne, Allah yayi musu baiwar kyau ga dukiya, shekaransu biyu da Aure Allah ya azurtasu, da haihuwan ɗa Namiji, wato Zaid, Zaid dai kyakkyawan gaske ne, domin tsananin kyawunsa ke sawa yake shiga ran jama'a, Zaid tun yana ƙarami yataso da wani irin Shu'umanci, ga mugunta, haka zalika baruwansa da shiga harkan kowa, hatta iyayensa kuwa, gaisuwa kawai keshiga tsakaninsu, duk yanda suka so yasake dasu amatsayinsu na mahaifansa, amma abun yaci tura, Sosai Iyayen Zaid ke nuna masa tsananin ƙauna, da tattali, asalin sana'ar Alhaji Ma'aruf shine Chanjin kuɗaɗe, yayi ƙaurin suna a sana'ar, sannan kuma yatara maƙudan kuɗaɗe, ganin harkan nasa natayin gaba dukiyarsa na ƙara yawa, yasanyashi tattarawa yakoma America da zama, can ya cigaba da business ɗinsa, duk ko yanda yaso Hajiya Safara'u tabiyo sa America suzauna ƙiyawa tayi, saidai Zaid yayarda yabi mahaifinsa, inda a can yasoma karatun sa,, Zaid yanada shekaru goma a duniya mahaifiyarsa ta haifa masa ƙanwa maisuna Labisat, Labisat dai kyakkyawar yarinyace suna kama da Zaid, saidai a gaskia Zaid yafita kyau sosai, domin idan kaga Zaid zakai tunanin ba ɗan Nigeria bane,,,, acan America mahaifin Zaid kasuwancinsa kawai yasa a gaba, amma sa'i da lokaci yana zuwa Nigeria duba iyalansa,, Yanayin yanda yake gudanar da kasuwancinsa a America yasanya bashida wani kyakkyawan lokacin da zai kula da ɗansa wato Zaid, kullum Alhaji Ma'aruf idan yafita office baya dawowa sai dare, shikuwa Zaid rayurwasa yakeyi da turawan abokansa, wanda yayisu acikin school ɗin dayake, kunsan dai su turawa, babu wani abun daya damesu iskanci sun maidashi kamar ruwan sha, domin dai dayawansu ba addinin Allah suka sani ba balle su kiyaye, tun Zaid na da shekara 17 yafuskanci abokansa na school suna neman mata, shikuwa sam alokacin mata basa gabansa, duk da kuwa cewa suna kawo masa tallen kansu, amma baya sauraransu, duka abokan Zaid turawa ne, sai mutum ɗaya wato *ABID* Abid cikekken ɗan Nigeria ne cikin garin Abuja shima gidansu yake, sannan babansa shine Minister'n Man Fetur na Nigeria gaba ɗaya, Abid hatsabibin ɗan iska ne kuma tantiri domin kuwa tun yana ƙaraminsa yasan yanda zai jagwalgwala mace, Zaid da Abid a bota suke sosai, domin jininsu yazo ɗaya,, duk da cewa Zaid yana da ƙarfin sha'awa amma bayabin mata, saidai wani zubin yakan ɗan mawa mace kiss da dai sauransu,, lokacin da Zaid yake matakin lavel 2 na degree ɗinsa lokacin yana da shekara 21, Allah ya jefomasa ƙaddaransa kuma Hargitsi mafarin halakarsa,,, wata rana sunje yawon shaƙatawa shida saiɗanun abokansa, ya haɗu da wata ƴar iskan baturiya mai suna Nicky, abun daya fa ra ɗaukar hankalin Zaid game da Nicky shine kyawu da surarta, Nicky irin fitinannun matan nanne, shu'umai wanda idan suka ɗiga tsamansu akan abu tofa sai sun sameshi, tunda Nicky tayi ido huɗu da Zaid gaba ɗaya hankalinta yatashi, domin kuwa Zaid yayi mata hundred percent, bawani ɓata lokaci tabayyana masa soyayyarta a gareshi, Zaid kuwa dake ɗan izza ne saiya soma ja mata aji,, daga ƙarshe dai daya tabbatar da cewa itaɗin bata bibiyar maza sai ya amsa soyayyarta suka cigaba da shan love ɗinsu,,
Watarana Zaid yana kwance a ɗakinsa, sai ganin Nicky kawai yayi sanye da wani irin ɗan iskan kaya wanda yabayyana komai na surarta a fili, ganin da yayi mawa Nicky a haka baƙaramin ɗaga masa hankali yayiba, wata irin sha'awa yakeji mai ɗaga hankali, koda Nicky tafahimci haka saita yi amfani da damanta tasake ruɗa Zaid da irin salonta, jawo Nicky yayi jikinsa yashiga sun batarta tako ina, a rannan sheɗan yaribaci Zaid har yakusanci Nicky, tun da yake a duniya baitaɓa sanin ya daɗin Sex yake ba sai awannan ranan, baisan ya ƴa mace take ba shidai kallon su kawai yake, amma sai gashi yau yasani,, wani irin gamsuwa Nicky tasamu da Zaid a ranan wanda bata taɓa samun irin shi da ga wani ɗa Namiji ba,, tundaga Wannan rana Zaid yazama mashahurin ɗan iska kullum yana tare da Nicky suna aikata Zina, arana sai Zaid yayi Sex da Nicky sau Biyar,
Zaid mutum ne mai ƙyan ƙyami, shiyasa kwata kwata baya neman sauran matan turawa domin yasansu kowa buɗe ma ƙafa suke yashige,, Nicky ce kaɗai abokiyar watsewarsa, itama dan yafuskanci cewa bata mu'amala da kowani na Miji ne, sannu ahankali Zaid yasoma shan giya, koda Abid yafuskanci cewa abokinnasa ya soma baza iskancinsa, sai yasake haɗasa da wasu ƴam mata gangariya, aikuwa Zaid baiƙiba, nanfa iskancinsa yaci gaba da tumbatsa, haryazo ya fi ƙarfin Nicky, Ƙaurin isknacin Zaid har yaɗara na abokansa,domin ko Abid yanzu Zaid yafisa sanin kan mace da kuma iya iskanci,,,, duk wannan halin da Zaid ke ciki Dadynsa Alhaji Ma'aruf baisaniba, yanacan yasa harkan kuɗinsa a gaba, yakuwa mallaki dukiya masu mahaukatan yawa,, akwana atashi Zaid ya kammala degree ɗinsa, cikin ikon Allah kuwa yasamu kyakkyawan result, domin dai yanada ƙoƙari sosai, iskancinsa baisa yadaina karatu ba,, bawani ɓata lokaci Zaid yawuce London domin yin masters ɗinsa acan, hmmmm zuwansa London yaƙara masa iskanci sosai, shima Abid biyosa london ɗin yayi suka ci gaba da zuba iskancinsu acan,, Zaid yazama tantirin shu'umi idan yaga mace matuƙar tayi masa tofa saiyayi sex da'ita,, duk wannan tsawon shekarun da Zaid yaɗauka aƙasashen duniya, sauɗaya tak yazo Nigeria nanma satinsa biyu kacal ya tattara ya koma,,
Kwanci tashi Zaid yakammala Masters ɗinsa, take kuma wani Babban banki dake london suka nemi da yayi aiki dasu, sam bai amince da buƙatarsu ba, domin shi yafiso yayi kasuwanci, maƙudan kuɗaɗe Dadynsa yasanya masa wajen gina masa wani katafaren kamfani a London, shahararren kamfani aka gina masa na ƙera takalma da jakakkuna new styles, masha Allah cikin ƙanƙanin lokaci kamfanin Zaid ya shahara a faɗin duniya domin, kaya masu kyau da inganci suke bugawa,, Zaid yana karatu kuma yana kasuwancinsa harya kammala P.H.D ɗinsa, isakanci kuwa yaci uban na da,, wasa gaske saiga Zaid ya mallaki Company's a ƙasa she da dama, lokaci ɗaya Zaid yayi wani irin mahaukacin kuɗi, baiyi ƙasa a guiwa ba ya dawo Nigeria yakuma gina wani kamfani'n da ake ƙera gyalelluka wato vails, tunda ya dawo Nigeria baisake komawa ko wacce ƙasa ba, domin yaji ƙasar tasa wato Nigeria tayi masa daɗi, company's ɗinsa na ƙasashen waje kuwa, yasanya amintattun mutanensa suna kula masa da su......
Cigan Labari...
Daga Club ɗinnan Zaid baizarce ko'ina ba sai guest house ɗinsa, koda ya isa yasamu tuni Asmee tazo tana jiransa,, tundaga falo Zaid suka soma watsewa shida Asmee,, ........
((Kuyi haƙuri jiya kunjini shiru, walƙahi wayatace ba charge.))
*13/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Lovely Brother Khabeer*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*Chapter 5 то 6*
Haka Zaid da Asmee suka ɓata dare suna iskancinsu, basa ko tsoron Allah mahalicci,, haƙiƙa zuciyar Zaid ta bushe ƙarau, baya ko tuna azabar da Ubangiji zaiyi masa, aduk sanda yaje garesa batare da ya tuba ba.......
Kasancewar yau basu da lecture sai 12 pm yasanya gaba ɗaya aikin gidan itatayi shi, yayin da Inna ke kishingiɗe akan tabarma,, da bala'i Baffa yashigo cikin gidan " Wallahi ni nagaji bazan iyaba ehe, ace akan yarinya kwara ɗaya tol duk inda nagilma mutane zagina sukeyi, to bata saɓuwa, ke Zahrah inakike ne dan Ubanki ?" Baffa yaƙare maganar cikin hargowa, Zahrah dake cikin kitchine tafito jikinta a sanyaye domin tasan kwanan zancen,, "Lafiya kuwa Malam kashigo gida kana ɓaɓatu ?" Inna dake kwance tatambayeshi, " Kema kinsani ai akan wannan yarinyar ce mana Zahrah taƙi fito da Miji tayi aure, tananan koda yaushe cikin bulayin zuwa makaranta, makarantan da ba tsinana mata komai zaiyi ba, to wallahi nagaji, ko ina gulma ake wai nakasa riƙe amanar da ɗan uwana yabani, naƙi aurar da yarinya nasata karatu, bayan nafi kowa tsanar wannan ɗan iskan karatun da takeyi " "Ke Zahrah !!" yaƙira sunan Zahrah da kakkausar murya, batare da yabari ta amsa masa ba yaci gaba da cewa " bazan iyawa zagin mutane ba, nabaki nanda wasu kwanaki ki fito da miji koda kuwa musaki ne na tattaraki nayi miki aure batare da wani kayan ɗakiba, kije can ki ƙarata " Baffa nakaiwa nan a zancensa ya sakai yashige cikin ɗaki, Inna tarufa masa baya,,, ɗaki Zahrah ta koma haɗe da zama akan ƴar yalolon katifarta, " ya Allah gani gareka kafi kowa sanin halin da nake ciki ya Allah kakawomin ɗoki " wasu zafafan hawayene suka shiga sauƙa daga kan fuskar Zahrah, maganar kenan koda yaushe Miji Miji, wai shin ina zata samo mijin da zai aureta ? tun da take a duniya Namiji ɗaya ne yataɓa cewa yanasonta, kuma shima tundaga wannan ranan bata sake sashi acikin idanun taba, tayi imani cewa tana da tsantsar kyau da kuma sura, wanda zai iya janyo hankalin ko wani ɗa namiji zuwa gareta, amma maiyasa babu wani Namiji dake kallonta ballan tana harya furta mata kalman so ? tayi mawa kanta tambayar da bata da amsa,, jin motsin Inna a tsakar gida yasa tayi saurin share hawayenta, haɗe da ficewa daga cikin ɗakin, kuɗi Inna taciro daga kunkuminta, haɗe da miƙamawa Zahrah tace "Ungo maza kaima wa Ladidi mai adashe kice mata ga zubina na jiya " "to" kawai Zahrah tace haɗe da nufar hanyar fita daga gidan, domin dai dama sanye take da hijab ajikinta, al'adar ta ce bata zama babu hijabi, saidai idan a ɗakinta take....
Tafiya take tana kallon ƙasa, yayinda hannayenta ke naɗe akan ƙirjinta, da gudun gaske ya shawo kwanar saura ƙiris ya doketa, Allah ne kawai yasa tayi saurin matsawa gefe,, parking motar yayi haɗe da leƙo kansa waje ta window'n motar " Uh sorry Zahrah ina fata dai bantaka ki ba ?" ɗan guntun murmushi tayi haɗe da cewa "A'a baka takani ba" wani irin shu'umin kallo yabita dashi haɗe da cewa "Ina zaki ne haka da tsakar rana ?" " Aika zani " Tabasa amsa a taƙaice,, "Okay shigo na rage miki hanya mana " yayi maganar yana mai yunƙurin buɗe mata murfin motar, "A'a kabarshi kawai nagode" bata jirayi mai zai ceba tasakai tayi tafiyarta,, murmushi kawai Bash yayi haɗe da figar motarsa yayi gaba.....
*Wacece Zahrah ?*
Malam Adamu Muhammad haifaffen ɗan jihar Yola ne, su biyu ne a wajen iyayensu shida ƙaninsa Hayatu, Malam Adamu yakasance mutum mai mutumci da kuma karamci, Matarsa ɗaya Zainab, Zainab, asalinta buzuwar Niger ce fatauci yashigo da mahaifanta Nigeria, Mahaifan Zainab dana Malam Adamu suna da kyakkyawan alaƙa kasancewarsu maƙotan juna, tun Zainab na ƙarama Allah yasanya mata soyayyar Malam Adamu acikin zuciyarta, kasancewarsa kyakkyawan bafulatani, duk da dai tafisa kyau nesa bakusa ba, cikin ikon Allah Zainab nakai lokacin daya kamata ace anyi mata aure, iyayenta suka Aura mata Malam Adamu, zama sukeyi na lafiya da ƙaunar juna,, watarana iyayen Zainab suka shirya don zuwa Niger, ahanyarsu ta zuwa sukai gamo da ƴan fashi, suka harɓesu, sosai Zainab tayi kukan rashin iyeyenta, da ƙyar dai Malam Adamu yasamu ya rarrasheta, akwana a tashi kwatsam ciki yabayyana ajikin Zainab, sosai sukayi murna da samun ƙaruwa da Allah yayi musu, cikin Zainab nada Wata Tara tahaifo kyakkyawar ɗiyarta mai matuƙar kama da ita, saidai ita ƴar harta ɗara Zainab a kyau duk da kuwa kyau irin na Zainab, anyi shagalin suna lafiya inda yarinya taci sunan mahaifiyar Zainab wato *FATIMA* ana ƙiranta da *ZAHRA* Zahrah tataso cikin gata da kulawar iyayenta, saidai muce masha Allah,, watarana ne Malam Adamu yatattara matarsa da ƴarsa suka koma garin Abuja da zama, cikin wata unguwa da'ake ƙira Suleja, yakama musu hayan wani ɗan ƙaramin gida,, sana'ar saida takalma Malam Adamu keyi, yana da ɗan teburinsa a nan yake kasa takalman roba da su silifas (slippers), cikin ikon Allah kuwa,Allah baya hanasa na abinci da kuma na ƴan biyan buƙatun da ba'a rasaba, Watarana Malam Adamu ya tsinci wasu maƙudan kuɗaɗe a ƙasa, daya bincika kuɗin shine yataradda adireshi (Adress) na mai kuɗin acikin jakar daya tsinci kuɗin, a shema wanda ya wurgar da kuɗin, a nan gaba da unguwarsu kaɗan yake kuma yasanshi sunansa Alhaji Umar, Malam Adamu baiyi ƙasa a guiwa ba wajen kaimawa Alhaji Umar kuɗinsa, aikuwa Alhaji Umar yaji daɗi sosai, nan yaɗauki maƙudan kuɗaɗe yabamawa Malam Adamu, amma Malam Adamu haka yaƙi karɓa acewarsa, shi don Allah yayi bawai don abiya saba, aikuwa Alhaji Umar yaji daɗin hakan, haka dai Alhaji Umar da Malam Adamu suka soma zumunci, watarana Malam Adamu na zaune, Alhaji Umar yaƙirasa yace mai yasayamasa gida anan suleja, bakaɗan ba Malam Adamu yayi farinciki, har ƙwallan murna saida yayi, gidane daidai da zaman talaka Alhaji Umar yasai mawa Malam Adamu, ɗakuna huɗu ne acikin gidan sai ɗan madaidaicin filin tsakar gida, da kitchine da kuma makewayi, Koda Zainab tazo taga gidan itama taji daɗi sosai, bawani ɓata lokaci suka tattaro suka dawo gidan,, a kwana a tashi Asaran mai rai, wata rana aka wayi gari Baban Malam Adamu ya rasu, sosai mutuwar tajigata ƴaƴansa, amma babu yanda suka iya duk wani mai rai mamacine sunriga da sunyi imani da hakan,, bawani ɓatalokaci Malam Adamu ya ɗauko mamansa suka dawo garin Abuja da zama,, baifi wata uku da dawowar Goggo (Maman Malam Adamu) Abuja ba, tace ga garinku nan, Allah sarki su Malam Adamu sunkuma jin zafin rashin mahaifiyarsu,, bayan wani lokaci Hayatu yayi aure, Malam Adamu ne yace masa yadawo nan Abuja su zauna, tunda akwai ɗaki a gidansa, Hayatu bai ƙi ba, yaɗauko matarsa suka dawo,, tundaga kan Zahrah Malam Adamu da Zainab basu sake haihuwa ba, Zahrah tanada shekara huɗu Malam Adamu yasanyata amakarantar furamari (Primary) Zahrah yarinya ce mai hazaƙa sannan kanta yana ja sosai, kwanci tashi Zahrah ta kammala makarantar furamari (primary) ɗinta, bawani ɓata lokaci Malam Adamu yasama mata gurbin cigaba da karatu (Admission) a wata junior school dai dai da ƙarfinsa,, Zahrah na aji ɗaya a junior school, Mama (Zainab) takwanta rashin lafiya, abu kamar wasa hardai takaisu ga asibiti, kwanan mama ɗaya a asibiti Allah yayi mata rasuwa, kuka kam Zahrah da Malam Adamu sunsha shi, domin kuwa sunyi rashin jigon rayuwarsu, haƙiƙa Zahrah tayi rashin uwa ta gari, shiko Malam Adamu yayi rashin mace ta gari,, sati ɗaya da rasuwar Mama Malam Adamu yakwanta jinya, abu kamar wasa saigashi ko tashi baya iyawa, Wata rana ne aka wayi gari Malam Adamu baya numfashi, Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un !! Zahrah tayi kuka bana wasaba lokaci guda tayi rashin farincikin rayuwarta,,,,, koda Alhaji Umar yazo ta aziya, baiyi ƙasa a guiwaba, cewa yayi ya ɗauki nauyin karatun Zahrah harta ƙare jami'a, yayinda riƙon Zahrah yadawo wajen Hayatu da matarsa (Baffa, Inna) sam Zahrah batajin daɗin riƙon da Baffa da Inna keyi mata domin tsananin tsangwama suke nuna mata, gahi Baffa yahau kan ɗan gadon da Babanta ya bar mata yacinye,,, Ayanzu Zahrah tana da shekara 20 aduniya, kuma harzuwa yanzu Alhaji Umar ne ke ɗaukan nauyin karatunta.....
Cigaban Labari
Adai dai bakin titin yayi parking motarsa, domin sam shikam baijin cewa zai iya shiga, wannan unguwar talakawan da tsadaddiyar motarsa, shi sam baisan ma uban me yasa Bash yayi guest house ɗinsa a wannan unguwar ba,, zama yayi a cikin motarsa haɗe da ɗaukar wayarsa yadanna mawa lambar (Number) Bash ƙira, ringing biyu kawai wayar tayi Bash da ke kwance jikin wata ƴar iskan sa ya ɗaga,, "Ina bakin titi " yafaɗa a taƙaice haɗe da kashe wayar tasa,, baiwani ɗau lokaci ba saiga Bash ya ƙaraso,
"kaga *SHU'UMIN NAMIJI* maifirgita ƴan mata, Shu'umi mai sace zuciyar duk wacce yaso, ko shaiɗan yana tsoron shu'umancin ka !!" Bash yafaɗa dai dai lokacin dayakema kansa masauƙi acikin motar, ɓata fuska Zaid yayi haɗe da cewa " Kai ni duk ba wannan ba waishin meyasa ka tsalleki ko wani unguwa kazo nan kayi guest house ɗinka ?, ka duba fa gidajen area'nnan gaba ɗaya na talaka wane " Zaid yaƙare maganar yana maibin gidajen da kallon ƙyama,, murmushi Bash yayi haɗe da cewa
" Bazaka gane bane my man, amma wallahi ƴan mata nake samu a arean nan bana wasaba, kai bana ta ƙaice maka, yarinya sai ta kawomaka budurci (virginity) ɗinta a ɓagas, badon komai ba sai don tsananin talauci daya adda beta, yanzu haka akwai ƴan mata a ƙasa idan kana buƙata.." Bash yaƙare maganar yana murmushi mai ɗauke da nuna shi tantirin ɗan iska ne,,
taɓe baki Zaid yayi haɗe da cewa "Bazan iya iskanci da low class ba gaskia, kudai kuyita fama harku ɗaukomawa kanku wata cutar, yaƙare maganar yana ƴar dariyan mugunta,,
gyara zama Zaid yayi haɗe da cewa " Nazo maka da wani babban harka ne idan zakayi " shima Bash gyara zama yayi da kyau haɗe da cewa "Inajinka abokina "
Zaid ya buɗe baki zaiyi magana kenan idanunsa suka sauƙa akan wata kyakkyawar budurwa, wacce ke sanye da hijab iyaka guiwarta, hijab ɗin irin mai roba ɗinnan ne, hakan yasa ya bayyana duk wata sura na jikinta, wani irin abu Zaid yaji daga ƙasan ƙafarsa harzuwa cikin kansa, yayinda tsikar jikinsa yashuga zubawa, a hankali ya lumshe kyawawan idanunsa, da alokaci guda suka kaɗa sukai ja, koda yabuɗe su don sake kallon wannan halittar da'idanunsa sukai masa to zali da'ita, sai yaga saɓanin haka, domin ko a alamar gilma wanta baigani ba, saurin fita daga motar yayi haɗe da soma waige waige ko Allah zaisa yaganta, amma ko alamar ta bai gani ba........
(Tofa readers waishin wace budurwa ce Zaid ya gani ?)
*14/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Lovely Brother Khabeer*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*Chapter 7*
" Lafiya kuwa Zaid wakake nema ne ?" Bash yatambayeshi,, ɗan taɓe baki Zaid yayi haɗe da cewa " bakomai kawai ina duba yanayin unguwar ne " yaƙare maganar yana mai komawa cikin motarsa yazauna,,, sama sama Bash da Zaid sukayi magana, domin kwata kwata hankalin Zaid baya jikinsa, burinsa kawai shine idanunsa su sake yi masa to zali da wannar kyakkyawar fuska da jikin, daya gani.....
Tunda Zahrah tafito daga gidan su Husnah tafuskanci cewa da akwai mai binta a baya, hakan yasanya taji wani irin tsoro ya ɗarsu acikin zuciyarta, don haka ta ƙara ɗaga ƙafufunta, "Assalamu Alaikum !!" muryan Namiji mai cike da kamala ya doki dodon kunnuwanta, cak ta tsaya da tafiyan da takeyi batare da ta juyo ba,, cikin takunsa na burgewa ya ƙaraso gareta, kyakkyawan saurayi ne, mai ɗauke da launin fata choculate colour, dogo ne amma ba har canba, yanada faffaɗan jiki mai burgewa, sannan yana da kwarjini ba laifi,, murmushi yayi mata haɗe da cewa "Ƴan Mata bazaki amsa sallaman nawa bane ?" saurin sunkuyar da kanta ƙasa Zahrah tayi haɗe da cewa "Wa'alaikassalam"
Lumshe idanunsa yayi domin kuwa bakaɗan ba zazzaƙar muryarsa tadaki ƙahon zuciyarsa " Sunana JABEER, Idan bazaki damuba, inaso kibani adireshi'n gidanku, sai nazo, domin a matsayinki na mace mai mutumci baikamata natsaidaki a bakin hanya ba " Jabeer yafaɗa hakan yana mai kafeta da idanu,, gaba ɗaya kanta ɗaurewa yayi don haka, batare da tace dashi ƙala ba, tacigaba da tafiya, da sauri sauri,, roƙonta Jabeer yashiga yi akan ta tsaya ta saurareshi, amma ina Zahrah ƙara ɗaga ƙafanta tayi domin ita tsoro ma yabata, ganin da Jabeer yayi cewa bazata tsaya bane yasanya shi ƙyaleta kawai tayi tafiyarta, amma a zuciyarsa ya ƙudura aniyar nemota komai daren da ɗewa ..... Zahrah tana komawa cikin gida kaitsaye ɗakinta tawuce, ajiyar zuciya tashiga sauƙewa a kai akai tamkar wacce tayi gudu, idanunta da suke lumshe ta buɗe su ahankali, haɗe da da sanya harshenta ta lashi lips ɗinta na ƙasa, Allah yasani gayen ya burgeta amma kuma tanajin tsoro gaskia, domin bata saba tsayuwa da samari ba......
Birgima kawai yakeyi akan makeken gadonsa, kwana huɗu kenan daganinta amma da ya rumtse idanunsa, hoton kyakkyawar surarta yake gani, baisanta ba, baisan wacece itaba, amma wani irin sha'awarta yakeji, tabbas yazama masa dole komawa unguwar Suleja ko Allah zaisa yasake ganinta,, wayarsa dake ringing ne yakatse masa tunanin da yakeyi, DADY shine sunan dake yawo akan screen ɗin wayara, ɗaukar wayar yayi a kasalance haɗe da karawa akan kunnensa "To" kawai naji yace haɗe da cilli da wayartasa gefe, tashi yayi daga kwancen dayake haɗe da ɗaukan rigarsa yasanya, ya fice daga cikin ɗakin.....
Kai tsaye babban falon Dadyn nasa yanufa, can ya iske Dadyn nasa tare da Mom ɗinsa, zama yayi akan ɗaya daga cikin kujerun falon, fuskarnan tasa babu yabo ba fallasa, yace "Dady gani " Gyara zama Alhaji Ma'aruf yayi haɗe da cewa " Banaƙira ka bane don muyi dogon magana, naƙiraka ne don na sanar maka cewa zuwa yanzu yakamata ace kafitar da matar aure, kagama karatunka, ga kuɗinan kana samu ba'adadi, to mai yarage maka idan banda Aure Zaid ? a gaskia banajin daɗin zamanka haka ba aure, saboda haka kafito da matar aure "
" Yauwa gaya masa dai Alhaji, tunda ni nayi maganar har nagaji bai ɗauka ba, ga Khausar ɗiyar ƙanwata nan ma, sai ayi tuwona mai na " Mom tafaɗa tana murmushi,,,,
Dasauri Zaid yaɗago yakalli Mom ɗintasa, jin abun da take faɗa, wai Khausar, cab aiko mata sun ƙare a duniya bazai auri muciya da zani ba, yanda yasan mata ciki da bai, yana da tabbacin cewa Khausar tana ɗaya daga cikin irin matannan marassa ni'ima wanda idan kana sex dasu zakana jinsu kamar dusa, babu wani ɗanɗano,,
"Kayi shiru" Dad yakatsesa daga tunanin daya keyi,,
" ka ƙara bani lokaci Dad insha Allahu zan kawota nan bada jimawa ba, amma gaskia maganar Khausar Mom ki barshi, domin kwata kwata ni bana jinta acikin zuciyata " yana kaiwa nan a zancensa yasakai yafice daga cikin falon,, da idanu kawai Dad da Mom suka rakasa, har abada shidai Zaid bamai iya masa sai Allah, duk yanda ka ɓullo zaice ba haka ba.....
Koda yakoma ɗakinsa wanka yayi, haɗe da ficewa daga cikin gidan baki ɗaya,, baizarce ko'inaba sai babban gidan giya dake Abuja, can yaje yacika cikinsa yayi tatul, daganan yasamu abokiyar shaiɗanansa, suka yi watsewarsu.....
Zahrah sunfara Exam, don haka tuni kanta yaɗau zafi, karatu kawai takeyi baji ba gani, cikin ikon Allah kuwa komai nata yana tafiya adai dai, domin dai tana sa ran cewa zata samu kyakkyawan sakamako,,,
Hadari ne yahaɗu sosai acikin garin, yayinda sama tayi baƙi, ruwa ake tsammata yanzu ko anjima, yau amakare suka fito da ga exam, duk yanda Husnah taso Zahrah tashiga su rage mata hanya ƙiyawa tayi dole yasa Husnah ta ƙyaleta, tana fitowa daga cikin makaranta, ruwa ya ɓarke tamkar dama jira ake tafito, duk adaidaita sahun da Zahrah tatare baya tsayuwa, domin ruwan ƙara ƙarfi yake, jikin wata bishiya Zahrah ta lafe, duk da kuwa cewa ruwan baifasa dukanta ba, gaba ɗaya jikinta ya jiƙe jagwab, ba abun da kayanta suke sai ɗigan ruwa, rigace irin rover gown ɗinnan ajikinta, saikuma rover hijab da taɗaura akan rigan, sanadin jiƙewan da sukayi yasanya, kayan lafewa acikin jikinta, take komai najikinta ya bayyana, hatta shatin breast ɗinta saida yabayyana, domin rigar ce kaɗai ajikinta, batasa breziya ba,, abu kamar wasa haka aka share 1 hour ana tafka ruwan sama, gashi duk bayan minti ɗaya dare ƙarayi yake, sanin cewa tsayuwarta a wajen kan iya haifar mata da matsala, yasanya ta shiga tafiya a cikin ruwan duk da cewa bata ko iya ganin gabanta,, gudu kawai yake shararawa akan titin batare da yayi tunanin komaiba, daidai Zahrah tahau kan tsakiyar titin, dai dai shikuma yaƙaraso wajen,,, wani irin burki Zaid yataka da ƙarfin tsiya, domin ƙiris yarage yabita kanta,, Zahrah kuwa tsabar firgici kasa motsawa tayi daga wajen, hannayenta taɗaura akan kunnenta haɗe da rumtse idanunta gam,, tundaga ƙasanta yasoma kallonta harzuwa samanta, saurin rumtse idanunsa yayi alokcin da idanunsa suka hasko masa shatin nipples ɗinta daya bayyana tacikin hijabinta, " wayyo Allah na !!" yafaɗa a hankali, yayinda ya sanya hanunsa yariƙe bananarsa da alokaci guda tayi wani irin harbawa,, cikin rashin ƙarfin jiki da kuzari yafito daga cikin motar haɗe da nufar inda take,, kallon fuskarta yashiga yi, jin hucin numfashin mutum akusa da'ita yasanyata buɗe idanunta ahankali, sake waro idanunta tayi domin ganemawa kanta shin abun data gani gaskiya ne ko ƙarya, kyakkyawar fuskarsa tashiga ƙaremawa kallo, tamkar taga baƙon halitta, waishin aljanine ko mutum ? tatambayi zuciyarta, kallon kallo Zaid da Zahrah suka shiga yimawa juna, yayinda ruwan sama keta dukansu, tsareshi tayi da idanunta, bata ko ƙyaftawa, ahankali yakai hanunsa zuwa kan fuskarta yashafa kumatunta, saurin ja da baya Zahrah tayi, haɗe da ƙwalalo idanunta waje, abun da wani ɗa namiji baitaɓa yi mata ba aduniya kenan wato taɓa jikinta, saidai ko muharraminta,, wani irin munafukin murmushi daya ƙawata zallan kyauwunsa yayi haɗe da komawa cikin motarsa yazauna, ƙofan dake gefen mai zaman banza ya buɗe, haɗe dayi mata nuni da hanunsa alamar tashigo, tsoro ne yakama Zahrah, amma tabbas bata da wani dama dayawuce tashiga motar tasa, domin idan ta tsaya tofa saidai ta bushe amma bazata samu abun hawaba gashi dare sai ƙarayi yake,, sumi sumi haka tashige cikin motar tazauna haɗe da takure jikinta waje ɗaya,, kallonta yayi tagefen ido haɗe dayi mawa motar tasa key, batare daya ce da'ita ƙalaba suka soma tafiya,, cike da tsananin mamaki take kallonsa ganin da tayi kaitsaye yanufi hanyar Suleja da'ita batare da ya tambayeta ba, saida suka kawo daidai inda yataɓa ganinta kafun yayi parking motar tasa haɗe da juyo da kallonsa gareta wani irin shu'umin kallo yajefeta dashi haɗe da cewa " inane gidan ?" kasa amsa masa tayi saima baki da tasake tana kallonsa kamar tasamu statue (gunki), a hankali ya hura mata iskan bakinsa akan fuskarta, take tayi saurin kawar da kanta gefe, "kabarni anan ma ya'isa nagode " tafaɗa a taƙaice haɗe da yunƙurin fita daga cikin motar, saurin riƙo hanunta yayi haɗe da cewa "Kifaɗamin inane gidan ?" yayi maganar cikin wata irin cool voice maisanya nutsuwa,, "kwanancan ne " tabasa amsa a taƙaice,,, a dai dai ƙofar gidan su yayi parking motar tasa, saurin buɗe murfin motar Zahrah tayi haɗe da ficewa, hartana jin tuntuɓe wajen shiga gida, tsabar sauri,, wani irin murmushi Zaid yayi, haɗe da fito da harshensa ya lashe pink ɗin laɓɓansa, "Sugar Baby !!" yafaɗa in a low voice, yakai kusan 2 minutes aƙofar gidan kafun yaja motarsa yatafi.......
*15/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Lovely Brother Khabeer*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*Chapter 8 то 9*
Koda Zahrah tashiga gida bata iske kowa a tsakiyar gidan ba, don haka kai tsaye ɗakinta tawuce, kayanta dake ɗigan ruwa ta cire haɗe da ɗaura zani a ƙirjinta, fita tayi ta shanya jiƙaƙƙun kayan nata akan igiya, kana ta dawo ɗaki, wata doguwar riga mai kauri tasanya domin sosai takejin sanyi a cikin jikinta, zama tayi akan katifarta haɗe da lumshe idanu, saurin ware idanunta tayi, alokaci guda, bakomai yasa hakanba kuma face, kyakkyawar fuskar mutumin ɗazu dake yi mata gizo acikin idanunta, tsikar jikinta ne yashiga zubawa, sakamakon tunowa da yanayinsu naɗazu da tayi, "Yanada kyau !!" tafaɗi maganar a fili, amma anya ba gamo kikayiba kuwa Zahrah ?" zuciyarta taje fomata wannan tambayar, take kuma tsoro yashiga zuciyar Zahrah saikuma tafara addu'a idan Aljani ne ma Allah yarabata da sharrinsa.....
Zaid kuwa daga gidansu Zahrah nasu gidan yayi, koda yacire kayan dake jikinsa kwanciya yayi luf akan makeken gadonsa, yanamai sauƙe ajiyar zuciya, lallai yau yayi gamo da gamdakatar, ashe gaskia Bash keyi da ya ce masa a area'n akwai kyawawan ƴan mata, saidai a yanda ya fuskanta ita ɗin ba ƴar hannu bace, domin ya hango hakan acikin idanunta,, murmushi mai sauti Zaid yayi haɗe da cewa "Kisaurari dawowana gareki My Sugar Baby !!".....
Bayan Sati Ɗaya da haɗuwan Zahrah da Zaid....
Tun randa Zahrah ta haɗu da wannan haɗaɗɗen gayen hankalinta ya kasa kwanciya, ko kwanciya bacci tayi, to fa shike zuwa mata a mafarkinta, dazaran tarufe idanunta kuwa kyakkyawan murmushinsa take gani, duk yanda taso yakice tunaninsa acikin zuciyarta hakan yacitura, saidai ako dayaushe tana mai gargaɗin zuciyarta da ta tsaya a iya matsayinta, kada ta haura matsayin da bata can can ci zuwa ba..
Ɓangaren Zaid kuwa iskancinsa yake bugawa son ransa, zina ƙara yaɗuwa takeyi a cikin jini da zuciyarsa,, yau yashirya cewa zaikai mawa Sugar Baby ɗinsa ziyara,,
Tsab yashirya kansa cikin wasu irin tsadaddun riga da wando, na blue jeans, bakaɗan ba kayan suka amshi kyakkyawan jikin Zaid, yayinda tulin gashin kansa yasha gyara sai sheƙi yake, agogon rolex ya ɗaura akan tsintsiyar hanunsa, haɗi da baɗe jikinsa da shu'umin turarensa mai rikirkita ƴan mata,, haƙiƙa Zaid yana da kyau mai burgewa, Zaid haɗaɗɗen Namiji ne wanda kowacce mace idan tagansa saita ƙyasa, bazan iya misalta muku haɗuwar Zaid ba amma Zaid ya wuce duk inda kuke tunani,ga kuɗi ga kyau, shiyasa yake abun da yakeso,,, car key ɗinsa ya ɗauka haɗe da ficewa daga cikin ɗakin,, kaitsaye parking space ɗinsa ya nufa, haɗaɗɗiyar motarsa ƙirar Range Rover blue colour yashiga haɗe da bata wuta yafice daga cikin gidan,, yana tuƙi amma earpiece ne sanye a kunnensa yanashan ƙiɗa, kai tsaye Unguwar Suleja yanufa,,
Zahrah ce zaune a tsakar gida, tana wanke mawa inna kayanta, sanye take da wata atamfa irin mai sauƙin kuɗinnan amma, duk da haka atamfar tayi mata kyau ajiki, Inna kuwa nagefe akishingiɗe tana sana'artata cin goro,, wani yaro ne yashigo cikin gidan bakinsa ɗauke da sallama, Zahrah ce ta amsa masa Inna kuwa ko kallonsa batayi ba, domin a tunaninta baraka dake binta bashine ta aiko mata,, " Wai Zahrah tazo inji wani a waje " yaron yafaɗa, zuciyar Zahrah ce tayi wani irin tsalle tamkar zata fito waje, yayinda inna dake kishingiɗe tamiƙe zumbur haɗe da cewa " Zahrah kuma ? kai yaro anya kaji da kyau kuwa ?" kai yaron yagyaɗa haɗe da cewa "Eh wani ne yace inkirata, kuma Zahrah yacemin,,
"Wanin dame yazo? a tsaye kagansa ? koko amashin ? kokuma dai amota ? yaro faɗamin da maiyazo ? " Inna ta tambayi yaron,, "Awata irin ƙatuwar mota yazo mai kyau " yaron yafaɗa, domin shidai abun daya gani zai faɗa,,
"hehehhe ! jekace tana zuwa ɗan yaro " Inna tafaɗa tana mai tashi tsaye, "To" kawai yaron yace haɗe da juyawa yafice daga cikin gidan,,
"Tashi maza maza kije kada ki ɓarar mana,, banza kinaji ana ƙiranki amma kinwani shantakewa a waje ɗaya " Inna tafaɗa tana mai hararan Zahrah, da take ƙame a waje ɗaya, gaba ɗaya hankalinta baya jikinta.... hijabinta dake rataye kan igiya tasanya haɗe da nufar ƙofar fita daga gidan cikin sanyin jiki,,, tana fitowa daga cikin gidan yakafeta da mayun idanunsa, haɗe da sanya harshensa ya lashi laɓɓansa, Zahrah kuwa ganin bataga kowa awajen ba sai mota yasanya ta juyawa daniyar komawa gida, *"ZAHRAH"* taji ankirasunanta da wani irin murya wanda bazata taɓa manta ta ba duk da kuwa cewa sau ɗaya tak ta taɓa jin muryar a rayuwarta,, saurin juyowa tayi don taga daga ina muryar tafito, daidai lokacin ya sauƙe glass ɗin window'n motar, idanunta sukai mata tozali da kyakkyawar fuskarsa wanda bazata taɓa mantashi ba har abada kuwa,, wannan shu'umin murmushin nasa ya yi mata haɗe da cewa " shigo mana, kodai tsorona kikeji ne ? " a hankali ta sauƙe idanunta daga kansa haɗe da kaɗa kanta alamar a'a, amma still tana tsaye bata shiga motar tasa ba, wani murmushin yakuma aika mata haɗe da buɗe murfin motar tasa yafito, saida yazo gab da'ita kafun yatsaya haɗe da sanya hanunsa yaɗago haɓarta, wanda hakan yasanya ta jefa idanunta cikin nasa, " Haka kikafiso ko ? kowa yazo wucewa yaganmu tsaye ?" yaƙare maganar yana mai rage girman idanunsa,, wani irin zubawa tsikar jikin Zahrah ya shiga yi, saurin ja da baya tayi domin kusancin nasu yayi yawa,, batare daya sake ce da'ita komaiba yajuya yashige cikin motarsa, haɗe da buɗe mata ƙofar mai zaman banza, cikin sanyin jiki Zahrah tashiga cikin motar amma bata rufe ƙofar motar ba, saishi ne ya jawo ƙofar yarufe da kanshi, kallonta Zaid yashigayi harnatsawon minti biyu kafun yayi murmushi, haɗe da cewa "Baki iya gaisuwa ba ne ?" wani irin kunya ne yakama Zahrah kwata kwata ita tama manta da ana gaisuwa, gaba ɗaya ganinsa ya ruɗata,, "Inawuni " tafaɗa cikin sassanyar muryarta,, "bani amsawa saida ma na roƙa " yafaɗa yana ɗan hararanta, ɗan guntun murmushi kawai tayi haɗe da sake sunkuyar da kanta ƙasa, tanamai wasa da yatsun hanunta, "Zahrah!!" yasake ƙiran sunanta cikin kasalalliyar murya, kasa amsawa Zahrah tayi saima ɗago kanta da tayi taɗan saci kallonsa, haɗa idon da sukayi yasa tayi saurin maida kanta ƙasa,, "Bakiyi mamakin zuwa na ba ?" yajefo mata tambaya, alokacin da bata shirya ba, da ƙyar ta'iya cewa "nayi" satan kallonsa tayi ta gefen ido, "Idan namiki kyau ne kijuyo kikalleni da kyau, bawai ki tsaya kina satar kallo naba, yafaɗi maganar kaitsaye, wani irin kunyane yakama Zahrah sam batasan cewa yana ankare da'ita ba, da sauri ta cusa kanta tsakankanun cinyoyinta, haɗe da ɓoye fuskarta, gyara zama Zaid yayi haɗe da cewa " dama nazo na ganki ne, kuma naganki zaki iya tafiya tunda kunyana ma kikeji " yafaɗi maganar ataƙaice, ahankali tabuɗe murfin motar da sauri tafice bata ko waigo tasake kallon sa ba, tashige cikin gida,, yana ganin wucewarta cikin gida, yasauƙe ajiyar zuciya haɗe da sakin ɗan guntun murmushi, "da sannu zaki shigo hannu " yafaɗa acikin zuciyarsa, wani yaro dayake wucewa yaƙira haɗe da basa wata ƙatuwar leda yace yakai gidan su Zahrah'n, daganan yayi mawa motarsa key yabar cikin unguwar tasu,
Zahrah nashiga gida yaro yabiyota da ƙatuwar leda, "wai inji wani a waje" har Inna najin tuntuɓe wajen ƙwatan ledan ahanun yaron, "to, to,to kace angode ko yaro" Inna tafaɗa tana washe baki, yaron baice da'ita ƙalaba yafice da ga cikin gidan,, zama Inna tayi akan tabarma haɗe da zazzage ledan, kayane suka soma faɗuwa acikin ledan saikuma bandir ɗin kuɗi ƴan dubu dubu ɗauri ɗaya daya faɗo, waro idanu Inna tayi haɗe da dafe ƙirji, afili tace " Nashiga Uku ni Salma mainake gani haka, ke Zahrah ɗan fashi, ko ɗan yankan kai, kika jajiɓo mana? " Zahrah dake ɗaki jin abun da Inna kecewa yasa tayi saurin fitowa danganin meke faruwa,, turus itama tayi domin ganin abun dake zube agaban Inna, ɗaukan kuɗin Inna tayi tashiga juyawa, haɗe da washe baki, "Lallai ko ma waye ne wannan mutumin dayazo wajenki Zahrah baƙaramin mai kuɗi bane " Inna tayi maganar tana mai shunshina kuɗin hanunta, saurin cusa kuɗin tayi aƙasan ƙugunta, haɗe da soma juya kayan dake zube gabanta, dogin riguna ne ƴan ubansu kala uku sai lufayu, guda uku, dagani kai kasan masu tsadan gaske ne, kuɗin Inna taciro tasoma irgasu, dan tsabar naci saida Inna ta irge kuɗinnan tas dubu ɗari ne cus, dafe ƙirji Inna tayi cike da tsananin mamaki tace " Dubu ɗari awannan zamanin ? lallai ne inji masu faɗi sukace
arziki na'inda yake, aikuwa yau miyar zallan nama zamuci acikin gidannan, Allah yakashe ya bamu, ke Zahrah tsayuwan mekike ? maza ɗauko hijabinki kijemini bakin hanya nan kisayo mini ɗanyen nama da kuma danƙwaleliyar kaza ƴar gashi, yau bushasha zanyi " Inna taƙare maganar cike da farinciki, haɗe da wurgi da guntun goton dake hanunta,, cikin sanyin jiki Zahrah takoma ɗaki taɗauko hijabinta, kuɗi takarɓa a wajen Inna, kai tsaye tawuce aikan da Innan tayi mata, zuciyarta fal da tarin tambayoyi haɗe da tunani.....
Zaid kuwa daga wajen Zahrah guest house ɗinsa ya wuce, bayan yabiya yaɗauko sabuwar karuwarsa da yayi, maisuna Laylerh,,
Gaba ɗaya Zaid ya ruɗe ganin da yayi mawa Lylerh tsaye a gabansa tsirara haihuwar uwarta, saiwani banƙaro masa ƙirji takeyi, duk don ta ɗauke hankalinsa, duk dacewa ba irin macen da bai gani ba, amma Lylerh ta ɗan rikitasa, domin ta nada abun dayake so sosai ajikin mace wato breast, shi namiji ne mai son breast sosai, madaran holandia dake riƙe ahanunsa, yashiga zuba mata akan nonuwanta harzuwa ƙafanta,, bakinsa ya ɗaura akan nononta yashiga tsotson su haɗi da lashesu, yayinda yazura yatsansa ta ƙasanta, yana mai wasa da gabanta, a hankali, babu inda Zaid baibi yasuɗe ajikin Lylerh ba, cikin zafi zafi yake murza breast ɗinta, hanunsa kuwa yajima da nutsewa aƙasanta, duk kuwa yanda Lylerh taso su haɗa baki da Zaid yayi kissing ɗinta ƙiyawa yayi, sai dai yayi romance ɗinta yadda yaka mata, kwantar da'ita yayi flat akan gado, yayinda ya haye saman ruwan cikinta hannayensa yakuma ɗaurawa akan breast ɗinta yashiga murzawa, yayinda ya shiga goga bananarsa a dai dai wajen fitsarinta,, wani irin shishita Lylerh keyi domin ko ahaka Zaid ya barta ta gamsu, cike da ƙwarewa Zaid ke sanya bananarsa cikin HQ ɗin Lylerh, saida yatabbatar dacewa tanutse ciki kafun yasoma aiki, gaba ɗayansu hankalinsu baya jikinsu, domin sunyi nisa wajen aikata zina,,, balaifi Zaid yasamu gansuwa da Lylerh, domin dai Lylerh ta tsuma kanta da maganin mata yanda yakamata,, kuɗi masu yawan gaske Zaid yabamawa Lylerh, amatsayin ladan iskancin da yayi da'ita, duk da cewa itaɗin ba gadon tsiya bace, domin Babanta mai kuɗi ne sosai.....
*16/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Lovely Brother Khabeer*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
(```kuyi haƙuri two days kunjini shiru, abubuwane sukai min yawa..```)
*Chapter 10 то 11*
Zahrah ce kwance a ɗaki, bayan ta dawo daga aikan da Inna tayi mata,, zuciyarta cike take da saƙe saƙe kala kala, na farko tanason sanin wayeshi, maikuma yakawosa gidansu, haƙiƙa tasan cewa ya girmewa ajinta, amma sai gashi zuciyarta ta maƙale da tunaninsa, duk yanda taso manta shi a cikin zuciyarta hakan yagagara, amma cire tunaninsa acikin zuciyarta yazama dole, domin kuwa hanyar jirgi da ban, ta mota ma da ban,,,, a ranan nan da ƙyar bacci ɓarawo yayi awun gaba da Zahrah, dazaran ta kulle idanunta, kyakkyawan murmushin sa ne ke yi mata gizo....
Yau tana ƙirga wa kwanansa shida kenan dazuwa wajenta, amma har izuwa yau ɗin tunaninsa yakasa barinta tayi sukuni, bakomai yafi ɗaukar hankalinta a tattare da shiba kamar ƙawataccen murmushinsa mai burgewa, (Murmushin shu'umanci) uwa uba kwarjininsa yana ruɗata, wani irin son sake ganinsa takeyi...
A ɓangaren Zaid kuwa abubuwane sukai masa yawa, yayinda hankalinsa ya karkata zuwaga harkan kasuwancin sa, kwata kwata baya samun zama, amma komai yake Zahrah na maƙale a ransa, burinsa ɗaya shine Allah yakai damo ga harawa, ko baici ba yayi birgima, har ya hasasho, yanda zai keta mawa Zahrah rigar budurcinta, tun da yaganta yayi rantsuwa, cewa sai ya ɗanɗani zumanta, kuma bazai bar rantsuwarsa yatafi a banza ba...
Zahrah na zaune a tsakar gida, idanunta kekan handout ɗin dake riƙe a hanunta,, idan kayi mata kallon farko zakai zaton karatu takeyi, amma idan kakuma kallonta, to akasin haka zaka gani, domin gaba ɗaya hankali da tunanin ta ya tafi ga Zaid ya hanata sakat, karatun ma bako da yaushe yake shiga kanta ba,, wani yaro ne yashigo cikin gidan bakinsa ɗauke da sallama, Inna ce tayi saurin amsa masa, "Wai ana ƙiran Zahrah a waje " yaron yafaɗa, baki Inna ta washe haɗe da cewa "ɗan albarkan nanne yazo na sani, je kace gatanan fitowa yanzu yanzun nan " wani irin bugawa zuciyar Zahrah tayi, hakanan ta tsinci kanta da faɗuwar gaba, take kuma taji zuciyarta tayi sanyi,, lufayan da Inna ke miƙo mata ta amsa haɗe da zurawa ajikinta, kaitsaye tafice daga cikin gidan,,,
Tsaye yake a jikin motarsa yasha ado cikin wata blue shadda, sosai kayan yayi masa kyau, domin kuwa shiɗin ma ba baya bane wajen kyau,, turus haka Zahrah taja ta tsaya, ganin wata baƙuwar fuska ba wacce take tsammani ba,, murmushi yayi mata haɗe da yi mata nuni almar ta ƙaraso,, gaba ɗaya jitayi farincikinta ya gushe, sam bashi taso gani ba, taso ace Mai kyau (Zaid) ɗinta ta gani,, cikin sanyin jiki ta ƙaraso inda yake haɗe dayi masa sallama,, amsa sallamar nata yayi fuskarsa cike da fari'a,, sake gyara tsayuwa Jabeer yayi haɗe da cewa " kiyi haƙuri a wancan lokacin na tsaidaki a'inda bai dace ba, amma yanzu gani nabiyoki har gida, ina fata zakiyi marhaba da zuwana "
Ɗan jim Zahrah tayi, domin ita bata da wani amsa da zata basa, ganin haka yasanya Jabeer ci gaba da cewa " kamar yanda na faɗamiki a farko ni sunana Jabeer, ina zaune ne a unguwar asokoro nida mahaifana, ni ma aikacik banki ne,, tun daga randa na fara ganinki na ji na kamu da soyayyarki, idan har bazan takuraki ba inaso kibani dama don gwada sa'ata agareki... " Jabeer yaƙare maganar yanamai kallon Zahrah, ɗan jim Zahrah tayi kamar wata mai nazari, ita dai batasan maizatace dashi ba, domin ita bata taɓa soyayya ba, kuma ita batama jisa acikin zuciyarta ba,,, ganin bazatace komai ba yasa Jabeer cigaba da yi mata bayanin kansa, haɗe da ƙoƙarin kafa gwamnatin sa wajen ta,, daga ƙarshe dai cewa tayi yabata dama tayi tunani,, yakoji daɗin hakan domin yanasa ran cewa zai samu karɓuwa a wajenta,,,, koda tazo tafiya maƙudan kuɗaɗe ya bata, amma sam Zahrah taƙi amsa, bayanda baiyi da'ita ba akan ta amsa amma taƙi, dole ya haƙura, saida yaga shigewarta gida kafun yayi mawa motarsa key yafice a unguwar tasu baki ɗaya........
Zahrah nashiga gida Inna tayo kanta tana mai cewa " Mai arzikin nan ne ko ? bansan a'ina kika samosa ba,amma gaskia banaso ya kuɓuce mana, saboda haka kiriƙesa da kyau "
cikin sanyin Murya Zahrah tace "Bashi bane Inna, wani ne daban" wata uwar harara Inna ta doka mawa Zahrah haɗe da cewa "to idan bashi bane wani ɗan iskan ne ? nifa kinganni nan banson harka da talakawa, domin a gaskia bazan ƙare rayuwata cikin talauci ba ehe, in ma baƙin ciki ne yasa kika kori mai arzikinnan to yazama dole ki bashi haƙuri ya dawo, kam bala'i ga samu gakuma rashi, ina bazai yi wuba, shi wannan ɗin a mai yazo ba dai a ƙafa ba ?"
"a mota" Zahrah tayi maganar kai tsaye, sam batajin daɗin abun da Inna keyi, shigewa ɗakinta tayi, yayinda tabar Inna tsaye tana faman ɓaɓatu ita kaɗai a tsakar gida....
Jigum tayi, zuciyarta cike da tarin tunani kala kala, "Bazai zo ba, dama nasan ya girmewa ajini, mai yasa nadamu dashi ? maiyasa nake yawan tunasa akowani lokaci ? maiyasa zuciyata keson jefa kanta inda bata dace da zuwa ba ? yazama dole na daina tunasa kwata kwata a rayuwata, to amma yazanyi da wannan daya kawomin tallen soyayarsa gareni ? " Zahrah tayi maganar a fili,, haka dai Zahrah tayi ta saƙe saƙe acikin zuciyarta...
Bayan Kwana biyu da zuwan Jabeer....
Misalin ƙarfe 8:30 pm, Zahrah ce kwance akan ƴar yalolon katifarta, yayinda idanunta ke lumshe, da'alama bacci keson ɗaukarta.... Shigowar Inna da sauri cikin ɗakinnata shiya sanya tayi saurin buɗe idanuwanta, domin shigowar Inna ɗakinnata a dai dai wannan lokacin bainuna alamar lafiya.... " Miye kika wani zura min idanu kamar mayya, tashi kije waje wannan mai arzikinne yakuma da wo wa " Inna ta faɗa cike da zumuɗi,, dumm haka ƙirjin Zahrah ya buga,, ganin Zahrah tayi saƙare yasa Inna, cewa "zaki tashi kijene kokuwa saina mangareki " sumi sumi Zahrah tamiƙe haɗe da ɗaukar hijabinta tana ƙoƙarin sanyawa a jikinta,, saurin fusge lufayar Inna tayi haɗe da wurgi dashi gefe, wani gyale dake hanunta, ta miƙomawa Zahrah'n haɗe da cewa " ungo yafa wannan banson wannan shirmen koda yaushe kina nanuƙe da lufaya kamar wata mayya !" badon Zahrah taso ba haka ta yafa gyalen da Inna ke miƙomata, har zaure Inna ta raka Zahrah, saida taga ficewarta kafun ta koma gida,, kasancewar gari gaba ɗaya yayi duhu hakan yasa bata iya hango wanda ke cikin motar, kuma zuciyarta bata bata akan cewa shiɗinne ba, saboda ba motar da yazo da'ita ranan bane watace daban,, don haka tafara zaton ko bashi bane,, wani irin daddaɗan ƙamshine yashiga yawo acikin ƙofofin hancinta, kallonta ta maida izuwa inda ƙamshin ke fitowa, mutum ne tsaye a wajen amma bazata iya shaida ko waye bane, saboda duhu,, wani irin tsoro taji yakamata kaddai mai satan mutanene yabiyota har gida, da sauri tajuya don komawa gida, taku ɗaya yayi kacal, ya cafko hanunta, wanda hakan ya haifar masa da zubawar tsikar jiki,, jawota yayi gab dashi, cikin wata irin murya yace " Shiiii idan kikayi magana saina yankaki !" jikin Zahrah ne yaɗauki rawa haɗe da ɓari, tsoro ne ya lulluɓeta a sakamakon jin abun daya ke faɗi, shikenan itakam Inna tajawo mata, tana zaman zamanta ta tilasta mata fitowa gashi wani zai yi garkuwa da'ita,, babban abun daya da gulamata lissafi, bai wuce yanda jikinsa da nata ke manne awaje guda ba, ga ƙamshin sa gaba ɗaya yagama rikitata,, a hankali ya ɗaura kansa a gefen wuyanta, wanda hakan yasanya tattausan sajensa gogar fatar wuyanta, lumshe idanunsa yayi haɗe da buɗesu a lokaci guda, " Kinshirya mutuwa yanzu kokuwa ?" yaje fo mata tambayar data kusa tsinka ƴaƴan hanjinta,, cikin rawan murya tace "dan Allah kayi haƙuri kada ka cutar dani wallahi ni marainiya ce, da Allah kaɗai na dogara " tuni hawaye sun wanke kan fuskarta, wata irin dariya Zaid yayi mai cike da mugunta, hannayensa yasanya duka biyu ya juyo da'ita gabansa, yazamana suna faced ɗin juna, wayarsa ya dannan take hasken tocila (torch light) yabayyana, rufe idanunsa yayi haɗe da kai hasken tocilan kan fuskarsa, cikin mayaudariyar murya yace " fatan baki manta da wannan fuskar ba" sai a lokacin Zahrah taɗago idanunta ta sauƙesu akan kyakkyawar fuskar Zaid, wata irin ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya ta sauƙe, haɗe da yin hamdala acikin zuciyarta,, wani irin ƙawataccen murmushi Zaid yayi mata, haɗe da kashe mata idonsa ɗaya, " matsoraciya " yafaɗa cikin murya mai sanyi,, hararan wasa Zahrah tayi masa haɗe da cewa "ko wama matsoraci ne idan har yaga mutuwa " murmushi Zaid yayi haɗe dayi mata wani irin kallo, mai ɗauke da ma'anoni dayawa, wani irin yawu ya haɗiye alokacin da idanunsa suka sauƙa kan cikakkun breast ɗinta... "Muje mota" yayi maganar yana mai nufar inda motarsa ke fake,, bamusu itama ta biyo bayansa,, kan kujeran mai zaman banza ta zauna, haɗe da takure jikinta waje ɗaya, sam itakam sa gyale bawai yawani damunta bane, tafiso koda yaushe tazamana cikin hijabi, domin yana kare mata tsiraicinta, gashi yanzu duk ta takura kowani motsi tayi sai surarta ya bayyana,, "Yauma bazaki gaisheni bako ?" Zaid yafaɗa daidai sanda yajefa wani sweet cikin bakinsa,, sunkuyar da kanta ƙasa tayi cike da kunya, itakam balaifinta bane, i dan ta gansa ne komai ke kuncemata,, kallonta yayi ta gefen idanunsa haɗe da cewa " kinsan maiya kawoni unguwarku yau ?" "A'a" tabasa amsa a taƙaice,, "SOYAYYA !!" yafaɗa cikin wata irin murya mai ɗauke da shauƙi,, "Soyayya kuma ?" Zahrah tatambaya domin sam bata fahimci inda kalamannasa suka dosa ba,, "INASONKI ZAHRAH !!" Zaid yafaɗi maganar yana mai kafeta da idanunsa, cikin tsananin mamaki Zahrah ke kallon Zaid, ko da wasa bata taɓa zaton zaiyi mata maganar soyayya anan kusaba, "Kinyi shiru sanar dani idan kinasona " Zaid yafaɗa yana mai kama hannayenta yashiga murzawa a hankali,, wasu irin ƙwallane suka shiga gangarowa daga cikin idanunta zuwa kan fuskarta, " kada ka yaudareni, ni macece mai rauni da kuma naƙasu, kaduba gidanmu, kaduba irin shigar dake jikina, ka dubi kanka kasan cewa nidakai ba ɗaya bane, akwai tazara mai tarin yawa a tsakaninmu, ban taɓa soyayya ba, bakuma naso nafara soyayya a'inda zuciyata zata wahalta, don Allah kajanye maganar soyayyata a gareka, domin nida kai bamu daceba " tuni hawaye sungama wanke fuskarta,, murmushi Zaid yayi haɗe da cewa "Ba labari nake baki ba, saboda haka ki farka daga baccin dakike, nabaki nan da 3 days ki koyamawa zuciyarki soyayyata, zan aureki idan har kin amince da hakan, bana buƙatar da cewar mu ko rashin sa,, ungo wannan idan kin koma ki kunnata saboda zan iya nemanki koda yaushe " yaƙare maganar yana miƙomata wata leda dake hanunsa,, kai tagirgiza alamar bazata karɓa ba, take yaɓata ransa, wanda hakan yasa taji ba daɗi, haka dolenta ta karɓa,, saida safe tayi masa, kana ta shige cikin gida,, tana shigewa shima ya ta da motarsa yayi gaba...
Tana shiga cikin gida Inna tayi yo kanta tana washe baki, sakamakon ganin leda da tayi ahanun Zahrah, wafcar ledan Inna tayi haɗe da cewa "ɗan albarka yaukuma mai yakawo mana ?" kwalin danƙareriyar iphone 11 pro max Inna tafara cirowa, a je kwalin tayi a gefe haɗe da zazzage ledan a ƙasa, kayan snacks dasu choculate ne suka zubo, saikuma mai gayya mai aiki wato farare bugun Abuja, dariya Inna tayi haɗe da buga shewa, itakam Allah yakashe ya bata, lokacin yin arzikinta yayi,, jin shewan Inna yasa Baffa dake cikin ɗaki fitowa, "lafiya kuwa.... " kasa ƙare maganar Baffa yayi sakamakon tozali da kuɗaɗen da ke gaban Inna da yayi........
(Readers maikuke tunanin zai wakana tsakanin Zaid da Zahrah ? Zahrah zata amince da soyayyar Zaid kuwa ? kokuwa zata ɗauki Jabeer ne tabar Zaid ? kuci gaba da bibiyata don sanin mai zai faru anan gaba...)
*19/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Lovely Brother Khabeer*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*Chapter 12*
*( INA MAI BAKU HAƘURI DOMIN KUWA KWANA BIYU, ZAKUJINI SHIRU BA NEW UPDATE, WATA ƘILA NAYI 1 WEEK BANYI TYPING BA, WATAƘILA KUMA BAZAN KAI HAKANBA, HAKAN YAFARU NE SABODA WANI DALILI NAWA, INSHA ALLAH AMMA ZAKUCI GABA DA JINA IDAN KOMAI YA DAI DAI TA, NAGODE....)*
*Kuɗanyi manage da wannan 👇🏼*
Kasa ƙare maganar Baffa yayi sakamakon tozali da kuɗaɗen dake gaban Inna da yayi, cike da tuhuma yake kallon Inna yamakasa ce da'ita komai, ganin haka yasa Inna ta washe baki, haɗe da soma tattare maƙudan kuɗaɗen, cikin hanzari Baffa yasanya hannayensa duka biyu ya wawashi kuɗin, haɗe da cusawa cikin aljihunsa, da sauri Inna tayo kansa tana muzurai, haɗe da cewa "Haba Malam yazakayi haka, aidai katsaya nayi maka bayani kafun ka kwasa rabonka ko" harara Baffa ya watsamawa Inna haɗe da taɓe baki yace " ba abun da bansani ba, nasan duk wani abu dakike shiryawa, kuma wallahi daga yau idan aka sake kawo kuɗi cikin gidannan ba ki jira dawowata munraba ba, ninasan matakin da zan ɗauka, yarinyace dai ƴar wa na ne, don haka babu wanda ya'isa ya gwadamin iko da'ita, kuma shima saurayin zaizo yasameni haka ake zuwa hira babu wani tambayar izini ba komai" Baffa yaƙare maganar yana mai nufar ƙofar fita daga gidan, yana fita Inna ta buga tsuka haɗe da cewa " shikenan kuma ae tunda yagano abun danake shiryawa, bazai taɓa barina naci arziki ni ɗaya ba, mcheeew !" taƙare maganar tana mai tattare ƴan ragowan kuɗaɗen da Baffa ya bar mata, raba snacks ɗin biyu tayi taɗauki rabi, yayinda tabarmawa Zahrah rabi, waya kuwa danƙamawa Zahrah abunta tayi, domin ita keypad ma bawani iyata tayi ba, balle kuma shafa shafa (touching screen)... Jigum haka Zahrah tayi zuciyarta cunkushe take da tarin tunani kala kala, da zaran ta kulle idanunta, mood ɗinsu na ɗazu ne ke faɗo mata, wanda hakan yasanya takejin gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, batasan dame zata ƙira wannan yanayinba, saboda batasan ma da akwaishi acikin duniyar nan ba, duk dacewa bawani abune yashiga tsakaninsu ba, amma kusancin da sukayi da juna duk ya dagula mata lissafi, ga fitinannen ƙamshin turarensa daya kama jikinta, tamkar wacce tayi wanka da turaren,daga wani ɓangare na zuci yarta kuwa kaico takeyi da mummunan hali irin na Inna da Baffa, wato su baruwansu da koma waye zaizo wajenta, sudai kawai abasu kuɗi suka sani, koda ma iskanci takeyi su baidame su ba kuɗi kawai suke so, haƙiƙa rashin iyaye babban matsalane arayuwar ƴa mace musamman ma idan batayi dace da iyayen riƙo nagari ba, sai kuga rayuwarta nashirin lalacewa, akan abun da bai kai yakawo ba, Allah ka zama gatan mu aduk inda muke Ameen,,, a hanakali taciro wayar daga cikin kwalinta, subahanAllah shine abun da tafurta lokacin da'idanunta suka sauƙa akan haɗaɗɗiyar wayar, jikin wayar ma kaɗai abun kalloce balle kuma kakai ga shafata, tabbas idan baza ta mantaba, wannan wayar itace wacce taji ƴan school ɗinsu na magana sabuwar fitowa ce, kuma burin kowanni ɗan gata da ƴar gata, shine su mallaki wayar, domin kuwa aƙalla kuɗinta zaikai dubu ɗari biyar da tamanin,, wani irin faɗuwar gaba taji ya shiga zuciyarta a lokaci guda, take kuma mugun zargin Zaid ya ɗarsu acikin ranta, tabbas akwai abun daya ɓoye acikin zuciyarsa, amma idan ba haka ba babu yanda za'ayi yasiya mata wayan dubu ɗaruruwa, batare da suna da wani kyakkyawan alaƙa atsakaninsu ba, a maimakon ta kunna wayar kamar yadda ya umarce ta, batayi hakan ba saima mai da wayar tayi cikin kwalinta haɗe da cusata cikin kayanta, taƙudura acikin ranta cewa idan yasake da wowa zata mayar masa da wayarsa, domin ita bata kai martaba da ƙimar da zata riƙe wannan zuƙeƙiyar wayarba,, sam bacci ya ƙaurace mawa idanun Zahrah kalaman Zaid ne ketayi mata yawo acikin kunnu wanta, bama kamar kalmar *INASONKI ZAHRAH* daya faɗa, gaba ɗaya zuciyar Zahrah kasa sukuni tayi a wannan dare, da ƙyar bacci ɓarawo ya ɗauketa......
Zaid kuwa yana barin unguwar su Zahrah guest house ɗinsa ya nufa, sai dai yau ba ya tare da kowacce karuwa, yana shiga cikin bedroom ɗinsa yasoma rage kayan jikinsa, saida yacire duk wani kaya dake jikinsa, kafun ya ɗaura towel a ƙugunsa kaitsaye ya shige bathroom,, a ƙalla ya kwashi kusan 1 hour a cikin bathroom ɗin kafun yafito, sanye da rigar wanka a jikinsa, gaban mirror ɗinsa yaje ya ɗanyi shafa, combat jeans black ya sanya haɗe da black t-shirt, sosai kyawun Zaid ya bayyana acikin wannan kayan, wayarsa kawai ya ɗauka yafice daga cikin ɗakin, makeken friedge glass ɗin dake cikin katafaren falon nasa yanufa, zuƙeƙiyar kwalbar wine mai tsadar gaske yaɗauko a cikin friedge ɗin haɗe da glass cup zama yayi akan ɗaya daga cikin kujerun falon, yayinda ya buɗe kwalbar wine ɗin ya tsiyaya a cup, kana yakai bakinsa, a hankali yake shan wine ɗin, yayinda idanunsa ke alumshe, bakomai yake hasa sowa ba sai kyakkyawar surar Zahrah wacce ke tafiya da imaninsa ako da yaushe, haƙiƙa ya kamu da tsananin sha'awar Zahrah, kuma alƙawari yaɗaukar mawa kansa idan dai har yacika *SHU'UMIN NAMIJI* kamar yadda abokansa ke ƙiransa, to sai ya keta mawa Zahrah rigar mutumcinta kota wani hali kuwa,, wayarsa yaɗauka haɗe da laluɓo numbern sim ɗin dake cikin wayar Zahrah, yana dialing aka sanar dashi cewa wayar a kashe take, wani irin munafukin murmushi Zaid yayi haɗe da sanya hanu ya shafi sajen dake kwance akan fuskarsa, kashe idanunsa ɗaya yayi haɗe da cewa "My Sugar Baby bakijin magana ko ?" yayi maganar tamkar wanda yake gabanta,, sosai Zaid ya sha wine a wannan dare, da ƙƴar ma yasamu bacci ya ɗaukesa bayan yagama kwarara aman giyan da yasha .......
*21/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*WRITTEN by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated to my lovely brother Khabier*
*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
```{{ Dan Allah kuyi haƙuri, kubarni na cigaba dayin littafina a yanda natsara, banson ƙorafi kokuma cece kuce, haka labarin Zaid da Zahrah yake, bakuma zan sauya ba, baikamata ace tun bakuji mai zai wakana gaba ba, kunsoma yanke hukunci, inyi kaza kar inyi kaza, kada Zaid yayi kaza, 🤦🏼♀ Please kudaina haka ba daɗi, inaso kusani a yanda na tsarashi ahaka zanci gaba da tafiya dashi, babu wani kwana kwana, kuma abu na farko da nakeso ku fara sani shine, kowa a duniya da irin tasa Ƙaddarar, so komai kuka gani sai ku ɗaukeshi a matsayin ƙaddara....}}```
*Chapter 13....*
Yaune kwanaki ukun da Zaid ya ɗibar mawa Zahrah suka cika cif cif, don haka yau da wani irin matsanancin faɗuwar gaba ta wayi gari, haƙiƙa bazata yaudari kanta ba, tasani cewa ƙwarai zuciyarta ta aminta da Zaid to amma babban abun dubawa shine, shin Zaid ɗin yadace da rayuwarta kuwa? ko kaɗan bata hango dacewarsu da Zaid ba, duk da tasan cewa tana da kyawun da kowani ɗa na miji zaizo da ƙoƙon soyayyarsa gareta, amma bata tunanin haɗuwarsu da Zaid zaiyi dai dai, kallo ɗaya zakaima Zaid kafahimci cewa shiɗin mai tarin arziki ne, haka ma iyayensa, itakuwa bakomai bace face *TALAKA* ƴar *TALAKAWA* wacce talauci yabayyana tambarinsa ajikinta, sam bata mawa kanta adalci ba matsawar ta ɗauki kanta takai zuwa matsayin da bana taba, wasu irin hawayene suka shiga gangarowa daga cikin idanun Zahrah, yayinda zuciyarta keyi mata zafi, batasan menene so ba, domin bata taɓa yi ba, amma a yanda takejin Zaid acikin zuciyarta, yasa tafara kokonton cewa takamu da tsananin soyayyarsa, gaba ɗaya wunin yau a susuce tayi sa, damuwarta ɗaya idan Zaid yazo maizatace dashi ? idan ta furta masa kalmar ƙi to fa har abada bazata taɓa yafemawa kanta ba, domin ta cutar da zuciyarta, idan kuwa ta furta masa kalmar so, tofa ba makawa tajefa kanta acikin ɗauri ne mai wuyar suncewa.... Wunin ranar dai haka Zahrah tayi shi sukuku babu daɗi, fargaba ne fal cike a zuciyarta....koda tayi Sallan la'asar banɗaki tashiga tayi wanka , zama tayi akan katifarta, haɗe da ɗauko wata hand bag ɗinta, wanda ciki take ajiyar kayan kwalliyanta, duk da cewa dai itaɗin ba mace bace ma'abociyar yawan kwalliya,, hakanan ta tsinci kanta da son yin kwalliya a yau ɗin, hoda (powder) ta murza akan fuskarta, haɗe da shafa janbaki (lipstick) dark maroon colour, akan laɓɓanta, black eye pencil, tasanya acikin idanunta, haɗe da shafa mascara akan zara zaran gashin idanunta, take fuskar Zahrah tasakeyin kyau, duk da dama cewa itaɗin mai kyauce,, wata Arebian gown maroon colour tasanya ajikinta, sosai da sosai rigar ta amshi jikin Zahrah, tayi mata ɗas, duk acikin kayanta Zahrah tana matuƙar son rigan, domin kuwa maman khausar ce takawo musu, ita da khausar ɗin, daga Saudiya,, rigace mai kyau da tsadar gaske, uwa uba idan ta sanya rigar ita kanta tasan tanai mata kyau,, kan katifarta ta koma ta zauna, bayan tagama kimtsa kanta, jigum tayi tana tunanin waishin maiyasan yata yin kwalliya batare da wani dalili ba? "saboda Zaid zai zo, zuciyarta ta bata amsa, "idan kuma baizo bafa ?" tatambayi kanta, take wani irin faɗuwar gaba ya ɗarsu acikin zuciyarta, wanda batasan dalilin faruwan hakan ba,, abu kamar wasa, har yammaci ta rufa babu Zaid babu alamarsa, tuni jikin Zahrah yayi sanyi laƙwas,, hardai akayi sallan Isha, ba'azo daga waje ance anaƙiran Zahrah ba,, tuni ta wanke ɗan kwalliyan da tayi a fuskar tata ma, domin zuwa yanzu tacire rai da zuwan Zaid... Zaune take a tsakar gida, gabanta ɗauke da kwanon shinkafa da wake, a hankali take tsakuran shinkafan tana kaiwa bakinta, kallo ɗaya zakai mata kahango tarin damuwa acikin zuciyarta,, kamar daga sama wani yaro yashigo, yace wai anaƙiran Zahrah a waje,, wani irin farincikine ya lulluɓe zuciyar Zahrah, domin kuwa tana kyautata zaton cewa Zaid ne,, koda tashiga ɗaki don ɗauko mayafinta saida tasake murza powder a kan fuskarta haɗe da sanya kwalli a idanunta, Zahrah dai bata tsayananba hadda shafa jambaki,, wani rover hijab tasanya ajikinta, kalar maroon, wato kalar doguwar rigan dake jikinta, gaba ɗaya lufayar iyaka cinya ta tsaya mata, hakan kuma yayi nasarar bayyana surar jikinta, kasancewar lufayan mai rover ce, tayi kyau kuma balaifi, tamkar dai balarabiya, abunka da farar fata,, turarenta mai sauƙin kuɗi (TONY MONTANA) tafeshe jikinta dashi, take ta ɗau ƙamshi,, a hankali take taku harta fice daga cikin gidan nasu,, koda tafito daga gidan cikin nutsuwa take takunta, yayinda kanta ke duƙe a ƙasa, zuciyarta kuwa bugawa tashiga yi akai akai,, kaitsaye tanufi wajen da taga motarsa na fake,, tun da tafito daga cikin gidan, ya kafeta da mayun idanunsa, masu rikita mata, sosai yau ɗin tayi masa kyau, hakanan yaji sha'awarta ta ninku akan nada,, tana ƙarasowa wajen motar ta sa, taja ta tsaya, still kuma kanta na kallon ƙasa tana wasa da yatsun hanunta, a. hankali yabuɗe murfin motar tasa haɗe da ziro ƙafafunsa waje, take wani irin fitinannen ƙamshin turarensa yacika ko'ina na wajen, a hankali ta lumshe idanunta, domin kuwa bakaɗan ba ƙamshin turaren nasa ya tafi da'ita,, kallonta ya shiga yi tundaga ƙasanta harzuwa samanta, kafun ya saki shu'umin murmushinsa, "MY ZAHRAH !!" yaƙira sunanta da wani irin murya mai sauƙar da kasala, kasa amsa masa Zahrah tayi saima sake sadda kanta ƙasa tayi tana mai wasa da yatsun hanunta,, murmushi yakumayi a karo na biyu, "yau kuma tsayuwa kikeji da shi ?" yayi tambayar cikin nuna halin ko inkula,, jin haka yasanya ta gane mai yake nufi, jiki a sanyaye ta nufi ɓangaren mai zaman banza tabuɗe murfin motar haɗe da shiga ta zauna,, a hankali Zaid ya yi ƙasa da kujerar dayake zaune, ɗan zamewa yayi ya jingina bayansa da jikin kujeran haɗe da lumshe kyawawan idanunsa, a hankali Zahrah ta ɗan saci kallonsa haɗe da cewa "Ina wuni !" jin muryarta da yayi ta ratsa kunnuwansa yasa sa ɗagowa, yazauna haɗe da kafeta da'idanunsa, yakai kusan 3 minute yana kallonta "kinyi kyau !!" yafaɗa in a unigue voice ɗinsa, wani iri Zahrah taji a cikin jikinta, wannan shine karo na farko a duniya da wani ɗa namiji ya fara faɗa mata cewa tayi kyau,, cikin salonta na kunya, ta ɗago idanunta takalleshi karab idanunta suka sauƙa acikin nasa idanun, wani irin shock taji ajikinta, da sauri tayi ƙasa da kanta, cikin salonsa ya ce " Idan kinajin kunyana ta ya ya zaki iya nunamin zallar soyayyar danake buƙata a wajenki ? inasonki da duka zuciyata My Zahrah ina fata kema zaki soni kamar haka ko fiye da haka ? " a yanda yayi maganar idan kakallesa zaka iya rantsewa cewa bashine yayi ba,, jitayi jikinta gaba ɗaya yayi laƙwas, wani irin zazzafar ƙaunarsa takeji yana huda kowani irin saƙo na jikinta, a hanakali ta ɗago manya manyan idanunta da suka cika da ƙwalla, ta sauƙe su akan kyakkyawar fuskarsa, cikin murya mai rauni tasoma cewa "bantaɓa soyayyaba, bankumasan ya akeyinta ba, ni marainiyace bayan Allah sai Baffana nakedasu acikin wannan duniyar, nasan kafi ƙarfin ajina, dan Allah kada kayaudareni da soyayyarka " taƙare maganar lokacin da hawaye suka shiga sauƙowa a kan fuskarta,, kafeta da idanunsa yayi harnatsawon wasu mintuna, shikaɗai yasan abun da yake saƙawa acikin zuciyarsa,, "Idan kin yarda dani to kibani soyayya da amincewarki, nikuma bazanci amanarki ba" yayi maganar cikin muryarsa mai sanyawa zuciyarta nutsuwa,, ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya Zahrah ta sauƙe haɗe da yimawa Allah godiya daya kawomata ma'agaji adai dai lokacin da ta ke buƙata, shirune yashiga tsakaninsu na ɗan wani lokaci, bayan Zaid yagama saƙa abun da zai saƙa acikin zuciyarsa, yasaki wani irin killer smile haɗe da mai da kallonsa ga Zahrah, "ya kamata ki kaini nagaidasu Baffa ko " ya yi maganar yana mai kashe ma ta idanunsa ɗaya,, murmushi kawai zahrah tayi haɗi da cewa "banaje na sanar dasu to " buɗe murfin motar tayi ta fice haɗe da shigewa cikin gida, bayanta kawai Zaid ya ƙura ma wa ido bakaɗan ba ya kwaɗaitu da yarinyar kuma insha Allah saiya cimma burinshi a kanta,, bawani jimawa Zahrah tafito daga cikin gidannasu, kamar dai ko da yaushe kanta duƙe yake a ƙasa harta ƙaraso garesa,, iso tayi masa zuwa cikin gidannasu, gaba ɗaya a takure take domin kuwa itace a gaba shikuma yana biye da'ita a baya, ahaka suka shiga cikin gidan,, cike da ƙyanƙyami Zaid yazauna akan tabarmar da Inna ta shimfuɗa ma sa a tsakar gidannasu, tunda yake a duniya yaune karo na farko a rayuwarsa da yafara zama cikin gidan talakawa, lallai idan yakama Zahrah ba zai mata da sauƙiba, da ƙyar ya'iya kai zuciyarsa nesa yagaisa dasu Baffa da suka ƙura masa ido, tamkar sunga baƙon halitta,, har rige rigen amsa gaisuwar tasa Inna da Baffa sukeyi, daganinsu kaga mayun ku ɗaɗe,lol, shirune yabiyo baya bayan sungama gaisawa, domin dai harga Allah Zaid bayi da abun cewa, saboda shi bai ma taba irin hakan ba, bayan iyayensa babu wasu wanda yataba gaisarwa da ladabi haka, sai gashi yau akan wata tatsitsiyar yarinya yazo yana kaskantar da kansa gaban talakawan unguwa, lallai yaci amanar jinkai dakuma ajinsa, amma yazaiyi tunda shiyake nema dole yayi biyayya,, ganin yayi shirune yasa Inna gyara zama hade da cewa, " munagodiya sosai bawan Allah ga me da taimakon mu da kakeyi, Allah ubangiji yasaka da alkhairi, " murmushi kawai Zaid yayi hade da mikewa tsaye, bandir din kuɗaɗe yaciro daga cikin aljihunsa, hade da ajewa akan tabarmar daya tashi,, tsadaddun takalmansa yasanya hade dayi musu sai anjima yafice daga cikin gidan, "bawan Allah harda dawainiya haka to to masha Allah, Allah yasaka da alkhairi " Inna tafada tana mai washe baki,, Zaid yana ficewa daga cikin gidan, Inna da Baffa suka dakamawa kudin wawa, Zahrah dake tsaye a gefe kuwa idanunta ne suka ciko da kwalla, sam batajin dadin abun da Baffa da Inna sukeyi, suna nuna zalamarsu afili,, "Miye kika yi wani ƙasaƙe kina kallonmu bazaki bisa ba " Baffa yafaɗa yana hararan Zahrah, jiki a sanyaye Zahrah tarufa mawa Zaid baya,,,, Zaid kuwa yana fita kaitsaye motarsa ya wuce, sosai yaji daɗin yanda ya hango zallan son kuɗi irin na Baffa da Inna, tabbas yanzu yasake samun ƙwarin guiwa akan burinsa, yanzu yasan cewa bazai wahala wajen samun galaba akan Zahrah ba,,, tana fitowa ya sakar mata kyakkyawan murmushinsa, wanda yake ƙara mawa kyakkyawar fuskarsa kyau aduk sanda yayi sa......
*Kuyi hakuri wallahi kwata kwata banjin yin typing dinne, abubuwa sunmin yawa, nasoma ace 2 weeks nayi, amma sai wasunku suka nuna rashin jin dadin hakan, so please kunamin uzuri duk dama nasan wasunku bazasu so hakan ba, a gaskia bako da yaushe zanna typing ba, saboda kowani ɗan adam yana buƙatar hutu a rayuwarsa, kuyi haƙuri duk bayan kwana ɗaya zandingayin new update....*
*27/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NA MIJI !!*
*WRITTEN by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated to my lovely brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*Chapter 14*
Wani irin kallo mai ta da tsikar jiki Zaid yayi mawa Zahrah, still fuskarsa ɗauke da wannan sheɗanin murmushinnasa, sadda kanta ƙasa tayi haɗi da soma wasa da yatsun hanunta,, Sunanta yaƙira da wata irin murya mai kwantar da zuciya, bata iya amsa masa ba saima ɗago kanta da tayi ta kallesa, wani irin baƙon yanayi ta tsinci kanta aciki mai wuyar fassaruwa, a hankali ya lumshe kyawawan idanunsa masu kalar bacci haɗe da buɗesu a lokaci guda,, "Zantafi !!" yafaɗa daidai lokacin dayake ɗaura sit belt a jikinsa, kasa ce dashi komai tayi saima wani iri taji dayace zaitafi ita a sonta bataƙi su tabbata a haka ba, domin ganinsa kaɗai yakansa taji wani irin nishaɗi a cikin zuciyarta,, wata ƙatuwar leda mai ɗauke da tambarin wani makeken mall yamiƙo mata, sadda kanta ƙasa tayi haɗe da girgiza kanta, alaman bazata karɓa ba,, ɗan ɓata fuska Zaid yayi haɗe da cewa " idan baki karɓa ba bazanji daɗi ba, kuma kinsan cewa bakyau maida hanun kyauta baya " wani irin sanyi taji a cikin ranta tabbas ko bakomai tasamu mai kulawa da rayuwarta, cike da girmamawa ta karɓi ledar, haɗe dayi masa godia,, murmushi kawai yayi mata haɗe dayi mata nuni da tashiga gida,, ba musu tajuya cikin takunta mai ɗauke da nutsuwa tashige cikin gidan,, tana shigewa cikin gida Zaid ya ɗaura hanunsa akan mararsa dayakeji tayi masa tauri kamar ansanya dutse, lumshe idanunsa yayi, haɗe da gangaro hanunnsa zuwa kan joy stick ɗinsa cikin wata irin murya yace "idan kika kama sugar baby baki mata kaca kaca ba bazan yafe miki ba, because ta wahalarni da yawa, tasa inata abubuwan daba halina ba, wato ƙasƙantar dakai dakuma yawan magana " wani munafukin murmushi yayi haɗe dayi mawa motar tasa key, kaitsaye guest house ɗinsa yanufa, domin kuwa a yanda yakeji yau bazai iya kwana bai yi sex ba, dole yasamu wata yayi mata cin kaca, saboda yakai ƙololuwa wajen sha'awa ga wannan ƴar iskan Zahrah'n takunna sa, domin ganinta ma kaɗai tayar masa da hankali yake.....
Yauma dai wata sabuwar karuwar yasamu mai suna Salima, tun da Salima ta sanya idanun ta akan Zaid soyayyarsa tatafi da ita, Salima yarinya ce ƙarama don bazata wuce 21 year ba, sosai ta liƙemawa Zaid, burinta a duniya shine Zaid yasota, amma kwata kwata Zaid bai damu da lamuranta ba, amma duk da haka bata fasa bibiyar sa ba,, Zaid kuwa fuskanta da yayi cewa Salima bata taɓa iskanci ba, yasanyashi fara sauraranta haɗe da ɗana mata tarkon shu'umancinsa, yaci alwashi cewa sai ya tarwatsa budurcin Salima,,, itama dayake soyayya tarufe mata ido, yasanya tayi saurin amincewa dashi,, zaune suke a tsakiyar tangamemen falonnasa dagashi sai dogon wandon jeans, yayinda Salima ke kwance a jikinsa, daga ita sai wata baƙar doguwar riga marar nauyi, gaba ɗaya Salima tasusuce game da soyayyar Zaid, a yanda takejinsa acikin zuciyarta zata iya mallaka masa komai nata a duniya,, a hankali yasanya hanunsa cikin kanta, wanda yasha kitson ƙari da akayishi da gashin doki,, wato attachment,, wani irin kallo yajefi Salima dashi, take ta langwaɓe kai, haɗe da matso da fuskarta dai dai da tasa,, bakinsu take ƙoƙarin haɗewa waje ɗaya, saurin kauda kansa gefe yayi haɗe da jawota jikinsa, lafewa tayi a cikin jikinsa haɗe dayin ƙasa da kanta, bakinta ta ɗaura a dai dai kan nipple ɗinsa, a hankali ta soma tsotson nipple ɗin nasa, saurin lumshe idanu Zaid yayi domin kuwa sosai yakejin wani iri acikin jikinsa,, kwalbar giyan dake gefensa ya ɗauka haɗe da kafawa abakinsa, sosai ya tuttula wa cikinsa giya,, domin yafijin daɗin sex idan a buge yake, hannayensa yasa ya zame rigan dake jikin Salima,, take surarta ya bayyana,, sake waro idanunsa yayi, domin kuwa gaba ɗaya Salima ta rikiɗe takoma masa Zahrah sak,, hmm giya tafara aiki,, wani irin shu'umin murmushi Zaid yayi haɗe da lasan laɓɓansa, duka hannayensa ya buɗe alamar ta taho garesa, cike da ɗoki Salima ta faɗa jikin Zaid, haɗe da ɗaura hanunta kan joy stick ɗinsa tasoma murzawa a hankali, abunku da tashen balaga itama dama tajima tana buƙatar wanda zai jagwalgwalata,to yanzu gashi tasamu baban ƴan iska, gaba ɗaya hannayensa ya ɗaura a kan breast ɗinta, bayan yacire mata duk wani kaya dake jikinta, balaifi tanada big breast, duk da cewa breast ɗinta bai kasance yanda yakeso ba, bakinsa ya ɗaura akan wuyanta yashiga bata wani irin kiss mai ta da hankali, still kuma hannayensa nakan breast ɗinta, yana murzasu a hankali,, tuni Salima ta shiɗe tafice a hayyacinta, domin kuwa salon Zaid na daban ne, ɗa gata Zaid yayi caɗak, haɗe da nufar bedroom ɗinsa da'ita, domin kuwa tuni tanarke, haɗi da sallama masa kanta,, gaba ɗaya Zaid yafice a hayyacinsa domin kuwa Surar Zahrah kawai yake hangowa a jikin Salima, cikin rawar jiki yafar mawa Salima, da ƙarfin gaske Zaid ya ratsa hanyar Salima ya wuce,, duk irin ihun da Salima keyi Zaid bayako jinta, Zahrah kawai yake hangowa, a maimakon Salima,, sosai Zaid ya gurji Salima son ransa har saida yaji mata ciwo, tun Salima na ihu har muryarta tadaina fita, sam batai zaton haka zafin sex yake ba, a tunaninta daɗi kawai a keji,,, saida yasamu nutsuwa kafun ya sauƙa daga kanta, kai tsaye toilet yashige, yasakar mawa kansa shower, yajima tsaye ruwa na dukansa, daga bisani yayi wankan tsarki, yafito daga cikin toilet ɗin,, sanye yake da rigan wanka hanunsa riƙe da ɗan ƙaramin towel yana goge kansa,, kallon inda Salima ke kwance shame shame tamkar gawa yayi, wani munafukin murmushi yasakar mata haɗe da kashe mata ido ɗaya, "ƴan matana !" yafaɗa da muryarsa ta yaudara,, da ƙyar Salima ta'iya ɗago idanunta dasuka kumbura saboda kuka ta kalleshi,, murmushi yasake yi mata haɗe da nufar inda mirror ɗinsa yake,, mai ya shafa a jikinsa sama sama, wata maroon jallabiya, ya zura ajikinsa, haɗe da feshe jikinsa da turarensa mai daɗin ƙamshi,, kan gadon da Salima ke kwance yanufa, kwanciya yayi a ɗan nesa da'ita haɗe da juya mata baya, sakayau yakejinsa, tamkar an sauƙe masa babban nauyin dake kansa, dan haka mintuna ƙalilan bacci yayi awon gaba dashi,, da kyar Salima ta'iya tashi ta shiga bathroom, ruwan zafi ta tara a cikin bath tub ɗin wanka, tashiga ta zauna, saida tayi kuka tsabar azaba, da kyar dai tasamu ta'iya gasa kanta,, kuka kam tayishi badon komai ba kuwa saidon azaba'n da tasha a wajen *SHU'UMIN NAMIJI,ZAID* kwanciya tayi itama a gefensa, take baccin wahala yayi gaba da'ita........
*ZAHRAH* kuwa a daren ranan nan sam bacci ƙaurace mawa idanunta yayi, wata irin soyayyar Zaid mai ƙarfine yake huda zuciyarta, sam takasa manta irin kallon da Zaid keyi mata, ga murmushinsa, daya tsaya mata a zuciya, haƙiƙa Zaid yacika *SHU'UMIN NA MIJI* domin kuwa ya shammaceta ya ɗauke mata zuciya batare da ta ankaraba,, har kusan ƙarfe 2 na dare kafun Zahrah tasamu bacci ya ɗauketa,, washe gari kuwa da dassafe ta shirya kanta cikin riga da sket na a tamfa, balaifi kuma ta ɗanyi kyau cikin shigarta ta,, ƙarfe 7 dai dai ta nufi makaranta, domin kuwa yau suna da lecture 7:30, sa'anta ɗaya yanzu Inna bata hanata zuwa makaranta akan lokaci, saboda haka yanzu bata latti......
Manage.......
*28/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*WRITTEN by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated to my lovely brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*Chapter 15*
Zaid kuwa ba shine ya farka daga bacci ba, sai wajen 8:30 am, abun haushi da takaicin ko sallan asuba baiyi ba, bathroom yashiga yasakeyin wanka, haɗe da ɗauro alwala, sallaya ya shunfuɗa haɗi da soma kabbara sallah, kokunya bayaji domin kuwa rana tafito faɗe faɗe, amma wai sai a lokacin yake sallan asuba, Allah wadaran halinka Zaid, ai dama ibada da iskanci basa taɓa haɗuwa waje ɗaya, babuma kamar zina, ya Allah kakaremu daga sharri da aikata zina, ameen....
Tsab yagama shirya kansa cikin wasu haɗaɗɗun riga da wando ƴan kanti, maroon colour, sosai kayan suka amshi jikinsa, kasantuwarsa mai farar fata, wandon irin pencil ɗinnan ne yayinda rigar takasance mai aninaye a gabanta, sannan tana da guntun hanu iyaka guiwa, facing cap maroon colour yasanya a kansa, ta ke kyau da kwarjininsa suka sake bayyana, haƙiƙa Zaid ya haɗu tako wani fanni, matashine maiji da gaye gakuma kuɗi da suka ɗaure masa gindi, feshe jikinsa da turarukansa masu ƙamshi yayi, haɗe da ɗaukar wayarsa ya zura cikin aljihun wandon sa, kallonsa yakai kan Salima da take ta sharan bacci, wani munafukin murmushi yayi haɗe da buɗe wata ƴar ƙaramar drower yaciro rafan kuɗi ƴan dubu dubu ɗauri ɗaya, rufe drower'n yayi haɗe da sa mata key,,, wurgi da kuɗin hanunsa yayi zuwa jikin Salima, haɗe da sakai yafice daga cikin ɗakin, bakinsa ɗauke da fito,, a ransa kuwa cewa yake "banzar yarinya ko daɗi ma bata da shi, mcheeeww nidai naja mawa kaina, a kwashe kwashena naje nasamu dusar mata !, amma bakomai zan fanshe ajikin kine sugar baby, wallahi duk randa na kamaki saina miki raga raga !!" kaitsaye wajen motarsa ƙirar BUGGATI yanufa, yana shiga cikin motar yayi mata key, tuni mai gadi ya wangale masa tankamemen gate ɗin gidan, shikuwa bawani ɓata lokaci ya cilla hancin motarsa waje.... Kaitsaye gidansu ya nufa, domin tunjiya Dadynsa keta ƙiransa akan yazo yanason ganinsa,, tafe yake acikin mota amma earpiece ne saƙale a kunnensa yanashan waƙa, bayan kiɗan dake tashi acikin motar tasa, gudu yake tsulawa baruwansa da wanda ke bayansa ko gabansa, a haka har ya'iso cikin gidan nasu, yanafita acikin motarsa yanufi ɓangaren mom ɗinsa,, zaune take akan kujera, tasha ado cikin shiga ta alfarma, yayinda wata yarinya ke duƙe a ƙasanta tana aikin yimata tausa aƙafafunta, daga kaganta kaga zallan hutu da jindaɗi, domin kuwa zoben hanunta kaɗai ya'isa yasai maka babban gida mai kyau awani garin,, tana ganinsa tasaki murmushi haɗe da kafesa da'ido, bakomai yasa tayin hakanba, face ƙoƙarin gano maike damunsa, dan taga fuskar tasa a ɗaure tamau,, "barka da hutawa Mom" Zaid yafaɗa dai dai lokacin daya zauna kan ɗaya daga cikin kujerun falon, Mom bata amsa masa ba saima kallonsa da taci gaba dayi, a hankali Hajara ta ɗago idanunta ta saci kallon Zaid,
"Zanci ubanki idan baki daina kallo naba shegiya munafuka mai baƙar fuska !!" Zaid yafaɗa cikin hargowa, tuni Hajara ta ruɗe ƙafofinta sun soma rawa, domin tabbas tasan yakamata tana kallonsa ne, itakam yau tashiga uku, taƙirawa kanta ruwa,, "ke Hajara tashi ki wuce ciki, anjima kya dawo ki ci gaba da matsamin ƙafan" Mom tafaɗa, sumi sumi Hajara ta tashi daga duƙen da take hartana jin tuntuɓe tsabar sauri tabar falon,,
"Wai Zaid maiyasa kake hakane ? dudduniya babu yarinyar daka tsana kamar Hajara, waima ni ba wannan ba, kokasan cewa ina da labarin duk irin abubuwan da kake aikata wa, sai yaushe zaka girmane Zaid ? ni bance kada kayi abunda kake so ba, amma kadaina bin mata dan Allah Zaid, wannan bahalin mutanen kirki bane !" Mom tafaɗa cikin rarrashi,, ko gizau Zaid baiyiba balle ya amsawa Mom,, bata damu ba domin dama tasan zaiyi wuya ya amsa mata ɗin,, bata sake ce dashi komaiba, saima tashi tayi tabar masa falon, domin bazata iya da wannan baƙin rannasa ba, ace mutum shi komai kayi masa bazaka burgesa ba, shegen baƙin hali da gadara, tamkar wani basarake,,, Mom na tafiya, wayar Zaid tasoma ƙara alamar shigowar ƙira, bai ɗauki wayar ba saima tashi da yayi yafice a falon, kai tsaye babban falon Dady ɗinsa ya nufa.... Maganar dai ɗaya ce, shine yafito da matar aure,, "to" kawai Zaid yacemawa Dady'nnasa, sun ɗan taɓa hira akan harkan kasuwancinsu, kafun daga bisani Zaid yayi mawa Dady'nnasa sallama yatafi.......
gaba ɗaya yau Husnah takasa gane kan Zahrah domin kuwa, duk bayan minti kaɗan sai Zahrah ta saki murmushi ita ɗaya... Yanzuma zaune suke akan wata kujera da akayita da suminti, irin nazaman ɗaliban cikin University,, gyara zama Husnah tayi haɗe da maida hankalinta ga Zahrah... "SOYAYYA !!" Husnah tafaɗa,tana mai tsare Zahrah da idanu,, murmushi Zahrah takumayi haɗe da kamo hannayen Husnah cikin ɗan yanayin damuwa tace "bansan yanda a keyinta ba, impact ma bansan ya'ake gane ankamu da'ita ba, amma tabbas inaga nafaɗa a soyayya ƙawata, domin kuwa dare da rana koda yaushe tunaninsa baya barin zuciyata, da gaske inasonsa Husnah ? " Zahrah ta tambaya lokacin da ƙwalla suka cika idanunta,, murmushi mai sauti Husnah tayi haɗe da cewa " Lallai ko wanene shi yacika JARUMI acikin JARUMAI da har ya'iya sace zuciyar kyakkyawar ƙawata, tabbas ko tantama babu Zahrah kinkamu da son sa, wanene shi ? a'ina yake ?"
"har yau bansan wanene shiba, Husnah, bansan koshi ɗin waye bane, amma tabbas nasan cewa yafi ƙarfin ajina, amma yazanyi tunda shiya koyamini sonsa, bantaɓa soyayya ba, a kansa nafara shiyasa nake jin sonsa fiye da komai a gareni " Zahrah ta ƙare maganar lokacin da hawaye suka wanke mata fuska, " Kuka banakibane lover girl, nidai gaskia yakamata kinunamin jarumi'n nan domin nabasa babbar kyauta.... " Ɗan murmushi kawai Zahrah tayi batare da tasake cewa komaiba, sosai Husnah tabata shawara dakuma ƙarin haske akan soyayya,, koda aka tashi a makaranta, cike da tarin tunanin Zaid Zahrah ta dawo gida, a zuciyarta kuwa cewa take "Inama da zai dawo yau tasake ganinsa, har abada bazata gajiya da ganinsa ba......"
"Hahahahaaahha gaskia SHU'UMI baka da kyau, wato dai kayi rantsuwa cewa saika lalata musu ƴa ko, hmm banga laifinka ba, domin kuwa da fari nima na kwaɗaitu da babyn kuma wallahi har gobe ina tsananin sha'awarta, amma tunda kamin shigar sauri ba damuwa, idan kaci ka rage naci sauran koba haka ba guys " Bash yafaɗa yana dariya,, wani irin abune ya tokare maƙoshin Zaid, bawai don wani abu ba, saidon kalaman da Bash ke faɗa, wai idan yaci ya rage yabasa ya ƙarasa, lallaikam, ai dudduniya babu wanda zaici Zahrah bayanshi,,,
Kallonsa Bash yakumayi haɗe da ɗage gira cikin shaƙiyanci yace "SHU'UMI yadai kodai ka kamune ?" wata uwar harara Zaid ya wurga mawa Bash cike da miskilanci yace "Banshirya faɗawa soyayya yanzuba, babuma so a tsarina, sai dai ina matuƙar sha'awarta fiye da komai aduniya, soon kuma komai zai dai dai ta "
gaba ɗaya abokan Zaid suka kwashe da dariyan mugunta, domin sarai sunsan waye Zaid idan yace saiyayi abu babu makawa sai yayi, haka kuma duk macen daya ɗana mawa tarko, to tabbas saita faɗa,,, haka dai sukaita zuba iskancinsu......
Jabeer ne tsaye a ƙofar gidan su Zahrah, yayi kyau cikin shigarsa ta kamala, wato jamfa da wando, haƙiƙa Jabeer ma kyakkyawane kuma shima yana da burgewa, saidai baza a taɓa haɗa shi da Zaid ba, because Zaid na dabanne,,, Baffa ne ya taho buja buja zaishiga gida, dawowarsa kenan daga kasuwa,, harƙasa Jabeer ya tsugunna yagaida Baffa, washe da baki Baffa ya amsa gaisuwar,, cike da jinkunya Jabeer yace "am Baba dama...dama nazo wajen Zahrah ne "
"To..to...to yaro sannunka da zuwa, ince dai tace tana fitawo ?" Baffa ya tambaya washe da baki,, "A'a" Jabeer yafaɗa yana sosa ƙeya,, buzur Baffa ya faɗa cikin gida, tundaga zaure ya soma kwaɗa mawa Zahrah ƙira.... Zahrah ! Zahrah !! Baffa yaketa faɗa harya shigo cikin gidan, Zahrah dake ɗakinta tafito tana amsa ƙiran da Baffa keyi ma ta,, "ke wace irin shashasha ce wai Zahrah ? yazakibar baƙo yanata jiranki a waje, to wallahi maza kiwuce kije kisa mesa,tunkan yayi zuciya yatafi, domin su masu kuɗi taurin ran tsiya garesu, sam basa son jira...." cikin ɗoki Zahrah takoma ɗaki haɗe da ɗauko hijab ɗinta, Zahrah bata tsayananba hadda feshe jikinta da ɗaya ɗayan turarenta, lol,, wani irin daɗi takeji a cikin zuciyarta, kenan shima yadamu da'ita kamar yadda ta damu da shi, tabbas yau zata faɗa masa kalaman soyayya masu ra tsa zuciya,,
Wani irin faɗuwar gaba taji, alokacin da'idanunta suka sauƙa kan Jabeer, murmushi Jabeer yayi mata haɗe da soma takowa gareta,, itama murnushin tayi masa amma na dole, ko kaɗan batajin sonsa a cikin zuciyarta, haka bakuma tajin ƙinsa, sai dai kuma bashi taso ganiba, Zaid ɗinta taso ace ta gani,,
"Amincin Allah yatabbata agareki, yake ma'abociyar kyawun zuciya da ta sura !!" Jabeer yafaɗa dai dai sanda yaƙaraso gareta,, sunkuyar da kanta ƙasa tayi haɗe da soma wasa da yatsun hanunta, cikin murya ƙasa ƙasa tace dashi "Ina wuni " lapia ƙalou " ya amsa mata yana mai kafeta da idanu.... a hankali ta ɗago idanunta ta saci kallon Jabeer wanda shima kallon nata yakeyi,, dai dai lokacin haɗaɗɗiyar mota ƙirar BUGGATI taƙaraso wajen, dai dai su motar taci wani irin mahaukacin burki,, wanda yasanya hankalinsu da wowa, kan motar,, take zuciyar Zahrah ta buga da sauri, domin kuwa ko tan tama batayi wannan motar Zaid ne.......
(To fa readers ga Zaid ga kuma Jabeer, wanene gwaninku a ciki ? yawan comment yawan typing.......)
*30/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*WRITTEN by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated to my lovely brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*(Agaskia bansan mai zance daku ba masoya na, ina godia ƙwarai da gaske domin kunbani haɗin kai ɗari bisa ɗari, nagode sosai, ina ƙaunarku ako ina kuke masu min shearing book ɗina zuwa wasu groups ɗin, haƙiƙa kuncancanci yabo nakuma yaba muku, Allah yabar ƙauna a tsakaninmu Ameen....)*
*HASSAN 80k* with
*HUSSAINI 80k*
*Inagodia sosai a gareku, Allah yabar zumunci......🤝🏻*
*Chapter 16*
A hankali Zaid yashiga sauƙe glass ɗin motar tasa, fuskarsa a matuƙar haɗe tamkar anyi masa mutuwa, wani irin mummunan faɗuwar gaba Zahrah taji alokacin da idanunta ya sarƙe da nashi, take idanunta sukayi rau rau da su, gyara tsayuwa Jabeer yayi haɗe da kallon Zaid yakuma dawo da kallonsa ga Zahrah wacce ta ke idanunta suka kawo ƙwalla,, *"FATIMA !! "* Jabeer yaƙira sunanta cikin tattausan murya,, kasa amsa masa tayi domin gaba ɗaya hankalinta naga Zaid,, cikin wani irin ƙunan zuciya Zaid, ya yimawa motarsa key, haɗe da soma ja baya, da wani irin ƙarfi yayi ribas ɗin motar haɗe da tada ƙura a wajen da gudun gaske yafigi motar tasa, yafara tafiya, tuni yata da ƙura a wajen da ya tsaya,, wasu irin zafafan hawayene suka shiga gangarowa a kan fuskar Zahrah,, cike da tsananin mamaki Jabeer ke kallonta, *Zahrah* yasake ƙiran sunanta a karo na biyu,, da gudu Zahrah ta juya ta shige cikin gida tana mai fashewa da kuka, Inna da Baffa suna zaune a tsakar gida sai ganin Zahrah sukayi ta faɗo musu tana kuka,,, cike da tsoro Baffa yanufi ƙofar gida, don ganin meke faruwa, amma ko da yafita baitarar da kowa ba, sai ƙurar motar Jabeer da ya gani,, tsuka Baffa yaja haɗe da dawowa cikin gidan, yana cewa "ƴar banza wata ƙilan koransa tayi, wannan mai jar fuskar bansan yazanyi da'ita ba mcheeww !! ".... Zahrah kuwa tuni ta wuce ɗakinta, kan ƴar yaloluwar katifarta, ta faɗa haɗe da sake kuka mai sauti, wani irin ƙuna da ciwo takeji a cikin zuciyarta, shikenan Zaid yatafi, yayi fushi da'ita, inama da tasan haka zata faru, wallahi da bata fita ba, Inasonka Zaid ! Inasonka !! dan Allah kadawo gareni !!!" taƙare maganar tanamai sake rushewa da kuka.......
Gudun bala'i Zaid ke shararawa a kan titi, gaba ɗaya idanunsa sun rufe, wani irin ɗaci yakeji acikin zuciyarsa, tun da yake a duniya baitaɓa jin abun daya keji a yauba, baisan meye sunan abun da yakeji ba, amma tabbas yasan koma menene to bashi da daɗi,, gani yake yi dudduniya babu wanda aka tozarta kamarsa,, ƴan mata buhu buhu ke kawo kansu garesa, amma wai yau shike ɗaukan ƙafansa yaje gun wata banza, bayan haka kuma ya taradda ita tsaye da wani suna soyayya,, da ƙarfi ya bugi steering motarsa haɗe da fidda iska a cikin bakinsa,, take idanunsa suka kaɗa sukai ja tamkar anzuba musu barkono, sam shi bai iya ɓacin rai ba, domin idan ransa ya ɓaci ba sauƙi,,,, faka motar tasa yayi abakin titi haɗe da da danna wani madanni dake jikin motar, take wata ƴar ƙaramar drower ta bayyana haɗe da buɗe kanta, kwalaben tsadaddun wine ne guda huɗu jere a cikin drower'n, jikinsa na ɓari haka yaɗauki kwalbar wine ɗaya, buɗewa yayi haɗe da kaiwa bakinsa, tunda yafara sha bai tsagaita ba harsai da yasha wine ɗin fiye da rabi,, sauƙe kwalbar wine ɗin yayi daga bakinsa, haɗi da sauƙe ajiyar zuciya akai akai, kansa ya ɗora akan kujeran motar haɗi da lumshe idanunsa, ahankali yabuɗe bakinsa, yana mai shaƙan numfashi ta bakinnasa,, yau yafara yin danasani'n kawo kansa wajen ƙasƙantacciyar baiwa, talaka jikar talaka, yau ne rana tafarko a rayuwarsa daya fara da nasanin furta mawa Zahrah kalmar so, wai ma menene so ɗin ? ya yaudari kansa, da ya zubar mawa kansa ƙima da mutumci, tahanyar furta ma Zahrah so, mai yasa baiyi amfani da dukiyarsa da kuma izzarsa ba wajen sawa a ɗauko masa ita, yayi mata fyaɗe ta ƙarfin tsiya ? kansa yashiga bugawa ajikin steering motar yana mai cije laɓɓansa,, yakai kusan 15 minute a wajen kafun daga bisani ya tada motar tasa yabar wajen, tuƙin ganganci yaci gaba dayi domin giya ta soma aiki tuni.. da ƙyar yasamu ya iya kai kansa Maitama inda a can guest house ɗinsa yake....
Yanashiga bathroom ɗinsa yasoma kwarara amai, saida yagama kafun ya wanke bakinsa,, yana fitowa kaitsaye yanufi wata ƴar ƙaramar drower, wata ƴar ƙaramar rover ya ɗauko daga cikin drower'n, haɗe da buɗeta take wasu kwayoyi suka bayyana, iban ƙwayoyin yayi haɗe da watsawa cikin bakinsa, ya kora da ruwan swan....Falo yakoma yazauna, wayarsa dake cikin aljihunsa ya ciro haɗe da cireta a security kai tsaye wajen tura saƙo (message) yashiga bai ɗau wani lokaci yana rubuta saƙon ba yayi sending,, kwanciya yayi flat a kan doguwar kujera, haɗe da lumshe idanunsa, har yanzu yanajin zuciyarsa babu daɗi, yana jin hakanne ba wai don yana son Zahrah ba, yanajin hakan ne saboda yana neman abu wani can daban shima yana nema,, knocking ƙofar falon aka shiga yi, wanda hakan ya tilasta masa tashi daga kwancen dayake yanufi ƙofar,, yana buɗe ƙofar tafaɗa cikin jikinsa, cike da ƙwarewar bariki, tanemi haɗe bakinsu waje ɗaya,, saurin kauda kansa Zaid yayi haɗe da sakarmata wani ɗan guntun murmushi wanda iyakansa kan leɓe, fari tayi da'idanunta haɗe da sake rungumesa ƙam tana mai shaƙan daddaɗan ƙamshin turarensa, janye jikinsa yayi daga nata, haɗe da sanya hannayensa duka biyu ya ɓalla aninayen rigar dake jikinta, take manya manyan breast ɗinta suka bayyana a fili, domin dama idan zata zo wajen shi bata sanya breziya saboda rinjaya da kuma ɗaukar hankalinsa,, hannayensa yasanya duka biyu ya damƙi breast ɗinta, cikin zafi zafi yake murzasu,, hanka ɗata yayi saman kujera, haɗe da ɗaukan fresh milk ɗin dake gefensa, yashiga tuttula mata ajikinta, sarai tagane nufinsa, don haka tuni tacire duk wata sutura dake jikinsa, yazamana babu komai jikinta sai fatar ta,, saida Zaid ya zazzage duka fresh milk ɗin nan ajikinta kafun ya ɗagota tsaye, bakinsa yaɗaura akan breast ɗinta ya shiga tsotsa da ƙarfi ƙarfi, yayinda ya cusa hanunsa a ƙasanta yana wasa da HQ ɗinta, gaba ɗaya Ramla ta shiɗe tafita a hayyacinta, a hankali Zaid ya kwantar da'ita, shikuma ya haye kanta.... Tun Ramla na gurnanin daɗi hatta dawo kukan daɗi, can kuma saiga Ramla na ihun azaba, domin kuwa Zaid ya riƙe wuta bana wasa ba, ihu Ramla keyi tsakaninta da Allah, domin kuwa kurzanta Zaid keyi tamkar anbasa brush ya wanke tayan machine,, ganin ihunta zai damesa yasanya hanunsa ya toshe mata baki,, saida Zaid yasamu gamsuwa kusan na uku kafun ya tashi daga kan Ramla, wanda a yanzu numfashin azaba kawai take fitarwa,, shikansa yasan cewa baiyi mata da wasa ba, domin dama da gayya yayi mata, haka al'adarsa take, idan har ransa ya ɓaci to fa baya samun relief harsai yasamu mace yayi ma ta cin kaca, sannan zaiji nutsuwa a zuciyarsa,, ko ajikinsa haka yashiga bathroom yayi wanka,, ko da yafito yashirya kansa, ɗan makullin motarsa yaɗauka, yafice daga cikin ɗakin ba tare da yace da Ramla ƙala ba..
Da ƙyar Ramla ta'iya yin wanka, harkukan azaba saida takumayi, tabbas yau Zaid yayimata cin da bai taɓa yi mata irin shiba, harwani zut zut wajen nata keyi, amma to yazatayi son kuɗinta ya ja wo mata, kwanciya tayi shame shame, akan gado, haɗe da ɗage ƙafafu sama, acewarta yau dolene HQ yasha iska saboda zafi yake tamkar anbaɗa masa barkono....🤣🤣
Zaid kuwa yanabarin Maitama kai tsaye *TRANSCOP HILTON* yanufa, domin yana da appointment da wani abokin business ɗinsa......
Kuka sosai Zahrah tayi a wannan daren harsai da ciwon kai ya sauƙa mata, wata irin zazzafar soyayyar Zaid ne ke huda jini da jijiyarta, batasan tana mawa Zaid tsananin so ba sai a yau ɗin, haka nan taji wani irin tsanan Jabeer ya ɗarsu acikin zuciyarta, a cewarta duk shine silan faruwar hakan,, haka tayi ta kuka babu mai rarrashinta........
Zaid kuwa bashine yadawo Maitama ba sai wajen ɗaya da rabi na dare (1:30 αм) koda ya dawo ya iske Ramla tana ta sheƙa baccinta tayi ɗaɗɗaya akan gado,, murmushinsa na mugunta yayi,haɗi da shigewa cikin bathroom yayi wanka... Babu tausayi ko lallama acikin sha'anin Zaid, haka yatashi Ramla daga baccin da takeyi, batare kuma da ya tsaya wani romance ɗinta ba, ya sake afka ma ta,, wannan karon kam Ramla hadda cizo ta haɗa masa amma kamar wacce ta ciji ƙarfe, ko gizau baiyi ba,,, iya wahaltuwa Ramla tayi a wajen Zaid, yanzu kam ko ɗaga kanta batayi, saboda tsabar wahala,, haka yaƙaraci sukuwarsa ya sauƙa akanta,, bayan yayi wanka, ya bata wasu ƙwayoyi na kashe zogi tasha, mintuna ƙalilan bacci yayi gaba da'ita,, shikuwa saida yakuma shan wata giyar kafun bacci yaɗaukesa.......
Washe gari....Haka Zahrah tatashi gaba ɗaya jikinta ba ƙarfi, domin jiya kwana tayi da zazzaɓi a jikinta,, a daddafe tayi shirin makaranta ta tafi.....
Haka ta wuni cikin makarantar sukuku batajin daɗin komai, Husnah ce ma mai ƙoƙarin kwantar ma ta da hankali.....
Abu kamar wasa yau Kwana huɗu kenan Zahrah bata sanya Zaid a'idanunta ba,, gaba ɗaya tashiga cikin damuwa bata wani walwalan kirki, ta kunna wayar daya bata ma wai ko ƙiransa zai shigo amma shiru ko saƙo babu balle ƙira,, takan kulle kanta a ɗaki tayi kuka sosai, domin gani take shikenan itakam ta rasa Zaid......
Zaid kuwa fushi yake da'ita amma bawai hakan nanufin yasauya ƙudirinsa akan taba ne,, yana nan akan bakansa kuma alƙawari ya ɗauka sai ya cika sa insha Allahu,, yau kwanansa biyar rabonsa daya sanyata acikin idanunsa, haka nan yaji yauɗin yanason ganinta.....tsab yashirya kansa cikin wani haɗaɗɗan milk colour yard mai kyau da tsadar gaske, sosai kayan ya amshi jikinsa, domin Zaid ba baya bane wajen iya gaye,, daddaɗan ƙamshi ne kawai ke tashi ajikinsa,, motarsa ƙiran Range Rover brown colour yashiga,, kaitsaye Unguwar su Zahrah yanufa, bayan yabiya ta *JABI LAKE* yayi mata siyayya.....
"Ke Zahrah wai mekikeyi ne da haryanzu bazaki tashi kije aikan da nayi miki ba ?" Inna dake tsaye abakin ƙofar ɗakin Zahrah ta tambaya... Cikin sanyin muryarta tace "Gani nan zuwa Inna yanzun zanje"
Hijab ɗinta ta sanya haɗe da zura flat shue ɗinta mai sauƙin kuɗi,,, kuɗi takarɓa a wajen Inna tayi ficewarta... tafe take akan layinnasu amma kanta duƙe yake a ƙasa kamar koda yaushe, kallo ɗaya zakai mata kafuskanci cewa tanacikin damuwa,, tazo shiga kwana kenan shikuma ya danno hancin motarsa,, sam bata lura da shiba kasancewar kanta duƙe yake a ƙasa,, cak ya tsaida motar tashi, yana mai kafeta da mayun idanunsa,, ci gaba da tafiya Zahrah tayi domin bata lura da shiba,, a hankali yabuɗe murfin motar haɗe da fitowa, cikin takunsa na ƙasaita yasoma bin bayanta,, kasancewar a hankali take tafiya yasanyashi saurin cimma ta,, "Ina zakije ?" muryarsa ta doki dodon kunnenta,, da sauri tajuyo gareshi, aikuwa tabbas shiɗinne, take taji wani irin shouck a jikinta, sakamakon karabkiya da idanunsu sukayi da juna, idanunta ne sukayi rau rau dasu, yayinda ƙwalla tacikasu tab,, kallon juna suka shiga yi har na tsawon wasu mintuna, batare da kowannensu ya ɗauke idonsa daga kan na ɗan uwansa ba,, "Ina zakije ?" yasake mai maita tambayar tasa gareta...Ƙasa tayi da kanta yayinda ƙwallan dake cikin idanunta suka gangaro,, cikin murya mai sanyi tace "Aika" kansa ya gyaɗa haɗe da miƙo mata hanunsa yace "Zo mu koma gida" ba musu ta miƙa masa hanunta yakama, wani irin abune yaratsa jiki da zuciyarsu, su duka biyun,, hanunta dake cikin nasa yashiga murzawa duk da cewa tafiya suke,,, ƙofar gefen mai zaman banza ya buɗe mata ta zauna, shikuma ya koma gefen driver yayi mawa motar key,, mintu 2 yakawosu ƙofar gidansu Zahrah'n.... kafeta yayi da idanunsa masu riki tata, yayinda yake sauƙe numfashi a hankali.......
*Happy New Month 🍝🥂*
*1/November/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*WRITTEN by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated to my lovely brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
```{{In ƙaramuku yawan typing, kullum batun kenan🤦🏼♀waiku don Allah bakwa tunanin nima ina da abubuwanyi da yawa ne ?, bafa typing bane kaɗai aikina, ina da miji, ina zuwa school, kuma komai yana buƙatar lokaci, saboda haka kuyi haƙuri, hakan ma ina ƙoƙari ni aganina...}}```
*Chapter 17 to18*
Tsawon lokaci Zaid yaɗauka yana kallon Zahrah batare da yace da'ita ƙalaba, ɗan nisawa yayi haɗe da sauƙe ajiyar zuciya, "maiya sameki kike kuka ?" yayi mata tambayar cikin taushin murya,, ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba haɗe da cewa "to bakai bane katafi kabar..... !" saurin toshe bakinta tayi jin ɓarakar da take shirin yi,,, murmushin gefen baki Zaid yayi, haɗe da yi mata wani irin kallo, "umm ƙarisa mana inajinki" yafaɗa da sassanyar murya...Sunne kanta ƙasa tayi domin kuwa ba shakka suɓutar baki na nema yakaita gajin kunya,, gyara
zamansa yayi haɗe da cewa "Waye shi ?"...ɗan satar kallonsa tayi cikin siririyar muryarta tace " Shi wa ?"... "ba'a dawomin da tambaya, amsa kawai nake nema, don haka faɗamin wanene shi...?" sai yanzu tagano abun dayake nufi,, jitayi gaba ɗaya jikinta yayi sanyi.. "Wanine !!" tabasa amsa cikin ɗarɗar... Kansa kawai ya kaɗa haɗe da taɓe baki, satan kallonta yayi ta gefen ido " kinasonsa kenan ?" ya jefo mata tambayar da ba ta shirya amsar sa ba... Satan kallonsa takumayi akaro na biyu, haɗe da girgiza kanta alamar a'a,, yaga abun datayi amma saiya share yayi kamar baigani ba, domin so yake tabuɗi baki tayi magana.... Tambayar yakuma maimaita mata,, cikin sanyi tace "A'a" numfasawa yayi haɗe da cewa " to wakike so ?"... Dum haka ƙirjinta ya buga, domin bata da iko ko zarran da zata fuskancesa gaba da gaba tace shi takeso, ko ma ba haka ba ita macece mai alkunya da kuma ƙima, furtawa namiji kalmar so, awajenta ba dai dai bane,, bata taɓayi ba bakuma zatayi azarɓaɓi ba.... "kinyi shiru" yafaɗa dai dai sanda ya ɗau gorar ruwan swan yakai bakinsa, idan tace dashi babu ƙwarai ta cuci kanta da zuciyarta ne, idan kuma tace dashi akwai to hakan nanufin yankewar alaƙarta dashine, saboda zaiga kamar bashi ta ke so ba....
Murmushi yayi haɗe da aje goran ruwan dake hanunsa, "MY ZAHRAH !!" yaƙira sunanta da muryarsa mai kashe mata jiki,, "Na'am !" ta amsa masa itama cikin sassanyar murya.... Ahankali ya lumshe kyawawan idanunsa haɗe da jingina bayansa ajikin kujeran motar,, kallonta ta maida kansa, tunda idanunsa a rufe suke yanzu zata samu chance ɗin kallonsa da kyau,, tabbas Zaid kyakkyawane na gani a nuna, yana da abubuwan ɗaukar hankali a tattare dashi, tanason Zaid sosai, ko don kyawunsa ma ya cancanta aso shi,... A hankali ya buɗe idanunsa da suka soma sauya launi daga farare zuwa ja, wani irin zubawa tsikar jikinta sukayi, sakamakon haɗuwar idanunsu waje ɗaya, wayyo Allah Zaid yana da mayun idanu masu matuƙar kyau da ɗaukar hankali, haƙiƙa kallon idanun Zaid sai wanda ya daure, domin suna da saurin kashe jiki da sauƙar da kasala... " Banagajiya da kallonki, amma ke kina gajiya da kallona bakima so ki kalleni, maiyasa ?" ya tambayeta dai dai lokacin daya ware idanunsa akan cikakkun breast, ɗin ta, da tudunsu suka bayyano ta wajen hijabin dake jikinta, sunkuyar da kanta ƙasa tayi tana mai wasa da yatsun hanunta, batare da tabashi amsaba...
"Oh Allah wannan yarinyar zata kasheni, lallai randa na kamaki bazan miki da sauƙi ba !!" Zaid yafaɗa a cikin zuciyarsa, shi bakomaine ma yake basa takaici da'ita ba kamar rashin magana da batayi, daga eh sai a'a kawai take cewa shi wallahi haushima take basa...
Ita kuwa Zahrah batasan wainar da Zaid ke toyawa ba, saboda kanta na ƙasa, shikuwa gogan tudun breast ɗin ta kawai yakafe da ido, harwani haɗiye yawu yake, tamkar (bestyna Jikar Hajiya tasamu zazzafan balangu,lol)... Daddaɗan sauti ne yasamo tashi daga cikin wayarsa, da alama ƙira ne yashigo wayar tasa "Baby" shine sunan dake yawo akan screen ɗin wayar ɓaro ɓaro, wani irin dokawa zuciyar Zahrah tayi, domin kuwa taga sunan dake yawo akan screen ɗin wayar tasa... A hankali yaɗauki wayar haɗe da karawa akan kunnensa, tunda ya ɗauki wayar baice ƙalaba saidai murmushi kawai da ya yawaita akan fuskarsa, hakan kuwa ba ƙaramin ƙona zuciyar Zahrah yayi ba, wato dai dama yana da budurwa,, har ya cire wayar akan kunnensa banji yace ƙala ba, "Ina wayar dana baki ?" yayi maganar cikin halin ko inkula, "Tana nan" tabasa amsa a taƙaice domin wani haushi ne ya tokare ma ta maƙoshi,, "Maiyasa bakya amafani da'ita ?" "Babu amfanin hakan " takuma basa amsa ataƙaice, kallonta yayi haɗe da fashewa da dariya harsai da fararen haƙoransa suka bayyana,, tamkar wani tv haka Zahrah tayi ƙasaƙe tana kallonsa bakaɗan ba yayi kyau da yana dariyan, lalle Zaid ƙarshene wajen kyau,, saida yayi dariya sosai kafun ya tsagaita haɗe da kallonta "Kishi ko Ƴan mata ?" turo ɗan ƙaramin bakinta gaba tayi haɗe da yi masa hararan wasa, lumshe idanunsa yayi gami da buɗewa alokaci guda, "Soyayyata tayi miki mummunan kamu amma zurfin ciki ya hanaki faɗa, shikenan to ni zantafi sai kificemin a mota ko" yaƙarasa maganar yana mai tamke fuska tamkar bashine ya gama dariya yanzu ba....Hmm Zahrah uwar kuka, take idanunta sukayi rau rau dasu, cikin muryar ta mai sanyin amo tace "Kayi haƙuri !!" kallonta ya kuma yi alokaci na barkatai "Hakan nanufin kin amince kina so na kenan??" A hankali tashiga kaɗa kanta alamar "eh" Kyakkyawan murmushinsa mai sauti yayi haɗe da kashe mata idonsa ɗaya, da sauri tayi ƙasa da kanta, tana ɗan murmushi, tana mai kuma jin wani irin farinciki na ratsa zuciyarta, ko ba komai yanzu ya fahimci cewa akwai soyayyarsa acikin zuciyarta.... Ledan dake bag sit ɗin motar ya ɗauko haɗe da miƙo mata cikin murya mai sanya nutsuwa dakuma nuna tsantsar soyayya yace "wannan kyautane a gareni, sauran kuma special gift na amsar soyayyata da kikayi very soon yana nan zuwa, amma bana fara baki wata kyauta..." ya ƙare maganar yana murmushi. Wani ɗan ƙaramin box ya ɗauko daga cikin wani keɓaɓɓen waje dake cikin motar, box ne mai kyaun gaske wanda aka ƙawata jikinsa da wasu irin furanni masu kyawu da ɗaukar hankali, koda ya buɗe box ɗin wani kyakkyawan zube ne ya bayyana, wanda akayisa da zallan gold, murmushi Zahrah tayi domin kuwa sosai zoben yayi mata kyau, hanunsa yamiƙa mata, alamar ta bashi nata hanun, cike da kunya tamiƙa masa lallausan hanunta, saida Zaid ya sauƙe ajiyar zuciya, lokacin da taushin fatar Zahrah da tasa suka haɗe waje guda,, kama hanunnata yayi da kyau haɗi da ciro zoben yasanya mata cikin yatsarta ta uku, ɗas zobennan yazauna acikin yatsar Zahrah, tamkar angwada hanunnata kafun ayishi, batasan sanda tayi murmushi ba harsaida haƙwaranta suka bayyana, bakomai yasa hakanba, face kyaun da taga zoben yayi mata a hanunta, dama ita mutumce mai tsananin son kayan ado, rashi ne yasanya ta dangana komai nata ga Allah.... "Cire zobennan daga yatsarki dai dai yake da cire sona azuciyarki, please ki tausayamin kada kicire domin ina tsananin sonki My Zahrah ta, ke ɗin ta dabance a wajena, kimin alƙawari bazaki taɓa cire zobennan ahanunki ba, har abada !!" Yanda yayi maganar idan ka kallesa zaka rantse da Allah cewa bashi bane, domin kuwa sam baiyi kama da irin mutanennan da zasuna baran soyayya ba, Wani irin farinciki haɗe da tsananin daɗi, su suka shiga huda zuciyar Zahrah, "Haƙiƙa Allah yayi mata babban zaɓi, har abada bazata taɓa daina mamakin soyayyarsu da Zaid ba, domin kuwa duk da kyawunta wallahi Zaid yakerewa ajinta, tayi imani da cewa Zaid ba'irin mazajennan bane, da ake samunsu saka ka acikin gari, irinsu Zaid sai wacce take da rabo da kuma tsananin sa'a ke samunsu, tabbas itakam tana da sa'a, tana kuma daɗa godemawa Allah ako dayaushe.." "My Zahrah !!" yakatsemata tunaninta tahanyar ƙiran sunanta,, "Nayi maka alƙawari bazan taɓa cire zobennan ahanuna ba, har gaban abada,harsai munhaifi ƴaƴa da jikoki, da shima zan mutu" Zahrah tafaɗa cike da kunya. .. Baki kawai Zaid ya hangame yana kallon Zahrah, bakaɗan ba kyawunta yaƙaru da ta ke magana, ashe haka shugar baby'ntasa take kyau intana magana baisani ba?.. Ɗan numfasawa yayi haɗe da gyara zamansa cike da salon yaudara, yace "Zantafi Dad ɗina yana ƙirana, amma gobe zandawo saboda nasake ganin wannan kyakkyawar Baby'n tawa !!".... Saurin cusa kanta cikin cinyoyinta tayi tana murmushi, (Allah sarki basaban ba su Zahrah anji kalaman love,lol)... "Inasonki My Zahrah !!" yafaɗa cikin shauƙin ƙauna,, yanzu kam ɗago da kanta tayi haɗe da watsa masa kyawawan idanunta, wani irin zubawa tsikar jikin Zaid yayi domin kuwa wani irin kallo Zahrah keyi masa "Nima Inasonka !!" Zahrah tafaɗa tana mai shagwaɓe fuska, haɗe da karya wuyanta gefe,, har abada bazai taɓa gajiyawa da murmushi ba, domin yanzuma murmushin kawai yayi mata,, cike da nutsuwa ta buɗe murfin motar, bayan ta ɗauki ledan daya tursa sa ta kan saita ɗauka,, wani irin kallo sukamawa junansu, kafun tashige cikin gida,, Zaid yana ganin shigewarta ya saki wata irin mahaukaciyar dariya, hadda riƙe ciki, dariya sosai Zaid yakeyi tamkar wani mahaukaci, bakomai yasa hakanba, face tunowa da kalaman Zahrah dayayi, "Wai ita da shi zasu haifi ƴaƴa hadda jikoki " Lallai yariyarnan ta haukace... Yakuma fashewa da dariya, saida yayi dariya sosai, kafun ya tsagaita hanunsa yasanya yasoma shafa, kwantaccen sajen dake kan fuskarsa,, " Very soon zakiga Special gift ɗinki !!" yafaɗa ahankali, kansa yajinjina haɗe da fidda iska tacikin bakinsa, key yayi wa motarsa, haɗi da harbata kan titi, yau ƙal yakejin zuciyarsa domin kuwa yanzu yafara buga game ɗin yana da tabbacin cewa kuma bazaiyi game over ba.....
Zahrah kuwa tanashiga cikin gida da lale marhaban, Inna ta tarbeta, domin tuni a leƙe leƙenta da ta sabayi waje, ta leƙosu cikin mota,, amsar ledan Inna tayi, haɗe da bajewa kan taburma tashiga ciro abubuwan dake cikin ledan, still kayayyakine na kanti masu kyau da tsadar gaske, sai kuma mayukan shafa, dasu powder, hadda su tsadaddun turaruka, gefe kuwa ɗaurin kuɗine ƴan dubu dubu masu yawan gaske,, jiki na rawa Inna ta ɗauka haɗi da kaiwa kan hancinta tashiga shinshinasu, "Um kuɗi masu gidan rana, kuɗi maganin damuwar babba da yaro, kuɗi masu saiwa mutum ƴanci, kuɗi basu zuwa gareka saikana da rabo, ni dai Allah yakashe ya bani !" Inna tafaɗa cike da jindaɗi,, kai kawai Zahrah ta girgiza, har cikin zuciyarta batajin daɗin abun da Inna da Baffa keyi, domin hakan kamar zubar mata da mutumci ne, saboda iyayen ƙwarai basa haka,,, wasu ƴan tsiraru daga cikin kuɗin Inna ta kama hanun Zahrah ta damƙa mata, haɗe da cewa "Saura kifaɗamawa wancan ƙwarnafaffen Baffan naki cewa Zaidu yaron arziki yazo, ni dake ne, tattare kayayyakinnan maza kisasu a ɗakinki, domin ban buƙatarsu, kuɗi ne nawa kuma na samu, saura kwana kaɗan nima nafara sanya lasa lasai, hmmm nimafa saina zama wata babbar ƙwaruwa acikin garin Abuja'nnan, domin kuwa Allah yabani bazan tauyewa kaina haƙƙi ba ehe !!" Inna taƙare maganar tana mai turo ɗaurin ɗankwalin ta gaban goshi,, ita dai Zahrah batace da'ita ƙalaba, saima tattare kayan tayi tanufi ɗakinta...
Dariya sosai Abid keyi hadda tsugunnawa ƙasa, sosai labarin da abokinnasa yabasa yasanyashi nishaɗi... Ɗan tsagaitawa da dariyan yayi haɗe da maida kallonsa ga Zaid wanda hanunsa ke ɗauke da glass cup yana sipping alcohol, "Gaskia kai ɗin Shu'umi ne, amma miye next target ɗinka ??" Wani irin murmushi Zaid yayi wanda yafiyinta idan zai gudanar da mugunta, *"RAPING ɗinta zanyi (Fyaɗe)"* Zaid yafaɗa a taƙaice.....
((😳😳😳 Readers...... 🙆🏻🙆🏻))
*3/November/2019*
*MRS SARDAUNA......*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
Phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated to My Brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD* *@fatymasardauna*
*Editing is not allowed📵*
*Chapter 19 to 20*
Jinjina kai Abid yayi haɗe da kallon Zaid, "maiyasa bazakayi amfani da soyayyar da take yi maka ba wajen biyan buƙatan ka, dole sai kayi raping ɗinta??" Abid ya tambaya, Murmushi Zaid yayi haɗe da sanya haƙoransa ya cije kyawawan lips ɗinsa, batare dayace da Abid ƙalaba, yaci gaba da shan wine ɗinsa,, sarai Abid yafahimci abunda Zaid ɗin ke nufi don haka shima baisake ɗago zancen ba, saima ɗaukar wayarsa da yayi yasoma latsa ta....
Kwance take akan ƴar yaloluwar katifarta, gaba ɗaya hankalinta da tunaninta sunaga tunanin masoyinta Zaid, wayar da Zaid yabata ne tasoma kara alamar shigowar ƙira, hanunta har rawa yake wajen son ɗaukar ƙiran, domin tana da yaƙinin cewa Zaid ɗin tane... "My Zahrah na !!" Muryar Zaid yadoki cikin dodon kunnenta, lumshe idanunta tayi alokaci guda haɗe da buɗesu, sosai taji nishaɗi na ratsa zuciyarta,, "Na'am !!" ta amsa masa in a low voice ɗinta, Zaid dake kwance kan makeken gadon sa,gyara kwanciya yayi haɗe da ɗaura hanunsa kan joy stick ɗinsa, haƙiƙanin gaskia ko muryan Zahrah yaji to fa sai sandar girmansa ta motsa, wani irin muguwar sha'awar Zahrah yakeji, ba dare ba rana, "Bakiyi bacci ba ??" yayi mata tambayar yana mai ƙasa da muryarsa,, saida ta ɗan ja numfashi kafun tace dashi " Eh" kansa ya jinjina kamar dai tana ganinsa, sake lafewa akan gadon yayi, haɗe da ƙasa da muryarsa sosai yanda yatabbatar da cewa zataji a jikinta, " Soyayyata ce tahanaki bacci ko !! ?" ya ƙare maganar yana mai rumtse idanunsa,, gaba ɗaya ji tayi tsikar jikinta ya shiga zubawa, take kuma kasala ta lulluɓe mata jiki, shiru tay na ɗan wani lokaci, domin takasa amsa masa tambayarsa, a zuciyarta kuwa mamaki take ga me da yanda Zaid ke sanin duk irin halin da take ciki,,...."My Zahrah !!" yasake ƙiran sunanta,, yanzu kam gaba ɗaya rasa control ɗinta tayi, domin yanda yake ƙiran sunan nata da salo acikinsa,, "Umm" tafaɗa cikin muryar shagwaɓa wacce batasan ma tayi taba,, "Ya Allah !!" Zaid yafaɗa acikin zuciyarsa, domin bakaɗan ba salon shagawaɓan nata yatafi dashi, yana matuƙar son mace shagwaɓaɓɓiya, lallai Zahrah tacika mace hundred percent,, "Naga kamar kinajin bacci, zan barki sai da safe ko Dear ?" yayi hakanne don gano wani irin yanayi take ciki,, " Ni banjin bacci fa !!" Zahrah tafaɗa still a shagwaɓe, (Like Jikar Hajiya, da Sugar dady'nta,lol 🙈)
Wani irin munafukin murmushi Zaid yayi domin kuwa yasamu abun da yakeso,, Zahrah kuwa takurewa tayi kan lasheshshiyar katifarta, babu abun da take fitarwa sai numfashi a hankali hankali, hakanan ta tsinci kanta cikin wani irin yanayi, mai wuyar fassaruwa,, lumshe idanunsa Yayi yana mai sauraran sauƙar numfashinta acikin kunnensa, sosai hakan ke yimasa daɗi, sai da suka kwashe kusan mintuna takwas, a haka kafun Zaid ya sauƙe ajiyar zuciya haɗe da da cewa "Tunanin mekikeyi ?" murmushi mai sauti Zahrah tayi, haɗe da cewa " nima bansani ba amma dai haddakai a cikin tunanin" ƙasa ƙasa Zaid yayi dariya, batare da taji saba....Sosai ya daure zuciyarsa sukayi hira, kalaman soyayya kawai yayita zuba mata, tun Zahrah na noƙewa har tasaki jiki, saida dare yayi sosai kafun sukayi sallama da juna, bayan ya tursasa ta faɗamasa cewa tana sonsa... Zaid yana aje wayar yasanya hannayensa duka biyu yakama kansa, wani irin baƙon al'amari yakeji a tattare dashi, haushin kansa ma yakeji, ba ɗabi'arsa bane yawan magana, amma sai gashi dolensa ya koya saboda Zahrah,, ƙwayoyin paracetamol ya haɗiya haɗe da ƙorawa da ruwa, domin ɗan maganan dayayi harkansa yafara ciwo.... Zahrah ma dai haka aka kwana a najin feelings, ƴan mata anshiga baƙon yanayi........
Bayan Sati Biyu....
Wata irin gagarumar shaƙuwa haɗi da soyayya ne, suka shiga tsakanin Zaid da Zahrah, wani irin sabo sukayi naban mamaki, sosai soyayyar Zaid ta faɗa ɗa a cikin zuciyar Zahrah, Zaid yayi matuƙar jajircewa wajen inganta soyayyarsa ga Zahrah, yayi mata babban ɗauri da soyayyarsa, kulawa sosai yake bata, koda yaushe suna cikin waya ba dare ba rana,, kuɗi kuwa sosai yasake mawa su Baffa da Inna, domin shi kuɗi ba matsalar sa bane,, Zahrah kuwa harta gaji da amsar kyaututtukansa, gaba ɗaya yanzu kayan da take sanyawa masu tsadar gaske ne, duk kuma aikin Zaid ne, lokaci ɗaya Zahrah ta sanja, mayuka masu tsada take amfani dasu, jikinta yayi fresh, yayinda a kullum surarta ke ƙara haukatar da Zaid cikin kogin sha'awarta,, zuwa yanzu Zahrah tayi sabon da taɗauki duk wani yarda da amincewarta tabaiwa Zaid, yanzu Zaid shine komai nata, son da take masa na da banne,,
Ƙarfe tara na daren yau, Zaid yaƙira ta a waya,, cike da shagwaɓa kamar yadda tasabar masa taɗauki wayar, "Baby nayi fushi, wanin yau duk baka ƙira ni ba sai yanzu !!" Zahrah tafaɗa tunkan Zaid yayi magana, tana mai tura ɗan ƙaramin bakinta gaba, murmushi Zaid yayi haɗi da sauƙe ajiyar zuciya, cikin muryan kasala, yace "My Zahrah, yau nagaji da yawa, saboda wuni nayi a office, amma kinsan ako da yaushe kini raina, domin bayanda za'ayi mutum yamanta da rayuwarsa !!" murmushin jin daɗi Zahrah tayi haɗe dayin fari da idanunta, tamkar yana ganinta, "naji daɗi dana zama rayuwarka, amma kasan nafi sonka ko ?" murmushin gefen baki Zaid yayi haɗe da cewa "Gobe dukanmu zamu tabbatar da wa yafi son wani tsakaninmu, domin kuwa gobe zanbaki special gift ɗinki, na tabbatar bazaki manta da wannan ranan ba, har gaban abada !!" murmushi Zahrah tayi haɗe da cewa "Bawani nan kaidai kace hakane don kawai ka kawar da zancen, amma aikasan nafi sonka, Ina tsananin sonka My Zaid, bantaɓa soyayyaba, kai ka koyamin, sai gashi kuma nafika iyawa " Zahrah taƙare maganar tana mai kashe idanunta ɗaya, tamkar tana gabansa,,, dariya sosai yayi, domin ƙwarai maganar Zahrah tabasa dariya,, "My Zahrah nima inasonki sosai, kikulamin da kanki kinji tawan, banso ki manta dani koda na second ɗaya ne acikin rayuwarki !!" ƙit ya kashe wayan bayan yagama faɗan hakan,, murmushine ya ƙwace ma Zahrah, gaskia tayi dacen masoyi, idan har ta auri Zaid to zata iya cewa, itaɗin ta musammance, tanakuma da babban sa'a acikin rayuwarta.......
Washe gari
SATURDAY....
Yau tunsafe takejin wani irin matsanancin faɗuwar gaba, wanda batasan dalili ba, gashi taƙira wayar Zaid a kashe, sam kashe waya ba al'adar Zaid bane ita tasan haka,, amma sai ta alaƙanta hakan da cewa ko yana baccine,, Zaune take a tsakar gida tayi jigum, ko abun karyawanta ma taƙi ci, gaba ɗaƴa jitake duniyar batai mata daɗi, komai yafice mata a cikin rai, muryar Habibie Zaid ɗinta kawai takeson ji, domin yasabar mata kowacce safiya, suna tare a waya,, Inna dakanta tafuskanci sauyawar Zahrah'n domin komai cikin sanyi takeyinshi,,
"Waike Zahrah lafiyarki kuwa ? tun ɗazu kin yi wani sukuku dake, abincin karyawanki ma gashi can a kicin (kitchine)), ko sawa a bakinki bakiyi ba, mai ke damunki ne wai ??" Inna dake tsaye gefen Zahrah tatambaya,,
"Banjin daɗi ne Inna, tunsafe gabana faɗuwa yake, gani nake tamkar wani abu zai sameni, wallahi Inna tsoro nakeji !!" Zahrah taƙare maganar lokacin da idanunta suka cika da ƙwalla,,
"Tsoro kuma ?, tsoron me kuma Zahrah ? to Allah ya kyauta, inma wankin danace kimin ne bakyaso, ai basai kin min ƙarya ba " Inna taƙare maganar tana nufar hanyar kicin,,, Zahrah dai batace ƙalaba saima ƙara faɗawa duniyar tunani da tayi.....
11:00 am wayar Zahrah tasoma ruri alamar shigowar ƙira,, har tuntuɓe tayi, agarin zuwa ɗaukar wayar domin a tunaninta Zaid ɗinta ne, yaƙira,, Besty Husnah, shine sunan dake yawo akan screen ɗin wayar,, cikin rashin kuzari ta ɗauki wayar haɗi da karawa akan kunnenta, "Hello, Zahrah, wai ina kikene kinfasan 11:30 am, muna da lecture amma haryanzu baki zoba, kinkumasan dai har text zamuyi yau, please kiyi sauri kada ki makara !!"
Ajiyar zuciya Zahrah tasauƙe haɗe da cewa "Wallahi duk yau banjin daɗi ne ƙawata, amma ganinan zuwa, gabana ke yawan faɗuwa, ba don text ɗinnan bama da bazan zoba gaskia !!" Zahrah tafaɗa cike da damuwa,
"SubahanAllah, faɗuwar gaba kuma Zahrah, to Allah yatsare, kidai riƙe addu'a, sai kin shigo" Husnah tafaɗa cike da kulawa..
Cike da kasala Zahrah ta aje wayar bayan taturamawa Zaid saƙonnin waya (text message's) kusan guda shida kenan, tatura masa daga safe zuwa yanzu,kan cewa tanemesa wayarsa akashe....
Wanka tayi sharp sharp, mai kawai ta shafa, ajikinta, bata tsaya wani fente fente ba tazura, wata maroon ɗin doguwar riga, wacce daga samanta har ƙasanta, maɓallai ne,, sosai rigan ta amshi jikinta, farin hijabi ta sanya, haɗe da ɗaukar jakar makarantarta, ta rataya akan kafaɗarta,,, sama sama tayi mawa Inna dake zaune atsakar gida tana taunar ƙashin kaza sallama,, tana sanya ƙafarta a ƙofar gida, faɗuwar da gabanta keyi ya tsananta, haka zuciyarta ke bugu da sauri sauri, sunan Allah tashiga ƙira acikin zuciyarta,, a hankali take tafiya tamkar wacce ƙwai yafashe mawa ajiki,, saida tayi tafiya mai nisa tsakaninta da gida, kafun ta ankara da wata baƙar mota jeap, dake binta a baya,, storo ne yakama ta don haka sai ta soma sauri,, da wani irin gudu motar tasha gaban Zahrah,, harsai da ƴaƴan hanjin cikin Zahrah suka kaɗa,, da hanzari wasu ƙattai su biyu suka fito daga cikin motar, ƙoƙarin soma ja da baya Zahrah tayi, amma ina tuni ƙattan nan sun cimmata, ɗaya daga cikinsune yakamota, haɗe da tukui kuyeta waje ɗaya, yayinda ɗayan kuma ya ciro wani farin hankacif (handkerchief) daga cikin aljihunsa ya manna mata akan hancinta,, take numfashinta yaɗauke, ta faɗa jikin wanda ke riƙe da'ita, buɗe murfin motar ɗaƴan yayi suka turata ciki, ba ɓata lokaci suma suka shige, driver ya tashi motar suka cilla kan titi......
Tafiya sukayi mai nisan gaske, tamkar zasubar cikin garin Abuja, still Zahrah na sume batasan inda take ba, suna isa gaban wani makeken gida mai kyau da tsari, gate ɗin gidan ya wangale, suka tura hancin motar ciki,, a wani rumfa dake cikin gidan sukayi parking, ɗaya daga cikin mutanen dasuka ɗauko ta ne, ya ɗago ta a wuyansa, yanufi wata ƙofa wacce ita kaɗaice ƙofa acikin kanfacecen compound ɗin gidan,, kan wani makeken gado, ya wurgata, haɗe da zaro wayarsa ya ɗaura akan kunnensa,, "Oga komai ya kammala !!" wannan ƙaton yafaɗa cikin wata bamagujiyar muryarsa marar daɗin amo,, "Okay" kawai naji yace haɗe da cusa wayartasa cikin aljihu,, fita yayi daga ɗakin haɗe da danna mawa ƙofar ɗakin da Zahrah ke ciki makulli,, yayi ficewarsa......
( 😢kuyi haƙuri banmuku long typing ba kaina ke ciwo shiasa...)
*5/November/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Brother Khabier....*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowe📵*
*NOTE: Abu nafarko da nakeso ku fara sani, shine ko wani ɗan adam da irin tasa ƙaddarar da Allah yatsara masa, kowani musulmin ƙwarai anaso ya yarda da ƙaddara mai kyau ko akasinta, da yawanku sun min ca akai, akan kada na bar Zaid ya aikata wa Zahrah fyaɗe, wasun ku sunce hakan bai daceba, wasunku kuwa sunce, saboda ita marainiƴa ce kada hakan yafaru akanta, wasuko cewa sukayi idan haka yafaru labarin ya ɓaci,, hmmm wallahi kuna ban mamaki da sukace wai kada haka tafaru da Zahrah saboda ita marainiya ce, tambayata anan shine, Shi maraya Allah baya sauƙar masa da mummunar ƙaddara ne??, baya yi wuwa, don kina/kana, matsayin maraya ace Allah bazai haɗaka da mummunar ƙaddara ba, kowa aduniya da irin tasa ƙaddarar da Allah yarubuta zata faru akanshi, kuma wallahi babu wanda ya isa ya hana ƙaddarar mutum ta riskesa,matuƙar Allah yatsara hakan, duk da cewa wannan ƙageggen labari ne, bawai da gaske bane, amma yazama dole nayi muku nuni da cewa, ƙaddara tana rayuwa ne ajikin ɗan Adam tamkar yadda jininsa ke gudu, acikin jikinsa, yanda kuma ba'a iya kaucemawa mutuwa, haka ma ƙaddara ba'a iya kauce mata, sai dai fatan Allah yakawo da sauƙi,, mata nawa akai mawa fyaɗe kuma marayu ba uwa ba uba, shi fyaɗe ba wai sai kana da uwa ko uba, ake yi maka shiba, ƙaddara ne da take faɗawa kan kowacce mace, idan har Allah (S.W.A) ya ƙadarta faruwan hakan.... Masu cewa idan Zaid yayi mawa Zahrah fyaɗe labarin yaɓaci, inaso ku saurara kuji, ko wani labari da irin nasa tsari da salon da yake tafiya, saboda haka ni nawa da'irin salon da yake tafiya kenan, saikuyi haƙuri idan ranku ya sosu, nima nawan ran ya sosu, kunga kenan dukan mu sai muyi haƙuri da juna....*
*Chapter 21 to 22*
2:00 pm.....
A hankali Zahrah tasoma buɗe idanunta da sukai mata, matuƙar nauyi, dishi dishi take ganin komai, yayinda ƙafafunta ne kawai ke motsawa ajikinta,, sannu a hankali idanunta suka soma washewa, gaba ɗaya ganinta yadawo, da haɗaɗɗen zanen p.o.p n dake saman ɗakin tafara yin tozali, saurin kulle idanunta tayi, take komai yashiga da wo wa cikin kanta filla filla, a matuƙar firgice ta tashi daga kwancen da take, haɗe da soma bin ɗakin da ta ganta kwance am ciki da kallo,, wani irin ihu ta kurma, haɗe da fashewa da kuka lokaci guda,, da gudu ta nufi wata ƙofa wanda take zaton nanne ƙofar fita daga ɗakin,, da iya ƙarfinta tashiga bubbuga ƙofar ɗakin tana kuka mai tsuma zuciya... "Kutaimakeni dan Allah, kubuɗemin natafi gida dan Allah na roƙeku, mai nayi muku kuka kamani !!?" abun da Zahrah ke faɗa kenan tana kuka,, sosai Zahrah ke dukan ƙofar tana kurma ihun neman agaji, amma ina ko gizau ƙofar batayi ba, bakuma alamar da wani wanda zai kawo mata ɗoƙi, tun Zahrah na bugun ƙofar da duka ƙarfinta, har dai gaba ɗaya ta rasa kuzari,, kuka sosai takeyi, a hankali ta zame jiki ta zauna ajikin ƙofar tana mai ci gaba da ruskar kuka,,,, "Wayyo Allah na, don Allah kuyi haƙuri, kubarni nayi tafiya ta !!" Zahrah tafaɗa cikin da sheshshiyar muryarta, wanda kuka yasa lokaci ɗaya ta daina bada amo mai ƙarfi,, "Wayyo Allah na Zaid kazo kataimakeni !!" Zahrah tafaɗa cikin muryar gajiya da kuka....Zahrah tayi kuka tamkar ranta zai fita, tayi ihun harta gaji, amma babu mai taimakonta, tun muryarta na iya fita haryazamto baya fita, idanunta kuwa tamkar an baɗa mata dakakken barkono haka sukayi jajur dasu, lokaci ɗaya wani irin masifaffen ciwon kai, yarufe ta, take jikinta yaɗauki zafi zau tamkar wuta, takure kanta tayi waje ɗaya, tana mai zubar da hawayen tausayin kanta, "Wayyo inama da Zaid yasan halin da take ciki tabbas tasan da yazo ya taimaketa...Abu kamar wasa zazzafan zazzaɓine ya rufe duk jikinta, a sanadin kukan da tayi.....
5:00 pm
key ɗin dake hanunsa ya sanya a cikin wajen sanya key da ke jikin ƙofar, take ƙofar ta fita a lock,, hannayensa dake ɗauke da zara zaran gashi, yaɗaura kan handle ɗin ƙofar, haɗe da turawa,, Ahankali ƙofar tashiga buɗewa,, Zahrah da jikinta ke rawar sanyin zazzaɓi, tayi saurin ɗago kanta ta kalli bakin ƙofar,, daddaɗan ƙamshinsa shiyafara kawo ziyara cikin ɗakin kafun shi kansa,, ƙafarsa tafara kallo, dake sanye cikin wasu baƙaƙen takalma, sanye yake da black 3 guater jeans, yayinda rigar jikinsa takasance Sleevless T-shirt white colour an mata rubutu da black paint,, kansa kuwa sanye ƴake da facing cap, black colour...
Cikin wani irin muguwar razana haɗi da kaɗuwa, Zahrah tamiƙe daga tsugunnen da take zumbur, haɗe da kafesa da rinannun idanunta, bakinta ne ya soma rawa, alamar akwai abun da takeson furtawa, amma takasa,, a hankali yasanya hanunsa ya cire facing cap ɗin dake kansa, take asalin kamanninsa suka bayyana,, wannan murmushin nasa daya saba yi ako da yaushe ɗauke a kan fuskarsa,, "My Zahrah !!" yaƙira sunanta still yana murmushi,, ƙirjin tane yasoma bugawa da sauri sauri yayinda zuciyarta ta shiga dokawa tamkar zata fito, da sauri sauri numfashinta ke fita, tamkar zai ƙwace mata, "Za..Zai...Zaid !!!" Zahrah tafaɗa cikin sarƙewar murya, akuma rarraɓe,,, giransa ɗaya ya ɗage sama, haɗe da sanya haƙoransa ya datse kan lips ɗinsa na ƙasa, idonsa ɗaya ya kashe mata, haɗe da soma takawa zuwa gareta,, a hankali tasoma ja da baya, yayinda idanunta ke safaran zubar da ƙwalla,, har ta ƙurewa bango Zaid baidana takowa zuwa gareta ba,, saida yazo gaf da ita kafun ya ja ya tsaya cak,, kallonta yashiga yi daga ƙasanta zuwa samanta,, hanunsa yasanya yashafi kan laɓɓanta,, "beutyfull lips !!" yafaɗa cikin wata shegiyar murya,, gangaro da hanunsa yayi zuwa gefen fuskarta, "Kina da kyau Zahrah ta !, shiyasa nake ƙara sha'awarki ako da yaushe, gaskia ke ɗin ta da bance, kin shirya karɓan special gift ɗinki kuwa ??" ya faɗa cikin wata irin kasalalliyar murya,, baki kawai Zahrah tasake tana yi masa wani irin kallo, mai ɗauke da tarin tambayoyi masu yawa,, "Uh kinyi mamaki ko ? ba abun mamaki bane ai, kinaso kisan dalili ??" yakuma jefo ma ta wata tambayar, batare da ta amsa masa ba yaci gaba da cewa " tun randa na fara ganinki, matuƙa sha'awarki ta kamani, ni Shu'umi ne, ba'a iyarmin, idan naso abu to fa saina same sa, bara na gayamiki wanene Zaid : Zaid manemin mata ne, Zaid ɗan giya ne, Zaid ba irin mazan nan ne da ake samunsu a sauƙaƙe ba, Zaid bai iya soyayya ba, baikuma san yanda ake yiba, sai dai Zaid ya gwane wajen iya yaudara, kada kiji wani ɗar, dazaran na gama dake zan fita acikin rayuwarki, amma inaso kisan cewa, kinyi babban kuskure, da kika yarda da cewa wai Zaid zai iya yi miki soyayyar gaskia, amma bakomai zo gareni shugar baby na... !!" Yaƙare maganar yana mai ware mata duka hannayensa alamar ta taho garesa,, da gudu hawaye wasu ke koran wasu akan fuskar Zahrah, wai shin da gaske Zaid ɗinne kokuwa mafarki take ? kanta tashiga gyaɗawa yayinda gaba ɗaya, jikinta ke rawa, gaba ɗaya duniyar ne tashiga juya ma ta, komai ganin sa take kamar al'amara,, ƙoƙarin kama hanunta Zaid ya yi, da sauri ta ja baya, da ƙyar ta'iya ɗaga hanunta tashiga nuna sa, cikin sarƙaƙƙiyar murya ta soma cewa "Mai yasa zakaimin haka ? menene ribar yaudara, idan kayimini shi, miye ribarka arayuwa, idan kayi mini fyaɗe don Allah kayi haƙuri ka ƙyaleni, bansan haka sharrin so yake ba, wallahi da ban fara shiba !!" taƙare maganar cikin matsanancin kuka.... Wata irin mahaukaciyar dariya, Zaid yashiga ƙya ƙyatawa, lokaci guda kuma ya tamke fuskarsa tamkar baita ɓa yin dariya ba a iyaka tsawon rayuwarsa,, hanunsa ya sanya ya fusge lufayar dake jikinta, da iyaka ƙarfinsa,, saurin sulalewa a ƙasa Zahrah tayi tana kuka haɗe da sanya hanunta ta kare ƙirjinta, hanunsa yasanya ya damƙo gashin kanta, wanda hakan yasanya ta sakin ƙaran azaba,, hanunsa yasa ya matse bakinta, cike da mugunta ya sanya ɗayan hanunsa akan wuyanta, da ƙarfin tsiya yaja wuyan rigarta, dayake rigan irin mai aninayen nan ne, take aninayen gaban rigar suka watse a tsakiyar ɗakin, gaban rigar nata ya buɗe,,, wani irin firgitaccen ihu Zahrah tasanya, haɗe da gantsara masa cizo akan hanunsa,, take yaɗauke ta da wani irin lafiyayyen mari akan ƙuncinta, har sai da bakinta ya fashe, cak haka komai nata yatsaya na ɗan wani lokaci domin kuwa zafin marin nasa saida yaratsa ko ina a cikin jikinta, da ƙarfin tsiya yasanya hannayensa duka biyu ya yaga rigar dake jikinta, take breast ɗinta suka fito ɓalo ɓalo,, wani irin munafukin murmushi Zaid yayi, haɗe da lashe kan lips ɗinsa,, hanunsa yayi ƙoƙarin ɗaurawa kan breast ɗinta, duka ƙarfinta ta sanya, tatureshi gefe, da gudu ta nufi ƙofar fita da ga ɗakin,, ihu take tana jijjiga ƙofar amma taƙi buɗewa...
Zaid kuwa gaban ɗan madai daicin friedge ɗin dake cikin ɗakin ya nufa, wata zungureriyar gorar da memmiyar madara ya ɗauko, sai da yasha fiye da rabi, kafun ya aje gorar,, kai tsaye inda Zahrah ke tsaye tana ruskar kuka ya nufa,,, wani irin damƙa yakuma yi mawa dogon gashinta,, da duka hannayenta biyu ta shiga dukansa, tamkar mahaukaciya, amma yana tsaye ƙiƙam ko motsi baiyi ba, alamar dukan ma bata shiga jikinsa,,, hannayen nata duka yakama ya murɗe,, ƙaran azaba kawai Zahrah ke sakewa,, hanunsa yasanya ya ƙarisa ɓarka rigar dake jikinta, take rigar tabar jikinta tayi ƙasa, domin yamata kaca kaca,, wurga ta kan makeken gadon ɗakin yayi, gum haka kanta yabuge da jikin gadon, amma sam Zahrah bata damu da bugewan da tayi ba, ƙoƙarin rufe tsiraicinta kawai takeyi, sleevless t-shirt ɗin dake jikinsa yacire haɗe da wurgi da'ita gefe, wannan goran madaran ya ɗauko, kai tsaye yayi kan Zahrah dake ƙoƙarin sauƙa a kan gadon,, damƙota yasakeyi cikin zafin nama, matseta yayi akan gadon, haɗe da ɗalewa kanta, wani irin masifaffen shouck yaji lokacin da fatar jikinsu, ta samu gamayya waje guda, da ƙarfin tsiya ya danna bakinsa cikin nata, wani irin zazzafan kiss yakeyi mata, tamkar zai cinye mata fatar baki, komai da zafi zafi yakeyi mata, cikin mugunta,, lokaci ɗaya idanunsa suka sauya kala suka dawo jajur dasu,, yanayin yanda ya danneta, yasanya ko kyakkyawan motsi takasa yi, domin gaba ɗaya nauyinsa yasakar mata,,, yana cire bakinsa acikin nata, ta saki wani irin ihu, haɗe da soma turjewa, still batare da ya ɗaga taba, yasanya hanunsa cikin aljihun 3 guater jeans ɗin dake jikinasa, wani abu kamar gam ya ɗauko mai ɗan faɗi, yana da kalan ruwan toka, ɓare abun yayi haɗe da manna mata akan bakinta, yayi hakanne saboda baison ta damesa da ihu,, madarar gorar nan Zaid ya ɗauka yashiga bul bulamata akan breast ɗinta zuwa kan lafaffen cikinta,, cike da ƙwarewa yashiga lashe duk wani inda yazuba madarar ajikinta,, da zafi zafi Zaid ke tsotsan kan nipples ɗinta, gaba ɗaya ya ruɗe ya zauce, tun da yake bai taɓa ganin mace mai kyawun sura irin na Zahrah ba, duk da cewa yaga mata iri da kala, amma wallahi acikinsu Zahrah da ban take, breast ɗinta kaɗai sun haukatar da shi, gaba ɗaya ya shiɗe numfashi kawai yake fitarwa sama sama,, tsabar baya hayya cinsa baisan ma wani irin sha yake mawa breast ɗin nata ba,... Zahrah kuwa ya rufe mata baki ba halin tayi ihu, ko tayi ma bazai fitoba, kanta kawai take juyawa, yayinda hawaye ke gangarowa daga cikin idanunta,, tun Zaid yana shan breast ɗinta cikin nutsuwa har dai yasoma sha a haukace, tamkar wani wanda zai tunbuƙesu daga jikinta,, gan garo da kansa yayi, zuwa cikinta yashiga tsotseta tas,, Zaid bai tsaya anan ba, gaba ɗaya ƙafofinta ya wage mata su, da karfi,, abun da baitaɓa yi mawa kowacce mace ba, yaushi yake shirin yi mawa Zahrah, bakinsa yasanya acikin privet part ɗinta, yashiga lashewa tamkar wani tsohon maye, bakinsa har fitar da wani irin tsinkekken yawu yake,, ayanda yakejinsa yau, idan duka mutanen duniya zasu haɗu akansa suce ya bar Zahrah, to ba zai barta ba har sai ya cika burinsa akanta,, domin kuwa yakai matuƙa kuma ƙololuwa wajen sha'awarta,,, jikinsa har rawa yake, haka Zaid yayi fatali da 3 guater jeans ɗin dake jikinsa, ba tausayi ko kuma imani, a cikin zuciyar Zaid, haka ya nufi ƙofar Zahrah, sam baya cikin hayyacinsa, bakuma yatare da nutsuwarsa, daƙarfin gaske yashigeta, tsabar azaba saida ihun da Zahrah tayi yafito fili, duk da cewa bakinta a rufe yake,, tun daga wannan ihun Zahrah batasake sanin a wace duniya take ba,, kamar ƴadda Zahrah ta tafi hutu numfashinta baya jikinta, haka Zaid ma, domin kuwa ko kawa ne ya sarƙe tsakaninsa da numfashinsa, ya shiga duniyar ƴan mata kala kala, amma tabbas wannan duniyar da ban take, daɗin wannan duniyar ta fita da ban da daɗin waƴancan duniyar, tun da yake aduniya, bai taɓa sambatu ba idan yana sex, amma sai gashi yau yafice a hayyacinsa, bakinsa harƙin rufewa yayi idanun sa kuwa sun sauya launi, ahhhhh !! ahhhhh !! shine abun da Zaid ke iya furtawa kawai, nan ma da ƙyar kalmar take fita.... Zaid ya share sama da 4 hours yana yi mawa Zahrah abu ɗaya, realising kuwa yayi yafi sau a ƙirga, sai da wani irin masifaffen ciwon kai, yakama sa tukun ya iya cire jikinsa daga na Zahrah, take jikinsa yasoma ɓari, tsayuwa ma gagararsa tayi, da ƙyar ya iya tattaro jarumtarsa, yanufi bathroom, cikin bathtub ɗin dake cike da ruwan ɗumi yafaɗa haɗe da lumshe idanunsa, har yanzun baidawo saiti ba, asama sama yakejin kansa......
(please and please kada ku saƙar min da guiwa don Allah, wallahi idan kuka faɗi bad magana, bazanji daɗin yin next page ba, ko waccenku nasan tasan ƙaddara, idan Zaid baiyi mawa Zahrah fyaɗe ba, labarina bazai tafi a yanda nake so ba, nasan zakuji haushi amma kuyi haƙuri....)
*7/October/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
Phatymasardaun
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Brother Khabier...*
*🌈Kainuwa Writers Association*
'''{{United we stand and succeed our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}}'''
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed 📵*
*Wannan page ɗin gaba ɗayansa kyautane a gareki ƴar uwa rabin jiki, My lovely Sister ZAHRAH (MOM PHADEEL) nagode sosai da kulawa Allah yabar ƙauna, kisani.inasonki sosai tawan, inakuma ji dake, kijima kiyi lasting..*
*Chapter 23 to 24*
A ƙalla Zaid yakai kusan 50 Minute a cikin bathtub ɗin wanka, a sannu sannu yasamu ciwon kannasa ya lafa, duk da cewa bai daina ji ba, amma bakamar ɗazu ba,,,a daddafe yayi wankan tsarki dana soso da sabulu, domin kuwa wata irin muguwar kasala yakeji ajikinsa,, sanye yafito daga shi, sai rigan wanka, wacce ta tsaya iyaka guiwarsa,, kallo ɗaya yayi murmushinsa yayi haɗe da sanya hanunsa ya shafi gefen kumatun ta, " Me daɗi na !! " yaƙira sunanta da wata irin murya , idanunsa ɗaya yakashe tamkar dai tana ganinsa, doguwar rigarta dake yashe a ƙasa, ya ɗakko yasanya mata ajikinta, duk dacewa gaba ɗaya doguwar rigar a kece take,, wayarsa yaɗauka haɗe da karawa akan kunnensa, mintuna kaɗan wanda yake ƙira ya amsa wayar, "kuzo ku maidata inda kuka ɗauko ta " Zaid yafaɗa a taƙaice, haɗi da datse ƙiran, har yakai bakin ƙofar fita daga ɗakin, saikuma ya tsaya cak, dawo da kallonsa yayi zuwa kan fuskar Zahrah,, murmushi yayi, haɗe da murɗa handle ɗin ƙofar yayi ficewarsa,, yana fita farfajiyar gidan, yashige motarsa ƙirar Venza haɗe da bata wuta yabar gidan... Mintuna ƙalilan da tafiyan Zaid, waƴannan mutanen da suka kawo Zahrah, suka kuma da wowa, kamar yanda yashigo da ita awuya, haka yanzuma ya ɗagata a wuyansa yayi waje da'ita, aransa yana matuƙar mamakin yanda jikinta yayi faca faca da jini, tamkar anyanka kaza....
9:50 pm... Dai dai suka ƙaraso cikin unguwar su Zahrah, sai da suka kawo daf da ƙofar gidansu, kafun suka tsaya, buɗe murfin motar sukayi, haɗe da tunkuɗo Zahrah da bata numfashi waje, take ta zube a wajen,, sukuwa banka mawa motarsu wuta sukayi suka ƙara gaba...
"Gaskia Malam nifa hankalina yasoma tashi, haba dan Allah, ace yarinya tun shaɗaya'n rana ta fita, amma har yanzu kusan goman dare bata dawo ba, gaskia duk inda Zahrah tashiga jikina yana bani ba lafiya take ba, domin kuwa sam ba ɗabi'ar Zahrah bace yin dare a waje! "
Ajiyar zuciya Baffa ya sauƙe, domin shima zuwa yanzu abun yafara da munsa, ace tun rana da ta fita haryanzu shiru babu labarinta,,
"Haba Malam kayi shiru, kamata yayi kaje makarantar tasu kaji ko lafiya, amma ka wani tsaya ƙiƙam "
"kinga dan Allah kada kici kani da bala'i, tun ɗazu kintsaya akaina sai faman ɓaɓatu kikeyi, ca nai miki bazanje makarantar tasu induba ba ko me ?, ni banson baƙar jarfa !!" Baffa yaƙare maganar cikin faɗa,,
Gum Inna tayi da bakinta,,domin tasan nasa masifar ta taka nata, inyafara bala'i, sai yakai har gobe bai gama ba...
Miƙewa Baffa yayi daga zaunen dayake haɗe da ficewa daga cikin gidan,,,, kasancewar gari yayi duhu, ga kuma matsalan wutan lantarki da ake fama dashi, kusan koda yaushe ba wuta, yanzun ma dai hakanne domin kuwa gaba ɗaya layinnasu dulum yake babu wani gida mai ɗauke da hasken lantarki,, har Baffa ya gota saikuma yaga tamkar wani ƙaton abune yashe a ƙasa, cike da ɗar ɗar yafito da ƴar ƙaramar wayarsa Nokia, ɗan madannin sama ya danna take hasken tocila (flashlight) ya bayyana,, haska tudun dayagani yayi, aikuwa mutum yagani yashe a ƙasa,, "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un !!" Baffa yafaɗa gabansa na dukan uku uku, sake matsowa yayi don tabbatar mawa idanunsa, mutum ɗinne ko kuwa, wani irin razana haɗe da faɗuwar gaba ne suka dirar mawa Baffa alokaci guda, sakamakon tozali da fuskar Zahrah da yayi, "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, Allahumma ajirni fil masibati wa'aklifni kairan minha, subahan Allah !!,, Salame Salame !!!" Baffa yashiga kwaɗa ƙira, aikuwa dagudu Inna mai kunnen jiyau, ta bazamo ƙofar gida, domin dai dawuya kaima Inna ƙira ɗaya bata jiba...
"lafiya kuwa Malam kaketa zundumamin ƙira?, ai saika sa na.... Kasa ƙarasa maganar Inna tayi, domin kuwa idanunta ne suka sauƙa kan Zahrah dake kwance magashiyan a cikin turbuɗin ƙasa,, "ƙara Inna ta ƙwanɗara, haɗe da afkawa kan Zahrah tashiga jijjigata, "Zahrah ! Zahrah !! " Inna tashiga ƙiran sunan Zahrah, cike da firgici,,,, kuka sosai Inna tashiga rerawa tana mai ƙiran sunan Zahrah, amma ina Zahrah batasanma a duniyar da take ba,, Baffa ne yayi ƙarfin halin sa Inna ta cicciɓota sukayi cikin gida da'ita, gudun kada jama'a su taru akansu... Cike da tsoro Inna da Baffa ke kallon busheshshen jinin dake manne a ƙafofinta, "Nashiga uku Malam mai yasameta ne? kagafa taƙi buɗe idonta !" Inna tafaɗa cikin ruɗewa, " Ina zansani Salame ba dake muka tsintota a ƙofar gida ba, yanzu dai bana kawo ruwa ki zuba mata kozata farfaɗo "
Ruwa Baffa yakawo Inna tashiga zubawa Zahrah akan fuskarta, amma ina aiko alaman motsi Zahrah batayi ba,, " Mun shiga uku malam, kagafa haryanzu taƙi motsawa !" Inna takuma faɗa, cikin tsoro, "Banaje nataro mai taxi sai muje asibiti !!" Baffa yafaɗa cikin gaggawa domin yatsorita da al'amarin Zahrah'n....
Mintuna ƙalilan Baffa yadawo damai taxi, wata baƙar riga Inna tasanyama Zahrah, haka suka ɗebeta, aka sanyata acikin taxi kaitsaye suka wuce asibitin cikin gari.....
Mai taxi na fakawa Baffa ya arta a guje, yayi cikin asibitin, yanashiga yataradda wasu nurses suna zaune, bawani ɓata lokaci Baffa yasoma kora musu bayani akan cewa yazo da marar lafiya ne,, taɓe baki ɗaya daga cikin nurses ɗin tayi, haɗe da yi mawa Baffa kallon rainin hankali, cike da gadara tace " Bama karɓan marar lafiya sai anyanki kati " jiki na rawa Baffa yace " Kiyi haƙuri bansani bane, nawa ake yankan katin? kuma a ina ake yanka ?" bakinta takuma taɓewa haɗe da cewa " 1k ne sannan kuma acan wajen ake yanka " taƙare maganar tana maiyi masa nuni da wani waje,,
"menene kuma 1k yarnan ?" Baffa yatambaya,, cike da shaƙiyanci duka Nurses ɗin suka sanya masa dariya, "Hmm lallaima tsohonnan wato kai bakasan komai ba, amma kaɗauko marar lafiyanka kukazo asibitinnan, Hmm talaka baijira kansa ba, to abun da ake nufi da 1k shine dubu ɗaya " again nurse ɗin taƙara magana tana yatsine fuska... "To to to shikenan banaje na yanka " Baffa yafaɗa, cikin hanzari yanufi inda wannan nurse ɗin ta gwada masa, sosai Baffa yajima kafun yasamu ya yanki katin, saboda zalunci ma mai yanka katin dubu ɗaya da ɗari biyar takarɓa a wajensa, babu kuma yanda ya'iya haka yabayar, yana kawo katin yamiƙamawa nurse ɗin, yatsina fuska ta sakeyi haɗe da cewa aje katin a can, zuwa anjima maduba,,,
"Dan girman Allah ƴarnan kitaimakeni, wallahi ɗiyatace nakawo ko numfashi batayi, bansaniba ma ko tamutu kotana da rai !!" Baffa yafaɗa cike da tashin hankali, ganin suna neman aje katin daya basu,
"What ! bata numfashifa kace ? " su duka Nurses ɗin suka faɗa cikin ruɗewa, "ƙwarai kuwa " Baffa yabasu amsa... Ai da hanzari nurses ɗinnan sukayi waje, yayinda wasu sukatafi ɗauko wannan ɗan gadon da ake ɗaura mutanen da aka kawosu emergency akai,, akan wannan gadon aka ɗaura Zahrah da hanzari suke turata,don kaita abata taimakon gaggawa.... duk yanda suka so ceto rayuwarta abun yafi ƙarfinsu, ɗaya daga cikin Nurses ɗinne ta sharce gumin dake kan goshinta, ɗan nisawa tayi haɗe da kallon ƴan uwanta, cike da gajiya tace " gaskia inaga bazamu iya aikin nan ba, domin kuwa case ɗin fyaɗe ne, ba kuma hurumin mu bane, dole sai mundangana ga Doctor S.S domin wannan aikin sane " "Cab gaskia inajin tsoro mar'uda yanzufa time ɗin shin sane, kinaga yadace mukai masa wannan case ɗin ?, kuma ma idan yasan abun da muka aikata tun farko, wallahi bazamu share ba.." wacce ke tsaye gefen Mar'uda ta faɗa,, " gaskia saidai yayi haƙuri Aisha domin kuwa tabbas shiɗinne kaɗai zai iya kamo bakin zaren, banaje naƙirasa " Mar'uda nakaiwa nan a zancenta tafice daga cikin emergency room ɗin.....
Zaune yake akan tankamemiyar ƙujeran dake cikin haɗaɗɗen office ɗinsa, kyakkyawan matashin saurayine wanda aƙalla bazai wuce 30 years ba, sanye yake da riga da wando baƙaƙe, yayinda yaɗaura farin suit akai mai matuƙar kyaun gaske,, riƙe yake da wani file ahanunsa, yana dubawa yayinda yake shan coffee ahankali, da'alama abu mai mahimmanci yakeyi, farine shi amma basosai ba, sannan yana da ƙawataccen saje akan fuskarsa, yana da manyan idanu dakuma dogon hanci, wanda suka taimaka wajen bayyana kyawunsa, masha Allah shima dai kyakkyawane na nunawa sa'a....
Knocking ƙofar office ɗinnasa akashi ga yi, ajiye kofin coffee ɗin nasa yayi, haɗe da yamutsa fuska, cikin wata irin murya yace "yes, come in " Mar'uda ce taturo ƙofar tashigo, cike da girmamawa tace " sorry for disturbing you sir, we have an emergency patient"
" but i have closed for today, inama ƙoƙarin tafiya gidane " Doctor S.S yafaɗa cikin gajiyawa..
"Sir, the patient has been raped and she is unconscious !!"
" Suban Allah, fyaɗe fa kikace Mar'uda !!" Doctor S.S ya faɗa cikin kaɗuwa,, kai Mar'uda ta ƙaɗa alamar eh, miƙewa yayi cikin gaggawa yace " Muje "... Doctor S.S na gaba Mar'uda, nabiye dashi haka suka nufi emergency room ɗin,, yana shiga cikin Emergency room ɗin yaji ƙirjinsa ya buga, da sauri yaƙarisa kan Zahrah dake kwance tamkar gawa, take sauran Nurses ɗin nan suka shiga cikin taitayinsu, domin sun san Doctor S.S baya wasa, musamman ma idan akan irin wannan case ɗinne na fyaɗe... Taimakon gaggawa Doctor S.S yashiga bawa Zahrah, bayan yasanya Nurses sun haɗa masa kayan aiki, bakaɗan ba Doctor S.S ya tsorita, ganin irin taɓargazan da akayi mawa Zahrah a ƙasanta, domin sosai wanda yayi mata fyaɗen, ya ɓarkata,, "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un !!" kawai Doctor S.S kefaɗa acikin zuciyarsa, domin kuwa duk wanda yayi mata wannan abun yacika marar imani kuma marar tausayi, Doctor S.S nayi mata ɗinki amma zuciyarsa ƙuna da tafarfasa takeyi, "Haryaushene za'a ɗauki mataki akan banzayen mazajen da sukeyi mawa yara mata ƙanana fyaɗe ?, har yaushe za'adaina yi mawa mata fyaɗe ?, haryaushene wasu mazan zasu daina cin mutumcin mata tahanyar yi musu fyaɗe ?, ako da yaushe yana matuƙar jin ciwo acikin zuciyarsa, aduk sanda yaji cewa anyi mawa mace fyaɗe, tabbas da ace yana da wani babban iko, to da ya ɗauki tsattsauran mataki ga duk wani namiji da yayi mawa mace fƴaɗe" haka dai Doctor S.S yaɗinke Zahrah tsaf, bayan yagama ɗinketa ne, yayi mata treatment ɗin goshinta wanda yake a fashe, aƙalla dai Doctor S.S yakai kusan 1 hour yanayi mawa Zahrah teatment, allurai yayi mata kala biyu, saida yakammala yi mata komai kafun yafice daga cikin ɗakin bayan yabawa Nurses umarnin kaita ɗakin hutu, duk dacewa bata farfaɗo ba... "Suwaye suka kawota ?" Doctor S.S yatambayi Mar'uda fuskarsa babu alamar wasa,, inda su Baffa da Inna ke zaune Mar'uda tayi masa nuni,, cike da ɓacin rai Doctor S.S yanufi inda suke...
"Kunkuwa san mekukeyi ? taya zakubanzatar da ɗiyarku, har aimata mummunan fƴaɗe irin wannnan ?, ko kunsan wani irin haɗari ƴarku tashiga, a sanadiyar wannan fyaɗen da akayi mata ?, maiyasa iyaye kuke sakaci da rayuwar ƴaƴayenku mata ne?, shin bakusan cewa ranan gobe, Allah zai tambayeku game da amanarsu daya baku ba ? ".. Doctor S.S yajero musu tambayoyi cikin matsanancin ɓacin rai,, jikin Baffa da Inna ne yayi laƙwas, domin su sam basuma san cewa fƴaɗe akayimawa Zahrah'n ba sai yanzu, take Inna tasoma share ƙwalla hadda shashsheƙar majina,, wani irin kallon tsantsar takaici Doctor S.S yayi mawa su Baffa haɗe da cewa "Kubiyoni Office " yanakaiwa nan a zancensa yanufi hanyar office ɗinsa,, haka su Baffa suka rufa masa baya jiki ba ƙwari, domin kuwa dukansu sun kaɗu dajin cewa wai fyaɗe akayimawa Zahrah, to waye ? suka tambayi kansu... Zama yayi akan kujera gaba ɗaya jin zuciyarsa yake ba daɗi, wani irin masifaffen haushin iyayen yarinyar ma yakeji, da ƙyar ya iya daure zuciyarsa, yace "Ya akayi abun yafaru ?" gyara zama Baffa yayi haɗe da cewa "Wallahi likita bansani ba, nidai natafi wajen sana'ata, dana dawo kuma sai bantarar da Zahrah a gida ba, shine kuma daga baya nataradda ita yashe a ƙofar gida !" Baffa yaƙare maganar yana matsan ƙwalla, laɓɓansa ya cije cike da takaici, domin gaba ɗaya abun ma yalura rashin kula ne yajawo, amma tun da shi ba ɗan sanda bane bai dace yatsare su da tambayoyi ba, " Yanzu dai maganar gaskia ƴarku tana cikin hatsari, tana matuƙar buƙatar taimako, wanda yayi mata fyaɗe yayi mata rauni sosai a gabanta, wanda yaja dole akayi mata ɗinki, amma ba'anan matsalar take ba, ba lallai ƴarku, ta farfaɗo yau ba, zata iyakaiwa gobe koma fiye da haka, sannan baizama lallai ta dawo cikin hayyacinta ba kodama ta farfaɗo ɗin, saboda ana yawan samun irin waƴannan matsalolin, dayawan mata idan aka musu fyaɗe yakan taɓa musu ƙwaƙwalwa, sai dai ako dayaushe fatanmu shine komai yazo da sauƙi ".... Bakaɗan ba hankalin su Baffa yatashi jin abun da Doctor ke cewa, ya ilahi wani irin iftila'i ne ya faɗo cikin rayuwarsu haka ????......
((Kuyi haƙuri jiya kunjini shiru abubuwane sukaimin yawa, Zee black nagode da kulawa...))
*10/November/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Brother Khabier....*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*((United we stand ans succeed our ambition is to entertain & motivate the mind of readers))*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Chapter 25 to 26*
"Yanzu likita ya za ayi kenan ?" Baffa yatambaya fuskarsa ɗauke da damuwa, ajiyar zuciya Doctor S.S yasauƙe haɗe da cewa " asamu wanda zai kwana da'ita, kafun gobe Idan Allah yakaimu " yanaƙare zancen, yasoma tattare files ɗin dake baje kan table ɗin dake gabansa..
Tuƙi yakeyi amma gaba ɗaya jinsa yake wani iri, duk wata ƴar walwala da kuzarinsa sun ƙaura daga garesa, sosai fyaɗen da akamawa yarinyar yataɓa ransa, hakanan yakejin matsanancin tausayin yarinyar na ratsa zuciyarsa,gaskia wasu mazan basu da imani, ka suma ƴar ƙaramar yarinya kamar wannan, ka danneta kakuma yi mata fyaɗe da ƙarfin tsiya, idan kai akamawa taka kuma bazakaji daɗi ba, ya Allah kasakama bayinka,... Horn biyu yayi kacal maigadi ya wangale masa tankamemen gate ɗin gidannasu, a parking space yayi parking motar tasa, haɗe da fitowa, kai tsaye ɓangarensa yanufa, domin yana da yaƙinin zuwa yanzu su Hajiyarsa sunshiga, ko yaje ɓangarensu bazai tadda suba,
"SADDIQ!!" wata ƴar dattijuwar mata dake tsaye a bayansa taƙira sunansa,, ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya Doctor S.S yayi haɗe da juyowa, ƙoƙarin ƙaƙalo murmushi yayi ya aza akan fuskarsa, "Hajiya barka da dare" yafaɗa cike da girmamawa, "Yauwa barka dai, sai yanzu kake dawowa ?" sunkuyar dakansa ƙasa yayi haɗe da sanya hanunsa abayan kansa yashiga shafa ƙeyarsa, "Hmm da kyau, duk nasan mai yajawo hakan, rashin iyali ne, kuma wallahi komai yakusa zuwa ƙarshe, a wannan karon ko kana so ko baka so,yazama dole kafitar da mata ko kuwa, in zaɓa maka cikin ƴaƴan ƙannena, bazanci gaba da sanya maka idanu ƙato dakai ace baka da mata ba !!" Hajiya tafaɗa cikin faɗa, "Kiyi haƙuri Hajiya Insha Allah nan ba da jimawa ba komai zai dai dai ta"
"Koda yaushe haka kake cewa, inanan inasa ido, idan naji shiru kuma kasan sauran " Hajiya tafaɗa, juyawa tayi kaitsaye tanufi ɓangarenta, shima nasa ɓangaren yanufa, jinsa yake amatuƙar gajiye, wanka yayi haɗe da bin lafiyar gado ya kwanta, abu na farko daya fara ziyartan idanunsa bayan yarufesu, shine hoton fuskar Zahrah, sosai hoton fuskarta keyi masa gizo,acikin idanunsa, da sauri yabuɗe idanun na sa, a zuciyarsa yana mai mamakin faruwar hakan, dayaga abun bana ƙare bane, kawai saiya dangana hakan, dacewa tsananin tausayinta ne yajawo hakan......
ZAID kuwa yana barin Zahrah kai tsaye TRANSCORP HILTON yanufa, domin dai yauma yana da meeting a can... Bayan sunkammala meeting ɗinne, kai tsaye yawuce ɗakinsa dake ɓangaren V.I.P,, yanashiga yasoma rage kayan dake jikinsa, direct bathroom yashige yasakarmawa kansa shower,, wani irin sanyi da nishaɗi yakeji a cikin zuciyarsa, tun bayan abun daya shiga tsakaninsa da Zahrah, yakejin ransa yayi fari, nishaɗi kawai yakeji acikin zuciyarsa, gaskia yau yasha zallan madarar daɗi, domin kuwa sosai ɗanɗanon Zahrah yayi masa hundred percent, yanason mace mai ɗanɗano sosai... Yana fitowa daga wanka, wayarsa dake aje kan gado, tasoma ƙara haɗe da kawo haske, alamar shigowar ƙira, saida wayar tasa takusa katsewa kafun yaɗauki wayar haɗe da karawa akan kunnensa, "Shigo ciki" Zaid yafaɗa a taƙaice haɗe da cilla wayartasa kan gado,, Abid ne yaturo ƙofar ɗakin yashigo,, rungumar juna sukayi, kamar yanda suka saba koda yaushe idan sun haɗu,,
"Daga ina haka ?" Zaid ya tambayi Abid, murmushi Abid yayi haɗe da zama akan hamshaƙiyar kujeran dake gefen gadon ɗakin, " yau nasha sweet abokina, wata babe nasamu mai zafi, inagayamaka tashayar dani zuma !!" Abid yafaɗa cike da nishaɗi,, Dariya sosai Zaid yayi hadda ƙyaƙyatawa, shiru kawai Abid yayi yatsaya yana kallon Zaid, domin dai Zaid baya dariya abanza, abune mai wuya kaga dariyansa, sai dai idan ya ƙulla wani abun... " Final !!" Zaid yafaɗa yanamai cije laɓɓansa,, zaro idanu Abid yayi cike da mamaki yace " what ! ? badai kanaso kacemin harka gama da Zahrah ba ??" ƙayataccen murmushi Zaid yayi haɗe da cewa "Tuntuni harma anwuce wajen " dariya Abid yayi haɗe da cewa " Har yau bansan kai wani irin mutum bane Zaid, idan kaso abu, to ko ta wani hali sai ka sameshi, Allah sarki, Innocent girl, tanacan tana fama, nasan kabata kaya da yawa, may be ma haryanzu bata san awace duniya take ba " Abid yafaɗa... Still murmushi Zaid yayi haɗe da gyara zamansa, wayarsa yajawo yashiga latsawa, amma fuskarsa ɗauke take da murmushi... Ganin haka yasa Abid sha re maganar domin yafahimci me abokinnasa yake nufi,, Jefi jefi suke hira da Abid.....
Washe gari... Har 9:00 am Zahrah bata farfaɗo ba, Doctor S.S yazo yasake dubata, yakumayi mata duk wani abu daya kamata, amma still ko motsawa batayi ba... Abu kamar wasa tun anasa ran farfaɗowar Zahrah har dai akasoma cire rai, domin kuwa yau kwananta biyu batasan inda take ba... Sosai Doctor Saddiq yake bawa Zahrah kulawa, kuma yau yake da yaƙinin farfaɗowarta insha Allah...
Ƙafantane yafara motsawa, sannu a hankali idanunta suka soma ɗan buɗewa, ƙwaƙwalwarta ne tashiga tariyo mata duk wani abu daya faru da'ita, wani irin ƙara Zahrah tasanya wanda yayi matuƙar firgita su Baffa da Inna dake zaune gefe da gadon da take kwance,, "Subahanallahi !!" Baffa ya faɗa cike da tashin hankali,,, ihu kawai Zahrah ke yi haɗe da fisge fisge, tamkar dai mahaukaciya,, Dagudu Baffa yayi waje don ƙiran likita,, duk yanda Inna taso riƙe Zahrah abun yagagara domin kuwa duk ta fusge ƙarin ruwan da akayi mata, cikin hanzari Doctor Saddiq yaƙaraso cikin ɗakin, cak yatsaya ganin yanda Zahrah ke ihu tana ta fusge fusge, wani irin mugun tausayinta yaji ya daki zuciyarsa,, tattaro duk wani kuzarin sa yayi yaƙarasa gareta, wani irin fusga Zahrah tayi, ai kuwa saiga Inna dake riƙe da ita, tafaɗi ƙasa warwas,, da hanzari ya kama hannayenta duka biyu, yana mai ƙoƙarin nutsar da ita, wani ihun takumayi wanda sautinsa ya zagaye kowani kusurwa na ɗakin, fuskar Zaid kawai take hangowa akan ta Dr Saddiq,
"Wayyo Allah na, Baffa kataimakeni zai kasheni, zai kasheni, wayyo !!!" abun da Zahrah take ta faɗa kenan cikin hargowa da son ƙwace kanta daga wajen Doctor Saddiq,, duk yanda Dr Saddiq yaso tayi shiru abun yacitura, domin da alama bata cikin hayyacinta,, wani irin cizo Zahrah ta gantsara masa ahannu, sosai yaji zafin cizon amma yasan tabbas yana saketa, guduwa zatayi, ko kuma ma tayimawa kanta rauni,, wani irin ƙara ta callara tana mai shirin turesa ta gudu, yayi saurin rungumeta ƙam acikin ƙirjinsa, wasu lafiyayyun cizo Zahrah tashiga gantsara masa akan ƙirjinsa, sake rungumeta yayi ƙaƙam acikin jikinsa, haɗe da rumtse idanunsa, yakuma datse lips ɗinsa da haƙoransa,, sosai yakejin zafi har cikin ƙwaƙwalwarsa, domin kuwa da iya ƙarfinta take cizon sa,, ganin cizo bazai wadatar ba yasanyata sanya hannayenta, duka biyu ta shiga dukansa tako ina,, tabbas duk wanda yaga abun da Zahrah takeyi yasan cewa bata cikin hayyacinta,, da ƙyar Dr Saddiq ya'iya danneta yayi mata wata allura wacce take kashe jiki, ta kuma gusar da ƙarfin jikin ɗan adam,, take tayi laƙwas haɗe da sulalewa daga jikinsa tafaɗa kan gado, kallonta yashiga yi gaba ɗaya tayi buji buji da tulin gashin kanta, gashi duk taɓalle maɓallan gaban rigarta, wanda hakan yabayyana kyakkyawar surar ƙirjinta,, saurin ɗauke idanunsa yayi daga kan ƙirjin nata, haɗe da sauƙe ajiyar zuciya, juyo da kallonsa yayi zuwaga kan su Baffa da suke tsaye cirko cirko, gaba ɗaya sunyi wani tsuru tsuru dasu, tamkar ace musu as su antaya a guje, bama kamar Inna,,
Kansa kawai ya jijjiga batare da yacemusu komai ba, yayi ficewarsa daga cikin ɗakin,, direct office ɗinsa ya nufa, da kansa ya haɗa tea mai kauri, kaitsaye ɗaki na musamman ɗin daya sa aka kai Zahrah yanufa, riƙe da kofin tea ɗin a hanunsa, baitaradda su Baffa a cikin ɗakin ba, don haka kansa tsaye yanufi gaban gadon nata,, kwance take flat daganinta kasan babu wani wadataccen ƙarfi ajikinta, saidai hawayene kawai ke ambaliya yana gangarowa ta gefen idanunta,,, "Zahrah" yaƙira sunanta, duk da yasancewa bazata taɓa amsa masa ba, saboda batacikin nutsuwarta...
Aje ƙofin tea ɗin dake hanunnasa yayi, haɗe da ɗaukar pillow yasanya a bayanta, da ƙyar yasamu ya iya jinginar da ita ajikin pillow'n, a hankali yake ɗiban tea ɗin cikin tea spoon yanakaiwa bakinta, duk yanda yaso ta buɗe baki tasha tea ɗin hakan yagagara, domin daya sanya mata ruwan tea ɗin acikin bakinta, zaidawo waje,, aje kofin yayi haɗe da harɗe duka hannuwansa akan ƙirjinsa, kallon fuskarta yashiga yi natsawon wasu mintuna, ajiyar zuciya ya sauƙe alokaci guda, haɗe da ɗaukar kofin tea ɗin yafice daga cikin ɗakin,, umarni yabawa wata nurses da tayi mawa Zahrah alluran bacci, domin duk yafahimci irin situation ɗin da take ciki a yanzun...
Gaba ɗaya ihun Zahrah ya karaɗe ɗakin, hankalinsu Inna gaba ɗaya atashe yake, kamar yanda tayi ɗazun, yanzuma haka takeyi, domin ihu da fusge fusge kawai take saidai yanzu, cewa take "Kutaimakeni, zai kasheni, wayyo Allah na, kutaimakeni !!!" abun da Zahrah take faɗa kenan cikin hargowa, da wani irin hanzari ta diro daga kan gadon, da take kwance, kaitsaye bakin ƙofa tanufa da gudun gaske, da sauri Baffa yasha gabanta, wani irin ƙara ta sanya, domin kuwa Zaid tagani tsaye a gabanta, amaimakon Baffa, wani irin ƙarfine yazomata aikuwa kyakkyawan hankaɗa tayimawa Baffa, saigashi jagwaf a ƙasa, dama bawani kuzari gareshi ba,, gaba ɗaya tayi buji buji da jikinta, ta tarwatsa gashin kanta, gudu kawai Zahrah take tsakaninta da Allah, daga zangar ta haɗu da mutane sai tasanya ihu, domin kowaye zatayi tozali dashi to fuskar Zaid take gani, akan tasa, hartakai bakin ƙofar fita daga cikin asibitin, cikin zafin nama ya cafko hanunta, wani irin ihu Zahrah tashiga kurmawa, tamkar wacce ake yankan naman jikinta, tun fitowarta mutane ke kallonta, atunaninsu mahaukaciya ce,, bai damu da ihun da takeyi ba, duka hannayen ta yahaɗe waje ɗaya, caɗak ya ɗagata haɗe da saɓata kan kafaɗarsa, yayi cikin asibitin da'ita,, wani irin ƙara tayi, take kuma jikinta ya sake numfashinta gaba ɗaya ya ɗauke,
Duk inda suka wuce sai ankallesu, wasu suna matuƙar tausayinta, da ƙuruciyarta amma hauka ta risketa, anasu zaton mahaukaciya ce..
A kan gado ya shimfuɗeta, haɗe da rufamata bargo, wasu allurai yayi mata, bayan yasanya mata drip ɗin dazai taimaka wajen bawa jikinta kuzari, koda bataci abinci ba....
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, ya Allah kataimaketa, haƙiƙa tanacikin mawuyacin hali, ya Allah kasa kada abun danake zargi yatabbata, Allah katsaremata ƙwaƙwalwarta, da kariyarka !!" Dr Saddiq yafaɗa cikin karyewar zuciya, haɗe da tsananin tausayin Zahrah,, sau da dama akanyi mawa yara ƙanana fyaɗe, firgici da tsoron da suke samun kansu ciki, yakan taɓa musu ƙwaƙwalwa, sai aga kamar sun zare, hakan yasa basa da wowa hayyacinsu cikin sauƙi,, a wannan rana dai Dr Saddiq da ƙyar ya iya barin asibitin, gaba ɗaya lamarin Zahrah ƴatsaya masa arai, tausayinta yakeji sosai....
Tsaf yagama shirya kansa cikin wasu mayun riga da wando, masu kyau da tsadar gaske, bakaɗan ba yayi kyau sai tashin daddaɗan ƙamshi jikinsa yake, SHU'UMIN NAMIJI kenan ganinka babu alkhari acikinsa, ƴar ƙaramar trolly bag ɗinsa ya shiga ja, bayan yaɗauki wayoyinsa da kuma duk wani abu dayasan zai buƙata,, wannan karan ko ɓangaren mahaifiyarsa bai jeba, motarsa ƙirar BUGATI yashige, yayin da driver yabamawa motar wuta, kaitsaye airport suka nufa, domin dai alƙawari Zaid yaɗauka yau bazai kwana acikin Nigeria ba, yawon shaƙatawa zai tafi New York City (America).. Yana shiga cikin jirgin baiwani jimaba, jirginnasu yaɗaga zuwa sararin samaniya.....
*((kuyi haƙuri page ɗin yau baida yawa...))*
*12/November/2019*
_________________________
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
phatymasardauna
*Dedicated To My Loveƙy Brother Khabier...*
*🌈Kainuwa Writers Association*
'''{United we stand and succeed our ambition is to intertain & motivate the mind of readers}'''
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*Wannan Page ɗin gabaki ɗayansa kyautane a gareku.*
*UMMIEE-ZARIA.*
*MRS MAI LAWAL.*
*MAMAN TEEMAH.*
*ZEE BLACK.*
*AYSHA HUMAIRA.*
*SA'ADAH GALADIMA.*
*MY ADIZATOU (Ummu Adnan.)*
*MARIYA...❤.*
*Chapter 27 to 28*
Tunda Zahrah tasume, bata sake sanin inda kanta yake ba, sai ƙarfe shida na yamma, alokacin anata ƙiraye ƙirayen sallan magriba, wannan karon sam batayi wannan iface ifacen da kuma fusge fusgen da tasaba yi ba, sai dai idanunta da ta tsayar waje ɗaya,wato kan ceiling ɗin dake saman ɗakin, hawayene kawai kefitowa daga cikin idanun ta, yana mai sauƙa a gefen fuskarta, "Zahrah !" Inna dake gefe taƙira sunan Zahrah.
Ko gizau Zahrah ba tayi ba, balle Inna tasaran zata amsa mata, gyra tsayuwa Inna tayi haɗe da jinjina kanta, tabbas tasan koma meyafaru da Zahrah sune sanadi, domin kuwa basu riƙe amanar da iyayenta suka basu kafun su rasu ba.
Dr Saddiq ne yaturo ƙofar ɗakin yashigo, bakinsa ɗauke da sallama, yayinda Baffa ke biye da shi a baya, "Yauwa likita kazo ko? ta farka amma kwata-kwata bata magana!" Inna tafaɗa cike da damuwa.
Ɗan guntun murmushi kawai Dr Saddiq yayi,haɗe da nufar inda Zahrah'n ke kwance, kallonta yayi na ɗan wasu mintuna, kana yajuyo da kallonsa wajen su Baffa... "Inaso Za'ayi mata gwajin ƙwaƙwalwa, domin sake tabbatar da lafiyarta, saboda haka zanturo Nurses su ɗauketa " Dr Saddiq yafaɗa.
Sosa kai Baffa yashiga yi, cike da damuwa yace "To kamar nawa ake buƙata likita? kuma naga tunda mukazo ka ke bata kulawa, amma banji anyi min maganar nakawo ko sisi ba, fatana Allah yasa gwajin ƙwaƙwalwar bashi da tsada !" Baffa yafaɗa cikin karyewar zuciya, domin kuwa idan gwajin yana da tsada tofa sai dai ahaƙura, saboda bashi da kuɗi.
Kallonsa kawai Dr S.S yayi batare da yace dashi ƙalaba, ya sa kai yayi ficewarsa daga cikin ɗakin.
Mintuna kaɗan da fitarsa, wasu nurses su biyu suka shigo, ɗaukan Zahrah sukayi, suka ɗaurata kan wani gado mai ƙafafun taya, suka fice da'ita, ba don idanunta da suke buɗeba, tabbas da idan ka ganta zakayi zaton gawace, domin kuwa babu abun dake, motsi a jikinta, sai hawaye kawai dake ambaliya a cikin idanunta...
Alhmdlh anyi mawa Zahrah gwadin ƙwaƙwalwa lafiya, saura kawai ajira fitowar result.
Babu abun dayake ɗaga mawa Dr S.S hankali a yanzu, kamar yanda take yawan firgita, gashi hawaye sun kasa daina zubowa daga cikin idanunta, babban abun damuwar kuma shine bata um balle um um, ko motsawa bakinta bayayi, sannan kuma waje ɗaya idanunta suke kallo, wato sama.
Result ɗin gwadin da'akayi mata yafito, kuma masha Allah, ƙwaƙwalwarta tana nan lafiya, babu abun daya sameta, kawai dai tashiga halin firgici ne, kuma dama ana yawan samun irin haka...
"Likita ya sakamakon, Allah yasa bata samu wani matsala a ƙwaƙwalwarta ta ba ? " Baffa dake zaune cikin office ɗin Dr S.S ya tambaya.
"ku kwantar da hankalinku, sakamako yayi kyau, domin kuwa brain ɗinta nanan lafiya"
"Alhamdulillah, Allah mungodema !" Baffa yafaɗa cike da jin daɗi,
"Kaine Babanta mahaifi ?" Dr S.S yatambaya sanda yake ƙoƙarin cike wani file dake gabansa.
"A'a bani na haifeta ba, ƴar ɗan uwana ne da ya rasu, amanarta yabarmin, gashi yanzu bansan wani tsinannen bane ya aikata ma ta wannan abun ba !" Baffa yaƙare maganar yana matsan ƙwalla.
Kallon sa Dr S.S yayi na tsawon wasu mintuna, kafun ya kau da kansa gefe, "Dawa take mu'amala, saurayi ko aboki ?" Dr S.S ya kuma tambaya.
"Bata mu'amala da kowa sai wani yaron arziki, shine ma yace yana sonta, kuma hargida yataɓa zuwa ya gaisheni, a zahirin gaskia bana tunanin shi zai yi mata wannan aika aikan" Baffa yafaɗa da ƙwarin guiwarsa.
"Maiyasa kake tunanin shi bazai iya yi mata haka ba ?" Dr S.S yakuma jefo mawa Baffa tambaya,
"Saboda shiɗin yaron kirkine kuma ɗan babban gida ne, mutane masu dattako" (readers kuji Baffa fa da sharri )
"Zaka iya tafiya, anjima zanzo na bata maganinta" Dr S.S yafaɗa a taƙaice, domin kuwa wani irin taƙuƙin takaicin Baffa ne ya cika masa zuciya,
Sumi sumi haka Baffa yafice daga cikin office ɗin, yana matsan ƙwalla.
"Wai maiyasa mutane suke wasa da amana ne ? idan har ɗan uwanka bazai iya riƙe maka ahalinka, idan baka raye ba, to waye zai iya riƙe maka su da gaskia dakuma amana? ƴar ɗan uwanka tamkar ƴa take a wajenka, idan baka nuna ma ta soyayya ba, to wazai nuna ma ta? irin su Baffa ne suke ɓatawa mutane suna, kuma suke tozarta marayu, ya Allah kabamu ƴan uwa masu amana, wanda zasu kula da namu ko bama raye Ameen." Dr S.S yafaɗa acikin zuciyarsa,
Yau kwanan Zahrah Biyu kenan bata magana, hawaye har sun gaji da fitowa daga cikin idanunta sun kafe, duk kuwa yanda su Baffa suka so ta faɗi koda kalma ɗaya ne, hakan ya gagara, domin kuwa ko kallonsu batayi balle su sa ran zatai musu magana. Sosai Dr S.S yake ƙoƙari wajen kulawa da'ita, baya wasa da lokacin shan maganinta, domin yana da yaƙinin zuwa yanzu, ɗinkin da akayi mata a ƙasanta ya warke.
Zaune yake a kan ɗaya daga cikin kujerun falon mahaifiyar sa, sanye yake da riga da wando na maroon ɗin bugaggiyar shadda, bakaɗan ba kuwa yayi kyau acikin kayan, kallo ɗaya zakai masa kafahimci cewa a kwai damuwa a tattare dashi, domin kuwa tun ɗazu aka aje masa plate ɗin snacks a gabansa, amma yakasa ɗaukan ko da ƙwaya ɗaya ne, yakai bakinsa, duk da kuwa snacks ɗin abune mafi soyuwa a garesa,,
Hajiya ce tsaye a kansa, tayi kusan minti ɗaya da zuwa amma sam baisan da zuwan nata ba,
"Saddiq!" Hajiya taƙira sunansa.
"Na'am, Hajiya sannu da fitowa!" Dr S.S yafaɗa cikin girmamawa.
Zama Hajiya tayi haɗe da kallonsa cike da kulawa tace " Wai meke damunka ne Saddiq ? ina lure da kai gabaki ɗaya kwana biyunnan bana gane kanka, idan kafita aiki baka dawowa da wuri, ga yawan tunani da kakeyi, meke faruwa ne ?" Hajiya ta tambaya.
Gyara zama Dr S.S yayi, domin sam baya ɓoyewa mahaifiyar tasa matsalarsa,ko ta me cece kuwa, cike da damuwa yace "Hajiya wata yarinya aka kawo hospital ɗinmu, duka dukanta bazata wuce 18 to 19 year ba, yarinyar tana matuƙar baƙatar taimako, domin kuwa, wani ne yayi raped ɗinta, ahalin da ake ciki yanzu, ko magana batayi, narasa wace hanya zanbi nashawo kan lamarin!" Dr S.S ƴafaɗa cike da raunin murya,
"Subanallahi fyaɗe kuma Saddiq ?"
"Eh Hajiya, shiyasa abun yake damuna" Dr S.S yafaɗa,
"Allah sarki! Allah ubangiji ya cigaba da tsare mana ƴaƴanmu, amma iyayenta sun maka case ɗin a kotu ne ?" Hajiya ta tambaya.
"A'a Hajiya banjin zasu kai case ɗin kotu, domin kuwa talakawa ne basu da wani ƙarfi " Dr S.S ya faɗa cike da tausayawa.
"To Allah yabata lafiya, amma miye na jefa kanka acikin damuwa haka Saddiq? irin wannan matsalolin naga dama an riga da an saba kawo muku, sai dai Allah yarufa asiri kawai, bakaci snacks ɗinba mai yasa ?"
"Zanci Hajiya ko zuwa anjima ma" Dr S.S yafaɗa lokacin dayake miƙewa daga kan kujeran dayake zaune,
"A'a ina zaka kuma ?" Hajiya ta tambaya.
"Lokacin shan maganin Zahrah yayi Hajiya, zanje ne na bata" yaƙare maganar yana mai duba wrist watch ɗin dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa.
"Zahrah! wacece kuma Zahrah ?" Hajiya ta tambaya,
"Itace yarinyar da akayi raped nata dana gaya miki"
"To to adawo lafiya"
"Ameen Hajiyana!"
Yana fita yashige cikin motarsa kaitsaye hanyar asibitinsu ya ɗauka....
Kamar koda yaushe zaune take akan gado, yayinda idanunta ke kafe a waje ɗaya, ruwan hawayene kawai ke tsiyayowa daga cikinsu,
Da Sallama ɗauke a bakinsa yaturo ƙofar ɗakin, harya ƙaraso tsakiyar ɗakin, batasan ma da zuwan sa ba,
Aje abubuwan dake hanunsa yayi akan ƴar ƙaraman drowern dake gefen gadon, "Zahrah!" yaƙira sunanta cikin kwantar da murya, bata amsaba kuma bata juyo zuwa garesa ba, dama kuma yasan hakan zai iya faruwa, domin bata taɓa amsawa idan yaƙirata, bakuma ta tankamai komai zaice, duk da kuwa yasan tanajinsa.
Magungunan da yakamata tasha ya ɓare, haɗe da zubasu acikin hanunsa, goran ruwan daya shigo da shi yaɗauka, haɗe da ƙarasawa gareta, hanunta yakama yana ƙoƙarin sanya mata maganin , wani irin firgita tayi haɗe da fasa ƙara, wanda yajanyo hankalin Baffa da Inna dasuke zaune a waje, da hanzari suka shigo cikin ɗakin, da gudu Zahrah taƙarasa jikin Inna ta rungumeta, wani irin kuka mai tsananin ban tausayi tashiga rerawa,, sai kawai Inna ma ta fashe da kuka, tana mai tausayin Zahrah har cikin zuciyarta, domin kuwa lokaci ɗaya gaba ɗaya ta lalace, ta rame har duhu saida fatarta tayi, "kice su fita Inna dan Allah! kice masa kada yasake zuwa inda nake natsanesa! natsani duk wani Namiji! na tsanesu kice su fita, ko kuma inkashe kaina!!" Zahrah taƙare maganar tana mai ɗaukar wani Scissors dake aje kan wani ɗan ƙaramin table.
"Suhanallahi Zahrah mekikeyi haka ?" Baffa yafaɗa yana mai ƙoƙarin matsowa gareta,
Ihu Zahrah tasanya mai ƙarfin gaske, haɗe da saita scissors ɗin dai dai saitin cikinta, da iya ƙarfinta taɗaga zata cakawa kanta, cikin matuƙar zafin nama, Dr S.S ya murɗe hanun ta, haɗe da bata wani kyakkyawan mari akan kumatunta, "saboda hauka zaki kashe kanki ne? wani irin rashin hankaline wannan!!?" yatambaya cikin faɗa.
Zamewa tayi ƙasa tana mai rushewa da wani irin kuka mai cin rai da taɓa zuciya, shikenan itakam rayuwarta tagama lalacewa, komai nata ya tarwatse bata da wani saurin farinciki a cikin rayuwarta..
Ransa amatuƙar ɓace yafice daga cikin ɗakin, yayinda Baffa ya rufa masa baya...
Dafa kafaɗunta Inna tayi cike da tausayawa tace "Kiyi haƙuri Zahrah komai yayi farko yana da ƙarshe, ki barwa Allah lamuranki insha Allah, Allah zai saka miki"
duk iya rarrashin da Inna tayimawa Zahrah, taƙi ji, kuka kawai takeyi tamkar ranta zai fita, ankawo mata abinci ma, taƙi koda kallonsa ne balle su sa ran cewa zataci, lokaci ɗaya idanunta sun kumbura suntum dasu, da ƙyarma take iya buɗesu, ga wani irin masifaffen zazzaɓi daya rufe ma ta jiki alokaci guda, take ta fara masassara, tana cikin wannan yanayin aka soma ƙiraye ƙirayen sallan magriba, dakanta ta ɗauro alwala tazo ta gabatar da salla, duk da kuwa irin ciwo da kanta keyi mata,, koda takai sujjadan ƙarshe, wani irin matsanancin kukane ya ƙwace mata, saida tayi mai isarta kafun ta ɗago da ga sujjadan, da ƙyar dai tasamu ta iya sallame sallan, tamiƙe akan sallayan kenan, wani irin juwa ya ɗebeta, take tayanke jiki tafaɗi, da hanzari Inna tayo kanta, jijjigata tashiga yi, haɗe da soma ƙiran sunanta, dai dai lokacin wata nurse tashigo cikin ɗakin,, "yauwa likita dan Allah zoki dubamin ita gatanan jikin yaƙi daɗi!" Inna tafaɗa cike da damuwa... Da taimakon nurse ɗin suka ɗaura Zahrah a kan gado, zuwa yanzu da ƙyar take iya fidda numfashi, jitakeyi tamkar kanta zai fita tsabar ciwo, ƴan gwaje gwaje nurse ɗin tayi mata, ganin abun bawani babba bane, yasa tayi mata allura, haɗe da bata wasu drugs tasha, cikin mintuna ƙalilan bacci yayi awun gaba da ita.
tun da Dr S.S yabar ɗakin bai zarce ko inaba, sai office ɗinsa, tattare duk wani abu dayasan zai buƙata yayi, haɗe da jawo office ɗinnasa ya rufe, kai tsaye motarsa yashige bai zarce ko inaba, sai gidan Aunty Raliya (babbar yayarsa)...
Yana shiga cikin gidan, su Meenal da Affan, sukayo wajensa da gudu, suna cewa "oyoyo Uncle S.S!!" cike da farinciki Dr S.S yaɗaga su sama, fuskarsa cike da annuri yace "Oyoyo babies ɗina, yakuke, ya school ?" "lafiya ƙalou Uncle ya office ?" Meenal ta tambaya cike da iyayi, murmushi yayi haɗe da jan kumatunta cikin dariya yace "hinyau su Meenal angirma, har wani iyayi kika iya ko?" dariya suka sanya dukansu, hadda wata kyakkyawar mata da tafito daga cikin kitchine, wanda a ƙalla bazata wuce 35 years ba,
"Manya sai yau kaga daman leƙomu?" matar tafaɗa dai dai lokacin da take zama akan kujera.
"Auntƴ Raliya bazaki gane bane, ayyuka ne sukai min yawa, a office shiyasa !" yafaɗa cike da gajiyawa.
"hmmm daman nasan haka zakace ai, kai dai koda yaushe cikin aiki kake tamkar inji."
"Saudat! Saudat! kawo mawa Uncle drinks " Aunty Raliya tayi maganar cikin ɗagawar murya..
mintuna ƙalilan Saudat mai aikinta, tacika masa gabansa da drinks hadda dangin su snacks, domin kuwa duk wanda yasan sa, to yasan abun dayake so...
cake ya ɗauka yakai bakinsa, haɗe da lumshe idanu, "Um gaskia Aunty cake ɗinnan yayi daɗi!" Dr S.S yafaɗa yana mai jinjina kai, alamar cake ɗin yasamu karɓuwa a wajensa,,
Dariya Aunty Raliya tayi, haɗe da cewa "yakamata na sa maka waiji, domin na lura nan da mintuna kaɗan zaka faɗo daga kan kujeran nan, tsabar santi "
Dariya suka sanya dukansu,,
Gyara zama Aunty Raliya tayi haɗe da cewa "Waini Uncle (Uncle shine sunan da take ƙiransa) ya maganan Aurenka da Zabba'u ne ? naji shiru ba ka sake ɗago zancen ba, ince dai komai lafiya?"
Take fuskar Dr Saddiq ya sauya,daga walwala zuwa akasinta...
(( kuyi haƙuri yau nayi typing ɗin, cikin yanayin rashin jin daɗi😥, please kuyi haƙuri da abun da kuka samu, dan ko editing banyi ba.
Next page zakuji labarin shu'umi ZAIDU🤣))
*14/November/2019*
*MRS S.S 😉😜🤣*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Lovely Brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
'''{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*(A gaskia ina matuƙar jin daɗin haɗin kan da kuke bani, bantaɓa zaton Shu'umin Namiji !! zai samu karɓuwa, a wajenku haka ba, Alhmdlh sai dai na godemawa Allah, domin a haƙiƙanin gaskia inajin daɗin addu'arku gareni, Allah yabar ƙauna a tsakaninmu, masoyana ina tsananin son ku a duk inda
kuke.🍹🍹)*
*Chapter 29 to 30*
Take fuskar Dr Sadeeq ya sauya, daga walwala zuwa akasinta.
"Ya dai naga ka haɗe fuska, a lokaci guda? Aunty Raliya ta tambaya,
"Bakomai Aunty, kawai gajiya ne" Dr S.S yafaɗi haka don son katse zancen da sukeyi,
"yazama dole fa muyi zancen nan Uncle, domin kuwa Hajiya da kanta taƙirani jiya, kuma duk akan batun auren naka ne, wai sai yaushene zaka fito da matar aure ? yaka mata ace zuwa yanzu ka aje mata hadda ƴaƴa, amma kwata kwata ko batun aure bakaso ayi maka mai yasa ne Uncle ?
A je cake ɗin dake hanunsa yayi, haɗe da gyara zama, cikin sanyin murya yace "bawai fa banson aure bane Aunty Raliya, nima inaso nayi aure, kawai dai Allah ne baikawo matar auren ba"
"baka dai ga dama ba, amma matan aure kam a kwaisu baja baja a gari, haka kuma a kwaisu da yawa acikin dangi, idan har bakason Zabba'u, ai ga Farida nan, ƴar Aunty Mariya, mai yasa bazakaje ku magantuba ? idan ma dukansu basuyi maka ba, sai kaje gidan Baffa Amadu a kwai ƴan mata dayawa, son kowa ƙin wanda yarasa, wayayyu kuma ƴan boko, amma idan kace ba haka ba, to fa duk wacce Hajiya ta haɗaka da'ita, kada kazo kace zakamin ƙorafi !" Aunty Raliya ta ƙare maganar cikin sigar faɗa faɗa, domin zuwa yanzu al'amuran ƙanin nata yasoma isarta, shikenan aita abu ɗaya, mutum duk hanyar da kabi dashi sai ya kauce..
"Shikenan Aunty zanyi tunani, kuma zanje gidan su Farida'n insha Allah !" Dr S.S yaƙare maganar yana mai tashi tsaye,,
"Au wai saboda nayi maka faɗa shine kake ƙoƙarin tafiya ?" Aunty Raliya ta tambaya.
"Bahaka bane,dama gaisheku kawai nazoyi" yafaɗa cike da ƙosawa.
"Shikenan to, dama akwai snacks ɗin dana haɗama, bana kawo ma saika tafi dashi " Aunty Raliya tafaɗa, tana me miƙewa tsaye.
"godiya nake, ki bamawa Meenal takawomin mota " yana kaiwa ƙarshen zancen nasa, yasakai yafice daga cikin falon,, Saudat ce ta kawo masa snacks ɗin cike a leda, yana karɓa yayi mawa motarsa key...
*NEW YORK CITY*
Kishingiɗe yake akan wani kujera da a kayisa kamar gado, wanda yake aje bakin wani ƙaton beach mai kyau da ƙayatarwa, kamar yanda kowa yasani beach wajene na shaƙawatan mata da maza,gaba ki ɗaya mutanen dake kai kawo a wajen nan turawa ne, babu kuma wata suturar kirki a jikinsu, wasu daga su sai ɗan pant da breziya wasuko riguna ne ƴan fingil fingil sanye a jikinsu, abun dai ba kyaun gani, domin komai nasu tsirara ake gani, amma duk da haka basu wani damuba, domin haka ɗabi'arsu take..
Sanye yake da 3 guater jeans mai kalan baƙi, yayinda rigar jikinsa ta kasance fara ƙal, sannan irin marassa hanun nan ne (sleevless t-shirt) gashin kansa kaɗai abun kallone, domin kuwa yasha gyara, ƙyal ƙyali da kuma walwali kawai yake fitarwa, kallo ɗaya zakai masa kasan cewa yana cikin jin daɗi da tsagwaran hutu, wani zungureren glass cup ne riƙe a hanunsa yana sipping wine ɗin dake cikin cup ɗin a hankali.
Hmm Zaid kenan Shu'umin Namiji ka huta abunka.
Tun daga nesa taketa faman sakar masa murmushi, amma gaba ɗaya yaɗauke kansa daga gareta, yayin da yayi kamar bai ganta ba, domin kwata kwata yanzu baison damuwa da yawan takurawa..
Tana ƙarasowa ta faɗa cikin jikinsa, cike da shagwaɓa tace " Barka da hutawa !"
Wani irin zubawa tsikar jikinsa yayi, domin kuwa yanayin yanda tayi maganar, sai ya tuna masa da Sugar babynsa wato (Zahrah) nature ɗin zahrah kenan shagwaɓa, samun kansa yayi da sakin wani ƙayataccen murmushi, haɗe da sanya hanunsa yashafi tattausan sajensa, "My Man !" kyakkyawar yarinyar, dake kusa da shi taƙira sunansa cikin muryan sangarta,, kallonta kawai yayi batare da ya amsa mata ba, sake kwaɓe fuska tayi, domin sarai tasan weakness ɗinsa, harshenta ta ɗaura akan laɓɓanta tashiga lasa a hankali tana mai marairaice idanu,, miƙewa Zaid yayi yanufi wata hanya da zata sadasa, da babban ginin hotel ɗin dake gefe da beach ɗin, tashi tayi itama ta rufa masa baya, tana tafiya tana kakkarya jiki, fatan ta ɗaya "Allah yasa yau tasamu ya kusanceta, domin a matuƙar matse take, gashi idan Zaid yana NYC bata ba kula samarinta, domin idan harta kulasu tofa lokacin rabuwarsu yazo"...
Yana shiga cikin wani katafaren ɗaki, wanda nan ne masauƙinsa, a wajen, ya faɗa kan gado haɗe da sauƙe nannauyar ajiyar zuciya,, turo ƙofar ɗakin tayi a hankali, saurin maida kallonsa bakin ƙofar yayi, domin ganin wayashigo masa ɗaki kai tsaye, saboda baisan tana biye dashi ba.. ƙamewa yayi ƙam tamkar statue kasa ɗauke idanunsa daga kanta yayi, tsaye take jikin ƙofar daga ita sai pant da breziya, wanda hakan yayi nasaran bayyana girman breast ɗinta a fili, wani irin yawu ya haɗiye a maƙoshinsa, "Wayyo Akeela zata kasheni, bana ɓuƙatar mace a dai dai wannan lokacin, amma dole na rage wannan masifaffen sha'awar dake damuna " Zaid yafaɗi haka a cikin zuciyarsa,, cike da kirsa haɗe da rangwaɗa Akeela taƙaraso garesa, kaitsaye ta faɗa kan faffaɗan ƙirjinsa, haɗe da manna masa kiss akan kwantaccen sajensa, wani kallo irin na cikakkun ƴan bariki, Akeela ta shiga jifan Zaid dashi, kyakkyawan murmushinsa yayi ma ta haɗe da sanya hanunsa, cikin dogon gashin kanta, yashiga shafawa, Akeela tana da tsantsar kyau da diri, sai dai ko da da taƙi ɗayane, bata kai Sugar baby'nsa ba, har yau yanajin jina ma Zahrah, domin kuwa tabbas Zahrah tacika mace iya mace,,
"Akee baby!!" Zaid yaƙira sunanta da wani irin tone mai tsuma zuciya, tuni taƙara narkewa a cikin jikinsa, haɗe da goga masa cikakkun breast ɗinta akan chest ɗinsa, rungumeta yayi tsam acikin jikinsa, yana mai jin wani irin feelings na taso masa, ƙoƙarin haɗe bakinsu waje ɗaya Akeela tayi, amma bata samu daman hakanba, domin kuwa Zaid kawar da kansa gefe yayi... Ko kaɗan bata damu da hakan da yayi ba, saima sake rungumeshi da tayi, cike da ƙwarewa Zaid ya sanya hanunsa, akan bayanta, ya shiga ɓalle ma ɓallan breziyan dake jikinta, jirkito da ita yayi zuwa ƙasansa shikuma ya haye kanta, cike da salonsa mai fitar da mutum a hayyacinsa, ya ɗaura bakinsa akan nipples ɗinta, yanda yake sucking ɗin nipples ɗinta, yasanya ta ficewa a hayyacinta lokaci ɗaya,, bawani ɓata lokaci itama tasoma nuna masa kalan nata salon, duk da kuwa cewa nasa salon ya ruɗata...
Sosai Zaid da Akeela suka dirji junansu, Akeela kam tasamu abun da takeso, domin kuwa Zaid yakawar mata da duk wata sha'awar dake jikinta, shikuwa Zaid ko da ɗigon gamsuwa bai samu daga Akeela ba, sam yarasa mai ke damunsa, daga sanda ya kusanci Zahrah zuwa yau, bai sakejin gamsuwa ajikin wata ƴa mace ba, kwatan kwacin wanda yasamu ga Zahrah, duk da kuwa fyaɗe yayi mata bawai a son ranta hakan yafaru ba..
Fuskarsa babu yabo ba fallasa haka yashige cikin bathroom yasakar ma wa kansa shower, hakanan yakejin ƙunci da takaici acikin zuciyarsa.
(Ya Allah! kataimakemu ka tsaremana rayuwarmu, Ya Allah!! ka tsarkake mana zuciyoyinmu, ka rabamu da sharrin shaiɗan, dakuma bautawa zuciya, Ya Allah!kakaremu daga sharrin zina!! Ya Allah kashiryar damu bisa hanya mai kyau,, Wallahi zina mugun ciwo ne, dake bin jini da jijiya, zina tana yaɗuwa acikin a halin duk wanda ya aika ta ta, Zina tana gurɓata rayuwa, Zina tana ɗaiɗaita imani, Ya Allah kakaremu, katsaremu da tsarewarka Ameen!!!)
Sosai Zaid da Akeela suka morewa Zina a wannan rana, domin dai wuni sukayi maƙale da juna, duk da kuwa bawani daɗinta yake jiba, masiface kawai irin ta zina dakuma bautawa zuciya, da biyewa shaiɗan, (wa'iya zubillah! ya Allah kashirya!!)
*ABUJA NIGERIA*
Yau kwanan Zahrah biyu da dawowa cikin hayyacinta, saidai har izuwa yau, bata daina ruskar kuka ba, su Inna sunyi rarrashin harsun gaji, tunda kuwa ta dawo hayyacinta Dr S.S baisake koda leƙo ɗakinnata ba, allurai da magunguna ma duk Nurses ne masu yi mata,
Kwance take akan gado, yayinda gaba ɗaya pillow'n da tayi matashi da shi, yajiƙe jagwab da hawaye. Inna ce taturo ƙofar ɗakin tashigo bakinta ɗauke da sallama, da sauri Zahrah tatashi daga kwancen da take, haɗe da kamo hannayen Inna cikin muryarta da ta daina fita tsabar kuka, tace "Kitaimaka Inna yau mubar asibitinnan, wallahi banjin zan iya sake kwana a cikin wannan asibitin !!" Zahrah taƙare maganar cikin kuka,,
"oh ni yazanyi dake ne Zahrah, tunjiya kike cewa mutafi gida, taya kike tunanin zamu tafi bayan ba a sallame mu ba? kiɗan ƙara haƙuri idan wannan likitan yazo saimu tafi ko !!" Inna taƙare maganar da sigan lallashi,
Kuka Zahrah tafashe dashi mai tsuma zuciya, ita kaɗai tasan irin ciwo da raɗaɗin da takeji acikin zuciyarta, ita kaɗai tasan yanda baƙinciki yaɗarsu acikin zuciyarta, inama da ace bawa yana da ikon kashe kansa, to tabbas ita kam da takashe kanta,ko zata samu sauƙi da kuma sukuni a ga me da raɗaɗin da takeji a cikin zuciyarta, ya ruguza mata duk wani farinciki na rayuwarta, ya tozarta mata rayuwa, ya wulaƙanta mata rayuwa, zataci gaba da yi mawa kanta addu'a, Allah yakawo mutuwarta nan kusa, ko zata huta da tsananin baƙin cikin da rayuwarta take ciki...
Har dare ya raba babu Dr S.S babu labarin sa, duk da kuwa cewa yana cikin asibitin, kallonta ta maida ga Inna dake zaune tana ta faman zuba gyangyaɗi, cikin takun sanɗa tanufi hanyar fita daga ɗakin, domin kuwa sosai tayarda da shawaran da zuciyarta ta bata akan cewa ta gudu, ta tafi wata uwa duniya, ko zata samu sassauci acikin zuciyarta, tabbas ta gudu shine shawaran da taji ya kwanta mata arai, don haka a yanzu zata bar asibiti, bakuma zata koma gidaba, wata duniyar da ba'a santaba zata faɗa, bata damu da tarayu ko kada ta rayuwa ba......
(tofa readers kunajin shawar da Zahrah ta yanke ko? Dan Allah kuyi haƙuri yau banmuku posting da wuriba, hakan yafarune saboda ƙarancin lokaci dana samu naje makaranta shi ya sa fatan zakumin uzuri, 👏👏👏 kuyi haƙuri yau page ɗin baida yawa, da nace zanbari sai gobe nayi posting, amma sai naga idan banyiba bazakuji daɗi ba.)
*16/November/2019*
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
phatymasardauna
*🎈Mrs Sardauna🎈*
*Dedicated To My Lovely Brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
'''{United we stand and succeed; our ambition is to entertein & motivate the mind of readers}'''
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*Chapter 31 to 32*
Dai dai ta ɗaura hanunta kan handle ɗin ƙofar kenan, aka turo ƙofar daga waje, cikin rashin sa'a ƙofar ya bugeta a goshi, saurin ja da baya tayi haɗe da rumtse idanunta gam, ji takeyi tamkar ta shaƙesa ya mutu, ta tsani ganin kowani irin namiji ne a rayuwarta, musamman ma shi,domin kuwa yanayinsu yana ma ta shige da Zaid, kuma gani take tamkar kowani namiji irin halin Zaid garesa,,
"Ganinki tsaye anan yatabbatarmin cewa guduwa zakiyi, Miye ribarki a rayuwa idan kika gudu daga gaban i yayenki ? nasan duk inda zaki bazakiyi rayuwa mai kyauba, idan kika zaɓi tafiya can wata uwa duniya mai zaki tsinta? ina mai tabbatarmiki cewa babu wani abun da zaki tsinta sai, zallan takaici, dakuma ƙuncin rayuwa, zaman bariki kikeso kiyi? kokuwa zaman kanki kike so kiyi? " da sauri taɗago manya manyan idanunta dasuke cike tab da ƙwalla ta watsa masa wani irin mugun kallo...
"Babu abun daya shafeka da rayuwata, idan naga dama nayi kowacce irin rayuwa ma baishafeka ba, duk ba kune kuka jefa rayuwata acikin matsanancin duhu ba, wallahi na tsani naji koda kalmar farkon sunan kune a cikin kunnuwana, ballan tana aƙira sunan Namiji akusa dani, natsaneku! natsaneku!! " wani irin kukane ya ƙwace mata maicin rai,
"Kacuceni Zaid! Kacuceni! natsaneka tsana mafi muni! mai nayi maka dana cancanci wannan sakamakon a wajenka? mai na aikata maka wanda yasanya ka cutar da rayuwata? bazan yafe maka ba Zaid! kacutar dani, karuguzamin duk wani buri nawa, ka tarwatsamin rayuwata, mai yasa saini kazaɓa maiyasa!!!" taƙare maganar cikin ƙaraji da matsanancin kuka, tamkar wanda takama Zaid ɗin a gabanta..
Wani irin mugun tausayin tane yaji ya daki zuciyarsa, haƙiƙa Zahrah abar tausayice, domin kuwa tanacikin wani hali wanda take buƙatar abokin rarrashi da kuma mai kwantar mata da hankali,,, juyawa kawai yayi yafice daga ɗakin, domin kuwa jin kukanta yake har tsakar kansa.
Nurse yaturo tazo tayi mawa Zahrah alluran bacci, domin idan ba alluran bacci akayi mata ba yana da yaƙinin cewa kwana zatayi tana ruskar kuka..
Duk yanda yaso bacci ya ɗaukesa, hakan ya gagara domin kuwa duk juyin da zaiyi wani irin matsanancin tausayin Zahrah ne ke cika masa zuciya, baisan wani irin tausayawa yake mawa Zahrah ba, amma tabbas yasan tausayinta da yakeyi, yayi ƙarfi a cikin zuciyarsa, da ƙƴar dai yasamu ya yakice tunanin Zahrah, a cikin zuciyarsa ya samu yayi bacci, wanda rabin mafarkansa ya kasance na Zahrah ne...
Wanene Dr S.S. ?
Dr Sadeeq yakasance ɗa na biyu a cikin gidansu, Alhaji KHABEER SARDAUNA shine mahaifinsa, Alhj Khabeer wanda ake ƙira da Alhj Sardauna, mutum ne mai matuƙar karamci da kuma kyautatawa na ƙasa dashi, hakan yasa talakawa suke matuƙar sonsa, kasancewarsa ɗan siyasa, Hajiya Habiba itace mahaifiyar Dr Sadeeq, mace ce itama mai tsananin karamci dakuma kyauta, tana da kyakkyawan hali wanda kowa yashaida hakan, Dr Sadeeq shine ɗa na biyu a cikin gidansu, yanada yaya wacce ake ƙira da Aunty Raliya, Aunty Raliya dai, tana aure ne a cikin garin Abuja, tana kuma zaune a unguwar Wuse Zone 2, bayan Dr Sadeeq a kwai ƙaninsa Samad, Samad dai baya zaune a Nigeria yana zamane a Australia, a can yake da karatunsa, tun Dr Sadeeq yanada shekaru 20, Allah yayiwa mahaifinsu rasuwa, mutuwar da ta matuƙar girgizasu, amma babu yanda suka iya dole su ɗauki dangana domin kowani bawa da kalan tasa ƙaddaran.. yanzu tsawon shekaru biyu kenan Hajiya Habiba tana matsawa Dr Sadeeq, a kan cewa yafito da matar aure, amma abun yagagara, da anfara maganar aure sai abun yalalace, ko daga baya yace baison yarinyar, ko yace bata da nutsuwa, da haka dai magana zata ɓalakuce,, yanzu ne Hajiyarsa ta hura masa wuta akan cewa lallai tabasa nanda kwana kaɗan yafito da matar aure dan bazata ci gaba da zuba masa idanu babba dashi ace bai aje iyali ba....
Washe gari..
Ƙarfe 3 da rabi na yamma Dr Sadeeq da kansa ya rubutawa su Zahrah sallama, domin ya fahimci cewa matuƙar bai sallamesu ba, za a iya nemanta a rasa, bakuma zai so hakan ba.
Koda suka fito daga cikin asibitin, duk yanda yaso Zahrah tashiga cikin motarsa ya kaisu gida ƙiyawa tayi, dole haka yanaji yana gani suka tari mai taxi, baiyi ƙasa a guiwaba wajen shiga motar tasa ya rufamusu baya...
Suna isa bakin ƙofar gida, idanun Zahrah ya sauƙa a dai dai wajen da Zaid yake faka motarsa kullum idan yazo, wani irin muguwar faɗuwar gaba taji, take kuma zuciyarta tayi rauni, kuka ne ya kuma ƙwace mata, da sauri tafice a cikin motar dagudu tanufi cikin gida,, saida Inna suka sallami mai taxi kafun suka lura da Dr Sadeeq dake tsaye a bayansu yana ƙarewa yanayin unguwar tasu kallo, "A'a Likita dama kana biye damune ?" Baffa ya tambaya washe da baki,,
"Eh Baffa ina biye daku, dama gani nayi yakamata ace nasan gidan saboda magungunan ta basu ƙareba, nakuma san basha zatanayiba matuƙar ba'a tilasta mata ba"
"Ƙwarai kuwa likita ai taurin kai gareta, dole saida takurawa, to mushiga daga ciki mana " Baffa yaƙare maganar yanamai yi mawa Dr S.S nuni da ƙofar shiga gidan.. Baiyi musu ba haka yabi bayan Baffa suka shiga cikin gidan,
Inna ce ta baje masa wani ƙaton tabarma ya zauna akai, yayinda ta ɗebomasa ruwa a kofi ta aje mai.
Gyara zama Dr S.S yayi haɗe da cewa "Baffa inaso muyi wata magana ne idan har bazaka damuba "
"Faɗi maganarka kai tsaye likita, kada kaji wani shakku" Baffa yafaɗa yana mai dawo da hankalinsa ga Dr Sadeeq.
"Maiyasa bazaku kai case ɗin Zahrah kotu ba? yakamata ace amatsayinta na marainiya a bimata haƙƙinta, bai kamata ace wani ƙaton banza ya keta mata haddi ba, sannan kuma abarshi yaci gaba da walwala, inaga yakamata ayi wani abu akai" Dr Sadeeq yafaɗa cike da damuwa.
Nannauyar ajiyar zuciya Baffa ya sauƙe haɗe da jinjina kansa, cike da rauni yace "Bazanƙi shawaranka ba likita, sai dai a gaskia bazan ɓoye maka ba, hakan da kake so bazai samuba, domin yanda ka ganmu nan haka muke rayuwarmu, mu talakawa ne, cin yau da ƙyar na gobe da ƙyar, kuma maganan nan ma da nake maka, bansan wanene yayi mawa Zahrah fyaɗe ba, to ka ga kenan babu batun ma ɗaukar fansa"
"Wanene ZAID ?" Dr S.S ya tambayi Baffa.
Washe da baki Baffa yace " shine yaron da Zahrah ta amince dashi, yake zuwa zance wajenta, idan kuma bazaka mantaba ai nafaɗa maka shiɗin yaron kirkine, na tabbatar da cewa baisan haka yafaru da ita ba, da nasan dole zaizo" Baffa yaƙare maganar yana mai jinjina kai..
"Shine yayi mawa Zahrah fyaɗe !" Dr S.S yafaɗa murya a kausashe,
Gaba ɗaya idanunsa Baffa ya zaro, alamar maganar ta dake shi, "Zaid fa kace likita !" Baffa yafaɗa cikin kaɗuwa,
"Ƙwarai kuwa domin kuwa jiya ta ambaci sunansa, nakuma ji da kunne na, amma tunda kace ba zaku kai case ɗin kotu ba, bakomai ni zan wuce" Dr Sadeeq yafaɗa yana mai miƙewa tsaye, bayan yaciro damin kuɗi ya a jewa Baffa kan tabarma,,
"A'a hadda ɗawainiya haka likita? to to munagodiya!" Baffa yafaɗa cike da farinciki,
(hmm mai hali dai baya fasa halinsa)
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un! Malam hayaƙi, hayaƙi Malam a ɗakin Zahrah !!" Inna tafaɗa cike da tashin hankali, ai da sauri Dr Sadeeq da baffa, suka nufi ɗakin Zahrah'n wanda hayakin haryasoma cika tsakar gidan, dayake ƙofar bata da wani ƙarfi duka ɗaya Dr S.S yayi mawa ƙofar ɗakin tabuɗe, gaba ɗaya ɗakin yaturnuƙe da hayaƙi yayinda wuta kecin wasu kaya dake aje tsakiyar ɗakin, gefe da kayan kuma Zahrah ce durƙushe tana kuka, har wutan yakusa ƙarasowa gareta,
Cikin zafin nama, Dr Sadeeq yasanya hanunsa, ya janyeta daga tsugunnen da take, kai tsaye waje yafito da'ita, domin kuwa hayaƙin yasoma shiga cikin maƙoshinsu, Baffa da Inna kuwa ruwa suka ɗebo suka kashe wutan,
Riƙeta yayi gam yayinda ya kafeta da idanunsa da suka rune tsabar ɓacin rai,
Baisan meyake damuntaba, rashin hankaline ko kuma sangartane baisaniba, yasan cewa tanajin ciwo a cikin zuciyarta, amma abun da take ƙoƙarin aikata mawa kanta, kama yake da taɓin hankali, ƙoƙari yayi wajen danne zuciyarsa, haɗe da saisaita muryarsa, "Maiyasa Zahrah ? bazaki ɗau ƙaddaranki ba ?" yayi mata tambayar cikin tausasa murya, hawayene suke gudu haɗi da ambaliya akan fuskarta, gaba ɗaya jitakeyi duniyar najuya ma ta, dawowanta gida yasake tada mata da mikin dake maƙare cikin zuciyarta, duk da kuwa dama cewa mikin bai wau ya kwanta ba ne,,
Saurin saketa yayi sakamakon ƙarasowar Baffa da Inna wajen, zamewa tayi aƙasa dabas tana mai sakin kuka,
Kallon Baffa Dr Sadeeq yayi, kafun Baffa yace komai Dr Sadeeq yace, "Baffa ni nawuce sai nasake zuwa "
"To Likita mun gode ka gai da gida " Inna da Baffa suka haɗa baki wajen faɗa, da "To" kawai Dr Sadeeq ya amsa musu haɗe da sa kai yafice daga cikin gidan,
Kama hanun Zahrah Inna tayi suka zauna akan tabarma, cike da damuwa Inna tasoma cewa "Maiyake damunkine Zahrah ? sai kace akanki aka fa ra yin fyaɗe? gaba ɗaya duk kinbi kinɗaga hankalinki, muma kin ɗaga mana namu hankalin, a gaskia nida Baffanki munsoma gajiyawa da wannan halin naki, bayan kinso caka mawa kanki almakashi, likita ya hana, yanzu kuma ƙona kanki kikesonyi, wai kina cikin hankalinki kuwa Zahrah?"
"Gaya mata dai Salame, domin nima nan nasoma gajiya da rarrashi, yanzu dakika ƙona kayayyakin daya baki, shiɗin kika ƙona ne? tambayanki nake shiɗin kika ƙona ?" Baffa yafaɗa cikin faɗa faɗa, domin ya lura idan suka biyewa Zahrah tofa bazata taɓa daina yunƙurin kashe kanta ba..
Zuciyar Zahrah ne tasakeyin rauni, " Allah sarki ni, komai nayi, ganin laifina suke, shin bancancanci rarrashi da kulawaba? fyaɗe akayimini amma hakan baiwani shiga jikin kowa ba, natabbata idan da iyayena suna da rai, to tabbas da bazasu taɓa kwantar da hankalinsu ba, kuma nasan dolene sai sun ɗaukarmin fansa, bakuma zasu taɓa gajiyawa daniba, wayyo Allah na mutuwa tayi mini yankan ƙauna daku iyayena !!" maganar da Zahrah take faɗa kenan a cikin zuciƴarta, hawayenta ne suka sake tsananta zuba, sai yau ta tabbatar cewa Maraici bashi da daɗi, sai yau tasake tabbatar da cewa Allah ne kaɗai gatan ta, Zaid ya cuceta, yayi mata babban tabo wanda hargaban abada ba zata taɓa mantawa dashi ba, "maiyasa Zaid ?" tasake tambayar kanta bayan kuma tasan bata da amsa,,
Haka Inna da Baffa suka wuce ɗaki suka barta zaune a tsakar gida tana tsiyayar hawaye, babu mai rarrashi.
Tuƙin mota yake amma gaba ɗaya hankalinsa yanaga yanda yabaro Zahrah, tsantsar tausayinta yakeji, yanason taimaka ma ta amma to tayaya? ta wacce hanya? duk alokaci ɗaya ya tambayi kansa, wayarsa ce tasoma ƙara alamar shigowar ƙira, Zabba'u shine sunan dake yawo akan screen ɗin wayar, ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya ya sauƙe haɗe da ɗaukan wayar yakara a kan kunnensa,
"Cike da sangarta Zabba'u tayi masa sallama, amsa sallaman yayi a daƙile haɗe da cewa "Ganinan zuwa" ƙit yakashe wayar haɗe da cillata kan kujeran mai zaman banza, shi sam baisan yanda zaiyi da Zabba'u ba, amma a zahirin gaskia ɗabi'u da tarbiyanta basu masa ba,duk da kuwa cewa ƴar uwa take a garesa.
New York City
Tsaye yake agaban wani tangamemen cupboard paper, wanda yake liƙe ajikin wani abu kamar allo, sanye yake da 3 guater jeans, yayinda yabar gaba ɗaya surar jikinsa a waje, kasancewar baisanya rigaba, babban abun ɗaukar hankali ajikinsa shine lafiyayyun, 6 packs ɗinsa, dake kwance raɗa raɗa akan cikinsa, riƙe yake da wani dogon pen a hanunsa da'alama dai wani abu yake zanawa mai mahimmancin gaske,, ƙayataccen murmushinsa yasake, haɗe da ɗaukan glass cup ɗin da wine ɗinsa ke ciki, yakai bakinsa, saida ya shanye duka wine ɗin dake cikin kufin, kafun ya aje kofin kan wani ɗan ƙaramin table dake kusa dashi,
Hanunsa yasanya akan kyakkyawar fuskar daya zana a jikin cupboard paper ɗin, a hankali yashiga shafa zanen , hanunsa yakai dai dai saitin bakinta, haɗe da shafawa, idonsa ɗaya yakashe haɗe da lasan laɓɓansa,
"Kinkasa barina My Sugar Baby, maiyasa ? " yayi tambayar yana mai tsare zanen dake jikin cupboard papern da ido,
"Bazaki amsaminba ko? fushi kike dani ko sugar baby na?"
Yasake tambayar wannan zanen dake jikin cupboard paper'n.
Murmushi yakumayi haɗe da matsawa daf da cupboard paper'n bakinsa yaɗaura adai dai kumatun ta yamanna mata kyakkyawan kiss, "Kikulamin da kanki kinji My Zahrah!!" yafaɗi maganar cikin shauƙi,, sai alokacin nalura ashe zanen fuskar Zahrah ne raɗau ajikin cupboard paper'n, bakaɗan ba kuma zanen yayi kyau,, kyakkyawan ƙyalle yasanya yarufe zanen, haɗe da ɗaukar wayarsa yafice daga cikin ɗakin...
Yana fita falo Abid dake tsaye tun ɗazu yana zaman jiransa, ya saki tsuka, haɗe da cewa " Wai don Allah maika tsaya yi ? tun ɗazu fa kasan nakejiranka, amma ka shanyani "
Zama Zaid yayi akan kujera haɗe da jawo kwalbar wine ɗinsa, yashiga shan abunsa, ganin haka yasa Abid sauƙe ajiyar zuciya haɗe da girgiza kai, wato dai yau ƴan halinne suka motsa, gaskia Zaid yanada wuyan sha'ani, bakoda yaushe kake gane gabansa da bayansa ba, duk da kuwa tsananin sabon dake tsakaninsu, amma shi kansa wataran idan Zaid ya juye tofa baya iya gane masa.
"Kana yawan shan wine Zaid, baka tunanin zata iya janyomaka matsala nan gaba ?" Abid ya tambaya cike da kulawa, domin kuwa, shi ko za'a kasheshi bazai iya shan rabin wine ɗin da Zaid yakesha a rana ba,
"Maiyashafeka da shan wine ɗina ?sanin kankane natsani sa'ido " Zaid yayi maganar cikin haɗe fuska,
Dariya Abid yayi, domin kuwa yanzu yatabbatar cewa Shu'umin cin nasa ne ya motsa, "Okay i'm sorry bazanƙara ba, amma yakamata ace musauƙa ƙasa, babes ɗin nan fa suna jiranmu " Abid yafaɗa yana mai duba agogon dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa,
"Kaje kawai ka sallamesu, nikam bana ma buƙatar ganinsu, mata duk a bubbushe, ba wani diri mai burgewa, sai kace 1, kaje can kata fama idan zaka iya" Zaid yafaɗa cike da ƙuncin rai,
Dariya sosai Abid yayi, haɗe da tashi kawai yafita daga falon, gaba ɗaya kwana biyun nan yarasa maiyake damun Zaid..
Abid na fita Zaid yagyara zamansa, haɗe da lumshe idanunsa, gaba ɗaya fuskar Sugar Babynsa ne yake yimasa gizo a cikin idanun nasa.
Abuja Nigeria
Zahrah ce zaune akan ƴar yaloluwar katifarta, ta tanƙwashe ƙafafunta, yayinda kanta ke kallon sama, ruwan hawayene kawai ke gangarowa daga cikin idanunta, kallo ɗaya zakai mata wata irin muguwar tausayinta yadaki zuciyarka, domin kuwa wani irin muguwar rama ce ta bayyana a jikinta,
Da sallama Khausar tashigo cikin ɗakin, kamar daga sama haka Zahrah taji muryar aminiyarta ta wato Khausar, tana kai kallonta bakin ƙofa taga Khausar ɗin tsaye tayi turus,,
Ai dagudu Zahrah taje tafaɗa jikin Khausar, haɗe da sakin wani sabon kuka mai sauti, duk da cewa Khausar batasan abun dayake faruwa ba, amma tasan cewa ba lafiya ƙawartata take ba, kawai itama sai tafashe da kuka, hakanan taji wani irin tausayin Zahrah'n yacika zuciyarta, rungumeta tayi da kyau a jikinta, ko kaɗan Khausar batayi yunƙurin hana Zahrah kuka ba, saida Zahrah tayi kuka sosai, kafun ta tsagaita, a hankali take sauƙe ajiyar zuciya,, hanunta Khausar takama suka zauna akan katifar Zahrah'n,,
"Zahrah!" Khausar taƙira sunanta cikin sanyin murya, Zahrah bata iya amsa mata ba, sai ɗago idanunta da suka kumbura suntum tsabar kuka, tayi ta kalli Khausar ɗin,
Zaro idanu Khausar tayi, cike da tashin hankali tace "Zahrah maiyake faruwa ne, tun ranan nake ƙiran wayarki a kashe, nazo gida kuma bansamu kowaba, nazo yafi sau huɗu bana samun kowa acikin gidan, dan Allah ƙawata kifaɗamin maiyake faruwa ?" Khausar tayi maganar cikin damuwa.
"Rayuwata taƙare Khausar, yacuceni,ya yi mini babban illa, dakuma tabo wanda bazai taɓa gogewa ba, ya nakasamin rayuwata, ashe haka ƙaddara zata zomin mummuna? nayarda cewa kowani bawa da'irin tasa ƙaddaran amma ni tawa ƙaddaran tafi takowa muni, danasan haka zata faru dani, dana roki Allah daya kasheni kafun yanzu na...." Saurin toshe mata baki Khausar tayi, cike da ruɗani haɗi da tashin hankali, Khausar tace "Kada kiyi saɓo Zahrah, kinsani acikin duhu, kisanar dani maike faruwa dan Allah, gaba ɗaya kinsani cikin tashin hankali !" Khausar tafaɗa cikin ƙosawa,
"Za..i..d yayi min fyaɗe Khausar !!!" Zahrah tafaɗa tana maisake rushewa da kuka,,
Tamkar anwatsamata ruwan zafi haka Khausar taji ajikinta, lokacin da maganan Zahrah yadaki dodon kunnenta, "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un! Fyaɗe fa kikace Zahrah ?" Khausar ta tambaya cikin matsanancin tashin hankali, lokaci guda hawaye suka shiga sauƙa daga cikin idanunta, take jikinta yayi sanyi laƙwas,,
"Yacutar da rayuwata Khausar, ashe haka soyayya ta ke? rama alkhairi da cuta, ashe haka duniya take cike da azzaluman bayi? maiyasa yayi min haka Khausar? mainayi masa? yaruguzamin duk wani farincikin rayuwata, wayyo Allah na Khausar ki karɓi wuƙannan ki kasheni dashi ko da zansamu sauƙi da salama acikin zuciyata !!" Zahrah taƙare maganar tana mai miƙomawa Khausar wata wuƙa da ke aje gefenta,,
Matsanancin kuka Khausar tasanya, haɗe da jawo Zahrah jikinta, ta rungumeta ƙam, kuka suka shiga yi wiwi, babu mai lallashin ɗan uwansa...
((Agaskia banson abunda wasunku sukemin,musamman masu cewa naƙara musu yawan typing, inaso kusani cewa, banda wadataccen lokaci, inazuwa makaranta, inada miji, sannan kuma nima inada wasu uzururrukan, yakamata kuna hakuri, amma wasu har baƙar magana su ke ƙoƙarin gayamin don kawai shekaran jiya nayi muku typing kaɗan, hmm wlhy kunbani mamaki, ni bana neman faɗa da kowa, saboda banɗauki duniya komai ba, shekaran jiya a matuƙar gajiye nake saboda naje school, amma haka na lallaɓa nayi muku typing, a she duk da haka wasunku basu godeba, haka sukaita ƙananan maganganu, wata har cewa take wai tagaji da wayon danake yi,koda yaushe sai nace na gaji, yes dole nagaji tun da dai ni ba engine bace, da za'ace bazan gaji ba, kuma ina da abubuwanyi. kuyi haƙuri my real fans na zage inata faɗa, wlhy raina ne yaɓaci wasu komai kamusu baka burgesu.
Nadawo gareku sisters masu cewa Zahrah tasoma basu haushi sbd abubuwan da takeyi, yaka mata ace kufahimceta, bawai inabin bayan tabane, amma yana da kyau ku yi imagine akan ya mace za taji idan har akai mata fƴaɗe?dole za taji matsanancin ciwo, acikin zuciyarta, kuma dole ne abun zai zama babban tabo wanda bazai taɓa gogewa acikin zuciyarta ba, saboda haka kuyi hakuri kuyi mata uzuri. ))
*18/November/2019**
*MRS SARDAUNA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written by*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Lovely Brother Khabier (My ƙwarnafi, da mita, lol 😄)*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*Kusha Sha'aninku Team ZAIDU👇🤣*
*1-Rhupys khair*
*2-Maimunerh minah*
*3-Saudat 0ne*
*4-maryam wazeer*
*5-Aisha salis*
*6-Mar'uda*
*7-Oum Zahrah*
*8-Oum Aboul*
*9-Oum saddiqa*
*10-Oum suwaib*
*11-Nana jasko👌*
*12- Halima nancy*
*13-Zuwaira ibraheem*
*14-Aminan bash*
*15-Saudi ghans, real tawajena*
*16- Surayyah*
*17-Shamsiyya-7 shams*
*18- Rauda Umar*
*Kunayi inajin daɗi team Zaidu 🤣 amma fa iyakune kawai team ɗin nasa waƴanda basa ganin laifinsa, lol, nasu Zahrah kam ba'a magana suna cikin ƙunci😥, saura kuma Dr S.S.😂*
*Chapter 33 to 35*
(Kuyi haƙuri nayi mistake, ƙawar Zahrah sunanta Husnah ne ba Khausar ba, kamar yanda nasa a page ɗin baya, Husnah nakeson sawa, to bestyna saita tsayamin arai nasa sunanta,lol.)
Kuka suka shugayi wiwi babu mai lallashin ɗan uwansa, da ƙyar Husnah ta'iya tsagaita kukanta,haɗe da daidaita nutsuwarta, duk da cewa zuciyarta bata daina bugu ba, tamkar ƴar uwa ta jini haka ta ɗauki Zahrah, saboda haka duk wani abu daya faru da Zahrah tamkar da ita yafaru, domin kuwa abokin kuka shi'ake gayawa mutuwa, wannan abotar tasu tasamo asaline tun suna yara, haka kuma sun ƙulla abotansu cikin gaskia da yarda da juna,,
"Bazance miki kidaina kuka ba, Zahrah domin idan nace miki haka, banyi miki adalci ba, sai dai zan sake tunatarmiki cewa akwai Sarkin sarakuna, mai tausayi ga bayinsa, mai amsa addu'an bayinsa, mai basu, mai kuma hanasu, shi ishashshene akan dukkan komai, yanaji,kuma yana gani, sannan kuma shi ya wanzar da faruwar haka a gareki, tunkafun ya halicceki ya tsara, cewa hakan zai faru a kanki, kada kiyi jayayya Zahrah, domin kuwa babu wani bawa a duniya daya isa ruguza tsarin Allah, Allah baya bacci, yanasane da wanda sukayi cuta, dakuma wanda aka cuta, zaifi kyau ki miƙa al'amuranki garesa, haƙiƙa nasan cewa abun da Zaid yayi miki, abune mafi matsanancin ciwo acikin rayuwar ƳAMACE, amma kashe kai, ko kice a kasheki banaki bane Zahrah, rungumar ƙaddara ita tafi dacewa dake, haƙiƙa nasan cewa har gaban abada bazaki mantaba, amma inaso kiɗauki ƙaddaranki, kimiƙawa Allah lamuranki, da sannu zakiga sakayya, ke ba jahila bace, da iliminki na addini dana zamani, saboda haka inaso kiyi amfani da wannan ilimin naki wajen ɗaukar ƙaddaranki hanu bibbiyu, kada kice na faɗi haka ne don banasonki, wlhy inasonki ƙawata, inajinki tamkar jinin jikina, kawai dai hakan shine mafita !!" Husnah tayi maganar cikin tsananin tausayawa, yayinda ruwan hawaye suka gama wanke fuskarta...
A hankali Zahrah taɗago idanunta dasuyi jajur tamkar anwatsa musu garin barkono, ta kalli Husnah, sosai maganar Husnah yadaki zuciyarta, sai dai yazame mata dole shiga ƘUNCIN RAYUWA, da ace zata buɗewa mutane ƙirjinta suga, cikin zuciyarta, to tabbas da tayi hakan, domin tasan duk wanda yaga ciwon dake mamaye da zuciyarta, to tabbas dole ne zai koka mata, domin kuwa wani irin danƙareren ciwone yabaibaye zuciyarta, wanda batasa ran zata warke har gaban abada,
" Ashe babban kuskurene ɗaukar soyayya ka bawa wanda yafika? menene aibuna dan nafito a mace? me maza sukaɗauki mata ne? a she dan kana talaka shikenan kai bakomai bane? bakuma ka da ƴanci? ya ketamin haddina da ƙarfin tsiya, yanunamin ƙarfi da kuma fifiko, duk dan kawai ina mace, maiyasa ya tsalleke dukkan mata yazo kaina nida banda kowa sai Allah? nayi masa kuka, nayi masa magiya, na roƙesa amma ya toshe kunnuwansa, yacire duk wani imaninsa ya cutar da rayuwata, kigayamin miye laifina dan nafita cikin hayyacina ? ki faɗamin shin bancancanci in haɗiyi zuciya in mutu ba, f...ya...ɗ...e fa yayi mini Husnah!!!" Zahrah tafaɗi maganar cikin matsanancin kuka,
Duk yanda Husnah taso ta sake danne zuciyarta kasawa tayi, kawai sai ta sake sakin kuka haɗe da rungume Zahrah ƙam acikin jikinta,
Saida sukayi kuka sosai, kafun suka soma sakin ajiyar zuciya, take zuciyar Husnah tayi sanyi, amma banda ta Zahrah, domin babu wani sanyi daya ragewa zuciyar Zahrah.
A hankali Husnah tashiga shafa bayan Zahrah, wacce haryanzu sheshsheƙan kuka take,
" Ki tsaida kukanki Zahrah, kuka baya maganin komai, sai dai ya sanyamiki ciwon kai, addu'a ita kaɗai ce magani, nasanki Zahrah, inakuma da yaƙinin cewa baki kai kukanki ga Allah ba, kiji rani inazuwa " Husnah tafaɗa tana me miƙewa tsaye, kaitsaye ficewa tayi daga ɗakin, yayinda Zahrah tafaɗa kan katifa taci gaba da kukanta,,,
Mintuna kaɗan Husnah tashigo ɗakin hanunta riƙe da wasu magungunan da likita ya kawowa Zahrah, wanda takarɓo wajen Inna,,
Ledan da tashigo dashi ta jawo, haɗe da ƙarasowa wajen Zahrah, tamkar ƴa da uwa, haka Husnah ta jawo Zahrah jikinta, cike da tausayi haɗi da rauni tace " Kidaina kuka dan Allah Zahrah, kinga ko na tahomiki da abincin da kikafi so, Shinkafa da Kifi, Mom ce ta dafa " Husnah taƙare maganar tana mai buɗe wni kula, wanda ta ciro a cikin ledan da tazo dashi,
"Nasan bakici komaiba, kuma koda nace kici ma, cemin zakiyi kin ƙoshi, amma dan Allah kici ko kaɗanne zanji daɗi Zahrah, baki da kowa sai Allah, amma kada kimanta nidake tamkar gudan jini muke, damuwarki damuwata ce " Husnah tafaɗa tana mai zub da ƙwalla,
Kallonta Zahrah tashigayi, take kuma zuciyarta ta karye, sai kawai tafaɗa jikin Husnah, tashiga sauƙe ajiyar zuciya,,
Cike da lallami Husnah tashiga bawa Zahrah shinkafa da kifin da takawo, duk dacewa maɗaci yafi abincin daɗi a bakinta, amma hakanan ta daure takeci, badon komaiba sai don Husnah tacancanci tayi mata komai a rayuwarta, itace mace ta farko data fara bata kyakkyawan kulawa wanda tunda abunnan yafaru da ita babu wanda yabata, sai likita..
Duk da cewa bata wani ci mai yawa ba, amma zaiyi mata amfani, domin kuwa cikinta yajima ba'asa mai komai ba a cikinsa,,
Husnah nagama bata abincin, ta ɗauko musu Al'Qur'ani guda biyu, miƙawa Zahrah ɗaya taƴi, haɗe da buɗe mata fejin farko, cemata tayi su karanta a tare, duk da cewa da ƙyar muryarta yake fita amma sosai tayi ƙoƙari wajen karanta Al'Qur'ani,n.
Babu abun da yagagari Allah, Al'Qur'ani littafine mai cike da tarin haske, yana wanke zuciyar maikarantasa, yanasanya nutsuwa ga ma'abocin karantashi, take ƙuncin dake maƙare acikin zuciyar Zahrah yasoma ragewa, sunacikin karatun wani irin bacci ya yi gaba da'ita,, take ta kwanta a wajen tahau bacci,,
Murmushi kawai Husnah tayi haɗe da ɗaukar Al'Qur'ani'n, dake riƙe a hanun Zahrah ta aje gefe,
"Kayafe ma ta ya Allah! domin nasan tsananin tashin hankali da damuwa, su sukayi tasira a cikin zuciyarta, wajen mantar da'ita kai kukanta gareka!" Husnah tafaɗa tana mai kallon sama, gudun kada ta tashi Zahrah a bacci yasanya tasoma karatun nata ƙasa ƙasa...
((Ƙawaye: bawai nishaɗantarwa kaɗai shine amfanin muba, mu mata ne, kuma mu ƙawayen juna ne, yana da kyau, mu ƙaunaci junanmu, tsegumi, ƙyashi, baƙinciki, hassada, duk banamu bane, kamar yanda akace ciwon ƴa mace na ƴa mace ce, yana da kyau muɗauki hakan da matuƙar mahimmanci, du kanmu zamuso ace munsamu ƙawa kamar Husnah, to amma ta yaya zamu samu ƙawa kamar Husnah? dole ne mu tsarkake zuciyoyin mu, mudaina mawa junanmu ƙyashi da hassada, mudaina bawa junanmu mugayen shawara, mudaina zuga wasunmu sukai kansu zuwaga halaka, kada ki bata gurguwar shawara wanda zata cutar da'ita, wai don takawo kanta gareki domin kibata shawara, kada ki zugata akan cewa ta aika ɓarna, idan har bazaki faɗa mata alkhairi ba, to kada ki faɗa mata sharri, dukanmu mata ne, kuma dukanmu zuciyoyin mu suna da rauni, ta yarda dake, saboda kunyi shekara da shekaru kuna tare, hakan yasa ta ɗauki duk wani sirrinta ta zazzage miki, maiyasa tayi haka? saboda ta ɗaukeki ƴar'uwa, tunda ta sanar dake duk wani sirrinta, mai yakamata kiyi? saiki riƙe mata amana, ki tsare mata sirrinta, amma saiki kaje ki ka tona mata asiri a wajen mutanen duniya, idan kikayi haka kincancanci a ƙiraki da suna ƙawa? maiyasa muka ɓata kanmu ? mukaraba kan abotanmu ? saboda bama iya riƙe sirrin juna, kuma bamaso kowa ya ƙaru, ko ya samu buɗi, saimu kaɗai, yana da kyau muriƙe abotarmu da kyau, domin a matsayinmu na mata idan bamuyi abota da junan muba, da waye zamuyi? da maza? suda basusan yanda zasu magance mana matsalolinmuba, sirrin mace fa sai mace ƴar uwarta, please Sisters dan Allah muyi ƙoƙari wajen gyara zuciyoyinmu, domin mukasance abokai na ƙwarai, masu rufa asirin juna.))
Zaune yake a katafaren wajen shaƙatawa dake farfajiyar gidan, sanye yake da riga da wando na jamfa hadda hulansa, bakaɗan ba yayi kyau, kasancewarsa matashi mai jini a jika, sannan kuma dama akwai kyau ɗin tubarkalla, Wayarsace ƙirar iphone Xs Max riƙe a hanunsa yana faman latsawa da dukkan alamu abu mai mahimmanci yakeyi, ƙamshin turarenta ne yafara cika hancinsa, a hankali yaɗago kansa yakai dubansa zuwa gareta, sanye take da doguwarriga na atamfa wanda yakama jikinta sosai, yayinda ta saƙala wani ɗan ƙaramin vail a wuyanta, balaifi tayi kyau, tunda dama kyakkyawace.
cike da takun ɗaukar hankali taƙaraso wajen dayake zaune bakinta ɗauke da sallama,
Amsa mata sallaman yayi yana mai ɗauke idanunsa daga gareta, domin komai najikinta bayyane yake a fili.
Kujeran dake kusa dashi ta ja, ta zauna, cikin sauyawa murya amo tace, "Barka da zuwa Jarumi na"
Kai kawai yaɗaga mata alamar yaji, batare daya Kuma kallon taba, sake lanƙwasa murya tayi, takuma cewa "Yakamata mu'isa falon baƙi ai, sai nake ga kamar zaman mu anan baiyiba, kasan fa kai ɗin maidaraja ne baidace ace nabarka anan ba" taƙare maganar tana mai kaɗa idanunta, alamar yanga.
"Inaganin nan ɗin ma yayi ai basai munshiga ciki ba" Dr Sadeeq yafaɗa yana mai gyara zamansa,
Harara Zabba'u ta ɓallamasa ƙasa ƙasa batare daya gani ba, a zuciyarta kuwa cewa tayi "Inbanda Allah yaɗigamin soyayyarka a cikin zuciyata, da mai zai sanyani tsayawa, har ka wulaƙantani "
Ɗago da kansa yayi ya kalleta, cikin muryan dakewa yace "Ni zan wuce "
"Haba Yaya Sadeeq maiyasa kakemin hakane wai ? ko minti 30 fa bakayi da zuwa ba, amma kuma kace zaka tafi " taƙare maganar tana kwaɓe fuska tamkar wata ƙaramar yarinya, ko kaɗan kuma hakan baimata kyau ba, domin kuwa shekarunta ya wucewa abun da take ƙoƙarin yi, (wannan saimu nida bestyna jikar Hajiya sweet 19,lol)
Hanu yasanya a cikin aljihunsa yaciro kuɗi, aje mata yayi akan table ɗin dake gabansu, haɗe da tashi tsaye yasoma tafiya,, ganin haka yasa Zabba'u daɗa ɓata fuska, cike da ƙuncin zuciya, tarufa masa baya.
Mai gadi na buɗe masa gate yafice da motarsa, Zabba'u naganin fitansa, tasaki tsuka cike da takaici, wai ace kamar ita babbar yarinyar da maza suke mararin samunta, amma wai ita wani ke wulaƙantawa, kwashe kuɗin da ya aje mata akan table tayi haɗe da sakai tayi shigewarta gida...
Zahrah kuwa ba'ita tafarka daga wannan baccin da takeyiba, sai ƙarfe 6 na yamma, lokacin anata ƙiraye ƙirayen sallan magriba, har zuwa lokacin kuma Khausar tananan bata tafi ba,,
Koda ta tashi a baccin, ji tayi gaba ɗaya tayi sakayau da'ita, a cikin kaso ɗari na ƙunci da damuwarta, babu kaso talatin, Allahu Akbar haƙiƙa karatun Al'Qur'ani warakace ga duk wani damuwar zuciya, harma da ta rayuwa.
Matsowa kusa da'ita Husnah tasakeyi, cike da tausasawa takama duka hannayenta biyu,
"Bazan gajiya da faɗa miki ba Zahrah, yin imani da ƙaddara mai kyau ko marar kyau, shi'ake so ga ko wani musulmin ƙwarai, kuma Allah baya ɗaurawa bawa abun da bazai iyaba, idan kika ƙara haƙuri ki kaɗau ƙaddaranki, to ina mai tabbatarmiki da zaki samu kyakkyawan sakamako awajen ALLAH, haƙiƙa nasan Zayd ya cutar da rayuwarki, amma Allah bazai barshi ba, da sannu Allah zai saka miki,kimin alƙawari bazaki na yawan kukaba, sannan bazakina yawan damuwa ba, duk da nasan hakan abune mawuyaci, amma idan kika daure zaki iya, sannan kuma kuka baya maganin damuwa, karatun Al'Qur'ani kaɗai zaki riƙa, insha Allahu damuwarki zata gushe, sannan kuma, kinyi kuskure Zahrah kinbari tarin damuwar da kika shiga, ya hanaki kai kukanki ga Allah, kin manta shine maikowa mai komai, dan Allah Zahrah kimin alƙawarin cewa zaki rage sanya kanki a damuwa, duk sanda wani tunani yake shirin zuwa miki, to ki gaggauta ɗaukan littafi mai tsarki, ki karanta hakan zai sanyamiki nutsuwa !!" Husnah tayi maganganunta cikin lumana dakuma son sawa ƴar uwarta ƙwarin guiwa,,
"Bansan mai zance miki ba Husnah, amma haƙiƙa kinwuce ƙawa ke ƴar uwace, kuma koda a cikin ƴan uwanma keɗin ta da bance, namiki alƙawari cewa zan maid komai nawa ga Allah, haƙiƙa rayuwata tana cikin ƙunci da kuma baƙin ciki, amma nasan babu a bunda yagagari Allah, kuma da sannu rayuwata zatayi haske, duk da banda tabbacin hakan !" Hawayene kawai ke tsiyaya daga idanun Zahrah, domin sosai takejin ciwon abun da Zayd yayi mata, yanzu tayarda cewa dama haka Allah yatsara mata, kuma zata rungumi Ƙaddaranta, har Allah yakawo ma ta mutuwarta,, amma dudduniya bata taɓa jin matsanancin tsana ga kowa ba bayan Zayd,,
Sosai Husnah tabawa Zahrah shawara masu amfani, wanda zasu taimaka wajen cireta a damuwa,, saida akayi sallan Isha kafun driver'n gidan su Husnah yazo ya ɗauketa...
Tiryan tiryan Baffa ya ɗebi ƙafa, har ofishin Alhaji Umar, gaba ɗaya abun da yafaru da Zahrah, Baffa ya kwashe ya faɗa masa, bakaɗan ba hankalin Alhaji Umar ya tashi, domin kuwa shi Zahrah tamkar ƴa yaɗauketa, saboda mahaifinta yayi masa taimako sosai, cikin faɗa da hargowa Alhaji Umar kecewa zai kai case ɗin koto, saurin dakatar dashi Baffa yayi, haɗe da yagyara zama, ban baki Baffa yashiga yi wa Alhaji Umar, akan cewa kada yakai case ɗin kotu, domin kuwa yaron yafi ƙarfinsu, sannan kuma idan har aka kai case ɗin kotu, tofa sunan Zahrah ne zai sake ɓaci, wanda basusan an ma ta fyaɗe bama zasu sani, sannan kuma zata rasa mijin aure, domin wasu zasuce ba fyaɗe aka mata ba, ita takai kanta, kuma dole su zasukwan a ciki, domin basu da kuɗi, a yanzu yanda rayuwar duniyar nan take, mai kuɗi shine sarki, kuma mai kuɗi shi kaɗaine mutum, haka wasu suka ɗauka, ko shari'a ake mai kuɗi shiyake nasara,, sosai jikin Alhaji Umar yayi sanyi, domin kuwa tabbas maganganun da Baffa yafaɗa haka yake, kuma yasan duk kuɗinsa bai isa yaja da wanda suka fisa ba, domin shi ɗan ƙaramin mai arziki ne akan wasu...
((Sau dayawa akan cutar damu ƴaƴan talakawa, amma bamu isa mu kai ƙara ba, mune da gaskia, amma mu'ake bawa rashin gaskia, maiyasa ? saboda mu bamu da kuɗi, wanda bashi da kuɗi kuma ba mutum bane a wajenku ko? anacin zarafin ƙananan yara dakuma ƴan mata, amma ba a iya ɗauka musu mataki, saboda kawai wanda suka aikata abun masu hanu da shuni ne, mukuma an maidamu ko'oho, Allah sarki Allah ka'iyar mana, kabimana haƙƙinmu gaduk wani wanda yazaluncemu Ameen.))
*20/November/2019*
*Voted, comment, and share please... Wattpad @Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymerhsardauna
*Dedicated To My Lovely Brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*( Masha Allah! ina matuƙar tayaki murnan kammala daddaɗan book ɗinki my sweetheart (Ladingo Ummu Fareesa) Allah ya baki ladan dake ciki, yakuma yafe miki kurakuran dakikayi aciki, haƙiƙa kinyi ƙoƙari sosai Sweetheart, kuma littafin HATSABIBIYA RAMLAT ya nishaɗantar, yakuma faɗakar, fatan mu Allah yaƙara miki basira da hazaƙa Ameen, ina miki fatan alkhairi My Sweetheart.)
*Chapter 36 to 37*
A hankali yake tafiya da motarsa har yakawo ƙofar gidan, dai dai tsayawur motar tasa, Baffa ya fito daga cikin gida.
cikin hanzari ya ƙaraso inda motar Dr Sadeeq ɗin ke fake, "A'a likita kaine da yammacin nan haka ?" Baffa yafaɗa fuska cike da annuri,
"Eh wlh nine Baffa, tun safe naso zuwa, to aikine yayimin yawa " Dr Sadeeq yafaɗa yana mai ƙoƙarin fitowa daga cikin motar tasa.
"To muje nayi maka iso zuwa cikin gidan ko, aikuwa mutumiyar taka tanacan ta kulle kanta a ɗaki, tana karatu "
"Karatu kuma Baffa? badai ta dawo normal ba ?" Dr Sadeeq ya tambayi Baffa cikin sakin fuska, domin har yaɗanji sanyi a cikin zuciyarsa daga jin maganan Baffan,
"Ƙwarai kuwa likita, ai yanzu duk wannan hargowan kukan ta dainashi!" Baffa yafaɗa dai dai sanda suka kawo cikin gidan,
Da fari'a Inna ta tarbi Dr Sadeeq, haɗe da baje masa tabarma a ɗan madaidaicin tsakar gidan nasu, shima cike da mutum tawa ya gaida ta.
Bayan sun gama gaisawanne yake tambayar ko Zahrah tana shan magungunanta ?
Take Inna tace yabiyota tayi masa iso zuwa ɗakin Zahrah'n,
Ba musu yabi bayan Inna duk da cewa yasan hakan baidace ba, amma bayida wani zaɓi sai hakan, domin kuwa shima yanason ganinta.
Zaune take akan katifa, yayinda hanunta ke ɗauke da wani ɗan ƙaramin Al'Qur'ani, tana karantawa ƙasa ƙasa, a hankali taɗago kanta jin muryar Inna abakin ƙofar shigowa ɗakin nata,
"Shigo mana likita " Inna tafaɗa tana mai wangale ɗan yalolon labulen ɗakin,
Yanashiga cikin ɗakin, Zahrah tamiƙe zumbur daga zaunen da take, take jikinta yasoma rawa,
Ganin yanda yanayinta ya sauya alokaci ɗaya, yasa Dr Sadeeq tsayawa cak a inda yake, yana mai ƙare ma ta kallo, kallo ɗaya yayimawa idanunta, yafahimci cewa tayi kuka, take yaji ba daɗi a zuciyarsa.
"Zahrah!" yaƙira sunanta cikin muryar nutsuwa,
Kasa amsa masa tayi saima kau da kanta gefe da tayi tana mai rumtse idanuwanta, domin kuwa sosai Likitan yake mata yanayi da Zaid.
Cikin muryar nutsuwa ya kuma cewa "Kifito waje inason magana dake"
Yanakai ƙarshen zance'nnasa, yajuya yafice daga cikin ɗakin.
Tunyanasa ran fitowar Zahrah hardai yacire rai domin kuwa babu alaman zata fito ɗin.
Daga ƙarshe dai kayan marmari da kuma sauran magungunanta da ya taho mata dashi, sai Baffa ya bawa yace a bata, don yafahimci batason damuwa, kuma yafuskanci cewa tana matuƙar tsoronsa, baikuma san dalilin hakanba.
Tanajin ƙaran tafiyar motarsa ta sauƙe nannauyar ajiyar zuciya, hakanan duk sanda ta kallesa takejin faɗuwar gaba, shigowar Inna cikin ɗakin shiyayi sanadiyar katsuwar tunaninta,,
Ƙatuwar ledan da Dr Sadeeq yakawo, wanda yake cike da kayan marmari Inna ta aje mata haɗe da watsamata harara gami dayin tsuka tafice daga cikin ɗakin, domin yanzu gaba ɗaya tsananin haushin Zahrah'n takeji.
Ko kallon ledan Zahrah batayiba ballantana ta duba miye a ciki, domin itakam yanzu anshata kuma haryanzu bata warke ba, don haka babu wani ɗa Namiji daya isa yasake yaudaranta, babu kuma wani Namiji da zata sake amincewa dashi a iya tsawon rayuwarta, tasan cewa ingancin rayuwarta yariga dayagama ƙarewa, domin kuwa tasan cewa babu wani namiji dazai aureta, bayan yasan cewa Zaid yariga da ya gama keta mata rigan mutumcinta.
New York City
Gudu sosai motar tasa keyi akan titi tamkar zai tashi sama, yayinda jami'an tsaron dake tsaron titi suke tayi masa magana amma bayako sauraransu, kai tsaye katafaren gidansa dake cikin New York ɗin ya nufa, tundaga fitowarsa acikin motar zaka gane cewa a matuƙar buge yake domin kuwa sai haɗa hanya yake gakuma zungureriyar kwalbar giya dake riƙe a hanunsa, yana shiga cikin katafaren falonnasa, yafaɗa kan kujera, haɗe da lumshe idanunsa,
"MY ZAHRAH!!" yaƙira sunanta cikin wani sweetness voice ɗinsa, sannan kuma cikin yanayi mai nuni da cewa mutum yana cikin shauƙi,, da ƙyar ya iya miƙewa yakai kansa zuwa ɗaki, yanashiga cikin bedroom, kaitsaye ya wuce bathroom saida ya amayar da gaba ɗaya giyan da yasha, kafun yasamu nutsuwa, amma duk da haka mayen giyan bai sake sa ba.
Buɗe drowern sa yayi, haɗe da fiddo wani irin ƙaton hoto wanda gaba ɗayansa aka rufesa da glass ma'ana akayi masa gidan glass, ba hoton kowa bane face hoton kyakkyawar fuskar Zahrah tana murmushinta mai burgewa.
Murmushi yayi haɗe da mannawa hoton kiss, cikin unique voice ɗinsa yace "Inakewarki My Zumata, haƙiƙa keɗin ta da bance, verysoon inanan dawowa gareki, har yanzu sha'awarki bata sakeni ba, banƙoshi dake ba babyna, kikulamin da kanki kinji Sweet Zahrah na!!" yaƙare maganar cike da tsananin shauƙi, domin kuwa wani irin feelings yakeji a ga me da Zahrah'n, yarasa maiyake damunsa akan Zahrah, aƙa'idansa idan yayi sex da mace sau ɗaya, to baya sake waiwayanta harsai idan ita tawaiwayesa, nan ma saiyaga dama ya amsa tayinta, amma yau gashi yana mugun kewar Zahrah saboda yasha zumanta mai daɗin ɗanɗano, haryanzu baisan menene so ba, sha'awa kawai yasani akan haka kuma ya dogara.
Haka Bacci yaɗauki Zaid yanata sambatu irin na mashaya yayinda yake rungume da hoton Zahrah akan ƙirjinsa, yana ji tamkar Zahrah'nce dakanta ya runguma a ƙirjinsa.
Washe gari bashine yatashiba sai ƙarfe 9 na safe, salati yasoma yi cike da ƙuncin rai, sam baisan maiyasa yake makara sallan asuba a kwana biyunnan ba, ( Nace Saboda Zina bata haɗuwa da ibada ) daƙyar ya'iya tashi yashiga bathroom domin gaba ɗaya jiyake jikinsa na masa ciwo,gashi kuma baida time ɗin da zaiyi gym, wanka yayi cikin mintuna ƙalilan, fitowa yayi sanye da rigan wanka ajikinsa, agurguje yamurza lotion ajikinsa haɗe da sanya hand dryer ya busar da gashin kansa, wata baƙar jallabiya yasanya haɗe da nufar inda darduma ke shumfuɗe, yatada kabbaran sallah, ko kunya bayaji.
(Tir da hali irinnaka Zaid, sallah da rana faɗe faɗe Allah yashirya)
Yana idar da sallah, ya buɗe ma'adanan clothes ɗinsa haɗe da zaro wasu riga da wando masu matuƙar kyaun gaske, koda yasanya kayan sosai suka amshi jikinsa kasancewarsu masu kalar fari, daga takalmi, belt harzuwa agogon dake ɗaure a hanunsa kalar maroon garesu, haɗaɗɗiyar rigar suit maroon colour yaɗaura akan kayannasa, take yafito a asalin Zaid ɗinsa, wato Abundance, Increase, Increment, Superabundance, Addition, Excess, Surplus, haƙiƙa Zaid kyakkyawane kuma cikakken namiji da ya isa ɗaukar hankali ko wacce irin mace ce afaɗin duniyar nan, haƙiƙa Zaid yana da kyakkyawar sura irinta cikakkun maza, haka kuma yanada matuƙar burgewa abubuwan da Zaid kedasu naburgewa suna da tarin yawa, tamkar yanda ma'anar sunansa ke da tarin yawa, shikansa yasan yayi kyau sosai, babu kuma abunda ke tashi a jikinsa sai tashin ƙamshi mai sanya nutsuwa da kuma sanya shauƙi,
Al'adarsa ce kullum kafun yafita saiya bawa hotonta kyakkyawan sumba (kiss), to yauma hakance takasance domin wannan hoton nata yaɗauko, ya manna mawa kiss, haɗe da maidashi ya aje, kaitsaye yafice daga cikin ɗakin, ko sauraran kayan breakfast ɗin da aka aje masa akan derny table baiyi ba yasakai yafice daga cikin Aljannar duniyar falon nasa,, yana fita yashiga cikin motarsa, kai tsaye yawuce babban hotel ɗin dazasu gudanar da meeting, domin yau sunada gagarumin meeting, zuwa yanzu gaba ɗaya duk an hallara a wajen shikaɗai kawai ake jira, domin shida ma'aikatansa ne zasuyi meeting ɗin.
Nigeria
Yau kimanin sati guda kenan tunda Dr Sadeeq yazo baisake zuwaba, ɓangaren Zahrah kuwa sosai takesamun sauƙi acikin zuciyarta, sakamakon karatun Al'Qur'ani da tariƙe babu dare ba rana, zuwa yanzu ta dangana komai nata ga Allah, tasan ko ba daɗe ko ba jima zai bi mata haƙƙinta.
Zaune take a tsakar gidannasu tazuba uban tagumi, amma a zuciyarta karatu takeyi, Inna ce kishingiɗe a gefenta, tana koran sauron dasuka addabeta kasancewar dare yasoma rufawa domin kuwa har an idar da sallan magriba,,
Baffane yashigo cikin gidan fuskarsa ɗauke da fari'a, Inna ce kawai ta amsa masa sallaman da yayi, kallon Zahrah yayi haɗe da cewa "tashi ki ɗauko hijabinki likita na jiranki a waje"
Wani irin mummunan faɗuwa gabanta yayi, domin dudduniya a yanzu babu abun da zai ɗaga mata hankali kamar ace wai wani naƙiranta a waje, sam itakam tagama cire ƙauna da sake zuwa ƙiran wani, bata ƙaunarma koda sake fita waje ne,
"Wai ba magana nakeyimiki bane Zahrah kin shareni kuma bayan kinajina!" Baffa yafaɗa cikin faɗa faɗa,
Kuka Zahrah tafashe dashi haɗe da ɗago idanunta, ta kalli Baffa cikin muryan kuka tace "Baffa kataimakeni dan Allah, wallahi banso wani abu yasake faruwa da rayuwata !! "
"Ikon Allah, Malam kajita ko zata sake ɓarar mana da daman da muka samu na biyu, saikace akanta aka fara yin fyaɗe!" Inna tafaɗa cikin ɗaga murya,,
Da gudu Zahrah tajuya ta shige cikin ɗakinta haɗe da faɗawa kan gado tashiga rera kuka mai sauti, itakam batasan yanda zatayi da rayuwarta ba, batasan wasu irin iyaye bane Baffa da Inna, son zuciyarsu tayi yawa, kansu kawai suka sani, anya kuwa zasu rabauta da rahamar Allah ? cutar da maraya abune wanda ba kyau, kuma sunsani amma suke take saninsu, "Ya Allah kataimakeni !" tafaɗa cikin muryar kuka,
"Banni da'ita Salame nida itane, ai inbazata fita ba shi zaishigo cikin gidan " Baffa yaƙare maganar yana mai nufar ƙofar fita daga gidan.
Dr Sadeeq ne tsaye a jikin motarsa yasha sky blue ɗin shadda sai tashin ƙamshi yake,
Baffa yafito fuska a sake kai tsaye yanufeshi, "Yauwa likita ka'iso saikuyi maganar acikin gida ko, kasan mutumiyar taka sai a hankali" Baffa yafaɗa still washe da baki, like namesake ɗina (fatiwasha lol), ba musu Dr Sadeeq yarufa masa baya suka shiga cikin gidan.
Yauma dai a tsakar gidan yazauna duk da cewa babu yawancin haske a tsakar gidan amma akwai hasken farin wata.
"Wai Zahrah bazaki tashi kije bane, nacemiki gashi yashigo har cikin gida, dan Allah Zahrah kada ki watsamana ƙasa a ido, kidubi girman mutumcin dayayi miki sanda kike ciwon hauka kitashi kije " Inna tafaɗa cikin lallami.
"Ciwon Hauka kuma Inna?" Zahrah ta tambaya cike da mamaki domin dai ita a saninta batayi wani ciwon hauka ba,
"Ƙwarai kuwa kedai tashi kije kawai" Inna ta faɗa still cikin lallami, bawai don tasoba haka tasanya hijab haɗe da ficewa daga cikin ɗakin.
Tun fitowarta a cikin ɗakinnata ya kafeta da idanunsa, har taƙaraso can gefe dashi ta zauna, haɗe da takurewa waje ɗaya tana matsan ƙwalla,
"Saiyaushe zaki daina kuka ne?" Dr Sadeeq yatambaya cikin tattausar murya,
Shiru tayi bata amsa masa ba domin jin kalamansa take tamkar zuban narkakken dalma acikin kunnuwanta,
"Matsowa yayi gaf da ita, har tana iya jiyo ƙamshin turarensa, babu wani tsoro kokuma ɗar ya sanya hannayensa akan kumatunta yashiga share ma ta hawaye, sosai jikinta yaɗauki rawa domin tayi matuƙar tsorata da hakan,
"Banason kukanki Zahrah, nasani dole kina buƙatar ayi miki uzuri, kinajin ciwo da damuwa a cikin ranki, kuma kinada buƙatar kyakkyawan kulawa, kidaina min kallon wani bare kokuma na daban, kiyi mini kallon ɗan uwanki, wanda zaki iya gayawa damuwarki, inaso kifaɗamin duka damuwarki kinji ƙanwata, nasan zakiji sanyi idan kika faɗi ko kaɗanne daga cikin damuwarki !!" Dr Sadeeq yayi maganar cikin lallashi dakuma tausasawa,
Kuka takuma sanyawa mai sauti, domin kuwa tabbas abun daya faɗa ɗin hakanne, tana buƙatar mai kulawa da'ita, tana buƙatar ɗan uwa mai ɗaukar damuwarta, saurin ɗago da kanta tayi ta kallesa, sakamakon jin hannayensa da tayi akan nata,
Kai ya jinjina mata batare da yace da ita komaiba, yana kallonta tayi kuka harta ƙoshi, a hankali take sauƙe ajiyar zuciya, kofin ruwan dake gefensa ya ɗauka, haɗe da kawai bakinta, babu musu taɓuɗe baki ta soma sha, domin kuwa yanda zuciyarta ta bushe tana buƙatar ruwan,, saida tasha fiye da rabi kafun ta tsagaita da shan ruwan, sosai taji zuciyarta tasoma dawowa daidai nutsuwarta kuma yasoma sauƙa,,
"Yaushe zaki koma makaranta ?" Yajefomata tambayar kansa tsaye, kallon mamaki tabisa dashi, domin kuwa ko a wasan mafarki bata sake kawo sake zuwa makaranta acikin zuciyarta ba, itakam ai duk wani farinciki yawuce mata,
"Kada ki yarda da abun da zuciyarki takecewa, ba'akanki aka faraba, haƙiƙa abune mai ciwo amma idan kika daure zuciyarki, zaki iyayin rayuwar farinciki kamar kowa" Dr Sadeeq yafaɗa cike da son ƙarafafa mata guiwa,
"Kada kayi ƙoƙarin yaudarana domin kuwa sam banda wani sauran farinciki, yaruguzamin duk wani burina, to yanzu inaso kasanar dani shin menene amfanin karatuna bayan zuciyata cike take da ƙunci? kuma miye amfanin farincikina bayan rayuwata ke waye take da duhu ?, zanfaɗama damuwata domin nayarda dakai, inajin ciwo mai zafi a zuciyata bankuma san ranan warkewarsa ba, shin maiyasa zaka ce nayi farinciki bayan kasan cewa bazantaɓa samuba ?"
Ɗan gajeren murmushi yayi haɗe da matse hannayenta gam acikin nasa, "Saboda inada yaƙinin baki farinciki mai ɗorewa, amma saikin daina sakanki a damuwa "
Wani irin kallo tawatsa masa wanda yake nuni da cewa tana buƙatar ƙarin haske akan maganganun nasa.
"Zahrah ke yarinyace mai ɗauke da tarin ƙuruciya, kinaga yadace kibar rayuwarki tatafi a haka ?"
Dr Sadeeq yatambaya yana mai kafeta da idanu.
"Haka Allah yatsaramin, BAZAN BUTULCE BA, yadda da ƙaddara yana da kyau, NAYARDA DA ƘADDARA TA, saidai kuma bazan mantaba har abada, babu mai aurena, babu kuma mai tallafawa rayuwata, zanƙare rayuwata acikin ƙunci, idan har kaɗaukeni ƴar uwa kamar yadda kafaɗa, to inaso ka yi tunani shin wacce ta tsinci kanta acikin mummunar ƙaddara irin tawa akwai sauran farinciki da yarage mata?, ni yarinyace haryanzu bangama sanin rayuwaba, amma tabbas nasan mai kyau dakuma marar kyau, saboda haka rayuwata a gurɓace take, yariga daya ruguzata, bakuma zata taɓa kafuwa ta tsaya da ƙafafunta ba har abada, BANI DA ZAƁI likita amma akwai Allah ya isarmin komai!!" gaba ɗaya hawaye yagama wanke mata fuska, wannan karan ba iya zuciyarta bace tayi rauni hadda tashi zuciyar, lallai ƙaddaran Zahrah mummuna ce, amma kuma yazama dole yatsaya yakawar mata da duk wani duhu dake rayuwarta shi mai iya dawo mata da farincikin tane idan harzata amince, amma yasani Zahrah ta yanke ƙauna gaduk wani ɗa namiji,
"Likita ga abinci ko" Inna takatsemusu tunanin da sukeyi su dukansu.
Inna tana aje abincin tajuya tashige cikin ɗaki, kallonsa yamaida kan ɗan ƙaramin bakinta dake bushe, sannan yakuma maida kallonsa kan idanunta, a matsayinsa na mutum mai karantar yanayin ɗan adam, take yakaranci halin da take ciki, bayajin yunwa ko kaɗan domin saida yaci abinci kafun yafito, amma saboda dalili ɗaya yasa yajawo kwanon abincin gabansa, shinkaface ƴar gida jalof, ko mai batajiba ballantana albasa, amma haka ya share, yakai loman abincin cikin bakinsa, taunawar farko yaci karo da dutse amma haka dolensa ya basar (readers likitafa yagamu da girkin manya Inna, lol🤣).
"Zo muci" yafaɗa a taƙaice,
Saurin kallonsa tayi haɗe da girgiza kanta, domin ita yanzu abinci baya gabanta, damuwarta ma abincine a wajenta,,
Babu alamar wasa akan fuskarsa kaitsaye yanufi bakinta da hanunsa wanda yake ɗauke da ƙwayoyin shinkafa domin da hanu yakecin abincin,,
Saƙare haka tayi tanakallonsa domin wannan shine karo na farko a rayuwarta da wani ɗa Namiji ba muharraminta ba ya taɓa yunƙurin bata abinci a baki,
Kai tagirgiza masa alamar bataso haɗe da kawar da kanta gefe,
"Kinaso muyi faɗa kenan, kuma hakan nanufin baki ɗaukeni ɗan uwaba, nasan wunin yau bakisa komai a cikin kiba, sbd haka banason gardama, idan kuwa kikace bahaka ba, to akwai alluran da na taho da'ita, yanzu sainasa Baffa da Inna su riƙemin ke na yi miki har guda uku!! " yaƙare maganar in a serious tone, aikuwa ya faɗar mata da gaba domin kuwa tsoron alluran da takeyi haryazarce tunanin mutane, "Haaaa" Dr Sadeeq yafaɗa still yana kusanta hanunsa ga bakinta, tamkar dai za abawa ƙaramin yaro abinci.
"Basaikabani ba zan iya ci!" Zahrah tafaɗa cikin raunanniyar muryarta,
"To ci ingani" Shima yafaɗa yana mai turo mata kwanon abincin gabanta, ahankali ta sa hanu ta tsakuri abincin, tamkar wacce akace ta tsakuro garwashin wuta da hanunta, daƙyar ta iya buɗe baki ta kai loman abincin bakinta, murmushi yayi haɗe da sanya hanunsa acikin kwanon abincin yasoma ci, duk da cewa ba daɗin abincin yakejiba, adole Zahrah take kai loman abincin bakinta bayanda ta'iyane kawai,,
Lomanta huɗu ta soma kwarara amai a wajen tamkar zata amayar da ƴaƴan hanjinta, miƙewa tayi daga tsugunen da take domin tasoma ɓata jikinta da amai, aikuwa wani irin jiri ne ya ɗe beta take ta faɗa kan Dr Sadeeq dashima yake yunƙurin tashi tsaye,, gaba ɗaya yatarota tafaɗa cikin ƙirjinsa, yayinda aman dake jikinta ya gogu ajikin kayansa,,
Da sauri su Inna da Baffa suka ƙaraso wajen domin tundaga ɗaki sukejin ƙaran amannata, "Lafiya likita maiyasameta kuma ?" duka suka tambaya cikin ƙosawa, da'alama dai sungaji da lamuranta.
" Bakomai inaga olsa (ulcer) ce kawai ke damunta " Dr Sadeeq yafaɗa yana mai ƙoƙarin shimfiɗeta a akan tabarman da suke zaune,
Saidai gaba ɗaya ba ƙarfi a jikinta, saboda haka duk ta narkemasa a cikin jiki, yayinda shikuwa zuciyarsa ke tsananta bugawa, addu'a yake a zuciyarsa Allah yasa ba abun da yake zargi bane ke damun Zahrah idan kuwa abun da yake zargine tabbas babban tashin hankali na gaba...
(Wani tashin hankali munbanu readers 😲, Allah yasadai bacikine da ita ba, da Zaidu ya yi aiki mai tsada 🤣 )
*Breakfast na baku kuji daɗinku*
*23/November/2019*
*Voted, Comment, and Share please....follow me on Wattpad @fatymasardauna
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Lovely Brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand & succeed; our ambition is to entertain and motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*Chapter 38 to 39*
A hankali Doctor ya kwantar da ita, cikin sanyin jiki yanufi motarsa don ɗauko jakarsa ta aiki, domin dama daga office yake yabiyo tagidannasu,, Allah yasa ba abun dayake hasashe bane yake shirin faruwa, lallaiko idan har ya zamana Zahrah ciki ne da ita, to fa shikansama yashiga tashin hankali, bawai ita kawai ba, domin yasan ɗan guntun tsarin daya shirya rugujewa zaiyi, to ina kuma ga Zahrah wacce bata gama warkewa daga ciwon dake jikinta ba, kuma ace taƙara faɗawa cikin azabar wani ciwon, tabbas yasan tashin hankalin da zata shiga sai ya take wanda tashiga a baya,, jiki a saluɓe haka Dortor Sadeeq yadawo cikin gidan, zuwa lokacin har Inna ta ɗauketa takaita cikin ɗaki.
Tana kwance akan ƴar katifarta, sai faman sauƙe numfashi take a hankali, dagani kasan aman da tayi ya galabaitar da'ita sosai, zama yayi gaf da'ita, haɗe da kama hanunta, lokaci guda yaji jikinta yaɗau zafi sosai, kayan aikinsa dake cikin jakarsa ya ciro ya fara yi mata ƴan gwaje gwaje,
Wata irin ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya Dr Sadeeq ya sauƙe sakamakon gano abun dake damun Zahrah da yayi, duk da cewa baiyi mata gwajin ciki ba, amma a iya ɗan bincikensa da yayi ya gano cewa bata ɗauke da ciki, ulcer ce kawai tayi mata mummunan kamu, sakamakon yunwa daya samu mazauni acikin cikinta.
Kallonsa yamaida kan Baffa haɗe da cewa " Bawani babban damuwa bane ulcer ce, yanzu zanje na ɗauko wasu allurai a asibiti sainazo nayi mata, insha Allah komai zaiyi dai dai"
"To likita Allah yayi albarka muna godiya sosai !" Baffa yayi maganar cike da yabawa ƙoƙarin Dr Sadeeq.
Miƙewa Dr Sadeeq yayi haɗe da sakai yafice daga cikin ɗakin, yana fita su Inna ma suka mara masa baya.
Kwanciya tayi lamo tamkar wacce ruwa ya ƙare mawa a jiki, gaba ɗaya jinta takeyi bata da kuzari, gawani irin zafi da ƙuna da ƙirjinta keyi mata,,
Koda Dr Sadeeq ya ɗauko magunguna da Alluran da yakamata ace yayi mata, sai da ya biya ta wani katafaren wajen sai da kayan marmari yasaya mata dangin su apple da su inabi hadda abarba, bai tsaya anan ba hadda fresh milk saida yabiya ya saya, gudu yashiga sharawa akan titi, burinsa ɗaya shine yaje yabata taimako mai kyau, sosai yakejin tausayinta, saboda ta cancanci a tausaya mata, daga wani ɓangare na zuciyarsa kuwa idan yatuno da cewa ba ciki bane da'ita, sai yaji wani irin sanyi da nishaɗi na ratsa zuciyarsa, wanda ya alaƙanta hakan da cewa bayason tasamu ciki saboda zata sake shiga wani hali marar daɗi. (kuji shifa😏 wai hakane reaɗers?)
Mintuna ƙalilan ya iso ƙofar gidannasu.
Koda yanemi Inna da tayi masa iso zuwa ɗakin Zahrah'n, cewa tayi yashiga kai tsaye ai anzama ɗaya su yanzu ɗan uwa suka ɗaukeshi (hmm)
Yanda ya barta haka yataradda ita sai dai yanzu idanunta a lumshe suke, "Zahrah!!" yaƙira sunanta dai dai lokacin da yake ƙarasawa kusa da'ita.
A hankali ta buɗe idanunta tasauƙesu a kansa, ɗan guntun murmushi yayi mata, wanda yasanya gabanta mugun faɗuwa, domin kuwa murmushin nasa yatuna mata da murmushin Oga Babba (ZAIDU manyan maza, lol), take taji wani irin abu ya toshe mata maƙoshi, yayinda zuciyarta tayi ƙunci.
Aje ƙatuwar ledan dake hanunsa yayi, haɗe da zama akan katifarta ta, "Tashi ki zauna" yafaɗa yana mai kafeta da ido, kai kawai ta girgiza masa alamar bazata iya tashi ba, ajiyar zuciya ya sauƙe, haɗe da kamo hannayenta duka biyu ya ɗagota zaune, duk da cewa yana matuƙar jin shock idan yataɓa jikinta, amma babu yanda zaiyi dole hakan shine mafita.
Ledar daya shigo da'ita ya buɗe, haɗe da ɗauko apple guda ɗaya ya miƙa mata, kallonsa kawai tayi haɗe da kau da kanta gefe,
"Magani bazaiyi aiki a jikinki yadda ya kamata ba, harsai kinci abinci, idan kuwa kikasha magani bakici abinci ba zai wahalar dake sosai, dan Allah banason gardama Zahrah, nasan kuma kema kina buƙatar abinci, don haka ki karɓi apple ɗinnan kici, ciwon ulcer bazai taɓa sake kiba matuƙar kina zama da yunwa!!" yaƙare maganar cikin lallashi.
Ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba haɗe da ɓata fuska, sam batason cin wani abu daga garesa, amma yana ƙoƙarin tursasata dole, kuma yayi gaskia dayace tana buƙatar abinci, tabbas ita kanta tasan tana buƙatar abinci.
"Yauwa Zahrah nasan dama keɗin maijin magana ce, karɓa kici ko!" yaƙare maganar yana mai marairaice fuska, haɗe da kusanto da apple ɗin dai dai saitin bakinta.
Hanu tasa ta karɓi apple ɗin, a hankali take gutsuran apple ɗin kamar mai gutsuran magani, duk da kuwa cewa taji test ɗinshi a cikin bakinta,, tana cinye apple ɗin ya miƙo mata goran fresh milk mai sanyi.
"Ungo wannan ma ko kaɗanne kisha, nasan zai taimaka kuma idan kika sha bazanmiki allura ba!"
Saurin kallonsa tayi, don tabbatar da abun da ya faɗa, aikuwa idan dai har bazai yi mata allura ba idan tasha, to lallai zatayi ƙoƙari tasha ɗin,
"Ka tabbata bazakamin alluraba idan nasha?" tafaɗi maganar a sangarce, cikin kuma yanayi na marar lafiya,
"Bazan miki allura ba Zahrah, idan dai harkika sha, kuma koda zan miki ma kaɗan zanmiki kuma bamai zafi ba!" yaƙare maganar yana murmushi.
Take tasake turɓune fuska haɗe da turo baki.
"Nifa wasa nake miki bawata allura dazan miki !" Dr Sadeeq yafaɗa yana dariya ƙasa ƙasa.
Karɓan goran fresh milk ɗin dake hanunsa tayi, haɗe da kafa kanta tasoma sha, tun asalinta ita mai son madara ce, haka kuma fresh milk yana ɗaya daga cikin abubuwan da takeso, sabo da haka sosai tasha har saida taji cikinta yacika, take kuma ɗan kuzari yasoma dawo mata, miƙo masa goran tayi alamar taƙoshi,
"Kishanye duka" yafaɗa a taƙaice,
"A'a naƙoshi" itama tabasa amsa ataƙaice,
"Okay to mai kikeson ci yanzu kuma?" yatambaya yana mai tsareta da idanu.
"Babu" ta basa amsa a taƙaice,
Kansa kawai yajinjina haɗe da ɗauko drugs ɗin daya taho mata dasu yasoma ɓarewa yana bata, sai ta rufe ido haɗe da ƙanƙame jiki sannan take iya sha, shiko dariyama take basa, bai taɓa ganin mai tsoron allura da magani kamarta ba.
Yana gama bata maganin yace ta kwanta, batayi ƙoƙarin musa masa ba, ta kwanta domin kuwa kafun yace mata kwantan, idanunta harsun fara rufewa,, "Zahrah!" yaƙira sunanta, shiru babu amsa kuma bata ko motsaba sai idanunta da suke buɗewa suna rufewa a hankali, da'alama dai yabata wani magani ne mai matuƙar kashe kuzarin jiki.
Dariya yayi ƙasa ƙasa haɗe da cewa "Yarinta da daɗi"
zuƙa zuƙan alluran daya taho dasu guda biyu, yaciro acikin ledan haɗe da haɗa komai da komai wanda ya kamata,
Riƙe alluran yayi a hanunsa haɗe da mai da kallonsa ga Zahrah wacce take kwance lamo, a hankali yasanya hanunsa ajikinta haɗe da juyata, saida ya rumtse idanunsa shima kafun ya'iya yi soka mata alluran, yana gamawa ya juyata ɗaya gefen ma yayi mata, sosai taji zafin alluran amma bata da bakin magana, sai dai hawaye da suka soma gangara daga cikin idanunta.
"kiyi haƙuri Zahrah ƴan mata, dolece tasa namiki alluran, inaso naga kinsamu lafiya ne!" Dr Sadeeq yafaɗi maganar cikin tausasa murya, bayan yashare mata ƙwallan dake sauƙa a gefen fuskarta, miƙewa yayi tsaye haɗe da sakai yafice daga cikin ɗakin, bayan yatattara kayan aikinsa.
Bai taradda Inna a tsakar gida ba sai Baffa, don haka a gurguje yayi masa sallama, yatafi sbd dare yasoma rabawa.
Ɓangaren Zahrah kuwa tun kafun Dr Sadeeq yafita bacci yayi awon gaba da'ita, domin daga magungunan har alluran da yayi mata suna saka bacci.
A hankali yake tuƙin motar tasa, fuskarsa cike take da annuri, Situation ɗin Zahrah kawai yake tunawa, sosai komai nata yake burgesa, musamman ma tsoronta, hakanan yakejin kansa cikin nishaɗi idan yana tare da'ita, baikumasan dalilin faruwar hakanba.
Koda ya yi parking motarsa kai tsaye ɓangaren mahaifiyarsa ya nufa, domin yau ko gaisawa basuyi ba ya fice daga gidan,
Koda yashiga falonnata bai isketa ba, don haka kaitsaye yanufi bedroom ɗinta domin yanada yaƙinin cewa zai taradda ita acan.
Knocking ƙofar bedroom ɗinnata yashigayi a hankali, jin knocking ɗin ya tsananta ne yasa taba wa mai knocking ɗin umarnin shigowa, domin dama tana da yaƙinin cewa shiɗinne kasancewar taji ƙaran shigowar motarsa cikin gidan.
Zaune ya'isketa akan sallaya, da'alamu idar da sallan nafilanta kenan.
Harƙasa ya durƙusa ya gaidata cike da girmamawa, cikin sakin fuska itama ta amsa masa gaisuwarsa haɗe da cewa " Ina kashigane yau tunsafe ?"
Ƙeyarsa yashiga sosawa a hankali, yayinda fuskarsa ke ɗauke da ɗan murmushi.
" Am Hajiya aikin office ne ya ɓoyeni, dana tashi kuma sai na biya ta gidansu Zahrah domin duba jikinta, to danaje sai nasamu batajin daɗi !" ya faɗi maganar fuskarsa ɗauke da alamar damuwa.
"Gidansu Zahrah kuma Sadeeq ?, to Allah ya sauwaƙa, a kwai a binci, a derny saika ɗebi iya yanda zaka iyaci, domin daganinka bakasa komai a cikin ka ba" Hajiya tafaɗi maganar cike da kulawa,
"To Hajiya zanci insha Allah" yaƙare maganar yana me miƙewa tsaye, sallama yayiwa mahaifiyartasa kafun yasakai yafice daga cikin ɗakin.
Yana fita Hajiya tasaki ƙwafa haɗe da cewa
"Nasan maganinka aure zanyimaka ko da baka shiryaba, natabbatar hakan zai sa ka rage yawan kaiwa dare a waje, kullum kai baka da hutu aiki tamkar engine, duk kuma rashin iyali shiya jawo hakan ".
Yana isa ɗakinsa yasoma rage kayan jikinsa, ɗan ƙaramin towel ya ɗaura haɗe da faɗawa bathroom yasakar mawa kansa shower, cikin zuciyarsa kuwa cunkushe take da tarin tunanuka kala kala, haƙiƙa yasan cewa yana buƙatar mace akusa dashi, domin dai shiba dutsi bane da zai zauna haka ƙiƙam ko da yaushe, dole yana buƙatar wacce zata na taimakawa wajen enjoying life ɗinsa, tun ba yauba yagane cewa yana ɗaya daga cikin maza masu yawan buƙata, amma kuma sosai yake ƙoƙari wajen shan pills wanda zasu sama masa relief, a gurguje yayi wankan yafito, wata brown ɗin jallabiya mai kyau yasanya bayan yatsane ruwan dake jikinsa, kulan abincin daya ɗauko a falon Hajiyarsa yajawo haɗe da buɗewa, jallof ɗin shinkafa ne sai coslow, kaɗan ya tsakura a cikin plate yasoma ci, gaba ɗaya tunanin Zahrah yacika masa zuciya wani irin feeling yakeji a kanta, idan yatunota sai yaji nishaɗi ya sauƙa acikin zuciyarsa, yanason komai nata, idan tana kuka tanayimasa kyau sosai, haka ma idan ta kwaɓe fuska bakaɗan ba take kyau, gaskia tana da abubuwan burgewa da yawa, da tunaninta yasamu ya kammala cin abincin duk da cewa baiwani ci mai yawa ba, saida yafita ya ɗanƴi exercise kafun ya dawo ya kwanta, domin a matsayinsa na likita yasan illan dake cikin kwanciya daga cin abinci..
Washe gari
Alhamdulillahi tatashi da ƙarfi a jikinta, sai dai ɗan abun da baza a rasa ba, tun tashinta da haushinsa ta tashi, domin jiya tanaji tana gani haka ya yaudareta yayi mata allura, bayan yagama kashe mata jiki da ƙwayoyin da ya bata, don haka bakinnan a ɗane yake ita adole tana fushi da likita.
Kasancewar yau Asabar babu aiki, yasanya bai tashiba harsai 9 na safe, wanka yayi yashirya cikin kaya masu kyau haɗe da baɗe jikinsa da daddaɗan turare, motarsa yanufa direct bayan yafito daga ɓangaren Hajiyarsa, JABI LAKE yanufa inda yayiwa Zahrah siyayya sosai.
(hmm readers kunaga zaƙewar doctor batayi yawa ba kuwa 🤔)
Yaukam har zauren cikin gidan yashiga anan yatsaya yasoma kwaɗa sallama, Cike da zumuɗi Inna dake zaune a tsakar gida tasoma amsa sallaman nasa, domin tasan bazai shigo hanu rabbana ba, sauran kayan maƙulashen da yasa yawa Zahrah jiyama ita tacinyesu.
"Iso mana likita, ai dakazo kawai ka iso, bawani nuƙu nuƙu nanma fa gidan kune !!" Inna tafaɗa fuska a sake,
Ɗan murmushi kawai Dr Sadeeq yayi haɗe da ƙarasa shigowa cikin gidan, akan tabarma ya zauna kamar koda yaushe,
Yana zama Zahrah tafito daga cikin banɗaki, daga ita sai ɗaurin zani a ƙirji sai kuma ƴar ƙaramar lufaya dake jikinta, kallo ɗaya zaka mata kasan cewa daga wanka take, saurin ɗauke idanunsa yayi daga gareta, yayinda ita kuma tayi saurin sunkuyar da kanta ƙasa, sam bata zaci ganinsa ba awannan lokacin. Sumi sumi haka ta raɓa tashige cikin ɗakinta.
Bayan sungama gaisawa da Inna ne ya yayi shiru haɗe da sunkuyar da kansa ƙasa, sarai Inna tasancewa wajen Zahrah'n yazo don haka kai tsaye tace masa yashiga yasamu Zahrah'n aciki.
Shikam harga Allah bayason shiga ɗakinta, domin kaɗaituwar mace da namiji a waje ɗaya hatsarine, amma ya ya'iya tunda yalura cewa iyayen riƙonnata ƙaramin tunani garesu.
Tsaye take atsakiyar ɗakin, saka rigarta kenan ko zip ɗin rigarma bata gama jaba, jin sallamansa yasa tayi saurin dawo da kallonta bakin ƙofar, harta fara zaton ko kunnenta ne yaji hakan ba sallamarsa bane, sai kuma taga yashigo cikin ɗakin, da sauri ta matsa jikin bango ta manne bayanta, domin gaba ɗaya bayanta a waje yake,
"Uh sorry nashigo kinasa kaya ko" Dr Sadeeq yafaɗa yana mai kallonta.
Harara ta gallamasa haɗe da turo bakinta gaba, dagani kasan fushi take.
Dariya yasanya harsai da fararen haƙwaransa suka bayyana,
"Fushi kikeyi dani ko?, to ai balaifina bane, dolece tasa nayi miki alluran don ki samu sauƙi, yanzuma kuma wasu alluran nazo nayi miki" yafaɗa yana gimtse dariyarsa.
Kuka Zahrah tasanya haɗe da sake matsewa ajikin bango,
"Dan Allah kada kamin, banason allura kataimakeni!" tafaɗa cikin muryar kuka da tsoro.
"Shiiii kada kitaramana jama'a madam, ni ba allura zanmiki ba wasa nake miki " Dr yafaɗa yana mai ɗaura yatsansa ɗaya akan laɓɓansa alamar tayi shiru.
"Ni bazansake yarda dakai ba, ai jiyama cewa kayi ba allura zakaminba, amma kuma shine kabani wani abu nasha kamin, ni bazan sake yarda dakai ba!" Zahrah tafaɗa tana matsar ƙwalla daga idanunta.
"Hahhh to ya'isa haka yanzu kam dagaske ba allura zanmiki ba, juyo na jamiki zip ɗin kinji ƴar ƙaramar ƙanwata !" Dr Sadeeq yafaɗa cikin tsokana,
"Dan Allah kafita banaso, zanzo na sameka, domin ni ba wani namiji da zai sake taɓamin jiki ehe !" Zahrah ta faɗa cike da shagwaɓa.
Wani irin zubawa tsikar jikinsa yayi, domin yanayin yanda tayi maganar kaɗai ya isa sanya jarumin namiji faɗawa cikin wani yanayi,
(Hahhhh likita bokan turai, to Zaid ma yafaɗa a wani hali, balle kai da bakasan salon mace ba 😂)
(Manage yau baida yawa sosai bacci nakeji kuma dama banda enough charge, wata acikin ku tataimaka ta tsammin charge pls 😥.)
*25/November/2019*
*Voted, Comment, and Share please. Follow me on Wattpad @fatymasardauna*
*1:58 pm*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
phatymasardauna
*Dedicated To My Lovely Brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*{United we stand & succeed; our ambition is to entertain and motivate the mind of readers}*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*( My Lovely, My Sweetness, My Happiness, My Best Friend ever, inasonki sosai da sosai ƙawata rabin raina, wannan page ɗin gabaki ɗayansa kyautane a gareki HAUWA Kulun MAJADAN 😂, JIDDATUL HUSSARY kiji daɗinki ki mo re ƙawata takaina HOUWER )*
*Chapter 40 to 41*
Nannauyar ajiyar zuciya Doctor ya sauƙe, haɗe da zura hannayensa a cikin aljihun wandon sa, "Shikenan to tunda kince haka, na baki two minute kacal kisameni a waje, idan kuwa bakifitoba zan dawo na sake iskeki, kuma wlh sai na danneki na jamiki zip ɗin da ƙarfin tsiya" dagajin yanda yayi maganar kasan cewa tsokana ce kawai.
Kai kawai ta iya jinjina masa alamar cewa taji zata fito ɗin,
Ɗan gun tun murmushi Dr yayi haɗe da sakai yafice daga cikin ɗakin.
Yana fita ta sauƙe nannauyar a jiyar zuciya, haɗe da sanya hanunta a bayanta, taƙarasa jan zip ɗin rigarta, zunbuleliyar hijabinta ta zura akan rigar haɗe da ficewa daga ɗakin, saboda tasan idan bata je bama tabbas zai biyota.
Zaune ta iskesa a cikin rumfar dake barandar gidan nasu, can gefe dashi ta zauna haɗe da kawar da kanta gefe domin kuwa ta lura gaba ɗaya idanuna akanta suke,
"Banason wasa matso kusa kisha maganinki !" yafaɗa babu alamar wasa akan fuskarsa.
Ɗan ƙaramin bakinta tacunno gaba haɗe da sake ɓata fuska, Allah ya sani ta tsani magani sosai da sosai, batama so ayi mata ko da zancen magani ne.
Batare da ya sake ce da ita komaiba yashiga ɓallo ƙwayan maganin daga jikin tablet ɗinsu, yana sawa a hanunsa, har sai da yagama ɓare iya wanda zatasha a yau ɗin, miƙo mata maganin yayi haɗe da bata goran ruwa,
Fuska a daƙune haka ta karɓi magananin saida ta rumtse idanunta sosai kafun ta iya haɗiye maganin, gashi dama irin magani mai ɗacin nan ne,
"Kishirya next week zaki koma makaranta " Dr Sadeeq ya faɗa yana mai latsa wayar da dake riƙe a hanunsa, bakuma alamar wasa akan fuskarsa.
Saurin dawo da kallonta garesa tayi, haɗe da girgiza kanta, "A gaskia ni bazan sake komawa makaranta ba !" Zahrah tafaɗa cikin ɓata rai,
"Maiyasa ? " Dr Sadeeq ya tambaya kai tsaye.
"Saboda babu amfanin hakan, ana karatune don a inganta rayuwa, to nikuma tawa rayuwar tajima da rugujewa, mai yasa zanɓata lokacina wajen gyara abun da bashi da kyau, bakuma zai gyaruba, na haƙura da komai zanjira mutuwata kawai !" Zahrah taƙare maganar cikin yanayi mai nuni da cewa zuciyarta tagamayin rauni,
" Idan ginin gida ya ruguje, ƙoƙari ake a sake gyarasa, akuma sabuntasa har yafi nada ɗin daya ruguje kyau, da kuma ƙawatuwa, shin kinsan maiyasa ake yin hakan? " Dr Sadeeq ya tambayeta bayan yamai da gaba ɗaya nutsuwarsa gareta.
"A'a" tafaɗa a taƙaice.
"Saboda yanada matuƙar amfani gamasu shi, sannan kuma yana da kyau idan karasa dama ta farko, kasake neman wata damar, domin sau dayawa anasamun nasara ne a gaba, bawai a farko farko ba, idan kika ci gaba da kashewa kanki ƙargin guiwa, to zuciyarki zata zama mai tsananin rauni, babu amfani idan kikace bazaki inganta rayuwarki ba, amma inaso kisanar dani fa'idan yin hakan, nuna kin yarda da ƙaddara yana ɗaya daga cikin mantawa da komai, idan kika zauna a gida, bazaki taɓa samun cigaba ba, nasan abun da Zaid yayi miki har yau yana cikin zuciyarki, kuma inada tabbacin cewa idan kinsamu wadataccen ilimi nan gaba, zaki iya yaƙi da azzalumai irin su Zaid, please Zahrah kada kicemin a'a, nayi hakanne saboda samamiki sauƙi, da kuma cireki a kaɗaici !" Dr Sadeeq yaƙare maganar cikin muryan tausasawa, dason ƙara mata ƙarfin guiwa.
Hawayen da suka shiga ambaliya akan fuskarta ta sanya hanu ta share
" Yar zuwa yau banajin akwai wani sauran farinciki daya ragemin a gaba, da wani ido mutanen duniya zasu kalleni? wasu zasu ɗauka cewa ni nakai kaina garesa, wasu zasumin dariya wasu ko zasumin Allah ya daɗa, babu wani namiji da zai tunkareni da sunan soyayya, rayuwata a yanzu tana gudana ne tamkar ruwan shayin da aka sa ma sa lipton amma ba asanya sugar da madara acikin saba, dan Allah kada ka matsa akan cewa lallai saina koma....."
"Ya'isa haka Zahrah, banason yawan gardama, shin bazakiyi ƙoƙari ki inganta rayuwarki ba? haƙiƙa Zaid yacutar dake, amma hakan bawai yana nufi ya ƙarar da rayuwarki bane baki ɗaya, matan da akamawa fyaɗe suna da yawa a duniyarnan, amma kuma hakan bai sa sun tauyewa kansu wani nau'i na jin daɗin rayuwarsu ba, ke mai yasa bazaki yi haka ba ? inaso ki manta da komai, kuma daga yau ɗinnan nagama maganata, next week zaki koma school insha Allah, tun yanzu saiki fara shiri !" Dr yafaɗa fuskarsa babu alamar wasa.
Aikuwa yanayin yanda taga fuskar tasa a ɗaure tamau yasa takasa ce dashi komai, hakanan yake mata kwarjini a cikin idanunta.
Miƙewa yayi tsaye, haɗe da cewa "Kibiyoni waje inason muyi wata magana"
Saurin kallonsa tayi, domin ita rabonta da fita waje tun randa mummunar ƙaddaranta ya rusketa, wanda kuma da bazata taɓa mantawa ba.
Jiki a saluɓe haka ta rufa masa baya, suna zuwa bakin motarsa taja ta tsaya, haɗe da sake tamke fuska.
Murfin ƙofar mai zaman banza ya buɗe haɗe da fiddo wata ƙatuwar leda,
" Idan har kika kumamin musu to tabbas zamu ɓata dake, sannan kuma wlh allurai shida zan danneki na miki da ƙarfin tsiya bandamu ba koda ma sun karye a cikin jikinki, ke kikaso!" Dr Sadeeq yafaɗa cikin tsare gida, yayinda yake miƙo mata zungureriyar ledan dake hanunsa.
"Dan Allah kayi haƙuri kada kamin allura, amma a gaskia ni baxan iya karɓan komai daga gareka ba, ni bazan sake karɓan abun kowa ba, domin kuwa da haka Zaid yasamu ya cuci rayuwata yasamin babban tabo mai wahalar gogewa!" Zahrah tayi maganar cike da tsoro da kuma ƙunan zuciya.
"Alluran dai kikeso kenan, shikenan bana ɗaukosu dama nazo dasu kusan guda goma" Dr Sadeeq yafaɗa yana mai niyar sake buɗe murfin motar.
A tamanin Zahrah ta ruga zuwa gida,
Dariya sosai Dr Sadeeq yashigayi, sosai yarintar Zahrah yake burgesa, haƙiƙa Zahrah yarinyace, domin kuwa kallo ɗaya zakai mata ka fuskanci cewa tsananin yarinta na damun ta sosai, akan allura gaba ɗaya ta ruɗa kanta.
Baiyi yunƙurin komawa cikin gidan ba, sai neman wani yaro yayi yabasa ledan yace ya kai cikin gidan, shikuwa key yayi mawa motarsa yayi tafiyarsa.
Zahrah kuwa tana shiga cikin gidan kaitsaye ɗakinta tawuce haɗe da banko ƙofar ta rufeta gam, faɗawa tayi kan katifarta tana mai sauƙe a jiyar zuciya, ko da taji ƙaran tashin motar Dr Sadeeq ɗin, wani sanyi taji a cikin zuciyarta, haka kawai yazo ya zurkuɗa mata wannnan maka makan alluran nasa, ai wlh bata saɓuwa.....
*New York City*
Kwance yake akan makeken gadon sa, daga shi sai ɗan wani 3 guater jeans, yayin da ya ware ƙafafunsa, duk da cewa akan gado yake, amma saboda tsabar iskanci irin na Zayd sanye yake da takalma (toms) aƙafarsa, yayinda hanunsa ke riƙe da wata zungureriyar kwalbar giya, gefensa kuwa wata kyakkyawar baturiya ce kwance tsirara bako ɗigon abun rufa tsiraici a jikinta, daganinta kasan irin cikakkun ƴan iskan nanne, gaba ɗaya ta tsare Zaid da idanunta, sai wani lasan baki takeyi tamkar tsohuwar mayya, bakomai yasa hakan ba, face yanda gaba ɗaya ta gama kwaɗaituwa da Zaid ɗin, amma kuma yaƙi amincewa ya kusanceta, gaba ɗaya wani irin muguwar sha'awarsa takeji, duk kuwa yanda ta nu namasa zallan karuwancinta a fili, yaƙi kusantar ta, saima sake je fata cikin kogin sha'awa da yayi,
Zaid kuwa da gangan yaƙi kusantarta, domin yanzu tsagwaran iskanci yake ji dashi, sai ya ɗauko mace yagama ƙwaƙuleta, yabarta batare da yayi sex da'ita ba, wayarsace tasoma ƙara alamar shigowar ƙira, har ƙiran ya katse Zayd bai ko kalli inda wayar take ba balle yasan wake ƙiransa,,
Cike da salo irin na ƴan bariki wanda ta yarda cewa idan hartayi masa zai kusanceta, ta sake matsowa daf dashi, a hankali ta zura hanunta acikin 3 guater jeans ɗinsa, haɗe da soma shafa kan mararsa a hankali, yayinda ɗaƴan hanunta ke kan faffaɗan ƙirjinsa tana shafawa slowly, ta yadda zaiji abun har tsakiyar kansa, cike da ƙwarewa tashiga murza ....
A hankali yaɗago idanunsa da suka soma sauya launi ya sauƙesu akan baturiyar, ai kuwa yayi kyakkyawan gani, domin kuwa fuskar Zahrah yagani ta bayyana akan ta baturiyar, bakomai yasa hakan ba face giyar da yasha da tasoma yi masa aiki, da ƙarfin gaske yajawo baturiyar jikinsa, haɗe da matseta ƙam a ƙirjinsa, take jikinsa yasoma ɓari,lokaci ɗaya yashiga bata kyakkyawan romance wanda yasanyata tafara nishin daɗi.
Gaba ɗaya baturiyar nan tadawo masa Zahrah acikin idanuwansa, baisan sai yaushene matsanancin sha'awar da yakemawa Zahrah zata sake saba, a kullum a ko wani daƙiƙa sha'awar Zahrah sake ninkuwa masa takeyi acikin zuciyarsa,
Hmmm duk jaraba irin ta wannan baturiya yau fa sai dai ta haƙura, domin kuwa Zaid tun kan abunnasa yagama shiga jikinta, yayi saurin tureta gefe, wani irin masifaffen ɓacin raine yazo masa, ƙarya ne yasani ba Zahrahn sa bace wannan, sharrin giyane kawai, idan har giya zata iya sanyawa yaga fuskar wata a matsayin Zahrah, to bata isa sawa ɗanɗanon wata yakasance tamkar na Zahrah'nsa ba, Zahrah da ban take komai nata na dabanne, cikinta a cike yake, bakamar sauran matan dayake mu'amala dasu ba, wanda su gaba ɗayansu a wage suke daga ciki har waje, ita kuwa Zahrah daga ciki har waje a haɗe take, bakomai yasanyashi ture baturiyar nan gefe ba face jinsa da yayi ya faɗa zuruf tamkar anzura ƙwallo a raga, bathroom ya wuce kaitsaye yasakarmawa kansa shower.
Itakuwa mayyar baturiyar dolenta ta maida ɗan fingilan rigarta ta fice daga cikin ɗakin, cikin matsanancin sha'awa, Zayd ya jangwalo mata bala'i.
Zayd kuwa a daddafe yayi wanka, domin kuwa wani irin ciwo marar sa ke yi, koda yafito a wankan a daddafe yasha tea da lamon tsami, kwanciya yayi lamo yana mai sauƙe numfashi akai akai, lallai yazame masa dole yakoma Nigeria kodan Zahrah ma, yazame masa dole yakomawa Zahrah domin kuwa bazai zauna sha'awarta ta kashe shi ba, amma ya ɗau alƙawarin cewa wannan karon bazai mata da ƙarfi ba, lallaɓata zaiyi tabasa kanta cikin sauƙi, da wannan tunanin bacci yayi awungaba dashi,
(Hmmm ayi bacci lafiya Zaidun Munubiya,lol).
Nigeria.
Yaune ranar da Dr ya shaidawa Zahrah cewa zata koma makaranta.
Don haka tun tashinta, tatashi tanajinta wani iri, gaba ɗaya ji take gabanta na faɗuwa, hakanan take tsarge, gani take tamkar kowa yasan maiyafaru da'ita, a daddafe tayi wanka, wata simple gown tasanya ajikinta, wanda bata da ado ko kaɗan, wata ƙatuwar lufaya ta zura wanda tsawonsa ya wuce guiwarta. Jin maganarsa a tsakar gidan, yasa taji ƙirjinta ya ɗan buga kaɗan, cikin rashin kuzari tafito daga cikin ɗakin.
Kamar yanda yayi mata kyau, haka shima yaga tayi masa kyau, duk da cewa babu ɗigon kwalliya akan fuskarta.
"Muje ko!" Yafaɗa a taƙaice, saurin ja da baya tayi haɗe da girgiza kanta, domin kuwa ko karen hauka ne ya cijeta, bazata yarda ta shiga motarsa ita kaɗai ba.
"Muje Baffa na jiranmu a waje" Dr Sadeeq yafaɗa domin yaga alamar a tsorace take,
Ajiyar zuciya mai ƙarfi ta sauƙe haɗe da bin bayansa, domin kuwa tuni yariga da yayi gaba.
(Please two days zakuna haƙuri dani domin typing ɗin ba ya yawa, ina busy ne sosai, dan Allah kada kuyi ƙorafi, insha Allah next page zanmuku da yawa)
*27/November/2019*
*Voted, Comment, and Share please...follow me on wattpad @fatymasardauna
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Lovely Brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*{United we stand & succeed; our ambition is to entertain and motivate the mind of readers}*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*Chapter 42 to 43*
Suna fita kuwa ta iske Baffa yayi ɗare ɗare agaban motar Dr Sadeeq sai washe haƙora yake kai kace anmasa kyautar ƴan kuɗaɗe ne.
Dakansa ya buɗe mata murfin motar ɓangaren gidan baya, cikin sanyin jiki ta shiga cikin motar, kaitsaye yashige ɓangaren driver haɗe da mawa motar key...
Tunda suka ɗau hanyar makarantar tasu Baffa ke faman zuba kamar wani kurna, yayinda Doctor Sadeeq ke amsa masa jefi jefi, domin hankalinsa gaba ɗaya yana ga Zahrah, wacce ke zaune tayi jigum a gidan baya, akai akai yake satan kallonta tacikin madubi..
A haka dai harsuka iso cikin makarantar tasu, dai dai bakin ƙofar hall ɗin da zasu gudanar da lecture yau, ya yi parking motar tasa, domin dama already ansanar dashi cewa yau a wannan hall ɗin zasu gudanar da lecture.
A hankali ta buɗe murfin motar ta fito kafaɗarta ɗauke da jakar makarantar ta, cikin takunta mai ɗauke da nutsuwa ta nufi cikin hall ɗin kai tsaye, ko wai gensu batayi ba, tanashiga hall ɗin kallo yadawo kanta, take taji wani irin muguwar faɗuwar gaba haɗe da karyewar zuciya, gani take tamkar kowa yana ganin abun da yafaru da ita rubuce akan goshinta.
Karab idanunta suka sauƙa akan Husnah wacce take faman aikin haɗa wasu takardu dake gabanta. wani irin sanyi taji zuciyarta tayi sakamakon ganin husnah, domin kaf makarantar bata mu'amala da kowa bayan husnah, da matuƙar farinciki Husnah ta rungume Zahrah, domin koda wasa batayi tunanin ganinta ba.
"Kamar mafarki nakeyi gaskia naji daɗi sosai ƙawata!" Husnah tafaɗa cike da tarin farinciki.
Zama sukayi a tare dai dai lokacin Sir Bature yashigo cikin hall ɗin, tsit haka ajin ya ɗauka ana ta sauraran lecture ɗin dayake yi musu, a zahirin gaskia tanajin abun da yake cewa, amma kwata kwata bata fahimtarsa, awa biyu suka ɗauka chur suna lecture, kafun daga bisani yafita daga ajin, gyara zama Husnah tayi haɗe da mai da kallonta ga Zahrah cike da kulawa tace " Yanzu ina likitan yake ?"
Ajiyar zuciya Zahrah ta sauƙe haɗe da cewa " Ba maganar Doctor bace damuwata Husnah, babban damuwata shine gani nake tamkar abun da Zaid yamin yana rubuce a gaban goshina, Husnah gani nake tamkar kowa yasan abun dake damuna !" Zahrah taƙare maganar cikin raunin zuciya.
" Kada kice haka Zahrah, babu wanda yasan abun da yafaru dake, kada ki ɗaga hankalinki ƙawata kinfasan kowa da irin tasa ƙaddaran, kuma zuwa yanzu na tabbatar kin mai da al'amuranki ga Allah, shima Zaid nasan kinbarsa da Allah "
Murmushi mai ciwo Zahrah tayi haɗe da kallon ƙawarta ta, cike da ƙuna tace " Banda wata hanya wanda tawuce barinsa ga Allah, nasan nan bada jimawa ba Allah zai bimikin haƙƙina " taƙare maganar cikin raunin zuciya,
Hannayenta Husnah ta kama suka fice daga cikin ajin, kai tsaye cafeteria suka nufa don cin abinci. Balaifi sosai tasamu nutsuwa a yau ɗin domin kuwa Husnah bata barta tayi kaɗaici ba. Ƙarfe 5 dai dai suka fito daga cikin lecture ɗin ƙarshe na ranan yau ɗin, kasan cewar ta kwana biyu bata zo makarantar ba, sai take jinta gaba ɗaya duk ta gaji, cikin nutsuwa take takunta yayinda kanta ke duƙe a ƙasa, ba abun da zuciyarta keyi banda bugawa, gaba ɗaya tsoron fita daga cikin school ɗin takeyi, gani take tamkar tana fita za'a kamata, da ƙyar take iya ɗaga ƙafafunta, dagani kasan bason tafiyar take ba. a hankali ta matsa gefe, haɗe da waigowa don ganin waye wannan ya matsa mata da horn ɗin motarsa, karab idanunta suka sauƙa akan sa, kasancewar gilasan motar tasa gaba ɗaya a sauƙe suke, sam batayi tsammanin ganinshi ba, murmushi yasakar mata haɗe da cewa " Da baki matsaba ai dana take ki !" yafaɗi maganar cikin yanayin tsokana, ɗan guntun murmushi itama tayi haɗe da taɓe baki, "ai idan haka ta kasance zanfikowa jin daɗi " Zahrah tafaɗi hakan da iya gaskiyarta.
"Shigo mutafi!" yafaɗa cikin tsare gida.
Saurin kallonsa tayi bakinta ɗauke da tarin tambayoyi, amma kuma takasa koda motsa bakinta ne balle ta furta wata kalman.
"Kintsaya kina kallona, ba dole idan bazaki bini ba, saina yi tafiyata!" yaƙare maganar yana mai niyar tada motar tasa.
Da sauri ta zagaya haɗe da buɗe murfin motar, gefen mai zaman banza ta shiga haɗe da tamke fuskarta tamau tamkar wanda yagayamata magana marar daɗi.
Da ƙyar ya iya ɓoye dariyan dake cinsa, domin kuwa tsoro ya hango ƙarara akan fuskar Zahrah, "Naɗauka ai zakijamin ajine, da sai na tafi na barki ba ruwana!" yafaɗi hakan cike da shauƙi.
Harara ta watsa masa haɗe da sake turo baki gaba, cike da shagwaɓa wacce batasan tayi ba tace "Nifa idan surutu zakamin ka sauƙeni nayi tafiyata"
Yanzu kam kasa ɓoye dariyarsa yayi saida ya dara kafun ya ce " Bazan sauƙe kiba ai bani na ɗauko ki na saki ba, zaki iya fita da kanki ma, ai nasan ke jaruma ce zaki iya kare kanki ako da yaushe, har ma zaki iya shiga cikin ko wani abun hawa da ƙwarin guiwarki !"
Saurin kallonsa tayi domin kuwa sarai ta fahinci inda maganganunsa suka dosa, wato dai shima ya hango zallan tsoron dake kwance akan fuskarta.
"Shikenan tunda haka kace" tafaɗi maganar tana mai ƙoƙarin buɗe murfin motar ta fita.
"Haba ƴar ƙanwata, nifa wasa nake miki, kiyi haƙuri ki bari na kaiki gida kinji ko!" Doctor yafaɗi maganar cikin lallashi, domin yafahimci cewa saurin fushi ne da'ita.
A cikin zuciyarta tayi hamdala, sakamakon hanata fita daga motar da yayi, domin dama burga ce kawai tsoron dake cikin zuciyarta bazai barta ta iya tafiya ba, duk runtsi tafiso shiɗin ya kaita domin tafi yarda dashi fiye da kowa a yanzun..
Kwantar da bayanta tayi akan kujeran motar haɗe da lumshe idanuwanta, gaba ɗaya jinta take a gajiye, ga wani irin ciwon kai dake damunta, a hankali take buɗe idanunta, a zabure tatashi zaune sakamakon ganin da tayi Doctor ya nufi wata hanyar da ita saɓanin hanyar gida.
"Inazaka kaini !" Tafaɗa a razane, kuma cikin yanayin tsoro,
"Saidake zanyi!" Yayi maganar babu alamar wasa akan fuskarsa.
"Dan Allah kayi haƙuri ka sauƙeni, ka barni naji da duhun dake cikin rayuwata, kada ka ƙaramin wani bala'in dan Allah!!" tuni hawaye sungama wanke fuskarta.
Wani irin kallo Doctor yayi mata haɗe da sakin murmushi bai kuma sake ce da ita komai ba, saima maida hankalinsa da yayi ga tuƙin da yake,
Yanzukam kuka mai sauti ta sanya haɗe da soma cewa " Dan Allah kada ka sake cutar da rayuwata, zan iya amincema ka kasheni amma bazan iya jure wa ba, idan kaci mutumcina, wlh na yarda ka wurgani kan titinnan mota ta taka ni, amma dan Allah kada kamin komai!!" taƙare maganar cikin matsanancin kuka mai taɓa zuciya. Daidai lokacin suka iso gaban wani makeken mall wanda yagaji da ƙawatuwa,
yana parking motar baiko kalletaba yayi saurin ficewa daga cikin motar haɗe da dannawa gabaki ɗaya ƙofofin fita a motar luck, domin yasan dole zatayi ƙoƙarin fita daga cikin motar,
Kuka sosai Zahrah keyi haɗe da sanya ƙarfinta tashiga dukan glass ɗin motar, tana mai ihun neman taimako amma babu kowa a wajen balle tasaran za a temaketa, domin kuwa wajen parking space ne.
"Ashe duniya cike take da azzaluman maza, ashe itakam rayuwarta a haka zata ƙare? wayyo Allah itakam ƙaddaranta kenan" abun da take faɗa kenan acikin zuciyarta tana kuka mai tsuma zuciya,domin a zaton ta hotel ya kawota zai kuma lalata mata rayuwa.
Daidai lokacin Doctor Sadeeq ya dawo hanunsa ɗauke da manyan manyan ledodi guda biyu, yana shiga cikin motar yakuma danna mata luck haɗe da mawa motar key da gudun gaske ya hau titi.
Zahrah kam muryanta har ya dashe kukanma harya daina fita domin gaba ɗaya ta gama sadaukar da cewa yau ce ranar mutuwarta, kukantane yasoma tsagaitawa ganin sun nufi hanyar unguwarsu, a hankali hawayenta suka daina zuba, yayinda tashiga sauƙe ajiyar zuciya akai akai, bakomai yasa hakanba face ganinsu da tayi sun shigo cikin unguwarsu tsulum, a bakin ƙofar gidan nasu yayi parking cike da kulawa yajuyo da kallonsa ga Zahrah wacce take ta sauƙe nannauyar ajiyar zuciya, alamar taci kuka ta ƙoshi.
"Banga laifin kiba Zahrah, domin dole zakiji matuƙar tsoro, a iya tsawon rayuwata bantaɓa cutar da wata mace ba, kuma bazan fara akan ki ba, bazan taɓa iya cutar dake ba Zahrah, inaso ki yarda dani, ban kuma yi haka don na cutar dake ba, nabiya dake ta mall ɗinne don inaso muje kiyi sayayyan abubuwan dakikeso da kanki, amma sai naga gaba ɗaya kinfirgita, kiyi haƙuri na tsorataki ko ƙanwata !!" Doctor Sadeeq yafaɗi maganar cikin tsananin tausayawa da kuma lallashi ga Zahrah'n..
Kuka kawai Zahrah takuma fashewa dashi haɗe da cusa kanta cikin cinyoyinta, a hankali ya kama hanunta haɗe da matsewa a cikin nasa hanun, "Banason kuka Zahrah, bana ce kiyi haƙuri ba!" Dr yafaɗa cikin damuwa.
"Bakaine zaka bani haƙuri ba likita, nice zanbaka haƙuri, nayi maka mummunar fahimta, dan Allah kayi haƙuri, wlh tsoro nakeji banso wani abu yasake faruwa dani...!" taƙare maganar tana kuka sosai.
"Idan kinaso nayi haƙuri to kidaina kuka kinji ƙanwata!" yafaɗi maganar yana mai ƙare matse hanunta a cikin nasa hanun.
A hankali tashiga share hawayen dake ambaliya akan fuskarta, ji takeyi zuciyarta tayi mata sanyi.
"Bakya kyau idan kina kuka, kinfi kyau idan kina dariya, kije gida kiyi wanka ki huta, banso kisake zubar da hawayenki kinji Zahrah, ungo wannan ledan kishiga gida, akwai waya a ciki na samiki sim da komai, akwai games dayawa a ciki,nasan zai ɗebe miki kewa, banson ganinki cikin damuwa Zahrah, kije gobe zanzo na kaiki school dakaina, Allah yasa bazakimin gardamaba " yaƙare maganar yana ƴar dariya.
Murmushi itama Zahrah tayi haɗe da ƙarɓan ƙatuwar ledan dayake miƙo mata, batare da tayi masa gardama ba, cikin rashin kuzari ta buɗe murfin motar tayi ficewarta, harsai da yaga shigewarta cikin gida kafun ya ta da motar tasa ya bar unguwar tasu..
Zahrah tanashiga cikin gida kai tsaye ɗakinta tawuce, jakarta da ledan da Dr Sadeeq ya bata ta ajiye. Kayan jikinta tashiga cirewa, zani ta ɗaura a kirjinta haɗe da sanya hijabi tafice daga cikin ɗakin, zaune ta taradda Inna a tsakar gida, sannu da gida kawai Zahrah tayi mata, haɗe da shigewa cikin bayan gida, tana fitowa a wanka ta bi lafiyar katifarta domin dama dai bata wani jin yunwa, ledan da Doctor yabata ta jawo haɗe da buɗewa, kyawawan dogin riguna ne suka bayyana acikin ledar saikuma dangin su snacks dasu choculate, kyakkyawar kwalin wayar da tagani acikin ledar taciro SAMSUNG GALAXY S10 shine sunan da ke rubuce ajikin kwalin wayar, wani irin faɗuwa gabanta yayi take nunfashinta yashiga gudu akai akai, bazata taɓa mantawa ba shima da haka yafara, daga ƙarshe kuma ya dasa mata babban tabo acikin zuciya da rayuwarta mai wahalan gogewa, saurin sake kwalin wayar tayi haɗe dayin watsi da kayan da suke zube a gabanta, talauci bahauka bane, bazata sake bari haka yafaru da'ita ba, hawaye ne suka shiga sauƙa akan ƙuncinta, haƙika soyayya bata mata adalci ba, kwanciya tayi lamo akan katifa tana nai sauƙe a jiyar zuciya, jin da tayi zuciyarta na shirin dawowa ɗanyea shakaf ne yasanyata tashi ta ɗauko littafi mai tsarki wato Al'Qur'ani tasoma karantawa domin rage damuwar dake damunta a zuciya....
"Salima kuma Hajiya?" Doctor Sadeeq yatambaya cikin muryar damuwa.
"Ƙwarai kuwa Sadeeq, ko ita Saleema'n tana da wani aibune? ƙwarai nayaba da hankalinta dakuma tarbiyanta, saboda haka nagama yanke shawarata, gobe zanfaɗamawa ƙanin mahaifinku yaje yatambayo maka aurenta, idan ma a so nane banso bikin yawuce nanda wata ɗaya " Hajiya tafaɗi maganar babu alamar wasa akan fuskarta.
Cike da sanyin jiki Doctor Sadeeq yace " Shikenan Hajiya, Allah yasa hakan shine mafi alkhairi, amma dakin ƙara haƙuri, nan bada jimawa ba zan kawo wacce nakeso"
"Hmmm ai aikin gama yariga daya gama Sadeeq, nagaji dajin wannan zancennaka, koda yaushe haka kake cewa, to yanzu dai nagaji da ƙaululan dakakemin saboda haka natsaida magana,zaka iya tafiya"
Gaba ɗaya hukuncin da Hajiyar tasa ta yanke masa baiyi masa daɗi ba, amatsayinsa na Namiji bai dace ace anyimasa dole akan aure ba, shi sam Saleema ma bata ɗaya daga cikin irin tsarin matan dayakeso, amma yazaiyi tunda dai Hajiya ta kafe, yasanta da wuyar sha'ani, idan tace eh zaiyi wuya kuma tace a'a, jiki a mace haka yafice daga falonnata, kaitsaye ɓangaren sa yanufa, yanashiga cikin falonnasa direct friedge yanufa, goran ruwa mai sanyi ya ɗauko, haɗe da zama akan kujera, saida yasha ruwan fiye da rabin gora, kafun yashiga sauƙe ajiyar zuciya, wayarsa yaciro acikin aljihun rigarsa, kai tsaye lambar sim ɗin dake cikin wayar daya bata, ya danna wa ƙira, saidai yaji saɓanin tunaninsa, domin kuwa cemasa akayi wayar a kashe take, nannauyar ajiyar zuciya ya sauƙe, haɗe da aje wayartasa a gefe, "Maiyasa nadamu da'ita sosai ne?" yatambayi kansa, bayan kuma yasan baida amsa,
"Inatausayinta sosai,amma kuma bayan tausayi inajin wani abu na daban a ga me da'ita, menene wannan abun ? yazama dole nasan menene amma tabbas ina da burin inganta rayuwarta " Ƙaran wayarsane ya katse sa daga zancen zucin da yakeyi, ganin da sabon number ake ƙiran nasa yasa bai ɗauki ƙiranba, saima tashi dayayi yawuce cikin bedroom ɗinsa...
Washe gari.
Yau tunda safe takammala shirinta, tayi kyau cikin shigar ta ta atamfa riga da sket, yayinda lufayant dake jikinta ya kasance hot pink colour, sama sama tasha ruwan shayin da Inna ta dafa, tana kammala shan ruwan shayin ta ɗauki jakarta haɗe da nufar hanyar waje. domin batamaso likita yazo yasameta, tafiso tayi tafiyarta, sam bataso yanashiga cikin rayuwarta, takuma yanke shawaran gaya masa yafita acikin rayuwarta, domin sam baikamata tasake bawa wani namiji dama ba.
Turus haka taja ta tsaya, domin kuwa tsaye tagansa ajikin motarsa, yasha ado cikin wata blue ɗin shadda, sam batai tsammanin ganinsa a daidai wannan lokacinba.
Murmushi yayi mata haɗe da soma takowa harzuwa inda take tsaye.
"Baki tsammaci ganina a dai dai wannan lokacin ba ko?" yatambayeta kansa tsaye yana mai kafeta da idanu.
Ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba haɗe da cewa "Ina kwana"
"Lafiya ƙalau, yakika tashi?"
"Lafiya" tabasa amsa a taƙaice, haɗe da sunne kanta ƙasa, domin hakanan taji yamata wani irin kwarjini.
"Muje kada kiyi latti ko" Doctor yafaɗa yana mai yi mata nuni akan cewa tashige gaba.
Bazata iya musa masa ba, domin kuwa yayi mata kwarjini sosai, don haka cikin sanyin jiki tanufi wajen motar tasa, shikuma yarufa mata baya, gaba ɗaya jitayi jikinta yayi sanyi, alƙawarin da ta ɗaukawa kanta nacewa zata faɗa masa yafita a rayuwarta gaba ɗaya ya ruguje, domin kuwa tanaganinsa taji bakinta yamutu murus, tana shiga cikin motar ta lumshe idanu, domin kuwa wani irin daddaɗan ƙamshi cikin motar keyi, cike da nutsuwa yake tuƙin nasa, yayinda jefi jefi yake satan kallon Zahrah, wanda gaba ɗaya hankalinta yana ga ababen hawan da suketa hada hada akan titin.
"Maiyasa ki kaƙi kunna wayar dana baki?"
Sunkuyar da kanta ƙasa tayi haɗe da soma wasa da yatsun hanunta, "Babu" tafaɗi hakan cikin sanyi murya.
"Ko kuma dai bakyason kyauta daga gareni ba "
Saurin kallonsa tayi, jin abun da yace, ai kuwa karab idanunsu suka haɗe a waje ɗaya, saurin sadda kanta ƙasa tayi, domin batason haɗa idanu dashi kokaɗan, "Bahaka bane, kawai dai banson rayuwata tasake cutuwa ne" tafaɗi hakan da iya gaskiyarta.
Kansa ya jinjina haɗe da cizon lips ɗinsa, "Eh ta wani wajenma kina da gaskia, amma ai bada wata manufa na baki ba, amma idan kinaga zaki takura to shikenan saikiyi abun da yadace" shima yayi maganar da iya gaskiarsa.
Daga haka dukansu basu sake ce da junansu komaiba, har suka iso cikin makarantar, yauma har gaban lecture hall ɗin su ya kaita, sai da kuma yaga shiganta cikin hall ɗin kafun yayi tafiyarsa.
Koda aka tashi yauma shiya zo da kansa ya ɗauketa, sai dai tunda suka kama hanya harsuka isa gida babu wanda yace da ɗan uwansa wani abu.
A daidai ƙofar gidan su ya tsaida motar, haɗe da juyo da kallonsa gareta ƙoƙarin fita tasomayi daga cikin motar, cikin wata irin murya mai sanyi yace "Inason magana dake"
Kallo ɗaya tayi masa ta kau da kanta gefe, "Wace irin maganace ?"
"Maganace mai matuƙar mahimmanci , amma kuma tana buƙatar ishashshen lokaci " Doctor yaƙare maganar yana mai duban agogon dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa.
"Inajinka" Zahrah tafaɗa a taƙaice,
"Bakina jina zaki ce ba, hankali da tunaninki nakeso kibani "
Gyara zamanta tayi haɗe da ɗan satar kallonsa, batare da tace komaiba.
Kwantaccen sajen dake kan kumatunsa ya shafa, haɗe da cewa " No kada kiyi zaton wani abu zance, dama alluranki ne banƙara sa miki ba, kuma akwai matsala idan banyimiki su ayau ba!"
Gaba ɗaya idanunta ta ƙwalalo su waje, yayinda tsoro yacika zuciyarta, "Dan Allah kayi haƙuri wallahi na warke, yanzu banajin komai ajikina!" taƙare maganar lokacin da muryarta ke rawa, alamun zatayi kuka.
"A'a ni gaskia banyarda da cewa kin warke ba, saboda naga kina yawan sanya kanki a damuwa kuma jiya ma dana riƙe hanunki naji zazzaɓi a jikinki, don haka kawai zan ƙarasa miki yanzu" yaƙare maganar yana mai shirin buɗe wani ɗan ƙaramin drower dake cikin motar, take allurai suka bayyana, ai a ɗari Zahrah ta buɗe murfin motar haɗe da rugawa zuwa cikin gida, ko tsayawa ɗaukar jakarta batayi ba.
Dariya sosai Doctor Sadeeq yasanya, hadda riƙe ciki, shi dama burinsa yaga yanayin tsoronta, domin idan tana cikin wannan yanayin tsoron sosai take burgesa, ɗaukar jakar nata yayi haɗe da fita acikin motar kai tsaye yanufi cikin gidan. Yana sallama Inna ta tarbesa da fari'a, haɗe da cewa "Ai dama nasan tare kuke domin daganin yanda tashigo a guje nasan cewa ba ita kaɗai bace" ɗan guntun murmushi yayi haɗe da cewa " waifa dan nace zanmata allurane, shine duk tabi ta ruɗe, kuma yau bazan bar gidannan ba harsai na mata alluran nan, ko yakikace Inna?"
Idanu Zahrah tasake gwalowa jin abun da yake cewa, gaskia ita daya mata allura gwamma yabata magani amma sam batason allura, kuma ita taji sauƙi, amma su sundage akan cewa wai bataji sauƙi ba, kafun ta gama zancen zucin da takeyi taji muryarsa a bakin ƙofar ɗakin yanacewa Inna ta ɗauko masa ita....
(Kuyi haƙuri jiya kunjini shiru, muna biki ne, yauma a daddafe nayi muku typing bacci nakeji)
*30/November/2019*
*Voted, Comment & Share please....Follow me on wattpad @fatymasardauna

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Lovely Brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed;our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*(Ina mai baku haƙurin rashin jina kwana biyu da kukayi, insha Allah hakan bazai sake faruwa ba)*
*Chapter 44 to 45*
Sake matse jikinta tayi ajikin bango, haɗe da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba.
"ZAHRAH!" taji muryarsa yana ƙiran sunanta, cikin tsoro da ɗar ɗar, ta buɗe ƙofar ɗakin nata, kallo ɗaya yayi mawa cikin idanunta yakau da kansa gefe, domin kuwa wani irin zubawa yaji tsikar jikinsa tayi, gaskia Zahrah tana da abubuwan ɗaukar hankalin ɗa namiji da yawa a tattare da'ita.
Batare da yakuma kallonta ba, ya miƙomata jaƙarta dake riƙe a hanunsa, da sauri ta fusge jakar haɗe da komawa cikin ɗakin ta,ta kuma datse ƙofar, murmushi kawai Doctor Sadeeq yayi haɗe da girgiza kansa, kallonsa yakomar ga Inna, cikin girmamawa yayi mata sallama, bayan ya cika mata hanunta da alkhairi, cike da farinciki Inna tayi sallama dashi, don tsabar daɗi ma har kusan ƙofa ta rakasa, tana mai zabga masa godiya.
Tafiya yake amma shi kaɗai yake murmushi, sosai Zahrah take burgesa, yanason komai na yarinyar, fushinta, dariyanta, tafiyarta, nutsuwarta, dama duk wani abu nata, tabbas Zahrah tana ɗaya daga cikin irin matar da yake fatan mallaka a matsayin matarsa ta sunna, ko dai zai jarrabane ?" ya tambayi kansa, saurin dukan seterin motar tasa yayi haɗe da cije laɓɓansa, "Ka dawo cikin hankalinka Sadeeq, maikake shirin aikatawa ne haka?" yatambayi kansa a fili.
"No baikamata nayi haka ba, dole zanyi haƙuri !" yafaɗi hakan cikin karyewar zuciya, dai dai lokacin kuma ya iso gaban makeken gate ɗin gidansu, mai gadi yana gama wangale masa gate ɗin ya cusa motar tasa zuwa cikin gidan.
Saida tagama ƙaremawa wayar kallo kafun ta danna madannin da zai sanya wayar ta kawo haske, nannauyar ajiyar zuciya ta sauƙe, haɗe da jingina bayanta da jikin bango, "Yazama dole kikawo sauyi acikin rayuwarki Zahrah, kada ki bari abunda Zaid yayi miki, yazama sanadiyar lalacewar duk wani farinciki dake cikin rayuwarki" zuciyarta ta faɗa mata hakan cike da ƙarfafa mata guiwa, "Amma tayaya hakan zai kasance, bayan banda wani ginshiƙi dazai taimakamin ?" Zahrah tatambayi kanta, sake gyara zamanta tayi haɗe da ɗaukar wayarta, kai tsaye tashiga wajen dazai sadata da apps ɗin wayar, Word Charm shine game ɗin daya ɗauki hankalinta, duk cikin apps ɗin dake wayar, dama tanason game ɗin, don haka kaitsaye tashiga tasomayi, take taji kewa da kaɗaicin da take ji sun soma ragewa, a wannan rana dai Zahrah batayi wani dogon tunani da takura kanta ba, dazaran taji ta takura zata ɗauki wayarta tasoma buga game, idan ta gaji da buga game ɗin kuwa, sai ta shiga Instagram shima sosai yake rage mata kewa (nima haka, lol)..
Tayi kyau sosai cikin blue rover gown ɗin dake jikinta, wata baƙar lufaya ta sanya a jikinta wanda yataimaka wajen ƙarawa shigar tata kyau da armashi, batayi wani kwalliya akan fuskarta ba, ta dai shafa man leɓe dakuma kwalli, amma duk da haka tayi kyau, dama mai kyau ko baiyi kwalliya ba kyawunsa baya ɓuya.
Kasancewar yau baza su jima a makaranta ba, yasanya bata ɗauki jakaba, sai wasu ƴan littatafai da ta ɗauka a hanunta, sai kuma wayarta, koda ta fito tsakar gidan zaune a bakin murhu ta iske Inna tana tuyan ƙosai, wanda Baffa yace ayi na karyawa.
"Inna ni zanwuce makaranta" Zahrah ta faɗa tana mai ƙoƙarin gyara zaman lufayan dake jikinta.
"Bazaki tsaya ki karyaba Zahrah"
Baffa dake fitowa daga cikin ɗakinsa ya faɗa.
Ɗan guntun murmushi Zahrah tayi haɗe da shafa cikinta "Banajin yunwa sosai Baffa, kuma ina tsoro kada na makara!"
"Eh kina da gaskiya, kinga kuwa tun ɗazu likita, yazo yana jiranki, bayanda banyi da shi ba akan yashigo, amma sam yaƙiya, don haka gwamma ki hanzarta, a dawo lafiya " Baffa yaƙare maganar yana mai yunƙurin komawa cikin ɗakinsa.
"Ameen Baffa nagode!" Zahrah tafaɗa cike da farinciki, domin kuwa karo na farko kenan a rayuwarta da taga tsananin kulawan Baffa a kanta.
Tana fitowa yasakar mata kyakkyawan murmushinsa, ga mamakinsa sai yaga itama ta sakar masa murmushi, wanda yayi matuƙar taɓa masa zuciya, domin kuwa bakaɗan ba tayi kyau, da tana murmushin.
"Saiyanzu ki ka ga daman fitowa? kinshanyani kamar kin aje dutse" Doctor yafaɗi maganar yana mai turo baki gaba, tamkar ƙaramin yaro.
Dariya sosai Zahrah ta shiga yi, domin yanayin yanda yayi maganar yazama dole wanda ya gani ya dara, hangame baki Dr yayi yana kallon yanda take dariyan, abun da bai taɓa gani ba kenan, tun haɗuwar su da'ita, bai taɓa ganinta tana dariya ba sai yau, ashe ma duk kyawunta da yake gani, bai ga komai ba, domin da tana dariyan tafi masa kyau.
Hanunta tasanya ta toshe bakinta, haɗe da tsagaita dariyan da takeyi, kallonsa tayi haɗe da cewa "Bakaga yanda kazama yaro ba dakana maganan nan, tamkar ɗan shekara takwas!"
Murmushi yayi haɗe da jefamata hararan wasa, cikin yanayin da yayi magana ɗazu yakuma cewa "Shine kikemin dariya ko? sai na faɗaki da mamana!" ai kamar yaƙara mata fower'n da riyan nata ne, nan take taci gaba da dariyanta, hadda ɗan guntun ƙwalla a idanunta, wani irin sanyi da nishaɗi yaji yana huda zuciyarsa, tabbas bashida wani buri da yawuce yaga Zahrah tana cikin farinciki Alhmdlh, yau gashi ta sanadiyarsa tana dariya dakuma nishaɗi,
"Kayi haƙuri, bazan sake shanyaka ba, amma gaskia ka iya shagwaɓa da yawa!" Zahrah tafaɗa dai dai lokacin da tayi mawa kanta mazauni acikin motar, haryanzu dariyane kwance akan fuskarta.
"Wato dai yau mugunta kike ji dashi, dariya hadda hawaye!" Doctor yafaɗa cikin nishaɗi.
"Bahaka bane, kai ɗinne dai kawai kabani dariya!" itama ta basa amsa cikin nishaɗi.
"Dagaske kike, saboda ni kike wannan nishaɗin? " Dr ya tambayeta cike da zaƙuwa, duk da kuwa cewa yasan sabo da shiɗinne take nishaɗin.
"Eh mana, saboda kaine, kasan kaban dariya sosai, kuma nasan bama ni kaɗaiba, duk wacce takalleka a irin wannan yanayin dole zatayi dariya"
Ajiyar zuciya Dr ya sauƙe haɗe da murza key ɗin motar, suka ɗau hanyar da zata sadasu da titi.
"Idan kina dariya kinfi ko yaushe kyau ƴan mata na!" Dr yafaɗa cikin muryar nutsuwa.
Saurin maida kallonta garesa tayi, jin abun da yafaɗa tayi kamar wani almara, sai kuma taga yanayinsa tamkar bashine yayi maganar ba.
Yi tayi itama kamar bataji mai yace ba, mai da kallonta tayi ga titi, tana mai kallon yanda ababen hawa suke gudanar da hada hadansu.
"Maiyasa ki ka ƙi cin abinci? ko kinfiso ki zauna da yunwa ne?" Doctor ya jefo mata tambayar da batayi zato ba.
Kallo ɗaya ta yi masa ta kau da kanta gefe, "Banjin yunwa ne, sannan kuma banaso na yi latti"
tafaɗi maganar a taƙaice.
Baice da'ita komaiba, saima buɗe ɗan ƙaramin drowern dake jikin motar yayi, wani haɗaɗɗen cake dake cikin wani ɗan ƙaramin kwali ya ciro, haɗe da ɗaura mata akan cinyarta, " Kici, kuma banson musu" yanayin yanda yayi maganar zai tabbatar ma da cewa, ba wasa yake ba.
"Nagode, amma zanci idan muka fito a lecture" itama ta faɗa kai tsaye.
"Yanzu nakeso kici, umarnine bawai shawara ba" yakuma faɗi maganar cikin yanayi mai nuni da cewa da gaske yake maganar.
Batason yi masa musu, domin koba komai yayi mata halacci a cikin rayuwarta, a hankali take gutsuran cake ɗin tana kaiwa bakinta, duk da cewa cake ɗin yayi mata daɗi.
Duk abun da takeyi yana lure da'ita, yanayin yanda take tauna abincin shiyafi komai burgesa.
Saida taci cake ɗin fiye da rabi, kafun ta dawo da kallonta garesa, "Naƙoshi" tafaɗa tana mai yatsine fuska.
"Dole sai kin cinye, domin kuwa ni idan nabawa mutum abuna, bai isa yacemin ya ƙoshi ba, dole sai yacinye koda kuwa ya ƙoshin"
Ɗan guntun murmushi tayi haɗe da cewa "Dagaske nake naƙoshi, amma da alama dole kakeson min"
"Dolen dole ma kuwa" yafaɗa dai dai lokacin da yagama parking motar tasa, domin kuwa harsun kawo cikin makarantar tasu, hanu ta ɗaura akan murfin motar da niyar buɗewa ta fita, tuni ya dannawa ƙofofin luck, saurin kallonsa tayi domin bata fahimci hakan da yayi me yake nufi ba.
"Babu inda zakije, matuƙar baki cinye cake ɗin nan ba" yafaɗi hakan yana me jingina bayansa a jikin kujeran da yake kai.
Ƙwaɓe fuska Zahrah tayi cikin sigar lallashi, tace "Kayi haƙuri, naƙoshi, idan naci da yawa, bazan iya karatu yanda ya kamata ba!"
"Um,Um, naƙi wayon, saura kaɗanne fa please kicinye shi mana Zahrah!" Doctor Sadeeq yaƙare maganar cikin lallashi.
"Um, Um, na ƙoshi, gaskiya idan naci zai cutar dani, zanyi ƙatuwa da yawa, ni kuma banaso nayi ƙatuwa!" cikin zallan shagwaɓa Zahrah tayi maganan.
Dariya sosai Dr Sadeeq ya sanya, domin kuwa maganar Zahrah ta bashi dariya, wai ita bataso tayi ƙatuwa hmm.
"To ai yaune kawai, kuma kinga bazakiyi ƙatuwa ba, nima banso kiyi ƙatuwa da yawa, amma inaso kiyi ƙatuwa kaɗan!" yanayin yanda yayi maganar kaɗai ya isa sanyawa mutum mutuwar jiki.
Batace dashi komaiba, domin bata fahimci inda maganar tasa ta dosa ba, ɗaukan ragowan cake ɗin tayi, tashiga turawa acikin bakinta, tamkar wacce aka bawa guba.
Dariya Doctor Sadeeq yashiga yi mata ƙasa ƙasa, domin kuwa yanda takecin cake ɗin, dagani kasan dole a kayi mata bawai a son ranta bane. tana cinyewa ya miƙomata goran ruwa, ai kuwa ba musu ta karɓa ta shiga sha, domin dama duk cake ɗin ya shaƙeta.
Cikin yanayi na shagwaɓa da ɓata fuska tace " Na cinye yanzu zan iya tafiya!"
Dariya Dr yayi haɗe da cire luck ɗin da yasanyawa ƙofofin motar "Zaki iya tafiya, amma kikula da kanki sosai, sannan idan kun fito a lecture wani zai kawo miki saƙo daga nine ki amsa"
"Wani saƙo?" Zahrah ta tambaya cike da ɗaurewar kai.
"Zakiyi latti,kiyi sauri kije" Dr yafaɗi hakan don kawar da tambayar da tayi masa.
Bata sake cewa komai ba tabuɗe murfin motar tafice, yauma dai sai da yaga shiganta cikin hall ɗin kafun yatada motarsa yabar cikin makarantar, direct shima asibiti ya nufa, domin yau yanada aiki sosai.
Sosai yau ta gane Lecture ɗin da akayi musu, saɓanin sauran ranakun da suka wuce wanda ba komai take fahimta daga cikin abun da ake koyar musu ba.
Fitowarsu kenan daga lecture, tafe suke su biyu, yayinda Husnah keta mita, wai jimawan da sukayi suna lecture, yasanya tanemi gaba ɗaya abincin cikinta ta rasa.
Dariya Zahrah tayi haɗe da cewa "Nikuwa kinga ɗigo na yunwa banaji, domin kuwa yau ɗure, a kamin dan dole na"
"ɗure kuma bestie? Amma badai Inna da Baffa bane sukaimiki ɗuren bako?"
"Doctor Sadeeq ne!" Zahrah tafaɗa a taƙaice.
"Doctor Sadeeq kuma? lallai kuwa Doctor yayi babban ƙoƙari, shiyasa na ganki yau kina cikin farinciki" Husnah tafaɗa tana mai ƙoƙarin gimtse dariyar da take ƙoƙarin taso ma ta, domin ita kam ta hango wani babban al'amari dangane da Doctor dakuma Zahrah.
"Maikike nufi?" Zahrah ta tambayi Husnah cikin tsare gida.
Husnah batakai ga bata amsa ba, wani mutumi ya ƙaraso garesu, hanunsa ɗauke da wata leda, sallama yayi musu suka amsa masa.
Kaitsaye ya miƙomawa Zahrah ledar dake hanunsa, haɗe da cewa "Gashi inji oga"
Take maganar da Dr yafaɗa mata ɗazu a cikin mota, cewar wani zai kawo mata saƙo, ya faɗo mata, cikin sanyin jiki ta amshi ledan, haɗe da ce masa ta gode.
"Saurin karɓe ledan Husnah tayi daga hanun Zahrah, haɗe da cewa "Allah yasa abun daɗi ne, domin yawuna haryafara tsinkewa, kinsanni ba baya bace wajen kwaɗayi"
"Wow special gift!!" Husnah tafaɗa sanda idanunta suka gane mata abun da ke cikin ledar,
"Amma ba haka naso ba, ƙawata naso ace wani abun ci ne kinga da sai na morewa bakina!" Husnah ta ƙare maganar tana mai ɓata fuska.
Dariya Zahrah tayi haɗe da sanya hannayenta ta dafa kafaɗun Husnah, cike da nishaɗi tace " Allah ƙawata, ki rage kwaɗayi, yanzu idan abun ci ne, yazuba mana wani abu a ciki, mukazo mukaci, ya cutar da mu,kuma fa? kinga kwaɗayi ya jawo mana kenan,kuma bai mana rana ba"
"Dan Allah malama sakeni, nayarda da Dr nasan babu abun da zai ɓamu wanda zai cutar da mu, kedai kawai mugunta ne irin naki, bayan kinsan inajin yunwa, muje cafeteria muci abinci please!" Husnah tafaɗa tana mai daɗa kwaɓe fuska.
"Yi haƙuri ƙawata bani nakar zomonba, muje sai kici abincin ko" Zahrah tafaɗa cike da kulawa.
"Ungo kayan shafanki, domin kuwa cigaba da riƙesu ma, ƙaramin yunwa zaiyi" Husnah ta ƙare maganar tana mai miƙomawa Zahrah ledar dake hanunta.
Dariya kawai Zahrah tayi haɗe da amsar kayan, sarai tasan Husnah bata da haƙurin yunwa ko kaɗan.
Ice cream kawai Zahrah tasha, yayinda Husnah kuwa ta cika cikinta da shinkafa. Yau darasi biyu garesu kacal, don haka suna fitowa kowa ya yi ƙoƙarin kama gabansa.
Waige waige tashiga yi ko zata hangosa, amma babu alamar komai irin motarsa, wayarta ce ta soma ƙara alamar shigowar ƙira, Number ne ke yawo a kan screen ɗin wayar babu suna, dama kuma batayi tunanin Numbern zai fito da suna ba, domin batayi saving numbern kowa ba, wama ta sani da zatayi saving number'nsa.
Har saida wayar ta kusa katsayewa kafun Zahrah ta ɗaga ƙiran, "Zahrah! na gaji, da yawa, aiki yamin yawa, please ga nan driver na, zaizo ya ɗaukeki ya kaiki gida, kiyi haƙuri kinji ƙanwata!!" Dr Sadeeq ya faɗi haka cikin kwantar da murya, da gajin yanda muryansa take fita slow kasan cewa a matuƙar gajiye yake.
A jiyar zuciya Zahrah ta sauƙe haɗe da cewa "Shikenan kahuta lafiya"
"Yauwa Ƴan mata na, ki kulamin da kanki" ƙit ya kashe wayar, ba tare da ya tsaya ya saurari mai zata ce ba.
Murmushi kawai Zahrah tayi haɗe da girgiza kanta, "Hmm wai itace ƴan mata, itakam yanzu ai ta wuce a ƙirata ƴan mata saidai sauran Zaid" tafaɗi hakan a zuciyarta, take kuma taji idanunta sun kawo ruwa. Dai dai lokacin motar Dr Sadeeq ta ƙaraso inda take tsaye, kasan cewar yayi mata bayanin cewa driver'n sane zaizo ɗaukarta, dan haka batayi wani jinkiri ba, ta buɗe murfin motar tashiga, ko kallon inda driver'n yake batayi ba, "ZAHRAH!" muryan Dr Sadeeq ya daki dodon kunnuwanta, saurin maida kallonta inda taji muryan tayi, ai kuwa shiɗinne kwance a jikin kujeran gidan baya, idanunsa ɗaya ya kashe mata haɗe da ɗage giransa ɗaya sama, "Surprise!" yafaɗa fuskarsa ɗauke da murmushi.
Murmushi itama tayi masa, haɗe dayin ƙasa da kanta, domin yanayin yanda yayi mata maganan, yasanya taji jikinta yayi sanyi.
"Dawo nan muzauna, ki bar driver yayi aikinshi"
Ɓata fuska Zahrah tayi haɗe da turo baki gaba, cike da shagwaɓa tace "Ni dai kabarni na zauna anan ɗin ma yayi!"
"Nace ki dawo nan muzauna ko!" yafaɗi hakan babu alamar wasa akan fuskarsa.
Cike da sakalci Zahrah ta dawo gidan baya inda yake zaune, ko kallonsa batayi ba saima langwaɓewa da tayi a jikin kujera. Har sukayi nisa a tafiyan babu wanda yace da ɗan uwansa ƙala, cikin shagwaɓa tace "Bakace min aiki yamaka yawa ba, amma mai yasa kazo?"
"Saboda ya cancanta nazo, ina da burin baki kyakkyawan kulawa a ko da yaushe, ko bakiyi farinciki da hakan ba?"
"Nayi farinciki sosai!" Zahrah tafaɗa kai tsaye, domin kuwa sam batason irin kallon da yake yawan yi mata a wasu lokutan.
Baisake ce da ita komai ba, shima sai ma komawa da yayi ya jingina bayansa da jikin kujeran motar.
A haka har suka iso ƙofar gidan su Zahrah'n, kallo ɗaya tayi masa haɗe da buɗe murfin motar tayi ficewarta, yana ganin shigewarta gida, yace driver ya ta da motar suje.
Bayan Sati Biyu....
Wani irin shaƙuwa ne mai ƙarfi yashiga tsakanin Doctor Sadeeq da Zahrah, kullum shi ke kaita mkaranta shi kuma ke ɗauko ta, sosai yake bata kulawa, baya son duk wani abu da zai ɓata ranta, ko ya sanya taji ba daɗi, ɓangaren Zahrah ma, sosai take kiyayewa dashi, tana iya ƙoƙari wajen ganin bata musa masa idan ya umarceta da tayi abu, ko kaɗan batajin wani abu a dangane dashi, tana dai yi masa biyayya tana kuma ganin girmansa, domin kamar yanda yace ta ɗaukesa, a matsayin ɗan uwa, to a matsayin ɗan uwan ta ɗaukesa, domin kallon yaya take masa, sannan kuma sosai wayarta take ɗe be mata kewa, yakanyi ƙoƙari wajen ganin ya ƙirata a waya, a kowani dare, sai dai hiran tasu bata tsayi suke sallama da juna, sosai rayuwarta tasamu canji, bakamar da ba, duk da cewa abune mawuyaci manta abun da ya faru da'ita, amma takanyi ƙoƙari ƙwarai wajen ganin ta gusar da duk wani damuwarta.
Tsaye yake a gaban tangamemen dressing mirror ɗin dake kafe a jikin bangon ɗakin nasa, yayi kyau sosai cikin riga da wandon shadda dake jikinsa, ba abun da jikinsa keyi banda tashin ƙamshi, hannayensa duka yazura a cikin aljihun wandon shaddan dake jikinsa, tabbas a kwai wani al'amari mai girma dake cikin zuciyarsa, haƙiƙa kuma akwai abun da yakeso ya furta,amma tayaya, baisan da wani manufa zata ɗauki zancen ba, baisan wani amsa zaiji daga bakinta ba, wannan shiya hanasa furta mata tsadaddan kalman dayake ta ɓoyewa tsawon lokuta, bayajin zai samu abun da yakeso daga gareta, bakuma yajin zai samu amincewarta, ya tabbatarwa kansa cewa, a yanzu lallashi take buƙata fiye da komai, sannan kuma bata buƙatar wata magana wanda zata zamo sanadiyar rugujewar ɗan farincikin da ta soma samu, sai zuciyar sa ta ƙarfafa masa guiwa, saikuma gangar jikinsa tayi sanyi laƙwas.
"Ba'asan jarumin Namiji da tsoro ba!" wata zuciyarsa ta furta masa hakan.
Ƙwarai ya yarda da cewa shi ɗin jarumi ne, amma kuma gurin da yake da muradin isar da saƙonnasa wajene mai rauni, dole zai fuskanci ƙalubale guda biyu, rashin nasara, ko kuma, yin nasara, wayarsa ya ɗauka ya sanya a cikin aljihunsa, kai tsaye ya fice daga cikin ɗakin nasa, yana shiga cikin motarsa ya bata wuta, kai tsaye unguwar su Zahrah ya nufa, sosai ya yarda da shawaran da zuciyarsa ta basa, lallai yazama dole ya bayyana mata sirrin dake kwance cikin zuciyarsa, sai dai yasan balallai ta aminta da ƙuɗirinsa ba, amma zai jarraba ya gani.
A ƙofar gidansu yayi parking motarsa, haɗe da ciro wayarsa, ya danna wa Number'n Zahrah ƙira, sai dai harzuwa lokacin zuciyarsa fat fat haka take bugawa. tana ɗaga wayar yace "Ina ƙofar gidanku, dan Allah kizo ki sameni" banji mai tace masa ba, sai gani nayi ya mai da wayar tasa cikin aljihunsa, haɗe da sauke nannauyar ajiyar zuciya....
(Tofa readers, mai kuke ganin Doctor Sadeeq zai faɗawa Zahrah, da haryakejin tsoron faɗa mata, sbd baisan daya zata ɗauki maganar ba, to zadai muji kome nene a next page insha Allah! Ko ina Baba Zaidu kuma 🤷♀)
*3/December/2019*
*Voted,Comment, and Share please..... Follow me on Whatsapp and Wattpad @fatymasardauna

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother Khabier*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
(😂Yasin bansan haka Baba Zaidu yake da masoya ba sai kwana biyu da bana taɓo sa, ashe dai masoyan Zaid sunfi maƙiyansa yawa, kusha kurumin ku mutanen Zaidu yau zan taɓo muku chapter'n shi, su Munubia nasan anyi missing 🤣)
*Chapter 46 to 47*
Tana aje wayan ta ɗauko wani rover hijab ɗinta ta sanya a jikinta, koda tafito daga cikin ɗakin nata, zaune ta iske Baffa da Inna, a tsakar gida, domin dai dama dare yasoma rufawa, cike da ladabi tace " Baffa Doctor Sadeeq yana ƙirana a waje"
Gyara zama Baffa yayi haɗe da cewa " to naji ƙaran tsayuwar mota ai, ashe dai likitane yazo, to adawo lafiya"
Muguwar harara Inna ta jefamawa Zahrah, cike da masifa tace "Wato ni banza bankai matsayin da zaki tambayeni ba ko? wato Baffanki kaɗai kika gani a wajen?"
Cikin sanyin murya Zahrah tace "Kiyi haƙuri Inna, naga shi ya kamata na sanarmawa hakanne, tunda ya na nan!"
"Wuce kije ƙiran da yake miki kinji Zahrah'u, barta Salame yau masifa take ji dashi" Baffa yaƙare maganar yana mai wurgamawa Inna harara.
Bata kuma sauraran abun da Inna zatace ba tasakai tayi ficewarta daga cikin gidan..
Duk da cewa babu wadataccen haske a wajen, amma tana iya hango kyawun da kayan jikinsa sukai masa, "gaskiya Dr kyakkyawane shima" tafaɗi hakan a cikin zuciyarta.
Da sallama ɗauke a bakinta ta ƙaraso inda yake tsaye, cike da fari'a Dr ya amsa mata sallaman da tayi haɗe da cewa "Wato sai anjamin aji kafun a fito ko?"
Ɗan guntun murmushi Zahrah tayi haɗe da cewa "Bawani batun jan aji, ni a hakan ma inaganin na fito da wuri"
Shima murmushin yayi haɗe da cewa "Kinyi kyau!"
Still murmushi tayi, cikin son kawar da zancen da yayi na cewa tayi kyau, tace "Lafiya kuwa naganka a dai-dai wannan lokacin?"
Gyara tsayuwarsa yayi haɗe da maida nutsuwarsa gareta "Maganar danazo miki da'ita Zahrah bata tsaye bace, yana da kyau mushiga mota, sai mu tattauna ko?"
Ɗan jim Zahrah tayi, haɗe da cije lips ɗinta, "Shikenan amma inafatan bazamu jimaba, kafasan banson fitowa waje da dare"
"Insha Allah, bazamu ɗau tsawon lokaci muna magana ba!" Dr yafaɗi hakan lokacin da yayimawa kansa masauƙi a cikin motar tasa, bayan ya kunna ƙoyin wutar dake cikin motar take haske ya gauraye cikin motar.
Gyara zama Zahrah tayi, haɗe da tattaro duka nutsuwarta "Inajinka" tafaɗa a taƙaice.
Wani irin numfashi Dr yayi, haɗe da fitar da iska daga bakinsa, sai yanzu yakejin cewa, bazai iya furta abun da yakawosa ba, gaskiya yanajin nauyi, baisan tayaya Zahrah zata karɓi muradinsa ba, kada maganar da zaifaɗa ma ta yazamo sanadiyar rugujewar nishaɗin da yake gani akan fuskarta yanzu, "Ta'ina zanfara?" ya tambayi kansa a cikin zuciyarsa.
"Lafiya kuwa, naga kayi shiru?"
Zahrah ta tambaya, cike da mamakin yanda yayi shiru, bayan yace akwai maganar da zasuyi.
Nannauyar ajiyar zuciya ya sauƙe, haɗi da maida kallonsa gareta, saida ya tattaro nutsuwarsa kafun yace...
"Yazakiji idan wani yazo miki da batun soyayya a wannan lokacin Zahrah?" abun da ya iya fitowa daga bakinsa kenan, domin a gaskia shikam yarasa ta'ina zai fara.
"So kuma? wani irin so?" Zahrah ta tambaye shi cike da mamakin kalaman nasa.
"So na Aure Zahrah!" yafaɗi maganar cikin ɗar ɗar.
"Au..r..e.. Kuma Likita? Aure fa kace, dama akwai wani wanda, zaiji kwaɗayi da sha'awar aure na ne? hmmm a gaskia bana tunanin haka, domin kuwa babu wani wanda zai so ni da rayuwata, a yanda nake ɗinnan!" Zahrah tafaɗi hakan da'iya ka gaskiyar ta.
"Kada kice haka Zahrah, akwai mata masu rauni da yawa irin ki, amma an auresu, kuma anzauna dasu, ke me yasa zaki yanke ƙauna da...."
"Dan Allah kadaina min wannan zancen Doctor, banjin zan sake son wani ɗa namiji a duniyar nan"
Zahrah ta katse shi da ga maganar da yakeyi, ci gaba tayi da cewa
"taya kake tunanin zansake kai kaina tarkon da ya ruguzamin rayuwa, shi So ɗin dakake faɗa yanzu, shine ya ruguzamin rayuwa ta, ya rabani da duk wani farinciki na rayuwata, shin idan kace min na sakeyin So, kamin adalci kenan? " Tuni hawaye sun gama wanke mata fuska.
"Kada kice haka Zahrah, kefa musulmace, kuma ke mace ce, nasan kina da sanin cewa, kyautatuwar rayuwar ƴa mace shine aure, haka kuma rayuwar ƴa mace bata cika hundred percent sai da aure, haka kikeso ki ƙare rayuwarki ba aure? ko kin manta cewa cikar mutumcin mace shine a ganta gidan mijinta? yin Aure shine burin kowacce mace ta ƙwarai, nasan kema wannan shine burinki, kada shaiɗan yayi amfani da abun da yafaru dake, ya ruguza miki rayuwa, ya hanaki aikata sunna!"
"Hakan shine burina amma ada, wa zai aureni a yanzu? waye zai ɗaukawa kansa duhu? waye zai ɗauki sauran da wani yaci ya rage, sauran da wani ya tarwatsa, ya zuba ƙazantarsa, acikin cikinta, waye zaiyi hakan? bazan yaudari kaina ba, nasan babu wani wanda zai aureni a yanda nake, bantaɓa aure ba, amma kuma niba budurwa bace a yanzun, ya cuceni yariga ya karɓe abun da nake burin bawa mijina na sunna, waye zai yarda da haka?"
"Nine nan Zahrah, Nasan komai a kan ki, kuma zanyarda da duk wata ƙaddaranki, nine wanda zan sharemiki hawayenki, kece damuwata bawai budurcin kiba, kiyarda dani dan Allah!!" Doctor Sadeeq yafaɗi hakan cikin jajircewa..
Kamar sauƙan aradu haka Zahrah taji sauƙan kalamansa a cikin kunnuwanta, cak ta tsaida kukan da takeyi haɗe da, da hangame baki tana kallonsa, gani take kamar ma baya cikin hayyacinsa, ƙaryane tayaya za'ace Namiji mai aji, kamar Doctor yace wai ya amince da ƙaddaranta zai aureta, wannan ba gaskia bane,
"Kada kiyi shakka ko kokonto, ba yaudara'nki nake ba, dagaske nake har cikin zuciyata, don Allah ki bani dama Zahrah, burina da fatana kawai ki amince min!"
Kai Zahrah ta shiga girgizawa, cikin tsananin ɓacin rai da danasin sauraransa da tayi tasoma cewa " Nayi Babban kuskure, haka kuma na tabka nadaman baka daman shigowa rayuwata da nayi, ashe dukanku haka halinku yake, macutane ku azzalumai, ashe bazaku taɓa sanjawa ba, dama ɗaya kawai idan aka baku, sai ku nemi shigo da manufarku, kaicona da abun da Zaid yayi mini baikasance IZNAH ga rayuwata ba, kaicona dana sake aminta da kai, kaicon zuciyata, kafita a rayuwata dan Allah, kaje banaso nasake ganinka ko kuma jinka, katafi kayi nisa da ni, kabarni na rayu cikin salama dan Allah!!" gaba ɗaya hawayen ɓacin rai yagama wanke mata fuska, ƙoƙarin fita daga motar ta somayi, cike da tashin hankali Doctor Sadeeq ya riƙo hanunta, ko kaɗan baiyi zato ko tsammani ba, saijin sauƙar mari yayi akan kumatunsa, Zahrah ce ta ɗaukesa da lafiyayyen mari, babu abun da ke kwance akan fuskarta banda tsananin ɓacin rai,
"Koda wasa kada kasake ƙoƙarin taɓani, mayaudari, dama haka kuke bakuma zaku canza ba!!" fuuuuu haka Zahrah tafice daga cikin motar tamkar kububuwa.
Tamkar statue haka Dr Sadeeq ya tsaya, komai nasa daina aiki yayi, sai numfashinsa dake fita da sauri, ganin komai yake tamkar al'amara, wai yau shine Zahrah ta mara da hanunta, a hankali yasanya hanunsa ya shafi kan kumatunsa inda Zahrah ta wankesa da mari, ko kaɗan baiga laifin Zahrah ba, kuma baiji zafin marin da ta masa ba, babban damuwarsa da tashin hankalinsa, shine yanda yaga Zahrah tana kuka wiwi, sannan kuma ranta yayi matuƙar ɓaci, tabbas da yasan abun zai ɓaci har haka, to da baiyi gigin furta mata kalmar cewa zai aure ta ba, ko da na minti ɗaya ne bayason ɓacin ran Zahrah, yanzu yasan haka zata kwana tana kuka, maiyasa? maiyasa na kasa jurewa? ni nake burin faranta rayuwa da zuciyarta, amma sai gashi da kaina nasake ruguza farinciki'nta maiyasa? yatambayi kansa da ƙarfi, cike da haushin kansa ya sanya hanunsa duka biyu ya daki siterin motar tasa, wani irin haushin kansa yakeji, yayi dana sanin sanar da'ita abun dake cikin zuciyarsa, "mai yasa na yarda nazamo LOSER?" ya tambayi kansa cikin ƙunan zuciya, yakusan 10 minute yana zaune a cikin motar, da ƙyar ya'iya tada motar yabar cikin unguwar tasu...
Zahrah kuwa tana shiga gida, kaitsaye ɗakinta ta wuce, zamewa tayi a ƙasa, tashiga rera sabon kuka, lallai tayarda cewa Ƙaddaranta mai girma ce, daga wannan sai wannan, bata taɓa zato ko tunani'n haka zai fito daga bakin Dr Sadeeq ba, ko da wasa bata taɓa ayyana wani abu a ranta ga me da shi ba, maiyasa zai zo mata da wannan maganar a daidai wannan lokacin? maiyasa zai sake maida ita uƙubar da tayi nasaran samun bakin fita daga cikinsa? tabbas yanzu kam tayarda cewa duhu yasamu mazauni a cikin rayuwarta
"Bawanda zai soni a haka, shima nasan ba sona yake ba, wata manufarsa kawai yakeson cimmawa, ashe ƙaddarorina suna da yawa?" ta tambayi kanta cike da ruɗu.
Sanin bata da amsar bawa kanta, yasanya ta cigaba da kukanta, ganin hakan bazai fishsheta ba yasanya ta ɗauro alwala tazo ta fara gabatar da salla, haɗe da miƙamawa mai kowa mai komai duka lamuranta...
Koda Doctor ya isa gida, baije koda ɓangaren mahaifiyarsa bane, kai tsaye ɓangarensa ya nufa, gaba ɗaya jiyakeyi duniyar ta masa ƙunci, saboda cimma muradinsa yasake sanya Zahrah a damuwa, kwanciya yayi lamo akan gado, zuciyarsa cike da tarin tunanuka kala kala, gaba ɗaya kalamanta ne suke yawo a ƙwaƙwalwarsa, babu kalman da tafi tsaya masa a rai kamar inda takecewa " Natabka nadamar baka daman shigowa rayuwata da nayi, katafi ba naso na sake ganinka ko kuma jinka!!" wannan kalamannata sunfi komai ɗaga masa hankali, sam shikam ya
ma manta da marin da tayi masa, saboda bai ɗauki marin a matsayin komaiba, shidai shiga damuwarta ne bayaso, baisan wani irin so yake mawa Zahrah ba, bayason ganinta a cikin damuwa, ba kuma yason ɓacin ranta, amma tayaya Zahrah zata fuskancin hakan? Yanaso ya aureta yakuma inganta rayuwarta, ba budurci'nta bane abun so a gareshi ita kanta ce abarsonsa, haƙiƙa kowani namiji yana burin auren mace yasameta a budurwa, shima kuma yana burin hakan, amma son da yakemawa Zahrah, yasanya zai iya karɓanta a yanda take.. Haka Doctor yayita saƙawa da kuncewa, da ƙyar bacci ɓarawo yayi nasaran ɗaukarsa.
Ɓangaren Zahrah ma dai hakanne takasance da ƙyar ta'iya runtsawa a wannan dare....
TURKEY*
*ZAID* ne zaune akan wata haɗaɗɗiyar kujera, sanye yake da riga long slive, white colour yayinda wandon jikinsa ya kasance baƙi, suit ne baƙi ɗaure a saman kayan nasa, sosai yayi kyu a cikin shigartasa, hanunsa riƙe yake da wani dogon kofi na glass, bakomai ne acikin kofin ba face giya, a hankali yake sipping giyar tasa, yayinda ya ɗaura ƙafansa ɗaya kan ɗaya, gefensa kuwa Abid ne zaune shima dai irin shigar Zaid ɗinne a jikinsa, sai dai shi nasa kalan sun kasance blue, "Lokaci fa yana tafiya Zaid, yakamata ace yau munkoma New York, amma bansan dalilinka nacewa muzauna anan ba, ni fa duk yanda instanbul takai ga haɗuwa da daɗin zama, batakaimin new york ba, kasan can akwai mata ƴan harka, amma ni gaskia nan a takure nake!" Abid yakai ƙarshen zancennasa cike da ƙosawa.
Kyakkyawan murmushinsa yayi haɗe da maida kallonsa ga wani kyakkyawan ruwa dake gudana a gefensu,
"Inason zaman Instanbul sosai Abid, domin yanayin garin yanasawa inajin shauƙin abar sha'awata!!"
"Bangane shauƙin abar sha'awan kaba? wai meke damunka ne? kusan tsawon watanni kenan dana fuskanci sauyawa a tattare dakai"
"Sha'awa nakeji Abid, matsanancin sha'awarta nakeji!"
Zaid yafaɗa cike da tsananin shauƙi.
"Sha'awa? wacece ita?" Abid ya tambaya cike da zaƙuwa, domin shikam yarasa wace irin macece Zaid ya kejin sha'awa'rta haka, ko da yaushe cikin maganarta yake, kuma ita kaɗai yakejin sha'awa.
"ZAHRAH NA!" Zaid yafaɗa cikin wata murya mai ɗauke da ma'anoni.
Dariya sosai Abid yasanya, hadda riƙe ciki, "Zahrah fa kace Zaid, wannan villager girl ɗin, koba sugar baby'nka ba?" Abid yatambaya yana ƙoƙarin gimtse dariyar da ta tasomai.
" Tana da matuƙar mahimmanci a wajena Abid, bantaɓajin irin abunda nakeji akanta ba, inason kasancewa da'ita a koda yaushe, inaso tazama ita ce mace guda ɗaya dazanna yin sex da'ita dare da rana, sha'awarta tamun mummunan kamu Abid, kasan yanda nakeji kuwa ?" Zaid ya tambayi Abid cikin sigar rashin wasa.
"Kokaɗan bansan ya kakejiba, amma kuma Zaid wannan ba sha'awa bane SO ne" Abid yafaɗi hakan da iya gaskiyarsa, domin shi abun da ya fahimta kenan.
Dariya sosai Zaid yashiga yi, haɗe da sanya hanunsa ya daki kafaɗan Abid.
"Shirmen banza, wai SO? menene SO Abid? kasan me kake faɗa kuwa, taya sha'awa zata zama SO, so fa kananufin wai inasonta ne, hahaha Abid ƙwaƙwalwarka ƙaramace, taya za'ayi nayi soyayya da'ita, sha'awace kawai kuma da zaran na sakeyin sex da'ita nasan komai zai wuce, tun farkoma danasan ban ƙoshi da'itaba, ai da banbari ta tafiba!!" yaƙare maganar yana mai ɗaga kofin giyarsa yakai baki.
Murmushi kawai Abid yayi, domin yafi kowa sanin cewa Zaid bayason gaskia, amma tabbas shikam anasa hasashen zuciyar abokinsa takamu da so, yana kuma da tabbacin idan har Zaid zaiyi sex da Zahrah sau ɗari, to wannan sha'awar bazata taɓa barinsa ba, saboda dama ba sha'awar bace So ne.
"Shikenan naji ba soyayya bane, sha'awa ce, amma kasan dai yanzu bazaka taɓa samunta ba ko, wataƙilama ta mutu, domin ina da tabbacin cewa baka shigeta da wasa ba"
"Dole zan sameta ne Abid, dole sai ta dawo gareni, kuma dole ta ƙara yarda da ƙudurina a karo na biyu, aure baya ɗaya daga cikin tsarina, amma idan taƙi yarda dani, saina aureta!"
Saurin kallon Zaid Abid yayi jin abun da yake fitowa daga bakin Zaid ɗin, "Aure kuma Zaid? Abid yafaɗa cike da mamaki.
"Ƙwarai zan'iya aurenta Abid, ƴan matan tana burgeni fiye da zatonka, inason komai nata, tana da kyau na fili dana baɗini, ni nasan mai naji a cikinta Abid, bakuma zanso nasake rasata ba, sha'awarta yasa koda yaushe cikin tunaninta nake, na kuma gama yanke hukunci, nan da sati ɗaya zankoma Nigeria, badon kowa ba sai don ita, nayi missing tattausan laɓɓanta masu zaƙi kamar zuma!!" Zaid yakai ƙarshen zancennasa yana mai lumshe idanunsa, da suka soma zama ja lokaci ɗaya.
Hangame baki Abid yayi yana kallon Zaid, "Anya kuwa ba aljana Zaid ya haɗu da'ita ba?" yatambayi kansa, tabbas baitaɓa ganin Zaid acikin hali makamancin wannan ba, gaba ɗaya Zaid ya sauya, yarage yawan yin sex da mata, a cewarsa wai bayajin daɗinsu, sannan kuma koda yaushe cikin tunani yake, to idan ba so ba meke da munsa ? Abid yakuma tambayar kansa.
A hankali Zaid ya buɗe idanunsa, haɗe da miƙewa tsaye kwalbar giyansa dakuma kofi ya ɗauka a hanunsa kai tsaye yanufi wani babban bene inda anan masauƙinsu yake, da kallo kawai Abid yabisa har ya ɓacewa ganinsa..
Yana shiga cikin ɗaki ya ɗaga kwalbar giyarsa ya kafa a bakinsa, saida ya shanye giyan tas kafun yayi wurgi da kwalba'r, kaitsaye ya nufi inda ma'ajin zane zanen sa suke, Caboard papers ne dayawa acikin wajen kuma duka ɗauke suke da hoton zanen fuskar Zahrah a jiki, wani ma iya bakinta kawai ya zana, wani ko iya idanunta ya zana, yana yawan yin zanen ne idan matsanancin kewa da sha'awarta ya da mesa, ɗaukan caboard paper'n dake ɗauke da zanen bakinta yayi haɗe da mannawa akan nasa bakin, wani irin zubawa yaji tsikar jikinsa tayi, domin kuwa ji yayi tamkar itaɗince da gaske, zamewa yayi ya zauna a ƙasa daɓas, haɗe da warwatsa caboard paper's ɗin akan jikinsa.
"Inakewarki Sugar Baby'na ,nayi missing komai naki, duk da cewa nasan kina fushi dani namiki da zafi, amma kiyi haƙuri wannan karon bazan miki da zafi ba, a hankali zan bi da ke tayarda zakiji daɗi har brain ɗinki, zakuma za ki saba da ni a sannu, na miki alƙawari zandawo gareki!, kina sona?" yatambayi zanen fuskarta dake jikin wani ƙaton caboard paper, "Nasan har yanzu kina sona ko Zahrah na?" still dai wannan zane yakuma tambaya, murmushinsa mai kyau yakumayi, haɗe da sanya hanu yashafi gefen kumatunsa.
" Kiyi murmushi Zahrah na, nakusa zuwa gareki, a yanzu zan iya sadaukar da komai na zuwa gareki, amma fa banso kina yawan fushi, duk da cewa idan kina fushi kinfi kyau !"
Haka Zaid yayita sambatun sa har bacci ya ɗaukesa a wajen.
Kwance take akan ƙirjinsa, yayinda fuskarta ke ɗauƙe da murmushi, a hankali ya matso da fuskarsa daf da tata, cike da matsanancin sha'awa ya kamo lips ɗinta na ƙasa yashiga tsotsa a hankali, cike da ƙwarewa yake cusa harshensa cikin bakinta, cike da soyayya ta soma tsotsan harshensa tana mai lumshe idanunta, a hankali yayi ƙasa da hanunsa zuwa ƙirjinta, cikin salo yashiga shafa breast ɗinta, yanayin yanda suke sucking tongue ɗin junansu, shiyasanyasu suka fice a hayyacinsu lokaci guda, ƙasa yayi da kansa zuwa ƙirjinta, yana shirin ɗaura bakinsa a kan nipples ɗinta kenan, taɓace masa ɓat, dai dai lokacin yafarka a hargitse, wani irin nannauyar ajiyar zuciya ya sauƙe, duk da cewa sanyin A.C na aiki a cikin ɗakin amma shi gumi yake haɗawa, da ƙyar ya'iya miƙewa ya shiga bathroom haɗe da sakarmawa kansa shower.
ba yau yafara wannan mafarkin ba, amma maiyasa Zahrah take gudunsa acikin mafarki, takan ɓacewa ganinsa a daidai lokacin da yake matsanancin buƙatar ta....
*5/December/2019
*Voted,Comment, and Share please..... Follow me on Whatsapp and Wattpad @fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymerhsardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*Chapter 48 to 49*
Yajima tsaye a gaban shower ruwa na dukansa, mafarkinsa na yau ne yatsaya masa a rai, duk da kuwa cewa ba wannan bane karo na farko, daya fara yin irin wannan mafarkin. Koda wasa baiyi niyar komawa America a yau ba, amma yanzu yaji ajikinsa cewa komawarsa can ɗin yafi masa, domin kuwa mararsa har ƙullewa take saboda sha'awa, gaba ɗaya kwana biyunnan da suka shuɗe baiyi sex ba. A gurguje ya shirya kansa, bayan yasanar da Abid cewa shima ya kimtsa zasu wuce America a yau. Suna zuwa airport basu wani daɗe ba, jirginsu yaɗaga zuwa sararin samaniya....
Nigeria
Washe garin ranan da Dr yazo da dare yafaɗi muradinsa..
Tun tashinta takejin ƙunci a zuciyarta, hakanan take jin ta tsani komai na duniyar, badon lecture'n da zasuyi yau mai amfani bane, to tabbas da bazata je makarantar bama.
Doctor Sadeeq ne tsaye a tsakiyar ɗakinsa, yayinda hannayensa duka biyu ke sanye cikin aljihun wandonsa, shima kallo ɗaya zaka masa kafahimci cewa yana cikin damuwa, kallon sa yamaida kan agogon bangon dake saƙale ajikin bangon ɗakin na sa, ƙarfe 7 da rabi na safe kenan, tabbas yasan yau ƙarfe takwas suke da lecture, yanaji a jikinsa cewa yayi mata laifi mai girma, sannan idanunsa suna matuƙar son ganinta, to amma a yanda yakeji bazai iya zuwa gareta ba, "idan ma naje nace mata me?" yatambayi kansa. " Nariga dana furta mata abun dake cikin zuciyata, dole zanbata lokaci domin samun dawowar nutsuwar ta" yafaɗi hakan a bayyane, wayarsa ya ɗauka haɗe da kutsawa cikin dialing call ɗinsa, numbern drivernsa yashiga ƙira kai tsaye, ƙara biyu wayar tayi, drivern yaɗauki ƙiran, kasancewar driver'n yasan gidan su Zahrah, yasan ya kai tsaye, bai tsaya yi masa wani kwatance ba, yace masa yaje ya ɗauketa ya kaita makaranta, da "to" kawai driver'n ya amsa masa, katse ƙiran yayi haɗe da cilla wayar tasa zuwa kan gado,
"Yasan balallai ta yarda tabi driver'n ba, domin yanayinta da yagani jiya, kaɗai ya isa ya tabbatar masa da hakan, amma burinsa ne ya bata ingantacciyar kulawa, shiyasa baiyi ƙasa a guiwaba wajen sa driver'n nasa kaita makarnta, saboda baiso ta hau wani abun hawa bayan nasa....
Ko kwalli, yau bata shafa ba, balle kuma uwa uba fawder, zumbuleliyar doguwar riga ta sanya, haɗe da ɗaura ƙaton hijab akai, kallo ɗaya zakayi mata kasan cewa tana cikin damuwa da ƙunci.
Koda tayi mawa su Baffa sallama, suma sun fahimci cewa yanayinta ya sauya, amma sai suka share babu wanda ya tambayeta.
Tana kai ƙofar gida zuciyarta tayi wani irin bugawa, sakamako'n ganin motar Dr Sadeeq, da tayi fake a ƙofar gidan nasu, tsayawa tayi cak ganin cewa driver'n sane yafito daga cikin motar, saɓanin shikansa Dr ɗin.
Cike da girmamawa Mudi driver ya ƙaraso inda Zahrah ke tsaye.
" Ranki shi daɗe barka da safiya! dama yallaɓoi ne yace nazo na kaiki makaranta, shi ba zai samu daman zuwa ba, wani aiki ne ya riƙesa, kawo jakar na karɓamiki" Mudi driver ya ƙare zance'n nasa yana mai ƙoƙarin karɓan jakar dake riƙe a hanunta. Saurin ja da baya tayi haɗe da fusge jakarta, cike da ɓacin rai tace.
"Kakoma kace masa bana buƙatar kulawarsa koda kaɗanne, ka kuma ce masa injini yafita a rayuwata, saboda bana buƙatarsa!" tanakai ƙarshen zancennata tasakai tayi tafiyarta.
Da kallo kawai Mudi driver yabita. "Uh ni naga bala'i, daga taimako kawai, to Allah ya kyauta" Mudi yafaɗa yana mai komawa cikin motar, key yayimawa motar haɗe da nausata kan hanya, tabbas zai koma ya shaidawa uban gidansa, duk abun da tace a faɗamai..
Cikin ikon Allah tana isowa bakin titi tasamu mai taxi, bawani ɓata lokaci tashiga yaja sukayi gaba, bayan ta sanar masa inda zai kaita.
Tun shigowarta cikin ajin, Husnah ta lura da mugun sauyawan da fuskar Zahrah'n tayi, domin kuwa kowa ya kalli idanunta, zai fahimci cewa tayi kuka har ta ƙoshi. kasancewar Zahrah'n na shigowa malami yashigo, yasanya Husnah bata samu damar tambayarta komai ga me da sauyawarta ta ba.
Koda aka fito daga lecture, kan dakalin da suka sama zama, yauma sukai mawa kansu masauƙi.
"Wai meke damunki ne Zahrah? gaba ɗaya kinsauya, bayan jiya ba haka muka rabu dake ba, sannan kuma na kula cewa, yau ba Dr bane ya kawoki, maike faruwa?" Husnah ta tambaya cike da kulawa, ga ƙawarta ta.
"Inacikin matsala Husnah! a she a yanzu babu wani, wanda zai taimakeka don Allah sai don biyar buƙatar kansa? na ɗauki yarda ta na basa, na ɗaukesa tamkar ɗan'uwa, na'aminta dashi, nayi saurin yadda haɗi da sakewa dashi, bantaɓa zaton haka zata faru ba, ashe shi abun dake cikin zuciya da ruhinsa daban ne, wani abune saɓanin tunani na!" Zahrah tafaɗa tana mai share ƙwallan daya gangaro daga cikin idanunta.
"Banganeba, kinsani a duhu, maikuma ya sake faruwa? ki faɗamin !" Husnah tafaɗi hakan cike da zaƙuwa, don ta ƙosa taji menene matsalar ƙawarta ta.
"Kinsan abun da yafaru dani Husnah, Zaid yaci mutumci na, ya ƙwaci budurcina da ƙarfin tsiya, ya halaka min rayuwa, shin kinaga akwai wani namiji dazai soni tsakani da Allah, bayan yasan abun da yafaru dani?" Zahrah ta tambayi Husnah.
"Haryanzu banfahimci inda kalamanki suka dosa ba Zahrah, zaifi kyau ace kiwarwaremin komai!" Husnah tafaɗi hakan cikin rashin fahimta.
"Ba gaskiya bane Husnah, bai faɗawa kansa da zuciyarsa gaskiya ba, baizamanto gaskiya ba, soyayyar da yakemin ba gaskiya bace, Husnah bazan yaudari kaina ba, domin nasan babu tayanda za'ayi cikekken namiji mai aji da lafiya kamar Doctor Sadeeq, yace wai ni yake so ya aura! ina kokonto akan al'amarin !" gaba ɗaya hawaye sun gama wanke mata fuska, lokacin da takai ƙarshen zance'n nata.
Nannauyar ajiyar zuciya Husnah ta sauƙe, domin kuwa sai yanzu ta fahimci inda matsalar ƙawartata take, dakuma abun da ke damunta.
"Doctor da kansa yace zai aure ki Zahrah?" Husnah ta tambaya, bayan ta aza hannayenta duka akan kafaɗun Zahrah.
Kai kawai Zahrah ta'iya gyaɗawa, alamar "eh''
"Ba wasa bane Zahrah kamar yanda kika ɗauka, haka kuma ba yaudara bane kamar yanda kike tunani, har yanzu keɗin mai kyauce, kuma haryanzu keɗin haɗaɗɗiyar mace ce abar so ga kowani irin namiji, ba'akanki a ka faraba, baikuma dace ki ɗau hukunci mai tsanani gawanda baiji ba bai gani ba, kina tunanin Doctor Sadeeq yaudaranki zaiyi ?" Husnah ta tambaya.
"Ƙwarai kuwa Husnah, ke kanki kinsani, namiji kamar Dr ba sa'an aurena bane, ko lokacin danake ɗauke da mutumcina yafi ƙarfina, balle yanzu danake fanko, inaso kisani wannan karanbani'n shi na tafka a karon farko, yazo yazamemin babbar matsala, domin kuwa nayaudari kaina, na sawa zuciyata soyayyar wanda har gaban abada yafi ƙarfina, yakuma yi mini rata, na yaudari kaina danaƙi amfani da tunanin cewa Zaid yafi ƙarfina, bazan taɓa yarda nasake aikata haukan dana aikata a baya ba Husnah!" Zahrah tafaɗa cike da raunin murya dana zuciya.
"So baitaɓa zama haukaba Zahrah, kada kicemin kin wulaƙanta Doctor saboda abun da Zaid yayi miki, kada ki yarda da tunaninki nacewa gaba ɗaya maza mayaudara ne, kowa da irin halinsa, kuma masu irin halin Zaid basa ɓoyuwa a kamanni da halaye, soyayyarsa ce kawai tarufe miki ido, har ki ka kasa hango mummunar manufarsa a kanki, yana da kyau ki nutsu kiyi tunani, inada tabbacin cewa Dr Sadeeq, ba zai taɓa cutar da rayuwarki ba, kema kuma yakamata kisan hakan, kada tunaninki ya gushe ki kasa tantance fari da baƙi, wlh ni ina da tabbacin cewa Dr Sadeeq ba mutumin banza bane, bakuma zan ɓoyemiki ba, tabbas idan kika tsaya wasa da damarki, to zata miki mummunan suɓucewa, haƙiƙa Dr Sadeeq haɗaɗɗen gaye ne, wanda ko wacce mace zatayi fatan samunsa a matsayin mijin aurenta, nasan idan nace miki kiyi soyayya yanzu na haɗaki da babban aiki, amma zai kyautu ace ki koyawa zuciyarki soyayyar Dr Sadeeq, shawara nake baki Zahrah, idan kuma har kikayi amfani dashi, bazaki taɓa danasani ba, dan Allah ƙawata kiyi tunani mai kyu!" Husnah tafaɗi hakan cikin son ƙarfafawa Zahrah guiwa.
Hawayen dake zuba daga cikin idanunta ta sanya hanu ta share.
"Bazan iya ba Husnah, bazan iya taɓa sake son wani ba a cikin rayuwata, kada ki ga laifina, nasan Dr Sadeeq yafi ƙarfina, yana da asali, yana da ƴan uwa, yanada gata, yana da kuɗi, yanakuma da ƴancin da zai zaɓi matar aure wacce ransa keso, nikuma fa? idan kikayi dubi da tushena, to ban cancanta da zama inuwa ɗaya da shi ba, nifa yanzu banda wani ƴancin da zan iya zaɓin mijin aure da kaina, sbd akwai nakasa acikin rayuwata, dole sai mai tawakalli ne zai iya aure na, to maiyasa zansanya kaina a cikin wahala? balallai farincikin da Dr Sadeeq ke ƙoƙarin bani yakasance dauwamemmeba, nafaɗamasa yafita a rayuwata Husnah, a yanzu bana buƙatar kowani namiji, zaifi kyautuwa a gareni nayi rayuwata ni kaɗai, nayarda da ƙaddarata, amma kuma yazama dole na kiyaye sake jefa kaina a haɗarin soyayya!"
Rungume Zahrah,
Husnah tayi ajikinta, sosai tausayin ƙawarta ta ya kamata, haƙiƙa Zaid yacutar da rayuwar Zahrah, ya rabata da duk wani sukuni nata, amma a kwai Allah.
"Haƙiƙa dole zakiji ciwo Zahrah, amma yana da kyau ki zurfafa tunani, ni ina da tabbacin cewa Dr Sadeeq auren ki yakeso yayi bada wasa ba, amma abun da kikayi masa baki kyauta ba, ki basa haƙuri, koda kuwa bazaki auresa ba, yayi babban ƙoƙari acikin rayuwarki, kiyi nazari, amma kuka ba naki bane, kuma yana da kyau rama halacci da alkhairi !"
Gaba ɗaya Zahrah jitayi jikinta yayi laƙwas, take marin da ta shararawa Dr Sadeeq akan fuskarsa ya dawo mata, wani irin faɗuwar gaba taji, ko kaɗan batayi tunanin zata iya kai hanunta jikinsa da sunan duka ba, amma a daren jiya ɓacin rai yasanya idanunta rufewa, harta iya ta mare sa batare da tayi tunanin komai ba, tabbas komai yayi mata bai cancanci mari daga gareta ba.
Gaba ɗaya kasa sakewa a cikin makarantar Zahrah tayi a wannan ranan, dole ta tattara yanata yanata ta dawo gida.
Zaune take jigum akan tabarma yayinda hannuwanta ke dafe da ƙuncinta, idan da za'a ce za'a kasheta idan bata faɗi, tunanin me take ba, to tabbas da sai dai a kashetan, amma ita kanta batasan tunanin mai take ba.
Inna da fitowarta kenan daga bayi, hanunta riƙe da buta, kama ƙugu tayi, haɗe da maida kallon ta zuwaga inda Zahrah ke zaune tayi jigum.
"Wai lafiyanki kuwa Zahrah? meke damunki ne? tun safe haka kike sukuku, yanzu kuma kinyi tagumi tamkar wacce akamawa mutuwa, kodai halinki na da, kike son dawowa dashi ne? to wallahi bazan ɗau wannan iskancin ba, tun wuri ma kisani!" Inna taƙare maganar cikin faɗa faɗa.
"Ko ɗaya bahaka bane Inna, narasa taya zan ɓullowa matsala ta ne!" Zahrah tafaɗa cike da sanyin murya.
"Matsala! wace irin matsala kuma?" Inna ta tambaya cike da son jin gulma.
"Inna wai Likita ne yace zai aure ni !" Zahrah tafaɗi hakan cikin sarƙewar murya.
"Likita yace zai aure ki!" Inna ta maimaita maganan cikin ƙaraji haɗe da sanya duka hannayenta biyu ta dafe ƙirjinta.
Kai kawai Zahrah ta'iya gyaɗa mata domin zuwa lokacin har ƙwalla sun soma cika mata ido.
Wani irin guɗa Inna tasa, haɗe da sake kama ƙuƙu, "Lallai kuwa, wannan babban al'amari ne, mai ɗauke da tarin farinciki, Allah yasa dai kin amince masa?" cike da zaƙuwa inna taƙare maganar.
"Bazan iya ba Inna, kuma ma ni yanzu babu batun aure a tsarina,zan zauna kawai naƙare rayuwata cikin ƙaddarata!" Zahrah tafaɗa lokacin da hawayen da suka cika idanunta suka samu daman gangarowa.
Salati Inna ta sanya, haɗe da soma tafa hannaye.
"Amma kedai Zahrah anyi shashar banza, sokuwa marar wayo, ashe dai baki da hankali, yanzu a yanda kike ɗin nan, kin samu ance za'a aure ki a haka, kice wai baki amince ba, lallai yau nasake tabbatar mawa da kaina cewa ke wawuyace, to wlh baki isa ba, baki isa ɓarar mana da alkhairan da zamu samu ba, aure dole ko kina so ko bakya so, wato kinfiso kita zama damu, goɗo goɗo dake ba aure ko, to kisa aranki cewa aurenki da likita ba fashi, dole!"
"Babu wanda zai mata dole!" Muryan Baffa dake shigowa cikin gidan yakaraɗe kunnuwansu.
"Maikake shirin faɗa ne malam, kakosan me ta aikata kuwa, Likita fa yace yanason aurenta amma taƙi?"
"Ƙwarai kuwa duk na saurari zancen ku, magana ta gaskia Salame, baza'ayiwa yarinyar nan dole ba, yanzu lokacin ta ne, yakamata a bar rayuwarta tasha iska hakanan!" Baffa yafaɗi maganar sanda yayi mawa kansa masauƙi akan wani ɗan dakali dake tsakiyar gidan.
"Laaaa shikenan kuma, kakosan abun da kake cewa? kana nufin zuba mata idanu zamuyi, ba mu isa mu sata dole ba? wani shan iska kake ƙoƙarin samawa rayuwarta, sanin kankane cewa babu wani wanda zaizo yace zai jajiɓeta a yanda taken nan, don kawai likita ya rufa mata asiri yace zai aureta, saikayi ƙoƙarin hure mata kunne."
"Tashi ki koma ɗakinki kinji Zahrah, kiyi tunani mai kyau, idan kin yanke hukunci to kisanar dani!" Baffa yafaɗa cike da kulawa.
Cikin rashin ƙarfin jiki haka Zahrah ta koma cikin ɗakinta, yayinda take jiyo bala'in Inna a tsakar gida.
Jingina bayanta tayi da bango, haɗe da lumshe idanunta, saiyanzu take jin cewa bata kyautawa Doctor Sadeeq ba, amma kuma shima baikyautu ace yazo mata da magana mai nauyi kamar wannan ba, ko da wasa bata taɓa kawowa a ranta cewa wani zai sota anan kusa ba, gaba ɗaya ta cire soyayya a tsari da jerin rayuwarta, tabbas sai dai ta yaudari kanta, amma tasan bazata taɓa ƙara son wani ɗa namiji ba a rayuwarta, ta yarda da shawaran da Husnah ta bata, amma kuma abune mawuyaci, tarayyanta da Dr Sadeeq yazama mai ɗorewa, shin dagaske aurenta yakeso yayi koko shima wata manufartasa yakeson cimmawa? tatambayi kanta tambayar da bata da amsa, "Idan bakiyi aure ba, haka zaki dawwama Zahrah?" wata zuciyarta tayi mata wannan tambayar. hawayene suka shiga gudu akan fuskarta, lalllai akwai babban ƙalubale a gabanta.
Zaune yake akan derny table ɗin dake tangamemen falon Hajiyar tasa, plate ɗin abinci ne aje a gabansa, yayinda yake juya spoon ɗin dake cikin abincin dake gaban nasa a hankali, kusan mintuna 10 kenan da kawo masa abincin, amma yakasa koda kai loma ɗaya ne na abincin bakinsa, gaba ɗaya hankali da tunaninsa baya garesa.
Cike da tuhuma Hajiya da tun ɗazu take kallon sa tace
"Wai meke damunka ne Sadeeq? gaba ɗaya yanayinka ya sauya, kowa yaganka yasan cewa kana cikin damuwa? gashi nace kaje gidan su Saleema, amma kayi banza da maganan bakaje ba har yau"
Ajiyar zuciya Doctor Sadeeq ya sauƙe haɗe da maida kallonsa ga mahaifiyar tasa.
"Inada damuwa Hajiya!" yafaɗi hakan cikin sanyin murya.
"Subahanallah! damuwa kuma Sadeeq, damuwar me?" Hajiya ta tambaya cike da kulawa, Allah yasani tana matuƙar son ɗan nata.
"Nasamu wacce nake so ne Hajiya!" Sadeeq yafaɗa cikin ɗar ɗar, don baisan ya Hajiyar tasa zata ɗauki al'amarin ba.
"Kasamu wacce kake so? wani irin magana ne wannan, wato so kakeyi kamai dani ƙaramar mace ko, to wallahi baka isaba, bazai taɓa yiwuwa ba, nariga dana gama magana da iyayen Saleema, har ƙanin mahaifinka yashigo cikin lamarin, saboda haka wannan batun kama dainasa tun kafun ranka yakai ƙololuwa wajen ɓaci, banason shirme!" Hajiya tafaɗi maganar a fusace, haɗe da tashi tabar masa falon.
Tabbas dama yasani ko da Zahrah ta amincewa aurensa, to balalle ne Hajiyarsa ta amince masa ba, amma yasan cewa yanamawa Zahrah so mai tsanani, kuma insha Allah, zai aure ta ya rayu da'ita har zuwa ƙarshen rayuwarsa, domin yaji hakan a jikinsa.
(Tofa readers kunji abun da Hajiyar Dr tace, shi kuma kunji abun da yace, koya zata kaya oho.... Kuyi haƙuri wlh yau ina busy! Shiyasa na muku kaɗan.)
*7/December/2019*
*Voted,Comment, and Share please..... Follow me on Wattpad @fatymasardauna
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
'''{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*Chapter 50 to 51*
Cikin rashin kuzari yamiƙe haɗe da nufar hanyar barin falon, ko kaɗan babu nutsuwa acikin zuciyarsa, ko sake bi takan abincin nasa baiyi ba, haka yafice daga cikin falon. kaitsaye ɓangarensa yanufa. Shirya kansa yayi cikin riga da wando na suit. kaitsaye asibiti ya wuce domin kuwa akwai wasu patient da zai gani.
Gaba ɗaya tunanin Zahrah ya kulle, hartakai ta kawo ko makaranta taje ma bata da wani aiki saina tunani, ko karatun ma da ake koyar dasu bata fahimta, abubuwane sukai mata yawa, tayi matuƙar danasanin marin da tayi mawa Dr Sadeeq, haƙiƙa idanunta sun rufe, batare da tayi tunanin komai ba ta yanke hukunci, sai dai kuma har yanzu tunaninta daya gushe bai dawo gareta ba, takasa yanke hukunci, haka kuma takasayin tunani mai kyau, saidai tayarda da abu ɗaya. shine Doctor Sadeeq sam basa'an auren ta bane, yafi ƙarfinta. Yau kimanin kwana huɗu kenan da faruwar haka a tsakaninsu, tundaga wannan daren kuwa harzuwa yau, Dr baisake zuwa gareta ba, saidai fa kullum safiya, yana turo drivern sa akan yaɗauketa yakaita makaranta. amma zancen dai ɗayane, bata taɓa yarda tashiga motar, koma sauraran driver'n nasa batayi.
Dariya sosai Mahmud yashiga yi, a lokacin da yagama jin matsalolin abokin nasa, haƙiƙa Sadeeq yabasa dariya, ko da wasa bai taɓa tunanin wai Namiji kamar Sadeeq zaiji tsoron furtawa mace kalmar soyayya ba.
Tsuka Dr Sadeeq yaja haɗe da ɓata fuska cike da takaicin dariyan da Mahmud ɗin ke masa yace
" Bawai nafaɗa maka matsalata bane don kasani a gaba kayita min dariya ba, mafita nake nema Mahmud, gaba ɗaya kaina ya kulle, inasonta banakuma tunanin zan'iya barinta, amma kuma naga alamomin cewa zan rasata a fili!" Dr Sadeeq yafaɗi maganar cikin son abokinnasa ya ƙarfafa masa guiwa.
Ƙoƙari Mahmud yayi wajen tsaida dariyar tasa haɗe da gyara zama
"Yazama dole nayi maka dariya Sadeeq, a matsayinka na likita bokan turai, ka kasa jure zafin soyayya, amma kuma ko kaɗan banga laifinka ba, sai dai kuma, akwai ƙalubale a gabanka!" Mahmud yaƙare maganar yana mai waina pen ɗin dake riƙe a hanunsa.
"Wani irin ƙalubale kenan Mahmud?" Dr Sadeeq yatambaya cike da zaƙuwa, saboda shi mafita kawai yake nema.
"Nasara ko kuma akasinta, sune babban ƙalubalen da zaka fuskanta, amma ina mai maka fatan nasara, duk dacewa banganta ba, amma nasan tahaɗu sosai, saboda nasan abokina ya'iya zaɓe!" Mahmud yafaɗi hakan cike da barkwanci, wanda hakan kuma halinsa ne.
"Bazaka taɓa canjawa ba Mahmud, kai ko da yaushe idan ana magana mai amfani saikayi yanda kayi ka sako wasa a ciki." Dr Sadeeq yafaɗi hakan yana mai shafa suman kansa.
Ƴar ƙaramar dariya Mahmud yayi haɗe da ɗaukan cup ɗin juice ɗin dake gabansa yakai zuwa bakinsa.
"Babu amfanin ƙara tada zancen a gareta Sadeeq, tunda ta nuna maka bata sonka, inaganin kabata lokaci, ko ba komai zatayi tunani mai kyau, amma fa hakan danace bawai yana nufin kada kasake zuwa gareta bane, zaka iya zuwa gareta ako da yaushe, amma kada ka sake ɗago mata da zancen inaga haka zaifi!" Mahmud yafaɗi hakan cike da son ƙarfafamawa abokinsa guiwa.
Ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya Dr Sadeeq ya sauƙe, haɗe da haɗiyar yawu, sai yanzu yasomajin sanyi a cikin zuciyarsa, domin kuwa da gaba ɗaya kansa ne ya kulle.
"Zanyi yanda kace Mahmud, sai dai kuma inajiyewa kaina tsoro, kada a gaba taƙi amsata, sannan kuma yanzu bansan da wani ido zan kalle ta ba!" Dr Sadeeq ya faɗi haka cikin ɗar ɗar.
Dariya Mahmud yakuma kwashewa dashi a karo na biyu, lallai yayarda cewa so mugun abune, domin kuwa shi kaɗai ke sa jarumi kuma gwarzon namiji acikin tsoro dakuma ɗar ɗar.
"Yanaga jikinka gaba ɗaya yaɗau rawa, kada dai kabani kunya, tsoronta kakeji tun yanzu, idan kuma akayi auren yaya kenan?" Mahmud yatambaya cike da shaƙiyanci.
Tsuka kawai Dr Sadeeq yakuma ja, haɗe da miƙewa tsaye, domin idan yabiye ta Mahmud to baƙin ciki sai ya cika masa zuciya, domin kuwa halin Mahmud ne tsokana da yawan barkwanci.
"Gwamma nayi tafiyata zaifi min, kayi dariyanka ka ƙoshi, ai nine nakawo kaina office ɗinka, kana da right ɗin da zaka iyamin komai" Dr Sadeeq yakare maganar yana mai gyara zaman suit ɗin dake jikinsa.
Ko sake sauraran Mahmud dake ta faman dariya baiyi ba, yayi ficewarsa daga office ɗin Mahmud ɗin.
Cikin ɗan kuzarin da yasamu yake tuƙa motar tasa, yanzu kam yagama aminta da shawaran da zuciyarsa ta basa. Kai tsaye gida ya koma, wanka yayi haɗe da shirya kansa cikin wani haɗaɗɗen riga da wando na jeans masu kyaun gaske, sosai kayan sukai masa kyau a jiki, suka kuma fito da asalin kyawu da kwarjininsa, babu abun dake tashi ajikinsa sai daddaɗan ƙamshin turare. Makullin motarsa ya ɗauka haɗe dasakai yafice daga cikin ɗakin.
Zaune take akan ƴar katifarta, daga ita sai wata riga marar nauyi, jakan kayan shafanta ne aje a gabanta, da'alama daga wanka tafito, domin kuwa wani sashi na jikinta ɗauke yake da danshin ruwa. Kallo ɗaya zakai mata kafuskanci irin ramar da tayi lokaci guda, gaba ɗaya ta zabge ta faɗa, hips da breast ɗin tane kawai suke a cike a jikinta. A hankali take shafa Vaseline ɗin dake riƙe a hanunta, Yanayin yanda take shafa vaseline ɗin idan ka gani, kace dole akai mata. tana gama shafa mai ɗin, ta murza powder kaɗan akan fuskarta, haɗe da shafa kwalli a cikin idanunta, take fuskarta ta tasakeyin fayau, yayinda idanunta, suka sake bayyana girmansu a fili,kasancewar kwallin yana taimakawa wajen bayyana girman ido.
Kallonta tamayar kan ɗan ƙaramin agogon bangon dake ɗakin nata, ƙarfe 5 na yamma kenan, kuma dai dai lokacin sukayi da Husnah cewa zataje ta sameta a gida. Cikin rashin kuzari, ta miƙe haɗe da ɗaukan kayanta riga da sket na atamfa tashiga sanyawa, duk da cewa atamfar mai sauƙin kuɗi ne, amma hakan baihana ta yi mata kyau a jikinta ba. Wani irin zazzaɓi takeji yana sanɗan jikin ta, idan ba don tariga da tamawa Husnah alƙawarin cewa zata zo yau ɗin ba, to tabbas da ta ɗage zuwa gidansu Husna'n saboda bata wani jin daɗin jikinta, takumasan cewa damuwace kurum tayi mata yawa.
Inna ce tashigo cikin ɗakin, adai dai sanda Zahrah ta gama sanya hijab ɗinta.
"Au ashema kinsan da zuwansa kenan?" Inna tatambaya tana mai ƙarewa Zahrah kallo.
"Banganeba Inna, zuwan waye kuma?" Zahrah taje fawa Inna tambaya cikin rashin fahimtan inda kalaman Inna'n suka dosa.
"Naga kinshirya tsab kamar kinsan da zuwansa, to koma dai menene kije yanajiranki a waje!" Inna tafaɗi hakan tana mai ƙoƙarin barin ɗakin.
"Waye Inna? kuma ni shirin nan da kika ga nayi, gidansu Husnah zani, amma waye ke nemana ?" Zahrah takuma tambaya cike da son ƙarin bayani.
"Waye kuwa zaizo neman ki a yanda kike ɗinnan, ai sai dai shiɗin da har ya yarda zaiyi JIHADI ya aure ki a haka, amma wai saboda son zuciya da butulci irin naki, kike neman watsa masa ƙasa a idanu!" Inna taƙare maganar dai dai sanda tayificewarta daga cikin ɗakin.
Wasu irin siraran hawayene suka samu nasaran gangarowa daga cikin idanun Zahrah, tabbas gaskia Inna ta faɗa, babu wani mai nemanta sai shi ɗin shi kaɗai, kuma tabbas tayadda shima JIHADI yayi kamar yadda Inna tafaɗa, ashe dagaske ne itakam ƙaddaranta tayi mata mummunan zane a goshinta, saurin share hawayenta tayi haɗe da sakai tafice daga cikin ɗakin.
Tsaye yake a jikin motarsa yayinda kansa ke duƙe a ƙasa, ɗan makullin motarsa ce riƙe a hanunsa yana kaɗawa, wannan karon kam sosai yake yaƙi da zuciyarsa don bayaso tasake sanya masa tsoro kokuma ɗarɗar.
A hankali take taku cike da nutsuwa har ta ƙaraso garesa, ɗan nesa dashi ta tsaya haɗe da yimasa sallama cikin sassanyar muryarta wadda bata fita sosai.
Lumshe idanunsa yayi haɗi da buɗesu a lokaci guda, badon komai ba sai don yanda sassanyar muryarta ta daki jiki da zuciyarsa.
"ZAHRAH!" yaƙira sunanta cikin murya marar fidda ƙaƙƙarfan sauti.
"Um!" Zahrah ta amasa masa batare da ta'iya motsa bakinta ba, haka kuma kanta a duƙe yake tunda tazo bata'iya ɗaga kai ta kallesa ba.
Kallonta yashiga yi tundaga ƙasanta har sama, tabbas duk da cewa a cikin hijab take, amma hakan bai hanasa hango rahamar da tayi ba, take yaji zuciyarsa tayi sanyi, tausayinta yasake kamasa.
"Inaso kimini iso cikin gida, inaga maganar mu acan zaifi, domin ina buƙatar zama!" yafaɗa cike da ƙosawa da tsayuwan da yakeyi.
Sumi sumi haka ta juya ta nufi cikin gida, harta shige cikin gidan bai ɗauke idanunsa daga kanta ba, "Wallahi Zahrah ta haɗu, komai nata mai kyau ne!" yafaɗi hakan a fili, cike kuma da shauƙin soyayya.
Jim kaɗan Zahrah tafito, tana mai wasa da yatsun hanunta, "Kashigo!" kawai ta'iya furtawa cikin murya mai sanyi. Tana gaba yana biye da'ita haka suka doshi cikin gidan.
Katuwar tabarma tabaje musu a hanyar zaure, yayinda ta je ta zauna a can ƙarshen tabarman ta takure waje ɗaya, tamkar amaryar da aka kaita ɗakin miji yau yau, lol.
Murmushi Dr Sadeeq yayi bayan yayimawa kansa mazauni, dole dai shi zai ci gaba da zama jarumi ako da yaushe.
" Miye haka? ai ko da yanka naman jikin mutane nake, ya kamata ace kin matso kusa dani, balle ma kuma ni ba'abun da nakeyi, ko na taɓa miki wani abune ?" Dr yafaɗi hakan cike da kulawa.
Saurin ɗago da kanta tayi ta kallesa, domin yadawo mata asalin Likitan da tasani, kuma gaba ɗaya ya sauya wasu ɗabi'un nasa.
Giransa ɗaya yaɗage sama, haɗe da cewa "Yadai, ko nayi wani sabon laifi ne akan wancan banda labari?"
Girgiza kanta tashiga yi ita kaɗai tamkar ƙadan garuwa, domin ita tama rasa maizata ce dashi domin kuwa da wani salon yadawo.
"Matso kusa dani mana!" yafaɗa cikin sanyin murya, mai ɗauke da lallashi.
Cikin rashin kuzari, ta koma tsakiyar ta barman ta zauna, bayan ta haɗa jikinta duka ta takure waje ɗaya.
Ajiyar zuciya Dr Sadeeq ya sauƙe haɗe da sanya hanunsa yashafi ƙasumbar dake kwance akan fuskarsa.
"Maiyasa zakisa kanki a damuwa Zahrah? yawan kuka dakuma yawan tunani marassa amfani, basa haifar da komai sai gajiyar da ƙwaƙwalwa, please banso kina wahalar da ƙwaƙwalwarki, nasan cewa abaya banine sila ba, amma yanzu nine sila.!" ɗanjim yayi kana yaci gaba da cewa..." Kiyi haƙuri Zahrah, nasan bankyauta ba, amma inaso kimanta komai, inaso ki fuskanci karatunki, ki maida hankali sosai kinji ƙanwata, bawanda zaimiki dole, ke mutumce kuma kowani ɗan adam yana da ƴanci, kema kina da ƴanci, saboda haka ki daina kuka kinji ƙanwar Likita!" Yanayin yanda yaƙare maganar kaɗai ya'isa yasanya zuciya hucewa daga cikin fushi.
Kuka kawai Zahrah ta fashe dashi mai sauti, domin kuwa sai yanzu nadaman abun da ta'aikata a garesa yadawo mata sabo fil. A hankali ta ɗago idanunta da suke ɗigan hawaye tamaida kallonta garesa, wannan fuskar ta mara? ta tambayi kanta, tabbas batayiwa kanta adalci ba, Dr Sadeeq baicancan ci mari daga gareta ba. kukane yakuma ƙwace mata, don batasan tayanda zata soma basa haƙuri akan abun da tayi masa ba.
Cike da damuwa ya dawo kusa da'ita, har suna iya juyo ƙamshin turaren juna.
"Subahanallah Zahrah kuka kuma? kinfasan banaso, kidaina kuka kinji, ki faɗamin idan ganina ne bakiso, yanzu zantafi Zahrah, nazo ne dama nabaki haƙuri akan abun da yafaru tsakanina dake, kiyi haƙuri Zahrah haka bazata...." Kasa ƙarasa maganar yayi sakamakon Zahrah da ta sanya duka hannayenta biyu ta toshe masa baki.
"Dan Allah kada ka ƙasƙantar da kanka awajen wacce bata dace ba, bata kuma cancanta ba, bakaine yakamata kabani haƙuri ba, nice yakamata na baka haƙuri, bai kyautu ace na mareka ba, nayi nadama Doctor, dan Allah kayi haƙuri, bansan yanda zanyi ba ne banda zaɓi, kayafemin!" Zahrah ta ƙare maganar cikin kuka, haɗe da karyewar zuciya.
Take yaji tausayinta yasake ninkuwa acikin zuciyarsa.
A hankali ya sanya hanu yazame hannayenta dake kan bakinsa, domin kuwa hakan da tayi masa har ya sanya tsikar jikinsa sun soma motsawa.
"Kinaso nayi haƙuri?" Dr yatambayeta.
Kaitashiga kaɗawa cikin kuka alamar "Eh"
"To kidaina kuka, domin kuwa daina kukanki shikaɗaine zaisanya nayi haƙuri nakuma manta da komai, kuma ko dama ni Zahrah batayi mini laifi ba, ƙanwata bata laifi a wajena, saboda haka share hawayenki kinji!" yaƙare maganar yana me miƙomata wani farin handkerchief wanda yafito dashi daga cikin aljihun wandonsa.
Karɓan handkerchief ɗin Zahrah tayi, cike da shagwaɓa tashiga share hawayen dake gudana akan fuskarta, ajiyar zuciya kawai take sauƙewa akai akai domin kuwa ko ba komai tarage wani nauyi dake maƙare a gefen zuciyarta.
"Yauwa ƙanwata, kinga kinfi kyau idan kina murmushi dakuma dariya, inaso akoda yaushe kikasance cikin farinciki!" Dr yafaɗa cikin nishaɗi, domin kuwa sosai yaji daɗin yanda Zahrah ta sauƙo daga fushin da takeyi dashi.
Tana gama share hawayen nata ta miƙamasa handkerchief ɗinnasa.
Kai yagirgiza alamar a'a haɗe da gyara zamansa "Nabaki kyauta, ki ajiye a wajenki, ko saboda gaba, domin naga ke kuka baya baki wahala, kinga duk lokacin da kika soma koke koken ki saiki share hawayenki da shi!"
Hararan wasa ta jefesa dashi, haɗe da murguɗa masa ɗan ƙaramin bakinta.
Dariya yayi domin sarai yana lure da'ita kuma yaga abun da tayi masa.
"Inazakije kikaci uban kwalliya haka? gashi kuma kinzo kinɓata shi da kuka." Yafaɗi maganar alokacin dayake ciro wayarsa daga cikin aljihunsa.
Turo bakinta tayi gaba, cike da ƙunƙuni tasoma motsa bakinta, da'alama wani abu takeson faɗa, "wai a hakanne nayi kwalliya, kawai dai yace banyi masa kyau ba" Zahrah tafaɗi hakan a cikin zuciyarta.
"Wayace miki hakane a zuciyata? ni na'isa nace kyakkyawar ƙanwata batayi kyau ba, to ma duk cikin garin Abuja wayakai ki kyau ne? babu fa!"
Dariya tasanya, wanda tajima batayi shiba, cab aikuwa ko da acikin makarantarsu akwai waƴanda suka fita kyau dayawa, balle kuma duka garin Abujan baki ɗaya.
Tsayawa yayi yana kallon yanda take dariyan, komai tayi ƙara kyau take.
Hanunsa ya sanya acikin aljihun wandonsa haɗe da ciro wani haɗaɗɗen choculate, ɓare ledan choculate ɗin yayi haɗe da miƙo ma ta. Kyawawan idanunta ta ɗago haɗe da watsa masa su, girgiza kanta tayi, alamar bata buƙata.
Kwaɓe fuska Dr Sadeeq yayi haɗe da marairaice idanunsa, take taji tsikar jikinta ya zuba, yayinda gabanta yayi wani irin mummunan faɗuwa, domin kuwa hakan da yayi yasanya fuskarsa ta koma yanayi da fuskar Zaid, saurin ɗauke kanta tayi daga garesa, haɗe da sauƙe idanunta ƙasa, yabuɗe baki zaiyi magana kenan wayarsa tasoma ƙara, alamar shigowar ƙira, cike da girmamawa yaɗauki ƙiran ganin cewa ƙiran daga Hajiyarsa ce.
"Kana'ina?" Hajiya tatambaya a kausashe.
Baikai ga bata amsaba taci gaba da cewa "Koma mekakeyi kabari, Inaso kaje gidansu Salima yanzu, umarni ne ba shawaraba!" ƙit takashe wayan batare da tajira taji mai zai ceba.
Ajiyar zuciya ya sauƙe haɗe da maida kallonsa ga Zahrah.
"Wani uzuri yatasomin, zantafi kikula da kanki!" yafaɗi maganar yana me miƙewa tsaye.
Miƙewa itama Zahrah tayi batare da tace dashi komai ba tashiga naɗe tabarman da suka tashi akai.
Wani irin kallo haɗe da murmushi mai tsayawa a zuciya yayi mata, kana yasa kai yafice daga zauren gidan nasu, yana fita yafaɗa motarsa yayi mata key.
Tanajin ƙaran tashin motarsa ta sauƙe a jiyar zuciya haɗe da komawa cikin gida.
Kamar yanda mahaifiyarsa ta umarcesa hakan yayi domin kuwa yaje gidan su Salima sungana da'ita, yarinyar bata da wani aibu, amma kwata kwata jininsa danata baizo ɗaya ba, domin kuwa sam bata burgesa kasancewarta mace mai rawan kai da shegen girman kan tsiya, har gwamma masa Zabba'u akan Salima, domin dai shikam Salima batayi masa ba. Haka dai suka gaisa sama sama, ko minti 20 baiyiba yabaro gidan nasu..
Bayan Sati Ɗaya.
Kusan ko da yaushe sai Doctor Sadeeq yazo gidan su Zahrah, amma kuma tundaga wannan lokacin baisake koda ɗago wani zance makamancin wancan ba, sai dai yana'iya ƙoƙarinsa wajen bata kyakkyawan kulawa. Sannan kuma dake ita ɗin me raunin zuciya ce take ta sake bashi yardanta akaro na biyu.
Ɓangaren gidansu Dr Sadeeq kuwa harsun fara shirye shiryen bikinsa, domin kuwa Hajiyarsa wannan karon bada wasa take ba, tace acikin 3 weeks takeso ayi bikin. Shi dai Dr Sadeeq idanu kawai ya zuba musu, domin kwata kwata baijin auren a jikinsa, da za'afasa auren to dazai fi kowa murna, saboda Zahrah yakeso Zahrah ce muradinsa, amma kuma haryanzu yakasa samun wani gamsashshiyar amsa daga gareta.
Ƙarfe 3 dai dai jirginsu ya sauƙa a babban airport ɗin dake cikin garin Abuja, motoci ne iri da kala har guda shida suka zo tarbansa, ciki kuwa hadda Dad ɗinsa, a hankali yake sauƙowa daga cikin matakalar jirgin sanyen yake da kayan sanyi hadda hula, yayinda fuskarsa ke ɗauƙe da wani haɗaɗɗen baƙin glass na maza, sosai yaƙara kyau da fari, kallo ɗaya zakai masa katabbatar da cewa yakai cikekke kuma gwarzon namiji, a gaskia yana da kyau da kuma kwarjini, uwa uba kuɗaɗe sun samu mazauni a jikinsa. Bakowacce mace bace zatayi tozali da haɗaɗɗen namiji kamar Zaid, kuma takau da idanunta ba, saboda Zaid yahaɗa duk wani abu da kowacce mace zata so awajen ɗa namiji, shidai matsalan sa ɗaya munanan halaiyansa. Yanda yake tafiya cike da izza shiyafi komai ɗaukar hankali, dakuma jan hankali zuwa garesa. Cike da farinciki Alhaji Ma'aruf yarungume ɗa'nnasa, duk da cewa babu wani shaƙuwa me ƙarfi a tsakaninsu amma yana matuƙar son Zaid.
Mota ɗaya suka shiga shida Dad ɗinsa, yayinda guard ɗinsu suka mara musu baya a cikin sauran motocin. Kwanciya yayi lamo ajikin kujeran motar haɗe da lumshe idanunsa, wani irin sanyi yakeji acikin zuciyarsa, koda wasa baitaɓa tunanin haka zai kasance dashi ba, kamarshi Zaid ace tunanin mace yahanasa sukuni harsaida yabaro duka abun da yakeyi ya dawo zuwa gareta, amma zaiyi maganin abun a yau bawai sai gobe ba yake da buƙatar ganin sugar baby'nsa, sai dai kuma wannan lokacin bada wasa yazo ba...
Zahrah ne keta kai kawo a tsakiyar ɗakinta, tabbas tayarda da duk wani shawara da zuciyarta ta bata, zuwa yanzu yakamata ace tayi abunda ya dace. Wayarta ne yasoma ƙara alamar shigowar ƙira, tana ɗaga wayar Dr Sadeeq yace "Gani na'iso ina ƙofar gida!"
"To" tace haɗe da aje wayar, ajiyar zuciya ta sauƙe haɗi da cije lips ɗinta, dama ɗaya kawai take dashi kuma tabbas idan tarasa wannan daman to zaiyi mata wahala tasake samun wani daman.
Hijib ɗinta ta sanya, koda tafito tsakar gida bata taradda Inna ba tana kuma da tabbacin cewa bama ta gidan.
Zaune yake acikin motar tasa, dagani kasan cewa yana cikin damuwa, domin gaba ɗaya har rama tasoma bayyana a jikinsa. Murfin motar tabuɗe tashiga, bakinta ɗauke da sallama, amsa mata sallaman nata yayi haɗe da gyara zamansa yafuskance ta " Baki taɓa min irin wannan ƙiran ba, naƙosa naji wace maganace zaki faɗamin mai matuƙar mahimmanci haka" gaba ɗaya hankalinsa ya tattara zuwa gareta.
"Dagaske kake Zaka aure ni?" Zahrah tajefo masa tambayar
dabai taɓa zata ba balle tsammani.
Kansa yashiga kaɗawa muryarsa har rawa take yace "Dagaske nake Zahrah, wallahi auren ki nakeso nayi, samunki a matsayin mata shine babban burina a yanzu." yafaɗi hakan da iya gaskiya'rsa
"So na kakeyi kokuma tausayina?" Zahrah takuma jifansa da wata tambayar.
"Sonki nake Zahrah, inamiki so mai tsanani, wlh inasonki da duka zuciyata!" Dr Sadeeq yabata amsa, cike da kulawa.
"Nayarda na Amince Zan aureka, muyi zama na har abada!" Abun da yafito daga bakin Zahrah kenan bayan tagamajin amsar da take buƙata daga garesa, cikin tsananin mamaki Dr Sadeeq yashiga kallonta, jin sauƙar maganarta yayi tamkar daga sama, kodai kunnuwan sa basu jiye masa dakyau bane?....
(To fa readers Ga Baba Zaidu yashigo Gari, ga kuma Zahrah ta amince da auren Dr Sadeeq, gashi kuma ɓangaren gidansu Dr anatashirye shiryen bikin Dr da Salima, koya zata kaya 🤷♀, please kusani a addu'anku wlh cikina ke ciwo sosai😥 idan kunga typing eror kuyi haƙuri gaba ɗaya banda wata isashshen nutsuwa ne 😭)
*10/December/2019*
*Voted,Comment,and Share please.... Follow me on Wattpad @fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI!!*
*Written by*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
'''{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & mitivate the mind of readers}'''
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*(This page is Dedicated to you HAROUN UMAR (H Umar) admin of 📖✍️BENEFICIAL WRITERS ASSOCIATION, inajinjinamawa ƙoƙarinka ako da yaushe haroun, kuma inagodia a gareka marar iyaka.)*
*CHAPTER 53 to 54*
Kasa motsa koda laɓɓansa yayi balle har yakai ga furta wata kalman, "dagaske ne abun da kunnuwansa suka jiye masa kokuwa mafarki yake?" yafaɗi hakan a cikin zuciyarsa.
"Kada kayi kokonto kokuma shakka, dagaske nake, na amince da aurenka, amma ina mai roƙon wata alfarma a gareka"...."Dan Allah kada ka wulaƙantani aduk yanda kasameni, kada kuma ka tozartani, nasan cewa tausayina yafi yawa acikin zuciyarka fiye da soyayya ta, saboda haka ina da tabbacin cewa ko gaba zaka iya sake samun wata mace,wacce itace zata kasance zaɓinka, kada haka yasa ka wulaƙantani dan Allah, kada kuma kacutar da rayuwata!" cikin sanyin murya ta ƙare maganarta ta, yayinda hawaye suka shiga fitowa daga cikin idanunta,suna sauƙa akan ƙuncinta.
Jiyayi gaba ɗaya wani irin matsanancin farinciki ya lulluɓesa, gani yake tamkar wasa Zahrah take masa, amma kuma ba'abun mamaki bane, saboda babu abun da yagagari Allah.
"Bansan ta'ina kokuma tayaya zan fara godemiki ba Zahrah, kin gusarmin da duk wata damuwa dake damuna, kinbani farinciki cikin ƴan mintuna ƙalilan, kiyarda dani Zahrah, inamiki Soyayyace ta gaskiya bawai, irin soyayyarnan tako oho ba, zan'iya sadaukar da duk wani abu nawa akanki Zahrah, soyayyar da nake miki, yasanya bana ganin laifi ko kuma aibun duk wani abun da kikamin, burina da fatana shine murayu tare dani dake amatsayin miji da mata, kuma aƙarƙashin inuwa ɗaya, Inasonki Zahrah, kuma namiki alƙawari komai wuya komai tsanani bazan taɓa gujemiki ba, ZANRAYU DAKE Zahrah!!" Dr Sadeeq yafaɗa cike da matsanancin farinciki, jiyake tamkar yajawo Zahrah jikinsa yabata kyakkyawan runguma.
Kuka Zahrah ta fashe dashi, wanda batasan dalilin yinsaba, ita ta amincewa kanta cewa zata auri Dr Sadeeq amma saitakeji tamkar dole tayimawa kanta.
Batayi zato ba saiji tayi Dr Sadeeq yajawota jikinsa haɗe da sanya hannayensa duka biyu ya rungumeta. "Inasonki Zahrah, kuma nayi maki alƙawarin bazantaɓa wulaƙanta ki ba har'abada, kidaina kuka kinji princess ɗina!" yaƙare maganar tasa cikin sigar lallashi.
Daddaɗan ƙamshinsa shiyaso birkita mata tunani don haka tayi saurin janyewa daga jikinsa, tana mai yin ƙasa da kanta.
Sam shikam ma yamanta da cewa hakan da yayi ba'abu bane mai kyau, gaba ɗaya murna yacika masa zuciya.
"Uh sorry baby, gaba ɗaya kece kikamantar dani komai!!" Dr Sadeeq yafaɗi hakan yana mai dafe goshinsa.
Ƙasa ƙasa Zahrah tayi murmushi haɗe da kawar da kanta gefe, hakanan taji wani irin nauyin Dr Sadeeq ɗin yaƙaru acikin zuciyarta, haka kuma yaƙara girma acikin idanunta.
Wani irin kallo Dr Sadeeq yashiga yimawa Zahrah duk dacewa takau da kanta gefe, sai yanzu nema yake ƙara ganin haɗuwarta fiye da da, tabbas da Zahrah bata amince dashi ba to da ya tabka babban rashi, domin kuwa Zahrah tahaɗu, macece ita da kowanni Namiji zaiyi fatan mallaka.
Sam batayi tunanin kallonta yake ba, don haka taɗan juyo dan itama ta saci kallonsa, aikuwa karab idanunsu suka sauƙa akan najuna, da sauri Zahrah tayi ƙasa da kanta haɗe da cusa fuskarta tsakan kanun cinyoyinta.
Dariya Dr Sadeeq yayi cike da shauƙi haɗe da shafa sajen dake kwance akan fuskarsa. "Yaushe kika farajin kunyana? lallai zamu ɓata idan harkinajin kunyana!" ya faɗi hakan cike da zolaya.
Ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba, haɗe da marairaice fuska cike da shagwaɓa tace "To bakaine kaketa kallo na ba, saikace baka sanni ba!"
Lumshe idanunsa yayi haɗe da buɗesu a lokaci guda, irin wannan salon shagwaɓan ai saita sashi bacci batare da yashiryawa hakan ba,lol.
"Ki faɗamin laifi ne don nakalli abar sona? saidai kiyi haƙuri amma kallonki yanzuma na fara, tunda kinamin kyau, kina kuma burgeni!" yanayin yanda yayi maganar abun burgewa ne, ga macen da tasan daɗin soyayya.
"Nidai kada ka wani ce inada kyau, daɗin bakine kawai nasan kakemin!" still da yanayin shagwaɓa tayi maganan.
Lumshe idanunsa yayi haɗe da fitar da iskan numfashi daga bakinsa, yanayin shagwaɓan Zahrah yafi komai burgesa a tattare da'ita, haka kuma sosai yake sauƙar masa da kasala. "Princess!!" yaƙira sunanta dawani irin murya mai taɓa zuciya.
A hankali ta ɗago idanunta ta kallesa, batare da ta amsa masa ba, ganin idanunsa a rufe, yasanya taɗan tsaya ƙaremawa fuskarsa kallo. "Duk kallona ɗaya da zaki yi bazai tafi a banza ba, sai kin biya kuɗi, gwamma ma kisani!" Dr Sadeeq yafaɗi haka batare da ya buɗe idanunsa ba.
Saurin ɗauke kanta tayi daga kallonsa haɗe da cewa "Niba kallonka nake ba"
"Zaki iya rantsewa cewa bani kike kallo ba?" yaje fo mata tambayar da batayi zato ba.
kanta tashiga girgizawa haɗe da cewa "Ai bankalleka sosai ba, kaɗan nakalleka!"
Dariya Dr Sadeeq yasanya wanda harsaida dimple ɗinsa suka bayyana, yanzu yayarda cewa Zahrah yarinyace ƙarama, kuma zakayi saurin kamata idan tamaka laifi.
Ƙoƙarin buɗe murfin motar Zahrah tasomayi, cikin mamaki Dr yace "ina zaki?"
"Zankoma gida ne, dama magana zan faɗa ma, shiyasa na ƙiraka, kuma nafaɗa ma, inada karatu, gobe muna da test a makaranta" Zahrah tafaɗi hakan dai dai lokacin da ta gama sanya ƙafafunta waje.
"Shikenan to My Princess kikulamin da kanki kinji, inasonki sosai!" Dr Sadeeq yafaɗa cike da kulawa.
Wani irin muguwar kunyarsace takama Zahrah, bashiri ta wuce cikin gida tana mai rufe fuskanta da tafukan hanunta.
Shima Dr ɗin murmushi yayi cike da jindaɗi, lallai idan ya auri Zahrah yakasance mutum mai sa'a, acikin satinnan insha Allah, zai sanarda ƙanin mahaifinsa azo a nemamasa auren Zahrah, a wajen Baffa.
"Aurenka da Salima fa?" Wata zuciyar ta jefo masa wannan tambayar, wani irin bugawa yaji ƙirjinsa yayi, gaba ɗaya amincewa dashi da Zahrah tayi yasanyashi manta halin da yake ciki na batun auren sa da Salima. Jiyayi gaba ɗaya jikinsa yayi sanyi, tabbas akwai ƙalubale a gabansa, domin kuwa yanada tabbacin cewa Hajiyarsa bazata taɓa sanja maganarta ba, gashi har ansoma shirye shiryen bikinsa da Salima, kuma shi a tsarinsa bai sha'awar auren mata biyu, Zahrah ita kaɗai ta'ishesa rayuwa, amma kuma tabbas yasan zai fuskanci matsaloli da yawa daga ƴan uwansa, matuƙar ya jajirce akan cewa Zahrah yakeso ba Salima ba, to amma dole zai jarraba sa'ansa, domin a gaskiya baijin cewa zai'iya haƙura da Zahrah.
Cike da sanyin jiki yayimawa motar tasa key, haɗe da nausawa kan titi.
Suna isa katafaren gidannasu, adai dai parking space motar tasu ta tsaya.
Bawani jinkiri Zaid yabuɗe murfin motar yafito, batare da yatsaya sauraran Mahaifinnasa ba, yanufi ɓangarensa kai tsaye.
Komai dake cikin ɓangaren nasa a gyare yake tsab, tamkar akwai wani wanda ke rayuwa a cikinsa, hakan kuma yasamo asaline da yawan gyara part ɗin da akeyi duk bayan kwana biyu, kasancewar Zaid mutum ne da bayason ƙazanta.
Direct bedroom ɗinsa yanufa, yanashiga yasoma rage kayan dake jikinsa, rigan wanka irin na maza mai gashi gashi a jiki yasanya, haɗe da sanya badroom slippers a ƙafafunsa, kai tsaye wajen fridge ɗin dake aje cikin ɗakin yanufa, maltina can yaciro haɗe da ɓalle ɗan ƙarfen da aka rufe bakin can ɗin dashi, yakai bakinsa, tunda yakai maltina can ɗin nan bakinsa bai ɗauke ba harsaida yatabbatar da cewa bakomai ciki ya shanye, cikin dustbin ɗin dake aje a ɗakin ya jefa can ɗin. Bathroom ya wuce haɗe da sakarmawa kansa shower. Wanka yakeyi amma gaba ɗaya tunaninsa baya garesa, yanaga shugar baby'nsa, amatuƙar matse yake da sha'awarta, haryanajin bazai iya daurewa yakai zuwa wani ɗan lokaci mai tsawo batare da'ita ba.
Bayan yafito a wanka yashiga shirya kansa cikin, haɗaɗɗun riga da wando masu kyau da tsadar gaske, gaskia komai na Zaid me kyau ne, domin kuwa kowani kaya yasanya saiya yi kyau, bakuma kayanne yake masa kyauba, shi ɗin kansa ne yake mawa kayan kyau,lol.
Haɗaɗɗen takalminsa sau ciki ƙiran kamfanin Gucci yasanya, aƙafansa, bayan ya ɗaura tsadadden agogon nan na Rolex a hanunsa mai kyau da burgewa. Daddaɗan ƙamshi ne kawai ke fita daga jikin shi, ƙamshine mai wahalar mantawa.
Black facing cap, yasanya akansa, domin kuwa yanayin garin ana ɗan busa sanyi, duk dakuwa cewa daga cikin sanyin yafito.
Wayarsa yaɗauka haɗe da car key ɗinsa, kai tsaye yafice daga cikin ɗakinnasa. Ɓangaren Mom ɗinsa yanufa. Hajiya Safara'u ne tsaye a gaban ƙatoton teburin cin abinci, yayinda Alhaji Ma'aruf ke zaune tana serving ɗinsa, batasan da shigowarsa ba saiji tayi ya rungumeta ta baya haɗe da ɗaura kansa akan kafaɗarta, cike da soyayyar mahaifiyarta sa yace "Barka da gida Momy!"
Cike da tsananin farinciki itama ta rungumesa haɗe da basa sumba a kan kumatunsa, "Barkanka da dawowa my son, ya gajiyar hanyar?"
"Alhmdlh!" Zaid yafaɗa a taƙaice, bayan ya janye jikinsa daga na mahaifiyartasa. Ƙoƙarin juyawa yakeyi, Mom tace "Inakuma zaka my son ba abinci kazo ciba?" cike da kulawa ta tambayesa.
Ɗan ɓata fuska Zaid yayi haɗe da cewa "Banajin yunwa Mom, idan nadawo zanci!" baijira jin maizasu ceba yasakai yafice daga cikin falon.
Da kallo kawai Mom tabisa har yafice, fuskarta ɗauke da damuwa, itakam ta rasa wani irin haline da Zaid, sam ba'a iya gane gabansa da bayansa.
"Miye abun shiga damuwa Hajiya Safara'u? zuwa yanzu yakamata ace duk wani hali na yaronnan Zaid kin gama saninsa!" Alhaji Ma'aruf yafaɗi hakan cike da nuna kulawa ga matar tasa.
"Nasan halinsa Alhaji, amma kuma ace mutum shi baya taɓa sanjawa, ko da yaushe fa Zaid bayason zama a cikin mu, sannan kuma sam baya sakewa damu!" Mom tafaɗi hakan cike da damuwa.
"Zauna muci abincin mu, aishi ba ƙaramin yaro bane, yasan me yakeyi!" Alhaji Ma'aruf yafaɗi hakan yana mai kama hanun Mom yazaunar da'ita a kusa dashi.
Zaid kuwa yana fita daga ɓangaren mahaifiyartasa, kai tsaye wajen motarsa yanufa, koda driver yanemi da yabarsa ya tuƙasa, ɗaga masa hanu yayi alamar baya buƙata, shida kansa yayimawa motar key, ya harbata zuwa kan titi.
Tafiya yake cikin nutsuwa yayinda airpiece ke saƙale a kunnuwansa, wayarsa ce tasoma ƙara alamar shigowar ƙira, ganin cewa babban manager'n company'nsa dake nan gida Nigeria ne ke ƙiransa yasanya shi ɗaga ƙiran. Banji mai Manager'n nasa yace masa ba, sai gani nayi ya'aje wayan, haɗe da buga dogon tsaki, lokaci ɗaya yakarkata akalar motar tasa zuwa wata hanya daban saɓanin hanayar daya nufa, wanda zai sadasa da unguwar su Zahrah.
Dr Sadeeq kuwa yana barin unguwar su Zahrah kaitsaye gidansu yanufa, acewarsa gwamma yayi maganin matsalarsa tunkafun tayi nisa.
Usaina mai aikin ɓangaren Hajiyarsa yasanya tane ma masa iso awajen Hajiyar tasa, domin kuwa bai isketa a falo ba.
Da sallama yashiga cikin ɗakin Hajiyar tasa, fuskarta ɗauke da fari'a ta amsa masa sallaman da yakeyi. Zaune take akan gado, yayinda take duba wasu kayayyaki dake zube a gabanta.
"Barka da huwatawa Hajiya!" yafaɗa cike da ladabi.
"Yauwa barkanka, kamar kuwa kasan ina nemanka, wai me kake nufi da auren nan ne Sadeeq? har yanzufa banga kana wani cuku cuku ba, kayan lefe ma saini kabarmawa ɗawainiyar haɗasu, gashi kuma Salima tacemin tunda kaje sau ɗaya baka sake zuwa ba, mai ke damunka ne wai?" Hajiya tatambayesa cike da kulawa.
Kansa yashiga sosawa haɗe da sake yin ƙasa da kansa, "Am...dama Am...." "Dakata banson wani kwana kwana, kafaɗi abunda zaka faɗa kai tsaye kawai" Hajiya ta katsesa daga kame kamen maganan dayake ƙoƙarin yi mata.
"Hajiya kamar dai yanda na faɗamiki ne, wallahi Hajiya dagaske nake, yanzu nasamu wacce nakeso kuma idan harkin yarda aurenmu bazai wuce nan da Sati uku ba, kamar yanda kikeso!" yafaɗi hakan cike da ladabi.
Sororo haka Hajiya ta tsaya tana kallonsa, "anya kuwa Sadeeq yana lafiya? " tatambayi kanta.
"Inagadai bakasan mekake cewa ba Sadeeq, wato nikakeson watsamawa ƙasa a cikin idanu ko, ya yi maka kyau, to inaso kabuɗe kunnuwanka da kyau ka saurareni, wallahi ko da wasa kakuma zuwamin da irin wannan zancen saina ɓata maka rai, nagama baka duk wata dama dazan baka, bakuma zan sake baka wata daman ba, tashi kabani waje, tunda nalura kai baka da tunani!" Hajiya ta ƙare maganan cikin faɗa.
Cikin rashin kuzari haɗe da sanyayewar guiwa Dr Sadeeq yamiƙe daga gaban mahaifiyartasa, haɗe da nufar ƙofar fita daga cikin ɗakin,
Saida yakai ɓaƙin ƙofar fita ckafun yatsaya cak, haɗe da juyo da kallonsa ga Hajiyar tasa cikin murya mai rauni yace "Hajiya dan Allah.."
"Fita kabani waje nace!!" Hajiya takuma faɗa cikin ɓacin rai tanamai yi masa nuni da ƙofar fita daga ɗakin...
*(Readers nifa Hajiyannan tasoma ban haushi yasin🙄🤣)*
*Kuyi manage da wannan ba lallai gobe nayi typing ba shiasa, namuku yau*
*11/December/2019*
*Voted, Comment, and Share please..... Follow me on Wattpad @fatymasardauna*
*6:17 pm*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
'''{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}'''
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
(Kuyi haƙuri shekaran jiya nayi mistake ɗin number 52 to 53 zansa, sainasaka 53 to 54🙏)
*CHAPTER 55 to 56*
Cikin sanyin jiki Dr Sadeeq yafita daga cikin ɗakin mahaifiyarta sa. Gaba ɗaya jiyayi zuciyarsa ta cika da ƙunci. Yana isa ɓangarensa ya zube akan ɗaya daga cikin kujerun falonnasa, "yanzu wazai je yasamu da wannan matsalar? tabbas yasan Hajiyarsa mutum ce mai kafiya, idan tace eh zai yi wuya ta dawo tace a'a"
hanunsa yasanya cikin sumar dake kwance akansa haɗe da yamutsa ta, sunan Aunty Raliya ce yafaɗo masa arai, tabbas ita kaɗaice ƴar uwarsa da zai kai mata matsalansa har ma ta tayasa magancewa, sai dai kuma yanatunanin itama ra'ayinta ɗayane da Hajiya, amma yasan idan yayi mata kyakkyawan bayani zata fahimcesa, zumbur yamiƙe daga zaunen dayake.
Ko bedroom baishiga ba yakuma ficewa daga cikin falon, mota ya koma, haɗe da kunnata, mai gadi ne ya wangale masa gate ɗin gidan yafice.
Hajiya najin ƙarar ficewar motarsa daga cikin gidan ta sauƙe ajiyar zuciya.
"Gaba ɗaya tunaninta ya kulle, batasan wani irin abu Sadeeq keshirin shigo mata dashi cikin gida ba, kusan sau uku kenan tana bashi dama, akan yafito da matar aure, amma dazaran lokacin da ta ibar masa yacika, sai ya farayi mata kame kame, yanzu da tagaji da sakarcinsa ta zaɓa masa mata, sai yake nema yawatsa mata ƙasa a idanu, bakuma zata lamunci hakanba.
Direct Dr Sadeeq gidan Aunty Raliya yanufa, domin baida wata ƴar uwa da ta wuce ta a duniyar nan.
Yanashiga gidan tunbai gama fitowa daga cikin motarsa ba, su Meenal da Affan ƴaƴan Aunty Raliya, suka rugo da gudu zuwa garesa, dama wasan ball suke a farfajiyan gidan nasu, hakan yasa duk wanda yashigo da kuma wanda zaifita zasu gansa.
Rungumesu yayi a jikinsa, haɗe da shafa kawunansu, "Oyoyo babies ɗina, ashe girma yazo muku, har wasan ball kukeyi!" yafaɗi hakan cike da nishaɗi.
"Eh Uncle ai harma nafita iyawa!" Affan yafaɗi haka cike da zumuɗi.
"Ƙaryayake Uncle baifini iyawa ba" Meenal tafaɗi hakan tana mai kama ƙugu, alaman ƙarya Affan ɗin yakeyi.
Murmushi kawai Dr yayi haɗe da sake shafa kansu, "kuyi wasa da kyau, idan nafito zan baku alewa!" yafaɗa yana mai nufar kofar da zata sadashi da babban falon gidan. Yayinda yabar su meenal sunata tsallen murna saboda yace zai basu alawa.
Da sallama ɗauke a bakinsa yashiga cikin falon.
Aunty Raliya dake zaune tana kallon tv, ta amsa amsa masa sallamar tasa, fuskarta ɗauke da fari'a, haɗe da yi masa iso.
Ƙarasowa yayi yazauna akan kujera, haɗe da sauƙe ajiyar zuciya, gaba ɗaya a gajiye yakejinsa, domin tun safe yau baisamu nutsuwa ya huta ba.
Aunty Raliya da kanta, ta jere masa kayan fruit da juice agabansa, cikin tsokana tace dashi
"Ango kasha ƙamshi, duk gajiyar shirye shiryen bikinne haka?"
Ɗan ɓata fuska yayi haɗe da ɗaukan apple ƙwaya ɗaya ya kai bakinsa.
"Ango labari ya sauya salo" yafaɗi hakan bayan ya cinye gutsuren apple ɗin dake bakinsa.
Cikin mamaki Aunty Raliya tace "bangane ba mekake nufi?"
Ajiyar zuciya yasauƙe haɗe da gyara zamansa.
"Akwai matsala Aunty!" yafaɗi hakan lokacin da gaba ɗaya yanayin fuskarsa ya sauya.
"Matsala! wace irin matsala Uncle?" Aunty Raliya tatambaya cike da ɗaurewar kai.
"Akwai wacce nakeso na aura, yarinyar tana matuƙar buƙatar taimakona, nayi ƙoƙarin na fahimtar da Hajiya hakan, amma taƙi saurarata, yanzu haka daga gida nake, nasoma yi mata bayani, tace natashi na bata waje, gaba ɗaya kaina yakulle bansan yazanyiba Aunty Raliya!"
Ya faɗi haka cikin damuwa.
Ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya Aunty Raliya ta sauƙe "Turƙashi, lallai kuwa kazo da babbar magana, amma maiyasa tunda baka bayyana wacce kake so ɗinba, sai yanzu da komai yariga da yayi nisa? kafasan Hajiya da kafiya balallai ne ta fahimce ka ba, shawarata a gareka shine, kamabar wannan zancen, domin balallai kasamu abun da kakeso ba!" Aunty Raliya tafaɗi hakan da'iyaka gaskiyarta.
Cike da rauni Dr Sadeeq ya kalli Yayartasa. "Dan Allah taimakona zakiyi Aunty, kije kisameta kibata baki, wallahi inamatuƙar son Zahrah, sannan kuma yarinyar tana buƙatar kulawata, nikaɗai nasan matsalarta, please Aunty!!" yafaɗi haka yana me marairaice fuska, hadda haɗa hannuwansa biyu ga Aunty Raliya'n alamar roƙo.
Kallon mamaki Aunty Raliya tashiga binsa dashi, "wai yaushe Sadeeq yazama bawan soyayya ne?" ta tambayi kanta.
"Abune me matuƙar wuya amincewar Hajiya, amma zan jarraba, saidai kafun naje gareta, dole sainasan wacece yarinyar kuma su waye iyayenta, saboda kada aje Hajiya ta amince, akuma zo asamu wani mummunan labari akan ta"
Wani irin bugawa ƙirjin Dr Sadeeq yayi, domin kuwa anzo wajen, lallai baizama dole kowa yafahimcesa ba domin sanin sirrin Zahrah, zai iya sanyawa kowama yaƙi amincewa da aurensa da'ita, wanda shi a wajensa baiga ta'inda aurensu zai zamanto rashin dacewa ba, amma ba'a ƴar ɓoye a harkan aure, domin koda anɓoye tofa sai ya bayyana.
"Sunanta Zahrah, a unguwar Maraba take, sannan kuma marainiyace bata da uwa bata da uba, baffanta ne yake riƙonta, yarinyar tana da hankali sosai Aunty, sannan kuma tana da tarbiya, bata da wani aibu ko abun kushewa a tattare da'ita, saidai kuma..." kasa ƙarasa maganar yayi, domin kuwa baisan yanda yayartasa zata ɗauki maganar ba.
"Umm inajinka saidai kuma me?" Aunty Raliya tatambayesa cike da zaƙuwa.
"Ƙaddarace kuma tana kan kowa, haka kuma babu wanda ya'isa ya tsallake mata idan har tafaɗo kansa, akwai wani tsohon saurayinta da ya yaudareta yayi mata fyaɗe, watannin baya da suka wuce, wanda hakanne ma sanadin haɗuwata da'ita, amma ni banɗauki hakan amatsayin wani abu ba dazai hanani aurenta, kasancewar kowa da'irin tasa ƙaddaran a rayuwa!"
Sororo haka Aunty Raliya ta hangame ido da baki tana kallon Dr Sadeeq har ya idar da zancensa mai kama da tatsuniya.
Salati Aunty Raliya tasanya cike da tsantsar mamaki haɗi da al'ajabi, lallai Sadeeq baisan meyake faɗa ba.
"Fyaɗe! fyaɗe fa kace Sadeeq, anya kuwa kansan mekake faɗa? yanzu kai saboda rashin hankali irin naka, karasa wacce zaka gani kace kanaso, sai yarinyar da taraba budurcinta wa ƙattin maza, yarinyar da wani yagama sanin sirrinta!" Aunty Raliya ta faɗi haka cike da ɓacin rai.
Saurin rumtse idanunsa yayi domin jin magananganun Aunty Raliya'n yake tamkar sauƙan aradu, a kunnuwansa.
Cigaba tayi da cewa " Lallai yanzu na tabbatar dacewa ba lafiyanka lau ba, taya kana cikekken namiji mai hankali da kuma kamala, karasa wacce zaka aminta da ta zamo uwar ƴaƴanka sai wacce wani ƙato ya haiƙemawa, yazama dole kasanja tunani Sadeeq, wannan ma ai zancen banzane, to gwarama kasani wannan yarinyar ba zaka taɓa aurenta ba matuƙar mu jininka ne!" Aunty Raliya ta ƙare maganar cikin hargowa.
"Haba Aunty maikikeson cewa ne? dan Allah kada kimin haka, nafaɗamiki matsalatane don bani da wacce tafiyemin ke, dama nasan za'a samu rashin fahimta, domin zakuga kamar Zahrah ba kamemmiyar mace bace, alhalin kuma bahaka take ba, tsautsayine yafaɗa mata, amma ni nayarda na amince zan aureta a haka, kada fa kimanta duk wanda yarufa asirin wani to Allah zai rufa masa nasa asirin, kitaimaka mu inganta rayuwar Zahrah, kitaimaka mucireta daga ƙunci, musanyata cikin farinciki!" yafaɗi haka cike da rauni.
Wani irin kallo Aunty Raliya tashiga yimasa, lallai Sadeeq baya cikin hankalinsa.
Murmushi mai ciwo Aunty Raliya tayi haɗe da cize laɓɓanta cikin takaici ta ce dashi.
"Kuskurenka na farko a rayuwa shine yarda dakayi cewa da gaske fyaɗe aka mata, shin ka ko san ƴan matan yanzu kuwa Sadeeq? to bari kaji wani abu, a shegen son kuɗi irin na ƴan matan yanzu, su da kansu suke saida budurcinsu ga wani daban, idan suka samu makahon da'idanunsa ya rufe ruf har yazo musu da zancen aure, sai su taƙarƙare su zabgamasa ƙarya kan cewa fyaɗe akamusu, bayan suda kansu suka kasa budurcin nasu a faifayi suka kai tallanshi kasuwa, ni ƴar uwarka ce ta jini bazan taɓa son wani abun da zai cutar da kai ba, saboda haka tun muna mubiyu nidakai, mubunne maganarnan anan, tun kafun ma yaje ga kunnen Hajiya, domin kasan idan taji cewa wacce kake shirin kawo mata ita amatsayin suruka, ba mutumiyar ƙwarai bace to zatayi mugun saɓa maka!!"
Take idanun Dr Sadeeq suka kaɗa sukayi ja, bakomaine ya sanya hakan ba face irin munanan kalaman da Aunty Raliya ta dinga jifan Zahrah dashi, tabbas yasan cewa mafi ƴawancin ƴan matan yanzu suna sayarda budurcinsu saboda abun duniya, amma banda Zahrah'nsa aciki, yasan Zahrah macece mai kamun kai, kuma duk wanda yayarda da ƙaddara dole ne ya tausayawa mata masu tsintar kansu a irin halin da Zahrah ta tsinci kanta a ciki.
"Ita bakamar yanda kike tunani bane Aunty Raliya, ki saurareni saina baki gaba ɗaya labarinta, marainiyace ta cancanci a tausaya mata, nima Namiji na tausaya mata balle ke mace, kuma dama ance ciwon ƴa mace na ƴa mace ne!" Dr yafaɗi hakan cike da son ganar da Yayarta sa, cewa ba bu wani aibu agame da aurensa da Zahrah.
Gaba ɗaya duk iya abun da yasani agame da Zahrah, bai ɓoye mata ba, sai da yasanar mata, atunaninsa hakan zai sanya Aunty Raliya ta ƙaunaci Zahrah, amma me sai gani yayi tana taɓe baki haɗe da kawar da kanta gefe alamar ma ta'inda maganar tasa take shiga tanan take fita.
Yana idar da zancen ta dubeshi haɗe da ɓata fuska tace "Kagama? kai a tunaninka zaka bani wata hujja dazata sanya naga dacewar aurenka da'ita ne, hmm niba yarinya bace Sadeeq, yakuma zama dole kasanja tunani, kakuma manta da maganar wata wai ita Zahrah, idan kuma kafison kafuskanci ɓacin rai daga wajen Hajiya, to kaci gaba da zama akan bakan ka harmaganan takai ga kunnen Hajiya!!" tanakaiwa nan a zancenta ta miƙe fuuu tawuce cikin ɗakinta tabarshi zaune.
Hannayensa yasanya duka biyu ya tallafi kansa, lallai akwai babban ƙalubale a gareshi, agun Aunty Raliya ma kaɗai ga'irin ɓacin ran daya fuskanta, inaga Hajiyarsa kuma.?
Miƙewa yayi daga zaunen da yake tamkar wanda ƙwai ya fashewa a jiki haka yake tafiya, gaba ɗaya ƙwaƙwalwarsa tasake dagulewa, yazone don yasamu mafita amma sai gashi abubuwa sun sake dagulewa.
Da ƙyar yake iya tuƙa motar tasa. Haka yanufi gida cikin rashin kuzari, sai dai fa haryanzu bai saduda da maganar Auren Zahrah ba, yanaji ajikinsa cewa Zahrah zata zamo matarsa Insha Allah.
Gagarumin meeting su ZAID suka gudanar mai zafi, a babban hotel ɗin nan wato SHERATON, sosai aka samu riba dakuma ƙarin buɗi a ɗaya daga cikin company'n nasa da suke Nigeria, hakan yasa yaƙarawa gaba ɗaƴa ma'akatansa albashi.
Sunjima suna meeting ɗin dan haka amatuƙar gajiye suka fito dukansu, lokacin har dare yasoma rufawa. Kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa, yayi yaga karfe 6 daidai na yammaci, ɗan ƙaramin tsuka yayi haɗe da soma yunƙurin cire rigan suit ɗin jikinsa wada yaɗaura akan kayan dake jikinsa,
saboda gajiyan da yayi bai iya tuƙi da kansa ba, sai driver'nsa yaƙira yayi driving ɗinsa.
Gyara kwanciyansa yayi ajikin kujeran motar haɗe da lumshe idanunsa, wani irin sarawa kansa keyi masa, daga wani ɓangare na zuciyarsa kuwa sosai meeting ɗinnan ya ɓata masa rai, domin kuwa ya hanasa ƙarasawa ga ZAHRAH'nsa, wacce saboda itane ma gaba ki ɗaya yadawo ƙasar, yayi missing din Zahrah sosai, yayi missing kyakkyawan murmushinta haɗi da kyawawan idanunta, yayi missing kallon kyawawan laɓɓanta masu daɗin tsotso. Gaskiya dole ya killace Zahrah tayanda zata zama nasa shi kaɗai.
Suna isa gida kai tsaye ɓangarensa ya wuce, a gajiye yashiga bathroom yayi wanka, koda yafito a wankan, direct masallaci ya wuce donyin sallan magriba. Sai da yajira aka yi sallan isha tare dashi a masallaci, kafun ya siɗaɗo yadawo ɗaki ya kwanta, yau ko abar ƙaunar tasa wato wine baisha ba bacci ɓarawo yayi gaba dashi.
Zahrah ce kwance akan katifarta sai juyi take ta kasa bacci, gaba ɗaya kanta ya kulle zuciyarta cike take da tarin tunanuka kala kala. "Anya banyi sauri kokuma gangancin yarda da kuma amincewa da soyayyar Dr da nayi ba?" zuciyarta ta tambayeta.
Zumbur haka ta miƙe zaune, haɗe da soma girgiza kanta
" A'a banyi kuskure ba, tabbas bayan shi babu wani maiso da nuna tausayi gareni!" tabawa kanta amsa a bayyane.
Wayartace takawo haske alamar shigowar ƙira, kasancewar ta sanya wayar a silent hakan yasanya wayar batayi ƙaraba.
"Doctor" shine sunan dake yawo akan screen ɗin wayar.
"Shima baiyi bacci ba kenan" tafaɗi hakan a bayyane.
Saida wayar ta kusa katsewa kafun Zahrah ta ɗaga ƙiran haɗe da kara wayan akan kunnenta.
"My princess bakiyi bacci ba kenan?" Dr Sadeeq yatambayeta cikin muryarsa mai ɗauke da damuwa.
"Um, kaifa me yahanaka bacci" Zahrah itama tatambayeshi.
"So da ƙauna dakuma tunaninki susuka hanani bacci! kefa mai yahanaki bacci?" yatambaya cike da son jin amsar da zata fito daga bakinta, "Allah yasa itama tunani na ne ya hanata bacci" yafaɗi hakan a zuciyarsa.
Kunyane yaɗan kamata amma sai ta basar haɗe da sauƙe ajiyar zuciya "A'a nikam karatu nake, shiyasanya banyi bacci ba, amma yanzuma zanyi baccin." tafaɗi hakan a taƙaice.
Ko kaɗan baiji daɗin amsar da ta basa ba, amma yasan cewa wataran dole zatayi tunaninsa kamar yanda shima yake nata tunanin.
"Naji daɗi sosai da kika amince dani Zahrah na! hakan yasa na ƙara jin sonki sosai da sosai a cikin zuciyata!!" cikin shauƙin so yafaɗi maganar.
"Umm banji mai ka faɗa ba!" Zahrah tafaɗi hakan cikin wani irin salo wanda batasan ma tayi shi ba, duk da kuwa cewa taji mai yace, iskancine kawai irin nata.
Lumshe idanunsa yayi da suka soma sauya kala, sosai yanayin yanda tayi maganar ya sauƙar masa da kasala.
"Bacci kika farane Zahrah na?" yatambayeta cike da kulawa, domin kuwa shi anasa zaton dagaske batajisa ba.
"Um!" Zahrah ta basa amsa a taƙaice cikin ƙasa ƙasa da murya, domin kuwa tanaso yayarda cewa baccin takeji, saboda har yanzu, bata gama amanna dacewa sonsa take ba, kuma koda za'a kasheta tasan cewa ba sonsa take ba, kawai dai ta tsinci kantane da amince masa, amma batun soyayya kam babu shi.
"To kiyi bacci mai daɗi kinji My princess, inasonki sosai, ki kulamin da kanki, banson koda ɗigon wani a bune ya raɓe ki!" Dr ya faɗi haka cikin shauƙin SO (Sisters kujisafa su likita ashe an iya kalaman love, lol.)
"Uhumm sai da safe." Zahrah tafaɗa a taƙaice bayan ta zare wayar daga kunnenta.
"Gaskiya abune mai matuƙar wahala koyawa zuciya So'n abun da bata so, ya Allah kataimakeni, haƙiƙa banajin tsanarsa haka kuma banajin soyayyarsa a zuciyata, sannan kuma inaji ajikina cewa zan'iya rayuwa dashi, to me hakan ke nufi, ba so bane kuma ba ƙi bane to menene?" tatambayi kanta a bayya ne, saidai kuma bata da amsar da zata bawa kanta.
Komawa tayi ta kwanta bayan ta kashe wayarta ta gaba ɗaya.
Cike da saƙe saƙe bacci yayi awungaba da ita.
Ɓangaren Dr Sadeeq ma, sai da yajima yana saƙawa da kuncewa, ba abun da yake ɗaure masa kai, kamar yanda ya kasa fahimtar cewa Zahrah, na son sane ko bata sonsa. da ƙyar dai shima bacci ya'iya ɗaukarsa.
Washe Gari.
Yau tun saven thirty suke da lecture, dan haka da wuri tasoma shirya kanta, sosai tayi kyau cikin shigar jar abaya haɗe da jan hijab ɗin dake jikinta, hand bag ɗinta ta rayata a bisa kafaɗanta. Kana tafice zuwa tsakar gida. Zama tayi akan taburma haɗe da jawo farantin ƙosai da kuma kofin kunun da Inna ta aje mata tasoma sha. Baffa ne yafito daga cikin ɗakin sa yanaganin Zahrah yace
"Yauwa kinfito ko, tun ɗazu kuwa likita yake jiranki a waje"
"Eh Baffa nafito" tabashi amsa cike da mamakin jin cewa wai Dr yajima da zuwa, yanama jiranta a waje, amma kuma bai ƙira ta a waya yasanar mata ba.
Aƙagauce taci abincin kasancewar har bakwai tayi.
Tana fitowa yasakar mata kyakkyawan murmushi, itama murmushin ta sakarmasa bayan tagama ƙaremawa kwalliyarsa ta yau kallo.
"Kinyi kyau my princess!" yafaɗa cike da nishaɗi, domin kuwa sosai tayi masa kyau, jan kayan da tasa ya karɓi kalan fatarta.
"Kaima haka" tabashi amsa a taƙaice.
Murmushi yakumayi haɗe da buɗe mata murfin motar nuni yayi mata da hanunsa alamar tashiga, wani murmushi mai tsayawa a zuciya tayi masa haɗe da shigewa cikin motar tayi mawa kanta mazauni.
Tafe suke suna hira cike da nishaɗi, wanda gaba ɗaya yawan hiran Dr ne maiyi mata shi.
A haka har suka iso cikin makarantar, ƙoƙarin buɗe murfin motar ta soma yi.
"Ya haka? baki sallameni ba fa, kike ƙoƙarin tafiya" Dr Sadeeq yafaɗi hakan cikin sigar zolaya.
Murmushi Zahrah tayi masa haɗe da yin fari da'idanunta "Bangane ba" tafaɗi haka cikin salo.
Lumshe idanunsa yayi haɗe da sanya hanu yashafi sajensa, "Inanufin bakice kina sona ba"
Dariya haɗe da kunyane suka kama Zahrah sai kawai ta buɗe murfin motar tayi ficewarta, domin kuwa bazata iya masa abun da yakeso ba.
Saida yaga shigewarta cikin hall kafun yaɗauke idanunsa daga kanta, yanason mace mai kunya gashi Zahrah takasance me kunya. Cike da tarin tunaninta yabar cikin makarantar.
Ita da Husnah suna fitowa a lecture sukayi mawa kansu ma zauni a inda suka saba zama ko da yaushe.
Cike da tsananin farinciki Husnah tace "Naji daɗi ƙwarai Zahrah da kika amincewa Dr, wallahi gayen ya haɗu da yawa ƙawata, tabbas idan kika auresa kin more don nasan za kisha madaran soyayya!"
Hararan wasa Zahrah ta wurgamawa Husnah, cike da son basar da zancen tashiga shafa cikin ta " Nifa yunwa nakeji" tafaɗa tana mai turo baki gaba.
"Kada dai kice zakimin sakalci, domin niba Doctor bane" Husnah tafaɗa cikin tsokana. dukan wasa Zahrah takai mawa Husnah, da sauri Husnah ta kauce.
Cafeteria suka nufa acan suka cika cikinsu, daganan suka sake shiga cikin wani lecture'n.
Jikin wata bishiya dake kusa da ƙofar fita daga makarantar yayi parking motar sa, gyara zama yayi haɗe da duba agogon dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa. Kallonsa ya mayar zuwa bakin tangamemen gate ɗin makarantar tasu, hakanan yakejin ba zai iya fuskantar ta gaba da gaba ba.
Amatuƙar gajiye su Zahrah suka fito a lecture. Tare suke tafe ita da Husnah, domin yau zataimawa Husnah rakiya ne zuwa super market. kai tsaye suka nufi ƙofar fita daga makarantar kasancewa driver'n gidansu Husnah najiransu a waje.
Wani irin faɗuwar gaba taji, ya risketa adai dai lokacin da ta fito daga cikin makarantar.
Daga ɓanagaren Zaid kuwa zuciyarsa ne tashiga dukan uku uku, alokacin da'idanunsa suka sauƙa akan Zahrah, hanu yasa ya murje idanunsa domin tabbatarwa da kansa cewa ita ɗince kokuwa gizo idanunsa suke masa.
Tabbas itaɗince Zahrah'n sane, har yanzu tananan da kyawunta, dakuma surarta mai ɗaukar hankalin duk wani lafiyayyen ɗa Namiji.
"ZAHRAH!" yaƙira sunanta a bayyane, duk da kuwa yasan cewa bazata ji sa ba. dai dai lokacin daya soma yunƙurin buɗe murfin motarsa don yaƙarasa gareta, dai dai lokacin itakuma ta shige cikin mota tare da Husnah.
*13/December/2019*
*Voted, Comment, and Share please.... Follow me on Wattpad @fatymasardauna
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated to My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
___________________
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 57 to 58*
Cikin Hanzari ya buɗe murfin motar tasa ya fito, sai dai baikai ga ƙarasawa garesu ba, motar su ta gangara kan titi haɗe da ɗaukar hanya.
Hannayensa duka biyu yasanya ya kama ƙugunsa, haɗe da furzar da iskan numfashi ta bakinsa, sam baiso haka ba, amma babu yanda ya'iya dole binsu zaiyi.
Kallonsa yamaida ga sauran cincirindon ɗaliban da suke tsaye a bakin gate ɗin makarantar.
Gani yayi gaba ɗaya sun saki baki da hanci suna kallonsa, sai kace wanda suka ga baƙon halitta, bama kamar ƴan matan dake tsaye a wajen.
Tsuka mai sauti yayi haɗe da komawa cikin motarsa, da gudun gaske ya cilla motar tasa kan titi, haɗe da rufa mawa motar su Zahrah baya.
"Yadai, naga lokaci ɗaya duk kinyi wata iri dake?" Husnah tatambayi Zahrah wacce tazama silently lokaci ɗaya.
A jiyar zuciya ta sauƙe haɗe da maida kallonta ga Husnah " Faɗuwar gaba nakeji Husnah, ban kuma san dalilin hakan ba" Zahrah ta faɗi haka cikin damuwa.
"To fa, Allah dai ya tsare, amma ki yawanta addu'a, domin hakanne zaisa koma mene ne yazo da sauƙi" inji cewar Husnah.
"Insha Allah!" Zahrah tafaɗi hakan tana mai kwantar da kanta a jikin kujeran motar, tanajin Husnah tace da Driver'n ya karkata akalar motar, ta sanja shawara shoprite kawai zasuje, bamusu kuwa ya sanja hanya zuwa Shoprite ɗin. Itadai Zahrah batace dasu komai ba.
Basu wani jima suna tafiya ba, suka iso tangamemen Shoprite ɗin. "Muje ko" Husnah tace da Zahrah tana mai ƙoƙarin buɗe murfin motar.
Cikin sanyin jiki Zahrah, tafito daga cikin motar suka nufi cikin shoprite ɗin.
Basket biyu Husnah ta ɗauka nata ɗaya na Zahrah ma ɗaya, acewarta Zahrah ta zaɓi duk wani abun da take so, sam bahaka Zahrah tasoba amma babu yanda ta'iya, domin kuwa Husnah kafiya gareta, idan tace kayi abu tofa wai dole sai kayi.
Kayan shafa suka soma ɗauka, kafun suka garzaya zuwa kan su jaka da takalma ƴan yayi, basu tsaya anan ba hadda kayan ciye ciye sai da suka ɗauka.
Cike da gajiyawa Zahrah ke tura Basket ɗin da kayanta ke ciki, ita mamaki ma take yanda Husnah tasa suka jidi kaya mai yawa har haka, amma idan tayi la'akari da irin gata da kuma kuɗin da mahaifin Husnah ke dashi, to sai tagama ba wani abun mamaki bane, kuma kuɗin kayan bazai mawa Husnah wahalar biya ba, domin kuwa anshagwaɓata sosai agida.
Daki daki aka lissafa kayan nasu, inda Zahrah ta ɗauki kayan dubu ishirin Husnah kuwa na dubu ishirin da biyar ta eba, ƙoƙarin miƙa wa Cashier ATM card ɗin dake hanunta Husnah ta soma yi. Amma sai Cashier'n yayi murmushi haɗe da cewa
"Ai Hajiya ba'a buƙatar kuɗin ku, domin kuwa an riga da an biya muku, tunkafun ku kammala sayayyan, sannan wanda yabiya muku yace idan ma kuna da buƙatar ƙari, to kukoma ku ƙara, duk shi zai biya kuɗin"
Cike da mamaki Zahrah da Husnah suka shiga kallon juna.
"Anbiyamana fa kace Cashier? shin ka kosan me kake cewa?" Husnah tatambayeshi cike da mamaki.
"Ƙwarai kuwa nasan me nake cewa, kudai ku ɗau kayanku kawai kuje, sannan ku gode mawa Allah, don shi yaje fo muku tsuntsu daga sama gasashshe " Cashier'n nan yafaɗi haka yana mai washe baki, kasan cewar shima anbarmasa kyautan ragowan canjin su.
Mamakine ya lulluɓe su Zahrah domin su a iyaka sanin su basu da wani wanda zai biya musu kuɗin siyayyan da sukayi, domin kuwa basu zo da kowa ba banda driver, inakuwa driver zaisamu maƙudan kuɗaɗe irin haka har ya biya musu kuɗin siyayya alhali shima yana fama da kansa.
"Kozaka iya faɗamana wanda ya biya mana kuɗin ?" Husnah ta tambaya.
"A gaskia bansan saba, sai dai da duk kan alamu irin larabawan nan ne da suke zuwa Nigeria lokaci zuwa lokaci" Cashier ɗin nan yafaɗa musu haka, domin shi a yanda yafahimta, da dukkan alamu wanda.yabiya musu kuɗin baiyi zubi da ƴan nan gida Nigeria ba, duk da kuwa cewa muma muna da kyawawan maza amma kuma kyawun wani ya ɗare na wani.
Idanu Zahrah da Husnah suka zaro atare, sakamakon jin abun da Cashier yace.
"Balarabe fa kace?" Husnah ta sake tambaya cike da mamaki.
"Eh Balarabe, kece Zahrah ko?" Cashier'n nan ya tambaya yana mai nuna Zahrah da hanunsa.
"Ya'akayi kasan sunana ?" Zahrah ta tambayesa cike da mamaki.
Murmushi kawai yayi haɗe da miƙa mata wata farar takarda.
"Ungo yace inbaki"
Cikin tsoro Zahrah ta karɓi takardan da Cashier ke miƙo mata, haɗe da buɗewa.
_"Kiɗauki duk wani abun da kikeso MY ZAHRAH! ban damuba koda duka Shoprite ɗin zaki ce kinaso, zan iya mallaka miki kome kikeso a duniyar nan, ko da kuwa dukiyata zata ƙare"_ abun da aka rubuta a jikin takardan kenan.
Wani irin bugawa Zahrah taji ƙirjinta yayi, "To waye?" tatambayi kanta a fili.
"Yadai me aka rubuta acikin takarda'n?" Husnah ta tambayi Zahrah cike da zaƙuwa.
Bata takarda'n Zahrah tayi domin batasan me zatace da'ita ba.
Husnah tana gama karanta takarda'n tasaki murmushi haɗe da kallon Cashier'n nan daya zura musu idanu... "Mungode sosai, idan ka haɗu da wanda yabiyamana kuɗin, ka isar mana da saƙon godiya" daga haka ta kama hanun Zahrah suka fice daga cikin Shoprite ɗin, bayan sun ɗau ledodin siyayyarsu.
"Saida sukazo bakin mota kafun Husnah ta saki hanun Zahrah, still fuskarta ɗauke da murmushi tace "Mekika fahimta game da wannan takardan, da kuma biya mana kuɗin sayayya da akayi?"
Cikin ɗaurewar kai Zahrah tace "Ni ban fahimci komai ba, sai ma tsananin mamaki da nake, taya haka zata kasance, anya kuwa ba wata maƙarƙashiyan ake shirin ƙulla mana ba Husnah?"
Dariya sosai Husnah ta kwashe dashi, domin kuwa maganar Zahrah takai a dara.
"Maƙarƙashiyan soyayya ba, babu wani aljanu, kawai dai inaga wani ne yaganki kuma ya yaba, shine kawai" Husnah tafaɗa tana mai danne dariyanta.
"Bangane ba me kike nufi?" Zahrah ta tambaya cike da ruɗu, domin ita kwata kwata ma bata fahimci inda kalaman Husnah suka dosa ba.
"Kada ki damu zaki gane mushiga mota"
Jiki a sanyaye Zahrah tabuɗe murfin motar tashiga, a gidan baya sukai mawa kansu masauƙi ita da Husnah..
Suna shiga driver yayi mawa motar key suka ɗauki hanyar Suleja unguwar su Zahrah.
(yauwa kuyi haƙuri jiya nayi mistake sunan unguwar su Zahrah ba Maraba bane, sunan unguwarsu Zahrah Suleja ne, kainane ya ɗau charge shiyasa)
Yanaganin tafiyarsu yasaki ƙawataccen murmushinsa, "Haryanzu tananan da halinta na tsoro, yayi imani Zahrah bazata taɓa sanjawa ba"
" komai naki yana burgeni Zahrah, inason komai naki!" Zaid dake cikin motarsa yafaɗi haka cike da shauƙi.
"Nifa gaba ɗaya kaina ya kulle, kimin bayani mana Husnah, me takardan nan take nufi ne?" Zahrah tafaɗi haka cikin zaƙuwa.
"Ki kwantar da hankalinki ƙawata, kawai dai bazai wuce irin mutanen nan masu alkhairi bane suka aikata hakan, wayasani ma ko Dr Sadeeq ne" Husnah tafaɗi hakan tana mai kallon Zahrah.
"Mene? kinanufin wai Doctor ne zaiyi haka? gaskiya banjin cewa shi ne, domin idan da shi ne, dole zai bayyana kansa na gansa, kodai ke akeso amawa wannan hidiman akayi mistake aka ambaceni" Zahrah tafaɗi haka cikin kokonto.
Dariya Husnah takuma sawa, haɗe da dafa kafaɗan Zahrah..
"Wai lafiyanki kuwa Zahrah? kinga yanda kika firgice lokaci ɗaya sai kace wacce ta aikata aikin rashin gaskiya, to ni miye ma abun damuwa ne don wani yabiyamana kuɗin sayayya? kinga bafa mu muka sa sa ba, ko ma waye shi yasanya kansa, kishare kawai ƙawata" Husnah taƙare maganar ta ta bayan ta ɓare sweet ta jefa acikin bakinta.
"Hmmm" kawai Zahrah ta'iya cewa, haɗe da mai da kanta jikin kujera, itakam gaba ɗaya kanta ya kulle, taya za'ace bakasan mutum ba, amma kuma ya biyamaka kuɗin siyayyan da kayi, irin haka ne mutum sai yaje ya jefa kansa a matsala.
Tafiya suke amma Zahrah ta kasa cewa komai, sai ma Husnah ce keta ƙoƙarin janta da hira, amma jefi jefi take amsa mata, domin kuwa wannan faɗuwar gaban da takeji har yanzu baidaina ba.
A haka har suka iso ƙofar gidan su Zahrah'n... Har cikin gida Husnah tayimawa Zahrah rakiya, kana ta fito tashiga mota suka tafi.
Zama tayi akan katifarta haɗe da zubawa kayan siyayya da sukayi ido, sam zuciyarta bata kwanta da wanda yabiya musu kuɗin kayan ba, zuwa yanzu ya kamata ace tayi hankali, domin sarai yanzu tasan salon yaudaran maza baida ƙarshe, suna iya yimaka komai don su samu biyan buƙatarsu, wannan yana ɗaya daga cikin babban dalilin da yasanya ta amince da auren Dr Sadeeq, ko ba komai idan ya aureta ta tsallake wani babban siraɗi na daga yaudaran da Maza sukeyi mawa ƴan mata a wannan zamanin.
Ƙaran wayartane yakatseta daga tunanin da takeyi, cikin sanyin jiki ta ɗaga ƙiran nasa, haɗe da kara wayar akan kunnen ta.
"Barkanki da hutawa My Princess!"
Dr Sadeeq yafaɗa cike da tsantsar kulawa.
Ɗan guntun murmushi tayi haɗe da cewa "Kaima barkanka dai ya aiki?"
Ɓata fuska yayi tamkar dai tana ganinsa haɗe da cewa "Aiki ba daɗi kokaɗan, ya kundawo a super market ɗin kenan?"
"Eh" tabashi amsa a taƙaice. Domin tsabar gajiyan da ta kwaso har wani bacci bacci takeji.
"Naga kamar kingaji da yawa, ki samu ki ɗan huta, zuwa anjima zanzo gida, inaso na samu Baffa, idan yabani dama zanturo magabata na ayi maganar auren mu, domin banso akai nanda wata ɗaya ban mallakeki ba!" yaƙare maganar cikin yanayin shauƙi.
Wani irin bugawa taji zuciyarta tayi, sakamakon jin abun da Dr Sadeeq yace. Wani irin yanayi ta tsinci kanta ciki, wanda baza'a ƙirasa da farinciki ba, ba kuma za'a ƙirasa da yanayin baƙin ciki ba.
"Zahrah na!" yaƙira sunanta jin cewa tayi shiru batace dashi komai ba.
"Umm" ta'amsa masa a kasalance.
"Naji kinyi shiru, ko dai bakiyi farinciki da hakan bane?"
Yajefo mata tambayar da batayi zaton zai mata shi a yanzu ba..
"A'a nayi farinciki mana, kawai dai kainane ke ɗan min ciwo" tafaɗi haka don ta kare kanta, gudun kada yafuskanci wani abu.
"Ayya kiyi haƙuri, anjima idan zanzo zan tahomiki da magani ko, yanzu ki kwanta ki huta, nasan ma stress ne, insha Allah zuwa anjima zaki ji ki normal" yafaɗi hakan cike da kulawa.
"To" kawai ta'iya cewa dashi, haɗi da zare wayar akan kunnen ta.
Nannauyar ajiyar zuciya ta sauƙe, haɗe da share ruwan hawayen da suka fito daga cikin idanunta. "Yazama dole nakoyi soyayyarka Dr Sadeeq, domin bayan kai babu wani wanda zai bani kulawa kamar haka, ya Allah kamin maganin matsalolina!" tafaɗi hakan a bayyane, bayan ta ɗaga idanunta zuwa sama.
Da ƙƴar ma ta'iya cusa abincin da Inna ta bata, domin kuwa hakanan taji zuciyarta ta cunkushe.
Kwanciya tayi akan katifarta tana ƴan tunani, take bacci ɓarawo ya siɗaɗo ya ɗauketa, batare da tashiryawa hakan ba....
Zaune yake akan wata haɗaɗɗiyar kujera, wanda take ita kaɗaice kuma na mussaman acikin bedroom ɗinsa, dake cikin guest hause nashi. ɗan ƙaramin table ne aje a gabansa, wanda samansa ke ɗauke da zungureriyar kwalbar wine da kuma glass cup.
Wayar sace riƙe a hanunsa, gaba ɗaya hankalinsa akan wayartasa yake, murmushine ɗauke akan fuskarsa, yayinda yake playback ɗin vedi'on daya mata ɗazu fitowarta daga cikin shoprite, batare da ta sani ba.
Harzuwa yanzu bai tantance mai yakeji a jiki da zuciyarsa ba a game da Zahrah, abu ɗaya yasani shine, yasan cewa "yana matuƙar buƙatarta a kusa dashi, fiye da tunanin mai tunani, yakuma ɗauki haka, amatsayin fitinanniyar sha'awarta da yake" sake playback ɗin vedion yayi bayan yakai ƙarshe akaro na barkatai domin kuwa yayi playback ɗin vedi'on yafi sau goma daga zamansa a wajen zuwa yanzu.
Wani irin sanyi haɗe da kewarta ne suke ratsa zuciyarsa alokaci guda.
"A hankali zankuma cimma burina akanki Zahrah, akaro na biyu ma ina da tabbacin cewa zanyi nasara akan ki, domin niban kasance Loser ba, bakuma zantaɓa kasancewa Loser ba, har abada !" yafaɗi haka cike da son ƙarfafamawa kansa guiwa.. A taƙaice dai haka Zaid yayita playback na vedio ɗin da yayi mawa Zahrah yana kallo, zuciyarsa cike da nishaɗi, abu ɗayane zai hanasa zuwa gareta a yanzu, shine plan ɗin daya shirya mata, bakuma zai je gareta ba, harsai ya tabbatar da cewa ta gama rufzawa cikin tarkonsa, da ya ɗana mata a karo na biyu....
(😲)
Doctor Sadeeq ne tsugune a gaban Baffa Amadu, wato ƙanin mahaifinsa. Bayan ya gama kora masa bayanin duk abun dake faruwa, hatta fƴaɗe'n da akayimawa Zahrah bai ɓoye masa ba, domin kuwa a yanzu Baffa Amadu shine Uba a garesu, kasancewarsa ƙanin mahaifi'nsu.
Ajiyar zuciya Baffa Amadu yasauƙe, haɗe dayin gyaran murya irin tasu ta manya...
"Haƙiƙa kazo da babbar magana Sadeeq, amma kuma duk na fahimceka, bakuma zanyi ƙasa a guiwa ba wajen ganar da mahaifiyarka dakuma ƴar uwarka, amma kuma kasan dole sai an haɗa da haƙuri, kasan su mata koda yaushe tunaninsu baya zurfafa, bakuma ko da yaushe suke gane abun da ake so su fahimta ba, amma tunda kakawo matsalan nan wajena, ka kwantar da hankalinka, ni nan zanje har gida na samu mahaifiyartaka, zamu tattauna akan matsalan!"
Wani irin sanyin daɗi ne yashiga huda zuciyar Dr Sadeeq, sai yanzu yakejin nutsuwa na sauƙar masa, yanzu fatan sa ɗaya, shine Allah yasa mahaifiyarsa ta amince, amma tabbas Zahrah itace burin ran sa...
Daga haka sukayi sallama da Baffa Amadu, bayan ya tabbatar masa cewa lallai zaice yasamu mahaifiyartasa da batun...
Cike da farinciki Dr Sadeeq yabaro gidan Baffan nasa, kai tsaye gidansu ya nufa....
Zama yayi dirshan akan kujeran dake falonsa, haɗe da soma cire safar ƙafansa, fuskarsa cike take da annuri dagani kai kasan yanacikin farinciki...
Turo ƙofar falon nasa akayi da ƙarfin gaske, wanda hakan yatilasta masa ɗago kansa da sauri, don ganin ko waye.
Dammm haka yaji ƙirjinsa yabuga, sakamakon ganin fuskar Hajiyarsa da yayi babu ko ɗigon annuri akanta, saima wani irin mugun kallo da take jifansa dashi.
Cike da girmamawa yace "Hajiya Barkanki da....."
Saurin ɗaga masa hanu tayi, alaman batason jin komai daga garesa..
Cikin ɓacin rai da tuƙuƙin zuciya Hajiya tasoma cewa....
"Lallai ka haifu Sadeeq, tunda har zaka iya kai ƙarana wajen ƙanin mahaifinka, yanzu akan wata watsatstsiyar yarinya, ka ke neman ka bijirewa auren ƴar uwa kuma aminiyata da aka baka? Ashe dama wacce kake ikirarin kana so ɗin, ba cikakkiyar mace bace, sauran layine? kaban mamaki ƙwarai Sadeeq, amma bakomai ni na sakema har haka ta faru, kuma tabbas zanɗauki ƙwaƙƙwaran mataki akan ka, daga kai har sakaryar yarinyar da ka bawa soyayyarta amanna, bansan cewa rashin hankalin naka har yakai haka ba, ashe har zuwa kamun ƙafa wajen mutane kakeyi, akan cewa azo a bani baki, nabarka ka auri wacce tagama raba budurcinta ga mazan layi, hmmm wallahi kasaurari hukuncin da zan yanke, kuma tun wuri ka gaggauta cire tunanin auren wannan yarinyar aranka, domin kuwa bamai yi wuwa bane!" fuuu haka Hajiya ta juya ta fice daga falon nasa ranta amatuƙar ɓace...
Kalmar "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!"
Shine abun da yafito daga bakin Dr Sadeeq, wanda yasanya hannayensa gaba ɗaya ya dafe kansa... "Me yasa Aunty Raliya? meyasa zakimin haka?" yatambayi kansa cikin takaici dakuma ɓacin rai. Tabbas yasan Aunty Raliya ce ta sanar da Hajiyansa komai, domin kuwa lokacin da yake gaban Baffa Amadu ta ƙirasa, bai ɓoyemata ba kuma yashaida mata cewa yana gidan Baffa Amadu'n, ashe ita harta gane mai yakawosa, shine kuma tasanar da Hajiyarsu komai... Take idanunsa suka kaɗa sukai ja,, ba abun da yake masa ciwo kamar aibata Zahrah da akeyi, kowa idan yatashi sai yajefeta da sunan wacce ta watsar da mutumcinta a waje, alhalin kuma itama ba laifinta bane, ƙaddarace dakuma tsautsayi, domin kuwa shi kansa sheda ne akan abun da yafaru da'ita, tunda har kusan haukacewa tayi. Rasama me yake masa daɗi yayi, da wanne zaiji ne? da soyayyar Zahrah, ko kuma da fushin da Hajiyarsa keyi dashi. Gaba ɗaya ma ji yayi zazzaɓi nason kamasa don haka kawai sai ya koma ɗakinsa ya kwanta, ba abunda yake ambata sai sunan Allah, domin kuwa shi kaɗai ne zai iya kawo masa ɗoki,, dama kuma mu dashi muka dogara shine mai kowa kuma mai komai, sarkin da babu kamarsa, Allah kenan buwayi gagara misali, maiyin duk yanda yaso mai kuma ƙwacewa da kuma bayarwa alokacin da yaso, ga kuma duk wanda yaso.....
Zahrah kuwa tunda ta faɗa duniyar bacci ba'ita tafarka ba, sai gaf da'ana ƙiraye ƙirayen sallan magriba.. Kaitsaye banɗaki ta wuce taje tayi wanka haɗe da ɗauro alwala tazo ta kabbara sallan magriba.
Kayanta marar nauyi tasanya haɗe da ɗauƙan wayarta dakuma ledan da kayan siyayyanta ke ciki, tafito farfajiyar gidan nasu, zaune ta iske Inna tana faman ƙoƙarin kunna redio'nta, wanda koda yaushe take tare dashi kamar jaraba.
"Barka da dare Inna" Zahrah tafaɗa lokacin da tayi mawa kanta mazauni a kusa da Inna'n.
Inna bata amsata ba, saima kafe ledar dake hanun Zahrah'n da tayi da ido, Allah Allah take taga mene acikin ledar, domin dama bakinta ya bushe neman abun lasawa takeyi, kasancewar tuwo ta tuƙa abincin dare, bakuma tajin cinsa, tafison tasamu ƙwalam taɗan lasa, like o'o da o'o lol.
Tun Zahrah batakai ga buɗe ledar ba inna tayi gajen haƙuri haɗe da fusge ledar daga hanun Zahrah tashiga dubawa.
Ganin cewa tarkacen su Chocolate's da kuma su biscuit's ne acikin ledar yasanya Inna jan uban tsuka haɗe da bankamawa Zahrah harara.
"Aikin kenan gayyar tsiya, mutum yasan bakacin abu, amma saboda tsinannen baƙinciki dakuma mugunta, ko da yaushe shiyake saya bini bini, bazai sayo abun da duka gida za'a amfana ba mcheeww!" cikin ƙufula Inna taƙare maganar, domin kuwa ita duk wannan shirmen banzan basonsu take ba, tafiso taga daƙwalen kaza, kokuma gasheshshen nama mai zafi, yauwa tanan tafi kauri, amma kwata kwata kayan kantin nan ita ba zaɓinta bane.
Da ƙyar Zahrah ta iya danne dariyan Inna dake cikinta aciki.
Buɗe ledan tayi gaba ɗaya haɗe sa sanya hanunta taciro wani ɗan madaidaicin cake wanda daganinsa kasan yasha madara.
"Ungo wannan Inna shikan nasan zaki iyaci, saboda kema nasayoshi" Zahrah tafaɗi haka tana mai miƙamawa Inna cake ɗin.
"Yauwa kokefa, amma da kya bani wasu tarkacen banza"
Take Inna ta ɓare cake ɗin, tahau ci har lumshe idanu take, domin dai sosai cake ɗin yamata daɗi.
Murmushi kawai Zahrah tayi haɗe da gyara zamanta, tasoma latsa wayarta....
Wani yarone yashigo cikin gidan bakinsa ɗauke da sallama, atare Inna da Zahrah suka amsa masa.
"Wai ana ƙiran Zahrah a waje" inji cewar yaron..
Wani irin faɗuwa Zahrah taji gabanta yayi harsaida tasanya hanu ta dafe ƙirjinta......
(🤔Miye Zaid yake sake shirya mawa Zahrah ne wai readers🧐.
Hajiya problem🤣 Team Dr saiku shirya kuyo gangami kuzo kuyi banbaki ga Hajiya kozata haƙura 😜)
(Ina jin bacci amma haka nayi tƴping ɗinnan, idan kunga tƴping eror kuyi haƙuri saboda typing ɗin dare nayi)
*Voted,Comment,and Share please..... Follow me on Wattpad @fatymasardauna
9:51 pm.....
(kuyi haƙuri banyi posting da wuri ba naje makaranta ne)
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
〰️〰️〰️〰️〰️〰️〰️
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 59 to 60*
Wani irin faɗuwa Zahrah taji gabanta yayi har saida ta sa hanu ta dafe kirjinta daya fara dukan uku uku.....
"Jekace tana zuwa" Inna tace da yaron,, bamusu yaron yajuya yafice daga cikin gidan...
"Yadai lafiyanki kuwa naga kinwani dafe ƙirji?" Inna tatambayi Zahrah, wacce lokaci ɗaya yanayinta ya sauya.
"Bakomai" Zahrah tafaɗa a taƙaice domin kuwa ko tayi ƙoƙarin ganar da Inna halin da take ciki tofa bazata gane ba...
"Tashi maza kije, ba kyau yin watsi da baƙo, wata ƙilama da alkhairi yazo miki, domin na lura keɗin baki da ƙashin tsiya" Inna tafaɗi hakan lokacin da ta miƙe daga zaunen da take.
Cikin sanyin jiki Zahrah takoma ɗaki ta ɗauko ƙaton hijab ɗinta ta sanya.
Tun kafun ta ƙarasa fita daga zauren gidannasu zuciyarta tasoma bugawa, wanda batasan dalilin hakan ba.
Wata mota ce tagani fake a ƙofar gidan nasu, kasancewar akwai hasken wuta, yasanya har kalan motar tana'iya hangowa.
Tsayawa tayi cak daga inda take, domin bazata sake tabka babban kuskuren da ta tabka a baya ba, batasan waye ba don haka bazata ƙarasa ba, idan wanda ke cikin motar yagaji ya fito, ya isketa daga inda take tsaye...
Cikin hanzari wani wanda baza'a ƙirasa da suna matashi ba, bakuma za'a ƙirasa da suna tsoho ba, yafito daga cikin motar hanunsa ɗauke da wani kwali, yayinda aka ɗaura wani kyakkyawan flower a saman kwalin... Ganin yanufota kaitsaye yasanya ta ɗan sake ja da baya..
"Sannu da fitowa ranki shi daɗe" mutumin nan yafaɗa..
"yauwa sannu" Zahrah ta bashi amsa a taƙaice...
" dama saƙone aka bani nakawomiki" wannan mutumin ya kuma faɗa cikin rusunawa haɗi da girmamawa, duk da kuwa cewa shiɗin ba yaro bane, domin yakusan haifar Zahrah'n ma, domin itama bawani yawan shekaru ne da'ita ba...
Cike da tsananin mamaki Zahrah, ta saki baki da hanci tana kallon mutumin dake tsaye a gabanta, yana miƙomata saƙon dake hanunsa...
"Wayekai?" shine kawai abun da ya iya fitowa daga bakinta, saboda gaba ɗaya kanta ya kulle...
Murmushi mutumin yayi haɗe da cewa "Ba'a bani daman sanar dake koni waye ba, kawai dai an umarceni dana kawomiki wannan saƙon, sannan dan Allah kada kice bazaki ansaba, saƙone mai mahimmanci, yanada kyau ki karɓa, sannan daganinki ke mai ilimi ce, kinsan bakyau maida hanun kyauta baya!" mutumin yafaɗi haka still yana mai sake miƙo mata kwali da flowern dake riƙe a hanunsa...
Kai Zahrah tashiga gyaɗawa, cike da tsarguwa tace " Kana da girma da kuma mutumcin da bazanyimaka gardama ba, amma kuma saidai kayi haƙuri, bazan karɓi abu daga wanda bansani ba, bankuma san menene nufinku a kai na ba" tafaɗi hakan da iyaka gaskiyarta....
"Hakane, amma ki ceci aikina, domin wanda ya ban saƙonnan nakawo zuwa gareki ya tabbatarmin da cewa, idan har baki karɓi saƙon ba, to abakin aikina, kitaimaka, ina da iyalai, kuma da aikina na dogara" mutumin yafaɗi haka cikin rauni.
Zaro idanu Zahrah tayi haɗe da jinjina maganar mutumin aranta, lallai kuwa kowaye ya aikosa yacika ɗan jin kai, ita kuma irin mutanen da tafi tsana kenan a rayuwarta wato mutum mai jin kansa....
Cike da kokonto haɗi da zullumi tasanya hanu ta karɓi abun da mutumin ke miƙomata.
"Zankarɓane kawai saboda kai, domin na fuskanci rashin karɓana zai iya sanyaka acikin matsala, amma koma waye ya turoka kace masa injini ya sanja hali, domin wannan ba hali mai kyau bane" daga haka tasakai tayi komawarta cikin gida..
Cike da murna'n cewa ta karɓi saƙon wannan mutumin yakoma mota haɗe da yi mata key yabar area'n unguwar tasu....
Zahrah tana shiga gida kaitsaye ɗakinta ta wuce, yayinda Inna ta rakata da idanu...
Zama tayi akan katifa, haɗe da tsurawa kyakykyawan kwalin nan idanu, ba iya shi kaɗai bane, abun ɗaukar hankali, hadda wannan haɗaɗɗen flower'n dake samansa ma abun burgewane, alal haƙiƙa ma ita flower'n ne yafi ɗaukar hankalinta....
Cikin sanyin jiki tasa hanu ta ɗauki flower'n haɗe da matso dashi kusa da fuskarta....lokaci ɗaya ta zabura haɗe da wurgi da flower'n gefe, take idanunta suka kaɗa sukai jajur dasu, jitayi kanta yafara juyawa, tabbas bazata taɓa mantawa da wannan ƙamshinba har abada kuwa, ajikin mutum ɗaya tasan wannan ƙamshi, bayan shi kuma batasakejin ƙamshin a jikin kowa ba,, hannayenta ta sanya duka biyu haɗe da dafe kanta dayake sara mata,, tabbas irin ƙamshinsa fulawar nan keyi, take taji wani irin tsanar flower'n ya cika mata zuciya, san nan kuma tsanarsa tasake dawo mata sabuwa fil, cike da ɓacin rai ta ɗauki flowern haɗe da fita waje da'ita, ko son ganinta ma batason yi, kai tsaye wajen da suke aje shara ta nufa, cike da tsanar flower'n ta jefa ta cikin kwandon shara, haɗe da furzar da yawu akan flower'n duk wani abu da zai tuna mata da Zaid ta tsanesa...
Ranta a ɓace takoma ɗaki, ita dai Inna dake zaune a tsakar gidan haka ta saki baki galala tana ganin ikon Allah..
"Wallahi na tsaneka, tsana mafi muni, bantaɓajin tsanar wani a raina sama da wanda nakeyi maka ba, ya Allah kada ka sake haɗa fuskata da tasa!" tafaɗi hakan a bayyane, kuma cikin tuƙewar murya...
Gaba ɗaya ƙamshin da taji flower'n nan nayi ya ɗaga mata hankali, sabuwar tsanar Zaid yasake ɗarsuwa acikin zuciyarta...
Lallai da zataga wanda yasanya akawo mata flower'n nan da ta gargaɗesa da kada ya sake kawo mata komai nasa, don bata so, domin kuwa duk wani abu da zai sanya tayi tunanin Zaid bata ƙaunarsa, koda sunansa nema batason ji"
Kwanciya tayi lamo akan gado, tana mai da numfashi, ji takeyi gaba ɗaya ta tsani ɗakin nata, domin kuwa ɗakin gaba ɗaya ya ɗau ƙamshin turaren dake jikin flower' ɗin nan....
Wayartace tasoma ƙara alamar shigowar ƙira, ganin Dr Sadeeq ne me ƙira yasanya ta ɗaga wayan, cikin son ɓoye damuwarta..
"Inaƙofar gida" abun da Dr Sadeeq yafaɗa kenan, a cikin wayar, domin kuwa shima dai yauɗin yana cikin damuwa....
Babban tabarma ta shumfuɗa musu a tsakar gida, kafun tanufi ƙofar gida don yi masa iso..
Kusan tare suka shigo cikin gidan, tana gaba yana biye da'ita a baya.. Gaba ɗaya yagama karantar yanayinta, ya kuma gane cewa tana cikin damuwa.
Zama yayi akan tabarman da ta shumfuɗa musu, haɗe da tanƙwashe ƙafafunsa.. Gaba ɗaya nutsuwarsa ya miƙa zuwa gareta, ta hanyar zuba mata idanu....
Gyara zama Zahrah tayi haɗe da ɗaga idanunta ta saci kallonsa, aikuwa karab idanunsu suka sauƙa akan na juna.. Cikin son basarwa tace " Sannu da zuwa, ya hanya?"
Ajiyar zuciya ya sauƙe haɗe da lumshe idanu..."Hanya ba daɗi duk nagaji da tuƙin ma, i hope you will find a driver that will take me home" cikin zolaya yaƙare maganar..
Kallonsa tayi kawai, haɗe da yin ɗan murmushi, shiru tayi batare da tace dashi komai ba...
"Meke damunki naganki haka, ko dai ciwon kanne?" Yatambayeta cike da kulawa..
"No bashi bane, ka wai dai gajiya ne, baisakeni ba haryanzu" tafaɗi hakan a taƙaice...
"Kansa yajinjina, haɗe da sake lumshe idanunsa, shi ɗinma ƙarfin haline kawai yasa sa yazo, amma tabbas damuwar dake damunsa tana da yawa.
"Meke damunka, naga gaba ɗaya kamar baka cikin farinciki?" Zahrah ta tambaya cikin siga da yanayi na nuna damuwa..
Wani irin sanyin daɗi yaji a zuciyarsa, badon komai ba, saidon kulawa da yasamu daga gareta.
Gyara zamansa yayi haɗe da bata duka nutsuwarsa...."Bazan ɓoyemiki ba Zahrah, tabbas inacikin damuwa, kuma duk akan kine, Ina tsananin sonki Zahrah, ina da burin baki farinciki a cikin rayuwarki, amma sai dai na haɗu dake a ƙurarren lokaci, inafata zaki fahimci abun da zance dake?"
Cike da ɗaurewar kai Zahrah take kallon Dr Sadeeq, domin kuwa sam ita bata fahimci inda kalamansa suka dosa ba.
"Mahaifiyata ta zaɓamin matar da zan aura, yanzu haka maganar da nakeyi miki, har ansanya mana rana, saura sati uku"
dummm haka Zahrah taji ƙirjinta yabuga, duk da cewa bata wani jin son Dr Sadeeq a ranta, amma bazata taɓa so kyakkyawan namiji mai nagarta kamarsa ya kuɓuce mata ba, take idanunta suka ciko da ƙwalla wanda batasan na menene ba.
"Dan Allah kada kiyi kuka kinji Zahrah na, nafaɗamiki hakane don kisan halin da nake ciki, amma bawai hakan nanufin bazan aureki bane ba"
Cike da kulawa yakama duka hannayenta biyu, haɗe da kafeta da idanu. Gaba ɗaya abun da yake wakana ya kwashe ya faɗa mata, hatta maganarsa da Baffa Amadu, saida ya sanar da'ita, sai dai ya ɓoye mata ƙiyayya dakuma maganganun da yayarsa da kuma mahaifiyarsa suka faɗa akan ta na ɓatanci.
Cigaba yayi da cewa "Ki kwantar da hankalinki, na miki alƙawari nan bada jimawa ba, zaki zamo mallaki a gareni, insha Allah zanzamo mijinki Zahrah!"
Hawayene suka shiga zirya akan fuskan Zahrah, cikin murya mai rauni tace " Dama nasan cewa nayi ganganci, domin kuwa kai ba sa'an aure na bane, nagode sosai da irin kulawa da kuma ƙoƙarin da kayi a kaina, bakuma zan taɓa mantawa da hakan ba, na yarda da ƙaddara mai kyau ko marar kyau, idan aurena dakai baiyi wu ba, na yarda haka Allah yatsara, tun da fari shiya gurɓatamin rayuwa, ya cutar dani, cuta mafi muni, ta yanda babu wani wanda zai lamuncewa haɗa zuri'a dani, tabbas daman nasan koda kai ka aminta da aurena, ba lallai iyayenka su aminta ba?....Kukane ya ƙwace mata sosai.
Sake damƙe hannayenta yayi acikin nasa, haɗe da kafeta da idanu, sosai tausayinta ya sake kamasa.
"Kinaso nasake shiga cikin damuwa ne Zahrah?" yayi maganar cikin tausasa murya.
Bata iya amasa masa ba, sai gyaɗa masa kai da tayi alamar "A'a"
"To idan har bakyaso nasake shiga damuwa, ki daina kuka kinji Zahrah na, insha Allah, zamu rayu tare dake, harma ki haifamin kyawawan babies, masu kyau kamarki, masu irin idanunki, da bakinki, harma da irin hancinki, da kuma..." sai yayi shiru, yana mai dariya ƙasa ƙasa.
Kunyane ya kama Zahrah haɗe da dariya, duk da kuwa cewa tana cikin halin damuwa, sai kawai ta kawar da kanta gefe, gaba ɗaya jinta take a tsarge sakamakon hanunta da ke saƙale acikin nasa...
"Zantafi saboda naga dare yasoma yi, amma saikinmin alƙawarin cewa bazakiyi kuka ba, bakuma za kisa kanki a damuwa ba, idan kikayi haka zanji daɗi sosai"
Abune mai matuƙar wuya, a dake ka sannan a hanaka kuka, amma tabbas zata jarraba wajen daure zuciyarta.
"Bazanyi kuka ba" tafaɗa cikin muryar da bata fita sosai, da badon yana kusa da'ita sosai bana ma to tabbas da bazaiji maitace ba..
"Kinyi alƙawari?" yatambayeta
"Eh" tafaɗi haka bayan taɗanyi jim.....
"Yauwa Zahrah na, nasan ai kina da cika alƙawari, taso muje mota na baki magungunanki" babu musu ta miƙe daga zaunen da take, haɗe da rufa masa baya.
Murfin motar ya buɗe haɗe da fiddo wata ƙatuwar leda.
"Ungo magungunan suna ciki, akwai bayanin yanda zakisha a jiki, please ki kulamin da kanki kinji" yafaɗi haka cikin lallashi, haɗe da miƙa mata ledan dake hanunsa.
Kasa amsan ledar tayi, saima kawar da kanta gefe da tayi.
Murmushi Dr Sadeeq yayi, domin kuwa sarai ya fuskanci hakan da tayi metake nufi.
"Kiyi haƙuri ki karɓa kinji Zahrah na" yakuma faɗan hakan cikin lallashi.
Baki Zahrah taturo gaba haɗe da cewa ...
"Kasan tun ba yauba nafaɗama cewa banaso domin kuwa hidiman da kakemin yayi yawa, mai yasa bazaka bari haka ba!" ta tambayesa cike da sakalci..
"Saboda kina da mahimmanci, kinkuma cancani namiki fiye da haka, amma yanzu dai banso kice a'a ki karɓa kinji" still cikin lallashi yayi maganar.. Badon ranta yasoba haka ta karɓi ledan.
"Saida safe" tace dashi cikin sanyin murya haɗe da juyawa ta nufi hanyar shiga gida.
"Kada kimanta kin ɗauki alƙawarin cewa bazakiyi kuka ba, bakuma zaki shiga damuwa ba, kada ki karya alƙawari kinji mai kyau na!"
Murmushi kawai tayi masa haɗe da ɗaga masa kai alamar taji.
Yana ganin shigewarta cikin gida, shima yashiga motarsa haɗe da bata wuta yabar unguwar tasu..
Tanashiga cikin gida, Inna tayo kanta haɗe da fusge ledar dake hanunta, babu magana ba komai ta shiga zazzage ledan akan tabarma, kallonta kawai Zahrah ta tsayayi cike da takaici, sai yanzu take godewa Allah dayasanya ba Inna bace ta haifeta, domin kuwa da Innace ta haifeta to tabbas da nan gaba kaɗan zuciyarta zata fashe, saboda wannan halin da Inna keyi ba hali bane na iyayen ƙwarai, batama tsaya ganin menene acikin ledar ba, ta wuce cikin ɗakinta, domin ita dama ba wannan bane a gabanta, yanzu babban damuwarta shine, yanda zata samo maganin matsalarta.
Ɗaukan kwalin nan da aka kawo mata tayi, haɗe da soma kiciniyar buɗewa, kasancewar bakin kwalin a nane yake da wani gam me kyau..
Tana buɗe cikin kwalin wani tsadadde kuma kyayyawan agogo na mata ya bayya, gefen sa kuwa wani irin awarwarone haɗe da zobe masu kyaun gaske, wanda dagani kasan na gold ne, domin kuwa kyawunsu kaɗai ya'isa ya bayyana haka, ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya ta sauƙe haɗe da mai da murfin kwalin ta rufe kamar yanda ta samu, ɗaukan kwalin tayi dukansa, haɗe da ɓoyesa a cikin kayanta, dawowa tayi kan katifarta ta kwanta zuciyarta cike tab da tunanin son gano wanda ya soma
bibiyar rayuwarta...
Hajiya Habiba (mahaifiyar Dr Sadeeq) ne zaune akan kujera gaba ɗaya ta tattara nutsuwarta ta miƙasa ga Baffa Amadu dake zaune akan ɗaya daga cikin kujerun falon...
Baffa Amadu ne yaci gaba da cewa " Banzo nan don na yi miki dole ba, amma Hajiya Habiba yana da kyau wasu lokutan muna ƙoƙari wajen bawa ƴaƴanmu dama akan abun da suka nuna zuciyarsu naso, musamman ma aɓangaren abun da yashafi aure, haƙiƙa Sadeeq yasameni da wannan maganar yakuma min bayani tayanda zan fahimta, Alhmdlh nakuma fahimta, yanzu saura ke, kada kice wai don ƙaddara ya taɓa faɗa mata, ɗanki bazai aure ta ba, kada kiyi haka, domin ita ƙaddara tanakan kowa mai kyau da marar kyau, sannan abu nagaba danakeso kisani, ko da ace alal misali yarinyar ta kasance karuwa ce, addini bai hana masa auren taba, wala Allah saboda auren saiki ga ta shiryu, balle kuma ma bahakan take ba, amma bazan miki dole akan cewa saikin amince ba, ɗan kine kuma kina da iko akansa"...
Nannauyar ajiyar zuciya Hajiya ta sauƙe, haƙiƙa Baffa Amadu yazo mata da magana mai girma.
ɗan nisawa tayi haɗe da cewa "Bawai naƙi aurensa da ita bane, saboda wani abu ba ne, kawai dai inajiye masa yanda tarbiyan yaransa zai kasance ne matuƙar takasance tana cikin gidansa, domin na tabbatar rashin wadataccen tarbiyan da aka bata a gidansu, shiya jawo faruwar haka a kanta, kaga itama bata samu tarbiya mai kyau ba, balle tayi ƙoƙarin bawa nata yaran, haƙiƙa Sadeeq yarone mai biyayya agareni, kuma harcikin zuciyata na ƙudurta aniyar cewa bazai taɓa auren wannan yarinyar ba, amma tunda harka shigo cikin al'amarin shikenan na'amince, amma kuma fa sai dai idan su biyun duka zai haɗasu ya aura, kaga dai Salima ƴar wajen ƴar uwata ne, haka kuma mamarta aminiyata ce, bayanda za'ayi na watsa musu ƙasa a ido, tahanyar cewa Sadeeq bazai auri Salima ba, kuma kaga yanzu saura ƴan satika ne suka rage, har anriga da anfara shirye shiryen biki"
"Ƙwarai kina da gaskiya ta wani wajen, amma kuma bamu iya ja da haɗin Allah, yanzu zansanar da Sadeeq ɗin duk yanda mukayi dake, zan kuma faɗa masa amincewarki, nasan shi ɗinma zai amince da umarninki, amma inaga zaifi kyau ayi bikin nasu a rana ɗaya, domin babu amfanin jan lokaci"
"Eh duk yanda kukace shikenan" Hajiya tafaɗi haka badon ranta yaso ba.
"Shikenan to duk dai yanda ake ciki, zai zo yasanar dake" Baffa Amadu yafaɗi haka bayan yamiƙe tsaye ya gyara zaman garen dake jikinsa...
Cike da mutun ta juna sukayi sallama shida Hajiya...
Zama Hajiya tayi afalon haɗe da yin jigum, tabbas ba'ason ranta ta amince da wannan auren ba, saboda ita gani take tamkar yarinyar ba kimtsatstsiya bace, ta amince ne kawai saboda Baffa Amadu yashigo cikin maganar, kuma tana matuƙar darajasa haɗe da basa girma, domin tana masa kallo ne tamkar marigayi mijinta, amma da ba haka ba da bazata taɓa amincewa ba, yanzu dai kawai sai dai tayi addu'an Allah yabasu zaman lafiya, amma ta wani ɓangare na zuciyarta, tunani take taya zataje ta tunkari ƴar uwarta Hajiya Furaira da wannan maganar, tasan Hajiya Furaira macece mai zafi, bazata taɓa son hakan ba, domin saboda bala'inta da zafin kishin ta, ne ma yasanya mijinta haryau yakasa ƙara aure bawai kuma don baya so ba, to ina kuma da idan taji cewa ƴarta ɗaya tilo zata haɗa miji da wata daban wacce bata da galihu, gaskiya zaiyi wuya ta amince... Haka dai Hajiya tadinga saƙawa da kuncewa daga ƙarshe ta tashi ta wuce ɗakinta....
Cikin matsanancin farinciki Dr S.S ke kallon Baffa Amadu sakamakon jin cewa wai mahaifiyarsa ta amince da aurensa da Zahrah, masha Allah ashe dai mafarkinsa zai zamanto gaskia, sai dai kuma farincikin nasa bai zama cikakke ba, domin kuwa sosai maganar haɗa auren Zahrah da Salima ya daki zuciyarsa, saboda shi a tsarin sa baida burin aje mata biyu acikin gidansa.
"Yanaji kayi shiru ne Sadeeq, ko baka amince da sharaɗin mahaifiyartaka bane?" Baffa Amadu yatambayeshi cike da kulawa.
Kansa yashiga sosawa yamakasa ce da Baffan nasa komai..
Murmushi Baffa Amadu yayi domin yafahimci halin da Sadeeq ɗin yake ciki. "Kada ka ɗaga hankalinka Sadeeq, atunanina ka kai namiji wanda zai iya riƙe mace sama da biyu, don haka wannan ba abun damuwa bane, kayarda da sharaɗin mahaifiyartaka, addu'anmu shine Allah yatayaka riƙo, yakuma baka dama da ikon yin adalci a tsakaninsu, yanzu yaushe kakeso muje gidansu ita yarinyar?"
Gaba ɗaya jiyayi jikinsa yayi sanyi, zuciyarsa kuwa jiyayi tayi masa wani iri. "Zansanarda Baffan yarinyar idan yafaɗamin ranan da zakuzo, saina faɗa maka" inji cewar Dr Sadeeq..
"To shikenan Allah yakaimu" daga haka sukayi sallama, Dr S.S yabaro gidan Baffa Amadu zuciyarsa cike da tarin tunani kala kala, yana farincikin cewa Zahrah zata zamo matarsa, amma kuma ta wani ɓangare na zuciyarsa kwata kwata bayajin daɗi. Zahrah tana buƙatar farinciki da kuma kulawa mai kyau, baikamata ace anraba mata farinciki ita da wata ba, to amma "Miye mafita?" yatambayi kansa, bayan yasan baida amsar tambayan nasa, amma koma dai mene ayau zaije yasamu Baffa yasanar dashi cewa yana neman abashi izini yaturo magabatansa don abasa auren Zahrah, yakuma ƙudurta aransa cewa, dakansa zai bada order a Dubai, na kayan lefen Zahrah, domin kuwa zaiyi rawar gani sosai, wajen ganin komai na Zahrah yafita da ban....
Amatuƙar mamakance Alhaji Ma'aruf ke kallon Zaid wanda yafaɗi maganar daya matuƙar basa mamaki.... "Aure fa kace Zaid, dagaske kake, yanzu kashirya zakayi aure?"
"Da gaske nake Dad aure zanyi, kuma inaso kaje da kanka ka tambayamin, banaso auren yawuce nan da sati biyu Dad"
Cike da tsananin farinciki Alhaji Ma'aruf yace "Alhmdlh! naji daɗi ƙwarai da gaske, domin zuwa yanzu yakamata ace ka aje iyali, insha Allah, zan je na tambaya maka aurenta, ƴar wayene kuma a ina take?"
"Ba ƴar kowa bace Dad, talakawa ne ma, amma ni ahaka naji na aminta ina kuma son na aureta" yafaɗi haka da iyaka gaskiyarsa..
Jinjina kai Alhaji Ma'aruf yayi haɗe da cewa "Zan sa rana sainaje naga mahaifinta"
"To" kawai Zaid yace haɗe da tashi yabar falon Dad ɗinnasa....
Fitowarta amakaranta kenan, tana sauri ta samu abun hawa, don bata son tsayuwa a bakin makarantar, kasancewar Dr Sadeeq aiki yamasa yawa bazai samu daman zuwa ɗauko ta ba...
Wani matashin saurayine yanufo wajenta, hanunsa ɗauke da wani babban kwali wanda aka rufesa da wani irin abu mai kyau, aka kuma ƙawatasa da flower mai walwali..
"Ranki ya daɗe barka da yammaci" saurayin yafaɗa.
"Yauwa barkan ka dai" itama ta mayarmasa amsa cikin ɗari ɗari dashi..
"Saƙo aka bani nakawomiki" yafaɗi maganar yana me miƙa mata kwalin dake hanunsa..
Cikin mamaki Zahrah ta shiga kallon saurayin nan dake tsaye a gabanta..
Murmushi saurayin yayi mata haɗe da sake miƙo mata kyakkyawan gift ɗin dake hanunsa.
"Waye ya aikoka?" tayi masa tambayar cikin dakiya...
"amsar tambayarki duka suna cikin nan" yaƙare maganar yana me nuna mata kwalin dake hanunsa.
Hakanan taji zuciyarta ta aminta da ta karɓi saƙon.. Hanu biyu tasa ta karɓa, batace dashi komai ba tayi wucewarta dai dai lokacin mai taxi ya ƙaraso tashiga.
Tsurawa kyakkyawan kwalin idanu tayi, sosai adon jikinsa yayi kyau haɗe da ɗaukar hankali, gaba ɗaya ta ƙosa, tabuɗe kwalin don ganin ko wanene yake son yin wasa da hankalinta, ta hanyar turo mata da saƙonni, batare da yabari tasan kowaye shiɗin ba.
Tana shiga gida direct ta wuce ɗakinta, ko mayafinta bata cire ba, ta zauna haɗe da soma yaye ledan da akayimawa kwalinnan ado dashi, tana buɗe kwalin tayi arba da wani ƙatuwar ta karda wanda aka naɗeta, cikin sauri ta ɗago takardan haɗe da soma warwareta, amatuƙar razane tayi wurgi da takardan sakamakon idanunta da sukayi mata tozali da zanen hoton dake jikin takardan.
(🤔Ga Zaid ga Sadeeq ko waye cikinsu zai mallaki Zahrah🤷♀)
*17/December/2019*
*Follow me ...*
*Wattpad user name* *@fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI!!*
*Written By*
*PHATYMASARDAUNA*
_(Shalelen Kainuwa)_
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 61 to 62*
Idanu ta ƙara zarowa domin tabbatar mawa kanta cewa abun da tagani gaskiya ne, ko kuwa, gizo idanunta keyi mata.
Tabbas dagaske ne bawai gizo bane, hoton zanen fuskarta ne raɗau ajikin takardan. Hanunta na rawa haka ta durƙusa ƙasa, haɗe da sanya hanu ta sake ware takardan, tabbas itaɗince babu ko kokonto, zanen fuskarta ce kwance ajikin takardan, amma saboda tsananin kyawun da zanen yayi tamkar azahiri haka zaka gani, hanu tasanya ta shafi zanen, cike da fargaba haɗe da ɗaurewar kai.
Lallai yazama dole a gareta tanemo wanda yake aikata mata waƴan nan abubuwan, kusan kwana uku yanzu kenan ana turo mata da saƙonni, bata kuma san daga waye bane.
Bata damu da ta duba sauran kayan dake cikin kwalin ba, ta tattara shi ta ɓoye acikin kayanta.
Zama tayi dirshan akan katifa tana mai da numfashi akai akai, sosai abun yabata mamaki, tabbas ko ma waye ne wanda yake bibiyarta ta tabbata yayi mata farin sani, amma kuma rainin hankalin yayi yawa, dole zataimawa tufkar hanci. Abun da ta ƙudurta kenan acikin zuciyarta domin iskancin yasoma isarta.
Ƙarfe 6:30 na yammaci Dr Sadeeq yayi wa gidansu Zahrah tsinke, bayan yasha adon sa cikin riga da wando na shadda ƴar bugu mai kyau. Zama yayi acikin motarsa yana mai jiran fitowar Zahrah, domin kuwa yamata waya yasanar da'ita cewa gashi nan, a ƙofar gidansu.
Kafeta da idanu yayi domin kuwa bakaɗan ba tayi masa kyau, cikin shigar doguwar rigan dake jikinta, lallai Zahrah ƙarshe ce wajen haɗuwa dakuma kyau.
Fuskarta ɗauke da murmushi Zahrah ta ƙaraso wajen da motar tasa take fake. Tsayawa tayi ajikin motar, batare da ta buɗe tashiga ba. Ganin haka yasa Dr Sadeeq buɗe murfin motar yafito.
"Yau kuma aji ake jamin ne?" ya tambayeta cikin yanayin tsokana.
Ɗan guntun murmushi tayi haɗe da juya idanunta. "Eh mana, ko bankai naja aji bane?" itama ta tambayesa cikin yanayi na shauƙi.
"Murmushi yayi haɗe da ɗage giransa sama "Kin isa har kinma wuce, ko bakisan cewa keɗin tamusamman bace?"
Hararan wasa Zahrah ta wurgamai haɗe da kawar da kanta gefe, batare da tace dashi komai ba. Haka take al'adar ta ne, bakoda wani lokaci take bada amsar tambaya ba, domin a cewarta shiru ma magana ne.
"Kona zagayo na buɗe miki murfin motar ne gimbiyata, saboda naga kamar bazaki iya ba ?" yafaɗi hakan cike da kulawa.
"A'a ba buƙatar hakan, ni dakaina ma zan iya" taƙare maganar tana mai buɗe murfin motar, haɗe da shiga tayi mawa kanta mazauni.
Shima komawa yayi cikin motar ya zauna. Bayan ya ɗaura duka idanunsa a kanta.
"Kinyi kyau sosai, fiye da ko yaushe" yafaɗi haka yanamai kashe idanunsa.
Ɗanguntun murmushi Zahrah tayi "Nagode" tace dashi ataƙaice
Jinjina kansa yayi azuciyarsa kuwa cewa yayi "Lallai Zahrah tana da aji, duk da ta rasa Virginity ɗinta hakan baisanya ta zama wata sakaka da'ita ba, yanason mace wacce ta'iya takunta, wacce bata sakar baki tayita dariya like mental problem, wasu matan da zaran kace dasu sunyi kyau tofa take zasu wage baki suita ƙyaƙyata dariya, babu wani ɗan jan aji ba komai. nima shaida ce irin su Sister Munubiya idan kace dasu sunyi kyau ae har kyautan kuɗi zasu baka tsabar daɗi🤣"
Sake gyara zamansa yayi haɗe da dawo da nutsuwarsa zuwa gareta.
"Zaki'iya zama dani a ko wani irin hali Zahrah?"
Ya jefomata tambayar da bata tsammaci jinsa ba.
Cikin yanayin mamaki Zahrah ta dawo da kallonta garesa, haɗe da cewa "Banfahimci maikake nufi ba"
"Inanufin zaki iya rayuwa dani ako wani irin hali na tsinci kaina? sannan zaki iya yarda na haɗaku ku biyu na aura?" yakuma maimaita tambayar tasa.
Dummm haka Zahrah taji ƙirjinta ya buga, idan da badon kada yace ta rainasa ba, to tabbas da zatace dashi yasake maimaita maganar da yayi. Domin idan kunnuwanta sunjiye mata dai dai, to kuwa bata da amsar da zata basa, domin koda ta basa amsa zata iya faɗuwa, saboda balallai ta bashi amsa dai dai da abun da ya tambaya ba.
Idanunsa duka ya tsura mata, amsa kawai yakeson ji daga bakinta.
Kasa ce dashi komai tayi, domin kuwa haryanzu bata gama haɗa amsar da zata basa ba.
"Nasani dama ba lallaine ki amince ba, Hajiya na ta amince da aurena dake, amma kuma kamar yanda nafaɗamiki a baya, tun tuni akwai zaɓin da tayimin, takuma umarceni da na aureku duka biyu, shin zaki iya aurena a haka, zaki iya zama da wata a matsayin kishiyar ki?" yafaɗi hakan cike da zaƙuwan son jin amsa daga gareta.
Jikinta ne gaba ɗaya yayi sanyi, take taji zuciyarta ta karaya, batasan ya'ake zama da kishiya ba, haryanzu ita yarinyace, bakomai tasani na game da al'amarin duniya ba, tanaji a labarai irin illan da kishiyoyi suke mawa junansu saboda kishi, amma ita yanzu ba wannan bane a gabanta, makomarta na gaba take tunawa, shinya zata kasance?" ta tambayi zuciyarta...
"Kinyi shiru kice wani abu mana zahrah ko zuciyata zata daina bugawan da takeyi" Dr yafaɗi hakan cikin yanayin damuwa.
"Bazan taɓa ƙin aurenka ba, sai dai idan har kaine kace kafasa aurena, sai dai kuma inajin tsoro, bansan mene zai kasance dani gaba ba, dan Allah kada soyayyar matarka ta ruɗeka, ka wulaƙantani, banda wani madogari sai ALLAH sai kuma kai" taƙare maganar cikin rawar murya, yayinda idanunta sukayi rau rau dasu, alamar zasu zubda ƙwalla.
Ajiyar zuciya mai ƙarfi ya sauƙe, haɗe da sakin ɗan taƙaitaccen murmushi. "Har abada kada kitaɓa tunanin zan wulaƙantaki Zahrah, inasonki da gaske bada wasa ba, namiki alƙwari zan kamanta adalci a tsakaninku, bazan juya miki bayaba insha Allah!" Doctor Sadeeq ya faɗi haka cike da lallashi.
Tuni idanun Zahrah suncika da ƙwalla, amma idan ta tuno cewa bata da zaɓi sai taji gwamma kawai ta daure zuciyarta, haka ta ta ƙaddaran take.
"Kada kiyi kuka kinji My Princess, ina tare dake ako wani lokaci, zankuma share miki dukkanin hawayenki nan bada jimawa ba namiki alƙawari"
Saurin maida hawayenta tayi haɗe da ƙaƙalo murmushin dole ta'aza akan fuskarta, wan nan damuwarta ne ita kaɗai, baikamata ace tabari Dr Sadeeq yagane ba, lallai tun yanzu yakamata ta zama mai juriya.
"Baffa yana gida kuwa?" Dr. Sadeeq ya tambaya.
Wasa da yatsun hanunta tashiga yi, haɗe da kaɗa masa kai alamar "Eh"
Kai yajinjina haɗi da cewa "Yanaga duk jikinki yayi sanyi? banace kada kisa damuwa a ranki ba" cikin kulawa yayi maganar.
Cike da shagwaɓa Zahrah ta langwaɓar da kanta gefe haɗe da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, "Nibansa damuwa a raina ba" tace haka cikin sanyayewar jiki.
Wani irin kallo maiɗauke da ma'anoni masu yawa Dr.Sadeeq yashiga yi mata, ji yake tamkar yajawota jikinsa ya rungumeta tsam acikin ƙirjinsa, saboda ako da yaushe idan yana tare da'ita wani irin feeling yakeji a jikinsa.
"Kije kimin sallama da Baffa inaso zamuyi magana"
"To" kawai tace dashi haɗi da buɗe murfin motar tafita. Dakallo kawai ya bita harta shige gida.
Tana shiga cikin gida ta iske Baffa yana ƙoƙarin fitowa daga ɗakinsa.
"Zahrah har kindawo? badai likitan yatafi ba?" Baffa yajeromata tambayoyi alokaci ɗaya.
"A'a baitafi ba Baffa, shine ma yace nace ma yana son magana dakai" Zahrah tafaɗi haka ga Baffa cikin girmamawa.
"To Allah yasa lafiya, yanzu kuwa zanje na sa mesa" ya faɗi maganar yana mai nufar hanyar fita daga gidan.
Zahrah kuwa ɗakinta takoma.
Sosai maganar Dr.Sadeeq yataɓa mata zuciya, bakomai take hangomawa kanta ba, sai yanda makomarta zai kasance acikin gidansa, tabbas ta tabbatar wacce zai aura, ba irin ta bane, tasan tana da galihu, saɓanin ita da take ko oho, sannan kuma dole zata ga banbanci daga ƴan uwansa, haka ma Dr.Sadeeq ɗin dole zai banbantasu, saboda waccar zai sameta a budurwa, saɓanin ita da zai sameta ba'a budurwa ba, kukane yaƙwace mata mai sauti, cusa kanta cikin cinyoyinta tayi tashiga rera kukanta, har abada cutar da Zaid yayi mata bazai taɓa gushewa ba.....
"Alhmdlh masha Allah! haƙiƙa naji daɗin wannan magana taka Likita, lallai kacika mutumin kirki kuma mutumin ƙwarai, Allah yasaka ma da gidan Aljanna, kuma idan dai Zahrah ce kada kaji komai natabbatar itama tana ƙaunarka, saboda haka nabaka izini ka turo magabatanka, don mu tsaida magana,kuma maganar bayarwa nabaka Zahrah!" Baffa yafaɗi haka cikin farinciki, duk da kuwa cewa dama tun abaya yasan cewa Dr.Sadeeq yanason Zahrah, amma sake tabbatar masa da Dr. ɗin yayi yanzu, yasanyashi jin daɗi, domin shima yanzu burinsa shine ya inganta farincikin marainiyar Allah wato Zahrah..
Farinciki ne sosai yakama Dr.Sadeeq, yaji daɗin aminta dashi da Baffa yayi.
"Nagode da wannan dama da kabani Baffa, Allah yajiƙan magabata" Dr Sadeeq yafaɗa cike da girmamawa.
"Mune da godiya Likita, ai mu ba'abun da zamuce maka saidai fatan alkhairi" Baffa yafaɗa shima cikin jin daɗi, domin yasan Zahrah na auren Dr.Sadeeq wahalanta yaƙare da yardan Allah,saboda yana da tabbacin cewa Dr.Sadeeq zai bata kyakkyawan kulawa, duk da kuwa cewa Dr.Sadeeq ɗin yasanar dashi cewa ba Zahrah ita kaɗai zai auraba, yasanar dashi komai, kuma Baffa yayi na'am da hakan, saboda shi baimaga wani aibu acikin hakan ba, ai namiji mijin mace huɗu ne.
(Nima nace wannan gaskia ne, sbd haka duk me mace ɗaya ya ƙara😜😂)
Cike da farinciki Baffa da Likita sukayi sallama, yayinda Baffa yakoma cikin gida, ya kumace da Dr.Sadeeq zai turo masa Zahrah suyi sallama.
Tanajin Muryan Baffa a tsakar gida, tayi saurin share hawayenta, haɗe da miƙewa tsaye, domin har Baffa yafara ƙwaɗa mata ƙira.
Fuska cike da fari'a Baffa yace "Likita ke yake jira, zai tafi"
Sumi sumi haka Zahrah ta fice yayinda tabar Baffa yana gayamawa Inna abun da ya wakana tsakaninsa da Likita.
Tun fitowarta yake ta zabga murmushi, kallo ɗaya zakai mawa fuskarsa ka gane cewa yanacikin farinciki.
"Kitayani murna My Princess saura ƴan kwanaki ƙalilan na mallake ki!" Dr Sadeeq yafaɗi haka cike da shauƙi.
Kunyane yakama Zahrah, don haka ta sanya duka hannayenta biyu ta rufe fuskarta, bayan ta ƙaƙalo murmushi ta aza akan fuskar ta..
"Baffa yabani daman naturo magabatana don asa mana ranan aure, kuma insha Allah, gobe magabatana zasu zo, za'asa ranan aurenmu nan bada jimawa ba, so sai ki shirya domin kin kusa zama amaryata!" yanayin yanda ya ƙare maganar kaɗai ya isa taɓa zuciya..
Kunyane yasake kama Zahrah, har batasan sanda murmushi mai sauti ya kufce mata ba, gaba ɗaya ta lura Dr.Sadeeq ya ƙosa da ayi aurensu bata kumasan dalilinsa nayin hakan ba..
"Kinyi shiru kodai bakya farinciki ne my princess?" yatambaya.
Ɗan satan kallonsa tayi haɗe da sakarmasa murmushi mai tsayawa a zuciya.
Ƙaran wayarsane ta katsesa daga kallonta da kuma zancen zucin da yakeyi. Ajiyar zuciya ya sauƙe ganin wacce take ƙiran nasa, maida wayar tasa cikin aljihu yayi batare daya ɗaga ƙiran ba.
"Dare yayi Zahrah kishiga gida, zamuyi waya, kikulamin da kanki " yafaɗi hakan yana me ƙoƙarin shiga cikin motarsa.
Murmushin dole Zahrah tayi haɗe da yi masa saida safe, tajuya ta nufi cikin gida, hakanan taji wani iri a zuciyarta duk da batasan me yasa baiɗaga ƙiran da ake mai ba, amma tana da yaƙinin cewa matar da zai aura tare da itane ta ƙirasa. Saurin kawar da tunanin tayi aranta, domin tuna hakan ma bashida amfani a gareta.
Washe Gari....
Kamar yanda Dr.Sadeeq yafaɗa hakanne ya kasance da da dare bayan sallan magriba Baffa Amadu shida amininsa suka zo gidansu Zahrah don tambayan aurenta, balaifi Baffa yayi musu tarba mai kyau, sunkuma ji daɗin hakan, duk da sun lura cewa suɗin basuda wani ƙarfi, ma'ana arziki...
Magana ta fahimta akayi tsakanin Baffa da kuma Baffa Amadu, a taƙaice dai Baffa yabasu auren Zahrah, yayinda sukuma suka ɗau alƙawarin cewa a cikin satin za'akawo kayan tambaya dakuma na lefe, daga nan sai asa ranan aure, amma basason auren ya ɗau lokaci, saboda rana ɗaya suke so ayi dana Salima.. Da to kawai Baffa ya amsa musu domin shi baida wani abun cewa banda hakan, sai dai a ƙasan zuciyarsa tunani yake taya zai samu kuɗin da zaiyi mawa Zahrah kayan ɗaki, domin dai bayanda za'ayi ace anyi aure ba kayan ɗaki... Haka dai sukayi sallama cike da mutun ta juna...
Baffa ne Zaune akan tabarma ya yi jigum bakomai ke damunsa ba, kamar sha'anin auren Zahrah, Allah yasani ko abincin da za'aci abikin bai tanada ba, balle wata uwa uba kayan ɗakin da za akaita dashi..
"Wai tunanin mekakeyine haka tun ɗazu?" Inna dake zaune gefensa ta jefo masa tambaya.
"Ba dole nayi tunani ba Salame, kinga dai yau iyayen yaron nan Sadeeq suka zo, kuma da duk kan alama basa so aja auren nan yakai wani lokaci, kin kuma san halin dai da muke ciki na rashin kuɗi"
"Yo dama akan wannan kake ɗaga hankalinka? hmm Malam kenan to ai ni banga abun ɗaga hankali anan ba, ca nake shi Sadeeq ɗin yasan duk halin da muke ciki, kuma shi yakawo kansa yace ya na so, bawai mu makai masa dole ba, saboda haka malam ka kwantar da hankalinka, Zahrah ya nema kuma Zahrah'n zamu bashi" Inna tafaɗi haka da'iyaka gaskiyarta...
Kallon Inna kawai Baffa yayi haɗe da girgiza kansa, yasan ma koda yayi ƙoƙarin fahimtar da'ita to fa bazata fahimta ba.
***
"What? Mom cewa fa kikayi wai bani kaɗai Sadeeq zai aura ba, anya kuwa Mom kinji abun da Hajiya Habiba tafaɗamiki da kyau?" Salima tatambayi mahaifiyarta Hajiya Furaira cike da mamakin jin abun da mahaifiyarta tace da'ita..
"Abun da na faɗa miki shi naji daga bakin Hajiya Habiba, Salima kicire Sadeeq a ranki, domin kuwa aurenki dashi bazai taɓa yiyuwa ba, da raina dakuma hankalina bazan taɓa bari ƴata taje kan kishiya ba!" Hajiya Furaira tafaɗi haka cikin ɓacin rai..
Kuka ne ya ƙwacemawa Salima cikin muryan kuka ta soma cewa "Wani irin cin amana ne wannan mom, sai da maganar aurena dashi ta kankama sannan wata banzar magana zata ɓullo, wallahi bazan haƙura da shi ba, bakuma zan taɓa zama da wata a matsayin kishiyata ba, dole ne Sadeeq ya aureni ni ɗaya batare da wata ba, bazan iya jure rashin saba Mom, dan Allah kiyi wani abu" Salima ta ƙare maganar cikin shaɓe shaɓe da hawaye.
"Mekikeso nayi Salima? so kike naje na basu haƙuri akan su sa Sadeeq ya aureki ke kaɗai? ko ko sokike na zubar miki da ƙima daƙuma ƴancinki? Hajiya Habiba ƴar uwatace kuma ƙawata, bantaɓa tunanin haka daga gareta ba, amma bakomai, zanyi maganin abun, kuma ni banzauna da kishiya ba, ƴa tama bazata zuana da kishiya ba, wannan alƙawarine na ɗaukar mawa kaina" still cikin ɓacin rai Hajiya Furaira take maganan...
Cikin matsanancin ɓacin rai Salima ta juya ta koma ɗakinta, ji takeyi zuciyarta na tafarfasa, kamar ita ace ta haɗa miji da wata, sam bazai yi wuba, lallai ko da mahaifiyarta bazatayi wani abu ba yakamata ace ita tayi, wayarta da mayafinta ta ɗauka, a fusace ta fice daga ɗakin nata, tana son Sadeeq tun ba yau ba, zata kuma iyayin komai akan sa.
Ɓangaren Dr Sadeeq kuwa tuni yasoma haɗa mawa Zahrah kayan lefe, sosai yake iya ƙoƙarin sa wajen ganin yasanya duk wani abu da yasan zai burge Zahrah.
Ɓangaren Hajiyarsa da Aunty Raliya kuwa, sam basu wani damu da auren ba, hakanne ma yasa suka tura masa aniyarsa, su dai sunfi bada ƙarfi wajen ganin Salima tasamu abun da take so, yayinda Hajiya Furaira ta kafe kan cewa ƴarta bazata auri Sadeeq ba matuƙar ba'a fasa aurensa da Zahrah ba, ranta bai ƙara ɓaci ba ma, sai da taji labarin cewa Zahrah ƴar talakawa ne, sannan kuma bata da wani galihu, ai take ranta yaƙara ɓaci, tace sam bata amince ba, yayinda Salima kuwa ta kafe akan cewa lallai sai ta ruguza auren da Dr.Sadeeq yake nema bayan nata.
Gaba ɗaya Zahrah ta ruɗe, zuwa yanzu wanda yake turo mata saƙo ya uzurawa rayuwarta, a yanda ta fahimta shine duk inda tayi yana biye da'ita, wani babban tashin hankali daya kunnu mata shine, sabbin saƙonnin da yafara turo mata a cikin wayarta, tagama iya hasashenta ko zata gano a ina yasamu number'n ta amma takasa samun daman sanin inda yasamu number'nta, gaba ɗaya yanzu salon saƙonnin nasa sun sauya salo, domin kuwa yanzu saƙon kalamai yaƙe turo mata masu daɗi, wanda kuma duk rabin saƙon yaba kyawunta yake, babban abun daya ƙara ruɗata shine irin maƙudan kuɗaɗen dayake turomata ta waya. sannan kuma idan ta gwada ƙiran number'n da yake turo mata saƙo dashi, bata samu domin da zaran taƙira wayan za'ace mata a kashe wayar take, hakan yasa tafara tunanin cewa kodai gamo tayi...
Ɗan ƙara wayarta tayi alamar shigowar saƙo, take taji gabanta yafaɗi, zuwa yanzu har tsoro take taji wayarta tayi ƙara, domin kuwa tasan idan har wayanta tayi ƙara to ko ƙiran Dr.Sadeeq ko kuma saƙon mutumin da batasan shiba...
Number'n nan ce dai, da aka saba turo mata saƙo dashi, yauma saƙonne aka kuma turowa..
_Tunaninki ya hanani sukuni My Zahrah, ina fatan dai kina lafiya, ina kuma fatan zuwa yanzu kindaina tsoro da kuma mummunan tunanin da kikeyi akaina, kina da kyau My Zahrah, komai naki me kyau da burgewa ne._
Abun da saƙon ya ƙunsa kenan.
Zahrah ta karanta saƙon nan yafi sau biyar, kwata kwata ta kasa fahimtar abun da saƙon yake nufi.
Saurin yin Deleting saƙon tayi haɗe dayin switch off ɗin wayar tata, bazata taɓa yarda wan nan mai saƙon ya haukata mata tunanin ta ba, yazama dole a gareta ta sanja layi.. Kwanciya tayi lamo tana mai addu'an Allah yasa bacci ya ɗauketa. domin bacci ne kaɗai zai kawo mata sauƙi a zuciyarta.
Zaune suke dukansu a ɗan madai dai cin tsakar gidan nasu, domin dama idan dare yayi sukan zauna a tsakar gida su ɗan taɓa hira, haka al'adarsu take..
Wani yarone yashigo cikin gidan bakinsa ɗauke da sallama, haɗa baki sukayi wajen amsa masa sallaman.
"Wai ana sallama da mai gidan nan" yaron yafaɗa.
"To kace inazuwa" Baffa yafaɗi haka yana ƙoƙarin miƙewa tsaye.
Kusan tare suka fita shida yaron sai da Baffa yaji wani irin faɗuwar gaba sakamakon wasu irin danƙara danƙaran motoci guda biyu da yagani fake a ƙofar gidansa.
Ja Baffa yayi ya tsaya turus yana me mamakin ganin waƴan nan rantsatstsun motocin a ƙofar gidansa, "Allah yasa da alkhairi suka zo" Baffa yafaɗi haka a cikin zuciyarsa.
Buɗe murfin motar Alhaji Ma'aruf yayi haɗe da sako ƙafarsa waje.
Sake waro idanu Baffa yayi haɗe da kafe Alhaji Ma'aruf dake ƙoƙarin fitowa daga cikin mota da ido.
Fuska cike da annuri Alhaji Ma'aruf ya ƙaraso wajen Baffa, haɗe da miƙa masa hanu alamar su gaisa.
Cikin ɗari ɗari Baffa ya ɗago hanunsa haɗe da miƙamawa Alhaji Ma'aruf suka gaisa.
"Inafatan kaine ma mallakin wannan gida, kuma Baffa ga Zahrah?" Alhaji Ma'aruf ya tambaya.
Saida Baffa yaji zuciyarsa tayi tsalle sakamakon jin an ambaci Zahrah, Allah yasa ba wani abun Zahrah tajawo musu ba.
"Eh nine ranka ya daɗe, Allah yasa lafiya?" cikin dar ɗar Baffa yafaɗi hakan.
Murmushi irin nasu na manya Alhaji Ma'aruf yayi haɗe da kallon Baffa..."Nazo da magana mai mahimmanci, inaga zaifi kyautuwa kabiyoni cikin mota mu tattauna, don maganar bata tsaye bace"
Kallon Alhaji Ma'aruf Baffa yashiga yi, haɗe da excort ɗin da suke bayan Alhaji'n, tabbas Alhaji Ma'aruf baiyi masa kama da irin mugayen mutanen nan ba, domin daga ka gansa zaka fahimci cewa dattijon arziki ne, hakanne yasa Baffa bai musa masa ba, yabisa zuwa mota..
Acikin mota kuwa bayan sun sake gaisawa, Alhaji Ma'aruf yayi gyaran murya haɗe da cewa...
"Sunana Alhaji Ma'aruf, kasancewar dare ne yasanya ka kasa shaida fuskata, domin ni ba ɓoyayyen mutum bane. Nazo gare ka ne domin nemawa ɗana Auren Ƴar Wajenka Zahrah, ina fatan bazaka watsa mini ƙasa a ido ba".......
(Kowani amsa Baffa Zai bawa Alhaji Ma'aruf🤔)
*19/December/2019*
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
*Wattpad user name fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
Written By*
*Phatymasardauna*
_(shalelen kainuwa)_
*Dedicated To MY Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*(Wannan page ɗin gaba ɗayansa ƙyautane a gareku Maman Teemah, and Ummu Fateema, inaƙaunarku Momy's ɗina)*
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 63 to 64*
Shirune yashiga tsakanin Baffa dakuma Alhaji Ma'aruf, bakomai ne kuma yasa hakan ba face nazari da Baffa yashigayi, lallai wannan abu da mamaki yake, neman aure mace ɗaya duk alokaci guda.
"Naji kayi shiru, Allah yasa dai ba wata matsala bace ta faru" Alhaji Ma'aruf ya faɗa, domin ko kaɗan baya fatan wani abun da zai zo ya gifta har ya katsewa Zaid cikar burinsa..
Gyara zama Baffa yayi haɗe da sauƙe ajiyar zuciya..
"A gaskiya Alhaji bazan ɓoyemaka ba, yanzu haka na bada auren Zahrah ga wani, wanda kuma tariga da ta aminta dashi, sai dai bazan yi saurin yanke hukunci ba, idan har Zahrah ta aminta dashi ɗan wajen naka, shikenan, saboda ni bazan mata dole ba, duk wanda takawo tace shitake so, to shi zan aura mata, amma kuma a iya sanina babu wani wanda yake zuwa wajenta, bayan likita'n dana bashi aurenta, sai dai kuma bansan shi ɗan wajen naka a ina yaganta har yaji yanada burin aurenta ba"
Ɗan jim Alhaji Ma'aruf yayi haɗe da sauƙe ajiyar zuciya. Lallai yakamata yayi duk abun da zaiyi, domin shikansa yanaso Zaid yayi aure, amma kuma yasan cewa nema cikin nema haramunne, tunda gashi har shi Baffan yarinyar ya ri ga daya shaida masa cewa yabada auren yarinyar ga wani, yazama dole suyi haƙuri kenan.
"Naji maganarka Malam Hayatu, nakuma gamsu, amma bayar da aurenta ga wani, ae bashi yake nufin anɗaura aurenta ba, koda yaushe ra'ayin mutane yana iya sanjawa, saboda haka zanbaka dama kayi tunani mai kyau" Alhaji Ma'aruf yafaɗi haka bayan yaciro wasu maƙudan kuɗi a cikin aljihun rigarsa ya ɗauramawa Baffa akan cinyarsa..
Ware idanu Baffa yayi sakamakon ganin maƙudan kuɗin da Alhaji Ma'aruf yaɗaura masa akan cinyarsa, badai yana nufin duk nasa bane.
Murmushi irin na manya Alhaji Ma'aruf yayi haɗe da cewa "Kada kadamu bawai nabaka kuɗinnan bane,don ka bawa ɗana auren ƴarka ba, nabaka ne kawai saboda shi meyin alkhairi ako da yaushe baya rasawa"
Cikin sanyin jiki Baffa yayi masa godiya haɗe da buɗe murfin motar yafita, zuciyarsa cike da ɗunbin mamaki...
Baffa na fita daga motar Alhaji Ma'aruf yamawa driver'nsa umarni akan cewa su tafi, aikuwa ba ɓata lokaci drivern yatada mota..
Saida suka ɓacewa ganinsa kafun Baffa ya iya ɗauke idanunsa daga kansu, kuɗin dake hanunsa yashiga juyawa, "Lallai wannan mutumi yanada ihsani, amma kuma yazo da babbar magana, da ace yanada dama to da a yanzu yabawa ɗan Alhaji Ma'aruf ɗin auren Zahrah, to saidai kuma yanzu ya saduda, sakamakon wa'azi mai tsoratarwa dayaji akan cutar da maraya, da kuma irin azabar da za'amawa mai cutar da maraya, tundaga wannan lokacin yaƙudurta aransa cewa bazai sake cutar da Zahrah ba, yanzu ma dolensa zai bata zaɓi, domin ita zatayi zaman auren ba shiba...
Yanashiga gida Inna da takasa zaune takasa tsaye, ta ƙaraso wajensa da sauri tana me cewa "Lafiya naga ka jima, har nafara jin tsoro naɗauka irin mutanen nan ne masu garkuwa da mutane suka kamaka, domin na leƙa naga wasu fankama fankaman motoci a waje"
Harara Baffa ya wurgamata, haɗe da jan tsuka "Bazaki taɓa sanja halinki ba ko Salame, wato ke dai koda yaushe kai da kuma idanunki sunaga ƙofar gida, kullum cikin leƙe kike, wato dai har dare ma yanzu leƙe kikeyi, Allah ya kyauta" yafaɗi haka yana mai nufar hanyar ɗakinsa...
Fuska Inna ta ɓata haɗe da kafe aljihunsa da idanu, domin kuwa tuni idanunta sun ƙyallaro mata tudun da aljihunnasa yayi, ƙwafa tayi haɗe da rufa masa baya, koma mene sai
taje taganema idanunta, idan ma abuncine aci da'ita..
Sake gwalo idanu Inna tayi, ganin kuɗin da Baffa ya'aje akan gadonsa, "Malam kace farar fita kayi, a shema baƙin arziki ne, nayi musu mummunar fahimta, ae irinsu muke fatan suta zuwa" washe da baki ta ƙare maganar...
"Akwai matsala Salame, amma jeki ƙiramin Zahrah" Baffa yafaɗa bayan yayimawa kansa mazauni, a bakin gadonsa.
"Yanzu kuwa" Inna tafaɗa tana me fita daga ɗakin..
Zahrah ce zaune akan gadonta, game take bugawa a cikin wayarta, da'alama dai game ɗin yayi mata daɗi, domin kuwa ita kaɗai sai murmushi take.
Inna ce tashigo cikin ɗakin haɗe sa shaida mata ƙiran da Baffa keyi mata, haka nan taji gabanta yafaɗi. Tare suka fito da Inna, dukansu suka ɗunguma zuwa ɗakin Baffa'n...
Gyara zama Baffa yayi haɗe da maida kallonsa ga Zahrah, wacce ta duƙar da kanta ƙasa.
"Bayan Likita akwai wani wanda kikasan yanasonki, ko kuma kika basa dama ya turo magabatansa wajena?" Baffa yatambayeta cike da kulawa.
"A'A Baffa bana mu'amala da kowa sai likita, bankuma bawa kowa izinin zuwa wajenka ba" tafaɗi haka cike da girmamawa, duk da kuwa cewa kanta ya ɗaure da jin tambayar da Baffa'n yayi mata...
Kai Baffa yajinjina haɗe da cewa "Ƙiran da akai min ɗazu wani ne yazo nemawa ɗansa aurenki, shine nayi tunanin ko kinsan da zuwansa"
Wani irin bugawa Zahrah taji ƙirjinta yayi, har batasan sanda ta ɗago da idanunta ta kalli Baffa ba.
Baffane yacigaba da cewa "Bansan ko su ɗin suwaye bane, amma ban ɓoyemusu komai ba, nasanar dasu cewa nabada aurenki ga wani, amma mahaifin yaron yace yabani lokaci nayi tunani, saboda hakane ma naƙiraki domin ni bazan miki dole ba, zanbaki dama ne ki zaɓi wanda kikeso"
Take idanun Zahrah suka kawo ƙwalla, sakamakon jin wani baƙon al'amari dayake shirin kunno kansa cikin rayuwarta.
"Kinyi shiru, ki kwantar da hankalinki bazan miki dole ba Zahrah, kema kina da ƴan ci, zan kuma baki ƴancin ki, sai dai abun da nakeson sani shine wanene yaron nasa, saboda bai yiwuwa a haɗaki aure da wanda bamusani ba, amma idan ke kinsan sa shikenan ba damuwa"
"Bansan saba Baffa, kuma ma koda nasansa bazan aminta dashi ba, saboda idan nayi haka ban yi mawa Dr.Sadeeq adalci ba" Zahrah tafaɗi haka cikin sanyayewar murya...
"Adalci, kaji shirmen banza don Allah Malam, wani adalcine yarage miki, wanda yawuce ki kai kanki cikin arziki kicisa yanda yakamata, saidai ko inkuma baƙin ciki kike mana"
Inna ta tsomo bakinta cikin maganar batare da angayyaceta ba...
"Tashi kije Zahrah, idan suka sake zuwa zan sanar dasu cewa hakan da sukeso bazai yi wuba" Baffa yafaɗa, yana mai wurgamawa Inna harara..
Cikin rashin ƙwarin jiki haɗe da ɗaurewar kai Zahrah tabar ɗakin.. Haushin Zahrah da Baffa ne yacika zuciyar Inna, amma ganin yanda Baffa yahaɗe fuska bai bata damar yin ƙorafi ba yasanya itama tafice daga ɗakin tana me ƙananan maganganunta wanda ita kaɗai tasan metake cewa..
Zama Zahrah tayi jigum haɗe da zurfafa tunanin ta, ba'abun dake bata mamaki da ɗaure mata kai, kamar neman aurenta da Baffa yace anzo anyi, "To waye zai zo neman aurenta batare da saninta ba? batare da ta kuma sanshiba, lallai koma waye baisan meyafaru da'ita ba, domin tasan daya sani, da baiyi gigin turo magabatansa nema masa aurenta ba" Haka dai tayita saƙawa da kuncewa har bacci ya ɗauketa......
Cike da tsananin mamaki Zaid yake kallon mahaifinsa, sakamakon ji da yayi mahaifin nasa nacewa "Wai anbada auren Zahrah'nsa ga wani" " Anya kuwa gidan su Zahrah Dad ɗinsa yaje? kodai yayi mistake ne yaje wani gidan amadadin nasu Zahrah?" duk wannan tambayar kansa ya mawa.
"Inaga zaifi kyautuwa kanemi wata My Son, domin kafasan nema cikin nema haramunne" Alhaji Ma'aruf ya faɗa yana me kallon ɗan nasa.
"Inaga ba gidansu kaje ba Dad,
domin ni nasan Zahrah tawace, baza'a bawa wani ita ba bayanni" Zaid yafaɗi haka bayan yayi sipping holandia milk ɗin dake aje cikin glass cup ɗin dake gabansa.
Kallon mamaki Alhaji Ma'aruf, yashiga yi mawa Zaid, sakamakon jin abun daya faɗa.
Baisan me yake shirin faruwa da ɗansa ba, amma tabbas ya hango wata irin soyayya acikin idanun Zaid ɗin me matuƙar zafi, wanda Zaid shikansa baisan da'ita ba...
"Akwai matan aure dayawa Zaid, zaifi kyau ka zaɓi wata, koda a cikin ƴan uwankane" Alhaji Ma'aruf yafaɗi haka cikin lallashi.
Murmushi kawai Zaid yayi haɗe da kallon mahaifin nasa...
"Kai mahaifinane saboda haka bana iya ɓoye maka komai, a gaskiya banjin zan iya zama da wata daban, idan ba Zahrah ba, zanyi komai da kaina kawai" yafaɗi haka yana me miƙewa tsaye... Da kallo kawai Alhaji Ma'aruf yabi sa dashi har ya fice daga cikin falon nasa. Ajiyar zuciya yayi haɗe da cewa "wataƙila idan kuɗi na magani, to zasu maya Zaid, ta hanyar samo masa auren Zahrah"
(hmm bakomai ake nema a samu ba, bakuma komai kuɗi yake iya saya ba)
Kai kawo Zaid yashigayi a tsakiyar tankamemen aljannar duniyar falonsa, gaba ɗaƴa yarasa me yake masa daɗi, shin maganar da Dad ɗinsa ya faɗa masa cewa anbada Zahrah, gaskiya ne kokuwa Dad ɗinnasa ne yayi mistake wajen gano gidan su Zahrah, dudduniya babu wani mahaluƙi daya isa yimasa shamaki da muradinsa, lallai lokaci yayi daya kamata ya bayyana kansa gareta, baidamu da yanda zata ɗaukesa ba, shidai burinsa kawai shine ya mallaketa amatsayin matarsa, lallai yanzune zai gudanar da babban takunsa, sannan kuma yazama dole yagano bayanshi wayake bibiyan Zahrah, har ake yunƙurin aura masa ita, dole yagano wannan, domin yayi imani cewa Zahrah tasa ce...
***
Fitowarsu daga lecture kenan, wayarta tayi ƙara alamar shigowar saƙo,, ko kaɗan batayi mamaki ba, domin zuwa yanzu tasaba da saƙonnin da'ake turo mata batakuma san waye yake mata hakan ba.
Ajiyar zuciya ta sauƙe bayan ta gama karanta saƙon, yau madai kalamaine masu tsayawa a zuciya, ɓoyayyen mutumin nata ƴarubuta mata, sai dai kuma duk sanda ya turo mata da saƙo, idan takaranta kalaman sukan tsaya mata arai suna kuma yawan yi mata yawo a ƙwaƙwalwarta, koda sau ɗaya ne bata taɓa tunanin mayar masa da amsa ba, amma hakanan taji yau tanason tambayarsa ko shiɗin waye.
"Waye kai?" Abun da tarubuta tatura masa kenan.
Zaid dake kwance cikin wata luntsumemiyar kujera yana sipping wine yaji wayarsa tayi ƙara alamar shigowar saƙo, ɗaga wayartasa yayi yaduba, murmushinsa me kyau yayi bayan yagama karanta tambayar nata..
"Kinason ganina?" shima yamayar mata da tambaya, tahanyar tura mata saƙo.
Zahrah na karanta saƙon tasoma typing kamar haka...."Mezai hana idan zaka bayyana kanka" tana gama rubutawa tayi sending..
"Kishirya ranan friday 8:00 pm zankawomiki ziyara, ina fatan zakiji daɗin ganina, sannan zan taho miki da kyakkyawan surprise" yana tabbatar da cewa saƙon ya isa zuwa wayarta, yayi switch off na wayarsa, sake gyara kwanciyansa yayi ajikin kujeran, haɗe da lumshe idanunsa, jiyake mararsa tana yi masa ciwo, kusan kwana uku kenan da yake fama da wannan ciwon maran, hakan kuma yasamo asali ne da wata irin sha'awa da ta damesa, sai alokacinne ma yake tuna cewa yajima baiyi sex ba, lallai akwai abun da yake damunsa, Zaid ɗin da baya iya kwana ɗaya baiyi sex da mace ba, wai shine yanzu yake iya kwanaki batare da yayi sex ba, shida mace ɗayama bata isan sa, amma sai gashi, yau ɗayan ma, yakasa nutsuwa yakusanceta, lallai yanzu kam yayarda da cewa akwai abun dake damun jiki da zuciyarsa....
Ɗan jim Zahrah tayi bayan tagama karanta saƙon nasa, idan bata mantaba yau Tuesday kenan saura kwana biyu jumma'a tayi, lallai tanaso taga wanene wannan wanda yaɗau lokaci yan ɓata tunaninta, ta wani ɓangare na zuciyarta kuwa, ji takeyi tamkar akwai wani gagarumin abu dazai faru da'ita, yayinda idan ta tuna aurenta da Dr.Sadeeq saitaji ta zama wani iri da'ita, bakuma aurenta da Dr. ɗinne bataso ba, a'a kawai dai tanaji ajikinta kamar basu dace da juna ba ita dashi...
Dariya sosai Salima tashiga yi, sakamakon labarin da ƙawarta kuma aminiyarta Laura tabata yanzun. Wani irin daɗi taji haɗe da sanyi acikin zuciyarta, gaba ɗaya labarin Zahrah Laura ta kwashe ta sanar da Salima, wanda Laura ta samo asalin labarin Zahrah ne daga bakin wata Asma da take unguwarsu Zahrah'n kuma har school ɗinsu ɗayama da Zahrah..
"Dama akan sauran wani Doctor yake wulaƙantani hadda jamin aji, hmm lallai kuwa bazanyi kishi da mai aji bama ballentana marar aji" Salima ta faɗi haka cike da kunfar baki...
"Ae magana taƙare Salima, kamar yanda na faɗamiki, tashi kawai zamuyi muje hargidansu, muci mata mutunci mukuma gargaɗeta da tafita hanyar Doctor Sadeeq" Laura tafaɗi haka cike da son zuga Salima.
"Gaskiya ne nima ina bayan maganarki Laura" wata wacce take zaune gefen Laura ta faɗi haka, tana me taɓe baki..
Kallonta Salima tayi haɗe da cewa "Shiyasa nake sonki ƙawata, bakida wasa, wajen sawa ayi rashin mutumci, idan kinshirya muje gidan nasu yanzu, domin akan Doctor sai inda ƙarfina ya ƙare" Salima tafaɗi haka tana maitashi daga zaunen da take.
Motar Salima suka shiga su duka ukun yayinda Laura ke tuƙasu, domin itace jagoran tafiyan kasancewa har gidansu Zahrah ta sani, saboda tasa Asma ta nuna mata....
Zahrah ce zaune a tsakar gida bisa kan tabarma, kwanon abincine aje a gabanta, gaba ɗaya ta kasa tsayawa taci abincin yanda yakamata domin kuwa yau Thursday gobe ne kuma haɗuwarsu da mutumin dayake ɓoye mata kansa, duka nutsuwarta baya gareta, hakanan takejin babu alkhairi a haɗuwarta da mutumin...
Wani irin bangaja da aka mawa ƙofar gidansu shiyasanyata ɗago kanta takai kallonta zuwaga ƙofar gidan nasu..
Wasu tsalan tsalan ƴan mata su uku ta gani, tsaye ko wacce ta kafa makeken glass akan idonta, yayinda suke taunar cingam cike da iyawa haɗi da salo......
(Manage please👏 rasuwa akai mana shiyasa banyi posting da wuri ba)
*21/December/2019*
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
*Wattpad user name fatymasardauna*
10:4 pm
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
_(shalelen kainuwa)_
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*(Wannan page ɗin gaba ɗayansa kyautane a gareku Members na BENEFICIAL WRITERS ASSOCIATION haƙiƙa kuɗin na daban ne, sannan kuma kuna da ƙoƙari sosai da sosai wajen sanbaɗomana comment, muna godia Allah yabar ƙauna)*
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 64 to 65*
Baki da hanci Zahrah ta sake tana kallon waƴan nan ƴan matan da suke tsaye suna me yimawa cikin gidannasu kallon wulaƙanci haɗe da ƙyama..
Cire glass ɗin dake idanunta Salima tayi, haɗe da watsamawa Zahrah wani irin kallo mai ɗauke da mugun tsana, cike da ƙyama ta furzar da yawu, haɗe da kallon Laura "Itace wan nan?" Salima ta tambaya tana me nuna Zahrah da hanunta cike da taƙama.
"Eh itace ƴar matsiyata" Laura ta faɗa tana yanatsina fuska.
"Lafiya kuwa bayin Allah? su waye ku? Zahrah ko kinsan sune?" Inna da fitowarta a ɗaki kenan ta tambaya, Tana me mamakin ganinsu haɗi da aljabi.
"Ba alkhairi bane ya kawomu, saboda baku kai matsayin da zamuzo muku da alkhairi ba, sunana Salima, nazone domin najawa wannan matsiyaciya kuma karuwar ƴar taku kunne, koda wasa Doctor Sadeeq basa'an aurenta bane, saboda yawuce ajin macen da taraba mutuncinta a titi" takawa taci gaba da yi cikin isa harta ƙarasa gaban Zahrah, da ta kasa ko motsi... "Banzo danna cutar dake ba, amma tabbas idan kika sake nakuma dawowa cikin gidan nan to zanyi miki babban illa, rabuwa dashi zai fi miki, idan kuma kika ƙi, hmmmm zakisan cewa bakin rijiya bawajen wasan makaho bane, bake kaɗaiba, hatta tsohon da yake riƙe dake sai ya ɗanɗana" Salima tana kai ƙarshen zancen nata tamaida glass ɗin ta dake riƙe a hanunta, haɗe da kallon su Laura "Muje" tace dasu, babu musu kuwa suka rufa mata baya, suna tafiya suna kareraya...
Tamkar statue haka Zahrah tayi ƙasaƙe tana kallonsu, harsuka fice daga cikin gidan.
Sallallami Inna tashiga yi haɗe da tafa hannuwanta duka biyu, "Lallai kuwa wa ƴan nan ƴan iska masu jajayen fuskar suncika marassa ta'ido, rashin kunya har cikin gida" Inna tafaɗi haka cike da mamaki.
Kai kawai Zahrah ta girgiza, haɗe da jawo kwanon abincinta ta ci gaba da ci, batare da ta tankawa Inna da take ta ɓaɓatu ba,, sai dai kuma sosai maganganun Salima suka daki zuciyarta, har wani ɗaci takeji a cikin maƙoshinta.. Tura abincin takeyi amma jinsa take tamkar maɗacin dayafi kowanne ɗaci, har wani zafi takeji a ƙirjinta. Tana gama cin abincin, ta kora da ruwa, haɗe da tashi kai tsaye tanufi ɗakinta.
"Karuwa" sunan da Salima taƙirata dashi yafiye mata komai ciwo, tunda take a duniya ba'a taɓa ƙiranta da sunan karuwa ba, sai a yau ɗin, wasu irin zafafan hawayene taji sunshiga gangarowa daga cikin idanunta, durƙushewa tayi a ƙasa haɗe da soma rusa kuka, filla filla kalaman da Salima ta faɗa mata suke dawowa cikin kanta, koda wasa bata taɓa tunanin za'afaɗi kalma na ɓatanci masu muni irin haka akan ta ba.
"Kacuceni Zaid, Kacuceni, me yasa ka aikata haka agareni, shin koda sau ɗaya ne bakayi tunanin yanda rayuwata zata kasance ba, bazan taɓa yafe maka ba Zaid har kuwa nakoma ga mahaliccina" cikin kuka ta ƙare maganar, domin kuwa sai yau tasake tabbatar da cewa Zaid ya cuceta, takuma ƙara jin matsanancin zafi dakuma ciwo akan fyaɗen da Zaid yayi mata.. Abu kamar wasa haka Zahrah tayita kuka tamkar ranta zai fita, sai gashi cikin mintuna ƙalilan ciwon kai yakawomata ziyara, wanda har sai da yakaita ga kwanciya.. Ƙiran Dr.Sadeeq ne yashigo cikin wayarta amma tanaji tana gani takasa picking call ɗin har wayan ta tsinke, taƙi ɗaga wayan ne kuma don bataso yafahimci cewa tana cikin damuwa. Wani ƙiran nasa ne kuma yasake shigowa, still dai har wayan ta katse, Zahrah bata ɗauka ba, domin har yanzu bata dawo cikin nutsuwarta ba.. Ƙira na uku ne yakuma shigowa cikin wayarta ta, ƙoƙari tayi wajen ɓoye damuwarta haɗe da ɗaukan wayar ta kara akan kunnenta..
Ajiyar zuciya Dr.Sadeeq yasauƙe sakamakon ji dayayi ta ɗaga wayan.
"Wani irin laifi me girma na'aikata haka da aka ƙi amasa wayata?" Dr.Sadeeq yatambaya.
Cikin sanyin murya Zahrah tace dashi "Bana kusa ne shiyasa"
Wata ajiyar zuciya yakuma sauƙewa cike da kulawa yace "Naji muryarki ta sauya ina fata dai kina halin lafiya?" cikin kulawa ya ƙare maganar.
"Lafiya ƙalau" tabasa amasa a taƙaice.
"Yakamata nazo muyi magana domin inaso nasan irin shirye shiryen da zakiyi, idan lokacin auren mu ya gabato, kinsan yakamata ace anfarayin komai akan lokaci, yanzu ina tuƙi ne idan na tsaya zanƙiraki"
"To" kawai ta'iya cewa dashi, har ya katse ƙiran.
Tanacire wayar akan kunnenta saƙo yashigo cikin wayar.
"Nakan ji wani iri a jikina idan har kina cikin wani irin yanayi, ki daina sa kanki a damuwa, saboda zaki iya cutar da zuciyarki, nikuma bazan so haka ba, saboda kece muradina" abun da saƙon yaƙunsa kenan..
Tsuka Zahrah tayi bayan tagama karanta saƙon, haɗe da kashe wayarta ta baki ɗaya, jira take kawai Allah yakaita gobe taga wayane yake raina mata hankali haka, daga goben kuma zata takamawa komaye birki, domin kuwa ko ma wayene bazai taɓa burgeta ba, zuwa yanzu babu wani ɗa Namiji da zaiyi tasiri acikin zuciyarta.
Zaid ne kwance akan makeken gadonsa wanda yasha bedsheet na alfarma, kwanciyar nan yayi irin wanda ba kyau, wato rufda ciki, wata doguwar takarda ne riƙe a hanunsa, wanda take ƙunshe da duk wani abu daya ƙunshi Dr.Sadeeq daga kan sunansa aikinsa har zuwa mazauninsa, dakuma a halinsa, kyakkyawan bincike Zaid yasa a kayi masa akan Doctor ɗin, saboda a cewarsa babu wanda ya'isa ya shiga huruminsa, saboda Zahrah tasace shi kaɗai, saboda haka dole ne zaitakawa Dr.Sadeeq birki..
Murmushine ya bayyana akan fuskarsa bayan yasanya duka hanunsa biyu ya shafi sajen dake kwance akan fuskarsa,, shi kansa yaƙosa gobe tayi yaga Zahrah'n sa, duk da kuwa cewa yana biye da duk wani shiga da ficenta, amma kwata kwata baya gajiyawa da ganinta, sam baisan meke damunsa ba, zuwa yanzu yafara kokonto dakuma tunani anya ba wannan abun da yakeji shi ake ƙira soyayya ba kuwa? Idan kuwa harda gaske abun nan da yakeji a game da Zahrah shi ake ƙira soyayya, to tabbas yakamu da so matsananci, sai dai kuma bayida ikon tabbatarwa kansa cewa so yake, hakanne ma ya hanasa gane wanni hali yake ciki, ko da wasa bai taɓa tunanin cewa Zahrah zata ƙisa ba, saboda haka ako da yaushe cikin ƙarawa kansa ƙwarin guiwa yake....
FRIDAY
Rana bata ƙarya, ranan yau ta kasance Friday kuma yaune Ɓoyayyen mutumin ta yayi mata alƙawarin baiyana kansa gareta, sai dai kuma baƙon al'amarin da ta wayi gari dashi yasoma tsinkar mata da zuciya, haɗe da sanyayewar jiki, domin kuwa yau ta tashi tana me jin faɗuwar gaba, haɗe da bugawan zuciya da akai akai, hakan kuwa baƙaramin tsoro yajefata ciki ba, saboda bata taɓa mantawa irin wannan faɗuwar gaban ta dinga ji a ranan da mummunar ƙaddaranta zata rusketa,, sai dai kuma babu abun da yagagari Allah, don haka ta shiga yin addu'o'i acikin zuciyarta, saboda ta samu salama..
Ƙarfe Uku na yammaci de de suka fito a lecture'n ƙarshe da suke dashi na wannan ranan, gaba ɗaya sukuku haka ta wuni a cikin school ɗin, Husnah tayi tambayan har ta gaji, akan ta faɗa mata meke damunta amma tace ba komai, to me zatace mata? ita kanta batasan meyake damunta ba.
Su Husnah ne suka kawota har ƙofar gida, saboda yanzu Dr.Sadeeq aiki yamasa yawa sosai, ga aikin office ga kuma hidiman hada hadan biki, gaba ɗaya baya samun isashshen lokaci, hakan yasa idan sun tashi a school take shiga motar da ake zuwa ɗaukar Husnah su sauƙeta a gida...
Tun azaure take ta kwaɗa sallama harta shigo cikin gidan nasu, amma babu wanda ya amsa mata, hakan yasa ta tabbatar cewa bakowa acikin gidan, har ɗaki ta leƙa amma babu Inna babu alamarta, saboda haka kai tsaye ta wuce ɗakinta. Zama tayi jigum tamkar wacce aka mawa mutuwa, fargaban haɗuwa da ɓoyayyen mutumin nan take, hakanan takeji dama bata nemi ganinsa ba, saboda gaba ɗaya jikinta yagaya mata babu alkhairi a haɗuwarsu, sai dai kuma babu yanda ta'iya tunda ya tabbatar mata da cewa yau ɗin zaizo, ganin da tayi tunani na shirin damunta, yasa ta ɗauko alƙur'ani mai girma tasoma karantawa, saboda hakan yana sauƙar da salama sosai acikin zuciyar wanda yake cikin ƙunci da fargaba....
Tana kai sujjadar ƙarshe ta sallan isha tafashe da wani irin kuka me tsuma zuciya, hakan yafarune kuma saboda ta kasa control ɗin kanta, sosai faɗuwar gaban da takeji yake tsanan ta aduk bayan wasu mintuna.. Cikin kuka tasamu ta sallame sallan isha ɗin, bayan ta gama faɗawa ALLAH buƙatunta, tana me kuma neman sauƙi a garesa, idanunta da suke cike da hawaye ta ɗaga haɗe da maida kallon ta ga yagalgalellen agogon bangon dake ɗakin nata, ƙarfe bakwai da arba'in, saura mintunan da basufi Ashirin ba yaƙaraso kenan, domin ƙarfe takwas yace mata zai zo...
Bugawan da agogo yayi 8:00 pm, yayi dai dai da bugawar zuciyar Zahrah, har saida taji cikinta yabada wani sauti. Kallon agogo takumayi akaro na barkatai, bazata iya tantance me takeji ajikinta ba, tsoro ne kokuma ruɗewa ne, takasa banbancewa.
Idanun Zahrah nakan agogo har ƙarfe takwas da minti biyar, ko ƙyafta idanun ta batayi ba, azahiri agogon take kallo, amma a baɗini ba da idanunta take kallo ba, da ƙwaƙwalwarta take gani, kallon agogon kawai take amma bata fahimta saboda tunaninta ba a kansa yake ba.
Saƙone yashigo cikin wayarta, wanda yayi dai dai da kusan ɗaukewar numfashinta.
"Inaƙofar gidan ku" bakinta na rawa haka takaranta saƙon saikace wanda aka turomata saƙon ranar mutuwarta.
Takai kusan minti huɗu tana sake maimaita karanta saƙon, sai kace wanda aka yo saƙon da wani harshe bana hausa ba, idan kaga yanda take karanta saƙon zakai tunanin bata iya hausa bane, kokuma bata gane abun da saƙon yake nufi ba, bakomai yasa hakan ba kuma face tsoro da taji ya daki zuciyar ta, yayinda gabanta yatsananta faɗuwa, tabbas wannan faɗuwar gaban bana haka kawai bane, lallai dole akwai abun da zai faru da ita, amma kuma yazama dole taje taga wanda yake turomata saƙonni, hanunta na rawa haka ta ɗau hijib ɗinta ta sanya, da ƙyar take iya jan ƙafanta ta fita daga ɗakin...
Inna ta iske zaune a tsakar gida, tana jin radio, "Inada baƙo a waje Inna" Zahrah tafaɗa cikin wata irin murya me rauni. Yanayin yanda Inna taji muryan Zahrah yasanya ta ɗago da kanta ta kalle ta, "Lafiyanki kuwa, meke damunki?" Inna tatambaya cike da mamakin yanda taga jikin Zahrah a sanyaye.
"Babu komai Inna" Zahrah tafaɗi haka tana me nufar hanyar ƙofar fita daga gidan..
Kasancewar akwai wadataccen haske a ƙofar gidan nasu na ƙoyayen wuta wanda maƙotansu suka kukkuna hakan yasa wajen baida duhu, zaka iya hango duk wanda ke tsaye dakuma wanda ke tsugunne, kai harma wanda ke kwance zaka iya ganinsa.
Bugun zuciyarta ne yaƙaru yayinda ƙafofinta suka soma yi mata nauyi, wani mutumi tagani tsaye ajikin wata mota da ta amsa sunanta mota, sai dai kuma yajuya baya, saboda haka bayansa kawai take iya hangowa, sanye yake da wandon jeans black dakuma black ɗin riga sannan kuma akwai hula irin fosin kaf ɗin nan akansa. A hankali take taka ƙafafunta dasuka mata nauyi tanufi inda yake tsaye, yayinda ta sanya hanunta ta cikin hijab ɗinta ta dafe ƙirjinta da takejinsa kamar zai daka tsalle yafito waje..
Abu na farko daya fara hargitsa mata ƙwakwalwa bayan ta isa gareshi shine fitinannen ƙamshin turarensa wanda har gaban abada bazata taɓa manta wan nan ƙamshin ba, wani irin killer smile Zaid yayi bayan yatabbatar da cewa ta karaso gab dashi, fuskarsa ɗauke da murmushi ya juyo zuwa gareta, haɗe da sanya hanunsa ya cire hular dake kansa, take kyakkyawar fuskarsa ta bayyana, wacce take ɗauke da murmushi.
Jikinta ne yaɗauki rawa yayinda idanunta suka ƙara buɗewa take numfashinta yasoma ƙoƙarin ƙwacewa, zuciyarta tashiga duka, ƙafafunta suka ƙage waje ɗaya, yayinda hawaye suka dinga fitowa daga idanunta tamkar anyi ambaliyan su.
Kallon yanda jikinta yake rawa Zaid yayi haɗe da dawo da kallonsa kan fuskarta jefa idanunsa yayi cikin nata. "ZAHRAH!" yaƙira sunanta da wata irin murya me sanyi, sakamakon ganin da yayi kamar cewa bata cikin hayyacinta...
"ZAHRAH" yasake ƙiran sunanta, de de lokacin ne kuma numfashin ta yashiga gudu yana neman ƙwace mata, aikuwa kasa fusgo numfashin nata tayi, lokaci ɗaya numfashinta yayi nasaran fita daga jikinta, take ta yanki jiki tafaɗi warwas a ƙasa, cikin mugun tashin hankali Zaid yayi kanta, haɗe da sanya hannayensa duka biyu ya ɗagota zuwa jikinsa, sunanta yashiga ƙira cikin tashin hankali dakuma ruɗewa, a matuƙar firgice ya sanyata acikin motarsa haɗe da shiga cikin motar da wani irin gudun gaske Zaid yafigi motar ya cillata kan titi... Gaba ɗaya ya ruɗe wani irin gudu yake shararawa baburuwansa da wanda ke gabansa ko bayansa, gaba ɗaya ya ruɗe sunan Zahrah kawai yake ambata, Allah yasa ba zuciyarta ta haɗiya ba..
Matsanancin gudun da Zaid yakeyi har ya wuce hankali, da wani irin gudu yashigo cikin asibitin yayin da ya ɗauko Zahrah caɗak a hanunsa tamkar wata ƴar tsana, haka yashigo da'ita cikin asibitin, ganin haka yasa Doctors sukayo kansa da sauri, hankalinsa a matuƙar tashe ya miƙa ta ga doctors sukayi emergency da'ita kai tsaye.. Taimakon gaggawa likitoci suka shiga bawa Zahrah domin kuwa bako maine ya haifar mata da ɗaukewar numfashin ba, face razana dakuma tsananin firgita haɗi da tsoro da suka rusketa alokaci guda, sannan yanayin yanda zuciyarta ke bugawa, yawuce mizani, idan har zuciyar tata tacigaba da bugawa da sauri sauri haka, tofa lalllai rayuwar Zahrah tana cikin haɗari...
(Niko nace idan Zaid yakashe mana Zahrah zamuci .... ko fans😂)
Iya ruɗewa Zaid ya ruɗe yakasa koda zamane, damuwarsa ɗaya shine Doctors ɗin da suke kan Zahrah, su sanar dashi meke faruwa, lallai idan har Zahrah tasamu wani matsala, to bazai taɓa yafewa kansa ba, sannan kuma babu uban da ya'isa yazauna lafiya, matuƙar likitocin nan suka kasa shawo kan matsalan Zahrah..
Kusan minti talatin likitocin nan sukayi suna ƙoƙarin shawo kan numfashin Zahrah, cikin ikon Allah kuwa sun samu komai yayi dai dai sai dai dole tana buƙatar hutu kodan zuciyarta ta samu salama...
Suna fitowa Zaid yayi kansu, gaba ɗaya idanunsa sun kaɗa sunyi jajur dasu.
Kallonsa ɗaya daga cikin manyan likitocin dasuke kan Zahrah yayi haɗe da dafa kafaɗunsa, "Ka kwantar da hankalinka, komai yayi dai dai, yanzu biyoni office ɗina"
Ba musu balle girman kai Zaid ya bi bayan liikitan.
Kasa zama akan kujeran da Dr ɗin yabasa yayi, babban damuwarsa shine yasan wani hali Zahrah take ciki.
"Nace ka kwantar da hankalinka, kazauna saimuyi magana ko" likitan yafaɗa yana me nuna masa kujera..
"Kaga Doctor bazamane yadameni ba, babban damuwana shine nasan wani hali take ciki" Zaid yafaɗi haka cikin damuwa..
"Zan faɗama ko wani hali take ciki, amma dole sai ka zauna"
Badon Zaid yasoba haka yazauna akan kujera haɗe da sanya duka hanunsa ya dafe kansa.
"Bawani babban abubane yake damunta, akwai abun da yafirgita ta ne, kuma dama anasamun irin haka, sau da dama firgici da tsoro, yakansa mutum yasamu ɗaukewar numfashi naɗan wasu daƙiƙu, amma idan tadawo hayyacinta komai zaidawo dai dai, sai dai kuma tana buƙatar hutu sosai, saboda haka bayau zaku samu sallama ba, dole sai kunjira zuwa gobe da safe, saboda yanzu haka akwai alluran damuka mata kuma suna sa bacci sosai"
Ajiyar zuciya me ƙarfi Zaid ya sauƙe, saboda jin bayanan Doctor da yayi, sun sauƙar masa da nutsuwa "Amma dole sai anan zamu kwana? me zai hana kabani ita mutafi gida, idan yaso saitayi baccinta acan" Zaid yafaɗi haka fuskarsa ɗauke da damuwa.
Murmushi Doctor yayi haɗe da cewa "Hakan bazai samu ba, saboda zata iya farkawa da kowani lokaci, bamu kuma san a wani hali zata tsinci kanta ba, bayan ta farka, saboda haka zamanku anan ɗin zaifi amfani" Doctor yafaɗi haka cike dason gamsar da Zaid.
Kai kawai Zaid yajinjina haɗe da kallon Doctor "Zan'iya ganinta kuwa? sannan kuma inaso akaita ɗaki na musamman konawane kuɗin ɗakin zan biya"
"Wannan ba'abun damuwa bane, zamu kaita ɗaki na musamman sannan kuma zaka iya ganinta, bana ƙira nurse sai a sanja mata ɗaki daganan saikaje ka ganta ko" Dr yafaɗi haka bayan yakara waya akan kunnensa. Cikin mintuna ƙalilan aka sanjawa Zahrah ɗaki inda aka kaita ɗaki na musamman.
Zaid ne tsaye akanta yana me ƙare mata kallo, karo na farko kenan daya farajin wani irin matsanancin tausayin ta acikin zuciyarsa, haɗe da wani shauƙi mai fisgar zuciya. A hankali yaƙaraso dab da gadon nataz haɗe da ranƙwafo da kansa dakuma ƙirjinsa zuwa gaf da'ita, lumshe idanunsa yayi haɗi da kai bakinsa gefen kumatunta ya yi mata kiss, haɗe da sa hanu yashafi gefen fuskarta, "I'm sorry Zahrah!" yafaɗi haka acikin maƙoshinsa. Karo na farko kenan a rayuwarsa daya soma bawa wata mace haƙuri.. Zama yayi a bakin gadon, haɗe da kama hanunta na dama yasanya acikin nasa hanun, a hankali yake murza hanunta haɗe da lumshe idanunsa.
Abu kamar wasa hankalin Inna ne yasoma tashi ganin Zahrah ta kwashe sama da awa ɗaya, a waje batare da ta shigo gida ba, gashi ta leƙa waje bataga ko da me kamannin Zahrah bane, kasa zama inna tayi gaba ɗaya hankalinta a tashe yake, Baffa ne yashigo cikin gidan bakinsa ɗauke da sallama, ko amsa sallaman nasa Inna batayi ba tayo kansa tana cewa "Yau wa Malam gwamma da ka dawo, ko ka haɗu da Zahrah a waje kuwa?"
"Zahrah kuma, ina Zahrah'n take?" Baffa yatambaya cike da mamaki.
Nan Inna tashaida masa cewa tunɗazu tafita bata dawo ba,bayan tasanar mata cewa wani ne yaƙira ta a waje.
Take hankalin Baffa yatashi, domin kuwa Zahrah bata taɓa irin haka ba, har maƙota ya aika ko taje amma aka ce masa bata zoba, take Baffa da Inna suka zuba tagumi, sun marasa ta ina zasu fara, Inna cema takawo shawara akan cewa aƙira Doctor Sadeeq koshine yazo ya ɗauketa, aikuwa Baffa yayi na'am take yadannawa number'n Dr.Sadeeq ƙira, bugu biyu Dr.Sadeeq yaɗaga wayan,, shima bakaɗan ba hankalinsa yatashi jin dayayi cewa wai su Baffa basuga Zahrah ba, ae take yashiga motarsa yataho gidansu Zahrah'n duk da cewa dare yayi...
Kallon agogon hanunsa Zaid yayi a karo na barkatai, ƙarfe 10 na dare kenan, ajiyar zuciya ya sauƙe akaro na uku, haɗe da furzar da iska a bakinsa, kallonsa yakuma mayarwa ga Zahrah, wacce take ta sharan bacci, hakanan yatsinci kansa da sakin murmushi mai sauti, komai na Zahrah me kyaune, tafiyin kyau ma idan tana bacci.
Zama yayi akan wata kujera dake kusa da gadon haɗe da jingina bayansa da jikin bango, lumshe idanunsa yayi tare da cije laɓɓansa sai yanzu ƴake tunanin ya makomarsa zai kasance idan Zahrah tafarfaɗo, domin kuwa ya hango muguwar tsanarsa acikin idanunta.
*23/December/2019*
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
*Wattpad user name fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI!!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 66 to 67*
Lokaci ɗaya hankalin Dr.Sadeeq yayi wani irin mummunan tashi, take ƙwaƙwalwar kansa tashiga charge, a iya tsawon sanin da ya yi mawa Zahrah, ita ba mace bace meson fitar dare, balle har tayi nisa da gida, sai dai kuma abun mamaki gashi yau annemeta an rasa, bayan ko ɗazu suna tare a waya shida ita, baikuma ji wani sauyi a tattare da'ita ba, sai dai kawai muryarta da yaji cikin sanyi. "To ina Zahrah taje?"
Yayi mawa kansa tambayar da bayi da amsa.. "Kodai Zahrah tayi hakane don batason aurena da'ita?" yakuma tambayar kansa, sai da zuciyarsa ta buga, shi kansa yatambayi kansa abun daya faɗar masa da gaba, kai amma Zahrah bazatayi haka ba, saboda ita da kanta ta tabbatar masa cewa ta amince da auren sa, saboda haka bazata bar gida saboda batason auren sa ba..
Kallonsa yamaida ga Inna wacce tayi tsuru tsuru da ido tamkar wata munafuka..."Da tazo fita bakiga wani alaman damuwa ko tashin hankali akan fuskarta ba?" Dr yatambaya cike da kulawa.
"Ƙwarai kuwa da damuwa tafita, saboda kwana biyun nan gaba ɗaya da damuwa take wuni sakamakon waƴansu tsinannun ƴan mata da suka zo, acewar ɗaya daga cikin su wai ita zaka aura Samira take ko Salma oho, haka nan suka zo hargida suka zagemu kaf, tamkar ma zasu mana luguden duka, to tundaga tafiyarsu dai take fama da ƙuncin rai har kawo yau, Allah dai yasa ma basune sukai mata wani abun ba" Inna tafaɗi haka cike da jimami..
Cike da mamaki Dr.Sadeeq yace "What Salima tazo har gidan nan taci muku mutunci?"
"Ƙwarai kuwa ashe dagaske kasanta, tabbas haka tace sunanta wai Salima, ita da waƴansu masu ƙoƙaƙƙun fuska, kamar an gasa nama"
Hanu Dr.Sadeeq yasanya yadafe kansa, lallai idan de har Salima bata ji kunyar zuwa ta zagar masa abar sonsa ba, to tabbas shima bazaiji kunyar zuwa har gidansu yaci mata mutumci ba, Uwa mahaifiyarsa kaɗai ze iya ɗagawa ƙafa akan Zahrah, amma duk wacce tace zata ci mutumcin Zahrah tofa shima zaici nata mutuncin, lallai yakamata ne yafara nemo inda Zahrah take kafun yasan matakin da zai ɗauka akan Salima. Sake dialing number'n Zahrah yayi amma still ce masa ake wai wayar akashe take, tun ɗazu yake ƙiran wayar anacemasa akashe wayarta ta take.. Tunanin ƙiran abokinsa inspector Adam ne ya faɗo masa, saboda yalura lamarin dole sai anshigo da hukuma ciki, tunkan suyi sake lokaci ya ƙure musu. Nan yashiga dialing Number'n inspector Adam amma har wayar ta katse bai ɗauka ba, sake ƙira yayi amma still bai ɗauki wayar ba, tsuka Dr.Sadeeq yayi haɗe da maida wayarsa cikin aljihunsa....
Asibiti
Sai yanzu tunanin halin da iyayen Zahrah zasu shiga yafaɗo masa arai, tabbas yakamata ne yasanar dasu halin da ake ciki, wayarsa yaɗauka haɗe da soma rubuta saƙo, domin bayason wayar da zaiyi yatashi Zahrah a baccin da takeyi, saboda haka gwamma yatura saƙo,a ganinsa hakan zaifi... wata number yaturawa saƙon, batare da yajira amsar da wanda yaturawa saƙon zai basa ba, ya maida wayarsa cikin aljihu.....
Dr.Sadeq ne yadubi Baffa dake a halin damuwa. "Banaje nasanarmawa ƴan sanda, akwai abokina inspector, inaga kawai gwamma naje gidansa na sanar dashi abunda ke faruwa, ina ga zaifi akan tsayuwan damuke" yafaɗi maganar yana me duba agogon dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa, ƙarfe sha ɗaya na dare kenan agogon sa yanuna masa..
Sallaman da sukaji ana kwaɗawa a ƙofar gidan ne yaɗauki hankalinsu, ae ba shiri Baffa da Dr. Sadeeq suka ɗunguma zuwa ƙofar gidan, Inna ma ba'a barta a baya ba ta rufa musu baya.
Wani mutumi me shigar cute baƙaƙe suka gani tsaye a bakin ƙofar gidan, yayinda yarufe idanunsa da tabarau, da ganinsa dai zaka gane irin body guard ɗin nan ne.
"Waye kai?" Dr.Sadeeq yatambaya yana me ƙaremasa kallo.
"Saƙo aka bani nasanar daku cewa Zahrah bata da lafiya, yanzu haka tana asibiti.." baikai ga idar da zancen nasa ba, Dr.Sadeeq yace "Meyasameta sannan kuma a wani asibiti take?" duka tambayar yayisune alokaci ɗaya, kuma
cikin ruɗewa..
"Zaku iya biyoni muje" Body guard ɗin nan yafaɗa yana me nufar wajen da motar da yazo da ita ke fake.
Kallon su Baffa Dr.Sadeeq yayi haɗe da cewa su shigo motarsa subi bayan body guard ɗin, hakan kuwa akayi motar Dr.suka shiga yayinda Dr.yashiga bin bayan motar body guard ɗin. Gaba ɗaya ba acikin nutsuwarsa yake driving ɗin ba. Fargabane cike a zuciyarsa, bayi da wani buri da yawuce yaga Zahrah, yakuma ji meke damunta, har aka kawota asibiti batare da sanin su Baffa ba..
Suna shiga cikin asbitin wannan body guard ɗin ya kalli Dr.Sadeeq haɗe da cewa ya biyosa ciki, su Inna kuwa su jirasa, da su Inna sunso ƙi, amma sai Dr. Sadeeq yace su yarda su jirasu anan ɗin, badon su Inna sun so ba, suka tsaya daga waje... Suna shiga cikin wani corridor guard ɗin yaciro wayarsa, haɗe da karawa akan kunnensa.
"Oga na faɗa musu sunma biyoni, yanzu haka munatare da wani inazaton ɗan uwanta ne, iyayenta kuma suna waje" Abunda Body guard ɗin yafaɗa kenan cike da girmamawa.
Tsuka Zaid yayi sakamakon jin abunda guard ɗin nasa ya ce, shirmen banza, cewa yayi yafaɗamusu bawai ya taho masa dasu ba, to yanzu dayakawosu ina zai sasu, wata tsukan yakuma yi, haɗe da sakai yafice daga cikin ɗakin bayan ya sake rufe Zahrah da bargo..
Cakume kwalan guard ɗin nan Dr.Sadeeq yayi cike da ɓacin rai yace "Bamason iskancin banza kace tana asibiti bata da lafiya, gashi munzo kuma kana ƙoƙarin raina mana hankali, wlh idan wani abu yasameta saina ɗaureka" Cikin ɓacin rai Dr.Sadeeq yafaɗi maganan domin kuwa yulura guard ɗin nema yake ya raina masa hankali....
"Idan har ka'iya ɗauresa, to tabbas zan iya yarda na ƙiraka da suna jarumi !!" muryar Zaid takaraɗe wajen, wanda yake ƙarasowa garesu cikin takunsa na isa..
Kallon Kallo aka shigayi tsakanin Zaid dakuma Dr.Sadeeq, wanda kowannensu da irin manufar tasa kallon.
Sama da 5 minute Zaid da Dr.Sadeeq suka ɗauka suna kallon juna, Zaid nayimawa Dr.Sadeeq kallon tsana, yayinda Dr.Sadeeq kuma kemawa Zaid kallon tuhuma, haɗe da son sanin koshi waye...
Kallon guard ɗin nan Zaid yayi haɗe da taɓe bakinsa cike da isa yanuna Dr.Sadeeq haɗi da cewa "Wan nan kuma waye?" yayi tambayar cike da rainin hankali, yana me ɗage kai sama bayan yajefawa Dr.Sadeeq wani irin kallo..
"Hmm ba buƙatar kasan koni ɗin waye, kai de zaifi kyau kasanardani ko kai waye, amma shishshigi baikamace kaba, saboda bakayi kama da me kula da lafiya ba, kafi kama da masu shiga inda ba'a buƙatarsu" Dr.Sadeeq yafaɗi haka shima yana me ɗauke kansa daga kan Zaid.
Murmushi Zaid yayi haɗe da kallon Dr.Sadeeq daga sama har ƙasa. Kansa kawai ya girgiza "Lallai bana buƙatar kowa, kasan yanda zakayi dasu" Zaid yafaɗi haka ga Guard ɗinsa, haɗe da juyawa yanufi ɗakin da aka kwantar da Zahrah, lokacinsa bana me aikin duba lafiya bane, lokacinsa muhimmine kuma sai me mahimmanci yake bawa...
Hasala Dr.Sadeeq yayi lokaci ɗaya yaji zuciyarsa tana masa zafi, yana da sauƙi amma watarana abu kaɗan ke ɓata masa rai, a zuciye ya juya yafice daga cikin asibitin.. Su Inna dake tsaye a harabar asibitin suna ganinsa sukayo kansa da sauri suna tambayarsa ko Zahrah tana lafiya?
Kasa amsa musu yayi saima cewa da yayi, su shiga mota su yasauƙesu a gida... Bayanda suka iya haka suka shiga cikin motar jiki a sanyaye, saboda sunga gaba ɗaya fuskar Dr.Sadeeq ɗin ɓacin raine shumfuɗe akanta, kenan akwai abun dake faruwa.. Da wani irin gudu yaja motar suka fice daga haraban asibitin...
Gyara zama Baffa yayi haɗe da kallon Dr.Sadeeq wanda da'alama tunaninsa baya jikinsa.
"Meyake faruwa ne Likita? kashiga kakuma fito da ɓacin rai, ina Zahrah'n takene me yasameta?" cikin damuwa Baffa yayi tambayar domin shi gaba ɗaya kansa ya kulle.
Daure zuciyarsa yayi haɗe da cewa "Tana nan lafiya, gobe da safe zamu zo mu ɗauketa"
Ajiyar zuciya Baffa yasauƙe me ƙarfi yagodewa Allah da ba wani abun bane yasamu Zahrah, to amma ae da anbarsu sun ganta...
A ƙofar gida Dr.Sadeeq ya sauƙesu haɗe dayi musu saida safe yaja motarsa yayi gaba..
Suna shiga gida Inna ta kalli Baffa haɗe da cewa "Anya kuwa Malam bakaganin cewa akwai matsala?"
"Bawai gani nakeba, tabbas ma nasan akwai matsala Salame, sai dai fatana ɗaya shine Allah yatsare Zahrah, amma tunda Likita yace gobe da safe zamu koma asibitin, saimu jira zuwa goben idan Allah yakaimu"
"To Allah yakaimu" Inna tafaɗa jiki a sanyaye... Da "Ameen" kawai Baffa ya amsa.
Kamar yanda Zaid ya kwana a zaune, haka Dr.Sadeeq yakwana juyi, gaba ɗaya kansa ya kulle, yarasa meke faruwa, baisan waye wannan gayen ba, amma tabbas yaji tsanarsa fiye da misali, amma babban abun tambayar shine me yasamu Zahrah har aka kawota asibiti? sannan kuma meke tsakaninta da wannan mutumin? tambayar dayake buƙatar a amsa masa kenan, amma babu wanda zai amsa masa, tambayar da ta kuma hanasa bacci kenan...
Ƙarfe bakwai na safe Zaid yasa aka turo masa nurses guda biyu, suka zo dankula da Zahrah, saboda yana buƙatar yaje gida yayi wanka.....
Tamkar amafarki haka fyaɗen da yayi mata yasake dawowa cikin idanu da ƙwaƙwalwarta, wani irin nishi tayi haɗe da sakin ƙara mai sauti, lokaci guda kuma ta ware idanunta da suka cika tab da ƙwalla, da sauri nurses ɗin nan sukayo kanta.
Kallon Nurses ɗin tashiga yi, haɗe da soma ƙaremawa ɗakin da take ciki kallo, tabbas idan ƙwaƙwalwarta bata juye ba, zata iya cewa nan ɗakin asibiti ne sannan kuma waƴan nan dake tsaye a gabanta nurses ne.
"Barkanki da tashi, me kike buƙata yanzu a kawomiki?" ɗaya daga cikin nurses ɗin nan ta tambayi Zahrah cike da kulawa...
"Idanunta dasuke zubar da ruwan hawaye, ta ɗaga ta kalli nurse ɗin haɗe da girgiza kanta alamar batason komai.
Hanun nurse ɗin takamo duka biyu haɗe da fashewa da wani irin kuka me ciwo, da'alama wani abu takeson faɗawa nurse ɗin.. Dai dai lokacin aka turo ƙofar ɗakin aka shigo, Zaid ne yasha adonsa sai zuba ƙamshi yake.
Tsayawa yayi cak daga bakin ƙofar sakamakon ganin yanda Zahrah take kuka..
"Me kukayi mata?" yajefawa nurses ɗin tambaya cikin yanayi na rashin yarda dasu.
"Bamuyi mata komai ba,ranka ya daɗe tashinta kenan tasoma rusa kuka" su duka biyu suka haɗa baki wajen faɗan maganar...
Tamkar wanda aka zuba mata narkakken dalma haka taji sauƙan kalamansa acikin kunnuwanta, rumtse jajayen idanunta tayi, ji takeyi tamkar zuciyarta zata faso ƙirjinta ta fito.
A hankali Zaid yasoma takawa zuwa gare ta.
"Zahrah" yaƙira sunanta dai dai lokacin daya ƙarasa kusa da'ita.. Tunkafun yagama rufe bakinsa yaji sauƙan wani irin gigitaccen mari akan ƙuncinsa, kafun ƙwaƙwalwarsa tagama tantance masa abun dake faruwa, yakumajin sauƙar wani marin aɗaya ɓangaren hagu na kumatunsa..
Kasa koda motsawa yayi saima hangame bakinsa da yayi haɗe da zaro idanu yana kallonta,, Gaba ɗaya marukan nan Zahrah ce ta shararawa Zaid akan fuskarsa..
Yanayin yanda idanunta sukayi ja kace barkono ko attarugu aka watsa mata a ciki.
"Kazone ka sake cutar dani? to gani kacutar dani, gani nace ka cutar dani!!" tafaɗi haka da wani irin tsawa..
Cikin matsanancin kuka Zahrah tasanya hannayenta duka biyu tashiga dukan sa, tako ina Zahrah ke kai masa duka tana kuka, ganin hanu bazai wadarta ba yasanya ta sanya bakinta, tashiga cizonsa a ƙirjinsa, hakama bai mata ba saida ta ɗauki wani ƙarfe dake kusa da'ita tashiga kwaɗa masa a jikinsa tana kuka me tsuma zuciya... Haka Zaid ya tsaya tamkar gunki Zahrah na cizo da yaƙushinsa, gakuma dukan da take kai masa, amma yakasa yi mata komai, yakuma kasa koda motsa hanunsa ne.. dai dai lokacin su Dr.Sadeeq suka shigo cikin ɗakin, turus suma sukayi sakamakon ganin abunda ke faruwa.
"Kasheni zaifi maka sauƙi aduniyar nan, akan ace kabarni da raina, natsaneka, dan Allah ka kasheni!!" Abun da Zahrah ke faɗa kenan tana kuka. Kowa a wajen tsayawa yayi yana kallon ikon Allah, bakomai ke tashi a ɗakin ba face kukan Zahrah, tun tana dukansa da'iya ƙarfinta har ƙarfin nata yasoma ƙarewa a hankali ta sulale zuwa ƙasa, saboda kuka har shiɗewa take...
"Zahrah" Dr.Sadeeq yaƙira sunanta, cikin wata irin murya.. Jin muryan Dr akunnenta yasa taɗago kanta, tana ganinsa tsaye tatashi a guje haɗe da nufar inda yake da sauri tafaɗa cikin jikinsa haɗi da rungumesa ƙa ƙam,wani sabon kukan kuma ta sanya, haɗe da soma buga kanta akan ƙirjinsa..
Duka hannayensa shima yasanya ya rungumeta..
"Wayeshi?" Dr. Sadeeq yayi mata tambayar acikin kunnen ta..
"Shine wanda yaruguzamin rayuwata, shine yarabani da budurcina, shine yayi sanadiyar lalacewar farinciki na!!" Zahrah ta bashi amsa cikin matsanancin kuka, muryarta ko fita batayi da kyau tsabar kuka...
Iya kaɗuwa Dr.Sadeeq ya kaɗu dajin cewa wai wanda yayiwa Zahrah fyaɗe ne tsaye a gabansa, kallon tsana Dr.Sadeeq yashiga yi mawa Zaid..
Zaid kuwa tuni idanunsa sun rune sun zama jajur dasu, jikinsa har rawa yake, koda sau ɗayane baiji zafin duka dakuma marin da Zahrah tayi masa ba, babban abun da yayi masa zafi, shine yanda Zahrah taje jikin wani ta lafe. Tun da yake a rayuwarsa baitaɓa jin abun da yaji a yau ba... Takowa yashiga yi harzuwa inda suke tsaye ita da Dr.Sadeeq, hanunsa yaɗaga domin ya ciro Zahrah daga jikin Dr.Sadeeq. Da sauri Dr.Sadeeq ya tura Zahrah bayansa, haɗe da damƙe hanun Zaid wanda yakawo daniyar taɓa Zahrah..
"Babban kuskuren da zakayi a rayuwarka shine kayarda hanunka yasake taɓa jikinta, kayi na farko yakuma isheka, saboda haka ka kiyaye! " Dr.Sadeeq yafaɗi haka cikin matsanancin ɓacin rai...
Hanun Zahrah yakama haɗe da janta suka fice daga cikin ɗakin, da sauri su Inna ma suka rufa musu baya, saurin dafe saitin zuciyarsa Zaid yayi, wanda yakeji tamkar zatayi tsalle ta fito waje.. Jingina bayansa yayi da bango haɗe da lumshe idanunsa.. Zafi yakeji a ƙirji dakuma zuciyarsa, take wani irin ciwon kai da zazzaɓi me zafi suka sauƙar masa alokaci guda..
Dr.Sadeeq dakansa yasanya Zahrah a mota, wacce har yanzu kuka take, ataƙaice dai tsabar kuka numfashinta har ɗaukewa yake.... Saboda tsabar gudun da Dr.Sadeeq keyi cikin mintuna ƙalilan suka isa gida, kowa acikinsu yana cikin tashin hankali. Inna ce takama Zahrah takaita ɗakinta. Bayan minti kaɗan Inna tafito daga ɗakin Zahrah da sauri. "Likita temaka numfashinta yana shirin ɗaukewa, taƙi daina kukan" Inna tafaɗa a ruɗe.
Dr.Sadeeq yana shiga ɗakin yace inna tabasa ruwa, aikuwa mintuna kaɗan Inna takawomasa ruwa, cewa yayi Inna taɗan basu wuri bamusu Inna tafita a ɗakin...
ɗago Zahrah Dr.Sadeeq yayi haɗe da kai kofin ruwan bakinta, sosai tasha ruwan, take ta soma sauƙe ajiyar zuciya, amma still hawaye na gangara akan fuskarta..
Idanunta dasukayi luhu luhu saboda kuka ta ɗago dasu takalli Dr.Sadeeq, saikuma tasake fashewa da kuka, haɗi da faɗawa cikin jikinsa tarungumesa ƙam, hanunsa duka biyu yasanya shima ya rungumeta, a hankali ya shiga hura mata kunnen ta, saboda hakan zai sa taɗan samu relief, koba komai kukan nata zai tsagaita. Har tsakiyar kansa yakejin kukanta.
Tsawon mintuna 15 yakai yana hura mata kunne, a hankali tasoma rage sautin kukan nata, bayan kamar mintuna 5 yajita shiru, sai sauƙar numfashinta da yake ji akan ƙirjinsa akai akai..
Yana duba fuskarta yaga tayi bacci, hawayene yaji suncika masa idanu, tabbas Zahrah taga ƙaddara a rayuwarta, wani irin tausayinta yakeji me tsanani, tabbas idan ya aureta zai yi iya ƙoƙarinsa wajen ganin ya mantar da ita duk wani damuwa da tshin hankalin da ta tsinci kanta ciki, zai kuma yi iyaka ƙoƙarinsa wajen ganin yabata farinciki me ɗorewa.
A hankali ya kwantar da'ita, haɗe da sanya hanu ya gyara mata dogon gashinta da ya rufe mata fuska. Yajima yana kallonta kafun daga bisani ya tashi yafita daga cikin ɗakin...
Zaune yasamu Baffa da Inna a tsakar gidan sunyi jigum. Yana fita suka tsaresa da ido da'alama bakinsu ɗauke yake da tarin tambayoyi..
Ajiyar zuciya ya yi haɗe da cewa "Tasamu bacci, kada ayi wani abu da zai tasheta, ni zan wuce office anjima zandawo"
Har bakin motarsa Baffa yarakasa bayan sun tattauna wata magana me mahimmanci....
Zaid ne zaune a cikin falon sa dake guest hause ɗinsa, kallo ɗaya zakai masa kafahimci cewa yana cikin tashin hankali, kwalaben giyane zube a gabansa, guda uku daga cikin kwalaben duk ya shanye giyan dake a
cikinsu, ba abun dake gigita masa tunani da ƙwaƙwalwa kamar yanda Zahrah ta nunamasa tsana a fili ƙarara, kallonsa yakai ga hanunsa na dama wanda yake fidda jini, bakomai yajawo hakan ba face ƙarfen da Zahrah ta kwaɗa masa akan hanun,, runtse idanunsa dasuka kaɗa sukai jajur yayi, haɗe da cije laɓɓansa, wani irin zafi yakeji acikin zuciyarsa a duk sanda idanunsa suka hasko masa lokacin da Zahrah taje ta faɗa ƙirjin Dr.Sadeeq, jiyake kamar ya kurma ihu, ko zai samu salama acikin zuciyarsa.... Ahankali yamiƙe tsaye haɗe da nufar ɗakinsa, Da ƙyar yake iya tafiya, saboda abuge yake mankas, kai tsaye ɗan ƙaramin drowern dake kusa da gadonsa yanufa, wani tablet yaɗauko haɗe da ɓarewa kusan guda takwas ya watsa a bakinsa, haɗi da korawa da ruwan swan... Faɗawa kan gado yayi yana me rumtse idanunsa, "Natsaneka" shine kalmar da tafi ɗaga masa hankali aduk cikin kalaman da Zahrah ta faɗa masa. itace kuma kalmar da takeyi masa yawo acikin kansa, cikin wani irin yanayi Zaid yatashi tsaye haɗe da nufar wajen da yake aje kayan shafansa, watsi yashigayi da duk wani abu dake kan dressing mirror ɗin nasa, lokaci ɗaya yayi buji buji da ɗakinsa, yayinda ya fasa gaba ɗaya kwalaben turarensa, har sai da wasu kwalaben suka yankesa a hanu da ƙafarsa, amma don tsabar baƙin kishi ko zafi baiji ba, idanunsa Zahrah kawai suke hangomasa kwance a ƙirjin Dr.Sadeeq. Lokaci ɗaya yaji wani irin juwa ta ɗebesa, harsai da yariƙe bango, a daddafe yaƙa risa kan gadonsa ya kwanta, ji yayi kansa yasoma juyawa, yayinda idanunsa suka soma rufewa, yasoma ganin komai bibbiyu, cikin mintuna ƙalilan idanunsa suka rufe ruf.....
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
*25/December/2019*
*Wattpad user name fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 68 to 69*
Ba'itace ta farka ba sai wajen ƙarfe ɗaya na rana..
A hankali take ware manya manyan idanunta da suka kaɗa suka zama jajur dasu, ba tun yanzu ta farka ba, kawai dai Allah ne be bata daman buɗe idanun nata ba sai yanzu. Tun farkawarta kuwa take cikin tsanani da kuma mamakin mutum mai taurin zuciya irin Zaid, lallai shiɗin yacika ɗan iska kuma shu'umi, duk da irin girman laifin da ya aika ta mata, hakan baisanya yaji ɗar ko kuma shakkan tunkarar ta ba, lallai shiɗin acikin ƴan iska ma daban yake,, haka nan taji gaba ɗaya zuciyarta ta ƙeƙashe takuma bushe, lallai tunda ya nuna mata shiɗin babban ɗan iska ne yakamata ace itama ta nuna masa iyakar iskancinsa, tunda har baiji kunyar tako ƙafa yazo gareta ba, to tabbas itama yakamata tacire kunya, wajen ganin ta koya masa hankali... Sai dai kuma kome zatayi bazata huce ba, saboda iyaka kuma maƙurar cuta Zaid yayi mata, ya mata illa dakuma tabon da bazata taɓa mantawa ba, harta koma ga mahaliccinta kuwa, Zaid ne ya surka mata farincikinta da wani irin mummunan baƙin duhu, ya katse mata jin daɗi da kuma walwalanta, ya lalata mata rayuwa a rana ɗaya, ya ruguza duk wani buri da fatanta, ya gwada mata ƙarfi ya amshi budurcinta cikin yanayi na tozarci, me yafi wan nan ciwo a rayuwar ƴa mace? tasan ƙiyayya amma kuma zafin ƙiyayyar da takeyi mawa Zaid na daban ne, tabbas idan da kisan kai yana da kyau a addinance to haƙiƙa ba abun da zai hanata kashe Zaid san nan kuma itama ta kashe kanta, saboda ƙuncin da ya mamaye zuciyarta ba'irin ƙuncin nan bane da yake fita, lallai ƙuncin zuciyarta dawwa memme ne, sai dai kawai ta roƙi Allah daya sassauta mata.....
Hawayen da suka fito daga cikin idanunta suka gangaro ta gefen kumatunta ta sanya hanu ta share haɗe da miƙewa zaune, babu amfanin ɓata hawayenta wajen fiddasu, yanzu lokaci yayi da shine yakamata yayi kuka ba ita ba. Kayan jikinta tashiga cirewa, haɗe da ɗaura zani akan ƙirjinta kana ta sanya lufaya....
Tana fitowa daga cikin ɗakin nata, Inna ta kalleta haɗe da cewa.
"Yauwa Zahrah kintashi ko? ya ƙarfin jikin naki de?" alokaci ɗaya Inna tajero mata duka waƴan nan tambayoyin..
"Eh Inna na tashi, ko zan samu ruwan zafi inaso nayi wanka ne, gaba ɗaya banajin daɗin jikina, gashi ina so naje gidan su Husnah" tafaɗi maganar tana me ɗan rumtse idanun ta, saboda wani juwa da taji yana ƙoƙarin ɗibanta..
"Kinkuwa ci sa'a yanzu na ɗaura ruwan abincin rana, gashi can inaga yama tafasa saiki ɗiba, amma idan kin ɗiba ki ƙaramin ruwa acikin tukunyar" Inna tafaɗi haka tana meyi mata nuni da tukunyar abincin dake ɗaure kan murhu...
Sosai taji daɗin jikinta sakamakon wanka da ruwan zafi da tayi, bayan ta idar da Sallan Azahar ne, tayi mawa kanta mazauni akan katifarta haɗe da ɗaukan jakar kayan kwalliyanta, mai kawai tashafa sai kwalli da ta zizara a cikin idanunta, ko powder bata shafa ba...
Doguwar rigar atamfa irin me sauƙin kuɗin nan tasanya ajikinta, haɗih da ɗaura hijab akan kayan nata mai kalar blue, yakumayi shige da atamfarta saboda shima atamfar kalan blue ne dashi (shuɗi). Me kyau de me kyaune ko a yaya kuwa, duk da batayi kwalliya ba kuma fuskarta a kumbure take saboda kuka, amma hakan bai hana kyawun fuskarta bayyana ba....
Kallon Inna dake ƙoƙarin sauƙe tukunyar abinci Zahrah tayi, tana me gyara zaman lufayar jikinta tace.
"Inna ni zan je gidansu Husnah, zuwa yamma zandawo insha Allah"
"Wani irin maganar zuwa gidansu Husnah kuma Zahrah? inace ɗazu ɗazun nan muka dawo dake daga asibiti, har kin yi sauƙin da zaki soma fita yawo?"
(Su Inna anfara soyayya da Zahrah fans, lol)
"Kada ki damu Inna yazama dole ne naje, amma bazan jima ba zandawo, dan Allah kada ki hanani zuwa Inna!" Zahrah ta faɗi haka cikin yanayi na nuna zaƙuwa.
"Shikenan tunda kin matsa, ai de kya tsaya kici abinci, idan yaso saiki tafi"
"A'a Inna banajin yunwa yanzu, idan nadawo zanci" takai ƙarshen zancen nata tana me nufar hanyar fita daga cikin gidan. Da kallo kawai Inna tabita harta fice daga gidan...
Tsayawa tayi tana kallonsa cike da mamaki, yayinda shima kallon nata yake cikin yanayi na mamaki...
Giransa ɗaya ya ɗage haɗe dayin murmushi.... "Ashe ma kinyi sauƙi, dana sani da ban bar aikin da nakeyi nazo duba kiba ae" Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana me takowa zuwa wajen da take tsaye.
Kunyarsa ne taji yakamata, sakamakon abun da yafaru ɗazu a tsakaninsu, wato rungumarsa da tayi, wanda tasan hakan ba abu bane me kyau haramunne, mace ko namiji su taɓa mutumin da ba muharrami'n su ba, duk da cewa ba'acikin hayyacin ta ta rungumeshi ba, amma tabbas hakan bai dace ba...
"Yade naga kina wani sunkuyar dakai kamar amaryar da aka kaita ɗakin mijinta" Dr.Sadeeq ƴafaɗi haka cike da zolaya.
Sai alokacin ta'iya ɗago kanta ta aika masa da
hararan wasa,,,,, " Yaushe kazo? kuma me yasa ka tsaya anan baka shiga cikin gida ba?"
"Ummm banjima da zuwa ba, dama inaso amin sallama dake ne, kinga bai dace ace koda yaushe ina shiga cikin gidanku kai tsaye ba, amma sai kuma naga kamar keɗin sauri kike zaki unguwa ko?"
Yaƙare maganar yana me leƙa fuskarta wanda ta sunkuyar da ita ƙasa.
Wasa da yatsun hanunta tashiga yi, haɗe da sanya haƙorinta na sama taɗan datse leɓenta na ƙasa..
"Yajikin naki?" yatambayeta don yaga bata daniyar basa amsan abun da yatambaya.
"Dasauƙi, dama ni lafiyata ƙalau" tabasa amsa a ta ƙaice..
"Eh hakane kuma dama kinsan wani lokacin, idan lafiya tayi mawa mutum yawa, takan iya sawa ya kwanta a gadon asibiti"
Saurin kallonsa tayi sakamakon jin abun da yace, "Lafiyan?" ta tambaya cike da mamaki.
"Eh itafa lafiyan, to baga example akan ki ba" yanayin yanda yayi maganar kaɗai ya'isa ya tabbatar maka cewa zolaya ne kawai ke damunsa..
"Hmm" kawai Zahrah tace haɗi da ɗan satan kallonsa, aikuwa karab suka haɗa idanu, saurin ɗauke nata idon tayi.
Hmm yalura sarai kunyarsa takeji, kuma shiɗin ma kusan hakanne, kawai de dauriya dakuma shariya yafita, shiyasa ya share abun, amma shikansa yasan cewa ya aikata ba dai dai ba, saboda da ta rungumesa baikamata ace yabiye mata ba, kamata yayi ace ya ɓanɓareta daga jikinsa, sai de kuma babu yanda ya'iya saboda alokacin tana cikin halin buƙatar taimako, kum san nan shi be rungumeta don yaji daɗi ba.
"Inazakije ne haka, da rana tsaka?" yajefo mata tambaya.....
"Gidan su Husnah zani" ta basa amsa a taƙaice, saboda ba da kowani lokaci tacika son dogon magana ba...
"Shikenan muje saina kaiki, domin kinsan samun abun hawa zaimiki wahala, saboda rana tayi sosai"
Kallonsa tayi naɗan sakanni, kafun ta rausayar da kanta gefe cikin yanayi na shagwaɓa tace "Dama kabarni, koda ƙafana ai zan iya zuwa, idan har bansamu abun hawa ba, balle ma nasan zan samu"
"Da gaske zaki iya takawa da ƙafa daga nan har gidansu Husnah? to shikenan tunda zaki iya, zaimafi kyau ki taka da ƙafan, saboda kisamu ki ɗan rage wan nan ƙiban dakika haɗa, gaba ɗaya duk yasa kin yi muni, kin zama wata super mama dake" yafaɗi haka yana me ƙare mata kallo.
Waro idanu Zahrah tayi haɗi da soma kallon kanta, wai tayi ƙiba, takuma zama super mama.
Take idanunta suka yi raurau dasu, yayinda ruwan hawaye ya soma cika cikin su, "ashe da gaske tayi ƙiba bata sani ba? gashi harya fara goranta mata, to me yasa ita bataganin ƙibanta?" tatambayi kanta...
Dariya Dr.Sadeeq yasanya domin kuwa yalura tayarda da maganarsa, shikuwa wasa yake mata, bawai dagaske tayi ƙiban bane, gashi har tana ƙoƙarin yin kuka, shikam ya lura gaba ɗaya kuka baya bata wahalar yi, hawayenta a maƙale suke, mintuna kaɗan saikaga sun tsiyayo"
"Kintsorata ne dan nace kinyi ƙiba? hmmm nan gaba kaɗan zakiyi bindiga ki fashe saboda tsabar ƙiba"
Sake waro manya manyan idanunta tayi zuwa yanzu kam har ƙwallan cikin idanunta sun gangaro akan fuskarta....
"Au kinfiso ki kumbura ki fashe ɗin kenan?" yatambayeta yana me danne dariyar da ta taso masa...
Kai ta girgiza masa alaman "A'a"
"To kinaso na faɗamiki me zakiyi wanda zaisa bazaki fashe ba?"
Dasauri ta ƙaɗa kai alamar tanaso yafaɗa mata...
"Yauwa ƴar gari ashe de kema bakyaso ki fashe, to abu ɗaya zakiyi wanda shizai hanaki fashewa, kinga de ni likita ne ko? nakumayi zurfi cikin karatun likitanci, saboda tsabar zurfin da nayi ina karatune ma yasanya nagano cewa idan mutum yacika matsantawa kansa da damuwa da kuma yawan koke koke to yakan iya kumbura kamar de yanda kikayi yanzu, daga nan kuma bayan kamar 1 week shikenan sai dai yayi bindiga yafashe fush, shikenan kuma sai de wani bashi ba, kinaso haka ta faru dake?" yafaɗi haka yana me zura mata manya manyan idanunsa.
"A'a" tabashi amsa cikin murya me sanyi, domin kuwa a haƙiƙanin gaskiya ta yarda da kalamansa, ko kaɗan bata gano cewa shiya shirya abunsa ba. take fargaba ya ɗarsu a zuciyarta....
Wata irin dariyane takama Dr.Sadeeq amma kuma ba halin yasaki dariyar tasa, dolensa ya danne ta matuƙar yanaso Zahrah ta gamsu da bayanan sa hundred percent,,, lallai yau yaƙara tabbatarwa kansa cewa Zahrah yarinyace kuma yarinta na damunta, amma inbanda haka ta'ina ta taɓa jin ance mutum ya yayi bindiga yakuma fashe da ransa.
Gyara tsayuwarsa yayi haɗe da cewa "To yanzu de zaɓi ya rage gareki Yarinya, ko ki daina kuka ko kuma ki fashe, saboda haka zaki biyoni muje ne ko kuwa a'a nayi tafiyata?"
"Zanbika" tafaɗa cikin muryar tsoro saboda gaba ɗaya kalaman likita sun rikitata...
Murmushin gefen baki Dr.Sadeeq yayi haɗe da juyawa yanufi wajen motarsa, yana me danne dariyarsa...
Zahrah kuwa tamkar wacce ƙwai yafashewa haka ta bi bayansa.
Saida suka hau titi kafun yajuyo da kallonsa gareta, gani yayi tayi jigum da'ita, da'alama tunani takeyi....
"Amma nace miki yawan sakai a damuwa shike sa mutum ya fashe ko? hala don ba ɓangaren likitanci kike karanta ba shiyasa bakisan da hakan ba"
Kallonsa tayi haɗe da ƙwaɓe fuska, cikin murya me sanyi tace "Ni ae yanzu bawai a damuwa nake ba, kawai de ina kallon hanya ne" ....
Kansa ya jinjina haɗe da cewa tayi masa kwatancen gidansu Husnah'n domin shi basani yayi ba....
A dai dai ƙofar gidan su Husnah ya tsaida motar tasa, haɗe da dawo da kallonsa ga Zahrah wacce ke ƙoƙarin buɗe murfin motar tayi ficewarta...
"Da yaushe zaki koma gida?"
Ɗan jim tayi kana tace "Ko zuwa bayan la'asar ma, irin ƙarfe biyar ɗin nan haka" yanayin yanda taƙai ƙarshen zancen nata tana me juya kyawawan idanunta, shi ya shagaltar dashi har ya tsaida idanunsa akan ta, sosai takeyi masa kyau idan tana juya idanunta, ya kuma lura cewa hakan al'adarta ne, idan hartana magana, to takan juya idanunta masu kyawun gani, musamman idan maganar tazo ƙarshe..
"Ya de?" Zahrah ta tambayeshi sakamakon ganin da tayi yakafeta da idanunsa..
"Babu, kikulamin da kanki kinji, zan zo na ɗaukeki idan 5 ɗin tayi, inafata babu wata matsala?" yatambayeta cike da nuna kulawa.
Murmushinta me kyau tayi masa haɗe da cewa
"Babu wata matsala"
Yana kallonta tabuɗe ƙaramar ƙofar dake jikin gate ɗin gidan su Husnah tashige... Yana tabbatar da shigewarta yayiwa motarsa key haɗe dayin reverse yaɗauki hanyar asibitinsu, saboda dama aiki yabaro yazo gareta, to yazaiyi tunda tazama wani ɓangare na jikinsa...
Da matuƙar farinciki Husnah ta rungume Zahrah tana mejin daɗin ziyarar bazata da Zahrah'n takawo mata, saboda bata faɗa mata zata zoba. Bayan Zahrah ta gaisa da Momyn Husnah ne, suka rankaya zuwa ɗakin Husna'n,,, ba ɓata lokaci Husnah ta cikawa Zahrah gabanta da kayan ciye ciye dasu drinks.
"Naji daɗin zuwanki sosai ƙawata, kamar kuwa kinsan ina kewarki, jiyafa har mafarkin ki nayi, da safe naƙira wayarki kuma najita switch off, ina fata dai kina lafiya?"
Hijabin dake jikinta ta cire haɗe da cewa "Lafiya amma ba sosai ba"
Da sauri Husnah ta dawo da kallonta ga Zahrah
"Meyafaru dear?" Husnah tatambaya cike da kulawa.
Kallon Husnah Zahrah tayi na tsawon minti guda....
"Babuƙatar tuna abun da yafaru Husnah, saboda kinsan inada raunin zuciya, tuna abun zai iya sake jefani cikin wani hali"
Damuwane ya bayyana ƙarara akan fuskar Husnah haƙiƙa tamkar ƴar uwa ta jini take kallon Zahrah saboda haka duk wata damuwa ta Zahrah damuwar tace itama.
"Zaki iya ɓoyewa kowa damuwarki amma bandani Zahrah, sai de kuma babu amfanin takuraki akan cewa lallai sai kin sanar dani, saboda bansan wani hali zaki samu kanki aciki ba bayan kin faɗamin"
Dafa kaɗan Husnah Zahrah tayi haɗi da daure zuciyarta...
"Nasake haɗuwa da.... da....wanda ya yimin fya......." kasa ƙarasawa tayi saikawai tafashe da kuka.
Ko bata ƙarasaba Husnah tafahimci me Zahrah take nufi.
Cike da tashin hankali Husnah tasoma salati...
Sake jawo Zahrah jikinta tayi haɗi da rungumeta...."Ki daina kuka, yanzu ba lokacin kuka bane Zahrah, kinmaci abinci kuwa ?" Husnah ta tambayi Zahrah cikin kulawa...
"Banajin yunwa Husnah!" Zahrah tafaɗi haka cikin shaƙewar murya, wani yunwa zataji ita da take cikin bala'in sake ganin Zaid...
"Kinsan de ba kyau zama da yunwa ko, kinga yau ni namayi abincin dakaina, bana zuba mana muci tare, kuma dan Allah kada kicemin a'a"
Babu yanda Zahrah ta'iya dole tabiyewa Husnah taci abinci, gaba ɗaya Husnah se zuba take tamkar kurna, takasa yin shiru koda na minti biyu ne, tayi hakanne kuma saboda ta gusarwa da Zahrah da muwarta, daga ƙarshe de har game, Husnah ta jona musu a tv suka buga, sosai kuma hakan ya ɗebewa Zahrah kewa....
Tare sukayi sallan la'asar daga nan kuma Husnah ta ɗebi Zahrah, suka tafi shoprite, dangin su ice cream da chocolate suka jida, daga nan sukayo gida.
Kamar yanda yafaɗa ƙarfe biyar da minti ɗaya dai dai ya ƙaraso ƙofar gidansu Husnah.. Ƙiran Zahrah yayi a waya ya tabbatar mata cewa yana ƙofar gidan su Husnah....
Zahrah na ajiye wayarta Husnah ta kalleta haɗe da kashe mata ido ɗaya.
"Ƙawata tazama ƴar soyayya, sosai yanayin soyayyarku da Man ɗin nan yake kasheni, kinfasan gayen naki ya haɗu over, da badan ke bace danayi snatching ɗin sa!" cike da zolaya Husnah ta faɗi maganar...
Dariya suka sanya su dukansu, haɗe da rungume juna.
Har bakin motar Dr.Sadeeq Husnah ta raka Zahrah, bayan Momyn Husnah ta cikawa Zahrah leda da dangin su turare dakuma kayan shafa hadda kyautar wani haɗaɗɗen leshi, sosai Zahrah tayi godia, hakan kuma yana ɗaya daga cikin abubuwan daya sanya bata son zuwa gidansu Husnah, saboda idan dai tazo tofa sai mahaifiyar Husnah tayi ɗawainiya da'ita wajen bata kyautan kayayyaki masu kyau da tsada...
Harsaida Husnah taga tashin motar su Zahrah kafun takoma cikin gida...
"Kinsamo abun daɗi shine kokimin tayi ko?" Dr.Sadeeq yafaɗi haka ga Zahrah wacce ta ɗaura ledan sayayyar da sukayi a shoprite ita da Husnah akan cinyarta...
"Murmushi me sauti tayi haɗe da cewa "Ba'abun daɗi bane, kayan shafa ne"
"Um um ni banyarda ba, kitaimaka kiban ko chocolate ɗaya ne, naci yunwa nakeji, yau duk banci abinci ba" yaƙare maganar yana me shagwaɓe fuska, sai kace wani ƙaramin yaro...
Dariya Zahrah tayi haɗe da satar kallonsa "wai ma ya'akayi yasan cewa acikin ledar hanunta akwai chocolate?" ta tambayi kanta.
"Kina mamakin ya'akayi nasan cewa a ledarki akwai chocolate ko?, ai ba abun mamaki bane, tunda nasan shiɗin favorite ɗin ki ne" yafaɗi haka cikin yanayin shauƙi, amma still idanunsa naga titi..
Buɗe ledar tayi taciro wani chocolate mai kyau da daɗi kusan yafi kowanne ma daɗi acikin sauran chocolate ɗin da ta saya, ta miƙa masa haɗi da cewa "Ga wan nan amma bazan iya baka kyautarsa duka ba, saboda haka kaci rabi kabarmin rabi"
Saurin kallonta yayi fuskar sa ɗauke da murmushi... " Naƙi wayon, idan har kinaso na karɓa saide kibani kyautansa duka"
Turo ɗan ƙaramin bakinta tayi gaba, haɗe da noƙe kai alamar hakan bazai yiwuba, kallon bakin nata yayi, harsai da yaji tsikar jikinsa ƴa zuba, hmmm lallai idan ya auri Zahrah, zai tsotse wan nan ɗan ƙaramin bakin nata ne yanda ya kamata🙈...
"Kici chocolate ɗinki ke kaɗai nikam na gode" yafaɗi haka a taƙaice domin dama wasa yake mata baci zaiyi ba, shi da yake fama da ciwon ciki idan yaci chocolate kuma yake nan?
Lokacin da suka iso gida biyar da rabi har ta gota... kallon Zahrah Dr.Sadeeq yayi haɗe da ɗan nisawa.
"Nagama haɗa miki kayan lefe da kuma sauran abun da suka dace, wace rana kikeso a kawo?"
Saurin ɗaga idanu tayi ta kallesa jin abun da yace.
Idanunsa ɗaya ya kashe mata, wanda yasanya taji gabanta yafaɗi, saboda a wajen mutum ɗaya ta saba ganin irin wan nan kashe idon, kuma shi hakan yazame masa al'adarsa ne, bakowa bane kuma face ZAID.
"Zamuyi waya" Zahrah tafaɗi haka don son kawar da tambayar tasa, saboda a yanzu bata da amsar da zata basa..
Ajiyar zuciya ya sauƙe haɗe da dafa steering motar da duka hannayensa biyu. "Shikenan idan kin nutsu zan ƙiraki" yafaɗi haka cikin sanyin murya..
Murmushi tayi masa irin me tsayawa a rai ɗin nan, kana tabuɗe murfin motar tayi ficewarta, sai de batare da yasani ba, ta aje masa wan nan chocolate ɗin...
Bayan kamar 2 minute da shiganta cikin gida yaja motarsa shima yayi tafiyarsa...
*ZAID*
Tunda yasha wan nan ƙwayoyin baisan inda kansa yake ba harsai ƙarfe uku na yammaci,, ko da ya buɗe idanunsa ji yayi duniyar na juya masa, amma haka adaddafe ya shiga bathroom yayi wanka haɗe da ɗauro alwala, sai yanzu zaiyi sallan Azahar don tsabar asara, gashi har la'asar ma takawo kai....
Yana idar da sallan azahar ya miƙe daga kan sallaya haɗe da zura slipper ɗinsa yafice daga ɗakin... Kai tsaye masallacin jikin gidansu yanufa don gudanar da sallan la'asar wanda ake ƙira yanzu.. Ko a cikin masallacin mutane sai mamakin ganinsa suke saboda abune mawuyaci ka gansa a masallacin da wan nan time ɗin, yafi yawan zuwa sallan isha ko asuba, amma banda azahar da la'asar saboda a wan nan lokacin ma kwata kwata baya gida, sai de yayi sallah a wani wajen. Baidamu da kallon da mutane suke masa ba, yana idar da sallan sa yatashi yayi shigewarsa cikin gida...
Tsab yagama shirya kansa cikin ƙananan kaya, riga da wando na blue jeans wanda suka matuƙar amsar jikinsa. Ba abun da yake sai tashin ƙamshi.
Zama yayi abakin gadonsa haɗe da sanya hanunsa duka biyu ya dafe kansa dake yi masa ciwo kaɗan kaɗan,, wani irin sabon al'amari yakeji a cikin zuciyarsa, baisan da wani suna ze ƙira abun ba, amma tabbas jiyake zuciyarsa na azalzalarsa akan Zahrah, san nan yanajin cewa itace muradinsa, saurin buɗe idanunsa da ke lumshe yayi sakamakon hasko masa marukan da Zahrah ta sharara masa akan fuskarsa da sukayi, hanunsa yakai kan ƙuncinsa ya shafa haɗe da sakin murmushi, tunda yake a a rayuwarsa wata mace banda mahaifiyarsa bata taɓa kai hanunta jikinsa da sunan duka ba ballan tana har akai ga mari, sai gashi yau, Zahrah ta shararamasa lafiyayyun maruka harguda biyu akan fuskarsa, takuma haɗa masa hadda duka, amma ko kaɗan baiji zafin abun ba, anya kuwa shine? kodai an musanyashine bai sani ba? meke damun ƙwaƙwalwa da zuciyarsa ne? shine Zaid kuwa? Yajerowa kansa waƴan nan tambayoyin....
*(Team Zaid saiku basa amsa, shi ɗin ne koba shiɗin bane?)*
*27/December/2019*
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
*Wattpad user name fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈 Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 70 to 71*
Yajima zaune a kan gadon nasa, gaba ɗaya kansa ya kulle yarasa meke damunsa, wai shin da gaske SO yake ko kuwa? anya kuwa yanaga zaman sa haka zai yi wu? zaifi masa kyau yanemi Abid domin shi ne kaɗai zai iya fayyace masa halin da yake ciki, tabbas shi koda son Zahrah Abid ɗin yace masa yanayi yanzu bazai musa masaba, idan kuwa har haka so yake to yana mawa Zahrah so me tsanani, saurin laluɓar wayarsa ƙirar Samsung dake kusa dashi yayi. Numbern Abid ya dannawa ƙira, bugu biyu Abid ya ɗaga ƙiran cikin muryan kasala yace "Mutumin ya akayi ne, ka katseni ina cikin holewata"
"mcheeww aikin ka kenan cin ƴaƴan mutane, kana ina yanzu inaso muyi serious magana da kai" Zaid yafaɗi haka cike da zaƙuwa.
Miƙa Abid dake kwance shame shame a gado yayi haɗe da sakin daria, wai yau shi Zaid ke cewa baida wani aiki se cin ƴaƴan mutane, hmm ai duk iskancinsa shikansa yasan a ƙarƙashin Zaid yake, domin kuwa Iskancin Zaid me lasisi ne.
Cike da ƙuluwa Zaid yace " Nifa bana ƙira ka kamin iskanci bane, da zaka tsaya kanamin dariya"
"Yi haƙuri mana nawan, maganartaka ce tabani dariya, zuwa anjima mu haɗu a Millinion Park ina fata de bawata matsala bace ta afku?"
Ɗan yamutsa fuska Zaid yayi haɗe da duban agogon Rolex ɗin dake ɗaure a tsintsiyar hanunsa. "Shikenan to muhaɗu ƙarfe 5 na yamma banakumason kamin african time, 5 nacika idan bakazoba, bazan tsaya ɓata time ɗina wajen jiranka ba" yayi maganar cikin yanayi da yake nuna cewa ba wasa yake ba..
"Okay" kawai Abid yace haɗe da aje wayartasa yajawo babe ɗin dake kusa dashi, suka ci gaba da watsewarsu ko kunyar Allah dayake ganinsu basayi, Allah karabamu da ƙeƙashewar zuciya Ameen.
Zaid yana aje wayartasa yasanya hanu yashafi cikinsa, sai alokacin yake tuna rabonsa da yasanya abinci acikin cikinsa tun jiya da yammaci, amma saboda tsabar yashiga tension ko yunwarma bayaji, murmushi yayi tunowa da yayi da yanda yaji muryan Abid, dagajin yanda yaji yanayin muryartasa yatabbatar masa cewa holewa da mace Abid ɗin keyi, "hmmm Abid ba dama wajen iya latsa mace" yafaɗi haka a fili, shikamma rabonsa daya kusanci wata mace harya manta, shi yanzu ko mace ma yagani bata wani burgesa, yanzu idan zaiyi sex to badakowacce mace yakeso yayi ba, face Zahrah ita kaɗai yakejin cewa zai iya sauƙewa damuwarsa yanzu, itakuma kaɗaice zata iya basa gamsuwa ɗari bisa ɗari. Miƙewa yayi yanufi wajen fridge ɗin dake ɗakin nasa, fresh milk ya ɗauka haɗe da tsiyayawa a cikin glass cup, zama yayi yasoma sipping fresh milk ɗin a hankali, gaba ɗaya hankali da tunaninsa sunaga Zahrah, ko yanzu wani hali take ciki? Allah masani...
***
Sake narke masa murya tayi cikin shagwaɓa tace "Nide bance bana sonka ba, aikaima kasan inasonka, kawai de nakasa sakewa da kai ne har yau!" taƙare maganar tana me rausayar dakanta gefe tamkar yana ganinta..
Dr.Sadeeq dake zaune cikin luntsumemiyar kujeransa na office ya lumshe idanunsa haɗe da gyara zaman wayar akan kunnensa, sosai shagwaɓan Zahrah ke sauƙar mai da kasala acikin jikinsa, yayinda idan yaji muryarta yake samun nutsuwa a cikin zuciya da ruhinsa...
"To meyasa bakya iya sakewa dani ne My Princess, kinkuwa san irin sonda nake miki? inasonki Zahrah fiye da tunaninki, amma bazaki gane hakan ba, sai idan nasameki a matsayin matata, na tabbata nan da 3 weeks kinzamo mallakina daganan kuma zaki gaskata soyayyata a gareki!" yafaɗi maganar tasa cikin yanayi na shauƙi..
Saurin kulle idanunta tayi haɗe da sanya hanu tarufe fuskarta, saikace wanda take aga banshi, sosai maganarsa yasa taji kunya,, ta lura haka Dr.Sadeeq ɗin yake watarana baruwansa kansa tsaye yake faɗar maganar da zaisanya taji kunya.
"My Princess kinyi shiru" Dr.Sadeeq yafaɗi haka a kasalance.
Numfashi Zahrah ta fesar haɗe da sake yin ƙasa da muryarta cikin shagwaɓan daya zamemata sabo tace "Munyi magana da Baffa, yace ku kawo kayan lefen duk sanda kuka shirya kawai"
Daɗi ne yakama Dr.Sadeeq harsaida yakasa ɓoye murnarsa idan kuwa hakane to tabbas acikin satin nan zai sanar da ƴan uwansa saisu shirya rananda zasu kawo kayan, shida zasuce yauma to tabbas da zaiso hakan.
"Naji daɗin maganarki My princess saboda haka kincancanci nabaki kyauta ta musamman, idan banzo da dare ba gobe zanzo insha Allah"
Murmushi kawai Zahrah tayi haɗi da cewa "Nagode amma kariƙe kyautarka bayanzuba"
"Meyasa?" yatambayeta cikin yanayi na ɓata fuska.
"Saboda hidiman da kakeyi yayi yawa, dan Allah kabari haka kaji!" taƙare maganar cikin yanayin shagwaɓa.
"Inde akan kine Zahrah bazan taɓa gajiyawa ba, zanyi wani aiki yanzu zanƙiraki anjima kinji princess ɗina!" yafaɗi haka cike da lallashi.....
Haka sukayi sallama cike da kulawa ga junansu, yanzu kam tagama aminta da Dr.Sadeeq insha Allah kuma idan ta auresa zata basa farinciki me ɗorewa, iyaka iyawarta.....
Sosai Zaid yashaƙa da irin yanda Abid yasanyasa agaba yaketa yi masa dariya,, tsuka Zaid yaja me tsayi haɗe da kawar da kansa gefe jiyake tamkar ya tashi ya rufe Abid da duka, idan banda iskanci taya zai sanyasa gaba yayi ta masa dariya bayan yagama jin matsalarsa...
Wani mugun kallo Zaid yajefawa Abid me ɗauke da tarin ma'anoni da yawa, ganin haka yasanya Abid saurin gimtse dariyarsa haɗe da kama hanun Zaid ɗin...
"Yi haƙuri Abokina, maganar ce tabani dariya"
Tsuka Zaid yakuma ja batare da yace komai ba.....
"Nafuskanci inda matsalanka ta dosa Zaid amma kuma nasan abune me wahala ka yarda da abun dazan faɗa ma"
"Bazaka gane yanda nakeji agame da'ita ba ne Abid, dakasan yanda nakeji a zuciyata da ka tausaya kasanar dani maganin matsala ta, kodai shine so ɗin da kake cewa?" Zaid yatambayi Abid cike da damuwa...
"Ƙwarai kuwa Zaid wan nan shine SO, sai de naka SO'n ya banbanta da sauran soyayya'n, kai naka soyayya'r me tsanani kakeyi, wanda tariga da tajima acikin jikin ka batare da ka sani ba, ina da yaƙinin cewa tun farko Son Zahrah kake bawai sha'awarta ba kamar yanda ka ɗauka!" Abid yafaɗi haka da iyaka gaskiyarsa...
Nannauyar ajiyar zuciya Zaid ya sauƙe haɗe da sanya duka hannayensa ya dafe kansa wanda yake ɗan sara masa a hankali.. Tabbas yanzu kam ko yaso ko yaƙi dolensa ya yarda da maganan da Abid yafaɗa masa, domin kuwa idan har ba soyayya ba menene ke damunsa dayake sawa yakejin zafi a zuciyarsa? idan ba soyayya ba menene yake sanya tunaninsa hargitsewa da zaran yatuno Zahrah? idan ba soyayya ba menene yake sanya sa rasa sukuni da nutsuwarsa aduk sanda yatunanota kokuma yaganta? lallai kuwa soyayya baimasa adalci ba da bai sanar dashi kansa ba tun sanda yafarasa batare da yasani ba..
Idanunsa da sukayi jajur dasu ya ɗaga haɗe da maida kallonsa ga Abid "Inasonta Abid inasonta sosai!"
Waro idanu Abid yayi yana me kallon Zaid idan da ba Zaid ɗin ne da gaske a gabansa ba, to tabbas da sai yace badaga bakin Zaid wa ƴan nan kalaman suka fitoba, yau Zaid da kansa yake cewa yakamu da son wata? lallai kuwa rayuwa tana shirin juyawa abokin nasa baya.
Miƙewa Zaid yayi daga zaunen da yake haɗe da sanya hanu ya kwashe wayoyinsa dake kan ɗan ƙaramin table ɗin dake aje gabansu.
Kallonsa Abid yayi cike da mamakin ganin yanda lokaci ɗaya yanayin Zaid ɗin ya sauya.
"Inakuma zaka?" Abid yatambaya..
"Zanje gidansu Zahrah Abid, idanuna sun matsamin zuciyata har bugawa take Abid, ita kawai nakeson gani, idan har zata amince inaso ayau base gobeba koda ƙarfe ɗaya ne na dare a ɗaura mana aure da'ita" yanakai wa nan a zancensa yayi tafiyarsa.. Hangame baki Abid yayi yana kallonsa harya ɓacewa ganin idanunsa. Anyakuwa Zaid yana cikin hankalinsa? Kodai asiri yarinyar talakawan nan tayi masa ne? Abid yajerowa kansa waƴan nan tambayoyin, bayan yasan baida amsa bai kuma da me basa amasar...
Zahrah dake zaune tana gudanar da assigment ɗinta, wani yaro yashigo cikin gidan nasu haɗe da kwaɗa sallama.. Amsa masa Zahrah tayi batare da taɗago kanta takalli yaron ba..
"Wai ana ƙiran Zahrah a waje" yaron yafaɗa yana me kallon Zahrah domin kuwa yasan cewa itace wacce aka aikosa yayi ƙiranta..
Sai alokacin Zahrah taɗago kanta ta kalli yaron, haka nan taji gabanta yafaɗi, to waye kenan yake sallama da'ita? ta tambayi kanta, wayarta dake kusa da'ita ta ɗauka haɗe da dubawa, 1 missed call tagani na Dr.Sadeeq, dayake wayartata a silent tasanyata shi yasa bataji ƙiran nasa ba, kenan shine yazo yaƙira wayarta bata ɗauka ba shiasa yaturo yaro. "Jekace inazuwa" ta bawa yaron amsa a taƙaice..
Miƙewa tayi haɗe da tattara takardunta tayi ɗaki. Mayafi taɗauka ta yafa akan kayan dake jikinta...
Tsaye yake ajikin motarsa yayinda yakifa kansa asaman motar yana me kaɗa key ɗin motarsa dake riƙe a hanunsa..
Kanta a ƙasa tafito daga cikin gidan tana me duba wayar dake hanunta. Tsayawa tayi cak bayan ta haɗe wani miyau dayazo me ɗaci ya maƙale mata a maƙoshinta.
Murmushi yasakarmata haɗe da soma takowa zuwa gareta..
Lokaci ɗaya idanun Zahrah suka sauya kala daga fari zuwa ja, juyawa tayi a fusace tanufi hanyar shiga gida, da sauri Zaid yasha gabanta haɗe da marairaice fuska cike da tashin hankali yasoma cewa....
"Dan Allah Zahrah kitsaya ki saurareni, dan Allah kada kimin haka Zahrah, inaso ki saurare....." kasa ƙare maganar nasa yayi sakamakon kyakkyawan marin da Zahrah ta shimfiɗa masa akan kyakkyawar fuskarsa...
Cikin ƙuna da kuma zafin zuciya haɗi da raɗaɗi Zahrah ta haɗa yatsanta na tsakiya dakuma babbar yatsarta, ta kaɗa ade de fuskar Zaid duk da kuwa cewa yakerema tsayinta..
"Natsaneka tsana mafi muni, natsani jin kowani irin kalma ce da zata fito daga bakinka, wlh wlh nayi rantsuwa sau biyu, idan har ka sake naƙara ganin fuskar ka to zanyi maka abun da baka taɓa tunani ba!" cikin matsanancin ɓacin rai taƙare maganar tana me raɓan gefensa zata wuce, Zaid da zuciyarsa tariga da ta karye baiyi ƙasa a guiwa ba yasake shan gabanta.
"Kimin duk abun da kikeso Zahrah, zanfi jin daɗima idan akace kece zakiyi silan mutuwa ta, dan Allah ki saurareni mana Zahrah!!" yaƙare maganar cikin rawan murya...
Kuka ne ya ƙwacewa Zahrah me tsanani cikin muryan kukan tasoma cewa.....
"Miye laifina Zaid? Menene aibuna? shin wani abu na aikata maka da ka zaɓi cutar da rayuwata? ashe de ganganci ne don na ɗau soyayyata na baka? me yasa ka yaudareni Zaid? meyasa dole saini kazaɓi ka tozarta? Kacutar da rayuwata ka dasamin ƙunci a cikin zuciyata, wlh natsaneka Zaid, Idan har yaudara zata zamemaka abun ado mezaka amfana dashi acikin rayuwarka? Miye ribar aikata zina da fasiƙanci? Natsaneka Zaid! Natsaneka!! Bana fata Allah yaƙara haɗa fuskata da taka fuskar har gaban abada! Dan Allah kafita a rayuwata Zaid!!!" cikin matsanancin kuka taƙare maganar tana me durƙushewa ƙasa domin kuwa zuwa yanzu tsayuwa ya gagarewa ƙafafunta...
Idanun Zaid ne suka kaɗa suka zama jajur dasu tamkar wanda aka zuba musu jan barkono. gaba ɗaya jikinsane yasoma ɓari, shi ɗin ma durƙusawa yayi agabanta cikin murya me tsananin rauni yaƙira sunanta,, saurin ɗaga masa hanu Zahrah tayi alaman batason jin komai daga garesa..
"Banason nasake koda jin muryarkane Zaid, kafita a rayuwata, wai mekake nema dani ne? ko kana tunanin zan sake aminta da kai ne? hmmm kayi babban kuskure Zaid idan kuwa har haka kake tunani, zaifi maka kyau, kamanta dani kakuma manta da wacece ni, ni na barwa Allah cutarwan da kayi agareni, kuma insha Allah nasan zai ɗaukarmin fansa,, sai de inaso kasani cewa har abada bazan taɓa yafe maka ba, inaso kuma kada kamanta da cewar natsaneka !" a fusace ta faɗa cikin gida haɗe da banko ƙofar gidan nasu.
Tashi yayi daga durƙuson da yake haɗe da bin bayanta da kallo, gaba ɗaya zuciyarsa tagama karaya, wani irin abu yakeji ajikinsa yayinda kansa yayi masa wani irin masifaffen nauyi, zafi yakeji azuciyarsa irin sosai ɗin nan.
Zahrah kuwa zamewa tayi jikin ƙofar gidan nasu tasaki wani irin kuka me tsuma zuciya. Se yaushene zata warke daga raɗaɗi dakuma ciwon abun da Zaid yayi mata? ganinsa yasake tasomata da mikin daya ƙi warkewa tsawon lokaci acikin zuciyarta, maiyasa Zaid yazame mata bala'i acikin rayuwarta? kuka tashiga yi sosai da sosai...
Zaid kuwa daƙyar ya iya jan ƙafafunsa yanufi motarsa, kasa tuƙa motar tasa yayi, gaba ɗaya idanunsa duhu suke gane masa, tabbas bazai taɓa iya tuƙa mota yana a irin wan nan halin ba,, da ƙyar ya'iya laluɓa wayarsa yaƙira driver'nsa... Mintuna kaɗan drivern Zaid yazo ya wuce dashi....
Saida tayi kukanta son ranta har sai da taji kanta yasoma ciwo kafun ta tsagaita, haɗe da miƙewa daga jikin ƙofar tashige cikin gida, direct ɗakinta ta wuce ta kwanta numfarfashi kawai take sauƙewa, lokaci ɗaya zazzaɓi yarufeta, harsaida tajawo mayafi ta lulluɓi jikinta....
Sanda yashiga falonsa ko gani bayayi sosai, wani irin ciwo kansa ke masa me tsanani wanda yasanya idanunsa sukayi nauyi, da ƙyar ya'iya jan ƙafansa yashiga ɗaki, kalaman Zahrah ne sukeyi masa yawo acikin kansa,, yatsani jin kalmar tatsaneshi da take yawan faɗa ɗin nan, wlhy a gurinshi da ta faɗi wan nan kalman gwamma ta sharara masa maruka koda kuwa guda biyarne akan ƙuncinsa.. Ya yanke shawara da de yakasance a irin wan nan yanayin ya gwammace yafita daga cikin hayyacinsa idan yaso bayan wasu tsawon lokaci yadawo cikin hayyacin nasa,, wasu ƙwayoyin magani yaɗauko harkala biyu, wanda suke gusarwa mutum da hankalinsa, maganin suna da hatsari sosai hakan nema yasanya ba'a sai dasu a bayyane sai de a ɓoye, kuma suna mugun sa bacci sosai... Saida ya ɓalli guda uku uku daga jikin kowani sachet, kafun ya watsa maganin cikin bakinsa, wan nan karon ko ruwa baisha ba haka ya haɗiye magungunan, yanda kalaman Zahrah ke dawowa cikin kunnensa yafi komai ɗaga masa hankali, kwanciya yayi lamo akan gado yayinda yake ƙwato numfashinsa dake ƙoƙarin ƙwace masa da ƙyar. wani irin fusga numfashinsa yayi lokaci ɗaya kuma komai najikinsa ya sake...
Zahrah kuwa zazzaɓine ya dirarmata me zafin gaske, wanda yasanya lokaci ɗaya jikinta yasoma ɓari ta fara rawan ɗari, har zuwa yanzu hawayenta bai tsaya ba. Zaid ya cuceta itakam duk irin ƙuncin daya jefata a baya bai ishe saba saida yakuma da wowa gareta, sai yaushene hawayenta zasu tsaya? sai yaushene zata samu farinciki ingantacce wanda babu algus acikinsa? tunda ta haɗu da Zaid ƙuncin rayuwarta yasoma, wani irin annoba Zaid yazame mata ne?.....
*(Kuyi haƙuri kuyi manage da wan nan, headache ke damuna, nida Zaid duk cutarmu ɗaya😜 banyi posting da wuri ba wlh network ɗin sim ɗi nane gaba ɗaya ya ɗauke😥)*
*29/December/2019*
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*(💗Wannan page ɗin baki ɗayansa kyautane agareku my wattpadi'ans inagodiya sosai a gareku💗)*
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 72 to 73*
Baki Labisat dake tsaye taturo gaba haɗe da ɓata fuskarta duk wai akan don Mom ɗinsu tace taƙira mata Zaid a ɓangarensa ne yasa take wan nan abun...
"Tsayuwan uban me kike bacewa nayi ki ƙiramin yayanki ba!" Mom tafaɗi haka cike da faɗa, ganin Labisat ɗin bata da niyar zuwa aiken datayi mata.
"Mom wlhy tsoro nakeji kada naje ya masifance ni!" Labisat tafaɗi haka cikin shagwaɓa.
Harara Mom tawurga mata bashiri Labisat takama hanyar fita daga cikin falon...
Aranta kuwa roƙon Allah take yasa idan taje kada ya masifanceta saboda shi abun faɗa baya masa kaɗan ko kaɗan, jiya jiya dawowanta daga boarding school amma Mom zata haɗata da masifan Yaya Zaid (Su yaya manya😂)
Kusan sau huɗu Labisat tana knocking ƙofar daze kaita cikin falonsa, amma shiru ba amsa, hakan yasanya tatura ƙofar tashiga,, bakowa acikin falon sai daddaɗan ƙamshinsa dake tashi.. Direct ƙofar bedroom ɗinsa tanufa haɗe da soma knocking ƙofar,, jin shiru ne yasanya tashiga ƙiran sunan sa...
"Brother! Brother!" ko gyaran murya bataji yayiba balle tasa ran zai amsa mata, batama tabbatar yana cikin ɗakin ko baya ciki ba..
Gajiya tayi da knocking ƙofar ta juya tayi tafiyarta...
"Mom inaga fa kamar Bro bayanan domin nayita knocking door ɗinsa amma bai amsa ba"
"Tabbas yana cikin gidan nan Labisat domin kuwa tunjiya daya shigo baifita ba, har me gadi na tambaya naji ko yaga fitarsa amma yacemin tunjiya daya shigo bai fita ba, miskilancin nasa ne ya motsa, banaje dakaina nasa mesa nikam ae be isa yanunamin halin ƙyaliya ba" Mom tafaɗi haka tana me miƙewa tsaye daga zaunen da take..
Itama ɗin de knocking tayi masa haɗe da ƙiran sunansa amma shiru bai amsata ba, hakan yasa ta murɗa handle ɗin ƙofar ta kutsa kanta ciki bakinta ɗauke da sallama..
Tsuka Mom taja sakamakon ganinsa da tayi kwance akan gado yayi ruf da ciki, lallai ma wato iskancine ya hanasa amsa mata, da fari hartayi zaton ko baya gidan ne..
"Zaid!" taƙira sunansa cikin kakkausar murya... Ko motsawa baiyi ba balle tasaran ze amsa mata..
Kafeshi da idanu tayi tana me nazartarsa, a iya saninta da Zaid baya bacci a irin wan nan lokacin, impact ma shiba mutum bane ma'abocin yawan bacci ba'a bisa ƙa'ida ba, idan kuwa harda gaske baccin yake to baya rasa ɗayan biyu kodai baida lafiya ko kuma yayi halin nasa nashan ƙwayoyi, "Sai yaushene Zaid ze san ya girma? sai yau shene zai dena nuna rashin damuwa da lafiyarsa?" tajeromawa kanta waƴan nan tambayoyin, "Haƙiƙa Zaid ɗanta ne amma ita kanta har yau batasan wani irin haline da shi ba, shi mutum ne me nuƙu nuƙu bakoda wani lokaci ne kake sanin gaba da bayansa ba, haka nan yake bakomai ne zaka masa ƙa burgesa ba yanada wani shegen shu'umin hali saide kawai Allah yashirya mata shi"...
A hankali tashiga takawa zuwa gaban gadon nasa..
Idanu Mom tasake warowa waje, tabbas idan de idanunta de de suka gane mata to kuwa Zaid baya numfashi, domin babu wata alamar da take nuna akwai nunfashi a tattare dashi saboda ko cikin sa baya motsawa, alama ta baya shaƙan numfashi kenan..
Hanunta takai setin hancinsa ko da zataji ɗumin numfashin sa.
Salati Mom tasa haɗe da dafe ƙirjinta, sakamakon wani irin bugawa da taji zuciyarta tayi.
"Zaid!Zaid!" Mom tashiga ƙiran sunansa cikin tashin hankali haɗe da soma jijjigasa.
Hawayene suka shiga bin ƙuncin Mom bashiri ta fita daga ɗakin, direct ɓangaren Alhaji Ma'aruf ta nufa saboda yana gida baikai ga fita office ba..
"Alhaji! Alhaji! katemaka wlhy Zaid baya numfashi zo muje ka gani, katemakeni kada na rasa ɗana mafi soyuwa a gareni!!" gaba ɗaya cikin tashin hankali Mom keyimawa Dad bayani..
Mamaki haɗi da al'ajabi ne yakama Alhaji Ma'aruf amma de yanzu balokacin tambaya bane gwamma yabita yaga meke faruwa da Zaid ɗin....
Shima sosai ya tsorita kuma hankalinsa yatashi daganin Zaid yashe a gado baya numfashi sai kace gawa...
Da ƙyar Abba ya'iya sungumarsa yasanyasa a mota, abunka da ƙaƙƙarfa kuma ma'abocin yin gym shiasa jikinsa yake ko ina a murɗe, san nan kuma me ƙaramin ƙarfi bazai iya ɗaga sa ba, Dad ɗin ma saida temakon Mom ya iya ɗagasa... Daga Mom har Labisat hankalinsu amatuƙar tashe yake haka suka shiga mota suka rankaya zuwa asibiti...
Direct Emergency aka kai Zaid cikin gaggawa likitoti suka shiga basa temakon gaggawa...
Jigum jigum haka Abba da Mom sukayi a wani ɗan corridor dake kusa da ɗakin da aka kai Zaid, iya ƙololuwar tashin hankali sun shigesa, kuka kawai Mom da Labisat keyi, kasa koda rarrashinsu Alhaji Ma'aruf yayi domin shima da akwai hali da kukan ze sanya ko da zaiji sassauci a cikin zuciyarsa...
Likitotin nan sunci baƙar wahala kafun da taimakon Allah suka samu suka daidai ta numfashin Zaid. Haka suka fito suna sharce gumi.... Kallon Alhaji Ma'aruf ɗaya daga cikin Doctors ɗin yayi haɗe da cewa "Ranka ya daɗe muje office" ƙoƙarin binsu Mom tasomayi Alhaji Ma'aruf yaɗaga mata hanu alamar tajirasu....
Handkerchief likitan nan yaɗauka ya ƙare share gumin dake tsatstsafawo akan goshin sa..
Ganin haka yasa Abba cike da tashin hankali yace "Yade Dr.Bilal meke faruwa ne, dan Allah kada kafaɗamin wani mummunan labari!"
Jinjina kai Dr.Bilal yayi haɗe da kallon Dad. "Kwakwantar da hankalinka Alhaji zuwa yanzu komai ya daidaita munshawo kan matsalan"
Nannauyar ajiyar zuciya Dad yasauƙe haɗe dayin hamdala acikin ransa...
Sake gyara zama Dr.Bilal yayi haɗi da cewa "Sai de kuma agaskia bazan ɓoye maka ba Alhaji ɗan ka yana cikin matsala wanda yake gab da rasa rayuwarsa matuƙar baikiyayewa kansa shan ƙwayoyi masu mugun haɗari ba, baya ga haka kuma idan har ya cigaba dashan giya nan da ƴan kwanaki tofa sai de kuma abun da Allah yayi!"
Yanzukam Dad ne yashare gumi ba Dr.Bilal ba, domin kuwa a iya tsawon rayuwarsa baitaɓa sanin Zaid nashan wasu ƙwayoyi masu bugarwa ba, yade san da ya nashan giya amma kuma atunaninsa yajima da dena shan giyan.
"Bangama fahimtarka ba likita, naji kace ƙwayoyi na bugarwa, kana nufin shiɗin ne yakeshan ƙwayoyin bugarwa?" Dad yatambayi Dr.Bilal cike da son sanin ƙarin haske akan batun..
"Wato a iya bincikenmu mungano cewa akwai wata ƙwaya me haɗarin gaske da yakesha lokaci zuwa lokaci, wanda kuma haɗarin ƙwayar yana da matuƙar yawa, bazanyi mamakin a ina yasamu ƙwayan ba, saboda nasan shiɗin isashshene, saboda ƙwayar ba ako ina ake samunta ba, a ƙa'ida ma anhana shigo da ƙwayar nan gida Nigeria, kawai de rayuwar yanzune da ta zama sai a hankali, zai iya yuwuwa kuma ba anan yake sayan ƙwayan ba daga can waje yake shigowa da abarsa, sai de kuma wan nan duk bashine damuwar ba, idan har ya cigaba da shan wan nan ƙwaya to ina me tabbatar maka da cewa zai iya rasa ransa ako da yaushe, duk da kuwa dama munsan mutuwa tana kan kowa yanzu ko anjima, amma tabbas kiyayewan shine yafi, san nan kuma giya tayi masa mummunan illa saboda tasamu mafaka acikin cikinsa, wataƙila yamai da ita ruwan shansa ne, amma kuma duk hakan ba wani babban matsala bane idan har ze kiyaye to da taimakon Allah komai zezo masa cikin sauƙi!"
Salati Alhaji Ma'aruf yayi a bayyane haɗe da sanya hanu yazame hular dake kansa, ashe bayan giya hadda wata tsinanniyar ƙwaya me haɗari Zaid yake sha? anya kuwa Zaid yanada cikakken hankali? shin wani irin haline haka da Zaid? amma babban abun tambayar shine laifin waye acikinsu, laifinsune su iyayensa kokuwa laifinsa ne shi kansa Zaid ɗin?
"Haƙiƙa dukansu suna da laifi, amatsayinsu na iyaye basu wani tsaya sunbawa Zaid kyakkyawar kulawa ba, kuɗi kawai suka sake masa haɗe da turasa makaranta har wata uwa duniya, amma duk da haka bekamata ace yakasance haka ba, idan su basa lura da al'amuransa shi ɗin mahaukaci ne da be san dede ba? tabbas yasan shiyake da alhakin kulawa da tarbiyan Zaid tunda shine yaɗaukosa daga wajen Mahaifiyarsa yadawo dashi America kusa dashi, tunda suke America bai taɓa tsayawa da kyau yakula da wani irin rayuwa Zaid ɗin keyi ba, shide kawai yabuɗe masa bakin aljihu yana ganin hakan shine gata, ƙwarai mafiyawancin iyaye ayanzu sunfi bada kulawarsune ga Ƴaƴa mata, yayinda ƴaƴansu maza kuwa ko oho, duk wata kyakkyawar tarbiya Ƴaƴa mata ake ƙoƙarin koyawa, yayinda Ƴaƴa maza kuwa suka zama hoto, aganin iyaye komiye ɗa namiji yayi adone bakamar ƴa mace ba, tabbas hakane duk abun da ɗa namiji yayi adone bakamar mace ba, amma hakan bawai yananufin shi ɗa namiji abarsa sakaka haka bane batare da annuna masa kulawa ba, shi namiji a koda yaushe ana ganin zai iya kula da kansa, amma yana da kyau ana nuna masa kulawa ana kuma jansa ajiki kodan yasamu inda zena faɗan damuwarsa, kowafa yanason yasamu tarbiya me kyau daga Namiji har mace, saboda haka yazama lalle iyaye su tashi tsaye wajen kulawa da ƴaƴansu maza saboda ba mata ne kaɗai suke buƙatan kulawa ba harsuma maza suna buƙata......
Dr.Bilal ne yakatse Dad daga tunanin da yafaɗa me zurfi tahanyar cewa da yayi dashi. "Zaid yana buƙatar hutu saboda haka sai nan da 4 hours kafun su samu ganinsa"
Jiki ba ƙwari haka Dad yafito daga office ɗin yanufo inda su Mom ke tsaye suna sharce hawaye..
"Yaya de Alhaji me likitan yacema?" Mom tatambaya cike da damuwar son sanin wani hali ɗanta yake ciki..
"Kada kidamu, ku kwantar da hankalinku jikinsa da sauƙi zuwa anjima kuma insha Allah zamu samu ganinsa yanzu likita yace yana buƙatar hutu ne, to dole zamu barsa yaɗan huta" Dad yaƙare maganar yana me kamo duka hannayen mom alamun rarrashi..
Hamdala Mom tayi haɗe da sauƙe ajiyar zuciya
Sake kallon Dad tayi cikin yanayi na tuhuma tace "Meyasanya naga fuskarka ɗauke da tashin hankali me tsanani Alhaji?"
Murmushin dole Dad yanemo ya ara akan fuskarsa bayason faɗa mata wan nan maganar yanzu yafiso saisun samu nutsuwa sunkoma gida tukunna, sai de kuma abun da shi besani ba shine tafikowa sanin cewa Zaid yanashan giya, saboda tasha kamasa acikin maye yayi mankas, san nan kuma tajima da sanin cewa yanashan ƙwayoyi, sede abun da bata sani ba shine haɗarin da ƙwayoyin suke ɗauke dashi....
********
Haka Zahrah tawayi gari yau da zazzaɓi sede duk da haka bata nunawa kowa cewa bata da lafiya ba, sede kuma idanunta sun kunbura sakamakon kukan da taci ta ƙoshi a daren jiya..
Haka de tashirya kanta tsab don zuwa makaranta amma kowa yaganta yasan bata da wani isashshen kuzari a tattare da'ita,, ko abun kari bata tsaya taci ba haka ta fice a gidan nasu....
********
"Kuka bazai taɓa yimiki maganin komai ba Zahrah, tabbas nasan kinajin raɗaɗi a cikin zuciyarki amma zuwa yanzu yakamata ace kimanta da baya kifuskanci gaba, aure zakiyi yanzu babu amfani kicigaba da sanya kanki cikin ƙunci!" Husnah tafaɗi haka ga Zahrah cikin yanayi na tausasawa, kasancewar duk wunin yau ɗin da sukayi amakaranta bata gane kan ƙawarta ta ba...
Hannayen Husnah duka Zahrah takama haɗe da kallonta. Cikin murya me rauni tasoma cewa.....
"Ni kaina inaso naganni cikin farinciki Husnah, amma nasan hakan bazai samu ba matuƙar Zaid yana raye a doron ƙasa, koda ma ace baya raye nasan bazanyi farinciki ba Husnah saboda yariga daya gama lalatamin rayuwa, bana tunanin cewa akwai wani namiji da zaiyi ɗokina idan ya aureni? Shifa budurci wani abune me matuƙar mahaimmanci a rayuwar ƴa mace Husnah, babu wani mutumci dakuma karamci wanda ya wuce mace takai budurcinta ɗakin mijinta, mafi ganganci da kuskure da mace zata aikata kafun aurenta shine ta yarda ta bawa wani kyautar budurcinta, mata irina suna da yawa Husnah wa ƴanda aka mawa fyaɗe aka ƙwaci budurcinsu da ƙarfin tsiya, san nan kuma akwai waƴanda maza suke ruɗansu da kuɗi ko kuma da soyayya harsu yi nasaran rabasu da budurcinsu, san nan akwai kuma wanda dan kansu suke bada kyautar nasu budurcin ga wani daban, rasa budurci abune me matuƙar ciwo Husnah musamman ma ga iri na wanda aka mawa fyaɗe, Yawancin maza suna fatan idan sunyi aure su samu matansu da cikekken mutumcinsu, inde kuwa har a matsayin budurwa suka aureta, haƙiƙa akwai wata soyayya dakuma girmamawa dake shiga tsakanin mace da mijinta matuƙar takawomasa budurcinta ɗakinsa, saɓanin haka kuwa shike hargitsa tunanin namiji, shike jagulawa mace zaman aure'nta, koda ace ya yarda ƙaddarane hakan amma tabbas wani lokaci abun zaina masa ciwo, duk da nasan cewa Dr.Sadeeq yasan komai daya faru dani, amma duk da haka tabbas nasan duk randa yakusanceni saiyaji ciwo acikin ransa, saikuma yaji wani abu saɓanin tunaninsa, shi a yanzu yana ganin cewa hakan bakomai bane, amma kuma hakan komai ne bakuma ze gane hakan ba sai randa ya aureni yakuma nemi dana basa haƙƙinsa na aure,, wan nan ranan nake gujewa kaina Husnah bansan ina zan tsoma kai da zuciyata ba amma nabarwa Allah komai!!" gaba ɗaya hawaye sungama wankewa Zahrah da Husnah fuska, lalle kuwa wan nan itace mummunar ƙaddara wand ba'a taɓa mantawa da'ita,, rungume Zahrah Husnah tayi cike da tsananin tausayin ƙawarta ta,,, tabbas duk abun da Zahrah tafaɗa gaskiya ne kai budurci ɗakin miji yafi komai daɗi a rayuwa saboda ko ba komai zaiƙara muku danƙon soyayya dakuma mutunta juna, duk da cewa Zahrah ba'asonta tarasa budurcinta ba amma kuma tabbas kamar yanda Zahrah ta faɗa hakan yake dolene Dr.Sadeeq zaiji zafin abun sosai aduk ranarda kusantar farko tashiga tsakaninsu, amma kuma babu wanda ya isa ya tsallakewa ƙaddararsa.....
Hawayenta tasanya hanu tashare kafun tashiga sharewa Zahrah ma nata hawayen,,,,
"Ki kwantar da hankalinki Zahrah komai zai zo cikin sauƙi insha Allah taso muje musamu ruwa muwanke fuskarmu ko"
Ba musu Zahrah ta tashi tsaye Husnah takama hanunta suka nufi wajen da sukasan zasu samu ruwa......
***********
Jigum haka su Dad dake tsaye agefen gadon Zaid sukayi, yanzu awa 5 kenan suna irgawa batare daya buɗe idanunsa ba, gashi kuma 4 hours likita yace musu zaiyi....
Babban yatsar ƙafansane tasoma motsawa kafun idanunsa da sukayi nauyi suka soma buɗewa a hankali,, da sauri Dad ɗinsa yaƙaraso jikin gadon yanayi masa sannu...
Ƙoƙarin tashi zaune yasomayi da sauri Dad ɗinsa yamaidasa ya kwanta "Ba sai ka tashi ba Zaid yakamata kabari kaɗan wastsake tukunna kafun kasoma yunƙurin tashi"
Ɗan yamutsa fuska Zaid yayi haɗe dabin ledar ruwan da aka ɗaura masa da kallo.
Dai de lokacin Labisat suka shigo ita da Dr.Bilal domin dama Mom naganin Zaid ɗin yabuɗe ido tace da Labisat tayi mata ƙiran Doctor...
Ƴan gwaje gwaje Dr.Bilal yayi masa haɗe dayi masa wasu ƴan tambayoyi, ko motsawa bakin Zaid beyiba balle Dr.Bilal yasa ran samun amsa, ganin haka yasa Dr.Bilal yin murmushi batun yauba yasan Zaid ɗin saboda haka shirun da Zaid ɗin yayi masa bawani abu bane daya kamata ace yadamu ba,, kallon Dad Dr.Bilal yayi haɗe da cewa
"Ko yanzu idan kuna buƙatar sallama se a baku saboda babu wata damuwa, se daifa a kiyaye kamar yanda na faɗa"
Kai Dad yajinjina haɗe da cewa "Shikenan Doctor insha Allah za'a kiyaye, muje sai nakarɓi takardan sallaman ko" Dad da Dr.Bilal suna fita Zaid yatattaro duka wani kuzarinsa dayayi masa saura yamiƙe tsaye, kafaɗun Labisat dake tsaye kusa dashi ya kamo haɗe da ɗaura hanunsa akan kafaɗan nata suka nufi hanyar fita daga ɗakin, domin kuwa koda Dr.Bilal be basu sallama ba tabbas bazai ƙara 1 hour a cikin asibitin ba...
Yana riƙe da kafaɗan Labisat harzuwa cikin mota, shida Labisat mota ɗaya suka shiga, yayinda su Dad da Mom suka shiga wata motar wanda duk su sukazo da ita... Direct gida suka nufa
Idanunsa gaba ɗaya suna a lumshe yayinda yajingina bayansa a jikin kujeran motar wanda yake zaune akai.
Ɗan satan kallonsa Labisat tayi hakanan taji wani irin mugun tausayin ɗan uwan nata ya kamata, tabbas basuyi wani shaƙuwa da yayan nata ba amma tafuskanci cewa yanacikin damuwa, takuma tabbatar da cewa sanadin damuwarne ma har ya kaisa ga kwanciya a asibiti, to wan nan wace irin damuwace yayanta yake ciki haka? tabbas zataso sanin damuwar dake damunsa saboda tana matuƙar son ɗan uwan nata bandashi batada wani ɗan uwa dasuke uwa ɗaya uba ɗaya shikaɗaine yayanta kuma garkuwanta......
Koda suka isa gidama Labisat ce tarakasa har ɓangarensa,, zama yayi akan kujera haɗe da jawo wani ɗan ƙaramin table ɗin dake tsakiyar falon yaɗaura ƙafafunsa akai..
"Yaya mezan kawo maka, yakamata kasa wani abu acikin ka!" cike da ɗar ɗar Labisar tafaɗi maganar saboda tasansa sarai ba'a iyarmasa yanzu saiya saceka..
"Friedrice" yafaɗa a taƙaice batare kuma daya buɗe kyawawan idanunsa dasuke a lumshe ba..
Jiki na mazari haka Labisat ta tafi kawo masa friedrice ɗin dayace, domin kuwa dama agidan nasu ba a rasa friedrice..
Mintuna kaɗan tadawo hanunta ɗauke da ƙaton tire hadda plate ɗin yankakkun kayan marmari akan tire ɗin,, adede gabansa ta ajiye tire ɗin haɗe da ɗaukan plate ta buɗe kulan da friedrice ɗin ke ciki ta zuba masa.
"Yaya gashinan na kawo" tafaɗa tana me tura masa plate ɗin friedrice ɗin gabansa.
Ganin da tayi bece da ita komai ba yasanyata miƙewa sumu sumu tafice daga falon nasa...
Jawo plate ɗin yayi gabansa yasoma tsakuran abincin yanaci kaɗan kaɗan duk da kuwa bawai buƙatar abincin yakeyi ba adole kawai yakeci... Lomansa huɗu ya aje spoon ɗin dake hanunsa haɗe da jawo plate ɗin yankakkun kayan marmarin dake gabansa yasoma sha, sai alokacin yasoma jin daɗin bakinsa, amma da kwata kwata bayajin ɗanɗanon komai,, fruits ɗinma baiwani sha me yawaba haka yature yakuma maidakansa yajingina da kujera,, idan akwai abun dayake ƙauna dakuma muradin gani yanzu arayuwarsa baiwuce Zahrah ba, dole yaje gidansu ayau ɗin koda kuwa idan yaje zata ɗauki wuƙa ne taluma masa a cikinsa.....
Yauma de kamar kullum Zaune take a tsakar gidan nasu, kwanon abincine aje agabanta tana tsakura da kaɗan kaɗan tana kaiwa bakinta domin kuwa haryanzu bata wani jin daɗin jikinta..
Inna ce zaune daga gefenta tana ta ƙoƙari wajen ganin ta seta tashan radion ta..
Wani yarone yayi sallama yace wai ana ƙiran Zahrah,, "Jekace tanazuwa" Inna tahanzarta faɗa, har yaron yakama hanyar fita daga gidan, Zahrah ta tsaidasa haɗe da cewa "Kace bazata zo ba"
Hangame baki Inna tayi tana kallon Zahrah "Bazakijeba fa kikace?"
"Eh Inna dan Allah kuma kada kitambayeni dalili" tayi maganar tana me langwaɓar da kanta gefe.
Harara Inna ta watsa mata haɗe dayin tsuka baƙin ciki kawai Zahrah'n takeyi mata wayasani ma ko wanda ke ƙiran nata da alkhairi yazo...
"Wai Bazata zoba" yaron nan yafaɗawa wanda ya aikosa.
Waro idanu Zaid yayi maganar ma shi dariya taso basa, amma a irin wan nan yanayin dayake ciki bayatunanin zai iyayin dariya...
"Wayene yacema bazata zo ba?" Zaid yatambayi yaron.
"Ita da kanta" yaron yabasa amsa domin kuwa shiɗin ɗan maƙotansu ne saboda haka yasan Zahrah'n.
Kai Zaid yajinjina haɗe da cije laɓɓansa,, Allah sarki rayuwa babu yanda bata juyawa mutum, amma in banda haka wai yau shine a wata ƙasƙantacciyar unguwa kuma ƙofar gidan su mace yakuma aika tace bazata zo ba, shine fa Zaid ɗin da har gobe ƴan mata suke rushing akan sa, to amma meyasa haka takasance dashi?" ganin da yayi yaron nashirin tafiya ne yasanya yace "Kaje kace injini nace tayi haƙuri tafito" bamusu yaron yakoma yakuma faɗi saƙon da akabasa umarnin yafaɗa..
Tsuka Zahrah taja haɗe da tashi tsaye "Kaje kace wai inji Zahrah kozai mutu a tsaye baza ta zoba" tanakaiwa nan azancenta tayi wucewarta ɗaki..
Abunda Zahrah tafaɗa shi yaron nan yazo ya sanarwa Zaid, kuɗi Zaid yaciro a aljihunsa 1k yabawa yaron dafari yaron yatsorita yaƙi amsa, amma Zaid yatilasta masa saida ya amsa, haka yaron yatafi yana murna...
Motarsa yabuɗe yashiga yayinda yakifa kansa a steering motar meyasa soyayya zata masa haka, idanunsa Zahrah kawai suke son gane masa tabbas yau bazai taɓa iya runtsawaba matuƙar baiga Zahrah ba, yana mawa Zahrah wani irin mugun so me tsananin zafi.. Jan motarsa yayi yakoma ƙarƙashin wata bishiya tayanda bakowa zai lura da cewa yana wajen ba, yaƙudurta aransa cewa koda zai kwana a wajen ne bazai gusa ba harsai idanunsa sun mai tozali da Zahrah....
Bayan awa ɗaya
Zahrah ce tafito daga cikin gidan nasu sanye da wani siririn mayafi wayarta ce riƙe a hanunta se kuma wani littafi. Zaid dake zaune cikin motarsa yana ganinta ya sake waro idanu haɗe da sauƙe ajiyar zuciya me ƙarfi, jiyakeyi tamkar yaje ya ɗauƙota can caɗak yatafi da ita... Yana kallonta tayi shigewarta wani gida dake kusa da nasu gidan.. Bayan kamar mintuna 8 da shiganta gidan yaga takuma fitowa da sauri yabuɗe murfin motarsa daniyar ƙarasawa gareta sai de kuma ko taku biyu baiyiba tashige cikin gida ko ganinsa ma ita batayi ba, haushine yasanyashi buga tayar motarsa da ƙafarsa, haka yakoma yayiwa motarsa key haɗe dayin reverse yabar unguwar tasu cike da ƙuncin rashin samun daman yi mata magana da be yiba, amma de yaji sanyi sosai a zuciyarsa daya ganta...
*********
Yau tunsafe Zahrah tashiga busy hidama kawai sukeyi ita da Husnah domin kuwa yaune ranar da Dr.Sadeeq yace mata za'a kawo lefenta,, yanzuma daga shopping suke sunje sun sayo kayan drinks da kuma su snacks wanda za'abawa baƙi. Zama sukayi akan tabarma suna me da numfashi saboda sungaji sosai,,, kallon Zahrah Husnah tayi haɗe da sakin murmushi.
"Ƙawata nifa yau daɗi nakeji jinake tamkar ma nice za'a kawowa lefen" dariya Zahrah tayi haɗe dacewa "To aike kince bayanzu zakiyi aure ba saikin gama school gashi Nuruddeen yana tsananin son kuyi aure amma ke kinƙi"
"Hmm ai zan masa maganane yaturo kawai domin ni mafa yanzu dagaske auren nakeso nagaji da rungumar pillow idan nazo bacci" Dariya suka sanya su dukansu hadda tafawa, "Allah yashiryeki Husnah" Zahrah tafaɗa tana dariya.. Haka de sukaci gaba da ƴan hirarrakinsu irin na ƙawaye..........
Ƙarfe biyar dai dai wasu rantsa rantsan motoci suka soma tsayuwa a ƙofar gidan su Zahrah duk macen da tafito acikin motar sai kaga tana yatsuna fuska haɗe da soma ƙarewa wajen gidansu Zahrah kallo, motocine kusan guda goma sha biyu suka kawo kayan lefen ahankali aka shiga fito da akwatuna ana shiga dashi cikin gidan su Zahrah.. Fuska babu yabo ba fallasa haka matan nan suka soma shiga cikin gidansu Zahrah,,,,, da fari'a Inna da tawagarta suka tarɓi mutanen haɗe da basu wajen zama, haka suka zauna wasu daga cikinsu suna yatsuna fuska kamar wanda akace su zauna akan kashi...
"Sannunku da zuwa lale marhaba" Wata mata maƙociyar su Zahrah tafaɗa ga matan da suka kawo lefen. Amma kuma daƙyar aka samu biyu daga cikinsu suka amsa mata..
Akwatuna ne harguda shabiyu aka jibge akan wata tabarma dake shimfuɗe,, su Inna ne suka fara ɗagawa matan da suka kawo lefen gaisuwa ciki ciki suka amsa musu cike da isa,,,,, Aunty Raliya ce ma tayi ƙarfin halin cewa "Ga kayanan munkawo Allah yasa ayi bikin a sa'a, Allah kuma yasa asamu kyakkyawar zuri'a" dagajin yanda tayi maganar kaɗai ya isa ya tabbatarmaka cewa kalaman ba anyi su bane cikin daɗin rai,,, da Ameen kawai su Inna suka amsa musu,,, kuɗi Aunty Raliya taciro acikin jakarta bandir ɗin ƴan dubu dubu har na dubu ɗari ta ɗaura akan wani akwati haɗe da kallon ƴan uwanta tace "Muje ko" dukansu miƙewa sukayi suka nufi hanyar waje,,, yayinda Inna tasa yaran maƙotansu suka kwashi kayan tarban baƙin da suka musu aka kai musu cikin mota, maman Badi'a ɗaya daga cikin maƙotan su Zahrah ita tazari dubu hamsin daga cikin kuɗin da suka aje tabawa ƴarta Badi'a tace takaiwa matan dasuka kawo lefen,,, dawowa da kuɗin Badi'a tayi tace ae sun riga da sun tafi koda tafita ƙurar motarsu kawai tagani,,, "To suko wasu irin mutanene haka ae ba haka akeyi ba, ko fa kayan basu tsaya sun nuna mana ba saikace wanda suke akan ƙaya" Maman Badi'a tafaɗi haka cike da mamakin hali irin na matan da suka kawo lefen,,, washe da baki wata mata daga cikin gayyar Inna tace "Kai amma kuwa Zahrah tayi goshi kuga kayafa kamar wanda za a buɗe kanti" ae kuwa basusan cewa Zahrah tayi goshi ba saida suka soma buɗe akwatunan,, kowanni akwati shaƙe yake da kaya nagani na faɗa,, take Inna tasoma rangaɗa guɗa hadda rawan murna.......
(Team Dr.Sadeeq da Zahrah saiku wanke ƙafa don zuwa gano kayan lefen Zahrah🤗)
*31/December/2019*
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
*Wattpad user name fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed: our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
(Kutayani jaje wlh sau biyu kenan typing ɗina yana gogewa😨😨 yanzu saida nayi 2000 words wlh ya kuma gogewa maganan danake wlh yanzu haka ina rubutun nan ina kuka😭😭 wlh abun da ciwo sosai😭😭)
*CHAPTER 74 to 75*
Hayaniya haɗi da guɗan da su Inna keyi shiyayi sanadiyar janyo hankalin Zahrah dakuma Husnah da suke zaune a ɗakin Zahrah sunyi muƙus,,,,
"Ke nifa tashi zanyi naje nabawa idanuna abinci, dan wlh bazan iya zama aɗaki kamar wata sabuwar amarya ba, ke dai da zaman yazamemiki dole saiki ta fama" Husnah tafaɗi haka tana me miƙewa tsaye daga zaunen da take,,, murmushi kawai Zahrah tayi mata haɗe da binta da kallo hartafice daga cikin ɗakin...
Hamdala Husnah tayi haɗe da nunatsantsar farincikinta alokacin da idanunta sukai mata tozali da kayan lefen ƙawartata,,,, lallai Dr.Sadeeq yayi ƙoƙari domin kuwa naira tayi kuka, koda kyawun akwatunan aka barka sun isa sanyaya maka rai, balle kuma aje ga kayan ciki masu kyau da tsadar gaske, wan nan shiyasake tabbatar mata da cewa Zahrah bazatayi kuka ba idan ta auri Dr.Sadeeq, saboda me sonkane kaɗai zai iyayin komai dayasan zai faranta maka rai....
Duk yawan atamfofin dake cikin akwatunan nan saida su Inna suka irgesu kaf, turame hamsin banda su laces haɗi da shaddodi dakuma dangin su materials,, ɓangaren dogin riguna ma akwati guda aka cika dasu, sosai kuma yasaki bakin aljihunsa wajen zaɓo masu kyau da tsada,, haka ɓangaren sarƙokima komai yaji domin kuwa kaf cikin sarƙoƙi da ɗan kunnayenta babu wani mai sauƙin kuɗi acikinsu gwala gwalanta har guda uku,, san nan kuma ɓanagaren jaka da takalma ma yayi ƙoƙari sosai, domin kuwa kusan kowani kaya yanada jaka da takalmi hadda mayafinsa,, wajen kayan shafa ma yayi ƙoƙari sosai wajen fidda naira yasai kayan shafa ƴan yayi masu kyau duk da kuwa yasan cewa ita ba gwanar kwalliyan fuska bace...
"Gaskiya kaya yayi kyau yarinya tayi goshi, ai wan nan kayan ko ɗiyar babban attijiri sai haka" Maman Badi'a tafaɗi haka bayan taƙarewa wani haɗaɗɗen leshi dake riƙe a hanunta kallo wanda a ƙalla kuɗinsa zai kai 50k,,,
"Ƙwarai kuwa yarinya tayi goshi Maman Badi'a ai dama tuntuni nasan fiye da haka ma sai yafaru, ga kaya kan nan harda nasadakarwa!" Inna tafaɗi haka cikin murna...
Wata dake zaune kusa da Inna tace "wan nan haka yake muma dai Allah yabawa namu ƴaƴan mazajen aure masu ƙashin arziki"
Duka matan suka haɗa baki wajen cewa Ameen domin kuwa babu wacce zataƙi ace ƴarta ce tasamu wan nan kayan more rayuwan....
Sai kusan magriba matan dasuka karɓi lefen Zahrah suka soma tafiya, bayan Inna ta yaga musu wani abu daga cikin dubu hamsin ɗin daya rage,, haka suka tafi suna mata godiya suna kuma zuba santin kayan domin kuwa koda maƙiyin Zahrah ne yaga wan nan uban kaya da Dr.Sadeeq yayi mata tabbas dole sai ya jinjina abun.....
Lokacin da Zahrah taga irin yawan kayan lefen da Dr yayi mata kasacewa komai tayi, sosai abun yabata mamaki domin kuwa bata taɓa zaton zai ɓarnata dukiya mai yawa harhaka wajen yi mata lefe ba, bayan kuma yasan cewa ita ba cikakkiyar budurwa bace,,, sai de taƙudura aranta cewa zata faɗa masa kayan sunyi yawa......
Gidansu Doctor...
"Gaskiya da sake Hajiya, yakamata a dakatar da wan nan batun auren na Sadeeq da yarinyar nan, kinkuwa ga gidansu Hajiya? wlhy ko suminti babu a tsakar gidansu zallan turbuɗin yashine, kallo ɗaya zakai musu kafuskanci cewa suɗin faƙara'une basu da komai, kwata kwata ma Sadeeq baisan inda zaije ya nemo aure ba domin a wan nan gidan bana tunanin akwai wata halitta da zata burge wani ɗa namiji acikinsa, kawai dai ni inaga ma asiri sukayi masa wlhy, amma bacin haka banjin dakansa zaije neman aure wan nan gidan!" Auntie Raliya ce ke faɗan haka cikin ɓacin rai.....
Ajiyar zuciya Hajiya tayi cikin ɗacin rai tace "Hmmm Raliya kenan aeni ban isa hana wan nan auren ba ko kinmanta cewa har ƙarana wajen Baffan ku Sadeeq yakai akan naƙi amincewa da aurensa, ni yanzu baruwana acikin lamarin aurensa ko mai ya jajiɓowa kansa shiya sani"
Ƙwafa Auntie Raliya tayi haɗe da sakai tafice daga cikin ɗakin Hajiyar, harga Allah ita sam batason wan nan auren da Sadeeq zaiyi, yarasa ma wacce zai kwaso musu sai wacce wani ya haiƙewa a waje san nan kuma ƴar talakawa futuk...
Auntie Raliya tana fita falo ƙawayenta da ta gaiyato suka kai lefe tare, sukayi caaa akanta kowacce tana ingizata akan cewa tasa afasa auren domin kuwa sam ajin Sadeeq yagirmewa neman aure a wan nan gidan matsiyatan,,, take kuwa Auntie Raliya tahau kan zancen tazauna dabas, takuma ƙuduri aniyar lalata zancen auren abune me sauƙi kuma dakanta zataje ta kwaso kayan lefen ƙanin nata........
Ɓata fuska Zahrah tayi haɗe da tunzuro ɗan ƙaramin bakinta gaba cike da shagwaɓa tace "Dagaske nake faɗa maka kayan lefen nan sunyi yawa, ko ɗazu dawowan Baffa daya gani shima haka yace, kuma kafasan ba kyau yin wasa da dukiya" taƙare maganar tana me langwaɓar da kanta gefe.
Murmushi Dr.Sadeeq yayi haɗe da kwantar da bayansa ajikin kujeran motar dayake zaune akai kana ya lumshe gajiyayyun idanunsa, sautin muryarta nayi masa daɗi sosai...
Shirune yashiga tsakaninsu har na tsawon minti ɗaya.
"Duk abun da mayi miki kin can can ci haka daga gareni ne Zahrah, dan Allah kibar maganar yawan lefen nan, ni banga wani yawa da sukayi ba, naso ma nayi miki wanda yafi wan nan to abubuwane sukai min yawa, amma kin wuce haka a wajena, kuma kinsan ku biyu ne" yafaɗi haka yana me kafeta da idanunsa..
Murmushi kawai Zahrah tayi haɗe da kawar da kanta gefe, sam bataso idan yana kallonta itama ta kalleshi saboda takanjin nauyinsa awasu lokutan,, amma kuma hakanan taji kalmar dayace su biyu ne yaɗan sosa mata rai, wato idan ma ta manta to yatuna mata...
Wani murmushin Dr.Sadeeq yakumayi sakamakon ganin yanda fuskarta ya ɗan sauya lokaci ɗaya yakuma san maganarsa ce batai mata daɗi ba, dama kuma yafaɗi hakanne don yagane cewa tana kishinsa ne ko a'a....
"Bansan wani irin daɗi da kuma farinciki zan tsinci kaina ciki ba aduk sanda wannan ranar taruskeni, amma kuma da zanfi kowa jin daɗi idan har Allah ya gwadamin wannan rana!" yafaɗi haka cikin shauƙi, dason kawar da wancen zancen nasu..
Cike da mamaki Zahrah taɗan saci kallonsa haɗi da cewa "Wace rana ce wan nan?"
"Ranar da zaki zamo mallakina, ranarda za'akawomin ke ɗakina amatsayin matata ta sunna, ranar da zan kwana ina kallon wannan kyakkyawar fuskar taki babuko ƙyafta ido"
Kunyane yakama Zahrah wanda haryakaita ga cusa kanta tsakankanun cinyoyinta, sautari Dr.Sadeeq yakan faɗi abubuwan da suke sanyawa takejin kunyarsa sosai...
Murmushi Dr.Sadeeq yayi haɗe da sake kwantar da jikinsa akan kujeran motar,,,, yana matuƙar son komai na Zahrah ciki kuwa hadda wan nan kunyar nata, tun asalinsa yanason mace me kunya, sai gashi kuma yanzu Allah yabasa, sai de kuma yasan nan gaba kaɗan zaisha fama da'ita saboda idan sunyi aure yasan wan nan halin nata na kunya zatai ta gwadamasa.
Kallon agogon dake ɗaure a hanunsa na dama yayi.
"8:30pm" yafaɗa a bayyane kana yadawo da kallonsa ga Zahrah wacce har yanzu bata ɗago kanta ba.
"Shikenan to tunda dai kunyana kikeji ni zantafi naga dare yasoma yi" yafaɗi haka adai dai lokacin da yake ƙoƙarin ɗaura sit belt ajikinsa..
Sai alokacin taɗago kanta amma bata yadda ta kallesa ba,, "Sai da safe" tafaɗi haka tana me ƙoƙarin fita daga cikin motar domin dama taƙosa yace mata zaitafi saboda tagaji da zaman motan gashi tana da assigment kuma gobe zasuyi submit ɗinshi, san nan kuma tana buƙatar kasancewa ita kaɗai domin tattaunawa da zuciyarta a game da sabon al'amarin dayake shirin kunnu mata kai....
Kansa yajinjina haɗe da cewa "Dama so kike natafi ko?"
Murmushi tayi masa kana taɗan girgiza kan ta alamar a'a, cikin murya me sanyi tace "Bahaka bane kawai de nafara jin bacci ne"
Kansa yakuma jinjinawa cike da gamsuwa haɗe da juyawa baya yaɗauƙo wata farar leda dake aje kan kujeran gidan baya na motar.
"Idan Allah yakaimu da safe zanƙiraki ina fata zakiyi bacci me daɗi" yafaɗi maganar yana me miƙomata ledan dake riƙe a hanunsa...
Shagwaɓe fuska Zahrah tayi haɗe da marairaice manya manyan idanunta da suke sauƙar masa da kasala aduk sanda ya kallesu,, "Gaskiya ni dai a'a nagaji da wayon da kakemin, kuma tun ba yauba na faɗa ma hidiman dakakemin yana yawa!"
Lumshe idanunsa yayi haɗi da buɗesu alokaci guda, idan yanaganin irin wan nan shagwaɓan nata to tabbas zata iya zautar dashi lokaci ɗaya, yafice a hayyacinsa, domin shi shagwaɓan mace nasanyawa yaji feeling ajikinsa sosai,, cikin murya me sanyi yace "Kiyi haƙuri ki ƙarɓa kinji princess ɗina, kinga ba kyu maida hanun kyauta baya!"
Sake turo baki tayi haɗe da kwaɓe fuska, abun mamaki sai taga shima ya marairaice mata fuska kamar wani ƙaramin yaro,, "Please!" yafaɗa cikin muryarsa da tayi ƙasa sosai..
Dole babu yanda ta'iya haka tasanya hanu takarɓi ledan haɗe dayi masa saida safe tafice daga cikin motar,,, yanaganin shigewarta cikin gida yasaki murmushi haɗe da sanya hanu yashafi sajen dake kwance akan ƙuncinsa, key yayi mawa motar haɗe dayin reverse yabar unguwar tasu. Yana tuƙi amma shikaɗai yaketa zuba murmushi, aduk sanda yake tare da Zahrah yakansamun kansa cikin farinciki da nishaɗi, tabbas yanayimawa Zahrah so me tsanani.....
Zahrah kuwa tana shiga cikin gida direct wajen da Inna ke zaune tanufa, ƙoƙarin zama tasomayi haɗi dayimawa Inna sannu da gida.
Washe da baki Inna ta amsa mata bayan ta kafe Zahrah da'ido, Allah Allah take taga menene acikin ledan da Zahrah ta shigo dashi..
Dariyane ya ƙwace mawa Zahrah sakamakon ganin yanda Inna ta tsareta da'idanu tamkar wata mayya.
"Dariyan uban me kike? banson shashanci wallahi" Inna tafaɗi haka ga Zahrah a hasale, ganin bata da shirin buɗe ledan...
Hannayenta tasanya ta toshe bakinta haɗe dasoma ƙoƙarin shanye dariyar ta.
Ledan da tashigo dashi ta buɗe tasoma dubawa gasassun kajine manya guda biyu sai kuma sauran kayan ciye ciye kamar su snacks dakuma chocolate,,
Ledan da kajin ke ciki ta ciro ta miƙamawa Inna ae kuwa hanun Inna har rawa yake lokacin da tazo karɓan ledan tsabar kwaɗayi.
Fari'ar Inna ne yasake yawaita sakamakon ganin kaji da tayi, babu wani ɓata lokaci ta yago cinyar kaza ɗaya takai bakinta,, tsabar daɗin kazar saiga Inna tana lumshe idanu haɗi da jijjiga kai.
Murmushi kawai Zahrah tayi haɗe da ɗaukan sauran kayan tawuce ɗakinta yayinda tabar Inna tayi pieces tana cin kaza hadda rausayar da kai gefe alamar daɗinta takeji....
Jigum tayi haɗe da sake takurewa waje ɗaya akan ƴar katifartata,,, tabbas Dr.Sadeeq yacancanci ta sadaukar masa da duka soyayyarta ko dan saboda halaccin da yayi mata a rayuwa, bazatace batasan menene so ba, itacema zata ba da labari akan so, domin ta ɗanɗana zafinsa me matuƙar ɗaci da dafi,, idan tace Dr.Sadeeq baya burgeta tayi ƙarya, haka kuma idan tace Dr.Sadeeq baida abubuwan burgewa ajikinsa da zasu sa mace tasosa nan ma tayi ƙarya? tabbas Dr.Sadeeq baida wani makusa daga halayya ɗabi'a harma da surarsa yacika cikakken namiji, amma babban abun dake damunta shine batajin tsananin soyayyarsa acikin zuciyarta, bawai tana ƙinsa bane, kawai de zafin soyayyar tasa ne bataji a jiki da zuciyarta, ba kamar yanda taji na Zaid ba,, ada batajin soyayyar Dr.Sadeeq acikin zuciyarta amma ayanzu tayi ƙoƙari wajen ganin takoyawa zuciyarta sonsa, takuma yarda cewa zata iya zaman aure dashi domin baida wani makusa atattare dashi wanda zaisa a ƙisa, murmushine yasuɓuce mata sakamakon tunowa da tayi da irin kallon dayakeyi mata ɗazu, tabbas ya iya nuna soyayyarsa a fili, abu ɗaya ne ajikinsa wanda yake ɗaukar hankalinta, shine ƙwayar idanunsa, duk da cewa shi ɗin namiji ne amma yanada idanu masu kyau wanda zasu sanya maka nutsuwa aduk sanda ka kallesu, hakan yasa ako da yaushe takeson kallon cikin idanunsa amma bata iyawa saboda kunya..... Tunanin Zaid ne yakutso kansa cikin zuciyarta harsai da taji faɗuwar gaba,, "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!" shine abun da tashiga nanatawa acikin zuciyarta,, wannan wani irin bala'i ne? tunda Zaid yashigo cikin rayuwarta shikenan kuma komai nata ya ruguje, lallai itakam taɗaukeshi amatsayin annoba wanda gani da jinsa babu alkhairi .....
Yau Kwanansa ɗaya da wuni ɗaya cur baisanya ko wani irin abinci abakinsa ba, sai ruwan giya dayake ta kwankwaɗa ba dare ba rana,, damuwa ce tayi masa mugun yawa abubuwa gaba ɗaya sun caɓemasa, kallo ɗaya zakai masa kafuskanci cewa yanacikin halin damuwa, domin kuwa lokaci ɗaya ya zabge rama ta bayyana kanta ajikinsa, yayinda manya manyan idanunsa suka sake fitowa waje,, wani irin zafi zuciyarsa keyi masa, baisan da yaushene kuma ta yaya yakamu da soyayyar Zahrah me tsanani haka ba, tunjiya yarasa nutsuwarsa a sakamon labari dayaji daga bakin wanda yasanya yana kulamasa da shiga da ficen Zahrah, inda yasanar masa cewa ankawowa Zahrah kayan lefe, iya ƙololuwar tashin hankali Zaid yashiga dajin wannan magana, sam be shirya wa rasa Zahrah ba saboda rasata dai dai yake da rasa rayuwarsa gaba ɗaya, akuma yanda yakejin matsanancin sonta a cikin zuciyarsa zai iya sadaukar da komai nasa gareta, ko da kuwa ransa ne...
Yanzuma zaune yake yatusa wani ƙaton hoton zanen fuskarta daya zana a daren jiya a gaba yana kallo, saboda tsabar kyawun da zanen yayi idan kagani bazamakace zane bane...
Idanunsa dake kan idanunta na cikin zanen ne suka kaɗa sukai jajur dasu. Saiyanzu yakejin tsanar kansa dakuma tsanar wannan banzan halin nasa, sai yanzu yake tsananin danasanin abun daya aikatawa Zahrah, haƙiƙa yasan cewa ya zalunci Zahrah ya cutar da'ita ya lalata mata rayuwa, kuma hakan da yayi mata shiya nisan ta masa ita, wani irin tsana ne Zahrah tayi masa haka? shin tasan irin zafi dakuma raɗaɗin dayakeji akanta kuwa? yadaina cin abinci tasanadiyar ta, wannan yasa ulcer tayi masa mummunan kamu, gakuma soyayyarta da ta sanya masa ciwo a zuciya,, ta wani ɓangare kuma yana fama da wani matsanancin ciwon kai wanda dashi yake kwana yake kuma tashi, cikinsa kuwa tamkar anhura masa wuta haka yakeji aciki,, hanu yasanya yashafi zanen fuskartata, tabbas idan baisamu Zahrah ba bazai taɓa iya cigaba da rayuwa ba,,, abun da Zaid baisani ba shine tuni ruwan hawaye sun cika idanunsa gangarowa kan fuskarsane kawai da basuyi ba, zumbur haka yamiƙe tsaye haɗe da zura silifas ɗinsa ko wayoyinsa bai tsaya ɗauka ba, haka yafice daga cikin ɗakin nasa....
Yana fita compound ɗin gidan nasu driver'n sa yaƙaraso garesa da sauri,,,, "Oga fita zamuyi ne?" driver'n yatambaya cike da girmamawa,, kai kawai Zaid ya ɗaga masa alamar "eh" jikin driver'n na rawa yace "Oga da wacce motar zamu fita?"
Cike da ƙosawa Zaid yace "Kowacce"
Driver yayi mamaki sosai dajin maganar Zaid domin yasan idan dai har fita Zaid ɗin zaiyi to sai yazaɓi motar dayakeso amma kuma sai gashi yau yace kowacce.. Wata haɗaɗɗiyar baƙar benz driver'n yatuƙo daga cikin parking space zuwa inda Zaid ke tsaye ya harɗe hannayensa acikin aljihun wandon track suit ɗin dake jikinsa..
Zaid nashiga cikin motar driver yabawa motar wuta yayinda me gadi ya wangale musu gate suka fice daga cikin gidan.....
Baffa ne zaune akan dakalin ƙofar gidan yana me latsa ƴar ƙaramar wayarsa, zaman da yayi Zahrah yake jira ta dawo daga aiken da yayi mata,, daf dashi motar tayi parking, hakan yasa Baffa ya kafe motar da'ido don ganin wanene zai fito daga ciki...
A hankali Zaid yabuɗe murfin motar yafito, kallonsa Baffa yashigayi daga sama har ƙasa saboda sarai yagane shine ɗan iskan me kuɗin da yamawa Zahrah fyaɗe, saida Baffa yagama ƙaremasa kallo kafun yakawar da kansa gefe...
Da sallama Zaid yaƙarasa wajen Baffa,, ciki ciki Baffa ya amsa masa sallaman, durƙusawa Zaid yayi haɗe dayin ƙasa da kansa cikin murya me sanyi yace "Kagafarceni Baffa, nasan ban kyautaba amma dan Allah kada ka hanani auren Zahrah, wallahi a yanda nakeji idan bansamu Zahrah ba mutuwa zanyi!"
Baki Baffa yasake yana kallon Zaid, namiji har namiji amma wai yana cewa idan bai auri Zahrah ba mutuwa zaiyi kuji iskanci fa,,
Sake ɗago kansa Zaid yayi haɗe da watsawa Baffa jajayen idanunsa, "Wlh Baffa yanzu da gaske nake aurenta zanyi, kada kace zaka hanani ita dan Allah, wallahi Zahrah tana da matuƙar mahimmanci acikin rayuwata!"
Yanzukam kallon tsab Baffa yashiga yi masa saida yaɗauki kusan minti biyu yana kallon Zaid ɗin kafun yaɗan nisa haɗe da cewa "Bantaɓa tunanin kana da idanun da zaka dawo ka kallemuba, amma sai gashi kadawo kana kallona har kuma kana roƙona dana baka auren Zahrah, idan da kanasonta tunfarko mai yasa baka aureta ba kalalata mata rayuwa? ni bazance maka komai ba saide ince munbarka da Allah saboda bamu da yanda zamuyi dakai, amma kuma kasani bazan baka auren Zahrah ba harsai da amincewarta, idan har tace ta amince zata aureka shikenan nime iya baka aurenta ne" Baffa yana kaiwa nan a zancensa yatashi yayi shigewarsa cikin gida.. Da ƙyar Zaid ya'iya tashi ya zauna akan dakalin da Baffa yatashi hannayensa duka biyu yasanya ya dafe kansa dake yi masa nauyi kamar ze faɗo ƙasa.....
Da ɗan sauri take tafiya tana latsa wayanta burinta kawai shine taganta acikin gida, duk sanyin da akeyi yau yagama ratsata, saboda haka take Allah Allah ta'isa gida.. sam bata lura da akwai mutum a ƙofar gidan nasu ba dan hankalinta gaba ɗaya nakan wayartata...
"Zahrah!" taji anƙira sunanta da murya wacce bazata taɓa mantawa da'ita ba a iya tsawon rayuwarta...
Ja tayi ta tsaya haɗe da maida kallonta inda taji sautin muryar tafito,, tabbas kuwa ba gizo kunenta keyi mata ba shiɗinne dai, kallonta yashigayi da idanunsa wanda suka zama jajaye, itama tsayawa tayi tana kallonsa, a wannan karon kam babu alamar wasa kokuma tsoronsa akan fuskarta,, kallonsa takeyi ido cikin ido...
"Dan Allah Zahrah ki saurareni, wallahi inasonki inamiki so me tsanani, inamiki soyayyar da babu wani wanda zaiyi miki shi a duniyar nan, meyasa bazakisoni ba Zahrah? Inasonki, Inasonki, Inasonki da duka zuciyata, dan Allah kiyarda muyi aure Zahrah!" cikin rauni yaƙare maganartasa saikace ba jarumin namiji ba...
Kallonsa Zahrah tashigayi tundaga ƙasan sa harzuwa samansa, wani irin murmushi tayi masa wanda ita kaɗai tasan ma'anarsa,,, "Bantaɓa tunanin zaka iyayin wannan jarumtar ba, ƙwarai kayi ƙoƙari dahar ka iya tunkarana da wannan maganar, sai de kuma tun awancan lokacin na faɗamaka kafita a rayuwata, idan duka mazan duniya zasu ƙare na gwammace na mutu babu aure dana aureka, ka kalleni da kyau bancancanci zama matar mazinaci kuma ɗangiya ba, niba irin matan nan bane da yacancan ci fasiƙai irinka su samuba, natsaneka Zaid tsana me tsanani, wlhy danaga ranar da zan zamo matarka gwamma acemin naga ranar mutuwa ta, katafi kawai Zaid kaje nabarka da Allah, kuma inaso kasani cewa yau ɗin nan za'a tsaidamin ranar aurena da wanda zuciyata ta aminta dashi, wanda yake kamili me tsoron Allah, shi ba kamar kai bane ɗan giya!" tanakaiwa nan azancenta tajuya daniyar shigewa cikin gida...
Dasauri Zaid ya kamo hanunta haɗe da jawota da ƙarfi tafaɗa cikin jikinsa, dai dau lokacin ne kuma motar Dr.Sadeeq taƙaraso wajen....
*Happy New Year 💃*
*2/january/2020*
__________________________
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 76 to 77*
Saurin turesa tayi haɗe da hankaɗasa gefe da iya ƙarfinta ta ƙwace jikinta daga nasa, wani irin mugun kallo tashiga yimasa haɗe da tofar da yawu aƙasa, da ace wulaƙanta ɗan adam abune me kyau to tabbas da akan fuskarsa zata tofa wan nan yawun ko hakan zai sanya ya gamsu da irin tsantsar tsanar da takeyi masa.
"Banafatan na sake haɗa jikina da wan nan ƙazamemmen jikin naka mai ɗauke da tarin najasa!" cike da tsananin ƙyamata Zahrah ta faɗi haka ga Zaid haɗe da juyawa tanufi hanyar shiga gida..
"Koda kuwa na daina aikata zina nakuma daina shan giya?" Zaid yafaɗi haka cikin dakakkiyar muryarsa...
Cak ta tsayawa daga tafiyan dakeyi, sosai maganar tasa ta daki zuciyarta..
A hankali yashiga takowa zuwa inda take saida yazo gaf da'ita kafun ya tsaya....... " I promise to leave all my bad habit if you wish to marry me, I love you Zahrah, trust me for the sake of God, i will not hurt you!" gaba ɗaya muryarsa tayi rauni dagajin muryartasa kasan cewa yana cikin matsanancin damuwa...
Idanunta da suka kawo ruwa ta ɗago ta watsa masa su,,,,, Shi ɗin ma kallon ta yakeyi da idanunsa wanda suka zama tamkar an watsa musu garin barkono,, sun ɗauki tsawon mintuna biyu suna kallon juna kafun da ga bisani Zahrah tajuya ta shige cikin gida, ko sake waiwayosa batayi ba yayinda yashiga ƙiran sunanta amma bata amsa masa ba harta shige cikin gida, because tagaji da wannan ɗan iskan yaudaran nasa, yanzukam bazata iya ɗauka ba....
Iskan dake cikin bakinsa ya fesar haɗe da meda duka hannayensa cikin aljihun wandonsa, cikin sanyin jiki haka yakoma cikin motarsa driver yayimawa motar key suka ɗauki hanyar fita unguwar batare da sun kula da Dr.Sadeeq dake zaune cikin motarsa ba...
Haƙoransa ya sanya ya danne laɓɓansa na ƙasa komai daya faru akan idanunsa ya wakana sai de baijiyo magan ganun da suka shiga tsakaninsu ba,, wani irin ɗaci yaji maƙoshinsa nayi, iya matuƙa ɓacin rai yashigesa, bakomaine yafi komai ƙona masa ransa ba kamar yanda yaga Zaid yajawo Zahrah jikinsa, hakanan yaji wani irin mugun kishi ya turnuƙe masa zuciya,, babban abun dayafi ɗaga masa hankali shine yanayin daya hango fuskar Zahrah, tabbas yafuskanci wani ɓoyayyen abu daga gareta,,, key yayi mawa motarsa cikin ƙunan rai yayi reverse haɗe da barin ƙofar gidan nasu batare da ya aika ayi masa ƙiranta ba..
Zahrah na shiga cikin ɗakinta ta durƙusa a ƙasa haɗe da fashewa da wani irin kuka me tsuma zuciya kaicon zuciyarta da ta so mata namiji irin Zaid, ashe da gaske shiɗin mazinaci ne tunda gashi da bakinsa yafaɗa, kuka tashiga yi tamkar wacce aka sanarmawa da ranar mutuwarta, yayinda wani abu yataso ya tokare mata ƙirji wanda batasan komenene shi ba kamar yanda batasan kukan me takeyi ba...
Driver yana parking motar Zaid yace yafita ya bashi waje, aikuwa babu musu driver'n yafita daga cikin motar..... Kansa ya kafa ajikin kujera haɗe da fidda wani irin zazzafan numfashi ta bakinsa, zuwa yanzu kam bazai iya jurewa ba, sam bazai iya jure raɗaɗi dakuma azaban soyayyar Zahrah dake damunsa ba, tabbas da ace zai iya to da yayi iya ka ƙoƙarinsa wajen ganin ya yakice soyayyarta acikin zuciyarsa amma hakan bazai yiwuba domin kuwa duk kowani kwanan duniya soyayyarta ƙara ninkuwa takeyi acikin zuciyarsa, zuwa yanzu soyayyar Zahrah babu inda bata ratsa acikin jikinsa ba,,,, a ƙalla yakai kusan 30 minute acikin motar yana saƙawa da kuncewa, da ƙyar ya'iya fitowa daga cikin motar kai tsaye yanufi babban parlour'nsa dake cikin guest house ɗin nasa, domin kuwa daga gidan su Zahrah guest house ɗinsa suka yiyo....
Yana shiga cikin falon ya faɗa kan doguwar kujera haɗe da lumshe kyawawan idanunsa, kansa ne ke saramasa yayinda juwa ke ɗibansa, lallai yazame masa dole yasamawa kansa mafita, yazama dole yafarka daga wannan mafarkin daya keyi tabbas al'amuransa a yanzu suna masa kama da al'amara,, tabbas yana buƙatar samun relief daga damuwar dayake ciki, amma sai dai babu amfanin shangiya a yanzu domin kuwa koda yashama bata basa wani relief ɗin da ya kamata, miƙewa yayi yashiga cikin ɗakinsa, kai tsaye wani ɗan drower yanufa haɗe da buɗewa, hanu yasanya ya ɗauko wata wayarsa ƙirar techno phantom 9 wanda dama yana ajewane saboda rana irin haka, kasancewar baifito da wayoyinsa ba duk yabarsu a gida,, yana kunna wayar ya laluɓo wata lamba haɗe da turawa lambar text message, yana ganin alamar saƙon ya isa inda yakeson yaje yayi switch off ɗin wayar haɗe da maidata inda ya ɗaukota kwanciya yayi akan makeken gadonsa wanda yasha shumfuɗa ta alfarma, cusa kansa yayi cikin pillow haɗe da soma fitar da numfarfashi akai akai....
A hankali taturo ƙofar ɗakin wanda kafun ma tashigo tuni ƙamshinta yarigata shigowa, sanye take da jan wando pencil wanda yayi matuƙar bayyana kyakkyawar surar jikinta yayinda rigarta yakasance baƙa me kyau, rigan irin masu faɗin wuyan nan ne hakan ne yasanya manya manyan breast ɗinta bayyana kansu tasaman rigar,, takalmine me uban tsini a ƙafarta yayinda ta tufke dogon gashin kanta da jan ribbon kalan wandonta,, kallo ɗaya zakayi mata kafahimci cewa wayayyar macece ƴar duma, shigarta kaɗai ya isa yabayyana maka ainihin ko wacece ita, saboda bashigane da mata masu mutumci sukeyi su fita ba kamar yanda ita tayi, domin kuwa ko ɗan kwali babu akanta, wani irin murmushine kwance akan fuskarta dake nuna alamar cewa tana cikin farinciki,, lumshe idanunta tayi haɗe da buɗesu alokaci guda, kallon surarsa kaɗai ya isa sanya mata nutsuwa, tajima tana tsumayi da kuma fatan Allah ya sake ɗaurata akansa, harta cire rai saikuma gashi yau shi da kansa ya gayyatota, lallai zata iya cewa a rana irin ta yau tafi kowa sa'a..
Duk da yaji ƙamshin turarenta acikin hancinsa hakan baisanya yaɗago kansa ba,,
Cikin taku irin na matan da suka goge wajen iya ɗaukar hankalin ɗa namiji tashiga takowa har zuwa inda yake kwance ya yinda juyawa ƙofa baya...
Hanunta tasanya a bayan wuyansa haɗe da soma shafawa a hankali,, cikin wata murya me sanyi dajan hankali tace "Man!"
Shiru yayi bai amsa mata ba, duk da kuwa cewa yanajinta,,, ganin bai amsa taba yasanya tayi murmushi haɗe da cire takalman dake ƙafarta ta hawo kan gadon,, bakinta ta sanya adai dai saitin tsakiyar bayansa tashiga tsotsa haɗe da shafa bayan wuyansa a hankali,,,, wani irin zubawa Zaid yaji tsikar jikinsa tayi, adai dai sanda take ƙoƙarin nuna masa wani sabon salo.... "Meenal!" yaƙira sunanta da wata irin murya wacce ta riga da ta cushe..
Murmushi Meenal tayi haɗe da mirginowa ta dawo gabansa suna fuskantar juna, lumshe idanunta tayi alokacin da tayi arba da kyakkyawar fuskarsa, wallahi tana matuƙar son Zaid komai nasa me kyaune daga ciki har waje, ba abunda yake ɗaukar hankalinta akan fuskarsa kamar wannan kyakkyawan sajen nasa dayake shan gyara da mayuka masu kyaun gaske..
"Nayi kewarka Man, ashe de kaima kayi kewata? katafi ka barni da tunanin daɗin da kajiyar dani, wanda har rana me kamar ta yau babu wani ɗa namiji da yajiyar dani kwatan kwacin wannan" Meenal taƙare maganar cikin yanayi na shagwaɓa haɗe da sake matsowa tashige cikin jikinsa,, ɗan guntun murmushi yasakar mata haɗe da soma ƙarewa fuskarta kallo, Meenal kyakkyawar yarinyace wanda kyawun nata kuma yazama na ɗan maciji, domin kuwa Meenal tantiriyar ƴar iska ce kuma cikakkiyar mazinaciya wanda idan ta kafamawa namiji ƙahon zuƙa duk nuƙu nuƙunsa sai ta jefasa cikin raminta, sai dai idan kuma shiɗin ya kasance gwaska na gasken gasken, tofa nan ne zasu dai dai ta, kamar dai Zaid da ta buga ta rawa yaƙi faɗowa raminta, domin kuwa shi ɗin ma ɗan iskane me lasisi san nan kuma gwaska ne me zaman kansa, wannan yasa Meenal takasa turasa a cikin raminta..
Hanu Meenal tasanya akan faffaɗan ƙirjinsa tashiga shafawa haɗe da cusa kanta acikin wuyansa cike da ƙwarewa take manna masa kiss,, tamkar wata mayya haka take sake shigewa cikin jikinsa..
Lumshe idanunsa yayi haɗe da cusa hanunsa cikin sumar kanta,, take yasoma sauƙe ajiyar zuciya akai akai domin kuwa gani yake tamkar Zahrah ce kwance haka a jikinsa,, idanu Meenal ta kafesa dashi cike da mamakin irin sauyawan da yayi, nafarko ta hango tarin damuwa acikin idanunsa yayinda na biyu kuma ta hango wani abu mai ɗaure kai acikin idanunsa,,, "Man!" taƙira sunansa cikin wata irin murya, idanunsa kawai ya jefa acikin nata idanun batare da yace da'ita komai ba,, dama haka takeso burinta shine yaɗaga kyawawan idanunsa ya kalleta,, take ta sauya salon nata kallon ta marairaice idanunta,, fuskarta ta matso daf da tashi fuskar lokaci ɗaya tasoma ƙoƙarin haɗe bakinsu waje ɗaya, kamar koda yaushe ƙin aminta da hakan yayi da sauri ya kawar da kansa gefe, saboda hakan baya daga cikin tsarinsa haɗa miyau da matan bariki, domin babu abu mafi saurin sanya shaƙuwa kamar haɗakar yawun baki, sosai kiss yake sanya shaƙuwa a tsakanin masu yinsa, domin haɗuwar yawun bakuna biyu wani sinadari ne na musamman,,,, bata damu ba domin dama tasansa bayawa mace kiss batakuma san dalilinsa na hakan ba, wan nan kuma ita duk ba damuwarta bane matuƙar zai kusanceta to zatafi kowa farinciki,,,,, hanunta ta sanya akan mararsa tashiga shafawa a hankali haɗe da ɗaura bakinta akan nipples ɗinsa, jawota yasakeyi jikinsa bayan ya cire mata ƴar ƙaramar rigar jikinta, kansa ya cusa acikin ƙirjinta yana me shaƙar ƙamshin turarenta, haɗe da sanya hannayensa a bayanta yasoma shafawa a hankali,, take Meenal tasoma sauƙe numfashi akai akai dama ƙiris take jira saboda akunne take ƙwarai... Lokaci ɗaya Meenal tarikice wasu irin salo take gwadawa Zaid masu sanya mutum ya fita a hayyacinsa, yayinda shima yagama ruɗata da nasa salon har saida yakusa sanyata shiɗewa,, amma kuma wani abun mamakin shine yanayin hakan ne cikin wani irin yanayi wanda baisan dame zai ƙira sunan yanayin ba, kwata kwata baijin wani abu mai suna sha'awa a jikinsa duk dakuwa irin romancing ɗinsa da Meenal keyi, lumshe idanunsa yayi haɗe da jawota yadawo da ita ƙasansa aniyarsa shine ya kusanceta amma kuma sai yaji zuciyarsa tashiga bugawa da sauri sauri yayinda Zahrah tashigo cikin ransa ta tsaya cak, take idanunsa suka haskomasa irin kallon tsanan da tayi masa ɗazu, nan danan yaji komai yafice masa arai, da sauri ya ture Meenal gefe haɗe da sanya hanu ya dafe kansa da yayi masa nauyi, da wani irin kallo Meenal da takai ƙololuwa wajen sha'awa ta bisa, meye haka yakeyi? badai halin nasa na wulaƙanci zai gwada mata ba? idan kuwa hakane Zaid yacuceta, saida yagama jefata acikin masifaffiyar sha'awarsa san nan yajuya mata baya, hanu tasanya ta rungumosa ta baya haɗe da soma goga masa breast ɗinta akan bayansa "Meke damunka Man? kada kabari damuwa ya hanaka jin daɗin rayuwa please" tafaɗi haka cikin narkakkiyar murya, hanunsa yasanya ya zameta daga jikinsa wani irin haushinta ma yake ji, miƙewa yayi direct ya wuce toilet ɗinsa ko waiwayota baiyi ba, baki sake haka Meenal tabisa da kallo harya shige cikin toilet ɗin,, kuka ta fashe dashi haɗe da matse cinyoyinta, tsakani da Allah take kuka domin kuwa iyaka cuta a wajenta shine abun da Zaid yayi mata...
Zaid kuwa yanashiga bathroom ya zame wandon dake jikinsa haɗe da nufar inda babban bathtub ɗin wankansa yake, ruwa ne me kyau da tsabta acikin bathtub ɗin, amma duk da haka saida ya zubar yakuma taran wani ruwan, turaren wankansa me daɗin ƙamshi ya sanya a cikin ruwan haɗe da shiga cikin ruwan ya kwanta a hankali,, lumshe idanunsa yayi haɗi da jingina kansa, zafi yakeji adai dai saitin zuciyarsa, tabbas yanaji ajikinsa cewa akwai abun da zai faru dashi bayan wanda yake faruwa dashi yanzu, "wace irin soyayya ce haka yake yiwa Zahrah me zafi?" tambayar da kullum sai yayimawa kansa kenan, lallai yau yasake tabbatar mawa kansa cewa yazama mutum me rauni, A she dama akwai wata rana da zai iya kasancewa haka? yaƙira Meenal ne don taɗebemasa kewa yakuma samu ya rage tarin sha'awar dake damunsa, domin kuwa har wani ciwo yakeji mararsa nayi masa, amma kuma sai gashi ya kasayin komai da Meenal, ashe ba Meenal ɗin bace muradinsa Zahrah ce, haƙiƙa yasake yardarwa kansa cewa abunda kake so shi yake wahalceka sannan kuma yasake tabbatar mawa kansa cewa ƘAUNA guda ɗayane tal aduniya, SO ne kawai yake da yawa, amma ƙauna ƙaunace,, kafun yaƙira Meenal yayi tunanin cewa idan tazo zata gusar masa da damuwarsa, sai kuma bayan tazo yaga ashe bazata iya ba, ashe yin sex da shan giya basune maganin damuwarsa ba, Zahrah har lau itace maganin damuwar sa,, anya kuwa zai warke daga damuwar nan tasa?
Yajima acikin bathroom kafun yayi wanka yafito jikinsa sanye da farar rigar wanka,, kallonsa ya maida kan gado inda yabar Meenal don ganin wani hali ta ke ciki domin kuwa sarai yaji kukanta lokacin dayake cikin bathroom,, dariyane taso ƙwacemai sakamakon ganin Meenal da yayi takure a can ƙarshen gado tana bacci, yayinda ta cusa hanunta na hagu a ƙasanta, sarai yasan Meenal jarabebbiya ce yanzu haka fingering tayi don samawa kanta relief, abun da yafi tsana kenan wato mutum yayi amfani da kansa don biyan buƙatarsa, amma kuma wannan halin Meenal ne,, kai kawai ya girgiza haɗe da nufan gaban dressing mirror ɗinsa, vaseline yashafa ajikinsa kasancewar garin ana ɗan yanayi na sanyi, saida ya feshe jikinsa da body spray kafun yasanya kayansa riga da wando na jeans masu kauri, sosai kayan sukai masa kyau, kuɗaɗe yaciro a cikin drower ɗinsa ya ajiye a kusa da Meenal daketa sharan bacci, kana yayi ficewarsa daga ɗakin, direct bai zarce ko inaba sai compound ɗin gidan, yanzu kam shida kansa yakeson yayi tuƙi, don hakane ma yazaɓi BMW blue colour amatsayin wacce zai fita da ita....
Dr.Sadeeq
Duk yanda Dr.Sadeeq yaso samawa kansa nutsuwa hakan yagagara domin kuwa sam zuciyarsa bata amince da zuwa wajen Zahrah da Zaid keyi ba, duk da yau yafara ganinsa aƙofar gidan su Zahrah'n amma jikinsa ya basa cewa ba yaune zuwansa na farko ba, amma bakomai zaiyi maganin abunne zai nisanta Zahrah da Zaid nisantawa me tsanani kuwa, da wannan tunanin bacci ya ɗaukesa...
Washe Gari.
Dasassafe Zahrah ta shirya tayi tafiyarta makaranta sai dai a ranta tana mamakin rashin ƙiranta da Dr.Sadeeq yayi, rabonta dashi tunjiya da yamma sunkuma rabu dashi akan cewa zai ƙirata sai gashi kuma har zuwa yanzu bai ƙirata ba, uzuri tayi masa akan cewa ko aikine yayi masa yawa domin tasan hakanan Dr.Sadeeq bazaiƙi ƙiranta ba...
Tana tafiya ba jimawa motar Dr.Sadeeq ta tsaya a ƙofar gidan nasu, fitowa yayi daga cikin motar yasha adonsa cikin blue ɗin shadda sosai kuma yayi kyau,, yaro ya aika cikin gidan yace yace ana sallama,, bajimawa yaron daya aika yadawo ya shaida masa ance me gidan yana fitowa.... Washe da baki Baffa yaƙaraso wajen Dr.Sadeeq dake tsaye " Maraba da Likita, dama kaine ai da kashigo ciki amma ka tsaya a waje sai kace wani baƙo"
Murmushi Dr.Sadeeq yayi cike da girmamawa ya sunne kansa ƙasa haɗe da durƙusawa ya gaishe da Baffa,, fuska cike da fari'a Baffa ya amsa gaisuwan,,,
"Aikuwa kayi rashin sa'a domin kuwa mutumiyar taka bata jima da fita a gidan ba, tatafi makaranta ko karyawa bata tsaya tayi ba, amma ina ga zaifi kyau mushiga daga ciki ko"
"A'a Baffa nan ɗin ma yayi, dama wajenka nazo ae"
"To to masha Allah, saimu zauna ae ko abisa dakalin nan" Baffa yaƙare maganar yana meyi mawa Dr.Sadeeq nuni da dakalin ƙofar gidan.
Duk yanda Baffa yaso Dr.Sadeeq ya hau kan dakalin su zauna ƙiyawa yayi, domin kuwa Baffa surikinsa ne baidace ace sun zauna gaf da juna ba kodan saboda kara da matuntawa,,
"Shikenan to tunda dae kaƙi zama, inajinka Allah yasa dai lafiya?"
Kansa yaɗan sosa haɗe da sakin murmushi "Lafiya ƙalau Baffa dama akan maganan aure nane da Zahrah..." sai kuma yayi shiru ya kasa ƙarasa maganar dake cikin bakinsa, gani yake tamkar idan yafaɗi maganar kai tsaye Baffa zaice masa yayi gaggawa ko kuma yace yayi rashin kunya...
"Ka kwantar da hankalinka Likita kafaɗi duk wani abu dake ranka" Baffa yafaɗi haka ga doctor ɗin..
"Am dama...dama inaso ne kabani izini nasake turo magabatana dan sukawo sadaki san nan kuma a tsaida ranar aure"
"Alhmdlh to ai wannan abun farinciki ne Likita, wannan ae bawani abun damuwa bane, nabaka dama ka turosu aduk sanda kakeso, sai de kuma zakaɗanyi haƙuri, saboda zansa lokacin da ɗan tsayi saboda kasan ba a yin aure kai tsaye haka dole sai anɗanyi mawa yarinya sayayya, ina fata hakan bazai sosa ranka ba?"
Murmushin jin daɗi Dr.Sadeeq yayi haɗe da cewa "Naji daɗi sosai Baffa, amma kuma maganar sayayya basai kun wahalar da kanku ba, domin zuwa yanzu gidan da zamu zauna baya buƙatan komai, saboda haka don Allah kada kusa kanku a wahala"
Murmushi Baffa yayi haɗe da cewa "Ƙwarai mungode da wannan ƙoƙarin naka, amma sai de nace kayi haƙuri, duk da cewa mahaifin Zahrah baya raye ni ƙaninsa ina raye kuma niɗin ma ubane a wajenta, zan yi amfani da ɗan abun da nake dasu wajen ganin namata kayan ɗaki iya dede ƙarfina, kamarde yanda kowani uba keyiwa ƴarsa, wannan shine kaɗai gatan da zamu iyayi mata a yanzu" Baffa yafaɗi haka da iyaka gaskiyarsa..
Ajiyar Zuciya Dr.Sadeeq ya sauƙe, haƙiƙa shi Zahrah kawai yakeso bawai wani abu na daban ba, kuma shi baiso akawota da komai, domin musamman ya ware mata ɓangarenta, kuma tuni yabawa wani abokinsa me saida furnitures a Dubai order akan akawomasa setin kujeru dakuma gado harma da duk wani abu wanda yasan zai ƙawata ɗaki,, amma tunda yaga Baffa yadage akan cewa shima zaiyi iya nasa ƙoƙarin shikenan zai ware wani ɗaki na da ban idan yaso sai a sanya kayan da Baffan yayi mata acan,,, cike da mutuntawa Baffa da Dr.Sadeeq sukayi sallama....
Baffa na shiga gida ya kalli Inna dake zaune,, "Salame inajin fa tafiyana yola yagabato idan banje jibi ba to zanje gata insha Allah"
Fuska ɗauke da mamaki Inna ke kallonsa, "Yola kuma Malam?"
"Ƙwarai kuwa, kinga fitana ɗin nan to yaron nan ne Sadeeq yazo min da maganar cewa inbasa dama yaturo magabatansa don sukawo sadaki akuma sa rana, to ni dai nace yaturosu duk sanda yakeso, yanzu dole zanje yola insanya fili dakuma gonan nan namu na gado a kasuwa idan aka siya intarkata kuɗin nan nasamu nasaiwa yarinyarnan kayan ɗaki dakuma kayan aikace aikace kamar de yanda kowani iyaye kemawa ƴarsu dan baiyiwuwa ace mu miƙata haka"
Ajiyar zuciya Inna tasauƙe haɗe da gyara zama " Duk naji batunka Malam, amma kuma mezai hana kabar shi mijin nata yayi mata komai, ae naga yana da halin da zai iyayi mata fiye da wannan ma"
Murmushi kawai Baffa yayi shi kam tun ba yau ba yasan cewa bakoda yaushe ne Inna take gane karatun da'ake biya mata ba, don haka baiƙara cewa da'ita komai ba yawuce ɗakinsa, domin yasan kozai shekara a wajen yanason ganar da'ita tofa bazata fahimcesa ba,,, Inna kuwa baƙin ciki ne yakamata ina ma laifin yace zaiƙara jari da kuɗin, sai yace wani wai zai siyawa Zahrah kayan ɗaki,, haka taita ƙananun maganganunta babu maijinta ma balle yatanka mata......
Da yamma Dr.Sadeeq yaƙira Baffa yasanar masa cewa Baffansa zaizo da dare donsu tsaida magana, duk da cewa Baffa yayi mamakin sauri irin na Dr.Sadeeq ɗin amma saiya share yace Allah yakawosu lafiya,,
Hargida Baffa yaje yasanarwa Alhaji Umar abun da Dr.Sadeeq yace, kuma dama Alhaji Umar ɗin tuni yasan da maganar saboda duk abun da yafaru Baffa yanazuwa ya sanarmasa har kawo lefen da akayi ma Baffa yasanar masa,, sosai Alhaji Umar yayi murna yakumace zaizo gidan Baffa'n da dare a ƙarɓi baƙin dashi......
Kamar yanda Dr.Sadeeq yafaɗa hakane yakasance domin ana idar da sallan Isha Baffa Amadu da wani shaƙiƙin amininsa suka zo gidansu Zahrah,, sosai Baffa da Alhaji Umar suka musu tarba na mutunci,, zama sukayi haɗe dayin magana ta fahimtar juna, nan Baffa Amadu ya miƙa sadakin Zahrah ga Baffa naira dubu ɗari (100,000) bawani ɓata lokaci Baffa yasanya lokacin aure wata ɗaya, aikuwa take kowannensu yacika da farinciki haka sukayi sallama cike da girmama juna.......
(Team Dr. Saiku fitarmana da ankon biki, nasan duk Baba Zaid ze saya mana auren Zahrah'nsa ne ae 🤣🤣😜)
*4/Junuary/2020*
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
~Fatymasardauna~
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 78 to 79*
Zahrah na zaune a ɗakinta Inna takutso kanta cikin ɗakin.
"Idan kin gama rubuce rubucen banzan naki kije Baffan ki nanemanki!" Inna tafaɗi haka aƙufule, ko jiran amsan da Zahrah zata bata batayi ba tayi ficewarta acikin ɗakin,,, da kallon mamaki Zahrah tabi bayan Inna wai meke faruwane tun dawowarta amakaranta tafuskanci cewa ran Inna a matuƙar ɓace yake da'ita, domin kuwa ko abincin rana Inna batayi mata tayi ba, kamar yanda ta sabayi mata kullum, to koma dai menene Allah yasa bawani abu bane me zafi... Tattara books ɗin dake gabanta tayi haɗe da miƙewa ta sanya hijab a jikinta kana tafice daga cikin ɗakin.....
Da sallama ɗauke a bakinta takutsa kanta cikin ɗakin Baffan nata,, zama tayi akan tabarman dake shimfuɗe a tsakiyan ɗaki, haɗe dayi mawa Baffa barka da gida,, fuska ɗauke da fari'a Baffa ya amsa mata..
Gyara zama Baffa yayi haɗe da cewa "Bakomai yasa nayi ƙirankiba sai dan na sanar dake abun dayake faruwa sannan kuma na danƙamiki haƙƙin ki a hanunki, yau da safe yaron nan likita yazo yasameni akan cewa zaituro magabatansa don sukawo sadakin ki, nakuma bashi dama, to yanzu dai sun riga da sun danƙamin sadakin ki a hanuna saboda haka ga abunki naira dubu ɗari ne cus nakine halak malak" Baffa yaƙare maganar yana me miƙa ma Zahrah maƙudan kuɗin dake hanunsa....
Gaba ɗaya jitayi jikinta yayi sanyi laƙwas gaba ɗaya duk wani kuzarinta ya gudu, hakanan taji wani iri a cikin zuciyarta.
"Ki karɓa mana Zahrah" Baffa yafaɗi haka ganin da yayi ko ɗago kanta takasa yi.
Girgiza kanta ta shigayi a hankali cikin muryarta me sanyi tace "Duk abun da ka yanke a gareni Baffa dai dai ne, amma maganar sadaki ka riƙe a wajenka, saboda ko kabani babu abun da zanyi dasu!" taƙare maganar cikin ladabi.
"A'a Zahrah ki karɓi abunki haƙƙin kine, saboda haka nima babu abunda zanyi dashi ki karɓi abunki saiki adana a wajenki, idan kuma wani abu zaki saya saiki saya, amma kada kiyi almubazzaranci dasu, zaifi kyau kisaya abu me mahimmanci wanda zai amfaneki yanzu ko gaba" maganar da tafito daga bakin Baffa kenan.
Shiru Zahrah tayi ita tama rasa yanda zatayi gaba ɗaya yanayinta yasauya, cikin sanyin jiki Zahrah tasanya hanu ta karɓi sadakin nata a hanun Baffa bawai dan ranta yasoba sai dan Baffa ya matsa akan cewa saita karɓa..
"Yauwa kinga idan kika riƙe abunki a hanunki ae yafi ko, sai kuma maganar sa rana, nasa nanda wata ɗaya, ai inaganin hakan yayi domin kafun lokacin insha Allah mungama iya ƙoƙarin da zamuyi wajen sayan ƴan kayayyakin ɗaki"
Wannan magana ta sa rana yafi komai rugaza mata zuciya, fiye da maganan sadaki, haka nan taji faɗuwar gaban da takeji ya tsananta,, amma haka tayi mawa Baffa sallama cikin sanyin jiki tanufi ɗakinta...
Zama tayi akan katifarta haɗe da rumtse idanunta, take hawaye suka shiga fitowa daga cikin idanunta suna gudu akan fuskarta,, shikenan yanzu saura mata wata ɗaya tazamo matar aure? tambayar da tayiwa kanta kenan, bazata iya faɗan wani irin yanayi ta tsinci kanta aciki ba, fargaba ne ko kuma tsoro ne shine abun da bata sani ba,, idanunta ta buɗe haɗe da maida kallonta ga kuɗaɗen dake riƙe a hanunta,, tsurawa kuɗin idanu tayi tamkar mai son gano wani abu ajikin kuɗin,, hawayene suka kuma ɓalle mata, batasan dawani idanu zata kalli Dr.Sadeeq ba, shi wani irin mutum ne? yasani ƙwarai cewa ita ba cikakkiyar budurwa bace da ita da bazawara duk ɗaya suke, amma kuma shine ya cire maƙudan kuɗaɗensa yabada amatsayin sadakinta alhali kuma farashinta baikai haka ba, ita ba irin matan nan bane dasuka dace a sayesu da tsada har haka ba, domin kuwa acikin abubuwa goma da zasu ƙara farashinta babu kaso tara, saboda haka bata cancanci wannan sadaki ba,, hanu tasanya ta share hawayenta, haƙiƙa bazatace batason Dr.Sadeeq ba amma kuma batajin son nasa acikin jini da jikinta, amma hakan bawai wani abu ne da zaisanya taƙi aurensa ba, domin shi ne ma mutum na farko aduniya daya cancanci ta aura, kodan halaccin daya gwada mata a rayuwa.... Cikin wata jakarta tasanya kuɗin sadakin nata, haɗe da dawowa ta kwanta akan katifarta, bazama ta iya ƙarisa assigment ɗin nata ba domin kuwa gaba ɗaya yanayinta yasauya damuwa ta bayyana a tattare da'ita,, da ƙyar ta iya jawo wayarta taƙira Husnah ta sanar mata da duk wani abun daya faru,, daɗine ya kama Husnah sosai take ta hau farinciki haɗe da cewa gobe zatazo yakamata su fara shirye shiryen biki tunda wuri, domin wata ɗaya bawani lokaci ne me tsawo ba idan har darai da kuma lafiya...
*****
"Kiyi kuka da kyau Saleema amma kuma kozaki mutu bazaki auri Sadeeq ba matuƙar bai fasa auren da zaiyi da waccar ƴar ƙasƙantattun mutanen ba, ni bazan iya haɗa iri da jinsin matsiyata ba!" Abunda Hajiya Habiba take faɗa kenan cikin ɓacin rai.
Ɗago kai Saleema tayi takalli mahaifiyarta ta fuska caɓa caɓa da hawaye, cikin muryar kuka Saleema tasoma cewa " Wlhy inasonsa Mom kuma bazan taɓa iya auren wani bayan shiba, nidai na amince zan aureshi a haka, idan yaso bayan auren sai nasan yanda zanyi naƙori ita yarinyar"
Kallon ke shashasha ce Hajiya Habiba tashiga yi mawa Saleema, cike da baƙin ciki taja tsuka haɗe da watsawa Saleema'n harara "Nibansan yaushe zuciyarki ta mutuba wlhy Saleema, ashe ke baki da hankali? to nifa kisani nagama maganata aure da Sadeeq ne anfasa, kuma suzo su kwashe lefensu bama buƙata, domin kuwa kamarni Hajiya Habiba bazan lamunci cinfuskaba, saboda abunda suke shirin yi yanzu cin fuskane a gareni" fuuuu haka tayi wucewarta sama, tabar Saleema tana ta ruskar kuka, saikace wanda akace ubanta ya mutu....
****
Baffa na zaune a wajen sana'arsa wasu maka makan motoci guda biyu suka faka adaf dashi.. Sosai yayi mamakin ganin Alhaji Ma'aruf yakuma dawowa garesa a karo na biyu, wanda ko kusa baiyi tunanin haka ba..
Bayan sun gaisane Alhaji Ma'aruf ya nisa haɗe da cewa "Nasan zakayi mamakin dawowata gareka Malam Hayatu, sai de kuma me nema baikamata ya gajiya ba"
Ajiyar zuciya Baffa yasauƙe haɗe da tattaro duka nutsuwarsa yadubi Alhaji Ma'aruf...
"Bazan taɓa ɓoyemaka ba Alhaji, kamardai yanda nafaɗa maka afarko yanzu ma hakane, domin maganan da nakeyi maka yanzu ma jiya aka kawo sadakin yarinyar, saboda haka sedai nace kawai kuyi haƙuri"
Kai Alhaji Ma'aruf yashiga jinjinawa, zuwa yanzu dolensa zaibawa Zaid haƙuri akan cewa yayi haƙuri yacire yarinyar aransa, domin kuwa idan ba wani ikon Allah ba to babu alamun cewa Zaid zaisamu auren yarinyarnan Zahrah..
Haka Baffa da Alhaji Ma'aruf suka rabu, bayan Alhajin yayi mawa Baffa alkhairi maiyawa, amma sam wannan karon Baffa yaƙi karɓa yace bai buƙata, duk yanda Alhaji Ma'aruf yaso Baffa ya amshi kuɗin hakan bai samu ba,, haka Alhaji Ma'aruf yayimawa Baffa sallama shida tawagar body guard ɗinsa suka bar wajen, sam Alhaji Ma'aruf baiji daɗin hakan ba, yaso ace ɗansa yasamu abunda yakeso.....
Cike da tsananin damuwa Alhaji Ma'aruf ke kallon Zaid dake zaune a ƙasa yayi shiru, gaba ɗaya ya sanja, komai nasa yazama sanyi sanyi, ga alamomin damuwa da suka bayyana kansu a jikinsa, baisan wani irin masifaffen soyayya ɗannasa ya kamu dashi ba, baimasan taya ya Zaid zai ɗauki maganar da zai faɗa masa ba, amma dai yazama dole yafaɗa masa gaskiya amatsayinsa na mahaifinsa.
"Zaid!"
Alhaji Ma'aruf yaƙira sunan Zaid murya a tausashe.
"Na'am Dad" Zaid ya amsa murya ƙasa ƙasa.
"Inaso kabani hankali da nutsuwarka, dan Allah Zaid ka kwantar da hankalinka, nasani kuma kaima kasani nema cikin nema haramunne, kacire wannan yarinya acikin zuciyarka domin kuwa yau naje nasamu shi Baffan nata, yakuma shaidamin cewa a halin yanzu har ya karɓi sadakinta, saboda haka zaifi kyau kacireta a zuciyarka, kanemi wata nasan babu wata mace da zata ƙika"
Tamkar wanda Dad ɗin ya watsa masa ruwan zafi haka yaji sauƙar maganganun mahaifinsa acikin kunnuwansa, da sauri yaɗago jajayen idanunsa ya watsawa mahaifin nasa su,, bakinsa na rawa yace "Ankarɓi sadakinta kuma Dad?"
"ƙwarai kuwa Zaid abunda Baffan nata yafaɗamin kenan, shiyasa nace ka cireta a ranka"
Kai Zaid yashiga girgizawa,,,,, "Bazai taɓa yiwuwaba Dad, wlhy wani bazai taɓa auran Zahrah ba matuƙar ina numfashi acikin duniyar nan, inasonta fa Dad meyasa bazaku gane hakan ba? bazan iya cigaba da rayuwaba idan har babu Zahrah a gareni, nasan laifinane Dad, amma duk da haka bai dace a hanani Zahrah ba, saboda inasonta inamata wani irin so me tsanani please Dad niko yanzu dan Allah a ɗaura mana aure idan yaso daga baya ni na amince zan shawo kanta, nasanma tana sona har yanzu, kuma nasan daga baya zata yafemin abunda nayi mata!"
Cike da tsananin mamaki Dad ke kallon Zaid wanda gaba ɗaya ya ruɗe alokaci ɗaya, anya kuwa ba aljanune suka shiga jikinsa ba ? Dad yatambayi kansa cike da tsananin mamaki, domin kuwa sam Zaid ba haka yake ba, shi mutum ne me nuƙu nuƙu amma kuma wani babban abun mamaki shine yauga Zaid nan yana faɗin wai bazai iya rayuwa ba idan babu wata,,
"Zaid!" Dad yakuma ƙiran sunansa cike da tausayawa domin shikam baitaɓa ganin soyayya irin wannan ba...
Zaid bai iya amsawa mahaifinnasa ba, saide idanunsa daya ɗago ya kalli Dad ɗinnasa dasu.
"Zaid ka kwantar da hankalinka, ba ita kaɗai bace mace a duniyar nan akwai mata da yawa, kana da ƴancin da zaka zaɓi duk irin macen da kake so" Dad yafaɗi haka ga Zaid cikin lallami...
"Idan ni inada ƴanci ita kuma dana cuta fa? nacutar da ita Dad cuta mafi muni, na zalunceta, banda wata hanya dazanbi na goge laifina a wajenta, sai ta hanayar aurenta, dan Allah Dad kayi wani abu, bazan iya jure rashin Zahrah ba!" yanzu kam har ƙwalla suncika idanun Zaid batare daya sani ba. (hmm so mugun wasa)
Miƙewa Zaid yayi daga zaunen da yake haɗe da sa kai yafice daga cikin falon Dad ɗin nasa, da kallo kawai Dad yabisa dashi harya fice, baisan me yake shirin faruwa da ɗan nasa ba amma ae so ba hauka bane.....
Zaid yana fita daga ɓangaren Mahaifinsa direct part ɗinsa yanufa, idanunsa gaba ɗaya sun rufe yayinda kansa ke matuƙar sara masa, sam bazai iyaba, bazaitaɓa iya jure rashin Zahrah ba, lallai yazama dole yakuma yarda da shawaran da zuciyarsa ta basa,, tabbas yazama dole ya kusanto Zahrah zuwa garesa koda kuwa hakan zai jawo faruwar abubuwa masu tarin yawa...key ɗin motarsa ya ɗauka yafice daga cikin ɗakin, gaba ɗaya zuciyarsa ta bushe babu wani abun dayayi saura aciki banda tsananin soyayyar Zahrah.....
Da wani irin mahaukacin gudu Zaid yafigi motarsa yafice daga cikin gidan saura kaɗan yabitakan me gadi daya wangale masa gate, Allah ne ya ta ƙaita Me gadin yayi saurin matsawa gefe, domin kuwa ko gama buɗe gate ɗin baiyi ba Zaid yayi yo kansa....
Tuƙi yakeyi amma kuma kwalbar giya ne riƙe a ɗayan hanunsa yana sha, jinkansa yake gaba ɗaya yana juyawa, yayinda zuciyarsa keyi masa zafi, idanuwansa Zahrah kawai suke hango masa, batare da Zaid yakulaba motarsa tayi karo da wata babbar mota, take motar tasa ta ɗagu sama haɗe da faɗowa ƙasa sannan kuma tashiga gungurawa kan titi, batare da Zaid dake cikin motar ya tsira ba.....
*(Dan Allah ku daina min kutse acikin labarin nan, kudaina saurin yanke hukunci, haryau ban ce ga wanda zai auri Zahrah a tsakanin Zaid ko Dr.Sadeeq ba, kubarni ni kaina nasan abunda ya dace, zaifi kyau ku sanyamin idanu kukuma ci gaba da bina harzuwa ƙarshen labarin nan, amma abun da wasunku sukemin banajin daɗinsa, suna nunawa kamar ina shirin yin abun da bai dace ba, suna nunawa kamar bansan me nakeyiba, dan Allah kuyi haƙuri zancigaba da rubuta labarin nanne kamar yanda yazomin acikin kai dakuma zuciyata, idan kukayi haƙuri komai zaizo cikin sauƙi kuma ina da tabbacin cewa ƙarshen labarin zai muku daɗi, nasan dama dole zan fuskanci ƙalubale a wajen wasunku, amma banyi tunanin abun zaiyi tsanani har haka ba,, amma bakomai namuku uzuri my lovely fans nasan ƙaunace tajawo hakan😅... kuyi haƙuri nayau baida yawa wlhy gaba ɗaya banganewa kaina bane shiasa inafatan zakumin uzuri)*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*(Wannan page ɗin baki ɗayansa kyautane agareki Masoyiyar asali MY SHALELE (marubuciyar RAGGON MIJI) kiji daɗinki Shalelena iya wuya munatare inakuma yi miki son so)*
*CHAPTER 84 to 85*
Kyakkyawan murmushinsa ne ɗauke akan fuskarsa still hannayensa a ware suke, alamar ta taho zuwa garesa.
Ahankali tashiga takawa tana nufar inda yake, ganin haka yasanya Zaid sakin ajiyar zuciya me ƙarfi, haɗe da sake sakin murmushi alokaci na ba adadi,, koda tazo gareshi yana shirin yaji ta rungumesa amma kuma sai yaji saɓanin haka, domin kuwa tana zuwa kusa dashi, sai gani yayi ta raɓa ta gefensa ta wuce batare dako kallonsa tayi ba. Cikin hanzari yasha gabanta haɗe da kamo hanunta. Cak ta tsaya daga tafiyan da takeyi haɗi da rumtse idanunta,, a hankali ya zame guiwowinsa ƙasa, ya durƙusa mata, duka hannayenta ya kama ya riƙe acikin nasa hanun....
Cikin murya me ɗauke da matuƙar rauni yace da'ita...... "Koda kalamaina baza suyi tasiri acikin zuciyarki ba, dan Allah inaso ki tsaya ki saurareni, ki dubi halin danake ciki Zahrah, banda wani sauran farinciki a duniyar nan idan har babuke a tare dani, haƙiƙa nayi nadama nakumayi dana sanin abun dana aikata a gareki, amma dan Allah Zahrah kiyi haƙuri kiji tausayina ki yarda muyi aure, wallahi namiki alƙawari zandaina duk wani abu danakeyi, zan baki farinciki me ɗorewa, zan mantar dake duk wani damuwa, me yasa bazaki cigaba da sona ba Zahrah? meyasa bazakiji tausayina ki yarda da tuban danayi ba, inasonki Zahrah so irin wanda bantaɓa yiwa kowa irinsa ba acikin wannan duniyar, zan iya fansar da komai nawa idan har zaki amince ki aureni, zan iya rayuwa babu komai babu kuma kowa, amma bazan iya rayuwa babu keba, zan iya sadaukar da duka dukiyata, dakuma duk wani abu nawa dana mallaka, matuƙar zansameki amatsayin matata, dan Allah Zahrah ki yarda dani mana, ninefa Zaid, nine mutumin da kika fara so acikin rayuwarki, shin mai yasa bazaki tausayamin ba, kikalli cikin idanuwa na Zahrah hakan kaɗai ya'isa bayyana miki irin tsananin ƙaunar danakeyi miki, inasonki, wallahi inasonki Zahrah!!.." gaba ɗaya zuciyarsa ta karye, sosai rauninsa ya bayyana... A kan fuskar Zahrah kuwa hawayene ke zuba tamkar anbuɗe famfo sannan kuma haryanzu idanunta akulle suke, yayinda harkawo yanzu hannayenta ke cikin nasa hanun. Bazatace yaushene ko kuma tayayane itama ta tsinci kanta da zamewa ƙasa ba, ta dai tsinci kanta da kafa guiwowinta a ƙasa. kukane yaci ƙarfinta bazata kuma iya cewa ga abu ɗaya dake damunta ba... Hanunta tashiga ƙoƙarin cirewa daga cikin nasa hanun, amma kwata kwata Zaid yaƙi bata daman hakan saima ƙara matsowa kusa da'ita da yakeyi...
"Zahrah!" yaƙira sunanta cikin wata irin murya da bata fita sosai...
Manyan manyan idanunta da suka cika da ruwan hawaye ta ɗago haɗe da waresu akansa, batare da tace dashi komai ba,, wani irin kallo yakeyi mata wanda yake ɗauke da tarin ma'anoni masu yawan gaske.. Hanunta dake cikin nasa hanun ya shiga murzawa haɗe da langwaɓar da kansa gefe yana me cigaba da kallon fuskarta. Hawayene yaziraro daga cikin idanun ta zuwa kan ƙuncinta, sam bata taɓayin zato ko tsammani ba, saijin sauƙar bakinsa tayi akan ƙuncinta, yayinda yasanya harshensa yana me lashe ruwan hawayen dake gudu akan ƙuncin nata. wani irin bugawa zuciyar Zahrah tashigayi da sauri, yayinda numfashinta keshirin ƙwace mata batare da tashiryawa hakan ba,, cikin ɗan kuzarin daya rage mata tayi saurin tureshi gefe haɗi da miƙewa tsaye, ƙoƙarin kama hanunta yakuma yi amma saidai baisamu daman hakan ba domin kuwa tuni harta fara tafiya. "Zahrah" yakuma ƙiran sunanta amma sai dai ko waiwayosa batayiba balle yasaran zata amsa masa.. Jefa ƙafarta kawai take batare dako da ganin gabanta tanayiba, gaba ɗaya ƙwalla suncika mata idanu, yayinda ƙirjinta ke mata luguden duka kanta kuwa tamkar anɗaura mata gungumen ice haka takeji yamata nauyi...
Cikin Hanzari Zaid yarufa mata baya, yana me ƙiran sunanta amma kuma bata amsa masaba, haka kuma bata tsayaba, dai dai lokacin wani me taxi yazo wucewa da sauri Zahrah taɗaga masa hanu, aikuwa take yatsaya,, ganin haka yasanya Zaid yaƙara sauri don yaga alamar tafiya zatayi batare da ta tsaya ta sauraresa ba,, amma ina yamakaro domin mai taxi ɗin yana tsayawa Zahrah ta buɗe murfin motar tashige haɗe da cewa mai taxi ɗin yatada motar sutafi.. Zaid na ƙarasowa wajen, me taxi ɗin kuma na figar motar ya cillata kan titi.. Wani irin iska me zafi Zaid ya fesar daga cikin bakinsa, sam baiso haka ba, yaso ace yaji koda kalma ɗayane daga bakinta, amma kuma duk da haka yamatuƙar jin daɗin ganinta, gashi kuma har kusa da'ita yasamu yazo, babban abun farincikin kuma shine har numfashinta ya shaƙa. Take yaji zuciyarsa tayi masa wani irin sanyi, yayinda daɗi da kuma nutsuwa suka cika masa ruhinsa.. Cike da farinciki haka yakoma inda yabar motarsa.....
Zahrah kuwa ko acikin taxi hawayenta kasa tsagaitawa sukayi, saima kara tuttulowa da suke tamkar ana hankaɗosu... Ahaka har mai taxi ɗin yakawota ƙofar gidansu. Kuɗinsa tabasa ko canji bata tsaya karɓa ba ta wuce cikin gida.. A zauren gidan nasu ta tsaya haɗe da sanya hanu ta share hawayenta, sam bataso kowa yasan halin da take ciki, ta barwa Allah dakuma zuciyarta...
Tana shiga cikin gida Inna tayo wajenta da sauri
"A'ina kika tsayane Zahrah? gaba ɗaya duk kinsa hankalinmu yatashi, munsan bakya kaiwa iwar haka baki dawo ba" Inna tafaɗi haka tana me ƙaremawa yanayin Zahrah'n kallo.
"Bansamu abun hawa bane Inna, yau Samad yana da wani uzuri shi yasa baisamu daman ɗaukoni ba" Zahrah tafaɗi haka tana me ƙwaƙulo murmushi ta aza akan fuskarta..
Da kallon tuhuma Inna tabi ta harta shige cikin ɗakinta, tana shiga cikin ɗakin ta dannawa ƙofarta sakata, a hankali tazame ƙasa haɗe da jingina bayanta da ƙofar, kana ta cusa kanta cikin cinyoyinta, wani irin kuka tashiga rerawa me tsananin bantausayi, Yazatayi da rayuwarta ne itakam, da badon kada tayi saɓo ba da sai tace wannan ƙaddaran nata yayi mata girma dayawa, amma sai dai kuma ba'aja da ikon Allah, haƙiƙa tayi imani cewa komai zaizo yawuce, domin kuwa komai yayi farko yana da ƙarshe, amma kuma sai dai tana da yaƙinin cewa kafun nan wataƙila zuciyarta tayi bindiga ta tarwatse,, "yazatayi da abun da takeji acikin zuciyarta?" tambayar da kullum saitayi mawa kanta kenan, amma kuma zancen ɗayane shine bata da amsar da zata bawa kanta.. Tana cikin kukan taji wayarta na ƙara, amma ko ɗago kanta batayiba haka wayar taƙaraci tsuwanta har ƙiran ya katse, wani ƙiran ne yakuma shigowa still har wayar ta katse batako ɗaga ido ta duba taga waye yake ƙiranta ba.. Kuka tayi sosai kafun tatashi daga durƙushen da take takoma kan katifarta,,,, kwanciya tayi luf tana me sauƙe ajiyar zuciya akai akai, yayinda tsikar jikinta ke yawanta tashi, idan tatuno kusancin da suka samu ɗazu ita da Zaid, bakomai ke dagula mata lissafi da kuma hautsina mata ƙwaƙwalwa ba kamar idan tatuna da yanda yasanya harshensa akan kumatunta yanashan hawayenta, yana me kuma yi mata wani irin kallo wanda yakasa ɓacewa daga cikin idanunta,,, batasan me Zaid yakeso a tattare da'ita ba, wataƙila rayuwarta yakeso, wataƙila kuma hauka yakeso yaga tayi, baisan yatakeji idan ta gansa ba, baisan metakeji agame dashi aduk sanda taɗaura idanuwanta akansa ba, sake gyara kwanciyarta tayi, tabbas tana da buƙatar samun wani wanda zata faɗawa gaba ɗaya damuwarta, tana da buƙatar wanda zai kwantar mata da hankali yakuma samamata nutsuwa, tana kuma buƙatar wanda zai fayyace mata abun dake cikin zuciyarta, koda hakan zaisanya tasamu sauƙi da salama,, haka dai Zahrah tayi bacci zuciyarta cike da tarin tambayoyi.....
Zaid ne kwance akan wata haɗɗɗiyar kujera mai kama da gado, wanda take aje cikin wani irin katafaren falo wanda aka ƙawatasa da kayan ƙyale ƙyale dakuma more rayuwa. Murmushine ɗauke akan fuskarsa, yayinda kyawawan idanunsa suke a lumshe, wani irin shauƙi me tsanani yakeji a tattare dashi, a iya ganinta da yayi jiyake tamkar anyaye masa gaba ɗaya damuwarsa ne, idanunsa yasake lumshewa haɗe da sake shaƙan daddaɗan ƙamshin da yakeyi masa yawo acikin hanci, ƙamshin da tun ɗazu yakasa barin hancinsa, "wani irin daddaɗan ƙamshine haka Zahrah'nsa keyi?" ya tambayi kansa,, tabbas zai so ace iyanzu Zahrah na kusa dashi, dakuwa kwana zaiyi manne da'ita yana shaƙan wannan daddaɗan ƙamshin nata, sannu ahankali wani irin muguwar kasala ke dirar masa, yayinda wani irin sha'awarta me tsanani ya kawo masa ziyara,, a hankali yasanya harshensa ya lashi laɓɓansa haɗe da sanya hanu yashafi ƙwantaccen beard ɗin sa wanda koda yaushe yake ƙara ƙawata masa fuskarsa,, a hanakali ya ware manyan idanunsa wanda suka soma sauya launi daga farare zuwa kalan bacci, wanda idan ka kallesu dole zasu sauƙar maka da kasala... Laptop ɗin dake kusa dashi ya ɗauka, haɗe da buɗewa, take hoton kyakkyawar fuskarta ya bayyana akan screen na laptop ɗin,, murmushi yayi haɗi da sanya hanu yashafi kan screen ɗin laptop ɗin..
"Inasonki Zahrah!"
ya faɗi haka cikin wata irin murya me ɗauke da matsanancin shauƙi. Take yaji yana matuƙar sha'awan kallon vedion dayayi mata ɗazu batare da tasani ba, lokacin fitowarta daga gidan Hajiya Shuwa. Wayarsa da vedion ke ciki ya ɗauka haɗe da kunnawa, kallon vedion yakeyi yana murmushi, amma kuma kwata kwata saƙonnin da suke shigowa ta Email ɗinsa sun hanasa sakat.. Kai tsaye fita daga ɓangaren vedion yayi ya kutsa cikin Email ɗin nasa, saƙonnin abokanan business ɗinsa ne, sama sama yakaranta saƙonnin, haryana shirin fita daga cikin Email ɗin sai kuma idanunsa suka sauƙa akan saƙon Jasheer wanda yaturo masa,, hakanan yaji gabansa yaɗan faɗi saboda yasan duk saƙon da zaizo daga Jasheer to akan Zahrah ne,, buɗe saƙon yayi haɗe da ƙurawa hoton da Jasheer yaturo masa idanu.. Wani irin abu ne yaji ya taso yatokare masa maƙoshi, yayinda idanunsa suka kaɗa sukai jajur dasu, take gashin jikinsa suka mimmiƙe, wani irin juyawa yaji kansa nayi masa,, shin dagaske katin ɗaurin auren Zahrah idanuwansa suke gane masa ko kuwa? sake waro manya manyan idanuwan nasa yayi aikuwa ba ƙarya idanun nasa keyi masa ba, sunan Zahrah ne rantaɓe ajikin katin dakuma sunan Dr.Sadeeq,, wani irin ƙara Zaid yayi haɗe da yin cilli da wayartasa, take ta bugi bango takuma faɗowa ƙasa lokaci ɗaya ta tarwatse.. Cikin matsanancin ɓacin rai jikin Zaid yasoma rawa take yaji wani irin matsancin zafi a dai dai saitin zuciyarsa, lokaci ɗaya wani irin tari ya tasomai, take yasoma tari babu ƙaƙƙautawa, sai ga jini na fita ta bakinsa abun mamaki, abun da bai taɓa gani ba arayuwarsa,, da ƙyar yasamu tarin ya tsagaita, amma kuma duk da haka ƙirjinsa bai daina yi masa ƙuna ba, yayinda zuciyarsa keyi masa zafi har cikin cikinsa kuwa yakejin zafin,, a hankali ya jingina bayansa da jikin bango, haɗe da rumtse jajayen idanunsa, numfashi yashiga fitarwa a hankali, daga ni kai kasan yana matuƙar jin ciwo,, cikin yanayi na wahaltuwa haka ya daddafa zuwa cikin ɗakinsa, ƙaramin drower'n dake gefen gadonsa ya jawo haɗe da ciro magungunansa, tsabar ɗacin da yakeji a maƙoshin sa da ƙyar ma ya iya haɗiye magungunan... Kwanciya yayi akan gado haɗi da rumtse idanunsa, baisan ina zai tsoma rayuwarsa ba, baisan tayaya zai fara jure rashin Zahrah akusa dashi ba... Kamar dai yanda Zaid yaga rana haka yaga dare, koda kuwa na minti guda ne baiji wani salama ko sanyi acikin zuciyarsa ba, haka ya share awanni masu yawa cikin ciwo,, sai da yayi sallan Asuba ƙafun wani irin bacci me nauyi ya sace sa batare daya shiryawa hakan ba......
*****
Zahrah kuwa yau da wani irin irin matsanancin ciwon kai ta tashi, gaba ɗaya idanunta sunyi luhu luhu dasu, da gani kai kasan cewa kuka tasha ta ƙoshi.
Yau ya kasance aurenta da Dr.Sadeeq saura kwanaki shida kenan tana ƙirgawa kuma acikin kwanakin nan ne zasu fara gudanar da shirye shiryen da suka tsara,, gaba ɗaya ji takeyi bata marmarin auren, sannan kuma ji takeyi komai yafice mata arai, bawai kuma don batason Dr.Sadeeq ɗin ba, tun shekaran jiya Dr.Sadeeq yakawo mata ɗinkunanta da kuma kayan da zata sanya a kamu da wajen diner, amma kuma ko duba kayan batayi ba balle taga ma ko sunyi mata ko basuyi mata ba, batasan meyake damunta ba, amma tabbas tasan akwai wani baƙon al'amari dayake ta kusanto rayuwarta aduk kwanan duniya. Yau hakanan tatashi taji ko gyaran jikin ma batason zuwa, amma kuma dazaran tace bazata jeba tasan Inna zata sanyata agaba da yawan tambayoyi, don haka ma gwamma kawai ta je ɗin zaifiye mata... Sauri sauri haka ta shirya tafito, saboda tasan cewa yanzu haka Samad na ƙofar gida yana jiranta... ai kuwa tana fitowa taga motar Dr.Sadeeq fake a ƙofar gidan nasu, murmushi kawai tayi haɗe da ƙarasawa wajen motar... "Allah sarki Samad yana da haƙurin jira, da Dr.Sadeeq ne da yanzun ya ƙirata a waya" tafaɗi haka a zuciyarta dai dai sanda taƙaraso gaf da motar, buɗe murfin motar tayi tashiga bakinta ɗauke da sallama, "Kayi haƙuri Samad nabarka kana ta jira" tafaɗi haka tana me ƙoƙarin rufe murfin motar, batare da takalli Inda Samad ɗin ke zaune ba.
Tana rufe murfin motar tadawo da kallonta wajen zaman driver fuskarta ɗauke da murmushi,, a maimakon taga Samad saitaga Dr.Sadeeq, mamakine ya bayyana akan fuskarta alokaci guda, sake ware idanu tayi tana kallonsa, da'alama dai ganinsa yabata mamaki sosai...
Murmushinsa me kyau yayi mata haɗe da kafeta da idanunsa wanda suke sauƙar mata da wani irin yanayi na kasala ajikinta.. Itama murmushin tayi masa haɗe da shagwaɓe fuska....
"Ni dai nayi fushi!" tafaɗi haka a shagwaɓe...
"Tuba nake"
Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana me kama kunnuwansa da duka hannayensa.. alaman ban haƙuri.
"Ni dai naƙi wayon" tafaɗi haka tana me kaɗa idanunta.. Murmushi yayimata haɗe da kamo duka hannayenta yasanya acikin nasa hanun, lumshe idanunsa yayi alokaci guda haɗe da buɗewa
"Nayi kewarki sosai Zahrah na!" yafaɗi haka cikin wata murya me sanyi.
Ɗan guntun murmushi tayi haɗe da soma ƙoƙarin janye hanunta daga cikin nasa hanun, amma kuma bata samu daman hakan ba. "Meyasa jiya kika ƙi ɗaga wayana?" yatambayeta cike da kulawa bayan yagama karantar yanayin da take ciki. Sai alokacin ne ma Zahrah ta tuno da cewa jiya taga missed calls ɗinsa, sanann kuma bata bi bayaba,, ƙaƙalo murmushi tayi haɗe da cewa " Kayi haƙuri nayi bacci ne alokacin"
Kansa ya jinjina badon wai ya gamsu da abun da ta faɗa ba,, ta da motar yayi suka hau kan titi. Saida sukayi nisa a tafiyar kafun yadawo da kallonsa gareta, sosai tayimasa kyau komai nata ya canja, sai dai kuma kallo ɗaya yayimawa fuskarta yafuskanci cewa tayi kuka, dafari yaso tambayarta meke damunta, amma kuma sai kawai ya share,,, sama sama yake janta da hira harsuka iso gidan Hajiya Shuwa... Yana ganin shigewarta cikin gidan ya sauƙe ajiyar zuciya ƴaɗe da kifa kansa akan steering motar, "meke damun Zahrah ne?" ya yiwa kansa tambayar a bayyane, amma sai dai kuma bayida amsar da zai bawa kansa.... A jiyar zuciya yakuma sauƙewa akaro na barkatai, zuciyarsa cike da tunani kala kala yaja motarsa yabar ƙofar gidan....... Ɓangaren Zahrah kuwa kwana biyun nan wasu irin magunguna masu ƙarfin gaske Hajiya Shuwa take bata tanasha, hakan kuwa shike taimakawa wajen hautsina mata tunaninta, wani irin abu takeji acikin jikinta wanda kai tsaye za'a iya ƙiransa da suna sha'awa, ko da yaushe yanzu Zahrah cikin jin feelings take, hattakai ta kawo yanzu alwala ma baya daɗewa ajikinta yake karyewa saboda sosai sperm ke fita ajikinta, duk kuma ɗaya daga cikin aikin magungunan ƙarin ni'iman da Hajiya Shuwa ke bata ne, lallai ita kanta tasan cewa Hajiya Shuwa tayi mata babban haɗi me matuƙar kyau...... (su Doctor za'asha nice😜🙈)
Tunda bacci ya ɗaukeshi da asuba bashi yafarka ba sai ƙarfe 9:30 am, da wani irin zazzafan zazzaɓi yatashi, wanda ya zamana ko ɗaga kansa ba ya'iyawa hatta numfashima da ƙyar yake iya fitarwa. Yana a wannan halin ne yaji anturo ƙofar ɗakin nasa, bai iya ɗago kansa ya dubi ko waye ba amma kuma duk da haka ya gane waye ne yashigo cikin ɗakin... Dasauri Alhj Ma'aruf yaƙaraso garesa...
"Lafiya Zaid meke damunka?" Alhaji Ma'aruf yafaɗi haka yana me kai hanunsa jikin Zaid, da sauri yajanye hanunsa daga jikin Zaid ɗin domin kuwa jiyayi jikin Zaid ɗin yaɗau zafi rau kamar wuta. "Subahanallah, bana ƙira Doctor yanzu" Dad yafaɗi haka yana me ƙoƙarin ciro wayarsa daga cikin aljihu,, bugu biyu Dr.Bilal yaɗauki wayar, cike da damuwa Dad yace yanason ganinsa jikin Zaid ne yatashi. take Dr.Bilal yace gashinan zuwa..
Zama Dad yayi jigum agefen gadon Zaid ɗin, gaba ɗaya yarasa mekeyi masa daɗi, sosai matuƙa cutar Zaid ke damunsa, yana matuƙar ƙaunar Zaid sam bayaso wani abu ya samesa, musamman ma yanzu da Dr.Bilal yashaida masa cewa Zaid ɗin yana ɗauke da ciwon zuciya me tsanani... Mintuna kaɗan Dr.Bilal yaƙaraso gidan, babu wani ɓata lokaci kuwa yashiga yiwa Zaid wasu ƴan gwaje gwaje, drip yaɗaura masa bayan yayi masa wasu allurai guda biyu wanda zasu taimaka wajen kawar da zazzaɓi da kuma ciwon da kansa keyi masa uwa uba kuma su sanyasa bacci, saboda idan yana a cikin hayyacinsa bazai taɓa barin zuciyarsa ta huta ba, yin hakan kuma shike ƙara sawa ciwon yayi tsanani... Bayan sun fito compound ɗin gidan ne Dr.Bilal yagyara tsayuwarsa haɗe da duban Alhaji ma'aruf,, bayani yashiga yimawa Alhaji Ma'aruf ɗin sosai agame da ciwon Zaid ɗin. Bayan sun kammala maganan ne Alhj Ma'aruf yakoma wajen Zaid da tuni wani baccin wahala yasake ɗaukansa......
*****
Rana bata ƙarya, ranar yau takasance laraba kuma yautake kamun Amarya, tun da safe gidan su Zahrah yake acike ƴan uwan Inna sun tattaro ƙwansu da ƙwarƙwatansu sun garzayo, don haka tuni gida yaɗauki hargowa da hayaniyan mutane yayinda amarya kuwa tunsafe take ƙunshe a ɗaki acewarta cikinta ne keyi mata ciwo,, Husnah da Suhaima ne suka taimaka wajen ɗebe mata kewa ta hanyar zama da'ita.....
Ƙarfe uku na yammaci kenan amma tuni gidansu Zahrah ya ɗinke da mutane, ciki kuwa hadda ƴan matan school ɗinsu wanda Husnah ce ta gayyacesu, domin ita dai Zahrah bata da wasu ƙawaye Husnah ce kaɗai ƙawarta... Kowacce ka kalla acikin ƴan matan nan tasha kyau cikin kayan anko ɗinta. Husnah ce tsaye akan Zahrah tana ta faman ɓaɓatu akan cewa Zahrah'n ta tashi su tafi shagon meckup domin tuni Dr.Sadeeq yaturo freinds ɗinsa waƴanda zasu kaisu shagon yin meckup ɗin suna ma jiransu aƙofar gida,, ita dai Zahrah yau jitayi gaba ɗaya bakinta ya mutu sambatajin wani kuzari ajikinta. Kayan da zata sanya da duk wani abun da zatayi amfani dashi, Husnah ta ɗaukar mata haɗe da kama hanunta suka fice daga cikin gidan. Wasu haɗaɗɗun motoci suka shiga kai tsaye aka wuce dasu wani shahararren shagon meckup....
Kwalliya sosai shahararriyar meyin meckup ɗinnan ta tsantsarawa Zahrah akan fuskarta lokaci ɗaya saiga Zahrah ta sauya kamanni asalin kyawunta yasake bayyana tamkar wata balarabiya ita kanta Zahrah saida tayi mamakin ganin kanta, tabbas dabadan tasan ita ɗin ceba, to da sai tace sanja mata fuska akayi, kowa yaga kwalliyanta saiyayi santi saboda tasha kyau iya kyau.. Wani doguwar rigan leshi me kyau da tsada ta sanya ajikinta, take kyakkyawar surar jikinta ya bayyana kansa acikin kayan, sosai ɗinkin yayi kyau yakuma amshi jikinta, zama tayi aka tsantsara mata haɗaɗɗen ɗaurin ɗankwali akanta, yayinda aka nannaɗe mata dogon gashinta atsakiyar kanta, ita dai tsayawa tayi kamar wata statue tana mamakin irin baiwar kyawun da Allah yayi mata, daga riganta har zuwa kan takalminta dakuma ɗan karamin fos ɗin dake rike ahanunta kalarsu yakasance light peach ne, yayinda stones ɗin kayanta suka kasance farare, lokacin da su Husnah sukayi tozali da Zahrah ihu dakuma shewa suka sanya haɗe da tsantsar mamakin irin kyawun da Zahrah tayi, kowa dai yasan Zahrah kyakkyawace amma kuma basuyi tunanin kyawunnata har ya kai hakaba, lallai duk namijin daya samu Zahrah amatsayin mata yayi babban gamdakatar. Take su Husnah suka shiga ɗaukarta hotuna da kuma vedios suna watsawa a instagram dakuma whatsapp, suna cikin buga selfie abokan ango suka ƙaraso don ɗaukar ƙawayen amarya,, duka ƴan matan kowacce da motar da tashiga, yayinda aka bar Zahrah da Husnah sukaɗai saboda Ango yace shi dakansa zaizo yaɗauki amaryarsa... Ƙawaye basu jima da tafiya ba wayar Husnah tasoma ƙara,, murmushi tayi haɗe da kallon Zahrah adai dai lokacin da taɗaga wayar takara akan kunenta, "To ranka shi daɗe gamunan fitowa" abun da Husnah tafaɗa kenan haɗe da miƙewa tsaye hannuwan Zahrah takamo haɗe da miƙar da'ita tsaye..
"Angonki yaƙaraso yace nafito masa dake" murmushi kawai Zahrah tasakar mawa Husnah kana ta sunkuyar da kanta ƙasa.. A hankali Zahrah ke takawa yayinda rigar jikinta kejan ƙasa, babu abun dake tashi ajikinta sai daddaɗan ƙamshin turare,, gaskiya Zahrah tayi kyau sosai ayau ɗin..
Ware idanu Dr.Sadeeq dake zaune acikin motarsa yayi yana me kallon Zahrah, shima yasha ado cikin wata farar gezina me matuƙar kyau da tsada yayi kyau sosai da sosai, kwarjininsa yasake fitowa fili..... Har Husnah ta buɗe murfin motar ta tura Zahrah ciki bai rufe bakinsa ba haka kuma bai ɗauke idanunsa daga kallon da yakeyi wa Zahrah ba, lallai ne godiya ta tabbata ga ALLAH (S.W.A) daya tsara wannan kyakkyawar halitta, kullum kuma koda yaushe yana kallon kyawun Zahrah amma kuma yau saiyake ganin kyawun nata yafi na koyaushe ƙawatuwa.. A hankali ya sauƙe wata irin ajiyar zuciya haɗe da lumshe idanunsa,,, Zahrah kuwa tunda tashiga cikin motar ta sunkuyar da kanta ƙasa tana me wasa da yatsun hanunta,, Motar Habeeb dake bayan ta su Zahrah Husnah tashiga,,, atare motocin suka tashi tafiya sukeyi ahanakali akan titin...
"Zahrah!" Dr.Sadeeq yaƙira sunanta cikin wata irin murya me sanyi dakuma sauƙar da nutsuwa. Kasa amsa masa Zahrah tayi, hakanan taji wani irin nauyinsa ya lulluɓeta.
"Kinyi matuƙar kyau sosai, sai yanzu nasakejin cewa nayi babban sa'a dana sameki, inasonki sosai Zahrah na, ina fata watarana nima kisoni tamkar yanda nake sonki!"
Sai alokacin Zahrah ta ɗago kanta, haɗe da sakar masa ƙawataccen murmushi, jiyayi gaba ɗaya ta kashesa da salon murmushin nata, a hankali ya matso daf da'ita haɗe da kamo hannayenta duka biyu ya riƙesu gam acikin nasa, wani irin soyayyartane yaji yana ƙara shiga jikinsa, jiyakeyi tamkar ya jawota jikinsa ya rungumeta kozai sake samun nutsuwa acikin zuciyarsa.... Harsuka iso katafaren hall ɗin daya cika maƙil da jama'a zuwan amarya da ango kawai ake jira, amma Dr.Sadeeq bai ɗauke idanunsa akan abar ƙaunarsa ba, wani abun daya ƙara rikitar da Zahrah takasa cewa dashi komai shine yanayin yanda yake mata magana da wata irin murya me sanyi... Motarsu na'isowa wajen taron, mc yasoma shela cewa ga ango da amarya sun ƙaraso, take guri yasake ɗaukan shewa yayinda kowa yazura idanun ganin ango da amarya, waƴanda suka zo wajen dan gulma suka sake miƙa wuya musamman ma familyn Dr.Sadeeq wanda anriga da angama gayamusu cewa amaryan ƴar matsiyata ne saboda haka suka baza idanuwan ganin ta don kashewa idanuwansu ƙwarƙwata.... Habeeb ne ya buɗewa Dr.Sadeeq ƙofar motar yafito, yayinda shikuma Dr.Sadeeq da kansa yazagayo ya buɗe mawa Zahrah nata ƙofar,,, cikin nutsuwa ta zuro ƙafafunta waje, kafun daga bisani tafito daga cikin motar, hanunta ɗaya Dr.Sadeeq yakama suka soma taku cike da nutsuwa,, wajene yaɗauki shewa masu murna nayi masu baƙinciki ma sunayi, haka masu ɗaukar amarya da ango hoto da vedio's ma duk sunayi,, gaba ɗaya family'n Dr.Sadeeq ƙamewa sukayi ƙam ganin kyawun amarya ya tsoratasu sosai, saboda basu taɓa tunanin haka zasuga amaryan ba, sunyi tunanin zasu ganta wata almajira da'ita amma kuma sai suka ga saɓanin tunaninsu, lallai ba'abanza ba Dr.Sadeeq ya liƙe akan cewa shi dole sai'ita, takai takuma cancanci ayi mata fiye da haka ma... Har amarya da ango suka ƙarasa mazauninsu mutane basu daina yimusu vedio's ba, haka kuma idanu bai ɗauke daga kan suba.........
*(Bazan'iya cigaba da typing ɗinnan ba, saboda banaso ayi bandani domin nima yau zantaka rawa sosai💃💃💃💃 idan kamu ya kammala zan cigaba da typing😜🤣 Team Zaidu muna tare iya wuya😘, Team Dr.Sadeeq kuna cikin ƙalbina asahun farko ma kuwa🤗)*
*12/January/2020*
*Follow me on Whatsapp and Wattpad*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*
*
*
*CHAPTER 86 to 87*
Sunkuyar dakai ƙasa Zahrah tayi gaba ɗaya ita kunyar mutanen dake tare a wajen takeyi, tunda take bata taɓa shiga irin wannan taron ba, sai gashi yau akanta ma akeyin taron, ba abun dake damunta kamar yanda idan taɗaga idanunta take ganin idanuwan mutane akanta kowa ita yake kallo da waƴanda suka santa haddama waƴanda basu santa ba,, matso da kansa yayi kusa da'ita haɗe da kawo bakinsa wajen kunnenta "Anan ma kunya zaki nuna?" ƙasa ƙasa yayi maganar. satan kallonsa tayi haɗe da ɗan sakin murmushi amma kuma batace dashi komai ba, haka dai masu yin vedio suka ci gaba da ɗauka yayinda..... Hmmmm kamu dai yayi kamu yakuma ƙawatar amma kuma sai dai sam amarya Zahrah ta kasa sakewa komai a ɗari ɗari takeyinsa, abu biyune suka haɗe mata kunya dakuma rashin sabo, saboda bata taɓa zuwa irin waƴannan wajen ba, wannan ne karonta na farko, gashi kuma kamun yatara mutane sosai, su Husnah sunyi rawa sosai sun raƙashe Amarya kuwa ae ko taka kafarta bata'iya ba gaba ɗaya nauyi da kunya sun hanata sakat.... sai gab da magrib aka tashi daga kamu kowa yasamu abun arziƙi ankuma cika ciki da abinci na musamman da kuma lemuka... Yanzu kam mota ɗaya Zahrah da Husnah harma da Suhaima suka shiga, yayinda Dr.Sadeeq shikuma yashiga wata motar ta daban... Jingina bayanta tayi da kujera haɗe da kwantar da kanta akan kafaɗan Husnah, duk hiran da Husnah da Suhaima keyi jinsu kawai takeyi, sosai sanyin AC'n dake cikin motar yake ratsata har hakan yaso sanyamata zazzaɓi, haka dama ita take matuƙar ta shiga hayaniya to kanta sai ya ɗanyi mata ciwo, uwa uba kuma idan sanyi yayimata yawa saita ɗanyi zazzaɓi.. Harsuka isa gida Zahrah ko uffan batace ba duk da kuwa yanda su Husnah kejanta da hira, amma iya abun da take iyayimusu shine murmushi... Fitowarta a wanka kenan, sauri sauri ta zura wata doguwar riga me kauri ajikinta,,, kallon ta ta mayar ga Husnah wacce taketa faman chatting a wayarta sai nurmushi kawai take zubawa..
"Wai ke da waye ne haka? a iya sanina dake ke ba mutum bace me yawan chatting da'alama dai munsamu ƙaruwa" Zahrah tafaɗi maganar cikin sigar tsokana... Dariya Husnah tayi haɗe da ɗage giranta sama. "Ƙwarai kuwa tawan, wallahi ɗazu na haɗu da wani guy a wajen kamunki, ina tunanin ya kwantamin arai"
Dariya Zahrah ta sanya haɗe da neman guri ta zauna akusa da Husnah haɗi da kwantar da kanta akan kafaɗan Husna'n....
"Husnah kinsan ya so yake?" tambayar da ta fito daga bakin Zahrah kenan..
Mamaki tambayar da Zahrah tayi mata ya bata amma kuma batasan menene dalilin dayasanya Zahrah tayi mata wannan tambayar ba...
"Eh zan iyacewa nasansa zankuma iya cewa bansan saba, saboda banyi wani zurfi acikinsa ba, amma kuma ke kinsan bana yaudaran kaina Zahrah, duk wasu alamomin so nasansu, saboda hakane ma nayardarwa kaina cewa nakamu da soyayyar Yazeed so matsananci!" Husnah tafaɗi haka tana me wasa da wayar hanunta, da'alama sunan Yazeed kaɗai da ta ambata yasanyata cikin shauƙi..
Ajiyar zuciya me ƙarfi Zahrah ta sauƙe haɗe da ɗago kanta daga kan kafaɗar Husnah, hannayen Husnah takama cikin murya me sanyi tace da Husnah "Wasu irin alamomi ne kesanyawa mutum yagane cewa yakamu da so? sannan kuma inaso ki sanar dani menene hukuncin zuciyar da ta makance har take ƙoƙarin sake son wanda yacutar da'ita, wanda kuma baida wani amfani a wajenta"
Kallon mamaki haɗe da ɗaurewar kai Husnah tashiga yi mawa Zahrah, ƙwarai itakam maganganun Zahrah sun sanyata a duhu me Zahrah take nufi?
"Banfahimci inda kalamanki suka dosa ba Zahrah, zanfi fahimta idan har kika warware maganar tazama abu guda, amma kuma ni a ganina babu amfanin zuciyar da zata so wanda baida amfani a wajenta, sai dai kuma amma kinsan shi so wani zubin yakan makantar da komai naka ne tahanyar da baka isa kayi yaƙi dashi ba, amma kuma shi so kala kala ne, kowani so da'irin ƙarfinsa haka kuma da irin rauninsa, wani son yana fita, wani kuma sai ahankali zai fita, wani kuwa baya taɓa fita har gaban abada, amma shi wanda baya fita har abada shi ake ƙira da ƙauna, ita ƙauna kuma idan zafinta yatashi ƙona ka, to ƙunan yakan kasance me tsananin zafi da raɗaɗi bakamar na so ba, ina fata dai Ƙaunar Doctor ce tasanya kikamin wannan tambayar?" Husnah tafaɗi haka tana murmushi.. Wasu siraran hawayene suka silalo daga cikin idanun Zahrah zuwa kan ƙuncinta.
"Zahrah kuka kuma?" Husnah tatambaya cike da mamaki domin ita sam bataga abun kuka acikin maganar da sukeyi ba, hasalima ita Zahrah'n ce tafara ɗago maganar ba wai ita ba.
Hanu tasanya ta share hawayenta haɗe da sakin murmushi, "Bakomai Husnah kawai dai idanuna ne tunɗazu sukeyimin zafi, kinsan ban saba da irin wannan kwalliyar da akamin ba, bacci ma nakeji bana ɗan kwanta, idan kingama ki rufe mana ƙofa" Zahrah tafaɗi haka fuskarta ɗauke da murmushin dole..
Har Zahrah ta kwanta Husnah bata ɗauke idanunta daga kanta ba, sosai ganin hawayen Zahrah'n yabata mamaki duk da kuwa cewa tana lure da'ita a ƴan kwanakinnan gaba ɗaya acikin damuwa take wuni, amma gudun kada ta dameta da tambaya yasanyata sharewa bata tambayeta ba, amma tasan damuwa kam akwai shi jingim acikin zuciyar Zahrah...
Kusan mintuna talatin hawaye na gangarowa daga cikin idanunta, amma kuma ko kyakkyawan motsi taƙi tayi gudun kada Husnah ta fuskanci cewa batayi bacci ba,, bazata taɓa bari kowa yasan damuwarta ba, ta yarda ta amince zata haɗiye duk wani damuwarta acikin rai da zuciyarta ita kaɗai, koda kuwa damuwartata zata kasheta, tabbas wannan abun da takeji ba abu bane wanda zai ɓoyu ba, amma kuma zatayi iyaka ƙoƙarinta wajen ganin ta maidashi ɓoyayyen sirrinta a haka har baccin gajiya ya ɗauketa, tana bacci babu jimawa kuwa ƙiran Dr.Sadeeq yashigo cikin wayarta, ganin ya nace da ƙiran ne yasanya Husnah ɗaga wayar ta shaida masa cewa Zahrah tayi bacci, to kawai yace haɗe da ajiye wayar..
Wani irin tausayinta ne yaji ya dirar masa acikin zuciyarsa, hakanan yaji yau soyayyarta yasake shiga zuciyarsa fiye da ko yaushe yayinda tausayinta yakuma ɗarsuwa acikin zuciyarsa, yaso jin muryarta acikin wannan daren amma kuma hakan baisamu ba, haka yashare yashiga cikin abokansa suka cigaba da sabgoginsu......
Kafe cak idanunsa suke akan haɗaɗɗen zanen POP'n dake mamaye saman ɗakin wanda aka ƙawatasa da ado me matuƙar burgewa, a hankali yake fitar da numfashi me zafi daga cikin hancinsa,, ahalin yanzu ba ciwon da yakeji bane damuwarsa, yafi damuwa da ganin Zahrah'nsa fiye da komai, yanzu kenan saura kwana uku a ɗaura mawa Zahrah'nsa aure da wani bashi ba, rumtse idanunsa yayi da sauri haɗe da haɗiye wani irin yawu me ɗaci daya tsaya masa a maƙoshi, abu kamar wasa saiga ƙwalla suna gangarowa daga cikin idanun Zaid, hanu yasanya yashafa gefen fuskarsa inda yaji sauƙar ɗumin wani abu kamar ruwa,, ruwan hawayen daya fito daga cikin idanunsa ya lakato ahanunsa koda yaga cewa hawayene ke fita daga cikin idanunsa sai yasaki wani irin murmushi me matuƙar ciwo, rayuwa kenan babu yanda bata juyawa bawa, watarana kaga me kyau watarana kuwa kaga mummuna, ƙaddara kenan babu tayanda bata zuwarwa bawa, haƙiƙa SO babban cutane ga bawa musamman idan baka samu abun da kakeso ɗin ba, tabbas ya jarabtu domin ko a iya haka Allah yabarsa ya horasa horo mafi tsanani ma kuwa, tabbas Zahrah itace rauninsa, rasata kuma shine abu wanda zaifiye masa komai ciwo acikin rayuwarsa, baisan wani irin zazzafar soyayya yakeyiwa Zahrah ba, ashe tun dama yaudaran kansa yayi ba sha'awarta yake ba sonta yake, amma kuma saboda wani banzan tunani da kuma banzar hujjan sa yasanya ya kasa yarda da hakan, idan yace zai misalta irin tarin yawan nadaman da yayi kawo daga randa ya yiwa Zahrah fyaɗe zuwa yau to tabbas yayi ƙarya, ya cutar da'ita, ya zalunceta, tabbas yasan bai kyauta mata ba, sannan kuma baiga laifinta da ta ƙishi ba tabbas shida kansa ya san cewa bai cancanci ta sake yarda dashi ba, saurin rumtse idanunsa yayi haɗe da dunƙule hannayensa da ƙarfi, bakomai ne yasanyasa yin hakan ba face tunowa da yayi lokacin da idanunsa suka rufe ya shigeta da ƙarfin gaske yanajin wani irin ihun da tayi amma saboda bushewar zuciya irin tasa haka bai saurara mata ba,, kansa yashiga duka da hannayensa biyu kamar mahaukaci, ihun da Zahrah keyi masa alokacin da zai keta mata haddine yashiga dawowa cikin kunnuwansa ji yake tamkar alokacin ne abubuwan suke faruwa,,, ihu yashiga yi batare daya sani ba, gaba ɗaya idanunsa sun kaɗa sunyi jajur dasu, Mum da shigowarta falon nasa kenan taji ihun Zaid na tashi daga cikin bedroom ɗinsa, cikin sauri hartana haɗawa da tuntuɓe tanufi ɗakin nasa,, kwance tagansa akan gado yaɗaura duka hannayensa akansa yana wani irin ƙara tamkar wani wanda aljanunsa suka tashi..
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un, Zaid! Zaid!!" Mom taƙira sunansa cikin matuƙar ruɗewa,, girgiza sa Mum tashiga yi cike da ruɗewa sunansa kawai take ƙira, a tunaninta Zaid ɗin nata ya haukace ne, yanajin muryar Mom ɗinsa acikin kunnensa yatashi a zabure haɗe da faɗawa cikin jikin mahaifiyartasa, abun mamaki saiga Zaid nan na kuka tamkar wani ƙaramin yaro, ita kanta Mum kasa motsi tayi haka ta tsaya kamar statue, wai da gaske Zaid ɗin tane wannan, kuka fa yake, anya kuwa ba aljanune suka shiga mata jikin ɗa ba?.
"Zaid" Mum takuma ƙiran sunansa cikin murya me sanyi domin kuwa itama tuni ƙwalla harsun cika mata ido... "Please help me Mum, i don't want to lost her!" abun da Zaid ke faɗa kenan yana kuka,, mamaki marar misaltuwa ne yakuma kama Mum wannan wace irin masifa ne ya ruski Zaid wace irin tsinanniyar soyayyace wannan datake shirin haukata mata yaro? lallai yazama dole tayi wani abu, bazata taɓa bari tanaji tana gani ɗanta ya rasa ransa akan wata ba, wai dama ashe haka so yake? idan kuwa haka so yake to sai dai muyi fatan Allah yarabamu dayin so me tsanani....
Kansa mum tashiga shafawa ahankali cike da tausayawa tace "Ka kwantar da hankalinka Zaid, kayi haƙuri kasamawa kanka nutsuwa, badai kana sonta ba?"
Kai Zaid ya kaɗa tamkar wani ƙaramin yaro.
"Insha Allahu zata zamo taka, zaku rayu da'ita rayuwa ta har abada, kadaina damun kanka kaji my son!"
Mum ta ƙare maganar cike da lallashi..
Kansa ya kwantar akan kafaɗan mahaifiyartasa lokaci ɗaya yashiga sauƙe ajiyar zuciya irin dai yaro ƙarami yayi kuka ya ƙoshin nan.... Bayansa Mum take shafawa a hankali sai gashi cikin mintunan da basufi 10 ba Zaid yasoma fidda numfashi a hankali cike da nutsuwa da'alama dai bacci ne ya ɗaukesa, Mum tana tabbatar da cewa Zaid ɗin yayi bacci ta tattaro duka ƙarfinta haɗe da zameshi akan kafaɗanta ta kwantar da kansa bisa kan pillow'n sa haɗe da ja masa bargo ta rufeshi, kallon fuskarsa Mum tashigayi cike da tsananin tausayinsa, tajima tana kallonsa kafun daga bisani tayi masa addu'a ta shafa masa akan fuskarsa, cikin sanyin jiki ta tashi tafice daga cikin ɗakin, gaba ɗaya zuciyarta tayi rauni......
*Washe Gari*
Tun safe kwararriyar me zanen lalle wanda Dr.Sadeeq ya ɗaukarwa su Zahrah bayan yabiyata maƙudan ƙuɗaɗe tazo gidan,, zanen jan lalle me matuƙar kyau aka tsantsarawa Zahrah akan hanu da ƙafarta, abunka da farar fata take zanen jan lallen yafito akan fatarta yayi kyau sosai,,, lokacin da ta wanke zanen lallen nata hakanan ta tsinci kanta da sakin murmushi ita kanta sosai zanen yayi mata kyau gashi ya ƙara ƙawata farar fatarta gwanin sha'awa. Wayarta dake ringing ta ɗauka haɗe da karawa akan kunnenta, cikin wata irin kasalalliyar murya taji yace "Amaryata" murmushi tasakar masa me sauti haɗe da cewa "Umm" Dr.Sadeeq dake zaune cikin motarsa yagyara zama haɗe da cewa "Ki ɗan bani aron minti 10 daga cikin lokutanki na yanzu inason ganinki" ya ƙare maganar yana wani lullumshe ido kamar wanda yake a gabanta. Ajiyar zuciya Zahrah tayi haɗe da cewa "Gani nan zuwa" tana aje wayar ta ɗauki wani haɗaɗɗen mayafi wanda aka masa ado da fararen duwatsu ta yafa ajikinta yayinda haɗaɗɗen gashinta dayasha saloon ya bayyana kansa ta cikin mayafin..
Tana fitowa tsakar gida ta kalli Husnah wacce yanzu ake zana mata nata lallen, murmushi tayi mata haɗe da kashe mata ido ɗaya, dariya suka sanya su duka domin sukaɗai suka san ma'anar hakan.... Murmushi yayi haɗe da sauƙe ajiyar zuciya alokacin dayaga fitowarta daga cikin gida,,, buɗe murfin motar tasa tayi tashiga bakinta ɗauke da sallama,, cikin murya me ɗauke da kasala ya amsa mata sallaman haɗe da maida kallonsa gareta. Murmushinta dake ƙara mata kyau akoda yaushe tayi masa haɗe da ɗan tsaida idanunta akansa,,,, shiɗinma kallonta yake batare dayace komai ba, azuciyarsa kuwa mamakinta yake ta yanda ta'iya tsaida idanunta akan sa a yau ɗin, bayan kuma yasani sarai batayi masa dogon kallo.
"Namiki kyau ne ƴan mata?" yatambayeta yana me duban kansa,, dariya ne ya kwace mata amma kuma saitayi saurin sanya hanu ta toshe bakinta,
"Wow! gaskiya wannan zanen lallen yayi kyau sosai!" yafaɗi haka yana me ƙoƙarin kamo hanunta, sam shi bai lura da zanen bama sai yanzu,, saurin maida hannayenta cikin mayafin dake jikinta tayi haɗi da cewa "Sai an biya kuɗi me yawa sannan ake kallon wannan zanen" murmushi yayi me sauti, ba ɓata lokaci ya sanya hanu acikin aljihunsa, kuɗi yaciro wanda baisan ko nawa bane, ya ɗaura mata akan cinyarta.
"Karki hanani gani please" yafaɗi maganar yana me marairaice fuska,
"Naƙi wayon kuma ni wannan kuɗin sunmin kaɗan" tafaɗi haka cikin sigar wasa.
"Laluma aljihunsa yayi dama da hagu amma kuma yaji babu ko sisi, kawai saiya marairaice idanunsa yana kallonta, dariya yanzu kam tashigayi, sai da tayi dariyarta ta ƙoshi sannan tace "Kasan baka da kuɗi kuma kakeson ganin zanen lallena?"
Jin shiru bai bata amasa ba yasanyata saurin ɗago kanta ta kalleshi, gani tayi ya zuba mata idanu kamar wani wanda bai taɓa ganinta ba, murmushi kawai tayi haɗe da kawar da kanta gefe, sosai takejin wani iri ajikinta idan yana kallonta.
"Zahrah na!" yaƙira sunanta cikin wata irin murya me sanyi. Zahrah bata iya amsa masa ba, sai dai ta dawo da kallonta gareshi..
Yabuɗe baki zaikumayin magana kenan wayarsa tasoma ƙara,,
"Hajiya"
shine sunan dake yawo akan screen ɗin wayar, dakatawa da maganar yayi haɗe da ɗaukan wayar yakara akan kunnensa.. Hajiya dake zaune akan kujera cikin yanayi na ɓacin rai tace
"Kana'ina ne?"
"Ina wajen Zahrah Hajiya" yabata amsa cike da girmamawa.
"Kabar duk abun da kake kazo gida inason ganinka" tana kaiwa nan azancenta ta kashe wayar.
A hankali ya zame wayar daga kan kunnensa haɗe da sauƙe ajiyar zuciya kallon Zahrah yakumayi haɗe da ɗan sakin murmushi.
"Hajiya nason ganina yanzu, ki riƙe wannan saboda hidimar walimanki na gobe, maybe bazaki sake ganina ba sai bayan na angonce!" yafaɗi haka yana me miƙa mata wasu kuɗaɗe masu yawa daya ciro daga cikin wata ƴar loka dake cikin motar.
"A'a ae bana buƙatar komai don mungama duk wani abun da zamuyi, kuma komai na walima yazama ready, sannan kuma inada kuɗi a wajena ka...."
"Shiiii kinsan banason yawan musu please ki karɓa kinji baby na, ki ajiye kobazakiyi komai dasu ba nasan zasu miki amfani wani lokaci" yafaɗi haka ta hanyar katseta daga maganar da takeyi batare daya bari ta ƙarisa ba,, badon ranta yasoba ta amshi kuɗin haɗe dayi masa godiya kana ta buɗe murfin motar ta fice, shima tada motar nasa yayi yabar ƙofar gidan, zuciyarsa cike da mamakin ƙiran da Hajiya tayi masa, Allah dai yasa ba wata matsalan ne takuma kunnu kai ba, idan dai har akan aurensa da Zahrah ne tofa shikam gaskiya sai dai kowama yayi haƙuri saboda ayanzu baijin zai iya sanja muradin sa...
Fuska ɗauke da mamaki Dr.Sadeeq ke cewa "tafasa aurena kuma Hajiya?"
"Badole tafasa aurenka ba, wace uwa ce zata yarda da irin abun da katsiro dashi? tun ma ba'aje ko inaba kana nuna banbanci ƙarara, gashi abanza ka jawo zubewar mutumcin dake tsakanina da Hajiya Furaira, yanzu da wani ido kakeso nasake kallonta!" Hajiya tafaɗi haka cikin ɓacin rai.
Sunkuyar dakai ƙasa Dr.Sadeeq yayi yana me hamdala acikin zuciyarsa da aka soke batun aurensa da Saleema, dama shi Allah yasani ko ya auri Saleema ba lallaine yakamanta mata adalci ba, saboda abun a bayyane yake yafi ƙaunar Zahrah fiye da kowacce mace a yanzu idan aka cire mahaifiyarsa dakuma ƴar uwarsa ta jini.
"Dama haka kakeso ai shikenan burinka yacika, gakuma kayan lefe dakuma kuɗin auren da kakai can sun dawo maka dashi, sai kaje kayi ta fama da wacce zuciyarka ta zaɓa ma ni tashi kabani waje !"
Sumi sumi haka Dr.Sadeeq yatashi daga gaban mahaifiyartasa cikin sanyin jiki yafice daga cikin falon...
Yana shiga ɗakinsa yasaki wani irin ajiyar zuciya, wayyo Allah shikam daɗi kasheshi, dama yafi kowa tunanin yanda zaman nasu zai kasance saboda shi a tsarin rayuwarsa bai da niyar auren mace sama da ɗaya bare yanzu daya samu Zahrah yasan cewa ita kaɗaima ta'ishesa rayuwa, yaji daɗin fasa wannan auren ƙwarai...
*Zaid*
Gaba ɗaya jikinsa yaƙi daɗi duk yanda yaso koda a daddafene yaje yaga Zahrah hakan yagagara, saboda wunin yau ma gaba ɗaya baiyishi cikin daɗi ba, kasancewar ciwon zuciyarsa yatashi yasanya Dr.Bilal ya dinga basa magani masu sanyasa bacci gudun kada ya matsantawa kansa da tunani, haka dai yanaji yana gani tashi zaune ma yagagaresa, haka ya kwana yana begen ganin Zahrah....
*Friday*
Kowa dake gidansu Zahrah shirin zuwa wajen walima kawai yakeyi, yayinda amarya Zahrah tasha kyau cikin wani haɗaɗɗen sari da aka ɓata lokaci wajen naɗa mata shi ajikinta, yauma dai meckup aka tsantsara mata akan fuskarta nagani na faɗa, take fuskar amarya Zahrah yaci gaba da walwali,, motoci Dr.Sadeeq yaturo suka kwashesu har zuwa inda za'a gudanar da walima,,, walima fa ya ƙayatar saboda Malami aka ɗauko na musamman yagudanar da wa'azi akan yanda ake zamantakewar aure, sanan kuma yaƙara da wa'azi me ratsa jiki harsaida amarya tayi kuka,, bayan anƙare walima ne kuma aka soma rabon abinci haɗe da kyaututtuka kamar su memo da kuma jaka wanda Dr.Sadeeq ne duk yayi su, sai dai babu hoton amarya da ango ajiki sai dai sunansu kawai. Walima fa yaƙayatar kowa sai dai yace Alhmdlh haka aka tashi a taron walima kowa yanacikin farinciki,, yayinda gobe asabar kuma take ɗaurin aure💃.
*(Maza kuzo fa, mata kuma ku faɗawa Mazajenku su je ɗaurin auren😂 🙊Nidai baruwana Team Zaid kada kuga laifina Dr.Sadeeq ne yace ingayyaci kowa da kowa 😂💃😜)*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*(Wannan fejin baki ɗayansa nakine My KHAIR74 kinasani nishaɗi sosai, kiyi farinciki marar iyaka kiji daɗinki akullum inayinki sosai KHAIR74)*
*Editing is not allowed📵*
*NOTE: Masoyana masu cece kuce inagaisuwa agareku, sannan ina mai baku haƙuri, idan akwai wacce wannan hukuncin baiyi mata daɗi ba tayi haƙuri dama shi Aure nufine na Allah, kuma ance matar mutum ƙabarinsa, abun danakeso ku fahimta shine, balallai ne koda yaushe mutum yasamu abun da rai dakuma zuciyarsa keso ba, SO baƙarya bane haƙiƙa so gaskiya ne, amma kuma bako da yaushe bane burin so ɗin ke cika ba, ita rayuwa dama haka take tana iya sauyawa ako da yaushe akuma kowani lokaci.....*
*CHAPTER 88 to 89*
Yauma dai kamar jiya agajiye take matuƙa, suna komawa gida ta yi wanka da ruwa me zafi sai alokacin ta ɗanji ta samu nutsuwa a jikinta. Kwanciya tayi luf akan katifarta haɗe da jawo wayarta tasoma buga game, tayi hakanne gudun kada tunani ya samu daman bijiro mta acikin zuciya...
"Kinada baƙo a waje fa Zahrah" maganar da tafito daga bakin Husnah wacce shigowarta ɗakin kenan..
"Baƙo kuma Husnah?" Zahrah tatambaya cike da mamaki.
"Ƙwarai kuwa amma sai dai gaskiya inaga ba ya ɗaya daga cikin abokan Doctor, yakamata kije ki gansa dan naga kamar yamatsu dason ganinki" Husnah tafaɗi haka bayan tayi mawa kanta masauƙi akan katifar da Zahrah take kwance...
Cike da mamaki Zahrah tamiƙe tsaye haɗe da ɗaukar mayafi ta rufa ajikinta, hakanan taji tamatsu da taga waye ne ke neman nata.....
Tana fita waje tasoma raba idanu ko zata hango wanda akace yana ƙiranta, sai dai kuma bata ga kowa ba...
"Zahrah" taji anƙira sunanta daga bayanta,, da sauri ta juya don ganin kowaye.
Wani kyakkyawan saurayi handsome guy tagani tsaye a bayanta yana ta zuba murmushi, kallo ɗaya zakayi masa kafahimci cewa shiɗin cikekken ɗan gaye ne, kuma ɗan hutu, domin kuwa fatar jikinsa da kuma kayan dake sanye ajikinsa kaɗai sun isa tabbatar maka da hakan..
Takowa yashigayi gareta, har saida yazo kusa da'ita kafun ya ja ya tsaya, kallon kallo suka shiga yiwa juna, Zahrah kallon mamaki da kuma al'ajabin me ya kawosa wajenta take yayinda shikuma yakeyi mata kallon ƙurilla,, wani yawu ya haɗiya a maƙoshinsa bayan yagama ƙare mata kallo daga samanta har ƙasanta... "Zahrah ko?" yafaɗi haka yana me nuna ta da yatsarsa...
Kai kawai Zahrah ta'iya jinjina masa alamar "Eh" still amma kuma idanunta nakansa..
Murmushi yakuma yi mata haɗe da gyara tsayuwarsa "Naji daɗin ganinki ƴan mata, sunana Abid, nasan baki sanni ba amma kuma idan babu damuwa me zai hana muje mota sai muyi maganan, saboda nazomiki da wata magana ce me mahimmanci" yafaɗi haka yana me sake dubanta da kyau...
Kallon sa itama ta sakeyi sosai kafun ta ce. "Kafaɗi duk abun da zaka faɗa anan inaji, amma bana buƙatar shiga cikin motarka" ta ƙare maganar tana me ɗage kanta sama.
Murmushi Abid yakumayi akaro na barkatai "lallai ba'a banza ba Zaid yakasa magance matsalarsa yarinyar akwai taurin kai" yafaɗi haka acikin zuciyarsa...
"I'm sorry bacutar dake zanyi ba, kada kiji tsorona, nazo miki da magana ne me matuƙar mahimmanci, nasan abune me wahala amma kuma keda kanki zakiso ace kinzamo silar ceto rayuwar da take shirin gushewa, nasan bazakiso ace ta sanadiyarki Zaid ya rasa rayuwarsa ba, kina da tausayi Zahrah, me yasa bazaki yarda ki aure sa ba?" abunda ya fito daga bakin Abid kenan..
Kallon baka da hankali Zahrah tashiga bin Abid dashi, da ƙyar ta'iya cewa "Bansan maganar Zaid bace takawoka wajena ba, da bantsaya ɓata lokacina wajen saurararka ba, don bazan ɓata lokacina abanza ba, dan Allah kufita a rayuwata, kacewa Zaid ya ƙyaleni na huta, domin kuwa ko maza sun ƙare a duniya bazan taɓa auren Zaid ba!" Zahrah tafaɗi haka cikin dakiya dakuma ɓacin rai...
"Ba gaskiya bane Zahrah, wannan maganar da kika faɗa ba daga cikin zuciyarki tafito ba daga bakinki tafito, kobaki furta ba raunin kalamanki sunnuna cewa kinason Zaid har yanzu, me yasa bazaki yafe masa ba? Allah ma muna masa laifi ya yafe mana, dan Allah Zahrah ki taimaka ki auri Zaid, haƙiƙa nida Zaid muna biyewa zuciyarmu muna aikata abunda baidace ba, amma kuma ina me tabbatar miki da Zaid ɗin dakika sani a yanzu bashine wanda kika sani ada ba, soyayyarki ta sanjawa Zaid tunani, soyayyarki ta juyamasa ƙwaƙwalwa, wallahi ke kaɗaice muradinsa acikin duniyar nan, Zaid baisan damuwa ba sai akanki Zahrah, yayi nadama me tsanani akan abun daya aikata miki, akan ki Zaid yafara sanin menene ƙunci, akanki yafara sanin menene ɗacin soyayya dakuma zaƙinta, haka akanki Zaid ya kasa fuskantar gabansa dakuma bayansa, akan kine kuma dalilinkine Zaid yakamu da ciwon zuciya me tsanani, ahalin yanzu Zaid yana acikin wani hali, Zahrah ke kaɗaice zaki iya sanjasa ki kuma ceto rayuwarsa please koba don nida Zaid ba kodan ceton rayuwarsa ki taimaka ki auresa!" Abid yaƙare maganar cike da raunin murya sosai yake matuƙar tausayin Zaid musamman ma dayaje yagansa yau, gaba ɗaya yafita hayyacinsa...
Murmushi me tsananin ciwo Zahrah tayi haɗe da sanya haƙoranta tacije lips ɗinta, kallon Abid tayi kana ta girgiza kanta
"Meyasa ku kazamanto mutane masu tsananin son kansu? Zaid rayuwarsa kawai zai rasa, amma ni gani da raina ta sanadiyarsa ne kuma narasa farinciki na, rayuwata tazamo marar amfani a gareni, ya katsemin farinciki dajin daɗi na, yakawo kansa gareni alokacin dayaga dama, yakuma sanyamin soyayyarsa alokacin dayaga dama, sannan yakuma ketamin haddina alokacin da yaga dama, yayimini duk wani abu da ransa keso alokacin dayaga dama, nima kuma yanzu nadawo mutum zankumayi duk wani abun daya dace alokacin dana ga dama, idan shi ne ya aikoka da waƴannan yaudararrun kalaman to kaje kasanar masa cewa kalaman naku basuyi aiki akai na ba, zaifi kyau kubarni nayi rayuwar aurena cikin farinciki da salama, domin kuwa gobe iwarhaka najima da zama matar wani insha Allah, inaso kuma kasani cewa najima da barin Zaid da Allah, haƙiƙa ya cutar dani, amma kuma dama hakan yakasance rubutaccen ƙaddarata ne wanda Allah ya rubuta, kaje kawai Abid bana tunanin sake burin haɗa rayuwata da ta Zaid!" hanu tasanya ta sharce hawayen da suka silalo daga cikin idanunta haɗe da juyawa tasoma tafiya...
"Komai yana hanunki Zahrah idan har kikace afasa aurenki da wanda zaki aura aɗaura da Zaid nasan iyayenki zasu amince, shin maiyasa bazaki cika muku burinku ba? kinasonsa shima kuma yana sonki, ki amince ki aure sa, wallahi namiki alƙawari ko nawa kikeso aduniyar nan zan mallakamiki shi koda kuwa duka dukiyata kika buƙata nabaki zan baki, amma bazan tilastaki ba sai dai inaso kisani idan Zaid ya rasa rayuwarsa a yanzu kece SANADI" Abid yana kaiwa nan azancensa yabuɗe murfin motarsa, wata ƴar madaidai ciyar jaka ya ɗauko, takawa yashigayi harsai da yazo kusa da'ita kafun ya tsaya... "Ki amshi wannan jakan idan kika buɗe laptop ɗin dake ciki zakiga yanda Zaid ya koma A SANADI'N SONKI" Abid yafaɗi haka yana me miƙa mata jakar.. Tsintar kanta tayi da kasa ƙin karɓan jakar, yana bata jakar ya juya yayi tafiyarsa,,, har motar Abid ta ɓule Zahrah na tsaye sororo hanunta riƙe da jaka,,, saurin share hawayenta tayi, haɗe da nufar cikin gidan su,,, sumi sumi haka ta shige cikin ɗakinta, abun yayi mata daɗi sosai data iske Husnah hartayi bacci,, mayafinta ta cire haɗe da neman waje ta zauna, kanta ta kifa akan guiwowinta, damuwane cike azuciyarta, takasa sanin wani hali take ciki, kanta ta ɗago takalli jakar da tashigo dashi, da sauri tajawo jakar haɗe da buɗeta, a hankali ta zaro laptop ɗin dake cikin jakar, saida ta ƙarewa laptop ɗin kallo kafun ta buɗeta, tana danna wani madanni laptop ɗin takawo haske take kyakkyawan hoton fuskarta ya bayyana akan screen na laptop ɗin, mamakine yakamata ganin hotonta wanda batasan ma dashi aduniya ba, balle tasan yaushe ko wace ranace aka ɗauketa hoton ba, ƙurawa hoton nata idanu tayi tamakasa yin komai, bata ɗauke idanunta akan hoton ba har saida hasken screen ɗin laptop ɗin ya gaji dan kansa ya ɗauke.. Ajiyar zuciya me ƙarfi ta sauƙe haɗe da sake kunna laptop ɗin, batasan inazata shiga ba, bata kuma san mezata fara dubawa ba, hakanan ta ji zuciyarta ta ingizata da tashiga ɓangaren hotuna,, tana kutsawa ɓangaren hotuna, hotunantane suka farayi mata wellcome, mamakine yasake kasheta ganin hotunanta kaca kaca babu adadi acikin laptop ɗin, wanda ita a iya tsawon tarihin rayuwarta ma bata kasance mace meyawan sonyin hoto ba, yanzu haka ko hotonta ƙwaya ɗaya bata dashi acikin wayarta,,,, bata da me amsamata tarin tambayoyin dake ranta dan haka kawai saita shiga wuce hotunan nata, hotunan Zaid takuma cin karo dasu wanda saida gabanta yayi wani irin faɗuwa yayinda ƙirjinta yashiga dokawa da sauri.. da ƙyar ta'iya view ɗaya daga cikin tarin hotunan nasa, sanye yake da wandon jeans baƙi dakuma wata farar riga saikuma hular sanyi daya sanya akanshi yayinda kunnensa ke sanye da farin earpiece, yayi kyau matuƙa a hoton domin kuwa fuskarsa ɗauke take da wannan ƙawataccen murmushin nasa wanda yake ƙara masa kyau ako da yaushe... Ƙura mawa hoton nasa idanu tayi, saitaga tamkar shiɗinne da kansa agabanta, batasan sanda wasu hawaye suka silalo daga cikin idanunta zuwa kan ƙuncinta ba,, tajima tana kallon hoton nasa, haka kuma hawaye na tsiyaya daga cikin idanunta, ɓangaren vedios takuma kutsawa, sai dai vedion farko da ta gani shine wanda yakusa tarwatsa mata zuciya, yakuma ɗaga mata hankali,, Zaid tagani kwance akan gadon asibiti ansanya masa oxygen, yayinda aka dasa masa wasu ƙarafan na'urori akan ƙirjinsa dai dai saitin zuciyarsa, da badon ɗan abu kamar computer'n dake gefensa wanda shike nuna alama yana da rai ba, to tabbas da saidai ace dashi gawa,,, wani irin sarawa taji kanta yayi, yayinda wani irin kuka yazo mata alokaci guda, saurin sanya hanu tayi ta toshe bakinta haɗe da rumtse idanunta, a hankali ta jingina bayanta da bango,,, hawayene suka shiga gudu wani na koran wani akan fuskarta,, duk yanda taso daurewa kasawa tayi saikawai tafashe da wani irin kuka me sauti, kuka take sosai yayinda ta rungume wannan laptop ɗin akan ƙirjinta,,,, kamar amafarki Husnah kejin gunjin kuka natashi acikin ɗakin, dayake ita ba me nauyin bacci bace yasanyata buɗe idanunta ahankali, aikuwa dagaske ba amafarki bane, kukan Zahrah taji raɗau acikin kunnenta, da sauri ta tashi zaune haɗe da dawo da kallonta inda sautin kukan ke fitowa,, sake waro idanunta tayi ganin da tayiwa Zahrah na kuka tsakaninta da Allah. "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un! Zahrah meyafaru kike irin wannan kukan?" Husnah ta tambaya cikin ruɗewa... Jin muryar Husnah acikin kunnenta yasanya, tataso daga inda take da sauri ta faɗa jikin Husnah ae kuma saita ƙara volume ɗin kukan nata,, kai Husnah ta dafe cike da tashin hankali, "Allah yasa dai bawani gagarumin abubane yafaru" Husnah tafaɗi haka acikin zuciyarta.
"Kiyi shiru dan Allah Zahrah, kinga dai yanzu dare ne sokike kowa saiyaji gunjin kukan ki? kiyi shiru kisanar dani meke faruwa" Husnah tafaɗi haka ga Zahrah cike da damuwa... Yau Zahrah tsintar kanta tayi da kasa daina kuka, ji ma take tamkar Husnah ingizata take da ta ƙara volume,, sororo haka Husnah tayi ganin Zahrah taƙi daina kukan, zame ta tayi daga jikinta haɗe da nufar inda aka aje musu ledan ruwa na pure water, guda ɗaya ta zaro acikin ledan haɗe da fasawa ta tsiyaya acikin cup,, dawowa tayi ta zauna haɗi dakai kofin ruwan bakin Zahrah, babu musu Zahrah ta amshi kofin takai bakinta, gaba ɗaya ruwan dake cikin kofin tashanye tas haɗe da aje kofin agefe, ajiyar zuciya tasoma sauƙewa akai akai amma na kuka,,, kwanciya tayi luf haɗe da sanya hanu ta dafe kanta dake matuƙar sara mata,,, idanu kawai Husnah ta zuba mata tana me mamakinta, gaba ɗaya aƴan kwanakinnan talura Zahrah ta maida kuka abinci da kuma ruwan shanta, ita yanzu hartama fara tunanin ko aljanune suka shiga jikin Zahrah'n,, bayan kamar minti goma Husnah taƙira sunan Zahrah,, amma kuma saitaji shiru Zahrah bata amasa mata ba, hakan ne yasanya tayi tunanin cewa Zahrah'n tayi bacci, raɓawa gefen Zahrah'n itama tayi ta kwanta, mintuna kaɗan bacci yakuma surarta, Zahrah na jin sauƙar numfashin Husnah nafita a hankali ta tabbatar da cewa Husna'n tayi bacci, ahankali ta ware idanunta dasuka cika tab da ƙwalla, sarai tanaji sanda Husnah taƙira sunanta, taƙi amsawa ne gudun kada ta tonawa kanta asiri, saboda batason wannan sirrin yafita daga cikin zuciyarta, har abada tafiso ta bunneshi ita kaɗai batare dakowa yaji koya gani ba, ada tana ganin cewa ita mahaukaciya ce datakeson wanda ya zalunceta, sai ayanzu ta sake tabbatarwa kanta cewa shi so babu ruwansa, idan zai shiga jikinka baya duba wani cancanta ko matsayi haka nan yake faɗa ma, ashe da fari tayi ƙarya da tace zatayi yaƙi da soyayyar Zaid a zuciyarta, ashe ba'a iya yaƙi da soyayyar da take acikin jini da tsoka,, ada tana tunanin cewa zuciyarta bata kyauta mata ba, ashe itace bata kyautawa kanta ba, yanzu ta gamsu cewa so ne ya lalata mata rayuwa ba wai Zaid ba, ashe so shine ya yaudareta, ashe so shine yaci amanarta, ashe Zaid bai aikata mata wani babban laifi ba So ne ya aikata mata laifi me girma, inama da ana ganin so, to da tayi masa roƙo takuma yi masa magiya akan cutarwar da yayi mata daya barta haka,, itakuma SO shine ƙaddaranta, ada ta ɗauka idan tafaɗawa mutane cewa tanason mutumin dayayi sanadiyar rugujewar rayuwarta, kowa zai ɗauketa mahaukaciya wacce batasan me takeyi ba, amma kuma ayanzu tagane cewa wanda duk ya mata kallon mahaukaciya akan soyayyar da takeyia Zaid, to ko kaɗan baisan menene SO ba, SO shine wanda ke sauyawa mutum tunani alokaci ƙanƙani batare daya shiryawa hakan ba, SO shine wanda ke makantar da idanun mutum yazamanto bayaji baya gani, haka kuma tasanadiyar SO wasu ke salwantar da rayuwarsu, SO shike sawa kabi wanda baidace dakai ba, SO shike sawa amaka wulaƙanci amma kuma gobe ka koma inda aka wulaƙanta ka, SO shike sawa mutum yazalunceka amma kuma bazakaga laifinsa ba,kuma koda ma kagani bazaka iya juya masa bayaba, SO yana da matuƙar haɗari sannan yafi kowani abu saurin ɗaiɗaita tunanin meyinsa, SO shikaɗaine abun da zafinsa ke narkar da zuciya,,,,SO shine babban jagoran zuciya haka kuma shine raunin ta,, hanu ta sanya takuma dafe kanta wanda takeji kamar zai zazzago ƙasa,, hmmm kamar dai yanda Zahrah taga rana haka taga dare bacci sam yaƙauracemawa idanunta.....
(Kada kuga laifin Zahrah dan ta ci gaba da son Zaid, haƙiƙa Zaid ya cancanci Zahrah taƙisa mugun ƙi mawa kuwa, amma kuma SO bazai taɓa barin haka yafaru ba, wallahi Soyayya tawuce gaban kwatance, so babu ruwanshi da wai ancutar dakai ko ba a cutar dakai ba, shi so kaitsaye yake abunsa batare da yatambayeka shawara ba, nikam bana ganin laifin Zahrah dan taso Zaid domin shi so baya fita acikin sauƙi, sannan kuma zafinsa yanada matuƙar illa, ba'akanta aka fara ba, sau da dama zakuga namiji yana zagi dakuma dukan matarsa amma kuma duk da haka tanazaune dashi saboda tana sonsa, haka kuma saudadama zakuga Saurayi yayi amfani da soyayyar da budurwarsa takeyi masa ya yaudareta sun aikata zina, daga baya kuma idan ciki yashiga jikinta sai kuga yagujeta, saboda yasamu abun dayakeso daga wajenta, amma kuma idan harson gaskiya takeyi masa saikuga bata daina sonsaba duk dakuwa irin girman abun dayayi mata,, wallahi soyayyar gaskiya bata taɓa gushewa koda kuwa girman laifin da mutum ya aikata maka bazai misaltu ba, haƙiƙa idan banda sharrin SO babu wata mace da namiji zaiyi mata fyaɗe kuma ta dawo tacigaba da sonsa, wannan sharrin SO ne kawai wanda bashida magani😭 nidai nace ko guba baikai so hatsari ba, wallahi so mugune, inkun ganshi kukamaminshi kumai duka😰)
Ƙarfe 2 na dare ciwon Zaid yatashi sosai, abun gwanin ban tausayi, zuwa yanzu kam ciwon nasa yasoma fin ƙarfin tunanin Doctor's domin kuwa sai anyi tunanin cuta tayi sauƙi saikuma tadawo, yanzu haka bincikensu yanuna musu cewa zuciyarsa ce takumbura, gaba ɗaya hankalin Alhj Ma'aruf yakai ƙololuwa wajen tashi, Mum kuwa yanzu bata da aiki saina kuka dare da rana, hakanne ma yasanya Alhj Ma'aruf yanke hukuncin tattara Zaid ɗin sutafi Jermany, saboda ya ga abun yana nema yafi ƙarfin likitotinmu na nan, saboda koda yaushe Zaid cikin aman jini yake, lokaci ɗaya ya lalace yayi wani irin rama, kamar ma ba
Zaid ba.....
Washe Gari (Asabar)
*ƊAURIN AURE*
Tun ƙarfe 8 na safe gidansu Zahrah yake acike yayinda ƴan uwansu na nesa suka soma hallara don ɗaurin aure,, hayaniya ne ke tashi kota ina acikin gidan...
Ɗakin Zahrah na garzaya don inga awani hali take ciki...
Kwance take akan katifarta yayinda duka jikinta ke rufe da bargo, amma duk da haka bargon bai ɓoye rawan da jikin nata keyi ba, karkarwa kawai takeyi acikin bargon yayinda jikinta yaɗauki zafin zazzaɓi zau..
"Kitashi kisha maganin nan dan Allah Zahrah, kinga fa babu amfanin zama da ciwo batare da kinsha magani ba" Husnah tafaɗi haka ga Zahrah cike da lallami..
Kai kawai Zahrah ta'iya kaɗawa alamar "A'a bazata sha ba" komagana ma yanzu bata iyayi saidai kawai ta kaɗa kai, hakan yafarune kuma saboda ciwon kai me tsanani da ta tashi dashi a safiyar yau ɗin,, duk yanda Husnah takaɗa ta buga akan Zahrah tatashi tasha magani ƙiyawa tayi, sai ruwan hawaye dake ta fita daga cikin idanunta, dole haka Husnah ta ƙyaleta..
10:30 tuni ƙofar gidansu Zahrah yasake cika da jama'a bamasaka tsinke, hayaniya ne kawai ke tashi tako ta ina, yayinda tsala tsalan motocin ango suka ƙaraso,, hmmm Dr.Sadeeq yasha kyau sosai cikin wata haɗaɗɗiyar gezina milk colour me matuƙar kyau da tsadar gaske, ɗinkin rigane da wando saikuma gare, amma kuma sunyi masa kyau sosai, yayinda ya ɗaura tsadadden agogo a hanunsa na dama, takalmin ƙafarsa kuwa ƙirar kamfanin GUCCI ne me matuƙar kyau,, ango fa yasha kyau iya kyau, sai yau nima nasake tabbatarda cewa shiɗin ma wani Handsome guy ne mezaman kansa, domin kuwa duk ƙwaƙwan mutum babu ta'inda zai kushesa, yahaɗu iya haɗuwa sonkowa ƙin wacce ta rasa😜, bakin ango fa yaƙi rufuwa sai murmushi kawai yake, yayinda abokansa keta tsokanansa,, shidai kawai murmushi yaketa zubawa, bazai taɓa iya misalta irin tarin farincikin dayake ciki ba, haƙiƙa yau yana cikin nishaɗi dakuma jin daɗi, yau takasance babban rana agareshi ranar da duk wani gauro da gauruwa suke jira, ranar da duk wani mai hankali da nutsuwa yake biɗar zuwanta wato RANAR AURE, shikam sai dai yace Alhmdlh yagodewa Allah mai kowa me komai daya nuna masa wanann rana... Baffa na hango shima yau cikin farinciki yake, yasha adonsa cikin farar shaddansa riga da wando dakuma gare, su uban amarya manya,,, 11:00 am dai dai dandazon jama'a suka shaida ɗaurin auren SADEEQ KHABEER SARDAUNA (Dr.Sadeeq) da amaryarsa FATIMA ADAM (Zahrah) akan sadaki naira dubu ɗari,, masha Allah ana kammala ɗaurin aure aka soma taya ango murna da Allah yasanya alkhairi, ae kuwa fuska asake haɗe da tarin annuri Dr.Sadeeq ke amsawa, hamdala kawai yakeyi acikin zuciyarsa shikenan Zahrah ta zama tasa mallakinsa halaliyarsa... Bayan angama musabahane kuma aka ɗunguma zuwa wani babban hotel wanda anan za'a gudanar da receiption....
Lokacin da labari ɗaurin auren ya'isa ga kunnen Amarya wani irin faɗuwar gaba wanda bata taɓa jin irinsa ba taji ya rusketa, shikenan yanzu tazama matar Doctor, zuciyar tane tashiga bugawa da sauri sauri yayinda har ƙirjinta yasoma amsawa, take taji wani abu maikama da tsananin tsoro ya lulluɓe mata jiki,ae kuwa sai neman ɗan kuzarinta tayi ta rasa,jitayi gaba ɗaya gaɓoɓinta sun mutu laƙwas kamar ansassare mata su,, sake duƙunƙunewa tayi acikin bargo tashiga rera kuka marar sauti, ita bata tsani Dr.Sadeeq ba ko kaɗan, amma kuma tarasa meke damun ƙwaƙwalwa da zuciyarta....
(Kuyi haƙuri Team Zaid wallahi nima Allah jikina gaba ɗaya yayi sanyi sai dai kuma kunsan ita ƙaddara bata taɓa sanjawa dole saitazo a yanda Allah ya aikota😭 yanzu haka jinake kamar ruwan jikina ya ƙare😥)
Ƙarfe 2 dai dai jirginsu Zaid yatashi daga cikin garin Lagos Nigeria zuwa Jermany saidai shi Zaid sam baisan wainar da ake toyawa ba saboda baya cikin hayyacinsa kwata kwata, tunda suka baro Abuja har suka iso Lagos baisan inda kansa yake ba....
Ɓangaren ango kuwa reception aka gudanar gangariya, anci kaji ansha fruits juice kowa cikin sa yayi haniƙan sai dai godiyar Allah da sanya albarka...
Amarya kuwa koda ruwane takasa sanyawa acikin cikinta, rashin lafiya sosai ya tsananta a gareta, zuwa yanzu kam hawayen ma sun kafe sundaina fitowa, sai numfashin wahala da take fitarwa ta bakinta kawai,, kasancewar anata hidima yasa babu wanda yadamu da cinta kokuma shanta, Husnah ce kaɗai ke tsaye akanta tana bata kulawa.
"Dan Allah Zahrah ba danniba kitashi inrakaki toilet kiyi wanka kizo kisamu koɗan sabon kayane kisanya kingafa zuwa anjima za'a zo ɗaukarki!" Husnah tafaɗi haka tana me ƙoƙarin tada Zahrah dake kwance zaune.
Da taimakon Husnah Zahrah taje banɗaki tayi wanka, koda tafito wata haɗaɗɗiyar doguwar rigar atamfa Husnah ta bata tace ta sanya, babu musu tasanya saigashi kuwa rigan tayi matuƙar yi mata kyau ajiki, da ƙyar Husnah ta lallaɓata tashafa mata powder haɗe da man leɓe, sai kace wata ƙaraman yarinya,,, komawa gefe Zahrah tayi ta takure bayan Husnah tagama shiryata, still Husnah maganar abinci tayi mata amma Zahrah tasake bushe idanunta tace ita sam bazataci abinci ba batajin yunwa (Ninaga jarfa saikace wanda aka mawa auren dole 😏)...
Ƙarfe 5 tsala tsalan motocin ɗaukar amarya suka shiga fakawa a ƙofar gidansu Zahrah motocine reras masu kyau har guda 15 suka zo don ɗaukar amarya yayinda motar da amarya zata shiga ta banbanta da duka sauran motocin don tafi duka sauran kyau..
Zahrah na zaune wata Aunty Ladi ƴar uwar mahaifiyarta wacce tazo daga Niger tashigo cikin ɗakin babban mayafi me kyau ta ɗauka haɗe da rufe Zahrah dashi, miƙar da'ita tsaye tayi cikin farinciki tace
"Allah yayi yauzaki tafi ɗakinki amarya muje ɗakin Inna'n taki aimiki nasiha"
aitun kan aƙarasa ɗakin Inna Zahrah ta ɓarke da kuka wiwi, (Wayyo Allah, wallahi duk rashin daɗin gidanku randa zaka barshi saikaji ciwo acikin ranka harna tuna da nawa ranan 😭🙈)
Nasiha Inna da sauran matan dake ɗakin suka shiga yi mawa Zahrah akan tabi mijinta sauda ƙafa inayi bari na bari, komin ƙanƙantan ɓacin ransa ta gujesa, duk kuma wani abu datasan bayaso kada ta aikata, sannan kuma taji taƙi ji tagani taƙi gani, takuma riƙi haƙuri don shine tubali kuma gini haka ƙinshiƙin zaman aure, bawai idan anyi aure kullum soyayya ake ci ba, a'a watarana dole sai kunɓatawa juna, dole sai kunyi haƙuri kundanni zuciyarku tukun zamanku zaiyi daɗi, sannan kuma idan tasan tayi masa laifi kada tayi girman kai, tasameshi har ƙasa ta duƙa tabasa haƙuri, domin kuwa har kullum shine sama da'ita, yanzu amatsayin uba yake agareta bata da wani wanda yafishi,, wayyo Allah Zahrah tayi kuka sosai harda shiɗewa, Allah sarki sabo turken wawa duk da cewa Inna watarana tana hantararta amma yau duk saitaji babu daɗi tafiyan Zahrah'n saiga Inna tana hawaye tana jan majina, shikenan Inna kuma fa cin kaza ya yanke mata lol 😂.
Su Inna suna gama nasu nasihar aka garzaya da'ita wajen Baffa,, wayyo Allah Zahrah tana ganin Baffanta ta faɗa jikinsa haɗe da sake ƙara volume ɗin kukanta, Allah sarki take Baffa shima yasoma hawaye, daƙyar ya'iya daure zuciyarsa yayi mata nasiha, duk dai maganar ɗayace shine tabi mijinta sau da ƙafa takumayi masa biyayya akan duk abun dayace, sannan kuma tazamo me haƙuri akan dukkan komai, sannan kuma yaroƙi yafiyarta akan abun dayayi mata baya, tana kuka tace tajima da yafe masa kuma ita baimata komai ba, itama tanemi yafiyarsa yakumace ya yafe mata😭
Haka Aunty Ladi da Husnah suka fita da Zahrah tana kuka Husnah kanta kuka take, yanzu itama haka watarana za'a zo a ɗauketa daga gaban Momynta akaita can cikin wasu dangin😭...
Anasa amarya acikin mota sauran ƙawaye da ƴan uwa ma kowa yashiga motar da ransa keso, bayan komai yakammalane motocinnan suka gangara kantiti, atare suke tafiya wani abayan wani, sannan kuma komai anitse akeyinsa babu wani hargowa...
Direct gidansu Dr.Sadeeq aka wuce da amarya, domin kuwa 8:00 pm nayi za a wuce wajen diner...
Abun mamaki tarba me kyau Hajiya tamawa amarya dakuma danginta, ko kaɗan bata nuna musu ɓacin rai kokuma tsana ba, sai dai su Aunty Raliya dasuketa binsu da wani irin kallo dake nuni da cewa baƙaunarsu sukeyi ba, ɗaki guda aka warewa amarya, balaifi ɗakin yayi kyau sosai, akan gado Aunty Ladi ta zaunar da Zahrah, mintuna kaɗan da shigowansu ɗakin wasu ƴan mata suka cika musu gabansu da kayan ciye ciye dakuma na sha abun gwanin burgewa, gaskiya sun samu tarba na mutumci daga Hajiyar Doctor......
Wayar Husnah ce tafara ruri ganin wanda ke ƙiran nata yasanya ta ɗaga wayar bawani ɓata lokaci
"Bestie'n mu how far?" abunda wanda yaƙirata acikin wayar yafaɗa kenan..
Dariyane yakamata amma saita taƙaita dariyan haɗe da cewa "I'am fine sai dai gaskiya na gaji"
Murmushi shima yayi haɗe da cewa "Ina Amaryata Allah yasa tana lafiya, nayi kewarta sosai rabona da'ita fa tun ranan alhamis" Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana me gyara kwanciyar dayayi akan gadonsa...
"Kamar kuwa kasan kainaketa so kaƙira, wallahi yau tun safe Zahrah taƙicin komai kuka kawai takeyi, gashi bata da lafiya temperature ɗinta ya hau sosai" Husnah tafaɗi haka ga Dr.Sadeeq.
"Subahannallah, keda su waye aɗakin?" Dr. yatambayi Husnah cike da zaƙuwa..
Kallon waƴanda ke cikin ɗakin Husnah tashiga yi kafun tace
"Gaskiya munada ɗan yawa"
"Oh my God to shikenan, please anjima kikawomin ita ina cikin boys guaters kinji"
"To shikenan zan kawota insha Allah"
Daga haka suka kashe wayar murmushi kawai Husnah tayi bayan ta'ajiye wayar tata gaskiya azamaninnan idan mace tasamu wanda ke sonta kamar irin sonda Dr keyiwa Zahrah yakamata ta riƙeshi da kyau hanu tara tara domin samun irinsu wahalane dashi, saboda yanzu zuciyoyin yawancin mutane duk taɓaci da yaudara.........
*Inasonku masoyana na Wattpad irin sosai ɗinnan, ina yaba ƙoƙarin ku wajen min comment, Allah yabar ƙauna*
*Kuɗin ma ae nadabanne masoyana na Whatsapp inajin daɗinku sosai iya wuya muna jone Insha Allah*
*Comment*
*Share*
*and Voted please*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 90 to 91*
Saida kusan gabaki ɗaya mutanen da suka kawo Zahrah suka soma watsewa zuwa wajen dinner, kafun Husnah ta matso kusa da amarya Zahrah wacce take aikin kuka. Hannayenta takamo haɗe da zama gaf da'ita.
"Please Zahrah kidaina wannan kukan, yanzu haka Doctor yace inkai masa ke yana boys guaters, kuma kinga babu amfanin kije wajensa kina kuka" Husnah tafaɗi haka ga cikin lallashi.
Zahrah dai bata kumace da'ita komai ba bata kuma daina kukan ba,, wayar Husnah ce tayi ƙara alamar shigowar ƙira, sunan Dr.Sadeeq ne keyawo akan screen ɗin wayar,, tana kara wayar akan kunnenta yace
"Yadai Husnah, najiku shiru"
Sake kallon mutanen da sukayi ragowa acikin ɗakin Husnah tayi.
"Gaskiya babu dama Doctor, saboda dazaran anga zamu fita za'ace ina zankaita" Husnah tafaɗi haka cikin ƙasa ƙasa da muryarta....
Ajiyar zuciya Dr.Sadeeq yayi haɗe da cewa
"Okay to bakomai zan san yanda za'ayi, ku shirya me meckup tana nan zuwa"
Cikin matsanancin ciwon kan dake ɗawainiya da'ita tashiga toilet ta ɗauro alwala, kan ƙaton darduman dake shimfuɗe a tsakiyar ɗakin ta hau ta kabbara sallah'n magriba,, tana idar da sallan meyi mata meckup ta ƙaraso, haka tanaji tana gani ta bada fuskarta aka zizara mata meckup wanda yaɗauki fuskarta sosai.. Yauma dai meyin meckup ɗinne ta shiryata tsab cikin wata haɗaɗɗiyar doguwar riga (wedding gown) na wani tsadadden leshi me matuƙar kyaun gaske, riga ce doguwa har tana sharan ƙasa yayinda bayan rigar aka sanya wani haɗaɗɗen net me matuƙar kyaun gaske, sosai net ɗin da aka sanya abayan rigan yakuma ƙawata ɗinkin, lace ɗin yakasance light pink colour yayinda kayan ƙyale ƙyale najikinsa yakasance golding ash colour, sosai kayan yayiwa Zahrah kyau,,, haɗaɗɗen ɗaurin ɗan kwali aka tsantsara mata akanta, take tasake yin kyau,,,, yau dai kwalliya da kuma kyawun da Zahrah tayi haryafi wanda tayi a ranan kamu, komai nata yau na musamman ne tasha kyau sosai, ga doguwar riganta me ɗaukar hankali, daddaɗan ƙamshi kawai take fitarwa ajikinta me sanya nutsuwa,, duk da irin wannan kyawun da tayi sai dai fuskarta babu wani wadataccen walwala domin kuwa idanunta sunyi luhu luhu dasu, cikinta kuwa banda kukan yunwa babu abun dayake yi mata, amma kuma saboda masifar taurin kai irin nata taƙi sanyawa cikin nata komai na abinci.. Husnah ma yau zama tayi akayi mata meckup nagani na faɗa, sosai itama tayi kyau, tasha adonta cikin wata doguwar riga na golding white lace, idan ka kalleta dole ka ƙara domin itama tayi kyau sosai dama kuma itaɗin ma ko babu meckup tana da kyau masha Allah....
Yauma dai ango tare da amaryarsa zasu wajen dinner kowa yariga daya tafi harsu Auntie Raliya kuwa....
Husnah ce riƙe da hanun Zahrah suka fito compound ɗin gidan inda motar ango ke jiransu.
Shikam gaba ɗaya kwana biyunnan salon kyawun na Zahrah namatuƙar tafiya da imaninsa babu ma kamar yau, gaba ɗaya komai na surar jikinta ya bayyana bama kamar hips ɗinta yafito raɗau acikin rigan..
Husnah ce ta buɗe murfin motar dayake zaune aciki, sai da ta tattaro ƙasan rigan Zahrah'n kafun Zahrah ta'iya shiga cikin motar ta zauna,, lumshe idanunsa yayi haɗe da shaƙan daddaɗan ƙamshin daya kawowa hancinsa ziyara, wani irin ajiyar zuciya me ƙarfi ya sauƙe,, kallonsa yakuma dawowa dashi kan tauraruwar da haskenta yacika idanunsa,,, murmushi yasakar mata me ƙayatarwa, yayinda ita kuwa kanta ke duƙe aƙasa tama kasa ɗago idanu ta kalleshi,, hanunsa ya sanya ya ɗago haɓarta, sai alokacin ta iya jefa idanunta cikin nasa idon, wani irin abu yaji acikin jikinsa, ita ɗinma hakane, da sauri ta rumtse idanunta,, abun daba ta tsammata ba, sai jitayi ya jawota jikinsa, haɓanta yakuma ɗagowa da hanunsa na dama, haɗe da sanya ɗayan hanunsa yashafi gefen kumatunta
"My Princess!"
yaƙira sunanta cikin wata muryarsa me sanyi. a hankali ta ware idanunta acikin nasa idanun, ƙasa ƙasa yayi da idanunsa haɗe da maida kallonsa ga ɗan ƙaramin bakinta dayasha lipstick, murmushi yakuma sakarmata haɗe da sake jawota ya ɗaurata akan cinyarsa.
"Kinyi kyau fiye da kullum my princess!" yafaɗi haka still yana me shafa gefen kumatunta da hanunsa, wani irin kunyarsane yakamata tunda take dashi baitaɓa yi mata irin kallon dayakeyi mata a yanzu ba, haka kuma baitaɓa jawota yaɗaurata akan cinyarsaba sai yau. Marairaice fuskarta tayi haɗe da sunkuyar da kanta ƙasa,, sweet ɗin dake cikin bakinsa ya cire, haɗe da ɗago fuskarta ya sanya mata acikin bakinta, kallonsa tayi da ɗara ɗara idanunta, kansa ya jinjina mata yana ɗan murmushi, ahankali tashiga juya sweet ɗin acikin bakinta, dama kuma tunsafe babu wani abu daya shiga bakinta inbanda ruwa, sai wannan sweet ɗin daya bata yanzu,, hanunta yakama yashiga murzawa ahankali haɗe da kafeta da idanunsa wanda lokaci ɗaya suka wani marairaice.... Sauƙeta yayi daga kan cinyarsa haɗe da kama hanunta ya buɗe murfin motar riƙe da hanunta haka suka fito daga cikin motar,, kamar wata jela haka take binsa still hanunta na riƙe acikin nasa, direct wani dogon gini dake cikin gidan nasu suka nufa. Ita dai kawai binsa take cikin takunta me ɗauke da nutsuwa yayinda rigar jikinta kuwa ke share wajen, don ma wajen babu datti, wani haɗaɗɗen falo ta tsinci kanta a ciki, suna shiga cikin falon Doctor yatsaya daga tafiyan da yakeyi haɗe da juyowa gareta, murza hanunta dake cikin nasa yayi haɗe da zaunar da'ita akan kujera, kaitsaye wajen wani fridge dake aje cikin falon ya nufa, buɗe murfin fridge ɗin yayi haɗe da ɗauko kwalin fresh milk wanda bashida sanyi sosai, glass cup ya ɗauka ya tsiyaya fresh milk ɗin aciki, saida yakusa cika kofin kafun yamaida sauran cikin fridge ɗin ya aje.. Inda Zahrah ke zaune ta sunne kai ƙasa ya nufo, aje kofin fresh milk ɗin yayi akan ɗan ƙaramin table ɗin dake kusa da kujeran daya zauna, jawo Zahrah yayi jikinsa haɗe da sake ɗaurata akan cinyarsa, kofin da fresh milk ɗin ke ciki ya kawo dai dai saitin bakinta, cikin muryar lallami yace
"Anfaɗamin bakici komai ba tun safe, banaso kina zama da yunwa fa, banso tayi miki illa, kisha ko kaɗanne kinji baby na!"
Tsintar kanta tayi da kasa musa masa, saidai amma kuma gaba ɗaya a tsarge take, bata taɓa zama akan cinyar wani haka ba, hakan yasa gaba ɗaya ta takura,, a hankali take ɗan shan fresh milk ɗin wanda harkusa da bakinta Dr.Sadeeq yake kawo mata kofin, shan fresh milk ɗin take cike da nutsuwa yayinda shi kuma gaba ɗaya idanunsa ke kanta, bakinta kawai yake kallo, karo na farko kenan arayuwarsa dayaji wani irin muguwar sha'awarta na fusgarsa,,, kafun shida ita su ankara tuni hartasha fiye da rabin kofin,, ɗan ya mutsa fuskanta tayi haɗe da sanya hanu ta shafi ɗakalallen cikinta
"Naƙoshi fa!" tafaɗi haka tana me langwaɓar da kanta gefe.
"Um'um ban yarda ba nasan kinajin yunwa sosai, ki ɗan ƙarasha ko kaɗan ne kinji _MY WIFE_!"
Kalmar nan ta_MY WIFE_ daya ƙirata dashi shiyasanya taji gaba ɗaya jikinta yayi mata wani iri,,, bakinta ta turo gaba haɗe da cewa
"dagaske ni na ƙoshi, gashi kuma duk kasa janbakina ya goge!" taƙare maganar akasalance.
Wannan shagwaɓan da takeyi masa shiyake sanyawa yaji gaba ɗaya jikinsa ya mutu, har wani rufewa idanunsa keyi,, yabuɗe baki zaiyi magana kenan wayarsa tasoma ƙara, kobai ɗaga ba yasan dalilin ƙiran, yanzu haka yasan anacan antaru a wajen dinner su kawai ake jira, miƙar da'ita yayi tsaye bayan ya aje cup ɗin dake hanunsa,, amaimakon ya riƙe mata hanu su tafi kamar yanda suka zo sai gani tayi ya ɗagata caɗak yayi hanyar waje da'ita,, a tsorace tanemi sauƙa daga jikin nasa amma kuma kyakkyawan riƙon dayayi mata yakasa bata daman hakan....
Bai direta ako ina ba sai acikin mota, yanashiga driver yaja motar suka fice daga cikin gidan... Kwanciya tayi luf ajikin kujeran motar haɗe da lumshe idanunta gaba ɗaya sanyin AC'n da motar ke busawa ne ke damunta, sam batason sanyi yacika yawa a waje. daga wani ɓangare kuwa amatuƙar takure take, saboda yanayin yanda yake murza hanunta dake cikin nasa. sosai hakan kesawa taji wani iri acikin jikinta, gani tayi gaba ɗaya yau ɗin ya sanja mata, yanayi mata wasu irin abubuwa da baitaɓa ƙoƙarin kwatanta yi mata shiba acan baya, ada sam baya taɓa yunƙurin kama hanunta sai dai idan yazama dole,kuma koda ma ya kama hanunta bawani jimawa zai sake, sannan kuma sam baya yawan jawota jikinsa kamar yanda yakeyi mata ayau, gashi gaba ɗaya taga yanayinsa ya sauya, idanunsa sunyi wasu kala tamkar wanda yakejin bacci... Zuciyarta nayi mata lugude haka suka iso wajen dinner inda mutane suka cika maƙil zuwansu kawai ake jira... Suna isowa waje yaɗauki sowa yayinda mc yasake musu daddaɗan kiɗa me daɗi ta romantic... kamar dai yanda kamu ya ƙayatar haka dinner ma yaƙayatar sosai Dr.Sadeeq yayiwa Zahrah ɓarin kuɗi lokacin da aka ƙirasu tsakiyan fili, sunsha liƙin kuɗi kam sosai, su Auntie Raliya ma sunzo sun liƙa musu, amma duk yanda akaso amarya tayi rawa kasawa tayi, saboda bata iyaba, bakuma al'adarta bane yin rawa agaban mutane, kunya ma bazai taɓa iya barinta ba,, saida Dr.Sadeeq yariƙe hanunta yashiga juyawa da'ita afilin rawan, take aka hau musu tafi yayinda wasu daga cikin abokansa suka ci gaba da yi musu ɓarin kuɗi,, suna komawa kan kujeransu mc yasanya musu daddaɗan waƙar Ed sheeran, shiru Zahrah tayi tana sauraran waƙar sosai dama takeson waƙar domin kuwa duk waƙan Ed sheeran yanayi mata daɗi... Koda aka yanka haɗaɗɗen cake ɗin da aka ƙawatashi da sunan ango da amarya, da ƙyar Zahrah ta'iya bawa Dr.Sadeeq cake ɗin abaki, gaba ɗaya nauyi da kunya sun isheta gawani zazzaɓin daya sake kawo mata ziyara lokaci ɗaya,,, lokacin da aka tashi a dinner tuni amarya Zahrah tayi laushi, hartakai bata iya dogon tsayuwa da ƙafafunta, ƙarfe 10 na dare aka tashi a dinner Aunty Ladi da kuma Husnah su suka sanyata a wata mota, direct aka wuce da'ita asalin gidan da zata zauna wato gidan aurenta.... Gidane me matuƙar kyaun gaske wanda aka kashe kuɗi sosai wajen ƙawatasa, baginin gidan sama bane amma kuma yanayin yanda akayi ginin yayi kyau sosai, wata haɗaɗɗiyar ƙofa suka nufa, suna buɗeta kuwa suka tsinci kansu cikin wani ƙawataccen falo me kyaun gaske. haɗaɗɗen falone wanda yasha kujeru light orange and milk colour, yayinda aka ƙawata jikin ƙofa da window'n da wasu irin haɗaɗɗun labulaye masu kyau, tsakiyar falon kuwa mamaye yake da wani haɗaɗɗen carpet Orange colour,, ga wani irin ƙaton tv plasma dake aje kan wani haɗaɗɗen glass,, falon dai ba'acika masa kayan ado ba amma kuma yaƙawatu sosai komai na falon me tsada ne,, direct wani ɗaki dake cikin falon aka wuce da Zahrah,, ɗakine me kyau wanda yaji royal furnitures milk colour, yayinda aka lailaye kan makeken gadon da wani irin zanin gado pink me kyawun gaske... Akan gado sukayimawa Zahrah masauƙi, Husnah dakanta ta haɗawa Zahrah ruwan wanka, koda tafito a bathroom ɗin hannayen Zahrah dake zaune kan gado ta kamo, haɗe da janta har zuwa cikin bathroom inda ta haɗa mata ruwan wanka...
Wani Turare ta bata tace inji Hajiya Shuwa, sannan kuma tayi mata bayanin yanda zatayi amfani dashi...
Zahrah tana fitowa a wanka Husnah ta shafa mata powder haɗe da lipstick, wani riga da sket na material marar nauyi Husnah ta bata tasanya, take tafito ɗas da'ita, a tsakiyar gado Husnah ta zaunar da Zahrah haɗe da rufe mata kanta da wani irin haɗaɗɗen mayafi me sheƙi da walwali, wasu turaruka masu ƙamshi Husnah takuma feshi jikin Zahrah dasu, take ɗakin yakuma ɗumamewa da ƙamshi,, sake matsowa kusa da Zahrah Husnah tayi cikin murya ƙasa ƙasa tace
"Dan Allah Zahrah karkice zaki ci gaba da wannan kukan naki, ki ɗan daure zuciyarki kinji ƙawata, kuma sannan kada ki hana Doctor haƙƙinsa, nasan zakiji tsoro amma please ki daure kinji ƙawata, banaje falo na amsa waya " Husnah taƙare maganar tana me miƙewa tsaye, idanu tayiwa Auntie Ladi suka fice a tare....
Tun Zahrah na jiran dawowan su Husnah hartasoma jin tsoro, domin kuwa gaba ɗaya gidan yaɗau shiru babu alaman akwai motsin wani mutum bayan ita,,, abun da Zahrah bata sani ba shine su Husnah wayo sukayi mata suka tafi suka barta, sunyi hakanne kuma saboda taƙaitamata wahalan kuka, domin sun san sunace mata zasu tafi zata ƙara fawan kukanta.....
Gyangyaɗine yasoma ɗaukarta, dan haka saita jingina bayanta ajikin saman gadon haɗe da lumshe idanunta da suketa tsiyayar hawaye...
A hankali yaturo ƙofar ɗakin bakinsa ɗauke da sallama, yasake shiga cikin wata farar shadda sabuwa ƙal sai sheƙi takeyi, ƙamshi ne kawai ke fita ajikinsa, daganinsa kasan yana cikin matsanancin farinciki,, ledan dake hanunsa ya aje, haɗe da takowa zuwa wajen datake zaune ta jingina bayanta da saman gado,, zama yayi akusa da'ita haɗe da ƙiran sunanta,, cikin murya me sanyi da kuma alamar bacci ta amasa masa,, ahankali yasanya hanunsa ya ɗan jaye mayafin dake kanta, hawaye yagani kwance akan fuskarta, hanunta yakamo haɗe da jawota jikinsa, hanu yasanya yashiga share mata hawayen dake kan fuskarta.
"Ki daina kuka kinji my wife, bacci zakiyi ne?" yatambayeta yana me ƙaremawa fuskarta kallo,, fuska ta kuma kwaɓewa, haɗe da kaɗa kanta, cike da shagwaɓa tace
"Ina Husnah?"
Ajiyar zuciya yasauƙe haɗe da sanya hanu yashafi lallausan gashinta dayasha gyara
"Husnah kuma Zahrah?" yatambayeta cike da mamaki..
"Eh tacemin zata amasa waya tana zuwa kuma haryanzu bata dawo ba!" yanzuma dai asangarce tayi maganar,, murmushi yayi mata haɗe da cewa
"Kada kidamu Husnah zata dawo gobe, taso muje kiyi alwala idan munyi salla saikici abinci ko"
Jitayi gabanta yayi wani irin faɗuwa amma kuma yazatayi da rayuwarta babu yanda ta'iya haka tabisa kamar jela harcikin bathroom,, saida yayi nasa alwalan kafun yabata waje itama ta ɗauro alwala,, tana fitowa daga cikin bathroom ɗin ya miƙo mata wata lufaya, a ɗaɗare tasanya lufayan daya bata, hanunta yakama suka hau kan sallaya, shi yajasu salla raka'a biyu, suna idarwa yayi musu addu'o'i haɗe da kama kanta itama yayi mata addu'a... A tsorace ta zauna akan gado haɗe da sake takure jikinta waje ɗaya...
Wani ɗan madaidaicin carpet Dr.Sadeeq yashimfuɗa haɗe da cika tsakiyar carpet ɗin da kayan ciye ciye, hanu ya miƙawa Zahrah alamar tataho garesa, cikin ɗari ɗari haka ta shiga takowa zuwa inda yake, hanunta yakamo yazaunar da'ita acikin jikinsa, hijabin dake jikinta yasoma ƙoƙarin cire mata, da sauri tasake ƙanƙame jikinta, ganin haka yasanya shi yin murmushi, ya fasa cire mata hijab ɗin,, juice ya zuba acikin kofi haɗe da kai kofin bakinta, babu musu tabuɗe bakinta ta kurɓi kaɗan, aje kofin yayi, haɗe da yago gasasshen nama yakai bakinta,, kanta tashiga girgizawa alaman bazataci ba.
"Kiyi haƙuri kici kinji Baby na, kaɗan zakici bamai yawa ba!" yafaɗi haka cike da lallami,,, shida kansa yake bata kazan, bata wani ci me yawa ba tace masa ta ƙoshi, dakansa yatattara wajen yakai kitchine,, yana dawowa ɗakin yasameta tsaye ajikin mirror tayi jigum,, fargabane yacika mata zuciya, wani irin tsoro ne taji ya ɗarsu acikin zuciyarta wanda bazata iya misaltashi ba,,
Kaitsaye drower ɗin dake cikin ɗakin ya nufa, wata doguwar rigan bacci sleeping dress yaciro haɗe da ƙarasowa gareta,, "Kije kiyi brush, wannan kayan kuma kisanya kizo kiyi bacci" hanunta na rawa haka ta amshi kayan sumi sumi ta wuce cikin bathroom, tana kammala brush tasoma cire kayan jikinta, warware rigan da Dr. yabata tayi tashiga ƙaremawa rigan kallo, doguwar rigace na bacci me net, amma kuma tana da faɗin wuya sannan kuma rigan irin me nuna jiki ɗinnan ne,, badon tasoba haka ta sanya rigan ajikinta, hmmm sam bazata iya fita da wannan rigan gaban Dr. Sadeeq ba, saboda gaba ɗaya rigan ta bayyana breast ɗinta, yayinda komai nata yafito fili, hijabin da tayi salla dashi ta ɗauka ta sanya,, a ɗaɗare ta fito daga cikin bathroom ɗin,, zaune tagansa akan gado tuni yasanja kaya zuwa farar jallabiya, murmushi kawai Dr.Sadeeq kejifanta dashi, cikin zolaya yace "Meye narufe jikin da hijabi?"
Ƙasa takumayi da kanta, yanzu kam ko ɗan shagwaɓan ma takasayi masa...
Sarai ya fuskanci halin da take ciki, "Zoki kwanta" yafaɗi haka yana meyi mata nuni da kan gadon dayake zaune,, kamar wacce ƙwai yafashewa haka Zahrah ta zo ta kwanta akan gadon, gaba ɗaya ta takure kanta waje ɗaya,,, miƙewa yayi daga zaunen dayake haɗe da kashe wutan ɗakin ya kunna na bacci, Zahrah najin takusan alamar yakusa zuwa kan gadon taji bugun zuciyarta ya tsananta, yayinda ƙirjinta yashiga wani irin luguden duka,, kwanciyarsa akan gadon yayi dai dai da kusan ɗaukewar numfashinta,,,, da ƙyar ta'iya ƙwato numfashinta, haɗi sa soma sauƙe ajiyar zuciya a ɓoye, kusan minti goma da hawansa kan gadon amma kuma taji baiyi mata wani abu ba, hakan yasa taɗanji zuciyarta tayi sanyi. Shiru tayi tana me jin sauƙar numfashinsa ahankali, wani irin mugun tausayinsa ne taji yaɗarsu acikin zuciyarta amma kuma ita bata da yanda zatayi, tunaninta ne ya katse alokacin da taji sauƙar hanunsa a bayanta,, ahankali ya juyota tadawo tana fuskantarsa,, kallon fuskarta yashigayi batare dayace da ita komai ba, kusan mintuna 4 yayi yana kallonta, cikin wata irin murya wanda batasanshi da ita ba yace
"kicire hijabin nan saboda kiji daɗin baccinki ko"
babu musu ta cire hijabin daga jikinta sai dai kuma bahaka ranta yaso ba, bargo yaja ya rufa musu hanunta yakamo ta cikin bargon yariƙe acikin nasa, "Ki kwantar da hankalinki, nasan kingaji, kiyi addu'a, kiyi bacci me daɗi" yafaɗi haka cikin muryar raɗa, hanunta yasake damƙewa acikin nasa hanun haɗe da lumshe idanunsa, zai bartane kawai saboda tausayinta dayake ji, amma bawai don baya sha'awarta ba, hasalima baita ɓa jin matsanancin sha'awarta irin nayau ba, hakan yafarune kuma saboda baitaɓa samun kusanci me tsanani da ita irin na yau ɗin ba, da wannan tunanin bacci ya ɗaukesa,,,, Zahrah ma dai baccin ne yaɗauketa batare data shiryawa hakan ba,, ƙarfe ɗaya na dare wani irin zazzafan zazzaɓi yarufe jikin Zahrah take tasoma karkarwa haƙwaranta har haɗewa suke, suna ba da wani sauti, hakan yafaru ne kuma sakamakon sanyin AC wanda yayi mata yawa, acikin baccinsa yakejin hucin numfashinta nafita da sauri, a hankali ya buɗe idanunsa ya sauƙesu akanta, da sauri yatashi ya zauna haɗe da kamo kafaɗunta,, "Zahrah!" yaƙira sunanta a hankali,, tanajinsa amma bazata iya amsa masa ba domin kuwa ba iya zazzaɓi ba hatta kanta jinsa take tamkar anɗaura mata gungumen ice, yamata nauyi Da sauri ya sauƙa akan gadon, AC'n yafara kashewa, kana ya buɗe wata ƴar drower maganin ciwon kai da zazzaɓi ya ɗauko haɗe da goran ruwa,, yana zuwa ya ta data zaune, ɓalle maganin yayi yasa mata abaki haɗi da kafa mata goran ruwa, babu musu ta haɗiye maganin, ajiye goran yayi haɗe da hawa kan gadon, hanunsa yasanya akan wuyanta, zafi yaji zau kamar wuta, ajiyar zuciya ya sauƙe, haɗe da cire rigan dake jikinsa, cikin bargon yakoma, haɗe da jawota kusa dashi, ahankali yasanya hanunsa a bayanta yayi ƙasa da zip ɗin doguwar rigan dake jikinta,, cike da nutsuwa ya cire mata rigan,, Zahrah tana jinsa amma kuma ayanzu babu wani abu da zata iyayi wanda zata kare kanta,, bashi kaɗaiba har ita kanta saida ta sauƙe wani irin ajiyar zuciya me ƙarfi alokacin da zallan fatar jikinsu suka samu haɗewa waje guda. lokaci ɗaya yaji tunaninsa yasoma sauyawa, nutsuwarsa tafara gushewa, haka kuma idanunsa sun soma rufewa,, haɗewar jikin Zahrah danasa jikin baƙaramin feeling me girman gaske ya sauƙar masa ba, tunda yake aduniyarsa yau shine karo na farko, da ya fara haɗa jikinsa dana mace haka, yasan yataɓa rungumar Zahrah amma ba runguma irin wannan ba,,,, Zahrah kuwa baƙaramin jin daɗin jikin nasa tayi ba, jitayi gaba ɗaya nutsuwa yasoma sauƙar mata, sake maƙalewa ajikinsa tayi haɗe da cusa kanta acikin faffaɗan ƙirjinsa har yazamana laɓɓan ta suna gogan fatar wuyansa,, jin yanda take ƙara shigewa jikinsa shiya ƙara taimakawa wajen ƙara masa wutar sha'awarta, hannayensa duka yasanya a bayanta yasake riƙeta gam, numfashi kawai yake fitarwa akai akai shi kaɗai yasan meyakeji acikin jikinsa,, yana cikin wannan irin yanayin yaji sauƙar numfashin Zahrah ahankali yana fita da'alama baccine yakuma ɗaukarta,,, haka yarungumeta ƙam acikin jikinsa yayinda yacusa kansa acikin gashin kanta yana shaƙan daddaɗan ƙamshinta dake ƙara rikitasa,, bakaɗan ba ya yi jarumta wajen ganin ya ƙyaleta baiyi mata komai ba, haƙiƙa bakowani irin namiji bane zai haɗa jiki da mace ace ya iya daure zuciyarsa baiyi mata komai ba, balle ma mace irin Zahrah wanda irinsu basu da yawa acikin mata,, da ƙyar bacci ya'iya ɗaukarsa.......
*(Kuyi Haƙuri idan kunga typing error ina busy ne)*
*18/January/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 92 to 93*
Ƙiran sallan asuban fari akan kunnensa,, a hankali ya ware idanunsa akanta, baccinta takeyi cikin kwanciyar hankali da'alama zazzaɓi da ciwon kan dake damunta sun jima da kama gabansu,, baisan lokacin da murmushi ya ƙwace masa ba, komai na Zahrah me kyau ne, har idan tana bacci kyawunta baya ɓuya, kallon zara zaran eye lashes ɗinta daya kwanto aɗan ƙasan idanunta yayi,, ahankali ya zare jikinsa daga nata jikin, cikin sanɗa yatura ƙofar bathroom yashige, gudun kada motsinsa ya tashe ta daga daddaɗan baccin da take,, saida yafarayin wanka kafun ya ɗauro alwala,, tsayawa yayi yana kallon yanda taketa fidda numfashi a hankali, badon sallah yazama dole akanta ba, to tabbas da babu abun da zai sanya ya tasheta a dai-dai wannan lokacin, zai bartane tasha baccinta ta ƙoshi,, ahankali yashiga girgiza ƙafanta haɗe da ɗan ƙiran sunanta, cikin murya ƙasa ƙasa... Da yake bata da nauyin bacci, ƙira biyu yayi mata ta buɗe idanunta,, da sauri ta sake jawo bargo ta rufe jikinta, kana tasoma raba idanu, murmushi yakumayi mata haɗe da sanya hanu ya shafi gefen kumatunta.
"Kitashi kiyi sallah, ni na wuce masallaci"
Bata iya amsa masa ba haryafice daga cikin ɗakin,, kallon kanta tashiga yi gaba ɗaya gashinta ya watse yayi buji buji dashi, da'alama dai tasha juyi acikin bacci,,, tana shiga bathroom ta haɗawa kanta ruwa me ɗan ɗumi, wanka tayi itama kana ta ɗauro alwala (🤔Yadai dukanku wanka sai kace 🙊)....
Tana fitowa daga bathroom ɗin ta zura wata jan doguwar riga marar nauyi, haɗe da zura hijab ajikinta, kan sallaya tahau haɗe da dai-dai ta tsayuwarta...... Koda ta'idar da sallan saida tayi azkar kafun ta miƙe daga kan sallayan,, harta zauna akan gado, maganganun Hajiya Shuwa suka faɗo mata arai inda take ce mata _"Kada ta sake ƙamshi yabar jikinta, sannan kuma idan tayi sallan asuba kullum tana shafa turare aduk wani lungu da saƙo na jikinta"_ batasan mene manufar hakan ba, amma dai ta ɗau maganar kuma zatayi aiki dashi. Gaban mirror tanufa haɗe da ɗaukan ƴar ƙaramar hand bag ɗinta dake aje kan mirror'n wani ɗan kwalban body spray ta ciro daga cikin jakar, haɗe da fesawa ajikinta, daga kan wuyanta har zuwa bayan kunnenta, sosai turaren yake da ƙamshi, take ɗakin ya gauraye da ƙamshin turaren,, tana shirin maida turaren cikin jakarta, Dr.Sadeeq yaturo ƙofar yashigo bakinsa ɗauke da sallama,, cikin murya me sanyi ta amsa masa sallaman nasa,, direct inda take tsaye ya nufo, batayi tsammani ba saiji tayi ya buɗe hannuwansa ya rungumeta ta baya haɗe da ɗaura kansa akan wuyanta,,,, idanunsa ya lumshe haɗe da buɗe hanci ya shaƙi daddaɗan ƙamshin dake fita ajikinta cikin wata irin murya yace
"Good morning madam!"
Kunyan sane yakamata, saikawai tayi ƙasa da kanta haɗe da cewa
"Ina kwana"
"Lafiya ƙalau, yajikinki?" ya amsa mata yana me cusa kansa acikin wuyanta..
"Da sauƙi"
Ta mayarmai da amsa cikin ƙasa da murya...
"Ƙamshinki yamin daɗi sosai, kinyi sallah ne?"
Kanta ta ƙaɗa masa alamar "Eh" hanunta yakama yajata zuwa kan gado... Zama yayi kana ya jawota jikinsa,, ɗago fuskarta yayi haɗe da jefa idanunsa cikin nata. Sunanta yaƙira cikin wata irin murya me ɗauke da nutsuwa..
Kanta ta ɗago ta kallesa, ganin idanunsa tsaye cak akanta yasanya tayi saurin meda kanta ƙasa..
"Meyasa kikejin kunya na sosai ne?"
Yayi mata tambayar da bata tsammata ba,, jijjiga kanta tayi alaman
"babu"
Sake matseta acikin jikinsa yayi haɗe da kwantar da kansa akan kafaɗanta.
"Mallakarki danayi wata babban nasara ce dana samu acikin rayuwata Zahrah, inasonki ne da duka zuciyata, dakuma iya gaskiyata, banda niyar cutar dake acikin rayuwar zaman aurenmu, abu ɗaya nakeso kiyi mini shine, ki rage yawan tunani da kuma kukan nan dakikeyi, inajin tsoro kada su haifarmiki da wata cuta, yanzu nasan kina da buƙatar hutu ko, ki kwanta ki huta, kafun anjima sai kiyi break fast"
Miƙewa tayi daga jikinsa haɗe da hayewa kan gadon ta kwanta, amma kuma bata ɗauke idanunta akansa ba, bayan kamar mintuna biyar da kwanciyarta shima yatashi daga zaunen da yake, kan gadon ya hau, har Zahrah taji bugun zuciyarta yasoma ƙaruwa, sai kuma taga ya lulluɓe mata duka jikinta da blanket, agefe da ita ya kwanta haɗe da juya mata baya... Shiru ɗakin ya ɗauka babu abun dake tashi sai sautin fitar numfashinsu,,, bayansa ta kafe da idanu, yayinda a cikin zuciyarta take wani tunani na daban, haƙiƙa duk duniya babu wani namiji daya dace yazamo miji agareta sama da Dr.Sadeeq, ya cancanta ƙwarai, shi mutum ne wanda zaiyi wahala asamu kamarsa, Dr.Sadeeq kuwa lumshe idanunsa yayi bawai don bacci ya ɗauke sa ba,, shima wani tunanin yakeyi daban, baisan meyasa aduk sanda idanunsa zasuyi masa tozali da Zahrah yakejin matsanancin sha'awarta ba, wanda ada kuma ba haka abun yake ba, bazaice da bayajin sha'awarta ba, yanaji sai dai kuma bakamar wanda yakeji yanzu ba, jiya bakaɗan ba ya'iya daure zuciyarsa, amma daba haka ba tabbas da baisan wani irin aika aika zaiyi mata ba, a hankali yaji idanunsa sun soma rufewa da'alama dai shima bacci bai ishesa ba, ae dole ma jiya sunsha gajiya sosai,, cikin mintuna ƙalilan bacci ya ɗauki ma'auratan biyu, yayinda kowanne daga cikinsu da irin samfurin tunanin dake cikin zuciyarsa....
***
10:00 am dai-dai ta buɗe idanunta, haɗe da waresu akan haɗaɗɗen zanen POP'n da ya cika saman ɗakin, kallonta ta mayar ga inda take tsammanin ganinsa, amma sai dai taga wajen wayam babu shi babu alamarsa. Da sauri ta tashi zaune haɗe da maida kallonta ga wani ɗan madaidaicin agogon bangon dake saƙale jikin ginin ɗakin.
"ƙarfe 10 nakai ina bacci?"
ta tambayi kanta cikin yanayi naɗan mamaki.. A hankali tazuro ƙafafunta ƙasa, haɗe da miƙewa tsaye, ɗakalallen cikinta daya soma mata kukan yunwa ta shafa, haɗi da ɗan yamutsa fuskarta, direct ƙofar bathromm ta nufa, ɗan tsayawa tayi ta kasa kunnenta ajikin ƙofar, koda zataji ƙaran ruwa, amma saitaji shiru da'alama dai bakowa acikin bathroom ɗin, murɗa handle ɗin ƙofar tayi tashige ciki,, ruwan wanka ta haɗa yayinda ta cika turaren ƙamshi acikin ruwan, wankanta tayi cike da nutsuwa... Sanye da wani ɗan madaidaicin towel pink colour ajikinta tafito daga cikin bathroom ɗin, hatta gashin kanta ajiƙe yaƙe, still ƙaramin towel ne kuma riƙe ahanunta tana goge gashin kanta dayake ajiƙe,, daidai lokacin Dr.Sadeeq yaturo ƙofar ahankali yashigo, suman tsaye yayi ajikin ƙofar yana me ƙare mata kallo daga sama har ƙasanta, yayinda ita kuwa batasan ma da zuwansa ba, kanta kawai take aikin gogewa, saboda bataji motsin buɗewar ƙofar ba, shikuwa dama yabuɗe ƙofar ne ahankali gudun kada ya tasheta a baccin daya barta tanayi,, wani yawu ya haɗiye, haɗe da jan ƙafansa a hankali yafice daga cikin ɗakin batare daya bari ta ganshi ba,, yana fita yajingina bayansa da ƙofar haɗe da sauƙe wani irin ƙaton ajiyar zuciya,, lumshe idanunsa yayi haɗe da sanya hanunsa acikin tulin sumar kansa yashiga shafawa a hankali,, ashe haɗuwar Zahrah yawuce yanda yake zato yake kuma tunani, wannan wace irin haɗaɗɗiyar surace Zahrah'n sa ta mallaka,, lallai Zahrah mace ce cikakkiya tagaban kwatance,, da ƙyar ya'iya jan ƙafansa ya koma cikin falo, kwanciya yayi akan kujera haɗe da lumshe idanunsa da suka sauya launi lokaci guda...
Zahrah kuwa tana gama goge gashin nata tayi amfani da hand dryer wajen busar dashi mintuna kaɗan gashin yabushe tashafa masa mai,,, wani lotion me ƙamshi ta shafa ajikinta haɗe da murzawa fuskarta hoda da kuma kwalli, light pink lipstick tagoga akan leɓenta, take fuskarta ta tasake yin kyau,, gaban makeken drower'n dake kafe ajikin bangon ɗakin taƙarasa haɗe da buɗewa, kayane jere reras acikin drower'n kala kala sai wanda ranka yaso zaka saka, wata jar atamfa taciro wacce taji ɗinkin pencil gown,, tana sanya doguwar rigan yayi mata kyau haɗe dayi mata ɗas ajikinta, daga kan guiwanta harzuwa ƙafarta atsage yake ta bayan rigan, tanason atamfar sosai saboda tana ɗaya daga cikin kayan da Maman Husnah ta bata, Husnah ce kuma takai akayi mata irin wannan ɗinkin duk da kuwa irin tsadar da atamfar take dashi, kallon kanta tayi acikin madubi, murmushi tasakarwa kanta saboda ita kanta ta yaba da yanda rigan tayi mata kyau ajiki, wani ɗan madaidaicin vail me kalan ja ta ɗauka haɗe da rufe jikinta, duk da kuwa cewa kayan yana da ɗan kwali, sai dai bazata iya tafiya daga ita sai wannan rigan agaban Doctor ba saboda sosai hips ɗinta suka bayyana, ga shi breast ɗinta sun bayyana kansu ta saman rigar kasancewar wuyan rigan yana da ɗan faɗi. Da turaruka masu daɗi ta feshe jikinta... A hankali ta buɗe murfin ƙofar ɗakin tafito, ɗan tsayawa tayi tana kallonsa,, kwance yake akan kujera yayinda idanunsa ke a lumshe, yasha adonsa cikin wata bugaggiyar shadda blue colour. Murmushi tayi domin kuwa yayi mata kyau, sosai kuma hasken fatarsa yasake bayyana acikin blue ɗin kayan. A hankali tashiga takawa har zuwa tsakiyar falon, ƙarewa falon kallo tashiga yi, ita dai haryanzu bata gamsu da cewa wai nan ɗin falon ta bane, koda wasa ma bata taɓa tunanin zata shiga cikin daula irin wannan ba,, bata ankara ba saiji tayi anriƙe mata hanu, da dauri ta juyo don batayi zaton idonsa biyu ba,, Murmushi yasakar mata haɗe da cewa,
"yaushe kika tashi?" yayi tambayar kamar bashi yaganta ɗazu ba..
Zama tayi akan kujera haɗe da cewa " banjima da tashi ba"
Tashi yayi daga kan kujeran haɗe da kama hanunta, kaitsaye haɗaɗɗen darny area'n dake cikin falon yanufa da'ita, jawo kujera ɗaya yayi daga cikin kujeru huɗu dasuka ke waye wani babban table, zaunar da'ita yayi haɗe da buɗe wani babban food flask, plate ya ɗauka yazu ba mata soyayyen dankalin turawa'n dake cikin kulan (Chips) wata food flask ɗin yasake jawowa pepper chicken ne dayasha albasa, shima zuba mata yayi haɗe da haɗa tea acikin wani cup, turo mata duka plates ɗin dakuma cup ɗin tea ɗin yayi gabanta,, saurin ɗago kanta tayi ta kallesa, kansa ya jinjina mata alamar koma me take tunani hakane, take ta shagwaɓe fuska haɗe da cewa "Bazan iya cinye duka wannan abincin ba yamin yawa"
"Bakomai kici sosai, nasan kinajin yunwa" yafaɗi haka yana me ƙoƙarin barin wajen.
"Kai kuma fa?" batare da ta shiryawa fitowar tambayarba, saikuma bakinta yayi saurinfurtawa,, tsayawa yayi da tafiyar haɗe da juyowa, murmushi yayi mata haɗe da cewa "Ni bayanzu zanci ba" harya fice daga cikin falon bata ɗauke idanunta daga kansa ba,, ajiyar zuciya ta sauƙe haɗe da ɗaukan fork tasoma cakan chips ɗin tana kaiwa bakinta, dama yunwa takeji sosai,, sosai taci chips ɗin saidai tea ɗin sama sama tasha shi, naman kuwa ko taɓa shi batayi ba, domin ita gaba ɗaya naman kaza baiwani dameta ba, tafison gasashshen naman sa, fiye da na kaza, sai da taji cikinta yayi haniƙan kafun ta kimtsa wajen haɗe da miƙewa takoma cikin falon,, haryanzu dai idanunta basu ƙoshi da ƙarewa falon kallo ba, rayuwa kenan wai yau ita Zahrah ce zaune acikin wannan katafaren gida dasunan gidan aurenta, ita da ko gado bata dashi akan zallan ƴar katifa take kwana sai gata yau ta kwana akan haɗaɗɗen gado harda lallausan bargo da ta rufa dashi,, a hankali ya turo ƙofar falon yashigo, wayarsace riƙe a hanunsa yana latsawa,, gaf da'ita ya zauna har kafaɗunsu suna gogan na juna, hanunsa ya sanya ya shafi ɗa kalallen cikinta, "Wannan ɗan ƙaramin cikin baiƙoshi ba"
Murmushi tayi masa haɗe da waro idanunta "Dan Allah kayi haƙuri wallahi na ƙoshi" tafaɗi haka tana me ɗauke hanunsa daga kan cikinta.. Kallonta yashigayi yana me karantar yanayinta yayinda ita kuma tayi ƙasa da kanta, batason haɗa idanu dashi kwata kwata, "taso muje" yafaɗi haka yana me miƙewa tsaye, babu musu ta miƙe, hanunta ya kama suka nufi wata ƙofa dake cikin falon, key ya sanya ajikin ƙofar ya murɗa, tura ƙofar ɗakin yayi, still hanunta na riƙe acikin nasa hanun suka kutsa cikin falo'n, falone ma dai-dai ci wanda aka kewaye tsakiyansa, da wasu kujeru dark purple masu kyau, yayinda tsakiyar falon kuwa aka cike sa da wani ɗan madaidaicin chanies carpet dark and light purple colour, wasu labulaye masu kyau kalan light purpule su suka ƙawata jikin ƙofa dakuma windown falon, wani ɗan ƙaramin plasma ne maƙale ajikin bangon falon, su kenan iya abun dake cikin falon amma kuma duk da haka falon yayi kyau, kasancewar kalan kujeru da labulayen kalane me ɗaukar hankali, ga kujerun sunsha pillow ƴan ma dai-dai ta gwanin ban sha'awa, yana riƙe da hanunta suka kuma shiga cikin wani ɗaki dake cikin falon,, gadone me kyau irin na zamani da drower'nsa me ɗauke da murafe shida, sai kuma su dressing mirror dakuma abun aje takalma da jaka,, kayan furnitures ɗin bawasu masu tsada bane daga kujerun har gadon bazasu wuce dubu ɗari huɗu ba, amma kuma anyi kayan da kyau da kuma inganci,, kallon sa Zahrah tayi alamar tanason ƙarin bayani,, murmushi yasakar mata haɗe da sa hanu ya shafa kumatunta, yace da'ita
"Kayan ɗakin da Baffa yayi miki ne"
Daɗi da farinciki ne suka cika zuciyar Zahrah take tacigaba da wurga idanunta tana kallon kayan, Allah sarki Baffa ashe haka yayi mata ƙoƙari batasani ba, lallai Baffa yafaranta ranta sosai, bata taɓa tunanin zata samu kaya haka ba, ashe dai Baffa yanasonta yana kuma ƙaunar fitar da'ita kunya, lallai wannan kaya sunfiye mata komai, saboda koba komai zata tsallakewa gorin wasu mutanen, wani irin tausayin Baffan nata ne taji ya sake ɗarsuwa aranta,, duk da cewa shiba mawadaci bane amma yayi ƙoƙari ya wadata ta da kayan ɗaki masu kyau dai dai da me rufin asiri, babu abun da zatace da baffanta sai godiya,, kan gadon taje ta zauna tana murmushin jin daɗi, sai taji tafi ƙaunar ɗakin ma fiye da wanda aka kaita daga farko, duk daɗin kyauta dai baikai ace da kuɗinka kacire ka saya ba.
"Yanaga kin wani zauna madam? taso muje nunamiki kawai nayi, bawai nace anan zaki zauna ba" Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana me miƙa mata hanunsa alamar takama sutafi,,
Shagwaɓe fuska Zahrah tayi haɗe da kwantar dakanta gefe
"Nidai nafison nan please kabarni anan!" taƙare maganar cike da zallan shagwaɓa..
Takowa yayi yazo gaf da'ita haɗe da sanya hanunsa ya ɗago kafaɗunta.
"Nan ɗakin hutawan kine, can kuma ɗakin aurenki ne ɗakin dana zaɓa mana ni dake domin muyi rayuwar auren mu, kodai baki yaba da zaɓin nawa bane? kokuma baki amshi kyautar danayi miki bane?"
Ɗara ɗaran idanunta ta ɗago ta sauƙesu akan nasa idanun, kanta ta girgiza cikin sanyin murya tace " Ba haka nake nufi ba, kuma nayarda da duk inda kazaɓamin zanyi rayuwa aciki, kayi haƙuri idan maganata ta ɓata maka rai ban....."
"Shiiiiii" ya katseta ta hanyar ɗaura hanunsa akan laɓɓanta, jawota jikinsa yayi , haɗe da sanya yatsarsa yashiga zagaye ɗan ƙaramin bakinta,, ƙasa tayi da'idanunta domin kuwa bazata iya jure kallon cikin idanunsa ba, sake matso da fuskarsa yayi daf da tata har numfashinsu na'iya gauraya waje guda, yayinda dogon hancinsa ke gogan nata hancin, atare suka lumshe idanunsu, ahankali laɓɓansa suka sauƙa akan nata laɓɓan, baikai ga soma yin kissing ɗinta ba ƙaran wayarsa ta karaɗe cikin kunnuwansu, da sauri ya sake ta,haɗe da sanya hanu acikin aljihunsa ya ciro wayarsa dake ta faman ƙara, katse ƙiran yayi haɗe da kashe wayar baki ɗayanta ya kuma maidata cikin aljihun rigansa.
Hannayenta dake cikin nasa hanun ya murza haɗe da ɗanyin ƙasa da murya "Kibani aron 1 hour inaso in ɗan fita"
Batasan lokacin da ta ɗago kanta ta kallesa ba, mamaki ya bata wai ta basa aron 1 hour shida ƙafarsa ae bazata ɗaure saba,
Baijirayi abun da zatace ba yakama hanunta suka fice daga cikin ɗakin, direct asalin falonsu suka dawo, matsawa kusa da'ita yayi ya manna mata kiss akan goshinta, haɗe da cewa "Sainadawo" adawo lapia tayi masa cike da kunyar sunbatar da yayi mata agoshinta,, tanajin tashin motarsa ta sauƙe ajiyar zuciya haɗe da zama akan kujera tamaida hankalinta ga tv, a zuciyarta kuwa hamdala take da Allah yasa bai sumbaceta ɗazu ba, itakam matuƙar kunyarsa takeji, sosai yakeyi mata kwarjini acikin idanunta.....
***
*GERMANY*
Tunda suka iso cikin ƙasar suka kuma sauƙa ababban asibitin dake cikin birnin Germany ɗin Zaid bai buɗe idanunsa ba, duk da kuwa irin kulawan da ƙwararrun likitotin asibiti'n suka basa, bawai baya cikin hayyacinsa bane, sarai yana a cikin hayyacinsa, ƙunci da kuma tarin damuwa me tsanani ne suka hanasa buɗe idanunsa, baison ya buɗe idanunsa kunnuwansa su jiye masa labarin cewa anɗaura auren Zahrah, baya buƙatar yin tozali da fuskar kowa acikin duniyar nan idan ba fuskar Zahrah ba,, yagama yarda da hukuncin da zuciyarsa ta yanke masa, lallai kwanciyarsa haka baida wani amfani, yakamata ne yatashi yayi yaƙi don samo soyayyar Zahrah, idan har bai manta da date ɗin daya gani ajikin katin auren ba, to jiya ne ɗaurin aurenta, wasu irin hawaye masu zafin gaske ne suka silalo daga cikin idanunsa haɗe da gangarowa tagefen kumatunsa,, a hankali ya ware idanunsa da suka jima da rikiɗewa suka zama jajur dasu, baya tunanin zaisake samun farinciki acikin rayuwarsa matuƙar yarasa abar ƙaunarsa Zahrah, tashi yayi zaune haɗe da rumtse idanunsa, ƙuna yakeji acikin ƙirjinsa sai dai kuma zafin wannan ƙunan baikai zafin ƙunan da soyayyar Zahrah keyi masa azuciyarsa ba,,, Alhaji Ma'aruf dake tsaye a wajen ɗakin da Zaid ɗin ke kwance, ta cikin makeken glass ɗin daya zamewa ɗakin window ya hango Zaid ya tashi zaune, da sauri yaje ya ƙira Doctor domin kuwa tunda suka zo Zaid ɗin bai motsaba sai yanzu,, ƙa'idansu ne idan zasu duba marar lafiya babu wani me shiga kansu harsai sun ga babu wani matsala sannan zasu bar ƴan uwansa suje kansa,, hakan yasa dole Alhaji Ma'aruf ya dakata daga waje likitan shi kaɗai ya shiga.. Bayan kamar wasu mintuna likitan yafito yabawa Alhaji Ma'aruf daman ganin Zaid ɗin, ae ba'iya Alhaji Ma'aruf kaɗai ba hadda Mum suka rankaya zuwa cikin ɗakin,, har gabansa dukansu suka ƙarasa, hanu Alhaji Ma'aruf ya ɗaura akan kafaɗan Zaid haɗe da cewa "Ya ƙarfin jikin naka?"
Bai amsa musu ba saima kallonsu daya shiga yi kamar wani wawa...
"Ina Zahrah?" shine abun daya iya fitowa daga cikin bakinsa kawai, saboda shine abun dake cikin zuciyarsa..
Kallon Kallo Alhaji Ma'aruf da Mum suka shiga yiwa juna, sukam dai basuda wani amsa da za su bashi domin kuwa sarai labarin Auren Zahrah ya isa ga kunnensu, yanzu haka itaɗin matar wani ce, babu amfanin ɗago zancenta...
Alhaji Ma'aruf ne yayi ta maza haɗe da sauƙe ajiyar zuciya cike da lallashi yakuma dafa kafaɗun ɗan nasa " Yanzu ba lokacin damuwa bane Zaid, bakuma lokacin daza ka sa kanka acikin ƙunci bane, kabar maganan Zahrah, yanzu samun lafiyarka yafi komai a wajen mu, idan kasamu lafiya sai ayi abun daya dace amma maganar Zahrah abarshi" Alhaji Ma'aruf yaƙare maganar cikin kwantar da murya.
Laɓɓansa ya cije haɗe da girgiza kansa
" Bazan taɓa samun nutsuwa da salama ba Dad har sai Zahrah tazamo tawa, Inasonta Dad, so ba irin na wasa ba, samunta ayanzu yafiyemin komai, taɓa kaji Dad, zuciyata takusa bugawa akan soyayyarta, ba irin bugawan da kasani ba Dad, Bugawa zatayi tayanda bazata sake aiki ba har abada kuwa!" Zaid yaƙare maganar yana me ɗaura hanun Dad ɗinsa akan ƙirjinsa dai dai saitin da zuciyarsa take....
"Baka da hankaline Zaid? ka kosan mekake cewa? wani irin mahaukaciyar soyayya ce wannan? anya kuwa Zaid baka zautu akan wannan banzar soyayyarba?" Mum ta tambayesa cikin yanayi na ɓacin rai, sosai abun nasa yanzu yake sosa mata rai..
"Mutuwa zanyi Mum akan Zahrah zan iyayin komai wallahi dagaske ni mahaukacine akan soyayyarta inason...."
"Kanasonta ko, shikenan tunda baka gujewa saɓon Allah saikaci gaba da sonta idan zaka sameta, domin kuwa yanzu ta riga da tayi maka nisa, saboda matar wani ce!" Mum tafaɗi haka ta hanyar katsesa daga maganar dayake...
Tamkar sauƙar guduma aka haka yaji sauƙan maganganun mahaifiyartasa acikin kunnuwansa,, kallonsa yamayar ga Dad ɗinsa,, kai Alhaji Ma'aruf ya jinjina masa alamar kalaman mahaifiyarsa gaskiya ne..
"Zahrah zata dawo gareka idan har Allah ya rubuta cewa itaɗin matarkace, amma yanzu kacireta acikin zuciyarka, saboda ahalin yanzu Zahrah tajima da zama mallakin wani, kasani kuma tunata da kuma cigaba da sonta zai iya jefaka cikin halaka" Dad yafaɗi haka ga ɗannasa cikin tsananin tausayawa...
Dafe ƙirjinsa yayi da sauri haɗe da cije laɓɓansa, da ƙyar ya'iya motsa laɓɓansa aniyarsa yafurta wata kalma, sai kuma labari yasha banban, tarine ya sarƙesa, take jini yasoma fitowa daga cikin bakinsa, ƙoƙarin riƙesa Dad yasomayi amma kuma kafun yakai ga riƙesa tuni yafaɗo daga kan gadon, Mum kuwa tuni tafice aɗakin taje taƙira Doctor's,, kafun Doctors ɗinma suzo tuni Zaid yayi mugun fita acikin hayyacinsa, gaba ɗaya jini ya ɓata gaban rigar dake jikinsa, idanunsa ne suka juye wani irin numfashi yaja me sauti, saikuma komai na jikinsa yasake alokaci guda, daidai lokacin Likitoti suka ƙaraso cikin ɗakin .... Taimakon gaggawa suka shiga bashi don ceto rayuwarsa cikin ikon Allah kuwa suka samu numfashinsa ya dai-dai ta, allurai suka narka masa wanda zasu sanyasa bacci...
Babban likitan dake kula da al'amuran Zaid ɗinne, ya rufe Dad da faɗa akan wai saboda me yasa aka faɗawa Zaid ɗin maganar da zata tada masa da hankali, haƙuri Dad yashiga bawa Doctor ɗin, sharuɗa masu tsauri Doctor ya shumfuɗa musu, akan cewa lallai dole babu wanda zai sake ganawa da Zaid ɗin harsai bayan kwana uku, sannan kuma koda sunkoma gida yazama dole akiyaye shiga damuwa dakuma ɓacin ransa, saboda yanzu zuciyarsa tazama kamar wani ɗanyen ƙwai sai anayi ana lallaɓata, zuwa yanzu abu kaɗan ne zai sanya ta buga, wanda hakan kuwa dai dai yake da rasa rayuwar Zaid ɗin baki ɗaya
***
Bayan awanni 4
Shikaɗai yasan irin raɗaɗi dakuma ciwon dake kwance acikin zuciyarsa, hawayene suke ta fita daga cikin idanunsa suna gangara akan ƙuncinsa,, "Da gaskene Zahrah'n sa tayi aure? me yasa Zahrah zatayi masa haka? Bazai taɓa iya jurwa ba, lallai koda Zahrah tayi aure bazai taɓa daina sonta ba, kuma koda duka mutanen duniya zasu taru akansa bazai sanja ƙudurin dake zuciyarsa na auren Zahrah ba, zaiyi duk wani abu wanda yasan Zahrah zata dawo garesa koda kuwa hakan zaijawo sanadiyar rasa rayuka ne, ZAHRAH kawai yasani kuma itace cikar burinsa"..... (😳 karya kasheni nima🏃♀🏃♀)
*(Gobe Birthday na💃💃 zan baku updated insha Allah💃💃gobe akwai show agidan Doctor 🙊 )*
*21/January/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 94 to 95*
*NIGERIA*
Tunda Doctor yafita baisake dawowa cikin gidanba harkuwa Zahrah ta ƙaraci zamanta acikin falon ta koma uwar ɗaka, sai dai kuma yayi mata waya yasanar mata cewa yana gidan Hajiyarsa wani uzuri ne ya riƙesa...
***
Idar da sallan isha ɗinta kenan ta miƙe haɗe da ƙarasawa gaban dressing mirror, lotion ɗinta me ƙamshi ta shafa ajikinta, powder kawai ta shafa akan fuskarta sai kuma man leɓe... Wata rubber pencil gown maroon colour ta sanya ajikinta, rigace irin marar nauyi ɗinnan sannan kuma an cika gabanta da fararen duwatsu wato (stones) wani maroon ɗin mayafi me ɗan kauri ta ɗauka haɗe da kafa ɗaurin ɗan kwalin nan na turban akanta, sosai tayi kyau saikace wata balarabiya, zama tayi akan gado haɗe da jawo wayarta, ajiyar zuciya ta sauƙe, har cikin ranta tana mamaki ƙwarai na rashin dawowan Dr.Sadeeq, tun safe daya fita haryanzu baidawo ba,, tashi tayi ta rage gudun ac'n dake cikin ɗakin, haɗe da ɗaukar wayarta tafice zuwa falo, hankalinta gaba ɗaya ta maida kan tashan MBC Bollywood da suke haska film ɗin nan me suna SANAM TERI KASAM bata taɓa kallon film ɗin ba amma kuma tana da waƙoƙin film ɗin acikin wayarta saboda sosai waƙoƙin sukeyi mata daɗi,, ta shagala a kallon film ɗin har idanunta sunfara kawo ƙwalla saboda tausayi, jitayi ansanya hanu anrufe idanunta , a razane ta ƙwalla ƙara domin kuwa sam bataji motsin shigowan mutum cikin falon ba, da sauri tature wanda yarufe mata idanun gefe haɗe da tashi tsaye,, ganin cewa shine yasanya tashiga sauƙe ajiyar zuciya akai akai,, murmushi yasakamar mata haɗe da cewa
"Matsoraciya"
Zama yayi akan kujera,, itama zama tayi tana me da numfashi sosai yatsorata ta donkuwa bata tsammata cewa shi bane sam ta manta ma da cewa babu mayafi ajikinta... Kafeta da'idanunsa yayi yana me ƙarewa kwalliyartata kallo,, sai alokacin ta ankara da irin kallon dayake jifanta dashi.
"Sannu da dawowa!" tafaɗi haka cikin sassanyar murya.
"Yauwa, kimin afuwa najima da yawa" yafaɗi haka yana me sanya hanunsa ya kama kunnensa alamar yana neman afuwa, murmushi kawai tayi masa haɗe dayin ƙasa dakanta...
Miƙewa tsaye yayi haɗe da cewa "Bari naje nayi wanka, akwai kayan fruit acikin fridge please kiɗan yanka min kafun na fito"
"To" kawai tace dashi haɗe da tashi tanufi wajen fridge ɗin shikuma direct ya wuce ɗaki donyin wanka...
Tana kammala yanka fruit ɗin ta ɗauko wani plate me kyau tarufe yankakken fruit ɗin, kan kujera ta koma ta zauna haɗe da sake maida hankalinta ga tv.. Sanye da tree guater jeans ajikinsa haɗi da wata farar t-shirt ya fito, ƙamshi kawai yake fitarwa, satan kallonsa Zahrah tayi haɗe da ɗan sakin murmushi, bata taɓa ganinsa acikin irin wannan shigar ba amma kuma yayi mata kyau sosai.. Akan lallausan carpet ɗin dake malale tsakiyar falon ya zauna haɗe da tanƙwashe ƙafafunsa, alama yayi mata da hanunsa cewa ta miƙo masa fruit ɗin, ɗaukan plate ɗin tayi taƙarasa gabansa, durƙusawa tayi har ƙasa kana ta aje plate ɗin,, "Miƙomin wancan ledan" yafaɗi haka yana meyi mata nuni da leda wanda shiya shigo dashi sam ita batama lura ba,, cike da nutsuwa taɗauko ledan kamar yanda ya umarceta ɗan duƙawa tayi haɗe da miƙa masa ledan,, amaimakon yakarɓi ledan sai taga ya jawota jikinsa, zaunar da ita yayi acikin jikinsa haɗe da sanya hanu ya zame ɗaurin turban ɗin dake kanta, take lallausan gashinta ya zubo harzuwa kan bayanta, kansa ya cusa acikin gashin nata yana me shaƙan daddaɗan ƙamshin dake tashi ajikin gashin nata,, "Kiyi mini afuwa my princess, banƙi dawowa haka kawai ba!" yafaɗi haka yana me ƙara matseta acikin jikinsa.
"Ni bakayi mini laifi ba sam sam, nasan ae bazaka ƙi dawowa haka kawai ba" tafaɗi haka cikin zazzaƙan muryarta..
"Yauwa my wife nasanki dama kina da haƙuri, natsaya a wajen ƴar uwarki Salima ne, ina fatan banyi laifi ba?"
Da sauri tajuyo da kanta tana kallonsa, "Salima kuma? bakace tafasa aurenka ba" tatambayeshi fuskarta ɗauke da tsananin mamakin jin abundayace..
Dariya yayi ganin yanda tawani zaro idanu kishi ya bayyana akan fuskarta ƙarara daga ambatan sunan Salima.
"Wasa fa nake miki Madam, miye na wani tsorita haka" yafaɗi haka yana me ƙarewa kyakkyawar fuskarta kallo..
Ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya ta sauƙe haɗe da ɓata fuska, ta juya da kanta batace dashi komai ba,, sarai ya lura taji haushi,,, yankakken apple ya ɗauka haɗe da kaiwa kusa da bakinta.. ƙin buɗe bakinta tayi saima daɗa kauda kanta da takeyi jefa apple ɗin yayi cikin bakinsa, haɗe da sanya hanu ya juyo da kanta yazama tana fuskantarsa...
"Fushi kike da mijinki? kiyi haƙuri banfaɗi haka don ranki ya ɓaci ba, wasa nake miki kiyi mini murmushi kinji Zahrah na!"
Hakanan taji zuciyarta tayi sanyi harbatasan sanda tasaki murmushi ba.. Yankakken apple yakuma ɗaukowa yakai bakinta babu musu ta buɗe bakinta yasanya mata... Tana zaune acikin jikinsa haka yaciyar da'ita domin kuwa atare sukasha fruit ɗin haɗe da ɗaura fresh milk akai.. Yana nan azaune ta tattare wajen takai kitchine haɗe da dawowa, miƙewa tsaye yayi haɗe da ƙarasawa gaban tv wanda yaketa ɓaɓatu shikaɗai ya kashe, kallonta yayi kamar zaiyi magana saikuma ya fasa, wutan falon ya kashe kana yakama hanunta suka nufi ɗaki, hmmm tun ɗazu bata ji tsoro ba sai yanzu da ta gansu sun hallara acikin bedroom, janta yayi har cikin bathroom sukayi brush... Da kansa yaciro wani ƴar fingilar rigan bacci wanda take shara shara kamar rariyan tata sai dai kuma tana da ado ata wajen wuyan.. Ganin yanufota kai tsaye ne yasanya tayi saurin saddakanta ƙasa, zuciyarta kuwa luguden duka tashiga yi mata, kamar anka mata tana sata, harga Allah ita tsoronshi take Allah yasa yauma karyayi mata komai.. Tunaninta ne ya katse sakamakon sauƙar hanunsa da taji abayanta, matsowa yayi gaf da'ita harsuna iya jiyo hucin numfashin junansu,, ahankali yayi ƙasa da zip ɗin rigar nata, lokaci guda yasanya hanu ya soma zame rigar daga kafaɗunta, rumtse idanunta tayi ƙam, haɗe da takure jikinta waje ɗaya, bazata iya hanasa ba, amma kuma dazai barta yace ta cire rigan da kanta da hakan yafiye mata komai daɗi, saboda ko bakomai zatayi iyaka ƙoƙari wajen ganin ta kare ƙirjinta, lokacin daya kawo ƙirjinta kasa jurewa tayi, dasauri ta duƙa ƙasa haɗe da cewa "Dan Allah kabarni naje toilet na cire da kaina"
Bai tanka mata ba saima ɗagota daya sakeyi tsaye, rungumeta yayi ta baya haɗe da ɗaura kansa akan wuyanta, hancinsa yasanya yashiga shaƙan daddaɗan ƙamshin da fatarta ke fitarwa, ahankali yake goga mata lallausan sajen sa akan fatar wuyanta yayinda yasanya hununsa duka biyu ya saƙalo ƙugunta, rumtse idanunta kawai tayi tanajinsa, yayinda zuciyarta kuwa ta ke bugawa da sauri. a hankali yashiga kissing ɗin wuyanta haɗe da soma yawo da hanunsa akan cikinta, wani iri Zahrah tasomaji acikin jikinta, yayinda gaba ɗaya tsikar jikinta ya shiga motsawa,, shi ɗin ma hakance ta kasance dashi, baisan sanda yasanya hanunsa yaci gaba da ƙoƙarin zame mata rigar dake jikinta ba,, har rigan tafaɗi ƙasa Zahrah bata ɓuɗe idanunta ba shima kuma baibuɗe nasa idanun ba, hanunsa yasanya akan lallausan fatar cikinta yashiga shafawa, cikin wani irin salo ya juyo da'ita yazamana suna fuskantar juna, dayake ɗakin babu wadataccen haske sosai, hakan yasanya baya iya ganin jikinta sosai, hanunsa yasanya duka biyu ya tallafi bayanta haɗe da kusanto da fuskarsa daf da tata, laɓɓansa yaɗaura akan nata laɓɓan tare da kama leɓenta na ƙasa yashiga tsotsa ahankali,, al'amarin dayayi mugun sanya mata shock acikin jikinta kenan, tunda take aduniyarta wani ɗa namiji baitaɓayi mata kiss ba sai Zaid, shiɗin ma kuma alokacin dayayi kissing ɗinta bata cikin nutsuwa da kuma hankalinta saboda haka babu wani abu da taji game da hakan, Dr.Sadeeq ma hakane takasance dashi saboda a iya tsawon tarihin rayuwarsa baitaɓa yiwa wata mace kiss ba, yau shine karonsa na farko... Ahankali yake shan lips ɗin nata yayinda ita kuma takasa koda ƙwaƙƙwaran motsi ne,, cikin wani irin salo ya soma tura bakinsa cikin nata bakin, harshenta ya laluɓo haɗe da soma yi masa shan lollypop,,, cikin mintunan da basu wuce 8 ba yasoma sauƙe wani irin numfashi, haɗe da sake ƙamƙameta acikin jikinsa, sosai yake kissing ɗinta yana fitar da wani irin numfashi me ɗauke da wani kalan sauti, yayinda itakuwa Zahrah ƙafafunta suka soma ƙoƙarin rugujewa ma'ana suka soma saƙewa da'alama dai abun yafi ƙarfinta,, ɗaukanta yayi caɗak yanufi kan gado da'ita, kwantar da'ita yayi haɗe da sake sanya bakinsa acikin nata,, haɗuwar fatar jikinsu waje ɗaya shiya matuƙar taimakawa kiss ɗin nasu yaƙara armashi a wajen Doctor, dan Zahrah kam tuni tazama statue.. A iya kiss kaɗai Dr.Sadeeq ya ruɗe yakuma sukurkuce, sucking tongue ɗinta kawai yake cike da nutsuwa yana me fidda wani irin numfashi, tuni idanunsa sunkaɗa sunyi jajur dasu, ƙasa yasomayi dakansa harzuwa kan cikinta, kissing ɗinka yashigayi akan cikin nata yana me shafa santala santalan cinyoyinta, hanunsa yasanya abayanta ya ɓalle maɓallin brezian dake jikinta, haba ai tuni hajiya Zahrah ta ruɗe ta sake ƙanƙame jikinta, saida yasamu shiɗewa haɗe da ɗaukewar numfashi alokacin da hanunsa suka sauƙa akan lallausan breast ɗinta wanda suke a tsaye ƙyam babu alamar kwanciya atattare dasu, bakinta yaƙara kamowa yacigaba da tsotsa yayinda yasanya hanunsa yana murza breast ɗinta ahankali, gaba ɗaya ya zauce ya ruɗe yakuma susuce yafita aduniyar mu yashiga wata duniya me cike da wani irin masifaffen sha'awa me matuƙar ƙarfi harji yake kansa nawani irin sarawa,, kuka ta fashe dashi me tsanani alokacin da taji sauƙar bakinsa akan nipple ɗinta, hmmm kukanta bazaiyi aiki ba da dukkan alamu, domin kuwa tsotsar dayakeyimawa nipple ɗin nata ma na dabanne,, da ƙyarma yake iya ƙwato numfashinsa,, duk yanda yaso ya share kukan nata yakasa, dolensa ya tsagaita haɗe da kwanciya akanta, cikin wata irin murya da take a shaƙe yace "Please Zahrah stop craying!" ae kamar cewa yayi ma taƙara volume ɗin kukan nata, kansa dake matuƙar yi masa ciwo ya dafa, haɗe da cije laɓɓansa, wallahi bazai iya jurewa ba komai zai iya faruwa dashi, yakai ƙololuwar sha'awa matuƙa, amma kuma yazaiyi da kukan da Zahrah takeyi masa yanajin tausayinta sosai, yasan ahalin yanzu metake tunawa, wancan mummunar ranan take tunawa, amma kuma haƙƙinsa ne ya mantar da ita komai. (Khair anya ruwanki bazaiyi tafasan banza ba kuwa🤔 naga mutumiyar taki tana neman hana doctor walwala🙊) Sake matseta ajikinsa yayi haɗi da haɗe bakinsu waje ɗaya, sauya salon kiss ɗin nasa yayi, wanda hakan ya tilasta mata dole tayi shiru, sai dai haryanzu jikinta bai daina ɓari ba, idan tace gangar jiki da ruhinta basa karɓan saƙon Dr.Sadeeq tayi ƙarya, amma kuma matuƙar tsoro takeji, ƙwaƙwalwarta azabar da Zaid yajiyar da'ita take tariyo mata, gani take shikenan itakam tata ta ƙare dan kuwa bazata iya jure azaba biyu ba,, salon romance ɗin da Doctor keyi mata yawuce gaban kwatance burinsa shine ya mantar da'ita wannan tsoron, ita kanta ta yarda da cewa saƙonninsa sun ratsata domin kuwa tuni ta gama jiƙewa to amma abun tsoron na gaba,, bai ɗauke bakinsa acikin nata ba haryagama ratsa cikin jikinta, wani irin wawiyar ajiyar zuciya ya sauƙe haɗe da sakin wani irin ƴar ƙaraman ƙara dake nuna alaman cewa mutum yagama lulawa cikin duniyar da babu irinta,, baisan dayaushe yazare bakinsa acikin nata ba, wani irin ƙara ta sake haɗe da soma rusa kuka kamar wanda ake zarewa rai.....*** Bayajinta balle kuma ganinta saboda idanuwansa rufewa sukayi ruf, duk kuka da ihun da takeyi baisan tanayinsu ba, wallahi shikam tunda yake baitaɓa sanin menene daɗi ba aduniya sai awannan lokacin, bazai taɓa iya misalta abun dayaji ba abun yafi ƙarfin tunaninsa ya shammaci hankalinsa, harya manta da cewa ita ɗin ba budurwa bace, baitaɓa kusantar wata mace ba Zahrah itace ta farko, kuma amatuƙar kame yajita gam, sai dai kuma fa har'abada baza'a haɗa virgin da kuma wacce ba virgin ba dole akwai banbanci amma shidai baiji banbancin ba saboda dama baisan kowaba sai ita*** Doctor ya hole iya holewa yayi gurnanin yayi sambatun harsau ba'adadi yayinda ƴar mutane kuwa tayi kuka kamar ranta zaifita harsaida idanunta suka kumbura alokaci guda kanta kuwa ba'a magana wajen yi mata ciwo..
***
After 1 hour.
Shikansa jikinsa zafi zau ya ɗauka yayinda yaji gaba ɗaya duniyar tana juya masa, to inaga kuma wacce ya bawa kaya, da ƙyar ya'iya kwantawa agefenta haɗe da jawota cikin jikinsa, baisan da wani kalma zaifara yi mata magana ba, kyakkyawan sumbata ya bata akan goshinta haɗe da rumtse idanunsa, wanda suke zubar da hawayen tsananin tausayinta,,, kusan 12 minute yana rungume da'ita acikin ƙirjinsa "Me daɗi na!" yafaɗi haka acikin kunnenta da'alama dai sunan daya bata kenan,lol. Zahrah da'idanunta sukayi luhu suna ta tsiyayar da hawaye kasa cedashi komai tayi.. (Su Me daɗi ansha wuya😂🙊🙈)
"I'am so sorry, banyi haka don nacutar dake ba, nakasa control ɗin kainane, Inasonki Zahrah, a iya daren yau soyayyarki ta sake ninkuwa acikin zuciyata, kiyafemin kinji me daɗi na bazan ƙara ba, please for give me!" yaƙare maganar cikin kwantar da murya, da'alama dai har yanzu giyar daɗin baigama sake shiba... Me daɗi dai taƙi cewa komai haka ya sauƙo daga kan gadon rungume da'ita kamar wata ƴar baby, direct bathroom yanufa da'ita, dakansa ya haɗa mata ruwan ɗumi haɗe da zaunar da'ita aciki, duk da cewa ita ba virgin bace amma kuma wannan ɗin ma kusan daidai yake dayinta na farko, saboda ta matuƙar shan azaba sosai, hakan yafarune kuma saboda yanda Hajiya Shuwa ta dinga ɗurka mata magungunan matsi dakuma na ciko da mace, sosai taji zafi aƙasanta lokacin da yazaunar da'ita acikin ruwan amma kuma yazatayi yazama dole ta daure.. Dakansa yayi mata wanka haɗe da naɗota acikin towel like wata ƴar ƙaraman baby, shima wanka yayi kana yafito daga cikin bathroom ɗin, shidakansa ya sanya mata rigan bacci, shima ya jallabiya ya sanya ajikinsa, haryanzu Zahrah bata daina tsiyayar da hawayeba,, new blanket yasanya musu domin kuwa wancan ya ɓaci da sperm ɗin me.... au 🙊Zahrah,, jawota yayi jikinsa haɗe da rungumeta tsam tsam jiyake kamar wani zaizo ya ƙwace masa ita (wai inji nuru ba kama bane Zaid yananan tafe😂 niko nace yayi ƙarya)
Hawayen da suketa ambaliyan sauƙa akan fuskarta yashiga share mata, haɗe da ɓare wani sweet yajefa acikin bakinsa, kwantar da'ita yayi akan ƙirjinsa haɗe da ɗago fuskarta ya tura mata sweet ɗin acikin bakinta, harshensa yasanya yana meyi mata wasa da sweet ɗin acikin bakinta, lumshe idanunta tayi tana me sauƙe ajiyar zuciya, yayinda yake shafa mata bayanta ahankali,,har wani irin nannauyan bacci yazo ya ɗauketa..... Kafeta yayi da idanunsa aransa yana me godia ga Allah daya basa wannan mata me ɗauke da tarin ni'imomi na fili dana baɗini, kai yasha sweet fa yau harwani jin kansa yake a sama.Lol,,, batare da yayi aune ba shima bacci ya ɗaukesa bayan yayi musu addu'a yashafa mata... Good night angon me daɗi...
(🙈🙈🙈🙈 bani nayi typing ɗinba yau🤣🤣🙈🙈... Kada kumantafa kuzo cin cake💃💃)
*22/January/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI!!*
*Written By*
*Phatymasardauna*
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed*
*CHAPTER 96 to 97*
Tun da ta tashi tayi sallan asuba take ta ruskar kuka tamkar wacce aka cewa wani nata ya mutu, ita kanta batasan kukan me takeyi ba, amma dai hakanan takeji zuciyarta babu daɗi, gashi gaba ɗaya jikinta ciwo yake, "Gaskiya Doctor mugune." tafaɗi haka acikin zuciyarta, gaba ɗaya ya gajiyar da ita, daga ƙasan zuciyarta kuwa wani abune yayi mata tsaye wanda kuma shine sanadiyar kukan nata, wannan wace irin rayuwa ce? wace irin ƙaddara ce wannan? rabonta da tayi farinci me tsayi tun kafun Zaid yashigo cikin rayuwarta, ada tana ganin rayuwar da takeyi acikin gidansu rayuwar ƙunci ce, ashe bata sani ba wannan rayuwar salama ce a gareta, SO baiyi mata adalci ba, so bai kyautawa rayuwarta ba...
Yajima tsaye akanta yana me ƙare mata kallo, mamakin yanda take kuka tsakaninta da Allah yake, a iya saninsa banda abun daya wakana atsakaninsu daren jiya baiyi mata komai ba, amma kuma sai gashi yanzu tana ruskar kuka, har a ƙasan zuciyarsa bayason kukanta, idan yaji kukanta jiyake gaba ɗaya nutsuwarsa ya ƙaura daga jikinsa,, ahankali yashiga takawa harzuwa inda take duƙe akusa da gado tana kuka, sam batamasan da shigowarsa ba kukanta kawai takeyi.... Hanunsa yasanya ya dafa kafaɗanta, da sauri ta juyo aɗan razane don bataji shigowarsa ba,, idanunsa ya ƙanƙance haɗe da waresu alokaci guda, zama yayi akan gado haɗe da ɗagota zuwa jikinsa...
"Me yasa Zahrah? me nayi miki? meyasa kike ƙuntatawa rayuwarki akan wani dalili naki? ban aureki don nazuba miki ido kita cutar da kanki ba, please ki daure zuciyarki kidaina wannan kukan banaso!" ya faɗi maganar cikin lallashi... Saurin ɗauke hanunsa dake kan wuyanta yayi, kansa yaɗan ɗafe haɗe da zaunar da ita akan gado, direct wani ɗan madaidaicin drawer yanufa, maganin da yasan zai sauƙar mata da zazzaɓi acikin mintuna ƙalilan ya ɗauko tare da ruwan gora ya dawo zuwa gareta. Maganin ya ɓalla ahanunsa tare da jawota jikinsa, bakinta ya buɗe ya jefa maganin aciki haɗe da bata ruwa, babu musu ta haɗiye maganin bayan ta rumtse idanunta, sai kace wacce aka bawa guba... Aje goran ruwan yayi haɗe da sake jawota jikinsa, kwantar da kanta yayi akan ƙirjinsa, yayinda yake shafa bayanta a hankali. Ajiyar zuciya haɗi da sheshsheƙan kuka kawai take sauƙewa. Shikuwa Dr.Sadeeq wani tunani na daban yakeyi acikin zuciyarsa, hakanan Allah ya halittamasa tsananin tausayin Zahrah acikin zuciyarsa, yana sonta sosai, bayason yaga tana cikin damuwa, bayajin akwai wani abu aduniyar nan da Zahrah zata nema agaresa matuƙar yana dashi tarasa, zai iya mallaka mata komai nasa, matuƙar zataji daɗi, za kuma tayi farinciki, bakinsa ya kawo daf da kunnenta cikin murya me sanyi yace
"Zahrah!"
Tanajinsa amma kuma saitayi sauri ta lumshe idanunta, tanaso ya ɗauka cewa bacci take.
Jin tayi shirune yasanya yashiga goga mata lallausan sajensa akan fatar wuyanta, yayinda yake yawo da hanunsa akan bayanta a hankali..
Luf tasakeyi acikin ƙirjinsa, tana jin saƙonsa yana tsarga mata hartafin ƙafarta, yayinda daddaɗan ƙamshin turarensa ke ƙara sanyaya mata jiki, batajin bacci ko kaɗan, amma kuma yazama dole ta ƙwaƙulowa kanta baccin dole, kodan ta samawa zuciyarta salama. "Ina laifin Dr.Sadeeq? mene bayi dashi wanda mace takeso tasamu ajikin ɗa namiji? miye laifin masoyin daya nuna maka haƙiƙanin so? ashe wani lokacin zuciya batasan menene halacci ba? me yasa SOYAYYA tazamo guguwa me hargitsa zuciyar ɗan adam tayi fatali da komai nasa?" itakam ko da a yanzu soyayya ta barta haka ta gama iya cutarta, cuta me muni ma kuwa.. Yajima yana shafa bayanta, harsai da ya ji sauƙar numfashin dake nuna cewa da gaske bacci ya ɗauketa. Kwantar da'ita yayi akan gado, haɗe da jawo blanket ya rufe mata duka jikinta, yasani sarai batason sanyi, don haka ya rage gudun A.C, kashe mata fitilan ɗakin yayi, kana ya jawo mata ƙofar ya rufe mata bayan yafita zuwa falo.. Laptop ɗinsa ya ɗauka haɗe da buɗewa, aikinsa ya shigayi cikin nutsuwa, ɗan kwana biyun nan da bai shiga office ba haryatara ayyuka masu yawa, gashi ansanar masa patients suna buƙatar taimakon sa, duk da ya ɗau hutu ma ashe bai tsira ba, ayyuka na nan akansa wanda yazamana dole sai shi zaiyisu...
***
*GERMANY*
Shikaɗai yake rayuwarsa acikin ɗakin, yau kwanansa ɗaya kenan baisanya komai na abinci acikin saba, yayi matuƙar ramewa alokaci guda, yayinda gashi dakuma sajen dake kwance akan fuskarsa suka ƙara yawa fiye da na da, duk da dama cewa shi mutum ne me yalwan suma, kallo ɗaya zakayi mai kasan cewa yana ɗauke da damuwa me tarin yawa acikin zuciyarsa, Zaid ɗin da dana yanzu sun banbanta, wan can Zaid ɗin zuciyarsa cike take da isa, ɗagawa, girmankai, rashin sanin darajan ɗan adam, Zaid ɗin da mashayine, mazinaci, wanda bai ɗauki zina abakin komai ba, haka kuma Zaid ɗin da, baisan menene damuwa ba, baisan menene rashi ba, samu kawai ya sani, sannan kuma baisan menene ƙunci da ɗaci ba, baikuma san menene wani abu waishi soyayya ba. Zaid ɗin daya kasance yanzu kuwa, wani mutum ne dayake cikin ƙunci, zuciyarsa tana cike da tarin damuwa, Zaid ɗin yanzu yarasa duk wani farincikinsa, yarasa jin daɗi, yarasa nutsuwar zuciya data ƙwaƙwalwa. "ko wannan baici yasa Zahrah ta tausaya masa ba? shin wai shi kaɗaine yataɓa aikata abun da baidace ba?" yatambayi kansa, abu biyune suke damunsa, zazzafar soyayya dakuma rashin nutsuwa da salama dake damunsa, yanzu shikaɗai yasan halin dayake ciki, baya iya bacci, baya iya cin abinci, bayajin daɗin komai nasa, gaba ɗaya duhu ya mamaye rayuwarsa, yanzu yafara zargin cewa zunubansa ma sunyi masa yawa, yasani ƙwarai, yasan abu me kyau da kuma marar kyau, amma saboda ruɗin duniya gaba ɗaya ya shagala. (Yawancin mutane yanzu rayuwarsu sukeyi saka ka, zasu aikata zina, zasu sha giya, zasu aikata duk wasu aiki dake jawo musu manya manyan zunubai, amma kuma yawancinsu sunfi gudun kunyar duniya data lahira, suna tsoron wani yakamasu suna aikata zina, amma basa tsoron kallonsu da Allah yakeyi, wasu sun maida zina manshafawarsu, suna ganin kamar hakan wayewace, bayan kuma suna sane dacewa aikata ta babban halaka ne, Ya ALLAH kaci gaba da karemu, kakuma tsaremu da sharrin zina, ka rabamu da zama da mazinata, Ameen Ya ALLAH!)
Yariga daya gama yanke hukunci cewa ko da su Dad ɗinsa basaso saiya koma Nigeria, bazai iya zama anan ba, zafi yakeji acikin zuciyarsa marar misaltuwa idan haryatuna da cewa Zahrah'nsa tana can gidan wani, sai yaji gaba ɗaya nutsuwarsa ta gushe, wataƙila ma wannan banzan Doctor ɗin ya kusanci Zahrah'nsa, ae kuwa baisan sanda ya ƙwalla wata irin ƙara ba, azuciye ya ɗauki wani flower dake gefen gadon, yayi jifa dashi, take kwalbar flower'n ya tarwatse a tsakiyar ɗakin, duk da haka hakan baiyi masa ba, saida yataka ya ƙarasa gaban mirror, da hanunsa ya daki mirror ɗin, take mirror'n ya tarwatse har saida ya yanka masa hanu, amma saboda tsananin kishi'n dake cinsa, ko zafin ciwon baiji ba.
"Hakane ma, yakusanceta" wata zuciyartasa ta faɗa masa..
"No!!! it will never happen, i Know Zahrah will not do it, bazata taɓa iya bawa wani kanta ba bayan ni, because she know we love each other" yafaɗi haka da ƙarfi cikin wata irin murya, me ɗauke da tsananin ɓacin rai, durƙushewa yayi a ƙasa haɗe da sanya hanu ya dafe saitin zuciyarsa wacce take bugawa da sauri, da dukkan alamu dai ya tsokalowa kansa. Haki yasomayi tamkar wani wanda yayi gudu, tarine ya sarƙesa, take jini yasoma fitowa ta bakinsa, shi kaɗai yayi tarinsa harya ƙare, ya galabaita sosai da sosai, da ƙyar ya'iya jan jikinsa ya shiga toilet, wanke bakinsa yayi kana yafito daga cikin toilet ɗin, numfashi kawai yake maidawa cike da wahala,, wani ɗan abu yadanna, bayan kamar minti 1 saiga wata cleaner tashigo cikin ɗakin, nuni yayi mata da inda jininsa ya ɓaɓɓatata, babu ɓata lokaci ta sanya kayan aiki ta gyara wajen, tana kammala gyaran kuwa wasu likitoti su biyu suka shigo cikin ɗakin.. Duba lafiyar jikinsa suka sake yi haɗe da basa wasu magunguna, wata allura sukayi masa da take matuƙar sa bacci, domin kuwa gwaje gwajen da sukayi masa yasa sungano cewa baya samun wadataccen bacci.
Suna fita ya lumshe idanunsa, wanda tuni suka zama jan gauta, saboda tsabar tsananin kishi dake cinsa, jiyake ma kamar idan ya ƙara kwana ɗaya ba acikin Nigeria ba ya cutu, gwamma yaje ya ƙwace Zahrah tunkan wanda ya ɗauka bakomai ba ya ɗanɗana masa zumarta. (Hahhh guy ae ka makaro,yasin doctor yajima da ɗanɗanawa🙈) **** Mintuna kaɗan dayi masa alluran, bacci me nauyi yayi gaba dashi...
Dad ne ya nutsu haɗe da dawo da kallonsa ga Mummy. "Inaga abu ɗaya zamuyi masa yamanta da wannan yarinyar, kawai na yanke shawara aure zanyi masa."
Shaye da mamaki Mummy take kallon Dad. "Aure fa kace Alhaji? wakake tunanin zata iya zama da Zaid, da irin wannan halinnasa? hmmm bana majin cewa Zaid zaiso wata mace bayan wannan Zahrah'n, ni nama fara tunanin cewa asirce masa zuciya tayi, amma inbanda haka taya lafiyayyen ɗa namiji kamar Zaid zai maƙalewa mace ɗaya kamar maye"
Murmushi Dad yayi haɗe da girgiza kansa, "itadai Safara'u haka take, idan ana magana me hankali saikuma tana sako wasu abubuwa kamar na wasa." dad yafaɗi haka acikin zuciyarsa, afili kuwa gyara zamansa yayi haɗe da sake fuskantarta...
"A wannan karon dagaske aure zanyi masa, saboda aure ne kaɗai zaisanya Zaid dawowa cikin nutsuwarsa, bandamu da ko yanason matar ko baya sonta ba, nasan watarana ahankali zai sota ya manta da waccar"
"To Allah yasa hakan shine mafi alkhairi, amma gaskiya nima banjin daɗin ganinsa acikin wannan halin dayake ciki yanzu,ko abincin kirki wallahi bana iya ci" Mum tafaɗi haka cikin tausayawa ɗan nata..... (Team Zaid kunji fa wai aure za'ayi masa me zakuce? wayaga Zaid da auren dole)
****
NIGERIA
Tunda ta kwanta bacci ba'ita ta tashi ba sai 11:30 am, ko tsayawa nemansa yau batayi ba tafaɗa bathroom, wanka tayi kana ta fito daga cikin bathroom ɗin... Mai kawai ta shafa kamar kullum sai kuma powder, itakam batason cika meckup akan fuskarta.
Riga da sket na atamfa tasanya, wanda yayi mata caras ajikinta, ɗan kwalin kayan kawai ta yafa akanta zuwa kafaɗarta. Direct falo ta nufa sai tashin ƙamshi take, kamar yanda tayi zaton zata ganshi a falo, sai taga saɓanin haka, domin kuwa babu shi babu alamarsa,, kallonta ta mayar kan dinning area saidai taga kan table ɗin wayam babu food flask ko ɗaya,, hahhh take idanunta sukayi raurau dasu, ɗan ƙaramin bakinta ta tunzuro haɗe da shafa cikinta, "Yanzu kenan Doctor da yunwa ya barta?" ta tambayi kanta...
Motsi ta soma ji daga ɓangaren kitchine, tsoro ne yaɗan kamata dan tasan Dr.Sadeeq da kansa kam bazai shiga kitchine ba, "to kodai basu kaɗai bane acikin gidan?" tasake tambayar kanta. Cikin sanɗa take takawa harta isa ƙofar kitchine ɗin, motsinne yasake tsananta, don haka cikin sanɗa ta tura kanta cikin kitchine ɗin.
"Kamata!!!" taji anfaɗa da ƙarfi. Wani irin ƙara ta ƙwalla haɗe da rugawa a guje ta koma cikin falo.. Dariya yashiga yi mata bayan yafito daga kitchine ɗin hanunsa riƙe da plate wanda yake ɗauke da soyayyen chips..
Zamewa tayi aƙasa haɗe da dafe ƙirjinta, nunfashi take fitarwa da ƙyar, da'alama ta tsorata sosai.
Zama yayi akan kujera har yanzu dariya yakeyi mata, yasan zata tsorata amma baiyi tunanin tsoron nata zai kai har haka ba.. "Yadai karfa ki sume min" yafaɗi haka yana me ɗan tsagaita dariyarsa...
Ɗan ƙaramin bakinta ta tunzuro gaba haɗe da miƙe ƙafafunta akan sofa, "Nidai Allah ka tsoratar dani, please kada ka ƙara zan iya mutuwa fa!" taƙare maganar cikin tsantsar shagwaɓa.
"Kindai tsorata kanki, ni bani na tsorataki ba ƴan mata, da wayace ki shigo kitchine ɗin cikin sanɗa?"
"To ba motsi naji ba, na ɗauka ko aljanine!" still cikin shagwaɓa takumayin maganar..
Kallonta kawai yashigayi yana murmushi, a garin gudu harta yada ɗan kwalin dake kanta bata sani ba, hakanne yabaiwa gashinta damar bayyana.
Jingina da kujera tayi, tana me sauƙe ajiyar zuciya, sai yanzu ta fara dawowa daidai.
Ƙaurin abinci yasoma ji da sauri yatashi ya nufi kitchine, aikuwa yana zuwa ya tarar da soup ɗin daya ɗora akan wutane yasoma ƙonewa, da sauri ya sauƙe haɗe da ƙwaɗawa Zahrah ƙira..
Saƙare tayi tana kallon yanda yake kwashe soup ɗin ƙwai da albasa yana sanyawa acikin wata ƴar ƙaramar kula, dariya ne ya ƙwace mata, cikin dariyan tace "Doctor dama ka iya girki ne?"
Hararan wasa yayi mata haɗe da cewa "Na bugawa a jarida ma kuwa"
Dariya ta ƙara kwashewa dashi, wai iya girkinnasa har na bugawa a jarida ne hmm. Ɗan matsowa tayi kusa dashi haɗe da leƙa tukunyar da akayi soup ɗin aciki, da sauri ta sanya hanu ta toshe bakinta, dariya ne yazo mata, gaba ɗaya cikin tukunyar yayi baƙi, soup ɗin yasoma ƙonewa..
"Miye wai kikewa dariya? yarinya zaki faɗa wa mutanen garinkune anjima, kin kuwasan daɗin girki na yafi na kowa ko" yaƙare maganar yana me ƙaƙalo ƙasan tukunyar daya ƙone zai zuba acikin kulan. Dasauri ta rike hanunsa haɗe da cewa "Idan kazuba wannan fa soup ɗinnan bazai ciwuba"
"Meyasa, ko hassada kikeminne?"
Yatambayeta yana me ɗage giransa ɗaya..
"Shikenan to, tunda kanaga kamar wasa nake ma, amma kuma idan kasa akan abincinka yayi ɗaci ni ba ruwana" tafaɗi haka tana me sake hanunsa.
Kallonta ya ɗanyi haɗe da marerece fuska. "Yazanyi to Zahrah, banaso kitashi kinajin yunwa banbaki abinci ba, shine na soyamiki chips yanzu kuma gashi nayi soup ɗin kince wai ya ƙone bazai ciwuba, ko zamuje resturant ne?" gaba ɗaya fuskarsa ta sauya da alama shagawaɓa yakeson yi mata..
Wani irin tausayinsa ne taji ya daki zuciyarta Allah sarki, ashe duk akantane yaketa shan wannan wahalan.. "A'a basai munje resturant ba, zan ma iyaci a haka fa ai ba duka soup ɗin bane ya ƙone, kuma ma basai muci da tea ba!" cikin yanayi na kulawa ta ƙare zancen..
Cikin jin daɗi yace "Yauwa tawan to ɗauki soup ɗin kije, bana haɗa mana tea ko"
"A'a kabarshi ni dakaina zan haɗa mana" tafaɗi haka tana me ƙoƙarin fara haɗa musu tea ɗin. Hanunta ya kama ya sumbata haɗe da ɗaukan kulan da soup ɗin ke ciki yanufi falo... Mintuna kaɗan tafito da ɗan wani tray wanda yake ɗauke da kofuna biyu na tea ɗinsu.. Aje tray ɗin tayi akan sofa haɗe da maida kallonsa gareta, gani tayi ya kafeta da idanunsa, wanda suke daɗa sawa tanajin nauyinsa..
Ɗan shagwaɓe fuska tayi haɗe da cewa "To miye kake kallona!"
Murmushi yasakar mata haɗe da tasowa daga inda yake zaune, zama yayi akan sofan, dakansa ya zuba musu soup akan chips ɗin, loman farko Zahrah ta tauna wani Chips da bai gama soyuwa ba, kallonta yayi haɗe da cewa "Ya kikaji yayi daɗi ko? ai nasan ma zaiyi daɗi"
Murmushin dole tayi haɗe da cewa "Yayi daɗi sosai"
Hanu yasanya yashafi kumatunta, "Yauwa My Zahrah ae dama nasan saikin yaba"
Da ƙyar ta'iya danne dariyarta, loman farko da yayi ya ɗago kansa ya kalleta, itama kallonsa takeyi, saitaga ya ɓata fuska kamar zaiyi kuka, bazata iya riƙe dariyarta ba yanzu kam yazama dole saita dara, sake shagwaɓe fuska yayi ganin yanda takeyi masa dariya. Da ƙarfi yajawota jikinsa haɗe da murɗe mata hannayenta "Wakikewa dariya?"
Cikin dariya tace "Kayi haƙuri nifa badakai nake ba, dariyarce kawai tazomin"
"Uhhh aini ba yaro bane nasan ni kikewa dariya, to amma ai balaifi na bane laifin gas ɗinne da bai ratsa kaskon suyan da kyau ba, kuma ko kema ae nasan haka zaiyi miki"
Itadai dariya kawai takeyi masa, gaskiya wannan girkin nasa kam yacancanci abugasa a jarida kamar yanda ya faɗa, onion and egg soup ya ƙone dankali kuma bai soyuba.
Haka suka haƙura da dankalin suka sha tea tare da snacks kawai. Bayan sungama cin abincin ya jawota jikinsa, haɗe da ɗaura kansa akan wuyanta, lumshe idanunsa yayi yana me sauƙe numfashi a hankali, wani abu yakeso daga gareta wanda yasan idan ya nema balallai yasamuba, kuma ma koda yasamu to ba a son ranta ta basa ba, shiyasani matuƙar zasu kasance waje ɗaya da'ita tofa har abada acikin sha'awarta zai kasance.. Jin yanda yake sauƙe mata numfashi akan wuyanta ne yasanya jikinta yin sanyi, ahankali kasala tasoma dirar mata, itama lumshe nata idanunta tayi, tana me yin wani tunani acikin zuciyarta.. Tsawon mintuna 15 suka ɗauka a haka babu wanda yace da ɗan uwansa ƙala, shi dai Dr.Sadeeq tsundum yake acikin kogin sha'awa, yayinda itakuwa take tsundum acikin kogin tunanin wani abu wanda bashida amfani a wajenta, wani abu wanda tunaninsa yazame mata jiki da jini, sai dai kuma tasan abun baidace da itaba, baidace da rayuwarta ba, ƙaddara ce kawai ta haɗasu, sannan kuma zuwa yanzu yakamata ace ta manta da babinsa, takuma daina tunasa, sai dai kuma duk yanda taso hakan yakasance abun yaci tura, dole zata haɗa da addu'a, saboda addu'a yafi gaban komai, duk da cewa dama tanayi amma dole zata ƙara akan wanda takeyi...
A hankali yajanyeta daga jikinsa haɗe da miƙewa yanufi ɗaki, da kallo kawai tabisa harya shige cikin ɗakin, "Meke damunsa?" tatambayi kanta a bayyane.
Ganin batada maibata amsa, baikuma dace ta zauna batare da taji damuwarsa ba yasanya ta bisa zuwa cikin ɗakin..
Kwance ta iske sa akan gado yayi ruf da ciki yayinda yasanya hanunsa ɗaya akan mararsa, sam bata fahimci wani abu game da hakan ba, ahankali taƙarasa wajen da yake, cikin murya meɗan sanyi tace "Bakada lafiya ne?"
"Lafiyana ƙalau, kawai dai bacci nakeji ne" yafaɗi haka ataƙaice, baison yayi magana me tsawo ta harbo jirginsa, tsakani da Allah bayason yasake takurata, jiyama da yayi, yauda safe da kuka ta tashi masa, saboda haka yanzu baison ya ɓallo liƙi gwamma yabari ko zuwa dare ne ma, amma kuma idan yatuno irin daɗin dayaji jiya, sai yaji kamar bazai iya haƙura ba.. Haurawa tayi kan gadon haɗe da kwanciya a bayansa, ƙurawa kwantaccen gashin kansa ido tayi, abubuwa da yawa nasa suna matuƙar burgeta, babu ma kamar idanunsa, idan yana kallonta harwani mutuwa jikinta yakeyi, babu ta inda Dr.Sadeeq ya gaza, komai nasa yayi 100%.
"Ɓacci bai isheki bane?" yayi mata tambayar batare daya juyo zuwa garetaba.
"A'a kawai dai ina hutawa ne" tafaɗi haka a taƙaice don talura kamar bayason damuwa.
Ƙarar wayartane ta karaɗe cikin ɗakin, da sauri ta ɗauko wayar dake aje kan ɗan ƙaramin drawer'n gefen gado.. Ganin Husnah ce me ƙiran yasanya ta ɗaga wayar da sauri, tana ƙoƙarin yin magana taji muryar Husnah tace "Gani a falo"
da sauri tatashi daga kan gadon haɗe da ficewa daga cikin ɗakin, ko bayani bata tsaya yiwa Doctor ba. Shikuwa da kallo kawai yabita harta fice daga cikin ɗakin, lumshe idanunsa yayi haɗi da sauƙe ajiyar zuciya.
Da gudu Zahrah taje ta faɗa jikin Husnah, rungume juna sukayi ƙam cike da kewar juna.
"Nayi kewarki sosai ƙawata" Husnah tafaɗi haka tana me ƙara rungume Zahrah.
Tureta Zahrah tayi haɗe da ɗan turo baki gaba. "Bawani nan ni ae nayi fushi, tunda ranan nan kin yaudareni kin gudu"
Dariya Husnah tayi haɗe da cewa "Yi haƙuri amaryar likita"
Dariya suka sanya su dukansu, saida Zahrah ta cikawa Husnah gabanta da su drinks kafun tazo ta zauna akusa da ita..
"Gaskiya dole ne nima acikin wannan shekaran nayi aure, kiduba kiga 2 days kacal amma gaba ɗaya sai wani shining kike" Husnah tafaɗi haka tana me ƙarewa Zahrah kallo.
Harara Zahrah ta wurgawa Husnah "Kinganki ko wallahi banason tsokana, ae ko a engine aka sani baici ace zuwa yanzu nafara walwali ba"
"Hahhh kedai faɗi gaskiya don da alama doctor madara na musamman yake shayar dake kullum"
Dariyane yakama Zahrah "wai madara" hmmm itasam bata fahimci inda kalaman Husnah suka dosa ba..
"Ke dai baki rabo da tsokana, wace madarace zatasa acikin 2 days kacal na sauya" Zahrah tafaɗi haka tana me duban skin ɗinta..
"Hahhhh madara mana irin taku ta masu aure, ae babe kawai ki manta, nasan kinbasa yasha kuma kema yabaki kinsha"
Sai yanzu Zahrah ta gano me Husnah ke nufi, duka ta ɗaka mata abaya haɗe da yin dariya. Husnah ma dariyan tayi, kana taɗauki drinks tasoma sha..
****
Hira sosai Husnah da Zahrah sukayi, duk da Husnah tace bajimawa zatayi ba. Bata jima ba kuwa tayi tafiyarta bayan tabawa Zahrah wasu ingantattun magunguna wanda Hajiya Shuwa ta bata tace takawo mata, har bakin gate Zahrah ta raka Husnah, cike da kewar juna sukayi sallama...
***
Kallon Dad ɗinsa yayi arikice gaba ɗaya idanunsa sun rufe, miƙewa yayi tsaye yasoma takawa ahankali, ganin zaifita daga cikin ɗakinne yasanya, Dad yayi saurin riƙosa, "Bazaka iya kulawa da kanka ba Zaid, badai Nigeria kakeso mu koma ba?" cike da kulawa Dad ya tambayeshi..
Kansa ya kaɗa kamar wani ƙaramin yaro, ajiyar zuciya Dad ya sauƙe haɗe da ƙara riƙe hanun Zaid ɗin.
"Shikenan ka kwantar da hankalinka gobe zamu koma Nigeria"
Wani irin sanyi Zaid yaji acikin zuciyarsa, badon komai ba saidon zaije yaga Zahrah'n sa, babu ruwansa da wani tayi aure, shi so yarufe masa ido, hargidan nata zaije... (🙆♀🙆♀ Anya Zaid bai samu matsala a ƙwaƙwalwarsa ba kuwa? )
Dad kuwa yayanke wannan hukuncinne saboda suna zuwa Nigeria zai ɗaurawa Zaid ɗin aure da ƴar abokinsa, wannan shi kaɗaine zaisanya Zaid ya nutsu yakuma dawo cikin hankalinsa....
*24/January/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 98 to 99*
Tana idar da sallan isha, ta ɗauki wata doguwar riga marar nauyi ta zura ajikinta, rigace irin shara shara ɗin nan, gashi kuma yaɗan kamata ta ƙasa, yayinda saman rigan kuwa ya buɗe, zura rigar kawai tayi batare da koda ta kalli kanta a madubi ba tafice zuwa falo. Sauri take batason Bollywood sufara haska film ɗin Bajrangi Bhaijaan bata kusa, ƙarfe takwas kuma dai dai zasu saka film ɗin, gashi yanzu bakwai ne hadda wasu mintuna, direct kitchine ta wuce taɗauko wani ɗan ƙaramin cup, fridge ta buɗe ta ta ɗauko babban cup ɗin milk shake dake cikin fridge'n ta tsiyaya, ahankali take tafiya tana ɗan zuƙan milk shake ɗin a bakinta, yajima yana jingine jikin ƙofa, kan ƙirjinta kawai yaketa kallo tun fitowarta daga cikin ɗakin, daga kan fatar cikinta har brezia'n dake sanye a jikinta, duk sun bayyana kansu a fili kasancewar rigar bata wani ɓoye sirri, sam bata lura dashi ba, hankalinta yana ga tv, hanu yasanya ya jawota jikinsa, saura kaɗan cup ɗin hanunta ya suɓuce ya faɗi ƙasa. Da sauri ta kalleshi haɗe da ɗan turo ɗan ƙaramin bakinta gaba.
Ta baya ya rungumeta, haɗe da ɗaura kansa akan wuyanta, cikin wata murya me sanyi yace "Ɗaukar alhaki ne, ko kuma kawai anyi danni ne?"
Cikin rashin fahimtan inda kalamansa suka dosa tace
"Bangane ba"
"Ummmm nima so nake nagane saina baki amsa" yafaɗi haka yana me ƙoƙarin zame wuyar rigar daga kan kafaɗunta.
Dasauri ta nemi matsawa daga jikinsa, amma saidai bata samu daman hakan ba, domin kuwa ya riƙeta gam.. Baidamu da yanda takeyi ba yasanya hanunsa yazame wuyar rigan, dake rigan dama tana da faɗin wuya sai gashi yakawo wuyan har kusan ƙasa da kafaɗunta, bakinsa ya ɗaura adai dai saitin wuyanta ta baya, wani irin lafiyayyen kiss yabata wanda saida yasanya tsikar jikinta suka tashi, da sauri ta juyo tana fuskantarsa, idanunsa da suka koma kamar na mejin bacci, ya ɗago ya watsa mata su, wani dokawa taji ƙirjinta yayi, yanayin da taga ƙwayan idanunsa shiyafi komai sanya mata faɗuwar gaba, har abada bazata taɓa manta mutumin data fara ganin irin wannan yanayin acikin idanunsa ba, kusan nasakamma har yafi na Doctor tsanani, domin kuwa bata taɓa mantawa da yanda idanun suka riƙiɗe suka zama jajaye suke kuma lumshewa alokaci guda ba, Zaid shine mutum na farko da ya fara kallonta da irin wannan yanayin, "mekenan hakan yake nufi? me yasa idanun suka sauya launi alokaci ɗaya?" tayi mawa kanta duka waƴannan tambayoyin da bata da me amsa mata su..
A hankali yake ƙara matseta haɗe da kusanto da fuskarsa daf da tata, burinsa kawai shine yaji bakinta acikin nasa. Kawar da kanta gefe tayi tana me sauƙe numfashi ahankali, gaba ɗaya tunowa da tayi da Zaid ya sanja mata yanayinta, Zaid ba mutum ne da zata manta dashi ba, lallai dole harta mutu yana cikin rai da zuciyarta, kodan abun da ya aikata a gareta.
Hanu yasa ya juyo da fuskarta, yazama suna fuskantar juna, baijirayi komaiba ya ɗaura bakinsa akan wuyanta, kissing ɗin wuyanta yake sosai, wanda hakan ya haifarmata da mutuwar jiki, cikin nutsuwa ya dawo da bakinsa kan nata bakin, ahankali yake sucking lips ɗinta, lumshe idanunta tayi tana me karɓan saƙon sa, karo na farko a rayuwarta da taji hakan dayakeyi mata yayi mata daɗi, batasan lokacin da ta gama sakar masa jikinta ba haɗe da sake buɗe masa bakinta, shikuwa dama abun da yake jira kenan, ba ɓata lokaci ya kamo tongue ɗinta yashiga tsotsa a hankali.. Wani irin numfashi kawai yake fitarwa, ko a iya haka idan ya tsaya yasan zaisamu gamsuwa, har abada shikam yanaji ajikinsa bazai taɓa gajiyawa da tsotsan baki da kuma harshenta ba, wani ɗanɗano na musamman yakeji acikin bakinsa idan yana tsotsan harshenta, yakan rasa duk wata nutsuwarsa idan laɓɓansu suka haɗe waje guda,yakan tsinci kansa cikin matsanancin shauƙi dakuma wani irin yanayi me daɗin gaske.
Ƙafafunta ne suka soma saƙewa, gaba ɗaya tsayuwar ta gagareta, yayinda shikuwa yaketa jifanta da salonsa iri iri, idan zasu shekara a haka sai dai ƙafafunsa su gaji suƙi ɗaukarsa, amma bawai shi ya gajiya da shan tausassun laɓɓanta ba, ƙoƙarin zamewa ƙasa takeyi da sauri ya riƙota haɗe da ɗagata caɗak kamar wata ƴar ƙaramar yarinya... Direct ɗaki yanufa da ita, bai direta ako inaba sai akan gado, ɗan ƙaramin ƙara tasanya haɗe da cewa "Wayyo nauyi!"
Dariya yayi haɗe da jan hancinta cikin muryarsa da ta soma sarƙewa yace
"Waye ne me nauyin?"
"Kai mana!" tafaɗa a shagwaɓance. Gaba ɗaya rigan jikin nata ya zame ƙasa, haɗe da soma bin ko wani ɓangare na jikinta da hot kiss, shiru tayi tanajin yanda yake tsotseta kamar wani maye, amma kuma fa saƙon nasa na yau yana shiga inda ya kamata domin kuwa tun ɗazu jikinta yagama mutuwa.
Kissing ɗin bakinta yaci gaba dayi, batasan lokacin da itama ta soma tayasa ba, baitaɓa tunanin zata taya saba, shiyasa sanda takama harshensa tana tsotsa a hankali, yaji gaba ɗaya ya ruɗe haɗe da zaucewa, jiyake kamar awata duniyar aka tsoma shi.. Yanayin yanda yake romancing ɗinta ne yasa har kuka sai da tayi masa wanda batasan na menene ba, jitakeyi kamar kan nipples ɗinta zasu cire, tsabar anbasu kyakkyawan sucking.
"wallahi doctor ma mugu ne" tafaɗi haka acikin zuciyarta..... Yau dai ba iya Dr.Sadeeq bane kaɗai yaji daɗin kasancewarsu tare ba, hadda ita kanta me daɗi'n nasa, sai dai kuma gaba ɗaya zautar dashi takeyi, yauma da ƙyar yasamu ya iya dawowa cikin duniyarmu, bawai don yasoba saidon gudun wahalar da ita... A hankali yasa hanu yashafa gashin kanta, haɗe da manna mata kiss akan goshinta, Zahrah dake kwance luf acikin ƙirjinsa ta lumshe idanunta haɗe da sake cusa kanta acikin ƙirjin nasa..
"I'am sorry me daɗi na na gajiyar dake ko? ba laifi na bane, inata so nayi controlling ɗin kaina amma nakasa, ke ɗince kin cika da...." saurin toshe masa baki tayi haɗe da sake ɓoye kanta acikin ƙirjinsa, kunya takeji tsantsa idan yaƙirata da sunan me daɗi'n nan, sai taji gaba ɗa tazama wata iri da ita.. Tsotsan hanunta dake kan bakinsa yasoma yi, da sauri tacire hanun nata haɗe da tashi zaune, bargo ta rufa ajikinta tayi toilet da sauri gudun kar ya tsaidata, jingina tayi da jikin ƙofar toilet ɗin tana sauƙe numfashi ahankali, gaba ɗaya abun daya wakana a tsakaninsu ne yashiga dawowa cikin kanta, tanaso ƙwarai taga tana farantawa mijinta rai, zatayi iyaka ƙoƙarinta wajen ganin tayi yaƙi da zuciyarta, wajen ganin ta basa farinciki me ɗorewa yanda ya kamata. Wanka tayi haɗe da zura rigan wanka tafito...
Tsaye tagansa daga shi sai 3 guater jeans ajikinsa, kallo ɗaya tayi masa tayi saurin ɗauke kanta, har yanzu bata taɓa amincewa yaga tsiraicinta cikin haske ba, sannan haka itama bata taɓa tsayawa takalli jikinsa acikin haske ba komai sunayinsa ne acikin rashin wadataccen haske, "Jikinsa yanada kyau" tafaɗi haka acikin zuciyarta haɗe da ɗan satan kallon 6 packs ɗin dake kwance akan cikinsa.
Raɓawa yayi ta gefenta yashige cikin bathroom ɗin fuskarsa ɗauke da wani irin murmushi.
Wata ƴar ƙaramar riga wacce ta tsaya iyaka guiwarta kawai ta sanya haɗe da sanya igiyoyin dake gaban rigar ta ɗaure cikinta, haurawa tayi kan bed ɗin ta kwanta.. Yana fitowa yakuma sanya wani 3 guater jeans ɗin haɗe da feshe jikinsa da turare.. Wutan ɗakin yakashe yakunna musu na bacci, hawa kan gadon yayi haɗe da jawota jikinsa, kwanciya ajikinsa yanayi mata matuƙar daɗi shiyasa aduk sanda yajawota jikinsa bata bijirewa. "Kinyi addu'a?" yatambayeta.
Kai kawai ta ɗaga masa alamar "Eh" addu'a yayi shima ya shafa kana ya lumshe idanunsa, ahankali yake shafa bayanta, cikin mintuna ƙalilan bacci ya ɗauke ta, sannu sannu shima bacci me nauyi ya ɗaukesa....
*****
Washe Gari.
Ƙarfe 5 dai dai jirginsu ya sauƙa acikin Nnamdi Azikwe International airport.
A hankali yake taka matattakalan sauƙowa daga cikin jirgin, sanye yake da riga da wando irin na sanyi navy blue colour, hatta takalman dake sanye a ƙafafunsa navy blue colour ne, yayi kyau sosai yaƙara haske, sai dai kuma sosai rama ta bayyana kanta ajikinsa. Yana gama saƙƙowa daga kan matattakalan yanufi wajen da motocin da sukazo ɗaukarsu ke fake, 4matic yabuɗe yashiga haɗe da hakincewa agidan baya, bayasan damuwa shiyasa bayason shiga mota ɗaya dasu Dad ɗinsa.. Harsuka isa gida tunani yakeyi, maiya kamata yayi? sai kuma yanzu daya dawo yakeji gaba ɗaya Nigeria'n tayi masa ƙunci haɗe dayi masa duhu,daya kulle idanunsa Zahrah kawai yake gani... Yana fita daga cikin motar direct ɓangarensa dake cikin gidannasu ya nufa. Falo'n sa tsab-tsab yake tamkar wanda wani yake rayuwa aciki, bedroom ɗinsa ya wuce, yana shiga yaƙarasa gaban wani tangamemen hotonta da yasa aka masa kalanda (Calender) dashi yakafa ajikin bangon ɗakin, rungume ƙaton kalandan yayi haɗe da lumshe idanunsa.
"I really Miss you My Zahrah!"
ya faɗi haka cikin murya me sanyi da kuma tsananin rauni, hanu yasanya yashafa daidai saiti laɓɓanta dake jikin hoton calender'n.
"Bana tunanin zan daina kewarki Zahrah na, tunaninki yazama abincin ruhina, inasonki sosai, lokaci yayi daya kamata ki dawo gareni, muyi rayuwar auren mu cike da tarin farinciki, nadaina komai Zahrah shan giya, zina, duk na daina please ke nake jira har yanzu, ina fata baki bawa wanina kanki ba?" yanayin yanda yake magana da hoton idan ka gansa kaitsaye dasunan mahaukaci zaka ƙirasa, domin kuwa me cikakken hankali bazaiyi haka ba.. Wayarsa ya ɗauka yayi dialing number'n Abid, bugu uku Abid ya ɗauki wayar baijirayi abun da Zaid ɗin zaice ba yace
"Wow surprise kenan?"
Ƴar ƙaraman tsuka Zaid yayi cikin muryarsa me rauni yace "Inason ganinka Abid, yanzu agidan mu please!" baijirayi me Abid ɗin zaice ba ya katse wayar haɗe da cilla wayartashi kan gado, yasan Abid bazaiƙi zuwaba shiasa baijirayi amsar saba yakashe ƙiran. Zama yayi akan wata kujera dake cikin ɗakin, kan ɗan madaidaicin fridge'n dake aje cikin ɗakin ya maida idanunsa, jiyake kamar yatashi yaje ya ɗau wine ɗinsa yasha, sai dai kuma wata zuciyar tana gargaɗinsa da cewa, Zahrah bataso, tun randa ta gayamasa wata baƙar magana akan shan wine da yake, bai ƙara shaba harkuwa rana me kamar ta yau, duk da kuwa irin azabtuwan da yakeyi idan baisha wine ɗin ba, saboda yariga daya saba. Shiru kawai yayi haɗe da kama kansa ya rumtse idanunsa.. Abid ne yaturo ƙofar ɗakin yashigo bakinsa ɗauke da sallama, ciki ciki Zaid ya amsa masa sallaman haɗe da watsa masa idanunsa da sukayi jajur dasu.. Cike da mamaki haɗi da tsoro Abid ya matso kusa da Zaid da ɗan sauri.
"Zaid meke damunka haka? yaushe kuka dawo? yajikin naka?" duka waƴannan tambayoyin Abid yayiwa Zaid su a lokaci ɗaya kuma duk amsarsu yake nema idan zai samu..
"Abid nakasa mantawa da ita, itace nutsuwar tunani na, banajin zan iya kaiwa lokaci me tsawo batare da na sanyata acikin idanuna ba, Inasonta sosai kai kasani!"
Kallon Zaid kawai Abid keyi yamarasa me zaice masa.. Kallon ɗakin yashiga yi sai alokacin ya Lura da maka makan hutunanta dake manne ajikin bangon ɗakin Zaid ɗin,wasu zane ne wanda Zaid ɗin yayi wasu kuwa hotunanta ne. Wani irin tausayin Zaid ɗinne ya tsirga masa me tsanani, shidai bazaice baitaɓa soyayya ba, amma kuma baita ɓayin kwatan kwacin irin wannan son me tsanani da Zaid keyi ba. Zama yayi akan kujeran dake fuskantar na Zaid, hanun Zaid ɗin yakamo haɗe da cewa "Kazama jarumi Zaid, kada kamanta fa yanzu Zahrah matar wani ce kuma...."
"Ya isheka haka Abid!!" Zaid ya katse Abid cikin tsawa sosai.
"Matar wani, Matar wani, abun da kuke ta faɗa kenan, meyasa ni bazaku duba halin danake ciki ba? shikenan don tana matar wani sai nadaina sonta? kafun wanda kuke ikirarin matarsace yasota nine nan nafara sonta, kada kataɓa tunanin zan daina son Zahrah Abid, bakuma zan taɓa samun nutsuwa ba harsai Zahrah ta zamo mallakina, kataimakeni Abid kazo muje gidanta mu ɗaukota tazo nan mu rayu tare nasan itama tana sona!" cikin murya me tsananin rauni yake faɗan maganar..
Kai kawai Abid yake girgizawa azuciyarsa kuwa wutar tausayin Zaid ne ta kunno, So yamakantar da zuciyar Zaid yasanya harya kasa tuna cewa Zahrah a yanzu ta haramta a garesa, shi duk iskancinsa baya tunanin Zaiso matar da take da aure, dukansu shida Zaid sunsani cewa shangiya da zina duk haramunne amma kuma saboda son zucia irin tasu suke aikatawa, yanzu kuma ga wani sabon saɓon da Zaid yafito dashi, yana goya masa baya akan komai, amma a wannan karon kam baya tunnin zae goya masa baya yaci gaba da son matar aure, haƙiƙa Zahrah takai macen da kowani ɗa namiji zai sota, amma kuma tunda ayanzu tazama mallakin wani babu amfanin Zaid yata takura kansa akanta. "Zaid!" Abid yaƙira sunansa araunace. Kansa kawai ya ɗago ya kallesa batare dayace dashi komai ba.
"Kada kaga laifina Zaid, mun hau wani mataki da yanzu dole ne mufaɗawa kanmu gaskiya, menene ribar da zakasamu idan kacigaba da dakon soyayyarta acikin zuciyarka? tazarar dake tsakanin ka da Zahrah a yanzu yanada matuƙar yawa, tana tare da mijinta kuma nasan zuwa yanzu tajima da zama shi kuma shima yazama ita, me yasa to kowannan bai isa yasanya kacireta acikin zuciyarka ba, akoda yaushe kada kana tunanin cewa wai Zahrah zata dawo gareka, so ne yasa mijinta ya aureta, kaga kenan haka nan kawai bazai rabu da ita ba, kasa aranka ma idan ƙaddara ta rabasu babu yiwuwar Zahrah zata amince ta aureka, kai da kanka kasan haka amma zuciyarka tana yaudaranka, haƙiƙa nima shaidane akan cewa har yanzu Zahrah tana sonka, amma hakan bawai yana nuni da cewa zata iya kashe aurenta ta aureka ba ne, kai koma da ace tafito agidan aurenta to bana tunanin Zahrah zata amince ta aureka, kamanta da ita Zaid, kasawa zuciyarka salama, akwai mata da yawa acikin ƙasarnan dama sauran wasu ƙasashen kasamu wata kabawa ajiyar zuciyarka, na tabbatar watarana komai zai zamo labari!" Abid yaƙare maganar yana me dafa ka faɗan Zaid almar son ƙarfafa masa guiwa..
Wata tsuka me ƙarfi Zaid yaja haɗe da ture hanun Abid dake kan kafaɗansa... har abada bazai daina yiwa wanda yace yarabu da Zahrah kallon mahaukaci ba, wai Zahrah'nsa ake so yamanta ya daina sonta, sai yaushe mutane zasu gane cewa cire so bakamar cire takalmi bane? miƙewa yayi daga zaunen da yake haɗe da shigewa cikin bathroom ko sake kallon inda Abid ke zaune baiyi ba.. Ajiyar zuciya Abid ya sauƙe haɗe da gyara zamansa akan kujeran, yana nan yanajiran fitowarsa koda awa ɗaya zai share a banɗakin bazai tafiba saiyajirasa, Zaid bayason gaskiya wani lokaci, kuma kozai mutu saiya faɗamai gaskiya, ae soyayya ba hauka bane, son matar aure mezai jawo maka inbanda wahala da ƙarin zunubai....
Zaid kuwa yajima tsaye ruwa na fitowa daga shower yana dukan jikinsa.... Ɗaure da towel a ƙugunsa yafito daga cikin bathroom ɗin, kallo ɗaya yayiwa Abid yaɗauke kansa, Abid na kallonsa har yagama shafa man lotion ajikinsa...
"Saboda nace kamanta da Zahrah shine kake fushi dani? kai kanka kasan abun da kakeyi ba daidai bane Zaid sannan....."
"Ya isa Abid!" Zaid ya katsesa aɗan kausashe.
Murmushi kawai Abid yayi haɗe da sa kai yafice daga cikin ɗakin, yasan Zaid ya hau sama bazai taɓa sauraransa ba, wanda yayi nisa bayajin ƙira.
****
Tun fitarsa ta shige cikin kitchine yau bataso ya sayo musu abinci tafiso ta girka musu da kanta, fried rice tayi wanda taji zallan tsokan kaza, da kanta ta haɗa shaka ta sanya acikin fridge, takammala komai yanzu saura kawai tayi wanka.. Ƙaran wayarta take ta jiyowa, da sauri tanufi ɗaki inda wayartata take. Wata number ce special ke yawo akan screen ɗin wayar, ɗan tsayawa tayi tana ƙarewa number'n kallo, har ƙiran ya katse bata ɗauki wayarba, wani ƙiranne kuma sake shigowa.... A hankali ta ɗaga wayan ta kara akan kunnenta.
"Zahrah!!!" taji wata murya wacce bazata taɓa mantawa da itaba ta ƙira sunanta, jikinta ne yasoma rawa yayinda bugun zuciyarta yaƙara tsananta shin dagaske ne kokuwa kunnuwanta ne basuji da kyauba, kusan mintuna biyar ba asake cewa komai daga cikin wayarba haka kuma itama bata ce komaiba..
"Wa....y..e?"
tayi tambayar cikin wararrun kalmomi yayinda tsoro ke sake ɗarsuwa acikin zuciyarta.
"Zahrah na! me yasa zaki barni? kin barni cikin ƙunci da tarin damuwa, yazanyi da soyayyarki ne Zahrah, bazan iya rayuwa ba idan babu ke, please ki taimaki rayuwata dakuma zuciyar da ta jima da matowa akan ƙaunarki!!"
Jikinta ne gaba ɗaya yaɗauki rawa harbatasan sanda wayar ta zame daga hanunta ba, take ta faɗi ta tarwatse a ƙasa. Itakanta batasan sanda ta zame ta durƙusa guiwowinta a ƙasa ba, hawayene suka shiga fitowa daga cikin idanunta. "Zaid" shine sunan da take ta nanatawa acikin zuciyarta, sai yaushene Zaid zai barta ta huta tayi rayuwar aurenta cikin nutsuwa? anya kuwa Zaid baisamu matsalan ƙwaƙwalwa ba? ta tambayi kanta, shiru tayi haɗe da lumshe idanunta ƙirjinta kuwa har yanzu bai daina bugawa da sauri ba.
Cikin tsananin mamaki yake kallonta, da sauri ya ƙaraso inda take durƙushe haɗe da tsugunnawa yaɗaura hanunsa akan kafaɗunta
"Meke faruwa?" yatambayeta cike da kulawa.
Da sauri tabuɗe idanunta da suke a lumshe, batasan yaushe yashigo ba.
Kallonta yakeyi sosai da alama amsa yakeson ji daga bakinta.
Dasauri tashiga goge hawayenta haɗe da tashi tsaye, kallonta yakeyi harta shige cikin toilet, idanunsa yasauƙe akan wayarta wanda ta tarwatse akan tiles gaba ɗaya ma screen ɗin wayar ya fashe, mamaki haɗi da ɗaurewar kaine matuƙa suka kamashi, "Meya faru? yaganta tana hawaye gakuma wayarta daya gani aƙasa a tarwatse" yayi mawa kansa tambayar cike da son sanin amsa. Tattare wayar yayi haɗe da komawa kan gado ya zauna zuciyarsa cike fal da tarin tambayoyi..
Zahrah kuwa tana shiga cikin toilet ta soma sauƙe ajiyar zuciya akai-akai, meta aikata hakane, gashi yanzu yazo ya ganta acikin halin damuwa, tasan dole ne shima saiya sanya kansa a damuwa, yanzu idan ya tambayeta metasan zata ce masa, wasu hawayenne suka kuma zubowa daga cikin idanunta, da sauri ta sanya hanu ta share.. Haka tayi wanka duk tanajin zuciyarta babu daɗi, ɗan ƙaramin towel ta ɗaura ajikinta, wanda yatsaya a iyaka cinyarta. A hankali ta buɗe ƙofar bathroom ɗin tafito, karaf idanunsu suka haɗe waje guda, da sauri ta kawar da kanta gefe, haɗe da nufar wajen drawer.. Kallon santala santalan cinyoyinta da suke bayyane a fili yashiga yi, wani iri yaji acikin jikinsa, da sauri ya ɗauke kansa..
Ganin da tayi cewa baya kallonta ne yasanya tayi saurin zura dogon wando na pencil jeans haɗe da wata farar top shirt me kyaun gaske ajikinta, yaune karo na farko da ta fara sanya irin waƴannan kayan ajikinta, ita kanta saitaga ta burge kanta domin kuwa hips ɗinta sunfito acikin wandon sunyi ɗas dasu kamar wanda aka zana.. Kasa daurewa yayi saida ya kafa mata idanunsa, sosai tayi masa kyau baitaɓa ganinta acikin irin wannan shigar ba, ta ɗau hankalinsa ƙwarai lallai Zahrah macece har mace komai nata me kyau ne... Tana tsaka da shafa turare ajikinta taji yaƙira sunanta. Tsayawa tayi cak daga abun da takeyi haɗe da juyowa sai dai bata kallesa ba ta amsa ƙiran dayayi mata.
"Zonan!" yace da ita ata ƙaice.. Ahankali tashiga takawa harzuwa inda yake, tana ƙarasawa garesa ta durƙusa a ƙasa haɗe da sunkuyar da kanta tana me wasa da yatsun hanunta.. Hanunta yakamo haɗe da jawota jikinsa ya zaunar da ita akusa dashi, cike da kulawa haɗi da lallami yashafa kumatunta yace "Kinyi kyau"
Tsintar kanta tayi dayi masa murmushi kawai...
"Meke damunki? Sannan menene dalilin dayasa naga wayarki a fashe gaba ɗaya kuma tatarwatse?"
Kanta tashiga girgizawa alaman babu
"Kinsan banason ƙarya, menene dalilin da yasa zaki ɓoyemin damuwarki? kada ki manta yanzu bake kaɗai kike iko da kanki ba, nima nan inada iko dake, saboda haka na cancanci ki sanardani damuwarki, ni mijin kine bazan taɓa son naganki acikin damuwa ba!" cike da lallashi ya ƙare maganar.
Mezata faɗa masa? tace masa Zaid ne yaƙirata a waya ko me? ko kuma tace masa hawayen da takeyi duk akan Zaid ne?
"Dagaske nake bakomai, na ɗaga wayar hanuna da kumfa shine ta suɓuce ahanuna tafaɗi" tsintar kanta tayi da basa wannan amsar, duk da cewa ƙarya ba ɗabi'arta bane amma yazama dole yau tayi, saboda sanar dashi gaskiyan lamarin daya faru bashida wani alkhairi saidai ma ransa ya sosu.
Ajiyar zuciya yasauƙe haɗe da jinjina kansa "Naji amma meyasaki kuka?"
Jitayi gabanta ya faɗi amma saita dake tace "Kuka nake saboda na fasa wayata"
Ɗan guntun murmushi yayi sam bai gamsu da maganganunta ba, amma kuma yazaiyi tunda ta ɓoyemasa gaskiya bazai tursasata ba..
"Saboda wayarki ta fashe kawai shine kike kuka? har yanzu dai ke yarinyace ƙarama Zahrah, amma mene abun kuka, idan kikace na saya miki wata kina ganin bazan saya miki bane?"
Kanta ta jinjina alamar "A'a"
"To indai hakane miye na kukan tunda kinsan zansaya miki wata wadda ta fita, kitaimaki zuciyata ki daina sa kanki acikin damuwa please, inasonki banason naga wani abu ya ɓata ranki!"
Raunannun idanunta ta ɗago ta kalleshi, wannan maganar daga cikin ƙahon zuciyarsa yake fituwa, tabbas ita kanta ta gamsu da ƙaunar da doctor yakeyi mata ɗari bisa ɗari, ya cancanci tasakamai da farinciki ne bawai akasin haka ba..
"Ki kwantar da hankalinki, gobe Insha Allah namiki alƙawari zamuje dake ki zaɓi irin wayar da kike so, shikenan?"
Kanta ta ɗaga tana ɗan murmushi, kamar da gaske maganar wayarce a cikin ranta.. Miƙewa yayi yafaɗa toilet, tanajin sauƙar ruwa aƙasa ta sauƙe nannauyar ajiyar zuciya, bataso doctor yasan cewa Zaid yafara bibiyar rayuwarta. Sumu sumu haka ta fice falo.
Tana zaune tayi jigum ya fito daga cikin ɗakin, sanye yake da blue ɗin wando kalan nata, sai dai nasa na maza ne babu ado kamar nata, saikuma farar polo shirt, murmushi tayi domin kuwa yayi mata kyau sosai, shima murmushin yayi mata haɗe da kashe mata idanunsa ɗaya...
Ita da kanta ta zuba musu abinci, yanaci yanata zuba mata santi, har batasan lokacin da tarin damuwar dake cikin ranta suka kau tasoma ƙyalƙyalewa da dariya ba ...
****
Zaid ne zaune agaban Dad ɗinsa ya sunkuyar da kansa ƙasa, magana Dad ɗin keyi masa amma kuma kwata kwata bayajinsa, hankalinsa da tunaninsa sunyi nisa sosai wajen tunanin Zahrah, muryarta dayaji ɗazu shiya kara rikita masa tunani, baisauraran Dad dake yimasa bayani amma duk da haka yaji abun da Dad ɗin yafaɗa na ƙarshe, cike da ƙuncin rai haɗe da tsananin mamaki yake kallon Dad ɗinnasa cikin wata murya me ɗaci yace
"Aure fa kace Dad? ni ɗin, kuma da wata ba Zahrah ba?"
Cikin takaici Dad yake kallon Zaid ɗin, wato tunkan ayi nisa ma yafara nuna masa cewa hakan bazai yiwuba kenan.
"Natabbatar kajini, kuma aure babu fashi!" Dad yafaɗi haka a ƙufule, domin kuwa shima yafara gajiyawa da halayyan Zaid na rashin hankali, taya zaka je kana yiwa matar wani soyayya me tsanani irin haka.
Wani murmushi Zaid yayi me matuƙar ciwo haɗe da sanya haƙoransa ya ciji laɓɓansa.
"Bazan iyaba Dad, kaima kafi kowa sanin hakan, aduniyar nan mace ɗaya kawai nakejin zan iya rayuwar aure da ita, bakowa bace kuma Zahrah ce, saboda haka please Dad maganar wani aure na da wata kabarshi don banaso, idan kuma ka matsa shikenan, amma idan kuka tsinci gawanta nayi mata mugun illa kada ku zargeni kufara zargin kanku" yana kaiwa nan azancensa ya tashi tsaye yafice daga falon mahaifinnasa.. Baki a wangale haka Dad yabi Zaid da kallo har yaɓacewa ganinsa..
"Lallaima kuwa Zaid ya ɗauko babban al'amari, amma kuma wannan karon sam bazai lamunta masa ba aure dole sai yayi masa, acikin satin nan ma kuwa" Dad yafaɗi haka acikin zuciyarsa...
Zaid kuwa yana fita a ɗakin Dad direct motarsa yashiga, dagudun gaske ya ja motar yafice daga cikin gidan, tafiya yake akan titi amma zuciyarsa ƙuna takeyi masa, har wani ɗaci yakeji a maƙoshinsa, wayarsa ce tayi wani ɗan gajeren ƙara alamar shigowar saƙo (Message), da sauri ya ɗauki wayar ya duba, domin kuwa tun ɗazu dama saƙon yake jira, adireshi ne na gidan da Zahrah take aka turo masa.. Wani mugun murmushi naga yayi haɗe da ɗan dukan kan steering motar, lallai dole zai cimma burinsa ne kota halin yaya kuwa...
Faka motan yayi yana me ƙaremawa gaban gidan kallo, gidane me kyau da kuma aji, dagani kasan ankashe kuɗi wajen tsara gidan, amma Zaid dake kishi yacika masa zuciya sam baiga wani kyawun gidan ba, saima ji da yayi ya tsani gidan.. Idanunsa ya tsaida akan tankamemen gate ɗin gidan tamkar wanda yake karantan wani abu, a hankali ya buɗe murfin motar tasa yafito waje, cikin takunsa na isa yashiga takawa harzuwa wajen gate ɗin....... (🤔Anya zaishiga kuwa?hmmm inaga dai yau Zaid aƙasam kanta zai kwana😂)
*(Kuyi haƙuri dan Allah kwana biyu kunjini shiru wallahi neighbour ɗitace tarasu ranan friday da dare shiyasa kuka jini shiru, naji mutuwar ajikina wallahi sosai shiyasa nakasa koda yin typing ɗinne ma, please kusata a addu'anku Allah ubangiji yayi mata rahama, yasa aljanna tazamo makoma a gareta Ameen thumma Ameen. Ina me ƙara neman afuwarku sosai 🙏🙏🙏)*
*Tuesday 28/January/2020*
*Fatymasardauna*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 100 to 101*
Tsayawa yayi yana me ƙarewa gate ɗin kallo, idan da zaibi son zuciyarsa ne, to tabbas da shiga cikin gidan zaiyi, amma kuma saidai wata zuciyar tana gargaɗinsa da kar ya shiga cikin gidan, bawai kuma don yanajin tsoro ba, kawai dai yana me tausayawa kansa ne, yasan idan yaga Zahrah dole sai ciwonsa yasake motsawa, duk da yanzun ma bawai ciwon nasa ya kwanta bane, komawa yayi cikin motarsa yazauna, haɗe da Kifa kansa akan steering motar, lumshe idanunsa yayi sai kawai ga hawaye suna fitowa daga cikin idanun nasa, wai yau shi Zaid ke kuka akan mace, lallai rayuwa juyawa take, gashi shikam tajuyo masa da saɓanin tunaninsa... Ƙarar motar dayaji shi yasanya sa ɗago kansa yakai kallonsa wajen gate ɗin gidan, ko ba a faɗa masa ba yasan motar RIVAL ce (wai Dr.Sadeeq ne rival ɗin nasa) balle ma kuma yagansa acikin motar, wani irin abune yazo ya tokarewa Zaid maƙoshinsa, baƙinciki, haushi, takaici, da kuma tsanar doctor ne duk suka haɗe masa waje guda. Ji yake kamar yafita acikin motar yaje ya shaƙo sa kozaiji salama acikin ransa.. Har motar doctor tashige cikin gidan bai ɗauke idanunsa akan gate ɗin ba, da sauri ya rumtse idanunsa lokacin da motar tagama shigewa cikin gidan aka kullo gate ɗin gidan, da ƙarfi ya danne lips ɗinsa haɗe da buga steering motar, yanaji yana gani wani zai yi masa rayuwa da Zahrah'nsa. "Yanzu Allah ne kaɗai yasan shigarsa mezaiyi mata, wata ƙilama rungumeta zaiyi, wataƙila kuma har kiss zaice zaiyi mata" wata zuciyar tafaɗa masa haka. Da ƙarfi ya shiga dukan steering motar, yana me jijjiga kansa, ƙwaƙwalwarsa bazata iya ɗaukar masa wannan tashin hankalin ba, jiyake komai na duniyan nan najuya masa, Allah yasa abun da zuciyarsa ta faɗa masa bahakanne zai kasance ba, bazai taɓa iya jurewa ba, hanunsa ya ɗaura adaidai saitin zuciyarsa haɗe da sake rumtse idanunsa, zafi yakeji haɗe da zogi acikin ƙirjinsa, da ƙyar ya'iya tada motar ya cillata kan titi a zafafe, gudu sosai yakeyi akan titi babu ruwansa da waƴanda suke gabansa ko suke bayansa, idanunsa sun rufe sosai.. Ikon Allah ne kawai yakawoshi gida, amaimakon yawuce ɓangarensa sai ya wuce ɓangaren mom ɗinsa..
Hajiya Safara'u ce tsaye agaban dinning table tana shirya abinci, batare da sanin shigowarsa ba saiji tayi anrungumeta ta baya, ƙamshinsa kaɗai taji tagane cewa tilon ɗanta ne, mamakine tsantsa ya bayyana akan fuskarta yaushe rabon Zaid yazo ya rungumeta haka? kansa ya ɗaura akan wuyanta haɗe da sauƙe ajiyar zuciya, wani abu me ɗumi da taji yana sauƙa akan wuyanta ne yasanya tayi saurin juyowa garesa, batayi mamakin ganinsa ahaka ba amma ƙwarai tayi mamakin ganin yanda hawaye ke zuba daga cikin idanunsa.
"Zaid!!"
taƙira sunansa cike da tsananin mamaki haɗe da tashin hankali.
Jajayen idanunsa ya ɗago ya kalleta haɗe da sake rungumeta.
"Mom nakasa jurewa, bazan iyaba, please ki ciremin soyayyarta acikin zuciyata, koda zan samu nutsuwa na minti ɗaya acikin ruhi na!" cikin matsanancin rauni yake maganar gaba ɗaya yazama abun tausayi yadawo saikace yaro ƙarami..
Ahankali Mom take shafa bayansa haɗe da jinjina kanta, tabbas da ace akwai yanda zatayi da ta cirewa Zaid soyayyar Zahrah acikin zuciyarsa, bazata iya jure ganin hawaye da kuma damuwar ɗanta ba.
Kamasa tayi suka zauna akan kujera, kansa yaɗaura akan cinyarta yayinda ita kuma take shafa tarin sumar dake kansa .
"Nakanji ciwo acikin zuciyata idan naganka kana kuka Zaid, bansan wani irin soyayya kakeyiwa Zahrah ba, amma kuma bamu da yanda zamuyi Zahrah matar wani ce yanzu" Mom tafaɗi haka cike da lallashi.
"Mom ki taimakeni, zafi nakeji acikin zuciyata, yanzu kenan bazan sameta ba? shikenan har abada saidai naƙare rayuwata a haka babu ita? bazai yiwuba Mom, dana sani tun farko daban yaudareta ba, dana sani tun farko dana aureta, duk nine najawa kaina ni da kaina na haramtawa kaina ita, nasan dabanyi mata fyaɗe ba dayanzu na sameta, nine fa nayi mata fyaɗe mom, meyasa nayi haka mom? kaicona yau nayi danasanin yi mata fyaɗe da nayi fiye da ko yaushe!" yafaɗi haka yana me sake fashewa da kuka kamar yaro..
Mamaki haɗi da ruɗani dakuma tsantsar kaɗuwa su suka bayyana akan fuskar Mom, kallonsa kawai takeyi zuciyarta na tafarfasa.
"Kana da hankali kuwa Zaid? Fyaɗe fa kace, anya kuwa ƙwaƙwalwarka bata fara taɓuwa ba?"
Sai yanzu yatashi daga kan cinyarta, bayi da wani zaɓi wanda ya wuce yafaɗawa Mom ɗinsa gaskiya...
"Ban haukace ba Mom, dagaske ne nine nayi mata fƴaɗe, nine nan na tozarta rayuwarta, nine nan na fara gurɓata mata rayuwa, na rabata da farincikinta da duk wani jin daɗinta, narufe idanuna naketa mata haddinta alokacin da take tsananin buƙatar taimakona, nayi mata fyaɗe mom nabiye son zuciyata nasan ban kyauta mata ba amma kuma babu yanda zanyi ne yazama dole......"
Tassssss haka mom ta ɗaukesa da wani irin lafiyayyen mari, marin daya matuƙar firgitasa ya ɗaiɗaita tunaninsa, tundayake yataso yayi wayo mahaifiyarsa bata taɓa sanya hanu ta mareshi ba sai yau, kai koda tsawa me ƙarfi bata taɓa yi masa ba, bakinsa ya hangame haɗe da sanya hanunsa akan ƙuncinsa inda ta maresa yana kallonta.
Itakanta mamakin marin datayi masa take, sai dai kuma ranta amatuƙar ɓace yake..
"Kayi mata Fyaɗe? kacuceni Zaid, bantaɓa tunanin zaka iya aikata wannan rashin imanin ga wata ƴa mace ba arayuwa, meyasa? meyasa? idan aure kakeso meyasa bakayiba? kahalakar da rayuwar ƴar mutane, kaicon wannan gurɓataccen halin naka, tabbas yanzu na yarda alhaki ne kawai ke bibiyarka, idan kuwa hakane to wallahi baka ga komai ba arayuwarka, niba azzaluma bace kuma bana zama inuwa ɗaya da mutum meyin zalunci, bansan zuciyarka tayi tauri harhaka ba, dahar kake tunanin aurenta, nayi danasanin tura mahaifinka nemamaka aurenta, ashe kai macucine agareta azzalumi, taya kake tunanin zata amince dakai?" kanta tashiga girgizawa haɗe da juyawa ta nufi matattakalan dake cikin falon ranta amatuƙar ɓace, sam batasan abun da Zaid ya aikata ga Zahrah ba sai yanzu, lallai da ita da kanta zata ɗaukawa Zahrah mataki.
Zaid kuwa har Mom tagama haura step ɗin dake cikin falon, bai ɗauke idanunsa akanta ba, mamakine ya lulluɓesa matuƙa, sake shafa kumatunsa yayi inda mom ɗin ta zabga masa mari, baitaɓa ganin ɓacin ran mahaifiyarsa irin nayau ba tun dayake. Miƙewa yayi yawuce ɓangarensa shi dai idan za amaresa sau million a basa Zahrah to bazai taɓa damuwa ba..
Mom kuwa tana shiga ɗaki wayar Dad taƙira tasanar masa komai, ɓacin ran da Mom tashiga kaɗanne akan wanda Dad ya tsinci kansa aciki, lallai Zaid yamaidashi mutumin banza, dayasan haka tafaru tsakaninsa da Zahrah da baije ne ma masa aurenta wajen Baffanta ba, wannan ma ai rashin ta ido ne, amma zaiyi maganinsa ne, jibi jibin nan zai ɗaura masa aure kuma dolensa ne yazauna da matar, hukuncin da Dad ya yankewa Zaid kenan.
*****
Tun jiya suka koma makaranta amma bata samu daman zuwa ba, doctor da kansa yace ta bari sai yau... Buɗe ƙofar ɗakin tayi ta fito, dagani sauri take, ta shirya tsab cikin riga da zani na atamfa ta rufa jikinta da wani ƙaton mayafi me ɗan kauri..
Kallonta yakeyi sosai, take yaji wani irin kishinta ya lulluɓemai zuciya, duk da ba wani kwalliya tayi sosai ba, amma shikam baijin zai barta tafita ahaka, kishi yake wani ya ganemai fuskar mata, ganin yanda yake kallonta ne yasanya taɗan shagwaɓe fuska haɗe da karyar da wuyanta gefe, don daganin yanda yake kallonta tasan akwai magana abakinsa.
"Banjin zan barki kifita a haka, maza je ki ɗauko hijab kisanya" yafaɗi haka cikin dakiya da'alama babu wasa a lamarin nasa. Bata musa masa ba ta koma ɗaki, hijab ta ɗauka ta sanya wanda ya tsaya iyaka guiwarta, tana fitowa yasake kafeta da idanu, har yanzun ma dai baijin zai iya barinta tafita ahaka, gaba ɗaya ma shi kullum gani yake tana ƙara yi masa kyau, nana gaba kaɗan zai hanata fita ne ma kwata kwata.
"Dan Allah yanzu kam kabarni natafi kaga fa zanyi latti!" tafaɗi haka cikin shagwaɓa.
Marairaice fuska yayi haɗe da sanya hanu yashafi sajen dake kwance akan ƙuncinsa, ba tare dayace komai ba yamiƙe tsaye yanufi hanyar fita daga cikin falon, ganin haka yasa itama ta rufa masa baya da sauri...
Tafiya suke amma yaƙi cewa da ita komai, kallon yanda ya haɗe fuska tayi, sai kawai tasaki dariya, wai ahakan shi fushi yakeyi da ita, sam yanayin fushi bayayi masa kyau akan fuskarsa.
"Meyasa bazaka kulani bane wai? idan makarantar ne bakaso sai ka maidani gida, amma kadaina fushi bakayin kyau kwata kwata idan kana fushi" tafaɗi haka tanaɗan dariya.
Sai alokacin ya juyo da kansa ya kalleta. "Ni ba fushi nake ba" yafaɗi haka cikin cushewar murya.
Murmushi kawai tayi batare da ta sake ce dashi komai ba, saima kwantar da kanta da tayi ajikin kujeran motar tana kallon yanda mutane suke ta hada hadan su.
A dai dai inda yake ajiyeta lokutan baya yauma anan yayi parking motar tasa, buɗe murfin motar tayi zata fita, da sauri ya riƙo hanunta, juyowa garesa tayi tana ɗan murmushi, shima murmushin yayi mata haɗe da matsowa daf da ita, kiss ya manna mata akan kumatunta haɗe da cewa
"Ki kulamin da kanki"
Tsadadden murmushinta tayi masa haɗe da jinjina kanta alamar zata yi yanda yace. Sai da yaga shiganta cikin hall ɗin da zasuyi lecture kafun ya ja motarsa yabar haraban makaranta baki ɗaya..
Tana shiga cikin hall ɗin suka ɗinke ita da Husnah sukaita hira, kafun lecturer yashigo....
Ƙarfe biyar na yamma suka kammala duk wani lecture ɗin da suke dashi, har bakin motar doctor ɗin Husnah ta rako ta..
Ƙoƙarin janta da hira yake amma tayi masa shiru, saboda gaba ɗaya agajiye take, dolensa shima ya ƙyaleta harsuka isa gida.
Da ruwan ɗumi tayi wanka, tana fitowa ta zura wata riga doguwa marar nauyi ajikinta, haɗe da faɗawa kan gado, numfashi kawai take sauƙewa na gajiya, mintuna kaɗan bacci ɓarawo ya saceta, koda Dr.Sadeeq ya shigo yasamu tana bacci baiyi yunƙurin tashinta, falo yakoma yayi zamansa....
*****
Bayan kwana uku.
Yau kusan kwanansa uku kenan a guest house ɗinsa yake kwana, gaba ɗaya abubuwan duniyane suka haɗu sukayi masa yawa, bayacin abinci a iya tsawon kwanakin nan, gashi ciwonsa ya dawo sosai, daga zaran yayi tari sai jini, magungunan nasa ma yadaina sha, addu'a yake Allah yasa wannan ciwon nasa yazamo ajalinsa ko zai samu sauƙin raɗaɗin dayakeji acikin zuciyarsa...
Horn ɗin motarsa yake dannawa a ƙofar gidannasu kamar zai tashi sama, da sauri me gadi ya wangale masa gate ɗin gidan ya tura hancin motarsa ciki, ko kyakkyawan parking baiyi ba, haka yafito daga cikin motar yanufi ɓangarensa, yana shiga falonsa yasoma ƙoƙarin cire rigar jikinsa, dai dai lokacin wata ƴar mata shiyar budurwa ta buɗe ƙofar ɗakin dake kusa da bedroom ɗinsa ta fito, tsananin mamakine yakashe Zaid, kallon tuhuma kawai yake aika mata dashi.
Yanda ta gansa sai da taji gabanta ya faɗi amma dayake dama tayi masa farin sani yasanya taɗan wayance haɗe da sakar masa murmushi..
Kallonta yakeyi daga samanta har ƙasanta, "wace ƴar iska ce haka da har tasamu daman shigo masa ɓangarensa har da kuma kutsawa cikin ɗaki?" tambayar da yayiwa kansa kenan.
"Wacece ke? Uban waya baki daman shigomin ɗaki?" ya tambayeta murya a kausashe.
Sai da taji tsoro amma kuma hakan bai hanata bayyana murmushi akan fuskarta ba. Wani ƙululun takaici da baƙincikine suka cika zuciyar sa, badon komai ba sai don murmushin dayaga tanayi masa.
"Dan ubanki bamagana nake miki ba!" ya kuma faɗa cikin tunzura.
Yanzu kam ta tsorata dashi sosai da sauri ta juya zata koma cikin ɗakin, taku ɗaya yayi ya fincikota, yana juyo da ita ya bata kyakkyawan mari akan fuskarta wanda ya sanyata fasa wata uwar ƙara, sosai zafin marin ya ratsata..
"Bazaki faɗamin mikikeyi a cikin ɗakin nan bako dan ubanki, inaga sainaci uwarki tukun zakimin bayani, banza me kama da fara!!" yafaɗi haka yana me ƙoƙarin zare belt ɗin dake jikin wandonsa, da'alama dai so yake ya jibgeta.
"Kada ka kuskura ka taɓa ta inagaya maka idan bahaka ba ranka zaiyi mummunan ɓaci!"
Muryar Dad da shigowarsa kenan yakaraɗe gaba ɗaya falon, aƙufule Zaid yajuyo yana kallon mahaifinnasa.
"Dole ne zan daketa matuƙar bata ficemin acikin ɗaki ba, taya ma zakubar wata kucaka tashigomin ɓangarena, dubeta fa ƙazama da ita, wata ballagazar mata, kunfi kowa sanin bana buƙatar ƴar aiki, me yasa to zaku ɗaukarmin? kurasa ma wacce zaku kawomin amatsayin ƴar aiki sai wannan baƙar yarinyar!" Zaid yafaɗi haka yana me nuna ta cike da ƙyama.
"Ba ƴar aiki bace matarkace, kuma wallahi kada kasake kace zaka saketa nafaɗa ma!" Dad ɗinsa yafaɗi haka cikin ɓacin rai, baijirayi me Zaid ɗin zaice ba yasakai yafice daga cikin falon..
Tsananin tashin hankali ne ya bayyana akan fuskar Zaid, kalaman Dad ɗinsa sunyi matuƙar sanyasa cikin mamaki.
"Matata?"
tambayar da ya yiwa kansa kenan, sake kallonta yayi, tana nan tsaye sai raba idanu take kamar mayya, dagani a matuƙar tsorace take..
"Da gaskene abun da Dad ɗina ya faɗa?" yayi mata tambayar babu alaman wasa akan fuskarsa.
Kanta ta jinjina masa alamar "Eh"
Wannan wani irin cin fuskane Dad ɗinsa yayi masa? aure batare da saninsa ba auren dole fa kenan? ae kuwa yau zataci ubanta ne, matsowa yashiga yi daf da ita hanunsa yasanya ya damƙi gashin dokin da akayi mata kitso dashi, yawun dake cikin bakinsa ya tofa mata akan fuskarta, cike da tsananin takaici ya tureta gefe, take ta ƙwalla ƙara domin kuwa kan table na glass tafaɗa daya tureta, baiko saurareta ba ya shige cikin bedroom ɗinsa, yanashiga cikin bedroom ɗin ya buɗe cikin fridge ɗinsa ya ɗauƙo kwalbar alcohol me matuƙar sanyi, da ƙarfi ya ɓalle murfin alcohol ɗin yakafa kwalban abakinsa, saida yasha fiye da rabi kafun yayi wurgi da kwalban gefe, wani irin haushin kansane yakamasa, baisan da yaushe yaɗau kwalbar giyan yakai bakinsa ba, yanaso yadaina aikata duk wani abu dayasan Zahrah bataso amma kuma yau baida wata mafita wacce ta wuce nashan alcohol ɗin, takaicine yasake cika masa zuciya, duk waccar shegiyar yarinyarce tasa sa shan alcohol ɗin don haka dole itama sai ya horata, yanzu idan Zahrah tasan yasha alcohol bazata taɓa jin daɗi ba.. Ɗaukar sauran alcohol ɗin yayi yafice zuwa falo, tananan ƙudundune ajikin kujera sai maƙyarƙyata takeyi, matuƙar tsoron Zaid takeyi, ko yanzu dataga fitowarsa saida gabanta yafaɗi..
Direct wajen da take zaune ya nufa, gashinta yakuma damƙowa haɗe da jawota zuwa tsakiyar falon, bakinta yakamo da hanunsa ya matse haɗe da tura mata kwalbar giyan acikin bakin nata, kuka take tana girgiza kanta amma yaƙi sakinta, adole wai saitasha alcohol ɗin, cikin rashin imani irin na Zaid haka ya danne yarinyar mutane ya ɗura mata giya acikinta da ƙarfin tsiya, sai da yatabbatar ragowan giyan dake cikin kwalbar yajuyemata shi acikinta kafun ya hankaɗata gefe, ganin yanda take kuka kamar ranta zaifitane, yasanyasa fashewa da dariyan mugunta, lokaci guda kuma ya tsume haɗe da kawar da kansa gefe, miƙewa yayi yafice daga cikin ɗakin, azuciyarsa yace "anjima kaɗan wanka zanmiki da ruwan ƙanƙara dan ubanki....."
(🙆♀🙆♀🙆♀🙆♀ Allah yajiƙanki yarinya kinshigo hanun mugu)
*Wednesday/29/January/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 102 to 103*
Kuka sosai Afra keyi, wani irin miji ne haka iyayenta suka aura mata? duk da cewa da amincewa da kuma yardanta akayi mata auren, amma sam bata tsammaci mugunta da shuɗewar hankalin Zaid har yakai haka ba, tun da take arayuwarta bata taɓa kwatanta koda shan codine bane ballantana uwa uba giya, iskancinta baije can ba, duk da cewa itama tana da nata wayewar. Wani irin amai tashiga kwarawa atsakiyar falon, lokaci ɗaya ta harar da duk wani abu dake cikinta, jingina bayanta tayi da jikin kujera tana me da numfashin wahala..
Zaid da shigowarsa falon kenan, yayi saurin toshe hancinsa haɗe da kawar da kansa gefe cike da bala'i yace
"Ke dan ubanki duk girman gidannan kirasa inda zakiyi amai sai a cikin falon nan? ki share wajennan yanzu kafun infito kokuwa idan nafito nasamu baki shareba nasa ki lasheshi yakoma inda yafito, ƙazama kawai, wai ahakane zanyi rayuwa dake mcheeww!" cikin ɓacin rai yaƙare maganar haɗe da shigewa cikin ɗakinsa..
Jikin Afra na rawa ta ɗauko moper tashigayin mopping ɗin wajen, ƙaramin aikinsa ne idan har yadawo yasamu bata gyara wajen ba yasata ta lashe aman, tabbas tasan zai iya, yau kaɗai tafuskanci cewa shiɗin tsananin mugu ne, wanda babu kamarsa, tana gama gyara wajen ta gudu cikin ɗakin da aka sauƙeta, ɗakin dake kusa da nasa, tanashiga ɗakin ta murza key, haɗe da faɗawa kan gado, tasaki wani irin kuka, danasani kawai takeyi acikin ranta, itafa tayarda ta auri Zaid ne saboda dama tuncan yana matuƙar kasheta aduk sanda tagansa sai taji inama dazai zamo nata, sannan kuma gayen akwai kuɗi uwa uba aji, duk da cewa ita ɗinma babanta me kuɗi ne amma baikai na baban Zaid dashi kansa Zaid ɗin ba, lokacin da babanta yazo mata da maganan auren Zaid, daɗine yakusa kasheta ganin irin damar da Allah yabata, ashe bata saniba gidan mutuwa takawo kanta, ita da har jinkanta tasomayi, har ɗagawa takeyiwa ƙawayenta, ita adole ta auri namijin duniya, batasan cewa wahala zata ruska ba, ta ɗauka cewa holewa zatayi, harta fara tunanin ƙasashen da zata sasa yakaita, sai gashi haɗuwarsu ta farko ma da lafiyayyen mari ya tarbeta...
Zaid kuwa yana shiga cikin ɗakinsa yafaɗa kan gado haɗe da lumshe idanunsa, kansa ne yake matuƙar sara mae, tun jiya yakejin ciwon kan, amma yau abun ya tsananta sosai, wata tsuka yaja me sauti, haɗe da sake gyara kwanciyarsa, shi wannan auren ma da aka laƙaba masa kaɗai ya isa ƙara masa ciwon kai, shiba yaro ba, shiba bagidaje ba amma ankama anyi masa auren dole...
******
Tsaye take agaban dinning area, ta kafesa da manya manyan idanunta, yayinda shikuwa baimasan tana kallonsa ba, hankalinsa gaba ɗaya yana ga agogon dayake ƙoƙarin ɗaurawa a tsintsiyar hanunsa.. Bakomai yasa take kallonsa ba, face kyawun da taga yayi mata, shadda ne milk colour ajikinsa ɗinkin riga da wando, rigar ta tsaya iyaka guiwarsa, yayi kyau sosai yasha hularsa light brown wanda taƙarawa kwalliyartasa kyau.. Yana ɗago kansa suka haɗa idanu, da sauri ta kawar da idanunta daga kansa, haɗe da sunkuyar da kanta ƙasa.
Murmushi yayi haɗe da takowa yaƙaraso inda take, hanu yasanya ya rungumota ta baya.
"Namiki kyau ne haka kiketa kallo na?" yatambayeta yana me shaƙan daddɗan ƙamshin jikinta.
Ɓata fuska tayi haɗe da cewa
"Namiji kuma dama yana kyau ne idan yayi kwalliya?"
Dariya maganar ta ta ta basa, juyo da ita yayi yazamana suna fuskantar juna.
"Eh mana bakisan maza sun mafi mata kyau ba?" ya faɗi haka yana me ƙarewa fuskarta kallo.
Idanunta ta waro haɗe da cewa "Maza sunfi mata kyau? cab aikuwa nidai baka fini kyau ba"
Dariya yayi haɗe da ɗan jan hancinta.
"Nafiki kyau sosai ma, nifa banasa jan baki, bana shafa powder, bana sa kwalli, bana kumayin jagira, haka kuma bana wani shafa mai wanda zai sa fatata tayi kyau, komai nawa daga Allah ne, ku kuma mata kullum cikin shafawa da gogawa kuke, kinga kenan dagaske munfiku kyau" yafaɗi maganar yana me ɗan ƙara fito da idnunsa waje.
Duk da tana cikin fushi, amma sai da tayi dariya.
"Kafaɗi komai ma, amma nidai bazan yarda cewa wai kafini kyau ba"
tafaɗi haka tana me ƙoƙarin zame jikinta daga cikin nasa.
Sake riƙeta yayi gam haɗe da cewa
"Dagaske namiki kyau? naga har wani kishi na kike"
Ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba haɗe da shagwaɓe fuskarta.
"Idan nayi kyau kaima baka barina nafita, to me yasa kai kakeson yin kyau ako da yaushe? kana tunanin bazanji haushi bane idan wata ta kalleka!" kafun taƙare maganar ma tuni idanunta sun soma kawo ruwa.
"Eh kumafa hakane, harma kintunamin, akwai wata kuwa a asibitin mu, kullum saitace namata kyau, sannan kuma saitace wai ina matuƙar burgeta, gaskiya nima kuma tana burgeni dan a ƴan kwanakin nan harma na fara tunaninta, to mezakice akanta?" yaƙare maganar yana me ɗaga mata giransa ɗaya.
Baki kawai tasake tana kallonsa yayinda wani malolon baƙin ciki ya tokare mata zuciya. Da ƙarfi ta soma turesa tanason ƙwace jikinta daga nasa.
Ganin haka yasanya yasake riƙeta da kyau haɗe da cewa
"Mekikeyi haka?"
"Kafi kowa sanin abunda nakeyi, inatunanin tsayuwan da kakeyi anan kana ɓata lokacin kane, domin wacce kake muradi tanacan tana jiranka, koba don itane kayi kwalliyar ba? ai bana tunanin ni inada wani amfani a wajenka, ka sakeni kaje tayaba kwalliyar taka banaso na ɓata bata gani ba."
Dagajin yanda take maganar kasan kishine tsantsa kecinta, domin kuwa har hawaye sun gangaro daga cikin idanunta..
Dariya sosai yashiga yi batare daya sake ta ba.
"Kasakeni nace, ai nasan baka buƙata ta!" tafaɗi haka tana me yunƙurin ƙwace hanunta dake cikin nasa.
Da ƙyar ya iya tsagaita dariyan nasa, yashiga dubanta da kyau, yasani dama da sannu zuciyar Zahrah zata nutsa acikin ƙaunarsa sosai, gashi kuma yafara ganin alama tunda har kishinsa ya bayyana acikin idanunta..
Fuskarta yatallafo da tafukan hanunsa haɗe da sanya bakinsa yashiga lashe hawayen dake fitowa daga cikin idanunta.
"Bazan iya jure ganin matata tana kuka ba, ki kwantar da hankalinki kinji me daɗi na, babu wata mace da ta isa ƙwace miki doctor ɗinki, ketawace ni ma kuma naki ne, babu wata kuma danake tunani bayanke kiyarda dani!!" yafaɗi maganar cikin lallausan murya yana me ƙara riƙe fuskarta acikin tafukan hanunsa.
Ajiyar zuciya ta sauƙe wanda harsaida ya bayyana afili, har cikin ranta taji daɗin maganganunsa, amma kuma afili bata nuna hakan ba, ƙoƙarin ƙwace kanta daga jikinsa tacigaba dayi.
"Nine bakyaso ko? shikenan tunda bakyaso nariƙeki" yafaɗi haka yana me sake ta yanufi hanyar fita daga cikin falon. Da sauri ta je ta rungumesa ta baya, wani murmushi yayi haɗe da juyowa gareta yazamana suna fuskantar juna.
"Dan Allah kada ka ƙaramin irin wannan wasan, gashi duk kasa ma naji natsani komai!" tafaɗi haka a shagwaɓe.
Murmushi yayi mata haɗe da sanya hanunsa yaɗanja kumatunta.
"Bazan sakeba, kiyi haƙuri kinji me daɗi na!"
Da sauri ta cusa kanta acikin ƙirjinsa haɗe da sanya hanunta ta mintsineshi acikinsa. Da ɗan ƙarfi yace "Ahhhshhhh!"
Dariya tayi masa haɗe da yi masa gwalo ta wuce zuwa dinning domin dama abinci take haɗawa.
Biyota yayi kan dinning table ɗin suka shirya abincin atare, acikin plate ɗaya sukaci abinci, gaba ɗaya yanzu doctor yagama shagwaɓata abinci ma shiyake bata abaki, har sai ta ƙoshi, tana ajiye cup ɗin ruwan dake hanunta, ta ɗan saci kallonsa, ta lura tun ɗazu yaketa kallonta.
"Kaima nayi maka kyaun ne, kaketa kallona haka?" ta tambayeshi.
Murmushi yayi mata haɗe da cewa
"Ae ni dama kullum kinamin kyau, ke mai kyauce ai ako da yaushe, amma kuma..." baiƙarisa maganar dake cikin bakin nasa ba yayi shiru.
"Amma kuma me?" ta tambayeshi da sauri domin atunaninta ta zaci zaice amma bata masa kyau sosai ne.
"Amma bakyason bani abun daɗi na, please yau ki tausayamin kinji, bazan iya bacci bafa yau idan baki bani ba!" yafaɗi haka cikin sigar shagwaɓa haɗe da ɗanyin ƙasa ƙasa da muryarsa.
Maganganunsa kunya suka bata da sauri ta sanya hanunta ta rufe fuskarta, jawota jikinsa yayi haɗe da sanya bakinsa adai dai saitin kunnenta cikin muryar raɗa yace
"Bazan iya jurewa ba Zahrah, inaso akullum kina bani kanki sau ba adadi, inason kasancewa tare dake ako wani lokaci" bakinta yashafo da hanunsa haɗe da lumshe idanunsa. "Nayi missing waƴannan lips ɗin amma yau zanyi musu sucking na musamman har ma...." bata jirayi jin ƙarshen zancen nasa ba ta ruga da gudu zuwa cikin ɗaki, bazata iya cigaba da sauraran waƴannan manya manyan kalaman nasa ba. Murmushi kawai yayi haɗe da miƙewa yafice daga cikin falon, dama sabiti zaije.
Tanajin fitar motarsa acikin gidan ta sauƙe ajiyar zuciya haɗe da lumshe idanunta, kwanciyarta ta gyara, tana me tuno kalamansa, itakanta tana tsananin son taji ta ajikinsa, musamman idan fatarsu ta haɗe waje guda hakan na haifarmata da wani irin yanayi me daɗin gaske, kallonta ta mayar ga agogon bangon dake kafe acikin ɗakin. Ƙarfe 11 na rana yau take da lecture saboda haka tana da ɗan sauran lokaci, domin yanzu ƙarfe 10 ma batayi ba, wani English Novel mesuna ( Just A Friend) tajawo haɗe da buɗe chapter'n da take ta soma karantawa, agurin wata ƴar class ɗinsu ta karɓo shi.
****
Ƙarfe 4 na yamma dai dai suka fito daga cikin lecture ɗinsu wanda shine na ƙarshe a wannan ranan, direct library ta nufa saboda akwai wani littafi da takeson dubawa, kasancewar akwai assigment ɗin da aka basu, idan ta samu littafin kuma sosai zai taimaka mata wajen yin assigment ɗin cikin sauƙi. Gaba ɗaya hankalinta naga littafin da take dubawa, sam bata damu da mutanen dake wajenba kasancewar kowa karatu kawai yakeyi. Tana zaro littafin daga ma'ajinsa ta saki murmushi, juyawa tayi daniyar tafiya idanunta suka sauƙa akan shi, waro manyan idanunta waje tayi haɗe da sakin littafin yafaɗi ƙasa. Jikinta ne yaɗauki rawa da sauri ta tsugunna ta ɗauki littafin haɗe da nufar hanyar waje, tsabar sauri har ƙafafunta harɗewa suke, batayi auneba saiji tayi ta buge mutum, da sauri taɗago don ganin waye ta buge, shiɗinne dai tsaye a gabanta yana me kallonta da jajayen idanunsa, da sauri taja baya, haryanzu jikinta rawa yake kamar wacce taga mutuwarta.
"ZAHRAH!"
yaƙira sunanta cikin wata irin murya me matuƙar rauni.
Kusan mintuna uku takasa amsa masa da ƙyar ta iya motsa bakinta,
"I..na..da au..re"
shine kalaman da suka fito daga cikin bakinta awawware batare kuma da ta shiryawa fitowar kalmomin ba.
Rumtse idanunsa yayi haɗe da dunƙule hanunsa. Cikin murya me ɗaci haɗe da bushewar maƙoshi yace
"Nasani!"
Bazata iya jurewa ganinsa ba da sauri ta bi ta wata hanyar ta wuce da gudu, ko takan littafinta daya kuma faɗuwa batayi ba.
Bayanta yabi da kallo haɗe da tsugunnawa yaɗauki littafin, juyawa shima yayi yafice daga cikin library ɗin. Sai dai ko daya fito, ko ƙyallinta bai gani ba.
Zahrah kuwa tana fitowa daga cikin library ɗin direct wani ɗan corridor wanda mutane basu cika yawan bi ba tanufa, kaitsaye ta tsinci kanta awani fili wanda bakowa acikinsa sai shuke shuke, zama tayi akan wani benci dake wajen, haɗe da fashewa da kuka, tashiga ukunta itakam, wannan wace irin jaraba ne, meyasa Zaid bazai barta ta huta bane, jitayi lokaci ɗaya ƙirjinta yayi mata nauyi kamar anɗaura mata gungumen dutse, wayarta dake ringing ta kalla, Dr.Sadeeq ne ke ƙira amma bazata iya ɗagawa ba, ahalin da take ciki yanzu ma batasan me zata ce masaba idan ta ɗaga. Da ƙyar ta'iya tashi tabi ta ƙofar baya tafice daga cikin makarantar gaba ɗaya, tana fita ta tare me taxi haɗe da gaya masa inda zai kaita, ko ciniki basuyi ba ta faɗa cikin motar haɗe da ce masa yaja suje.
Yana kawota ƙofar gida ta basa kuɗinsa haɗe da ficewa acikin motar ta kutsa kanta cikin gidanta.
Bata damu da duhun dake cikin ɗakin ba haka ta faɗa kan gado ko mayafin dake jikinta bata cire ba.. Zazzaɓine me zafin gaske ya rufeta alokaci guda..
Zaid kuwa yana fita daga cikin library ɗin direct wajen da motarsa ke fake ya nufa, buɗe murfin motar yayi, ya shiga ya zauna, kifa kansa yayi akan steering motar yana mejin zafi da raɗaɗi na ratsawa har cikin ƙwaƙwalwarsa, akaro nafarko daya yardarwa kansa cewa zai haƙura da Zahrah kenan, tabbas yazama dole ya yi haƙuri da ita koda kuwa hakan nanufin mutuwarsa ne, yau Zahrah da bakinta ta faɗa masa cewa tana da aure, maganar dayajita tamkar anwatsa masa tafasheshshen ruwan zafi, bayajin zai iya yin rayuwa idan babu Zahrah, amma kuma ayau yaɗaukarwa kansa alƙawarin cireta acikin zuciyarsa, duk da yasan hakan zai zamo kamar yaudaran kansa ne yakeyi, amma kuma dole zai jarraba....
****
Cikin matsanancin tashin hankali Dr.Sadeeq yadawo gida, yaje makarantar su Zahrah yanemeta sama da ƙasa bai ganta ba, gashi yaƙira wayarta bata ɗauka ba daya ƙara ƙiranta kuma yaji wayar akashe, hankalinsa atashe yake sosai, yana shigowa cikin ɗakin yadanna madannin ƙoyin wuta take haske ya gauraye gaba ɗaya ɗakin, wani irin ajiyar zuciyar dabai taɓa yin irinta ba ya sauƙe, haɗe da lumshe idanunsa, da sauri yaƙaraso gareta haɗe da sona ƙiran sunanta, jin shiru bata amsa saba yasanya yakai hanunsa jikinta, zafi zau yaji jikin nata, take tausayinta yakamasa, shidai yasan hakanan Zahrah bazata dawo gida bata jirasa yazo ya ɗauketa ba, sannan kuma haka nan bazata kashe wayarta ba. Zama yayi akan gadon haɗe da ɗagota ya kwantar da'ita ajikinsa. Mayafin dake jikinta ya zare haɗe da sanya hanu yashiga shafa kumatunta.
"Zahrah!" yakuma ƙiran sunanta cikin sassanyar murya.
"Na'am!" ta amsa masa cikin wata irin murya, dagaji kasan tanajin jiki.
Kanta yashiga shafawa ahankali, zuge mata zip ɗin rigar dake jikinta yayi, haɗe da cire rigar gaba ɗaya daga jikinta, kwantar da ita yayi akan gado, kana ya nufi wajen da ɗan ƙaramin drawer ɗinsa ke aje, maganin da zai sauƙar mata da zazzaɓi cikin gaggawa yaɗauko.
Dakansa ya lallaɓata tasha maganin, abun gwajinsa ya ɗauko yashiga gwadata, cutar dayaga tana damunta shiyayi matuƙar ɗaga masa hankali, wani irin zufane yashiga keto masa.
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!!"
kawai yake ambata acikin zuciyarsa, duk sanyin A.C'n dake cikin ɗakin amma Dr.Sadeeq gumine ke tsastsafowa daga jikinsa.
"Taya akayi Zahrah takamu da wannan ciwon?" tambayar dayake tayi mawa kansa kenan.....
(😲Wani ciwo mun banu🙆♀
Banyi editing ba idan kunga typing error kuyi haƙuri!)
*Thursday 30/January/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 104*
Hanu yasanya akan goshinsa ya share zufan dake tsastsafo masa. Tashi yayi tsaye haɗe da tattara kayan aikin nasa ya ajiye a gefe. Direct bathroom ya shiga haɗe da sakar mawa kansa ruwa....
Tun shiga wankansa har kawo yanzu da ya fito yake shirya kansa tanajin sa,amma idanunta alumshe suke kamar meyin bacci.
Zama yayi akan gadon haɗe da ɗagota ya jawota zuwa jikinsa, kanta ya kwantar akan ƙirjinsa haɗe da soma shafa bayanta a hankali, still ɗaya hanunsa yasanya yana me shafa gashin kanta.
Cikin murya me ɗauke da nutsuwa ya soma cewa.
"Meyasa haka Zahrah? me yasa kika zaɓi ƙuntatawa kanki? tun bayauba nasha faɗa miki cewa ki daina yawan sanya kanki cikin damuwa, na faɗa miki kirage yawan tunani, har acikin zuciyata inamiki wani irin so wanda bansan iyakacinsa ba, bana so nagan ki cikin damuwa, ganin farincikin ki yafiyemin komai aduniyarnan, kinkuwa san meke damunki yanzu? damuwar da kike yawan sanya kanki aciki tahaifar miki da matsala wanda baikamata ace yarinya ƙarama kamarki tana ɗauke da wannan ciwonba, mekika nema kika rasa aduniyar nan? banaso ki ɓoyemin komai inaso kifaɗamin shin azamana dake ina cutar dake ne? ko kuwa inayi miki wani abu wanda ba kya so ne?"
Kanta tashiga girgizawa alamar "A'a" tuni hawaye sungama wanke mata fuska.
"To idan dai har hakane yakamata ki faɗamin damuwarki koda nima zanji sauƙi acikin zuciyata"
yafaɗi haka a gareta cikin tausasawa.
Kuka ta fashe dashi haɗe da sake rungumeshi cikin kukan tace.
"Nakasa daurewa ne, nakasa daure zuciyata, idan dai yana cikin wannan duniyar bazai taɓa barina ba, bazai barni ba harsai yakasheni sannan zai huta, naso namanta dashi amma nakasa, bansan meyasa ba kullum zuciya ta me rauni take kasancewa akansa, dan Allah kayi haƙuri banfaɗi haka agareka don na ɓata ranka ba, kawai dai nafaɗi abun dake zuciyata ne!" taƙare maganar tana sheshsheƙan kuka..
Rumtse idanunsa yayi haɗe da cije laɓɓansa, dama yasani duk duniya damuwarta bazata wuce akansa bane yajima da sanin wannan. Ɗagota yayi daga jikinsa yazamana suna fuskantar juna. Cikin wata irin murya yace..
"Ba iya miji bane ni agareki, ni ɗan uwa ne wanda baki da kamarsa, najima da sanin cewa har yanzu Zaid yana cikin rayuwarki, nasan Inasonki so me tsanani, sai dai kuma duk irin soyayyar danakeyi miki Zaid yafini sonki, da ace zan iya to da najima da mallakawa Zaid ke amma bazan taɓa iyawa ba Zahrah nima masoyinki ne na haƙiƙa kamar yanda Zaid yakejin bazai iya rayuwa ba idan babuke, haka nima nakeji ajikina, batun yauba nasan Zaid yana nan kwance aƙasan zuciyarki, bana yaudaran kaina nakan faɗi abu ne aduk yanda natsaya na fahimceshi, koda kuwa abun dana faɗa bazasuyimin daɗin ji acikin kunnuwa naba, duk da kuwa nina faɗesu, bana ɓoye gaskiya saboda biyan buƙatar kaina"
Kafaɗunta yakama da duka hannayensa. Ci gaba yayi da cewa
"Yanzu zanyi miki magana ne a matsayina na mijinki kuma wanda yake sonki, har yanzu duk da na aureki kina aƙarƙashin ikona bazan taɓa takuramiki ba, inamatuƙar son farincikin ki, idan har kinaji ajikinki cewa bazaki iya rayuwa ba idan babu Zaid shikenan zan iya....." rumtse idanunsa yayi da ƙarfi ya kasa ƙarasa maganar, da sauri ya miƙe yafice daga cikin ɗakin.
Zahrah wanda tun fara maganarsa tayi saroro tana kallonsa, tana ganin ficewarsa ta fashe da kuka.
"Me doctor yake shirin cewa? badai zai haƙura da ita ba?" tambayar da tayiwa kanta kenan, sam haka bazai taɓa yiwuwa ba, wace irin banzace ita? taya ya zata iya jure rashin masoyi kamar doctor Sadeeq? kuka tashiga rerawa me tsuma zuciya, kaiconta tunda dai harta bari Dr.Sadeeq ya iya sanin sirrin dake cikin zuciyarta, yanzu da wani idanu zata kalleshi bayan yasan cewa akwai son wani maƙare acikin zuciyarta? lallai koda ace Zaid ubantane yakamata tayi ƙoƙarin mantawa dashi....
Dr.Sadeeq kuwa yana fita daga ɗakin falo yanufa, yanazuwa ya buɗe fridge haɗe da ɗaukan goran ruwa yakafa a bakinsa, saida yasha ruwan fiye da rabin gora kafun ya kai goran ƙasa, ajiyar zuciya kawai yake sauƙewa akai akai.
"Meyake shirin aikatawa ne haka?" yatambayi kansa. Girgiza kansa yayi haɗe da ware idanunsa, idan yace zai iya rabuwa da Zahrah to yayi ƙarya, amma kuma idan yazamana bashine zaɓin ranta ba, to fa tabbas yazama dole ne yarabu da ita, badon kowaba saidon samun ingantaccen farincikinta, yasani shima abune me wahala ya iya jure rashinta, amma kuma itama yakamata aduba zuciyarta, yakamata tasamu abun da takeso.
key ɗin motarsa dake aje kan ɗan ƙaramin stull dake falon ya ɗauka haɗe da sakai yafice gaba ɗaya daga cikin falon, motarsa yashiga ya fice daga cikin gidan, bayajin zai iya zama acikin gidan gaba ɗaya zuciyarsa a dagule take..
Zahrah kuwa tanajin alamar fitansa daga cikin gidan tasake fashewa da kuka, duk da kuwa zafin zazzaɓin dake damunta. Kuka tayi sosai amaimakon zazzaɓin nata ya ragu sai gashi ya ƙara hawa, to taƙi tabar zuciya da ƙwaƙwalwanta su huta...
****
Da ƙyar ya iya kai kansa gida, tsabar yana acikin wani irin yanayi har idanunsa soma rufewa sukayi, yazamana duhu duhu kawai yake gani, hanunsa dafe da saitin zuciyarsa yafito daga cikin motar, taku biyu yayi duhu ya mamaye duka idanunsa take wani irin juwa ta ɗebesa saigashi yashe a ƙasa bayako da numfashi, da gudu ma aikatan gidan sukayo kansa suna ƙiran sunansa
"Oga! Oga!!"
Oga baimasan sunayi ba, wani daga cikin masu bawa flowers ruwa ne ya ranta aguje yaje yasanarwa Mummy dama Dad na nan atare suka fito amatuƙar ruɗe.
Ganin da suka mawa Zaid yashe a ƙasa yafi komai ɗaga musu hankali, da taimakon ma'aikatan wajen Dad yasanyasa amota direct suka wuce asibiti Mom sai kuka take.
Emergency aka karɓesa, Lallashin duniya Dad yayimawa Mom akan tayi shiru ta daina kuka amma taƙi, duk da cewa tana fushi dashi amma bata ƙaunar taga ko taji wani abu yasameshi, yanzu idan akace ya mutu yazatayi da rayuwarta?
Sama da 1 hour likitoti suka kwashe akansa suna bashi taimakon gaggawa. Ɗaya daga cikin likitotin ne ya kalli Dr.Bilal haɗe da ɗaga masa kai alamar wai Zaid ɗin babu rai ajikinsa. girgiza kai Dr.Bilal yayi alamar bai yarda cewa babu rai ajikin Zaid ɗin ba..
Hmmm likitotin nan sunsha matuƙar wahala kafun suka samu numfashin Zaid ya dawo dai-dai. Dukansu haka suka fito suna gumi domin kuwa da fari harsun cire rai dashi, sun ɗauka dagaske ya mutu.
Da gudu gudu sauri sauri Dad yataho wajen Doctor Bilal, hanun Dad Dr.Bilal yakama suka wuce office ɗinsa.....
"Yajikin nasa doctor? dan Allah kafaɗamin wani hali yake ciki a yanzun?" Dad yatambayi Dr.Bilal cikin yanayi na matuƙar ruɗewa.
"Ka kwantar da hankalinka Alhaji, yau Zaid ya hau matakin ƙarshe wanda da taimakon Allah muka samu da ƙyar muka shawo kan matsalan, amma bazan taɓa ɓoye maka ba idan har yasake shiga cikin yanayi irin wannan to fa tabbas wata ƙila saidai haƙuri, ba'aja da ikon Allah amma kuma fa da matuƙar wahala idan zai sakeyin numfashi, dama wannan shine matakin ƙarshe kuma gashi yakawosa idan irin haka tasake faruwa kuma to saidai dukanmu muyi haƙuri, haka Allah dama yake abunsa, duk wani me rai mamaci ne, koda ciwo ko babu ciwo, watarana dole mutum saiya mutu idan lokacinsa yazo, haka kuma gaba ɗaya zamu zama tarihi, saidai aba da labarin mu kamar yanda aka bamu na waƴanda suka shuɗe kafun zuwanmu iyaye da kakanninmu kenan!" Dr.Bilal yafaɗi haka yana me tattara nutsuwarsa ga Dad.
Gumi kawai Alhaji Ma'aruf ke sharewa sai ambatan
"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!" yakeyi gaba ɗaya ji yayi duniyar tayi masa nauyi.
"Doctor menene mafita?" Dad yatambayi Dr.Bilal cikin sanyayewar guiwa.
"A yanzu kam dai bamu da mafita Alhaji Ma'aruf, sai dai mujira muga me Allah zaiyi, wataƙila Zaid zai iyakaiwa kwana uku batare daya farka ba, wataƙila kuma ko nanda kwana biyu ya farka, amma yazama dole ku kula dashi, yanzu bakamar da bane, yanzu abu kaɗan na ɓata masa rai zuciyarsa zata hau zafi, sannan kuma idan ya yawaita yin tunani to fa akwai babbar matsala, yazama dole ku tsaya akansa ku lura, akwai magungunan dazan rubuta muku, idan yatsaya akansu insha Allah zasu taimaka masa sosai."
Sai alokacin Alhaji Ma'aruf ya ɗanji sanyi acikin ransa.
"Nagode ƙwarai Dr.Bilal kuma Insha ALLAH zamu kiyaye sosai!" Dad yafaɗi haka yana me miƙewa tsaye. Musabaha sukayi da Dr.Bilal kafun ya fice acikin office ɗin.
*****
A daddafe ta tashi tayi sallan isha. Tana kan sallayan bata tashiba yashigo cikin ɗakin, idanunta ta zuba masa, bada kayan da yafita ya dawo ba, yanzu rigane da wando na jeans ajikinsa, kallonsa takeyi kamar wani wanda bata taɓa ganinsa ba, shima kallonta yayi haɗe da yi mata murmushi, ya wuce cikin bathroom, mintuna kaɗan yafito daga cikin bathroom ɗin.
"Kizo kici abinci" yana faɗa mata haka yafice daga cikin ɗakin.
Wani irin kunyan sa ne yaka mata, amma kuma babu yanda zatayi, abundake cikin zuciyarta ta faɗa.
Miƙewa tayi sumi sumi ko hijab ɗin dake jikinta bata cire ba ta fita zuwa falo.
Zama tayi akan sofa kusa da inda yake zaune, haɗe da takure jikinta waje ɗaya, shawarma ne da gasashshen kifi (roasted fish) ya sayo musu, tura mata plate ɗin yayi gabanta.
"Kici sai kisha magani" yafaɗi haka fuskarsa ɗauke da ɗan murmushi, kallonsa tayi kamar zatace dashi wani abu kuma saita fasa tasoma cin abincin da kaɗan kaɗan. Shikuwa sannu a hankali yake sipping country yoghurt ɗinsa yana me kuma latsa wayarsa.
Haka suka zauna shiru babu me cewa da ɗan uwansa ƙala.
Tana kammala cin abincin ya bata wasu magunguna daya shigo dasu, babu musu ta amsa tasha. Ganin yatashi yabar falonne yasanya itama ta tashi ta koma ɗaki, wanka tayi kana ta fito ta sanya wata sleeping gown wacce ta tsaya iyaka cinyarta, ko guiwa bata ƙarasa ba, sosai rigar tayi mata kyau ta kuma fito da farar fatarta fili, dogon gashinta ta kama ta tubke a tsakiyar kanta haɗe da ɗaureshi da ribbon, turarenta me daɗin ƙamshi ta shafa, tana nan tsaye a cikin ɗakin yaturo ƙofar ɗakin yashigo.
Wani irin yawu ya haɗiye a maƙoshinsa, sanda idanunsa sukayi masa tozali da ita, sosai tayi kyau acikin rigar, ga fararen cinyoyinta sun bayyana kansu a fili, da ƙyar ya iya daure zuciyarsa, murmushi kawai yayi mata haɗe da kawar da kansa gefe, shi kaɗai yasan me yakeji acikin zuciyarsa, yana tsananin kishin matarsa, kamar yanda yake tsananin sonta.
Kan gado ta koma ta kwanta, agogon hanunsa yacire haɗe da cire rigarsa, 3 guater jeans yasanya..
Zama yayi a gefen gadon haɗe da jawo laptop ɗinsa yasamo dannawa, dama yanada ayyukan da suka masa yawa yanaso ya ɗan ragesu, bayaso ya kwanta shiru tunani ya damesa.
Hanu tasa ta share hawayen dake fitowa daga cikin idanunta.
"fushi Dr.Sadeeq yakeyi da ita kenan?" tambayar da take ta yiwa kanta tun ɗazu kenan, bazata iya jure fushinsa akanta ba, duk da baifito ya nuna mata hakan afili ba, amma duk wasu alamu sun nuna hakan, bayason yi mata magana me tsawo sannan kuma baya sake mata kamar yanda ya saba, idan tabarsa haka batayi masa adalci ba, ayanzu bata da wani wanda ya wuce mata shi, shi ɗinne dai komai nata, bazata iya ɗaukar fushinsa akanta ba.
Aikinsa yake cikin nutsuwa amma kuma gaba ɗaya tunaninsa akanta yake, ba abun dayafi damunsa kamar cutar hawanjini dake da munta, yasani sarai cutar hawan jini bata da kyau tana cutarwa sosai, musamman ma ga yarinya kamarta hakan yasa yake tsananin tausayinta.
Baizataba saiji yayi ta rungumeshi ta baya, haɗe da ɗaura kanta akan wuyanshi, me makon tace wani abu sai kawai ta fashe masa da kukan shagawaɓa.
Lumshe idanunsa yayi har a cikin zuciyarsa bayason kukanta idan tana kuka hankalinsa tashi yake.
Jawota yayi ta dawo gabansa.
"Menene?" yatambayeta yana me ɗora idanunsa akanta.
"Bazan iya jure fushinka ba, dan Allah kayi haƙuri wallahi inasonka banason kajuyamin baya, banda kowa sama da kai, idan kajuyamin baya bansan yanda rayuwata zata kasance ba, kayi hakuri kaji!!" kuka take sosai alokacin da take faɗar maganar.
Wani irin sanyine yaji yana ratsa zuciyarsa kalmar "Wallahi tana son shi" da ta faɗa yafi komai da ɗaɗa masa rai, yaji daɗin maganar sosai, amma sai ya dake bainuna mata hakan afili ba.
"Ni nace miki ina fushi dake ne?" abunda yatambaya kenan.
Da sauri tashiga kaɗa kanta alamar "Eh"
Cike da mamaki yace "yaushe nace haka?"
"Kaine kake bani abinci abakina harsai na ƙoshi, amma yau turamin abincin gabana kayi kace naci ni kaɗai, sannan tunda kafita baka dawo gidan nan ba, gashi kazo baka kulani ba saima laptop ɗinka daka fara latsawa, kasabarmin bazan iya jurewa ba, dan Allah kada kayi fushi dani naroƙeka, bazan iya samun nutsuwa ba matuƙar baka tare dani, bazan iya zama dakowa ba bayan kai, inasonka sosai!"
Tunda ta fara maganar yake kallon ɗan ƙaramin bakinta hartakai ƙarshe.
Jawota yayi jikinsa, haɗe da sake lumshe idanunsa, sun kai kusan mintuna uku a haka, babu wanda yasakeyin magana kafun ta ɗago kanta daga cikin ƙirjinsa. Buɗe idanunsa yayi ya sauƙesu acikin nata, kallon juna sukeyi cikin wani irin yanayi me wuyar fassaruwa, ahankali ta matso da fuskarta daf da tashi haɗe da lumshe idanunta, bakinta ta buɗe ahankali ta ɗaura harshenta akan lips ɗinsa, jiyayi kamar anjona masa shocking ajikinsa, ahankali ta tura harshenta cikin bakinsa tana me yawo dashi, kasa jurewa yayi cikin hali na zaƙuwa ya kama harshenta yashiga tsotsa.. Sosai suke kissing ɗin junansu, numfashinsu har ƙoƙarin ƙwace musu yake. Igiyar dake gaban rigarta yaja take rigar ta buɗe ta gaba, sake lumshe idanunsa yayi haɗe da fitar da wani irin numfashi me sauti alokacin da idanunsa suka sauƙa akan breast ɗinta, kansa ya cusa acikin ƙirjinta yana kai mata kiss tako ina.. Cikin mintuna ƙalilan Dr.Sadeeq da Zahrah suka fice a cikin hayyacinsu babu ma kamar doctor, gaba ɗaya idanunsa sun rufe numfashi kawai yake fitarwa ta bakinsa... Soyayyar su tayau ta da bance, yau tsantsar soyayya ya gwada mata wacce tasa ta manta komai acikin duniya har batasan sanda hawaye suka gama wanke mata fuska ba, shi ma kansa yau yazautu da tsananin kulawan data basa, ita kanta mamakin yanda yake shiɗewa akanta take, sai dai kuma idan ta tuno cewa ko wacce mace da irin baiwar da ALLAH ya mata saitaji sanyi acikin ranta, ko a iya nan aka tsaya, zata ta godemawa ALLAH ...
Cike da shagwaɓa ta ture kanshi dake kan breast ɗinta. "So kake ka ciremin nipples ɗina ne wai?"
Duk da haryanzu yana acikin magagin duniyar daɗin dayashiga bai sake saba amma saida yayi dariya.
"Dama Nipples yana fita ne?" shima yatambayeta cike da mamaki, domin a iya tsawon rayuwarsa shi bai taɓajin inda akace nipples yafita daga jikin breast ba.
"To bakai bane tun ɗazu fa kaketa sha, kuma zafi yakemin!" araunace tafaɗi maganar.
"To ba nipples din bane yace yana sona!" yafaɗi haka yana me kwaikwayon yanayin maganarta.
Dariyane yakamata sosai, da ƙyar ta samu ta zame hanunsa dake kan breast ɗin nata, tana ƙoƙarin tashi yayi saurin kamota ya kwantar da ita, kwanciya yayi asamanta haɗe da sakarmata duka nauyinsa.
Ɗan ƙaran wahala tasake haɗe da lumshe idanunta.
"Ina da nauyi ne? ke ɗazu da kika hau kaina ai bance kina da nauyi ba"
"To ae ɗazu banice na hau kanka ba kaine ka ɗaukeni ka ɗaurani akan ka batare da nace inaso ba"
"To amma dana ɗauraki wayace ki sakemin duka nauyinki harma da kama min....."
Da sauri ta sanya hanu ta toshemai baki bataso ya faɗi abun da tayi masa, ita kanta batasan tayi masa haka ba alokacin tana wata duniyarne na daban. (Khair uwar gulma harkin baza kunnuwa kiji metayi ko, to bazakiji ba nima banji ba balle ke😂)
"INASONKA!!!" Zahrah tafaɗa cikin wata irin murya me ɗauke da tsananin shauƙi.
"Nima INASONKI!!!" shima yafaɗa cike da tsananin ƙauna, wani irin kallo sukayiwa junansu, cike da sha'awar juna suka sake haɗe bakinsu waje ɗaya.......
(Zahrah da Doctor fa sun zama one love ga soyayya ga jaraba, doctor ya koya mata🤭)
*Vote*
*Vote*
*Voted please🙏*
*(Comment and vote please my lovely fans, my wattpadians idan kun karanta kuna min vote kunji😥)*
*Happy New Month*
*Saturday 1/January/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 105*
*ZAID*
Kwanansa biyu acikin asibitin kafun ya samu ya dawo cikin hayyacinsa, sai dai kuma tunda ya dawo hayyacinsa baice da kowa komai ba, ko su Dad ɗinsa da sukeyi masa ya jiki, da kai kawai yake amsa musu, shikaɗai yasan meyakeji acikin jiki da zuciyarsa.
Zaune yake akan gadon asibitin yayi jigum, babu wani abu dake yi masa daɗi acikin duniya, Matakin daya ɗaukarwa zuciyarsa yayi masa tsauri sosai, a haƙiƙanin gaskiya yasan yaudaran kansa yake, cire soyayyar Zahrah acikin zuciyarsa, ba abu bane me sauƙi, yana sonta so sosai, so irin wanda ba a misaltashi, so ne dayakai ƙololuwa, ko ina acikin zuciyarsa tambarine na ƙaunarta, rumtse jajayen idanunsa yayi haɗe da sanya haƙuransa ya ciji laɓɓansa, dai dai lokacin aka turo ƙofar ɗakin aka shigo, ko kallon bakin ƙofar baiyi ba, balle yaga waye ne yashigo cikin ɗakin.
Turus haka Afrah taja ta tsaya tana me ƙaremasa kallo, mugun tsoronsa takeji, yanzuma Momynsa ce tace tazo ta duba ya jikin nasa shiyasa ta shigo, amma da bazata shigo ba. Karambani irin na Afrah yasanya taɗan matsa kusa dashi cikin murya me sanyi tace.
"My Dear yajikin naka?"
Da sauri ya buɗe jajayen idanunsa ya watsa mata su, take jikin Afrah ya soma rawa, tsananin tsanarta tahango acikin ƙwayar idanunsa, yanayin yanda taga idanunsa sunyi ja shi kaɗai ya isa firgita mutum, da sauri ta juya tafice a ɗakin, zuciyarta cike tab da sabon tsoronsa, gani take kamar zai tsaidata ya jibgeta, aitana tsintar kanta a wajen ɗakin tashiga sauƙe ajiyar zuciya akai akai...
Shikuwa idanunsa ya maida ya rufe, wani irin ɗaci yakeji acikin maƙoshinsa, yayinda ransa yakai ƙololuwa wajen ɓaci, hakanan shikam Allah ya ɗaura masa tsanar yarinyar dako sunanta ma baisani ba, anzo anwani ƙaƙa ba masa ita amatsayin mata. "Shegiya me ƙananan idanu, daganinta munafukace" yafaɗi haka acikin zuciyarsa, jingina kansa yayi da bango, yaci gaba da tunanin yanda zai samawa rayuwarsa salama...
*****
Gyara zama Husnah tayi haɗe da miƙa duk wata nutsuwarta ga Zahrah.
"Kina mamakina ko Husnah? nasan dole dama zakiyi mamaki, amma kuma idan kika yi tunani me kyau tawani wajen baizama abun mamaki ba"
Zahrah tafaɗi haka da iyaka gaskiyarta, saboda ita yanzu tama daina mamakin kanta kwata kwata.
"Dole ne zanyi mamakinki Zahrah, wani irin so ne haka kikeyiwa wanda ya tozarta rayuwarki? bazan tuna miki abun da Zaid yayi miki ba, saboda na tabbata har kikoma ga Allah bazaki daina jin ciwon abun da Zaid yayi miki acikin zuciyarki ba, a gaskiya bana ma tunanin kinacikin hankalinki Zahra, saboda baidace ace kina da aure akanki, kuma kina zancen wani daban ba mijin kiba"
Husnah tafaɗi haka cikin yanayi dake nuna ranta ya ɗan ɓaci da jin kalaman Zahrah.
Wani irin murmushi Zahrah tayi haɗe da sanya hanunta akan kafaɗan Husnah.
"Nasan dole zakiji haushina Husnah, amma kafun ke kiji haushina ninafara jin haushin kaina, ada nayi tunanin cewa banda hankaline, amma daga baya nagane cewa so so ne, kinsani nima kuma nasani so bayashawartarka kafun yashiga zuciyarka, so baruwansa da anzalunceka ko kuma kazalunta, shidai so so ne a kullum haka yake baya tambayarka shawara idan zai saka ka aikata wani abu, hakanan baya kuma sanjawa, shi ɗinne dai akullum akuma ko da yaushe yana nan, nasan Zaid yacutar dani, amma kuma ina matuƙar jin tausayinsa acikin zuciyata, tabbas da ace inada iko ko wani hali dana sanjawa Zaid rayuwarsa nasan Allah zai bani lada" Zahrah taƙare maganar tana me cije laɓɓanta.
Kallon baki da hankali Husnah tashigayiwa Zahrah.
"Ki sanja masa rayuwa fa kikace, anya kuwa kina cikin hankalinki Zahrah?" Husnah tafaɗa cike da mamaki.
"Inacikin hankalina Husnah ban haukace ba, ada nima nayi tunanin ko na haukace ne,sai kuma nagane bahaka bane" hanunta ta ɗaura akan hanun Husnah..
"Zaid bai taɓa tunanin haka zata kasance dashi ba Husnah, yayimini fyaɗe ne bisa bin umarnin zuciya dakuma gangar jikinsa da yayi, yamin fyaɗe ne saboda yanaji ajikinsa cewa sha'awata ce ke damunsa, Allah ba azzalumin kowa bane saidai wanda yazalunci kansa, ada nayi kuka sosai Husnah, nayi nadaman sanin Zaid acikin rayuwata, sannan kuma naji ƙunci da ciwon abun da ya aikata a gareni, ada inatunanin cewa fyaɗen da Zaid yayi mini yatashi abanza, saboda banida wani wanda zai tunkaresa, har yaƙwatarmin haƙƙina a wajensa..." ɗan tsagaitawa da maganar tayi haɗe da sakin wani murmushi, cigaba tayi da cewa.
"Nasani ko badaɗe ko bajima Allah zaimin sakayya, amma kuma bansan tawani hanya zai saka minba, ashe tahanyar da Zaid yabi ya yaudareni ta hanyar Allah zai sakamin, kinsan wace hanyace?" Zahrah ta tambayi Husnah.
Cike da zaƙuwa Husnah ta girgiza kanta alamar "A'a"
"SO! naso Zaid so me tsanani, shine namijin dana fara bawa soyayyata tunda nazo duniya, haka kuma shine namijin da na aminta dashi ɗari bisa ɗari, bantaɓa tunanin cewa ze iya rumtse idanunsa yaketamin haddina cikin rashin tausayi da imani, hadda wulaƙanci ba, nayi kuka harnagaji alokacin da Zaid ya lalatamin rayuwata, Zaid yayi amfani ne da soyayyar da nakeyi masa wajen cutar dani, Allah daya tashi sakamin Sai yasanya masa soyayyata me tsanani acikin zuciyarsa, yakuma nesantashi dani, tsananin soyayyar da Zaid kemin shine sakayyar da Allah yayimini, sannan kuma alhakina, na bibiyarsa sosai, Zaid yana sona, son da bazaiyi mishi amfani ba, nayi masa nisa tayanda bazai iya samuna ba, inada tabbacin cewa ayanzu yana cikin tsananin halin nadama wacce bazata amfaneshi da komai ba"
Ɗan numfasawa Zahrah tayi haɗe da duban Husnah.
"Kina ganin Zaid yacancanci samun mace mai hankali da nutsuwa, wacce zata gyara masa rayuwa ko a'a?" ta tambayi Husnah.
Harara Husnah ta wurga mata haɗe da taɓe bakinta...
"Mazinaci, fasiƙi, ɗan giya, ta'ina ya dace da mace me hankali da nutsuwa, ae sai dai ko yasamu wata daga cikin karuwan ƴan matansa ya aura, sai su ƙare rayuwarsu a haka, amma wace me hankalince zata yarda ta aureshi" Husnah tafaɗi haka da iyaka gaskiyarta.
Murmushi me ciwo Zahrah tayi haɗe da cije laɓɓanta, kanta ta girgiza kana tace....
"Zaid bai cancanci zama da karuwaba Husnah"
Dasauri Husnah takalleta haɗe da cewa.
"Meyasa kikace haka?"
"Sauyin rayuwa yake buƙata, dole yana da buƙatar wacce zata tsaya akansa ta basa kulawa, zuciyata tanayimini wani hasashe na daban" Zahrah tafaɗi haka tana me kafe Husnah da idanu.
Harara Husnah takuma wurgawa Zahrah haɗe da taɓe baki, cikin takaici tace.
"Amma dai kinsan mazinaci sai mazinaciya ƴar uwarsa ko, taya zakina haɗa kamilar mace da wani taƙadarin ɗan iska Zaid, cab hmm gwamma ma kisake tunani, me kuma zuciyarki take hasasho miki akan sa?" Husnah ta kuma tambaya.
"Kece zaki iya Husnah, banda wata wacce ta wuceki, banda wata ƙawa sama dake, amma bansan yazaki ɗau abun ba amma nasan....."
"Mekike son cewane wai Zahrah? naga kinata wani kwalo kwalo, ki faɗi abun da kikeson faɗi kai tsaye" Husnah tafaɗi haka ta hanyar katse Zahrah daga maganganun da takeyi.
"Ke yakamata ki auri Zaid Husnah, ko saboda nima, zaki samu lada sosai ba ɗan kaɗan ba...."
Cikin tsananin mamaki Husnah tamiƙe tsaye daga zaunen da take, wani irin kallo tashiga yimawa Zahrah, cikin wata irin murya dake ɗauke da tsananin ɓacin rai da takaici tace.
"Ni" tanuna kanta da ɗan yatsarta. "Allah ya sauwaƙemin, bantaɓa tunanin zaki zomin da irin wannan zancen ba Zahrah, ashe dama bakyasona, bakya ƙaunata? nagode ƙwarai da kikanunamin hakan adai dai wannan gaɓan, amma inaso kisani idan mafarki kikayi cewa ni Husnah na auri ɗangiya mazinaci to kigaggauta yin sadaka!" taƙare maganar cike da ɓacin ran abun da Zahrah ta gaya mata...
Haka Husnah ta suri jakarta tayi tafiyarta Zahrah naƙiranta ko waiwayowa batayi ba, balle ta tsaya sake sauraranta.
Jingina bayanta tayi dajikin wata bishiya wanda suke zaune a ƙasanta, wasu siraran hawayene suka gangaro takan kumatunta.
"Kowa kallon mahaukaciya yakeyi mata, to sai yaushene wasu mutanen zasu gaskata cewa soyayya ba ƙarya bane? sai yaushene wasu mutanen zasu gane cewa ita soyayya babu ruwanta da illa ko aibin mutum? menene laifinta don taji tausayin Zaid? So baƙarya bane, kuma duk inda so yake akwai tausayi, haka kuma akwai tsananin sha'awa." Ƙaran wayartane ya katse mata tunanin da takeyi, dasauri ta share hawayenta haɗe da ɗaukar wayar takara akan kunnenta..
"To" kawai naji tace haɗe da jefa wayarta ta acikin jaka, tashi tayi daga inda take zaune haɗe da gyara mayafinta, jakanta ta ɗauka ta nufi inda Dr.Sadeeq ke jiranta.
Tun daga nesa daya hangota yaketa zuba murmushi, komai na Zahrah'nsa me kyaune, tafiyanta ma kaɗai abun ɗaukar hankali ne, duk da cewa ba dagangan take hakan ba, haka asalin takunta yake ɗauke da nutsuwa, bawai ita ta ƙirƙiri hakan saboda burgewa ba.
Buɗe murfin motar tayi ta shiga bakinta ɗauke da sallama, lumshe idanunsa yayi haɗe da kamo hanunta yasanya acikin nasa hanun cike da nutsuwa yake murza ƴan yatsunta.
"Nayi missing wannan kyakkyawar matar, nayi missing wannan kyakkyawar fuskan, haka kuma nayi missing wannan daddaɗan jiki me laushin, nakumayi missing wannan tausassun laɓɓan masu daɗin sucking, kuma ma nayi missing wasu abubuwana wanda suke sani nishaɗi sosai suke kuma.." da sauri tasa hanu ta toshemasa baki haɗe da shagwaɓe masa fuska..
"Ni dai dan Allah kayi shiru!" tafaɗi haka a sangarce.
"Ni dai gaskiya naƙi wayon bazanyi shiru ba saina ƙarisa!" yafaɗi haka cikin yanayi na kwaikwayon maganarta.
Ɗan ɓata fuska tayi haɗe da sanya hanu ta shafi ɗakalallen cikinta.
"Yunwa nakeji sosai fa, rabona da abinci tun breakfast"
Ɗan waro kyawawan idanunsa dake ɗaukar hankalinta waje yayi.
"Meyasa kikeson barin kanki da yunwa ne? kinsan fa bazan yafe miki ba idan har kika cutarmin da unborn ɗina" yayi maganar yana me kafeta da idanunsa.
Zaro idanu Zahrah tayi haɗe da kai hanunta kan cikinta da sauri, ta shafa wai ko zataji tudu.
"Unborn fa kace? badai ajikina ba?" tayi tambayar cike da zaƙuwar jin amsarsa da alama taɗan tsorata da kalaman nasa.
"Yes Unborn ɗina dana sa miki daren jiya mana, banaso wani abu yasameshi seriously!"
Wani ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya ta sauƙe haɗe da jingina bayanta da jikin kujeran motar, gaba ɗaya ya faɗar mata da gaba.
"Ita da take tsananin tsoron haihuwa, tun yanzu yafara mata wani zancen unborn" tafaɗi haka acikin zuciyarta..
"Ya naga duk kin wani firgice ne haka, bakyason baby ne?" yatambayeta adai dai lokacin da yake tada motar.
"A'a" kawai tafaɗa murya a sanyaye. Baice da ita komaiba yaja motar suka fice daga cikin makarantar...
Direct wani hotel suka nufa don cin abinci, a cewarsa bazai iya haƙuri har sukoma gida batare da tasawa cikinta wani abuba.
Bata iya cin komai acikin hotel ɗin ba, sai pepper meat da kuma kunun aya kawai.. Koda suka koma gida tuni bacci ya cika idanunta, kwana biyunnan sosai take ebo gajiya amakaranta, da ta dawo kuma tayi wanka shikenan sai bacci. Yaukam basu dawo da wuri ba sai gab da magriba, saboda haka bata ba bacci... Wanka tayi da ruwan ɗumi take taji gajiyan yasauƙa daga jikinta..
"dogon wando na pencil jeans ta sanya ajikinta, sai kuma wata riga wacce tsayinta yakawo har gaba da guiwanta, gefe da gefen rigan atsage suke har wajen ciki, gaban rigar kuwa akwai aninaye masu kyau, rigace me kyau irin wacce ake ƙira da shirt gown (my favorite) sosai rigannan tayi mata kyau ajikinta yayinda hips ɗinta kuwa suka bayyana afili, kasan cewar rigar nada tsagu ta kowani ɓangare dama da hagu, batayi ƙoƙarin kame dogon gashinta ba, tazura lufaya haɗe da hawa kan sallaya ta gabatar da sallan magriba.
Tana idar da sallan ta miƙe haɗe da fita zuwa falo. Buɗe ƙofarta yayi daidai da shigowansa cikin falon, shima dawowarsa kenan daga masallaci.
"Waw!!! Kinyi matuƙar yin kyau sosai fiye da kullum" yafaɗi haka yana me ware mata duka hannayensa alamar tataho zuwa garesa..
Wani irin sanyin daɗi taji acikin zuciyarta lokacin da taji kalamansa, babu musu ta ƙarasa garesa haɗe faɗawa cikin ƙirjinsa.
Kansa yaɗaura akan wuyanta haɗe da sanya harshensa yasoma yawo dashi yana lashe fatar wuyanta. Hanunsa ya ɗaura adai dai kan hips ɗinta, cike da zolaya yace.
"Barin taɓa naji ko ciko akayi, anaso a yaudareni"
Dariya ne yakamata. Cewa tayi
"Allah ya sauwaƙe inyi cikon hips, taɓa da kyau kaji hips ɗina ne da Allah yaban bawai soso ba"
Shima dariya yayi haɗe da sake matseta acikin jikinsa.
"Nasani to ko kema kina ɗaya daga cikin mata masuyin cikon hips ɗin tunda ai naga mata sunayi sosai"
Da sauri ta ɗago ta kallesa lokaci guda ta ɓata fuska.
"Wato mata kake kallo sosai idan kafita ko? harkasan ana cikon hips, hmmm thank you" tafaɗi haka tana me ƙoƙarin zare jikinta daga nashi..
Da sauri yasake matseta ajikinsa haɗe da tausasa muryarsa.
"Tuba nake madam, amma nisam mata basa gabana, inadake mezanyi da wata kuma daban, ke kaɗai ce kinkuma isheni, amma kinsan ba abun mamaki bane dan nasan hakan, saboda yanzu hakan ya yawaita sosai, wasu mata basa haƙuri da surar da Allah yayi musu, dole wai sai sunyi ciko, inakaranta labarai, ina kuma gani a Instagram, amma kema kinsan baruwana da duk wata mace ina da me daɗina mezanyi da wata me ɗaci!" yafaɗi haka cike dason shagwaɓata.
Aikuwa take ta hau dariya sosai taji daɗin kalamansa, amma kalman me ɗacin nan yabata dariya sosai, ko wace macece me ɗaci oho.
(Please maza kuna faɗawa matayenku kalamai masu daɗi, koda ita ɗin bata da wani kyau, ka hure mata kunne kace ai ita kyakkyawace, wallahi zataji daɗi sosai, kai inda halima kadinga ƙiranta da sunan me daɗi🤣🙈wallahi yanzun sai gaka ranta yayi fari ƙal, kuma always zakaga tana cikin farinciki, wayyo wayaga anƙira su O'O da sunan me daɗi, ai nasan sai sunkusa sumewa saboda daɗi😂😂😂)
Zama sukayi akan kujera haɗe da jawota ya ɗaurata akan cinyarsa, kansa yacusa acikin ƙirjinta, bayan ya ɓalle aninayen dake jere agaban rigarta, sosai ƙamshin dake fitowa acikin ƙirjinta yake yi masa daɗi, yanason ƙamshinta, domin kuwa yana sa masa nutsuwa sosai.
Lumshe idanunta tayi, tana mejin daɗin kissing ɗinta da yakeyi a ƙirjinta, hanunta ta sanya acikin gashin kansa tana yamutsawa a hankali. Ƙaran wayarsane yakaraɗe musu kunnuwansu, akasalance Dr.Sadeeq ya jawo wayartasa batare daya duba wanda ke ƙirannasa ba ya kara wayar akan kunnensa. Waro manyan manyan idanunsa waje yayi haɗe da cewa
"Dagaske kake?"
Banji me wanda yaƙirasa a wayar ya faɗa masa ba saiji nayi kawai yace
"Okay ganinan fitowa."
Kallonsa Zahrah tayi, tanameson jin ƙarin bayani daga bakinsa.
"Lumshe mata idanunsa yayi haɗe da ɓuɗesu alokaci guda.
"Friends ɗinane sukamin surprise wai suna waje, banaje na shigo dasu, please mintina kisanja wannan kayan kinji, ina kishinki sosai banason kowa yakallemin ke!" yaƙare maganar yana wani lumshe idanu, domin kuwa cike yake da shauƙinta.
Murmushinta me kyau tayi masa haɗe da tashi daga kan cinyarsa tana cewa.
"Yanzu kuwa zan sanja kayan."
Ɗaki ta wuce shikuma yayi waje don shigo da abokansa.
Zama tayi akan gado bayan ta sanja shigarta zuwa riga da sket na material marar nauyi takuma yane jikinta da mayafi, tanajin hayaniyansu acikin falon.
"Maza kenan wai nan su fa taɗi suke, amma kuma yawancin zancen nasu kama yake da musu" tafaɗi haka acikin zuciyarta. Bata ida zancen zucin da take ba, Dr.Sadeeq ya shigo cikin ɗakin.
Hanunta yakamo haɗe da kai mata sumbata a goshinta.
"Ko wani irin kaya kika sanya sai sunyi miki kyau, kyau ajininki yake ƴan mata na!" yafaɗi haka yana me ƙare mata kallo.
"Ƴan mata kuma?" ta tambayeshi tana ɗan murmushi.
"Eh mana ƴan matace ke a wajena ae har gobe, kuma ke sabuwace a wajena, tunda har yanzu bangama lashe zuma na ba" yafaɗi haka yana me kashe mata idanunsa ɗaya.
Kunyansane ya kamata, amma babu yanda ta iya shidai duk irin kalamansa kenan.
"Ki kawowa baƙinmu drinks kinji"
"To" Kawai tacemai.
A tare suka fita ita tayi hanyar kitchine shikuma yayi cikin falon..
Hanunta ɗauke da wani ɗan madaidaicin trey wanda ke ɗauke da kayan drinks da kuma ƴan madaidaitan glass cups tafito daga cikin kitchine ɗin, kanta aƙasa tanufo cikin falon saida takawo cikin falon kafun ta ɗago kanta fuskarta ɗauke da ɗan murmushi, wani irin bugawa taji zuciyarta tayi, lokaci guda idanunsu ya sauƙa acikin na juna, take ta saki trey ɗin dake hanunta yafaɗi ƙasa, ƙaran faɗuwarsa yajawo hankalin gaba ɗaya waƴanda suke cikin falon......
*(😳Waye Zahrah tagani🙆♀ badai Zaid bane yabiyota har cikin gida? kai ina ai Dr.Sadeeq yasan Zaid bazai barshi yashigomasa cikin gida ba, to waye ne wai??? 😂 kutaimaka kufaɗamin waye, bazan iya jiran next page ba😂😂)*
*(Kuyi haƙuri dan Allah jiya banyi muku update ba🙏🏻)*
*Vote and Comment please my lovely fans🙏🏻*
*4/February/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI!!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 106*
Da sauri Dr.Sadeeq yataso ya taho gareta, durƙusawa yayi yashiga tayata tattare wajen, saboda har wasu daga cikin cups ɗin dake kan tray ɗin sun face. Bisa tsautsayi ta zo ɗaukan wani fasashshen cup kwalba ya caketa a ƴar yatsar hanunta, take ta saki wani ɗan ƙaramin ƙara, cike da kulawa Dr.Sadeeq yace.
"I'am sorry kibi a hankali, muga hanun yayi jini ne?" yaƙare maganar yana me kama hanunta wanda kwalban yasoketa.
Murmushin ƙarfin hali tayi haɗe da cewa
"Yayi jini amma baso sai ba" hanunta Dr.Sadeeq yakama yashiga hura mata iskan bakinsa ahankali, yama manta da cewa basu kaɗai bane a cikin falon.
"Sannu amaryarmu, munsa kin yanke da ƙwalba ko, i'am really sorry" wani daga cikin abokan Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana ɗan murmushi.
Murmushi itama ta ƙaƙalo haɗe
da girgiza kanta, alamar
"bakomai"
"Tashi ki gaishesu sama sama ae duk sune silar jin ciwonki" Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana me miƙar da ita tsaye.
Ɗan matsawa tayi wajen da suke zaune tashiga gaidasu cikin sassanyar murya, amma bata yarda ta kalli inda yake ba, shima kallo ɗaya yayi mata ya sadda kansa ƙasa, "Itaɗince dai duk da taƙara kyau hakan baihanasa ganeta ba" yafaɗi haka acikin zuciyarsa, zuciyarsa ne ke ingizasa daya ɗaga idanunsa ya kalleta, amma kuma yaƙi bin umarnin zuciyartasa saboda yasan hakan baidace ba.
Dr.Sadeeq dakansa yakawo musu wani drinks ɗin ita kuwa ta wuce ɗakinta..
Zama tayi akan gado haɗe da sauƙe wata irin ajiyar zuciya me ƙarfi, bazata taɓa manta wannan fuskarba, tabbas shine.
"To meya kawo JABEER gidanta kuma? kodai shima abokin doctor ɗin ne?"
tayi mawa kanta duka wa ƴannan tambayoyin, ganin da tayi cewa tunani bazai fishsheta bane, yasa ta miƙe ta ɗauko ɗan ƙaramin Al'Qur'ani'n ta tashiga karantawa a hankali...
Yanashigowa cikin ɗakin yajingina bayansa da jikin ƙofa haɗe da sauƙe ajiyar zuciya.
Kallonsa tayi haɗe da ɗan sakin murmushi.
"Yadai sai kace wanda yayi gudu?"
"laifine idan nayi gudu dan nazo naga matata?" shima yatambayeta yana me tsareta da idanunsa.
"A'a, amma ae abun bana gudu bane, tunda dai batashi sama zanyi ba inanan tare dakai" tafaɗi haka tana me gyara zamanta.
Takowa yayi yaƙaraso gareta, zama yayi gab da ita haɗe da ɗaura kansa akan wuyanta.
"Ya hanun naki?" yatambaya yana me ƙoƙarin kamo hanun nata wanda taji ciwo dan ya duba.
"Da sauƙi bayama min zafi sosai"
Iskan bakinsa ya hura ahanun kafun yaɗago ya kalleta.
"Amma nayi mamaki ƙwarai da abun daya faru ɗazu, ko dai tuntuɓe kikaji ne?"
Da sauri ta shiga kaɗa kanta. "Bankula da gabana bane alokacin danake tafiya shine kawai na buge da kujera" batasan sanda ta mulmulo wannan ƙaryan ta rantaɓa masa ba.
Kansa ya jinjina haɗe da sanya hanunsa ya rungumota zuwa jikinsa.
"Nagodewa Allah ma dayasa bakece da kanki kika faɗi ba, tray ne kawai ya faɗi, da bansan inda zansa kaina ba" yafaɗi haka yana me shafa gashin kanta da hanunsa.
Ɗan shirune yashiga tsakaninsu kowannensu da abunda yake saƙawa acikin ransa, tabbas bazata iya haƙura ba sai ta tambayeshi waye Jabeer agareshi, to amma tace masa me? tace masa me ya haɗasa da Jabeer tsohon saurayinta ko kuma me? bari dai tayi masa wani wayon, tafaɗi haka acikin ranta...
Ɗan sake gyara zamanta tayi haɗe da cewa. "Amm wai duka waƴannan abokanka ne?"
Murmushi yayi batare daya ɗago ya kalleta ba yace "Eh"
Kanta ta jinjina haɗe da sake cewa "Dukansu fa nake nufi"
Murmushi yakumayi saidai a wannan karon ya ɗago idanunsa ya kalleta.
"Eh dukansu abokaina ne, meya faru?" yatambayeta yana me tsareta da idanunsa..
Murmushi ta ƙaƙalo haɗe da cewa
"Babu ko mai kawai dai naga sunyi yawa ne, kuma naga wasu daga cikinsu banga fuskokinsu a wajen bikinmu ba shiyasa"
"Ae mu maza ba irinku bane munfiku yawan jama'a, wasu daga cikinsu basu samu daman zuwa bikinmu ba shiyasa bakisansu ba, kamar Jabeer baisamu halattaba saboda baya Nigeria yana Polland yana karatu, kuma baijima da dawowa ba, sauran kuma wani uzururruka ne suka hanasu zuwa, kinsan maza da sabgogi" yafaɗi haka yana me sake kwanciya acikin jikinta.
Yanzu tasamu amsar da takesonji cikin sauƙi, kenan dama Jabeer baya Nigeria ne shiyasa bainemeta ba, da sauri ta yi watsi da tunaninsa haɗe da ƙoƙarin zame Jikinta daga cikin nasa jikin.
Ƙara rungumeta yayi batare daya bata daman tashi ba, kallon cikin ƙwayar idanun juna suka shigayi, kallon tsananin SO Dr.Sadeeq keyi mata, yayinda ita kuma nakasa fassara wani irin kallo takeyi masa, na ƙauna nane ko na SO oho, Lumshe idanunsa yayi haɗe da buɗesu alokaci guda, yanayin yanda taga idanun nasa sun mareraice shiyasanya taji tsikar jikinta ya tashi, aduk sanda ta kalli cikin idanunsa takanji wani abu na ratsa har cikin ɓargonta, hakanne ma yasa bata ɗaukan lokaci me tsawo tana iya kallon cikin idanunsa, sosai idanunsa keyi mata kyau.
"Baby bacci nakeji!"
yafaɗi haka cikin murya me sanyi, yana me sake lumshe idanunsa.
"Ɓacci a wannan lokacin? Yanzu fa lokacin sallan isha ne"
ta faɗi haka cike da mamakinsa, tasan dai shiba mutum ne dayake da saurin bacci ba.
Hanu yasa yaɗan murza idanunsa, kansa kawai ya kaɗa mata batare dayace da ita komaiba yakoma jikinta ya kwanta. Yana lumshe idanunsa ladanin masallacin kusa da gidansu yasoma kwaɗa ƙiran sallah'n Isha. Jiki babu ƙwari haka yayi alwala yawuce masallaci..
Koda ta idar da sallah batayi yunƙurin tashi akan sallayan ba, zama tayi tana me rero karatun Al'Qur'ani ahankali.
Yana shigowa ta rufe Al'Qur'ani'n domin dama takai ƙarshen suran da take karantawa.
Direct bathroom ya wuce, tanajin ƙaran ruwa tasan wanka ƴakeyi.. Bawani jimawa sosai yafito daga shi sai towel ɗaure aƙugunsa, kallo ɗaya tayi masa ta ɗauƙe kanta, har yau bata iya jure ganinsa a haka, tashi itama tayi ta wuce bathroom ɗin donyin wanka.
Dogon wandon jeans kawai ya sanya ajikinsa haɗe da feshe jikinsa da turarensa me daɗin ƙamshi.. Kwanciya yayi lamo agadon haɗe da lumshe kyawawan idanunsa.
daga ita sai wani ɗanƙaramin towel tafito ɗaure ajikinta, yanzu kam bata wani jin kunyarsa sosai, tana iya fitowa gabansa a haka, sai dai idan taga ya kafeta da idanu, sai taji gaba ɗaya tayi wani irin da ita. Kallonta yayi yakuma sake lumshe idanunsa, yayi imani idan yaci gaba da kallon wannan haɗaɗɗiyar surar tata zata iya zautar dashi.
Turare kawai ta shafa ajikinta, ko sleeping dress batasanya ba, yau kuma da towel takeson kwana, kashe musu wutan ɗakin tayi ta kunna musu na bacci, wanda bashida haske sosai.
A maimakon tanufi gefensa ta kwanta, sai ji yayi ta haye kansa.
"Wayyo mama lutiya zata karyani!" yafaɗi haka aɗan shagwaɓe.
Sake sakar masa duka nauyinta tayi akansa, haɗe da cusa kanta cikin wuyansa.
"Kai nauyinka baisa na karye ba sai nine zan karyaka, ko kamanta kafini nauyi" taƙare maganar tana me manna masa wani irin hot kiss akan wuyansa.
Lumshe idanunsa yayi sosai yaji kiss ɗinnata ya ratsa shi.
"Wai yaushe kika zama haka ne princess?" yatambayeta, don harga Allah kwana biyun nan yana mamakinta.
Cikin rashin fahimtar maganan nasa tace "Bangane ba"
"Naga ne kindaina jin kunyana, sannan kuma nima da nake da kunyan nema kike ki lalatani ki maidani marar kunya"
Cizo takaimasa akan ƙirjinsa, wanda yasanya sa sakin wata ƴar ƙara.
Yana dariya yace
"To ƙarya nayi ai gaskiya nafaɗa, yanzu bakyajin kunyana ko kaɗan, har kaya kike cirewa a gabana..."
Wani cizon takuma kaimasa batare da ta bari yaƙarisa abunda yakeson faɗa ba, da sauri yatureta takoma ƙasansa shikuma yazama yana samanta, yayi mata rumfa da kirjinsa, duka hannayenta yakama yariƙe acikin nasa.
Cikin dariya ta soma ƙoƙarin ƙwace kanta daga jikinsa don talura cizon da tamai yakeson rama wa.
"Dan Allah kayi haƙuri bazan ƙaraɓa!" tafaɗi haka aɗan tsorace dan ta lura dagaske cizonta zaiyi.
"Ae babu maganar haƙuri yarinya, aƙirji kika cijeni, nima kuma dan haka aƙirjinki zan cijeki" yafaɗi haka yana me warware towel ɗin dake jikinta.
Cikin dariyan data kasa hanashi fitowa tashiga yi masa magiya amma yace sam shi sai ya rama.
Yana ɗaura bakinsa akan ƙirjinta, tayi shiru lokaci guda ta shiga sauƙe ajiyar zuciya akai akai, harwani lumshe idanunta take tsabar daɗin abun da yakeyi mata da takeji, shikuwa dagangan yayi mata haka so yake ya tsokalota sai yayi mata wayo yayi baccinsa, hanunta tasanya ta ɗago kansa, wani irin kallon tayi masa wanda ya rikirkitasa, bakinsu ta haɗe waje ɗaya, atare suka soma sucking lips ɗin juna, shida yake shirin mata wayo sai gashi ya susuce alokaci ɗaya, har yazo yafita ɓuƙata..... Bargo yaja ya rufe musu duka jikinsu, yana kwance akanta bacci me daɗi ya ɗaukesu.....
*****
*_ZAID_*
Tunda aka sallamosu daga asibiti baice da kowa ƙala ba, haushin kowa yakeji, tuƙuƙin baƙin ciki zuciyarsa keyi masa, ji yake yatsani kowa, bayamaso wani yashigo cikin lamarinsa..
Zaune yake a cikin falonsa, dagashi sai 3 guater jeans ko riga baidashi duk da kuwa irin sanyin da ake busawa a gari amma shi haka yake zaune a tuɓe, bawai kuma don bayajin sanyinba taurin kai dana zuciya ne kawai irin nasa ya hanasa suturta jikinsa.
Ƙafansa nakan rug yayinda kansa ke kalllon sama ya lumshe duka idanunsa, sake muskutawa yayi akaro na barkatai, haɗe kuma da ƙara ƙanƙame idanunsa da suke a lumshe, waishi adole so yake yayakice tunanin Zahrah acikin zuciyarsa, amma duk yanda yaso cire tunanin nata acikin ransa ya kasa, hanu yasa ya ɗan bugi kansa da ƙarfi, dai dai lokacin Afrah tafito daga cikin ɗaki daga ita sai wata ƴar ƙaramar riga dake sanye ajikinta, ko guiwarta rigan bata wuce ba.
Wani irin ƙamshin turaren dayaji acikin hancinsa ne yasanya sa buɗe idanunsa, ya watsa su akanta, kallonta yashigayi daga sama har ƙasa. "gatanan dai kamar wata ƴar kaza amma shegiya sai fitinan tsiya" yafaɗi haka acikin zuciyarsa, saboda ya lura kanta yana rawa, nema take ta shigarmai rayuwa taƙarfin tsiya, kuma zaiyi maganinta ne.
Afrah kuwa zuciyartane tashiga dukan uku uku, tsoronsa ne yasake shiganta bama kamar yanda taga idanunsa sun juye sunyi jajur dasu, harta juya zata koma ɗaki, saikuma ta tuno da shawarar da ƙawarta Asma ta bata, Asma tace mata " Zaid ɗan duniya ne yanason mata sosai, saboda haka tayi duk yanda zatayi ta shawo kansa ta hanyar nuna masa surarta a fili, idan ta nuna masa bata da kunya zasu dai dai ta" tunowa da waƴannan kalaman na Asma yasa Afra taji tasamu ƙwarin guiwa.. Sanja takunta tayi zuwa wani salo da ban, direct wajen dayake kishingiɗe ta nufa tana me motsa kowani gaɓa dake jikinta.
Bai taɓa yin zato ba saiji yayi Afra tafaɗo cikin jikinsa kamar wacce aka jefo, baikai ga buɗe idanunsa ba yaji ta saki wani irin munafukin ƙara..
"Wayyo Allah ƙafa ta honey kataimakeni na karya ƙafa ta" abun da Afrah ke faɗa kenan cikin iyayi.
Wani irin kallon takaici Zaid keyi mata, waishi zata gwadawa bariki, tafaɗo kansa da gangan sannan kuma tana yi masa ihun banza wai yataimaketa.
Da sauri yasake maida kallonsa gareta alokacin da zuciyarsa ta ƙitsa masa wani abu akanta.
"Tabbas hakanne ma, sai yanzu yasake lura da ita, amma ba ya gwadata ya gani" yafaɗi haka acikin zuciyarsa..
Da ƙyar ya iya buɗe bakinsa yaƙira sunanta "Afrah"
Dasauri Afrah dake yashe aƙasa tana kukan ƙarya ta ɗago kanta tana kallonsa jin da tayi yaƙira sunanta. "Kodai Target ɗina yafara aiki ne?" ta tambayi kanta .
"Ba ƙiranki nake ba da bazaki amsa minba!" yafaɗa murya aɗan kausashe.
"Kayi haƙuri honey ƙafa ta ce kemin zafi shiyasa" tafaɗi haka cikin yanayi na shagwaɓa tana wani yayyarfe hannu, ita adole so take ya faɗa cikin tarkonta.
Cike da tsananin takaicin ƙiransa da sunan honey da takeyi yasanyasa rumtse idanunsa da ƙarfi, ji yake kamar yaje ya shaƙeta bazai saketaba harsai yaga bata numfashi, amma akwai abun da yakeson ganowa a tattare da ita dolensa saiya daure.
"Zo muga me yasamu ƙafartaki"
Jiki na rawa Afrah ta matso garesa dama haka takeso yace, tana matuƙar so taganta akusa dashi, haɗa jiki dashi kuma shine burinta batun yau ba.
Hanu yasa ya kama ƙafarta ta, a hankali yashiga shafawa cike da wani irin salo, wayyo Allah Afrah dama haka takeso, ita kanta batasan sanda ta lumshe idanunta ba, wani irin daɗi takeji acikin jikinta, "Gaskiya shawarar Asma tayi aiki" tafaɗi haka acikin zuciyarta, cigaba yayi da shafa ƙafannata ahankali harzuwa wajen cinyoyinta, tuni ta narkemasa ajiki taƙara kusanto da kanta garesa, hanu tasanya akan faffaɗan ƙirjinsa tashiga shafawa ahankali, duk iskanci irin na Zaid saida ya tsaya yana kallonta, tabbas yanzu ya gano abun dayakeson ganowa atattare da ita, wani irin baƙinciki da ɓacin raine suka tokare masa maƙoshinsa.
"Hakan da Afrah keyi masa alamace dake nuna ita babaƙuwa bace a harkan tasan namiji kenan kome?" tambayar da yake tayiwa kansa kenan, shiba ƙaramin ɗan iska bane, yanda Afrah keyi masa alama ne dake nuna cewa tasaba irin haka da wasu mazan. "Kenan ita ƴar iska ce?" still yakuma tambayar kansa. Hanunsa yasanya ya damƙi gashinta haɗe da miƙar da ita tsaye, da fari ta ɗan tsorita amma ganin irin kallon dayakeyi mata yasa taɗanji sanyi acikin ranta, ganin sunnufi hanyar ɗakinsa yasa ta shiga sakin murmushi, daɗi taƙeji yau Allah zai cika mata burinta..
Suna shiga cikin ɗakin yasanya hanunsa da ƙarfi ya yaga ƴar fingilan rigar dake jikinta, take komai nata ya bayyana, hankaɗata yayi kan gado haɗe da soma yunƙurin zare belt ɗin dake jikin wandonsa,, idanu Afrah ta zaro waje amatuƙar tsorace, bata taɓa tsammanin haka daga garesaba ta ɗauka kasheta zaiyi da soyayya amma meyake shirin yi matane haka "Dukanta zaiyi ne ko kuma turmusheta zaiyi batare dayatsaya sunɗanyin romancing juna ba?" waƴannan tambayoyin sune suka cika zuciyarta fal...
(Me Zaid yakeyi hakane🤔 hahhhh da'alama dai yau amarci za'aci agidan Baba Zaid, team Zaid karkuyi nisa saboda nan gaba kaɗan Zaid zai buƙaci taimakonku, yayinda komai ya wakana tsakaninsa da amarya, inaga dole saikun shigo cikin lamarin😂)
*(Thank you my wattpadfans💋 Comment da vote ɗinku suna ƙaramin ƙarfin guiwa sosai, SON SO nake muku)*
*Vote and Comment please😘*
*6/February/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI!!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motive the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 107*
Tana ganin yagama zare belt ɗin jikinshi, tasoma ƙyaf ƙyaf ta idanu, kamar wacce aka kamata tana sata, tsoronsa ne ƙarara, ya bayyana akan fuskarta, ganin sa a haka tun farko, ya isa ruɗata, amma kuma dayake bariki ne a gabanta, ya sanya bata fuskanci hakan ba, sai yanzune taga, gaba ɗaya yacika mata idanu.
Cike da tsantsar rashin mutumci irin nasa, yasanya hanunsa ya jawo ƙafarta, zama yayi akan gadon, haɗe da sanya hanunsa akan fuskarta, ya matse mata baki, idanunsa yaɗaura akan ƙirjinta, wani irin murmushi yasake, haɗe da cije laɓɓansa, wai wannan tatsitsiyar yarinyarne, takeson ɗaukar hankalinsa, yaga waƴanda suka fita komai, bai kuma ji wani abu akan su ba, balle kuma ita ƙaramar alhaki, yanaji ajikinsa cewa. "A yanzu ba ayi wata mace wacce zata ɗau hankalinsa sama da Zahrah ba"
Hanunsa yakai kan wuyanta, yashiga shafawa a hankali, tsuru Afrah tayi tana kalllonsa, karo na farko a rayuwarta, da taji wani irin mugun fargaba ya daki zuciyarta, akan abun da ta aikata, "Me zata ce masa yanzu idan har yanemi haƙƙinsa awajenta?" take idanunta suka kawo ruwa taɗago ta kallesa.
Ko kallonta baiyi ba, ya ci gaba da shafa wuyanta, lumshe idanunta tayi, a zahirin gaskiya tana amsar saƙonsa, amma kuma acikin zuciyarta, tsoro ne yayi tasiri.
Ɗayan hanunsa yasanya ya yakice duk wani abu na sutura dayayi saura ajikinta.
Kamar wata mutum mutumi haka Afrah ta tsaya tana kallonsa.
"Tashiga ukunta idan wannan ingarman namijin ya haiƙe mata, batare da ya tsaya yayi romancing ɗinta ba"
ta faɗi haka acikin zuciyarta, bata ida tunanin nata ba, taga yayi off na wutan ɗakin..
Kwanciya yayi akanta, haɗe da sake mata gaba ɗaya nauyinsa, da ƙyar take iya fidda numfashi, sosai yayi mata nauyi, idan ba mugunta bama, taya zai kwanta akanta haka, aiko katifa ce saita lotse balle kuma ita.
Cikin zafi zafi yashiga kissing lips ɗinta. Yi yake kamar zai cijeta, dagani kai kasan muguntane ke cinsa, baƙaramin zafi kuwa hakan keyi mata ba, gaba ɗaya ya taune mata baki, lokacin daya ɗaura hanunsa akan breast ɗinta kuwa, saida tasaki kukan wahala, komai bayayi mata shi cikin nutsuwa, duk wani abu da ƙarfi yake yi mata, abu yake kamar me huce haushi.
Ganin da yayi zata cika masa kunne da kuka ne, yasanyasa sanya hanunsa ya matse mata baki. Yunƙurin ƙwace kanta takeyi amma ina bazata iya ba riƙon Zaid ba wasa ba.
*****
Wani juyawa kansa keyi masa lokaci ɗaya ya firgice, idanunsa ne suka kaɗa sukayi jajur dasu, yayinda jikinsa ke ɓari kamar wani mazari, iya ƙololuwar ɓacin rai a yau Zaid yashigesa, da ƙyar ya iya laluɓawa, ya sauƙa akan gadon, jefa ƙafafunsa kawai yake batare daya koda kalli gabansa bane, yana shiga cikin bathroom ya banko ƙofar da ƙarfin gaske.
Jikin Afrah ne ya ɗauki tsuma, take ta fashe da wani irin kuka me taɓa zuciya.
"Wayyo Allah na, nashiga uku, me zancewa Zaid? kaicona, nakasa haƙuri, gashi yanzu na jawa kaina" abun da Afrah ke faɗa kenan acikin zuciyarta, gaba ɗaya tsoron ma tashi daga kan gadon take, da ƙyar ta iya jan bargo ta rufe jikinta dashi.
Ruwa ne ke dukan kansa, yana tsaye agaban shower kamar wani statue, iyaka ƙololuwar ɓacin rai, yau ya shigesa, baitaɓa tunanin zaiji ciwo acikin zuciyarsa, wai dan yasamu Afrah ba a cikakkiyar virgin ba, sai gashi abun ya juye tunaninsa.
"Ashe dama haka maza sukeji, idan basu samu matarsu a cikakkiyar budurwa ba?" yatambayi kansa.
"ZAHRAH"
itace wacce tafara faɗo masa acikin ransa, take fyaɗen da yayi mata yashiga dawowa cikin kansa filla filla, tamkar alokacin komai ke wakana haka yaji acikin jikinsa, da sauri yasanya hanu ya kama kansa, haɗe da kurma wani uban ihu, yama manta da cewa acikin toilet yake.
Wani irin nadama ne me girma ya ruskesa acikin zuciyarsa, sai yanzu ya tabbatar da cewa bai kyautawa Zahrah ba, yaku ma cutar da ita cutarwa me girma, ya ruguza mata alfaharinta.
"Meyasa yayiwa Zahrah haka? me yasa yarabata da budurcinta? wani irin cutarwa ne yayiwa Zahrah haka?" yatambayi kansa cikin tsananin tsana da ƙyamar kansa.
"I hurt you Zahrah, why do i did this to you? I'am stupid, i dont have sense, meyasa zan aikata haka? kaicona dana cutar da rayuwarki, na gusar miki da farincikin ki, na hanaki mallakawa mijinki budurcinki, na ƙwace budurcinki taƙarfin tsiya, forgive me, i hate my self, because of what i did to you, natsani duk wata rayuwar duniyar nan, rayuwa batamin daɗi Zahrah!!" cikin wani irin murya me haɗe da sautin kuka Zaid ke faɗan haka.
Haƙiƙa yau baida abun da zaice, yasan Allah ba azzalumin kowa bane, sai wanda ya zalunci kansa, gashinan shi ya zalunci kansa, kuma yagani, gashi yanzu Allah ya haɗashi da wata ballagazar mace, wacce ta raba budurcinta ga mutanen titi, yanzu ga abun da Zina ta haifar masa, bayajin son Afrah ko ɗigo acikin zuciyarsa, amma kuma yaji matsanancin ciwon samunta a haka da yayi, to idan dai shi yaji ciwon samunta ahaka, me mijin Zahrah kuma zaice? shida yake so da kuma ƙaunarta.
Jingina kansa yayi da jikin bangon toilet ɗin, yayinda ruwan dake fitowa acikin shower ke dukan bayansa. Rumtse jajayen idanunsa yayi, haɗe da sanya haƙoransa ya danne laɓɓansa, jiyake kamar yata gwara kansa ajikin bango, har sai kan ya rabe gida biyu, koda zaiji salama, acikin zuciyarsa, hanunsa na dafe da saitin zuciyarsa, dake yi masa zafi, yajima a tsaye ruwa na dukansa, har sai da jikinsa yasoma karkarwa kafun ya kashe shower'n....
Buɗe ƙofarsa, yayi dai dai da bugawan zuciyar Afrah, take jikinta yacigaba da karkarwa kamar anjona shocking.
Ko kallon inda take baiyi ba, direct gaban drawer ɗinsa ya nufa, wata farar T-shirt ya ɗauka ya sanya ajikinsa.
Ganin baice da ita komai ba, yasanya ta daɗa firgicewa, batasan me ze mataba nan gaba, cikin muryarta me ɗauke da tarin tsoro, haɗi da fargaba tace.
"Dan Allah kayi haƙur......"
"Get out!!"
yafaɗi haka batare daya bari ta ƙarasa maganar dake cikin bakinta ba.
Cikin kuka takuma cewa
"Dan Allah kayi...."
"I say get out!!!"
yafaɗi haka atsananin tsawace, har sai da Afrah taji ƴaƴan cikinta sun kaɗa.
Gaba ɗaya ta ruɗe ta firgice, yanayin yanda taga idanunsa sunyi jajur dasu, shine abun da yafi komai ɗaga mata hankali, da gudu ta fice daga cikin ɗakin, ko kayanta bata tsaya ɗauka ba, sai blanket ɗin da tayi amfani dashi wajen rufe jikinta.
Kwalbar turaren dake riƙe a hanunsa ya yi wurgi dashi, zuwa wajen wani ƙaton mirror wanda ke kafe ajikin bango, take mirror'n ya fashe, haɗe da tarwatsewa a ƙasan tiles.
Wani irin huci yake fitarwa ta bakinsa, yayinda yasanya duka hannayensa ya kama ƙugunsa, jiyake gaba ɗaya duniyar na juya masa.
"Me ake da irin wannan rayuwa, me ɗauke da takaicin?" yatambayi kansa.
Idanunsa ya sauƙe akan fridge ɗin dake ɗakin, wanda yake a cike da kwalbar wine ɗinsa, a irin wannan halin dayake ciki, wine ce kaɗai zata iya bashi nutsuwa, duk da yasan ba lallaine ta iya ciresa acikin ƙuncin dayake ciki ba, amma tabbas zata iya rage masa damuwa, sai dai kuma bayajin aduniya zai iya ƙara aikata wani abu na saɓon Ubangijinsa, ko a iya nan Allah yaɗauki rayuwarsa, haƙiƙa ya jarabtu, soyayyar Zahrah kaɗai da Allah, yasanya masa, yazamemasa babban jarabawa acikin rayuwarsa.
Zama yayi a bakin gado, haɗe da bin blanket ɗin dake shimfuɗe akan gadon, da kallon takaici, bakomai ne yafaɗo masa arai ba, kamar randa yayiwa Zahrah fyaɗe, haka gaba ɗaya tsakiyar gadon ya ɓaci da jininta, yasamu Zahrah a cikakkiyar budurwa.
"Yayi gaggawa? me yasa bai bari ya amshi budurcinta ta hanyar aure ba?" wasu siraran hawayene suka fito daga cikin idanunsa, suka sauƙa akan ƙuncinsa, sakamakon tunowa da yanda ya farke Zahrah da yayi.
Ahankali ya taka ƙafarsa ya ƙarasa gaban wani tangamemen hotonta, dake liƙe ajikin bangon ɗakin.
Zama yayi agaban hoton haɗe da cewa.
"Kiyafemin Zahrah, a yanzu nayi nadama marar amfani, ni dakaina namiki fyaɗe, nidakaina nasa aka je har ƙofar gidanku aka ya da ke, meye amfanina Zahrah? me yasa nazamo mugu maƙuntaci agareki? nagodewa Allah dayasa baki aureni ba, domin ban cancanci zama miji a gareki ba, ni ban dace dake ba Zahrah, to tayama zan dace dake? ninefa wanda yayi miki fyaɗe, nine azzalumin dana rufe idanuna, na aikata ba dai dai ba akan ki, to taya zaki yarda ki aureni, a'a ko kin yardama ni bazan yarda ba, domin ni dake bamu dace ba, bazan yarda nasake cutar dake akaro na biyu ba, inasonki Zahrah so ba irin wanda kika sani ba, inamiki son da aduniya banayiwa kowa irinsa, sonki ajinina yake, har abada bazan taɓa daina sonki ba, ki hukuntani Zahrah, kimin duk irin hukuncin da kikeso, nacancanci ki hukuntani Zahrah, ko kasheni kikayi bazanga laifinki ba, saboda nasan koda kasheni ɗin kikayi bazaki huce daga abun dana aikata a gareki ba, ki ɗaga hanu ki dakeni Zahrah, kice Zaid natsaneka, banasonka, ki faɗi haka agareni Zahrah dan Allah, ki faɗa ko zanji salama acikin zuciyata!!!"
kuka sosai Zaid keyi kamar wani yaro ƙarami yana me rungume da hoton Zahrah acikin ƙirjinsa.
Yayi kuka irin wanda bai taɓayin irin saba, yayi kuka wanda har sai da ya haifar masa da ciwon kai, kusan sama da awa ɗaya ya ɗauka yana zaune, agaban hoton Zahrah, da ƙyar ya'iya jaye jikinsa a wajen, ya faɗa bathroom, alwala yayi haɗe da buɗe kofar yafito, idanunsa sunyi luhu luhu dasu, kallo ɗaya zakayi masa kasan ya sha kuka ya ƙoshi.
Blue ɗin jallabiya yasanya, direct ya wuce masallaci, duk da cewa kowa yagansa zai gane cewa yana a cikin damuwa, amma sam baidamu da hakan ba, uban kowa ma yasan yana cikin damuwa, shiba damuwarsa bane, matsalansa ma kaɗai ta ishe sa.
Tunda tashiga cikin ɗakinta take kuka, yau ne karo na farko a rayuwarta, da tayi babban nadamar bada kanta da tayi a waje, yau tayi nadama ƙwarai, yau ta ga sakarci dakuma wautanta, da ta ɗauki kyautar budurcinta sukutum, ta dan ƙawa wani banza, wanda yayi mata ƙaryan zai aureta, me ake da irin wannan rayuwar, wayewar banza, wayewar wofi, taɗauki zugan ƙawayenta, da suke ce mata wai inmace batasan daɗin sex ba bata waye ba, ta biyewa son zuciyarta taje ta bawa wani banza kanta, batare da sadaki ba ya haye kanta, ya karɓi budurcinta, batare da ko da sannu ba, wace irin banzar hallakakkiyar waye wace wannan? wayewar da zata saka kaji kunyar Allah da ta mutanen duniya, kaicon irin wannan wayewar, tir da irinta, bata taɓa manta yanda su Asma ke zugata akan cewa wai yakamata ta bada kanta ga saurayinta Ameer, ta kuma san duniya, duniya ma ta santa, har cewa suke wai ita baƙauyiya ce, saboda kawai bata yarda wani namiji ya taɓa jikinta, haka suke wareta acikinsu, haka suke nuna mata kyara, wai don kawai bata bari maza suna taɓata, tabiye sharrin zuciya data ƙawaye, ta kuma ɗauƙi shawararsu, ta yi watsi da mutuncin kanta, gashi yanzu tun aduniya, ta shiga kunyar mijinta, takuma shiga halin nadama da danasi, ga kuma tozarcin da zata fuskanta daga wajen mijinta.
Zama tayi daɓas aƙasa tashiga rera kukanta, haɗe da tsinewa Asma da ma duk wasu ƙawayenta, da sukayi ruwa da tsaki, wajen tsundumata, cikin halakan data faɗa, shikuwa saurayinta Ameer, wanda shiya fara saninta ƴa mace, ta zuba masa tsinuwa yafi guda ɗari biyu, da ƙyar ta iya lallaɓan kanta tashiga toilet donyin wanka..
Yajima acikin masallacin kafun ya dawo gida, abun dayajima baiyiba kenan, wai yaje masallaci yajima har haka, karatun Al'Qur'ani yayi, kuma da yardan Allah yaɗan samu salama acikin zuciyarsa..
Afrah najin shigowarsa cikin gidan, ƙafafunta yasoma rawa, take taji wani irin ciwon ciki ya kamata, mugun tsoronsa takeji, tun ada ma, balle yanzu kuma da wannan abun yashiga tsakaninsu, ta tabbatar sai yakasheta acikin gidannan, kuma ya kashe banza.
Yana shiga cikin ɗakinsa, ya ɗauki magungunansa yasha, tashi yayi yafice daga cikin ɗakin nasa, direct ɗakinta ya nufa.
Tanajin motsin ana buɗe ƙofarta ta miƙe zunbur, take wani irin fitsari ya zubo mata, tsabar tsoro, aikuwa tana jefa idanunta, cikin nasa, taji numfashinta, na shirin ɗaukewa.
Da rinannun idanunsa yake kallonta, ganinta da yayi yasake tuna masa ɓacin ransa, jiyake ya tsaneta, amma kuma yazama dole yayi mata tambayoyin dake cikin ransa..
"Zauna" yafaɗi haka cikin dakiya.
Jikin Afrah na rawa ta zauna aƙasan tiles.
Ƙafansa ɗaya yasanya, yataka kan gado, haɗe da ɗan ranƙwafowa.
"Dama ke karuwa ce?" first tambayar daya fito daga cikin bakinsa kenan.
Ƙirjin Afrah ne ya buga, take hawaye suka ɓalle akan fuskarta, kanta tashiga girgizawa alamar
"A'a"
Laɓɓansa ya cije cike da takaici yace.
"Da bakinki nakeso, ki bani amsa bada kai ba."
"A....a wallahi ni.....ba..ba..ka..ruwa..bace!" murya a sassarƙe tabashi amsa.
"Kinsan me ake ƙira da karuwa?"
Yatambayeta.
Dasauri ta kaɗa kanta, saikuma tatuna da abun dayace mata, baki na rawa tace "Karuwa itace mebin maza, wacce take zaman kanta"
"Good, ashe kinsan mene ake ƙira da karuwa, kenan ke ɗin karuwa ce?"
Da sauri tace "Wallahi niba karuwa bace"
"Idan ke ba karuwa bace, dan ubanki ina kikai budurciki!!!" amatuƙar tsawace yayi maganar, saboda ya matuƙar harzuƙa.
Guntun fitsarin da take ta riƙewane ya silalo, tsabar ta tsorata, ƙyarma tafara tamkar wata mejin sanyi, tsabar tsorata da yanayinsa da tayi, ta makasa ce dashi komai.
"Shirun da kikayi ya nuna alamar cewa eh ke cikakkiyar karuwace, mazinaciya, me kike nema arayuwarki, kina ƴar ƙaramar yarinya dake?" yatambayeta yana me ƙare mata kallo.
Kanta tashiga girgizawa, akaro na barkatai.
"Kayarda dani, wallahi niba karuwa bace, bantaɓa karuwanci ba!" tafaɗi haka tana kuka.
"Okay to tunda dai kince ke ba karuwa bace, ba naci ubanki, wataƙila zaki faɗamin inda kika kai virginity ɗinki" yafaɗi haka yana me ƙoƙarin zare belt ɗin wandon jeans ɗin dake sanye a jikinshi.
Da gudu ta rarrafo ta ƙaraso garesa, zubewa tayi akan ƙafafunsa tana kuka.
"Dan Allah kayi haƙuri, kayafemin, wallahi sharrin shaiɗanne, dakuma na zuciya, amma bantaɓa zaman karuwanci ba!" kuka take wiwi kamar wacce akace uwarta ta mutu.
Tsayawa yayi cak yana me kallonta, kuka take tsakaninta da Allah.
"Mene naka najin haushinta Zaid? mene naka nacewa zaka daketa? idan ita karuwace kai menene?" wata zuciyarsa ta tambayesa.
Rumtse idanunsa yayi haɗe da cije laɓɓansa, da ƙyar ya iya janye ƙafafunsa ya zauna, abakin gado.
Afrah dake duƙe a ƙasa tana kuka ya kalla.
Cikin wata irin murya a cushe yace. "Afrah!"
Dasauri Afrah taɗago fuskarta ta kalleshi, duk taɓata fuskar ta da majina, ansha kuka anƙoshi.
"Zo" yace da ita ataƙaice.
Babu musu ta ƙaraso gabansa ta durƙusa.
"Meyasa kika zaɓi banzatar da mutuncinki a waje Afrah?" tambayar dayayi mata kenan, sai dai wannan karon, ba acikin tsawa yayi mata tambayar ba.
Cikin kuka Afrah tasoma cewa "Bansan dalili ba, amma nabiyewa son zuciyata ne kawai, nabiyewa zugan shaiɗan da kuma shaiɗanun ƙawaye, najefa rayuwata a halaka, nasan irin wannan ranan zatazo, amma bantaɓa kawo cewa al'amarin zai kai har haka ba, domin wanda ya fara sanina amatsayin ƴa mace, yayimini alƙawarin aure, saboda haka bantaɓa kawowa araina cewa rashin kasancewata ba a budurwa ba zai kawo min wani abu, saboda na ɗauka wanda yafara sanina a cikakkiyar ƴa macena shine wanda zai aureni, ashe shima ƙarya yakemin, ba aurena zaiyi ba, yayi hakane kawai,dan na amince nadinga bashi kaina, aduk sanda ya buƙata!" taƙare maganar tana me tsananta kukanta.
Rumtse idanunsa yayi, haɗe da cije laɓɓansa, akaro na sau babu adadi.
"Banason kuka" yafaɗa ataƙaice yana me kawar dakansa gefe.
Duk da cewa kukan nacinta, amma haka ta haɗiye, tasoma ƙoƙarin yin shiru.
"Kinyi wanka?" yatambayeta still kansa na na kallon wani wajen.
"Eh" tafaɗa murya a raunane.
Miƙewa yayi daga zaunen da yake, haɗe da dubanta.
"Zanshiga na kwanta, banason naji koda motsinkine, ki zauna anan ɗakin, banason damuwa" yanakaiwa nan azancensa, yasakai yafice daga cikin ɗakin.
Afrah kam kan gadonta ta haye taci gaba da rera kukan danasani, ahaka har baccin wahala ya ɗauketa.
Zama yayi akan gado, haɗe da ɗaura idanunsa akan hotonta, hawayene suka zuraro daga cikin idanunsa, abune mawuyaci yadaina sonta, duk da yasan a yanzu ta haramta agareshi, kuma yana gudun ɗaukarwa kansa zunubi, amma kuma akan sonta, baya iya control ɗin zuciyarsa, akullum maganaɗisun ƙaunarta, ƙara fusgarsa take, saidai kuma kamar yanda yaɗaukarwa kansa alƙawari, zai ci gaba da addu'a har Allah yakawo masa sauƙi da sassauci acikin zuciyarsa akan soyayyarta..
*(So ba ƙarya bane, So gaskiyane, amma kuma wanda baitaɓa yiba bazai gane ya yake ba, haka kuma wanda baiyi zurfi acikin saba, bazai taɓa gane ya zafinsa yake ba, ba acire so alokaci guda, a sannu komai yake gushewa, ƙauna acikin jini take, bata taɓa gushewa, watarana a sannu so zai gushe, amma ƙauna tana nan. Ku yiwa Zaid da Zahrah uzuri, wallahi soyayya ta wuce gaban kwatance, idan kanason abu baka ganin laifinsa, shi so hana ganin laifi ne, meyin so shikaɗaine zai gane inda kalamaina suka dosa.)*
*(Yau fejin nasu Zaid ne, bazamu waiwaya gidan Doctor ba, team Doctor da Zahrah i'am sorry)*
*9/february/2020*
*Fatymasardauna*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 108*
Kaikawo take tayi a cikin kitchine ɗin, sauri take ta kammala aikinta, tsaye take acikin kitchine ɗin, tana wanke wani plate dake riƙe a hanunta, sosai nayi mamakin ganinta a haka, rigace irin T-shirt me faɗinnan sanye ajikinta, duka duka tsayin rigar ko rabin cinyanta bai ƙarasa ba, bata kuma sanya wando dan rufe cinyoyinta ba, wani irin slipper ne me kyaun gaske sanye aƙafarta, wanda aka ƙawata samansa da wani kyakkyawan follower,
Irin yanayin shigar nata yasanya tayi kama da irin yaran turawan nan.
Sam bata ji motsin shigowarsa ba, hakan yasa bata kawo cewa akwai wani mahaluƙi dake kallonta ba.
Sake gyara tsayuwarsa yayi, haɗe da jingina bayansa, da jikin ƙofar fita daga kitchine ɗin, sosai tayi masa kyau, babu abun daya fi ɗaukar hankalinsa ajikinta, kamar hips ɗinta, ga santala santalan cinyoyinta, da suka bayyana kansu, gwanin ban sha'awa, gaskiya komai na Zahrah me kyau ne, ta cika mace hundred percent, yajima yana fata da burin samun cikakkiyar mace, me cikar halitta ka marta, a matsayin matar aurensa, sai gashi Allah Ya dubesa ya basa Zahrah.
Ɗan tsayawa tayi, haɗe da sanya hannayenta bisa ƙugunta, tana me sauƙe numfashi, a hankali, da'alama dai akwai gajiya a tattare da'ita.
"Kin gaji ko?"
Cike da mamakin jin muryarsa, acikin kunnuwanta, da tayi ta juyo, tana me fuskantarsa.
Murmushin sa me kyau, ya sakar mata, haɗe da soma takowa zuwa gareta.
"Yaushe kadawo bansani ba?" ta tambayeshi, cike da tsananin mamaki.
"Najima da dawowa, nadai tsaya kallon abar sona ne" yafaɗi haka yana me lumshe gajiyayyun idanunsa, sosai yakejin gajiya ajikinsa, baƙaramin aiki yau yasha a office ba.
"Sannu da dawowa!"
tafaɗa tana sakarmasa murmushi.
Jawota cikin jikinsa yayi, haɗe da rungumeta, kansa ya ɗaura akan wuyanta, wata ajiyar zuciya, me ƙarfi ya sauƙe.
"Nayi kewarki sosai my lovely wife!" cikin murya, me sanyi, ya yi maganar.
Murmushi takuma sakar masa, haɗe da langwaɓar da kanta gefe gudu. "Nima nayi kewarka Hubby na!" cikin salo ta ƙare maganar.
"Dagaske kema kinyi kewata my wife? nifa dukanki nayi kewarki!" yafaɗi haka yana meyi mata wani irin kallo, dake ɗauke da wani tarin ma'anoni masu yawa.
Ganin kallon dayakeyi mata, yasa tasaki murmushi me ɗan sauti, ƙoƙarin janye jikinta daga nashi tasoma yi.
Ƙam ya riƙeta, haɗe da sake mannata acikin chest ɗinsa, da alama dai bayason tacire jikinta acikin nasa jikin.
"Uh dan Allah, Kabarni na ƙarisa aikina, kuma mafa duk ƙauri nake, amma kaketa mannani a jikinka, kaɗan bari nayi wanka kaji!" tayi maganar cikin yanayi na lallashi, tasani sarai, idan dai ba lallashinsa tayi ba, to bazai bari ta kammala aikin data fara ba.
"Nidai naƙi wayon, kuma ni banji wani ƙauri da kike ba, princess nadawo amatuƙar gajiye, gashi kuma ganinki ahaka yasake ɗaura min wani gajiyan, please kiyarda ko 30 minute ne kiban, ina da buƙatarki fa akusa dani...."
Bata bari ya ƙarasa zancen nasaba, tayi saurin toshe masa baki da tafin hanunta, shagwaɓe fuska tayi, haɗe da marerece idanunta, kanta ta girgiza masa akan kada yace komai.
Hanunsa takama, suka fice daga cikin kitchine ɗin, haka yake binta tamkar wani raƙumi da akala, suna shiga cikin bedroom, ta zaunar dashi akan gado, bathroom ta wuce direct, ruwan wanka me ɗan ɗumi, ta haɗa masa acikin bathtub, haɗe da sanya masa turaren wanka, me daɗin ƙamshi, acikin ruwan, take banɗakin ya gauraye da ƙamshi, tana fitowa daga cikin bathroom ɗin, ya kafeta da manyan idanunsa, durƙusawa tayi ta cire masa takalmi, da kuma safar dake ƙafarsa, ita da kanta tacire masa suit ɗin jikinsa, dakuma necktie ɗin dake saƙale a jikin wuyansa, Hanunta ta sanya, ta shiga ɓalle masa aninayen rigar dake jikin sa, ahankali ta zare masa rigar, shi dai haka ya tsaya, yana kallonta, yana me kuma lumshe idanunsa, lokuta zuwa lokuta, murmushine ya bayyana akan fuskarta, lokacin da idanunta, suka sauƙa akan faffaɗan chest ɗinsa, haƙiƙa yanada jiki me kyau, tasan hakan kuma, bazai rasa nasaba, da yawan gym ɗin dayakeyi ba.
Kallonsa tayi haɗe da sake sakarmasa murmushi, hanunsa ta kama daniyar janshi zuwa cikin toilet, da ƙarfi yajawo hanunnata, tafaɗa jikinsa, matseta yayi ajikinsa, haɗe da matso da fuskarsa gaf da tata.
"Ahakane zanje nayi wankan, bayan baki ciremin kaya ba?" yafaɗi maganar ƙasa ƙasa.
Cikin rashin fahimta tace.
"Wani irin kaya kuma, bayan wanda nacirema yanzu?"
Hanunta yakama, ya ɗaura akan belt ɗin dake saƙale jikin wandonsa, tsareta yayi da idanu, da'alama dai har wandon ma, so yake ita tacire masa da kanta.
Kunyan sane ya kamata, amma tasan wayon da zata masa.
"Naji zancirema, muje cikin toilet ɗin" tafaɗi haka tana nufar ƙofar toilet ɗin.
Jin abun da tace, yasanyasa, rufa mata baya, suna shiga cikin toilet ɗin tadawo baya, da sauri tafice daga cikin toilet ɗin, ta rufosa ta baya.
Dariya tashiga ƙyalƙyalawa, tana mejin daɗin wayon da tayi masa.
"I am sorry Hubby, kayi wanka kaji, banaje na kula da girkina, kada ya ƙone!" tafaɗi haka cikin muryar da ta tabbatar cewa zai jiyota.
Jin da tayi yana ƙoƙarin buɗe ƙofar toilet ɗinne, yasanya da sauri ta fice acikin ɗakin gaba ɗaya, tana dariya.
Murmushi me sauti shima yayi, kana ya girgiza kansa, waishi Zahrah zatayiwa wayo, hmmm.
Kwanciya yayi acikin bathtub ɗin , sosai yaji daɗin ruwan wankan data haɗa masa, ga ɗumi ga kuma ƙamshi me daɗi, a hankali gajiyarsa ta soma warwarewa.
Tana kammala girkin, ta zuba acikin manyan food flask, haɗe da jeresu cikin basket's masu hanu, sosai takejin, gajiya ajikinta, amma yazatayi, tunda ita tasanya kanta, duka kwanukan datayi aiki dasu, saida ta wankesu tas, kana ta gyara kitchine ɗin nata, lokaci ɗaya komai na kitchine ɗin, yadawo tsab dashi.
Tana shigowa cikin ɗakin, bata ko kalli inda yake ba, da sauri ta faɗa cikin bathroom, sam bataso ma yaganta a haka, wujiga wujiga da ita, duk ƙamshin kayan girki take, ruwan ɗumi ta tara tayi wankanta, take itama taji rabin gajiyarta, ya kama gabansa, towel ta ɗaura ajikinta, haɗe da buɗe ƙofar bathroom ɗin tafito.
Tsayawa tayi tana kallonsa, Tsaye yake agaban dressing mirror, yayi matuƙar kyau, cikin sky blue ɗin, shaddan dake jikinsa, agogo yake ƙoƙarin ɗaurawa a tsintsiyar hanunsa, yayinda tulin gashin kansa ke ta faƙan ƙyalli, da'alama dai yasha gyara, da man gashi, na musamman, akan fuskarsa kuwa, ƙawataccen sajensa ne, ya samu waje, ya kwanta luf akan ƙuncinsa.
"Wallahi duk wanda yace Dr.Sadeeq, bai haɗu ba yayi ƙarya" Zahrah tafaɗi haka acikin zuciyarta.
Dawo da kallonsa yayi gareta, fuskarsa ɗauke da murmushi yace. "Sannu da fitowa, Hajiyar wayo"
Itama murmushin tayi masa, haɗe da takowa zuwa garesa, hakanan ta tsinci kanta, da matuƙar son rungumesa, lokaci ɗaya ta faɗa jikinsa, haɗe da ɗaura kanta akan ƙirjinsa, shima dama nema yake, sosai ya matseta acikin jikinsa, tare da sanya hanunsa, akan bayanta, yana shafawa, a hankali, lumshe idanunsu, sukayi su duka, suna masu, sauƙe ajiyar zuciya.
"Kayi kyau sosai Hubby!" Zahrah tafaɗa cikin murya me sanyi.
"Nagode my princess!"
yabata amsa, yana me faɗaɗa, murmushin dake, kan fuskarsa, yanason Zahrah har acikin ɓargonsa, so sosai yakeyi mata, ko kaɗan baya fata Allah, Ya nuna masa, ranan dazai ɓata mata, alƙawari ya ɗaukarwa kansa, cewa Insha Allah, Bazai taɓa wulaƙanta Zahrah ba, koba komai itaɗin farincikinsa ce, sannan kuma tana da, wani irin girma, na musamman, acikin idanunsa, itace mace ta farko, daya fara sani, acikin rayuwarsa, itace macen data fara, jiyar dashi wani daɗi, wanda bai taɓa sanin akwai irin shi, acikin wannan, duniyar ba, Zahrah ta shayar dashi zumanta, wanda ɗanɗanonsa, keda wahalan mantawa, duk da cewa bai sameta, amatsayin cikakkiyar budurwa ba, amma haƙiƙa tanada wani, matsayi na musamman agareshi.
"Hubby!!"
taƙira sunansa cikin wani irin cool voice.
"Ummm princess ɗina, ya akayi ne?" yayi maganar yana me duban fuskarta.
Murmushin dake ƙara mata kyau, ako da yaushe idan tayishi, tasakar masa, haɗe da zare jikinta daga nasa, body lotion ɗinta tajawo tasoma shafawa, batare da tace da shi, komai ba.
"Na lura tunda nace miki, yau zamu fita, kike ta ɓare ɓare, kodai ma nace na fasa ne" yafaɗi haka yana me jingina kansa da bango, alamar nazari.
Da sauri ta juyo ta kalleshi.
"Dan Allah, Hubby karkace ka fasa, kaga fa har na kammala abincin!" tafaɗi haka a shagwaɓe.
Murmushi yayi haɗe da cewa "Cigaba da abun da kikeyi, wasa nake miki"
Murmushin jin daɗi tayi, haɗe da ɗaukan powder, tasoma shafawa akan fuskarta.
Batayi wani kwalliya sosai ba, janbaki da kwalli kawai ta saka, saikuma mascara, wanda sakasa yazamemata sabo, dazaran ta goga akan eye lashes ɗinta, sai kaga kamar eye lashes ɗin kanti tasanya, sosai kuma tayi kyau.
Wata haɗaɗɗiyar abaya gown, wanda aka sanya mata, acikin kayan aure, taciro ta sanya, sosai rigan ta amshi jikinta, da ɗan madaidaicin vail ɗin rigar, ta yane kanta zuwa wuyanta.
Wani flat shoe, me igiyoyi ta zura a ƙafafunta, kana ta fice zuwa falo, domin dama tuni Dr.Sadeeq ya jima, a falon yana jiranta.
Yana ganinta, ya lumshe idanunsa, yayinda murmushi ya faɗaɗa akan fuskarsa, cike da zolaya yace.
"Baƙuwa mukayi ne? sannunki da zuwa, ɗan ƙaraso ki zauna anan" ya ƙare maganar yana meyi mata, nuni da gefensa.
Dariya ne yakama Zahrah, tsayawa tayi agabansa, haɗe da ɗanyi masa fari da idanu.
"Yadai malam ko ka ƙyasa ne?" taƙare maganar tana me kama ƙugunta da duka hannayenta.
"Sosaima kuwa, gaskiya kinyimini, minti biyu please!" yafaɗi haka, yana me kashe mata idanunsa ɗaya, haɗe da ɗage giransa sama.
Dariya suka saka, su duka biyun, haɗe da miƙa masa hanu suka tafa.
Riƙe da hanun juna, suka nufi dinning area, plate ta ɗauka ta zuba musu fried cous cous, dakuma sauce egg, wani plate ɗin takuma ɗauka, ta zuba musu pepper soup, take gurin ya gauraye da ƙamshi. Harshensa yasanya ya lashe laɓɓansa, haɗe da ɗan lumshe idanunsa.
"Babe abincin nan fa zaiyi daɗi, tunkafun naci, har naji taste ɗinsa acikin bakina"
Dariya kawai tayi, haɗe da turo masa plate ɗin abincin gabansa, zama tayi akan cinyarsa, da hanunta take eban abincin, tana kaiwa bakinsa, idan tasamai abincin abaki, sai ya tsotse mata yatsunta kaf, kafun yake sakewa, ita dakanta taciyar dashi, kana itama taci, suna kammalawa ta tattara komai dake, wajen takai kitchine, fitowa tayi daga cikin kitchine ɗin, hanunta ɗauke da baskets guda biyu, aje baskets ɗin tayi akan dinning table, kallonta tamayar kansa.
"Yakamata muje ko, kaga dare fa yanata ƙarayi"
Wayarsa dake riƙe ahanunsa, yajefa acikin aljihun rigansa, haɗe da ɗaukan duka baskets, ɗin yanufi hanyar fita daga cikin falon, da sauri ta wuce cikin ɗaki, ta ɗauko hand bag ɗinta, kana ta rufa masa baya.
Saida suka hau titi, kafun ya dawo da kallonsa gareta.
"Ina zamu fara zuwane, gidan Hajiya ko kuma gidan Inna?" ya tambayeta.
"Mufara zuwa gidan Hajiya, inaga zaifi ko" tafaɗa tana kallonsa.
Kansa yajinjina, kana yaci gaba da tuƙa motar..
Yana danna horn, mai gadi ya wangale masa makeken gate ɗin gidan nasu, tura hancin motar tasa yayi zuwa cikin gidan.
Tana fitowa acikin motar, ta ɗauki ɗaya daga cikin baskets ɗin ta riƙe a hanunta, hanunsa yamiƙo alamar ta bashi basket ɗin ya ɗaukar mata.
Waro idanunta tayi, haɗe da cewa "Karufamin asiri, kabarni na ɗauki basket ɗinnan, salon nabaka, Hajiya taganka tace na mallake mata ɗa"
Dariya maganarta ta ta basa.
"Ko Hajiya batace ba, ai dama kin mallakeni" yafaɗi haka yana dariya, dariya kawai itama tayi, amma bata yarda, ta bashi basket ɗin ba.
Yana gaba tana biye dashi a baya, haka suka nufi ƙofar da zata sadasu da falon Hajiyarsa.
Da sallama ɗauke a bakinsu suka shiga cikin falon, huwaila me aikin Hajiya dake zaune aƙasa tana kallo, itace ta amsa musu sallaman nasu, cike da ladabi tashiga gaidasu, Dr.Sadeeq ya amsa haɗe, da tambayarta ina Hajiyarsa, "Tana sama" Huwaila tabasa amsa. "Je kice mata munzo" yafaɗi haka yana me zama akusa da Zahrah, da sauri Huwaila ta haura sama don cika umarninsa.
Kallonsa tayi haɗe da ƙoƙarin matsawa daga kusa dashi, hanu yasa ya danne mata cinya, "Ina kuma zaki?"
"Afalon Hajiya fa muke, idan tafito taganmu a haka, gaskiya zanji kunya" tafaɗi haka tana me ƙoƙarin zame hanunsa dake kan cinyarta.
Ɗaura kansa yayi akan kafaɗanta, haɗe da sanya hanunsa ya rungumeta, mamaki gaba ɗaya ya gama kashe Zahrah, da sauri tasoma ƙoƙarin ƙwace jikinta, amma takasa. "Me Doctor yakeyi haka ne?" ta tambayi kanta.
"Please ka sakeni agidan Hajiya fa muke!" tafaɗi maganar aɗan tsorace.
Sake rungumeta yayi, haɗe da kashe mata idanunsa ɗaya, ta buɗe baki zatayi magana kenan, Hajiya dake tsaye tana kallonsu, taɗanyi gyaran murya.
Da sauri Zahrah ta zame daga kan kujera ta zube a ƙasan sofa, tare da sanya gefen mayafinta, ta rufe fuskarta, wani irin matsanancin kunyane ya kamata, shikenan Doctor yaja mata.
Fuska ɗauke da murmushi Hajiya ta ƙaraso cikin falon, haɗe da zama akan kujera, cikin yanayi naɗanjin kunya Dr.Sadeeq ya gaidata.
Fuska a sake ta amsa masa, tana me binsa da kallon ƙauna, irin wanda ke tsakanin uwa da ɗanta, sosai taji daɗin ganinsa a haka da tayi, kallo ɗaya zakayi masa kafuskanci cewa, yana cikin farinciki, da kuma jin daɗi, hakan kuwa bakaɗan yafaranta ranta ba.
Cikin sassanyar murya Zahrah ta gaida ta, tana me sake sunne kanta ƙasa.
Babu wata alama ta tsana kota tsangwama, Hajiya ta amsa gaisuwar Zahrah haɗe da cewa "Tashi ki zauna akusa da mijinki kinji"
Kunyan Hajiyane yasake kamata, hakan da tace ya tabbatar mata cewa duk taga abun da sukayi.
Murmushi Hajiya tayi, haɗe da cewa "Kidaina jin kunyata, ni kamar uwa nake agareki, tashi daga ƙasan nan kinji"
Wani irin daɗin kalaman Hajiya, Zahrah taji, jikinta a sanyaye ta zauna akan kujeran da Dr.Sadeeq ke zaune, sai dai bata yarda sunyi gaf da juna ba.
Lokaci guda Hajiya tasa aka cika musu gabansu da kayan ciye ciye, daɗine yashiga ɗawainiya da Dr.Sadeeq, bai taɓa tunanin Hajiyarsa zata nuna wa Zahrah wannan ƙaunar ba, musamman idan yayi la'akari da cewa bason aurenshi da ita takeyi ba, amma haƙiƙa yaji daɗin kulawan da yaga Hajiyarsa ta nunawa Zahrah.
Basket ɗin da suka shigo dashi, ya ɗauka yakai har gaban Hajiya, zama yayi akusa da ita haɗe dayin ƙasa da muryarshi.
"Hajiyata abinci fa surukarki tayi miki, me daɗin gaske" yafaɗi haka yana me buɗe coolers ɗin da abincin ke ciki.
Murmushin jindaɗi, Hajiya tayi haɗe da kallon Zahrah cike da jin daɗi tace.
"To Matar likita, harda sanya kanki a wahala haka, Allah yayi albarka, nagode sosai!"
Wani irin daɗi Zahrah taji, lokaci ɗaya girma dakuma ƙiman Hajiyan ya ƙaru acikin idanunta.
Shikansa likita yaji daɗi marar misaltuwa, kana kallonsa kuwa zaka fuskanci hakan.
Sun ɗan jima agidan Hajiya, kuma sun samu ƙauna daga wajenta sosai, koda suka zo tafiya, jaka guda Hajiya tabawa Zahrah, wanda ke ɗauke da kayan shafa dakuma daɗaɗan turaruka, Zahrah tayi godiya gareta sosai, cike da farinciki suka bar gidan..
Bayan sun ɗauki hanyar gidan Inna, Zahrah ta sauƙe wata irin ajiyar zuciya, haɗe da sakin murmushi akaro na barkatai.
"Bazan iya misalta maka, irin tarin farincikin danake ciki ba a yau, naji daɗin samun soyayyar Hajiyarka da nayi!" tafaɗi haka cike da nuna jin daɗinta a fili.
Murmushi yayi shima haɗe da jinjina kansa "Kema kenan, inaga nikuma? gaskiya naji daɗi sosai da Hajiyata ta gwada miki ƙauna, dama nasan wata rana dole komai zai wuce, saboda nasan Hajiyata, tanason abunda nake so sosai"
Murmushi sukayi su dukansu...
Fuskarta ɗauke da mamaki take kallon gidansu, wanda yasha gyara aka kuma rantaɓamasa sabon fenti me ɗaukar idanu.
"Da gaske nan gidan mune?" tatambayi Dr.Sadeeq.
Dariyane yakamashi, amma sai kawai ya matse, haɗe da cewa "Nima dai ina kokonto, kodai munyi ɓatan hanya ne? amma mushiga mutambaya ko nan ne"
Jiki asanyaye tashige gaba, shi kuma ya bita a baya, tundaga zauren gidan mamakinta ya ƙara tsananta, komai na gidan an gyarashi ya zama tsab, da sallama ɗauke abakinta, ta kutsa kanta cikin gidan, tabbas gidan sune, saidai kuma ko wani lungu da saƙo nacikin gidan nasu yasha fenti, Inna dake cikin ɗaki tana kallo, tafito sakamakon jin murya irin ta Zahrah da tayi.
Da gudu Zahrah ta taho ta rungume Inna, haƙiƙa tayi kewar Inna, duk da bawani zaman daɗi sukayi ba, amma dai naka naka ne.
Cike da farinciki Inna ta ce "Zahrah Amarya, sai yau aka leƙo mu?"
Dariya Zahrah tayi haɗe da yiwa Inna nuni da Dr.Sadeeq dake tsaye.
"A'a likita ashe tare kuke? ku iso ciki"
Sosai Zahrah tasha mamakin ganin falon Inna, gaba ɗaya falon an mamaye ƙasan sa da tiles, gashi yasha fenti, hadda wani ɗan ƙaramin tv plasma ne manne ajikin bangon falon. "Lallai su Inna sunsamu ƙaton ci gaba" tafaɗi haka acikin ranta.
Inna dakanta takawo musu ruwansha, hadda lemon fanta.
Daɗi ne gaba ɗaya ya cika zuciyar Zahrah, bayan Dr.Sadeeq sun gaisa da Inna, yafita ya basu waje don su tattauna, yasan dole bazasu rasa maganar da zasu tattauna su biyun ba.
Yana fita Zahrah kamar an zungureta tace "Inna wai wayamuku wannan gyaranne haka?"
Murmushi Inna tayi haɗe da cewa "Waye kuwa zaiyi mana wannan aikin haka idan ba ɗan albarkan mijinki ba"
"Doctor?" Zahrah ta tambaya cike da mamaki.
"Ƙwarai kuwa shi, ai bamu da bakin godiya agaresa, harfa kuɗi yabawa Baffanki, ya ƙara jari, acikin sana'arsa, mukam yanzu rayuwarmu tamana daɗi Alhamdulillah!" Inna tafaɗi haka cike da jin daɗi.
Wani irin girman sane yasake cika idanunta, lallai Dr.Sadeeq yacika mutumin kirki, koda wasa kuma baitaɓa gaya mata cewa, yasa anyimusu gyaran gida ba, lallai dole zatayi masa godiya ta musamman.
Koda Zahrah ta bawa Inna delicious ɗin da tayi mata, sosai taji daɗi, dama Inna kurace wajen cin nama, tuni ta raɓashe tashiga cin pepper chicken ɗin da Zahrah takawo mata, sai santi take, tana cewa wai batasan sanda Zahrah ta koyi girki har haka ba.
Itadai Zahrah murmushi kawai take tayiwa Inna. Koda Baffa yadawo yaga Zahrah, baƙaramin daɗi yaji ba, kowa yaganta yasan Alhamdulillah tana cikin jin daɗi, koda Zahrah tazo tafiya, Sosai Baffa yaƙarayi mata nasiha, ya nusar da ita cewa bin mijinta dayi masa ladabi, haɗi da haƙuri, yanada matuƙar mahimmanci acikin rayuwar aurenta, sosai taji daɗin nasiharsa, cike da farinciki sukayi musu sallama...
Basu suka isa gida ba sai ƙarfe 9 na dare.
Yana zaune akan gado yana danna laptop ɗinsa, Zahrah tashigo cikin ɗakin, sanye take da wata fitinanniyar sleeping gown ajikinta, kallo ɗaya yayi mata ya kasa ɗauke idanunsa akanta, sosai ta tafi da duk wani tunaninsa.
Murmushinta me tsada ta sakarmasa haɗe da kashe masa idanunta, cikin wani irin tafiya taƙaraso garesa, ba yau yafara ganinta ba, amma haka yasake baki yana kallon ƙirjinta, dake matuƙar ɗaukar hankalinsa, sosai yakeson breast ɗinta, komai nata yabayyana kansa ta cikin rigar, dayake rigar irin me net ɗin nan ne, wani irin yawu ya haɗiya a maƙoshin sa, alokacin data ƙaraso daf dashi, ta zauna acikin jikinsa, hanu tasanya ta saƙalo wuyansa, kanta ta ɗaura akan ƙirjinsa, cikin wata irin murya me sanyi ta ce.
"Kamar yanda banida kamarka aduniyar nan, haka banida bakin da zanyi maka godiya, nagode sosai, kataimakeni, kakuma taimaki iyayena, bansan dame zan biyaka ba, ka bani kulawa alokacin danake tsananin buƙatarta, ka ƙaunace ni da zuciya ɗaya, kaso farincikina, Inasonka sosai, ina kuma alfahari dakai ako da yaushe, nagode sosai...."
Hanunsa yasanya ya rufemata baki, haɗe da girgiza kansa.
"Kada kice haka my princess, kin wuce haka a wajena, kin cancanci nayi miki komai aduniyar nan, banason godiyarki, Inna da Baffa iyayenane nima, saboda haka babu wani godiya da zakimin, Soyayyarki ce tasanya hakan, ina sonki Zahrah na!!" yaƙare maganar yana me jifanta da wani irin kallo.
Murmushi tayi domin tafuskanci, ma'anar kallon dayake yi mata, hanu tasanya ta zuge zip ɗin dake gaban rigarta, take kyawawan breast ɗinta suka bayyana, harwani juyawa yaji kansa yayi alokaci guda, ɗago tsumammun idanunsa yayi ya kalli fuskarta, idanunta ɗaya ta kashe masa.
Ɗagota yayi ya ɗaurata akan cinyarsa, a hankali ya cusa kansa cikin ƙirjinta, wani irin numfashi su dukansu suka sauƙe alokaci guda. Cike da nutsuwa, ya sanya harshensa, yana me lasan kan nipples ɗinta, kamar wanda yasamu alawa, cike da salo ta nutsa hanunta, acikin gashin kansa, tana meyi masa wani irin abu, lokacin daya soma sucking breast ɗinta, saida taji numfashinta ya soma seizing, kukan shagwaɓa tasanya masa, alokacin daya rabata da rigar jikinta, wannan kukan da takeyi masa shi ya sanya sa, ƙara ficewa acikin hayyacinsa, gaba ɗaya Zahrah tagama gano rauninsa, da zaran tasoma wannan kukan shagwaɓan nata, susucewa yake, wutar sha'awarta ne ke, sake ruruwa acikin jikinsa, kwantar da ita yayi flat akan gadon, haɗe da soma bin kowani sashi na jikinta da hot kiss, sai sauƙe wani sexual erection sound yake. Lokaci guda idanunsa sun rikiɗe daga farare zuwa ja, wani irin sha'awarta ne ke azalzalansa, bakinsa ya ɗaura akan nata, haɗe da laluɓo harshenta yasoma sucking, take itama tasoma mayar masa da martani, lokaci guda, suka fara manta kawunansu.
Slowly haka yake fingering ɗinta, yana me ƙara tsotse laɓɓanta, duk yanda Zahrah taso daurewa kasawa tayi, saida tasakar masa kuka, gaba ɗaya ya gigita ta, bata da wani buri wanda ya wuce ta jishi acikin jikinta, shiɗin ma dai hakanne ya kasance, a ɓangarensa, burinsa kawai shine, yaji wannan daddaɗan ɗumin nata, na ratsa cikin jikinsa, gaba ɗaya taushin breast ɗinta, sungama gigita masa tunani.
Ahankali yaja bargo ya rufe musu duka jikinsu, ɗakin ne ya ɗauki shiru, ba abun dake tashi, sai sautin numfashinsu, dake sauƙa akai akai, babuma kamar na Dr.Sadeeq, dayake abu kamar zai shiɗe, da'alama, Zahrah ta wullasa cikin duniyarta, wanda yayi matuƙar zautar dashi, yayinda itakuwa keta zuba masa kukan shagwaɓa, wanda ke ƙara rikitasa..
*(LOVE IS SO SWEET!!!)*
*✅ote me on Wattpad*
*fatymasardauna*
*11/february/2020*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Editing is not allowed📵*
*CHAPTER 109*
Da wani irin zazzafan zazzaɓi, ta wayi gari, a jikinta, ga kuma wani iri ciwon kai me tsanani, daya rusketa, harta kai, da ƙyarma take iya ɗaga kanta. Gaba ɗaya Dr.Sadeeq ya ruɗe, saiwani tarairaya, haɗe da shagawaɓata, yake yi, magani ya bata da ƙyar ma ta iya sha, taɓara, kawai take ta yi masa, zama yayi akan gadon, haɗe da jawota jikinsa, ahankali yake shafa lallausan gashin kanta, cike da tausayawa yake kallonta.
Cikin yanayi na lumshe idanu, haɗi da sanyin murya tace
"Ya kamata ace kafita office, lokaci yana ta ƙurewa fa"
"Banjin zan iya tafiya ko ina, nabarki acikin wannan halin Zahrah!" yafaɗi haka murya a raunane.
Murmushi ta ƙaƙalo, haɗe da ƙoƙarin ɓoye ciwon nata, tace "Nifa namaji sauƙi, yanzu ma bacci, nakeso na koma"
"Um um banyarda ba, nidai zan zauna dake, gashi kinƙi yarda kuma na gwadaki naga meke damunki"
"Dan Allah Kashirya, ka tafi office, sannan nidai banason ka gwadani, ciwon kaine fa da zazzaɓi, kawai ke damuna, kuma nasan sanyin AC n daya bugeni, daren jiya ne, ya haifarmin da hakan!" aɗan shagwaɓe ta faɗi haka, tana me wani narkar masa da idanunta.
Hanu yasa, ya shafa, kan kumatunta, cike da tsananin ƙaunarta yace. "Baby jiya da dare na matsamiki ko? kiyi haƙuri kinji, wallahi idan ina tare dake, banason abun dazai rabani, da wannan ɗumi, da kuma daɗin naki, amma kimin afuwa, idan ina takuraki, kinji" yaƙare maganar, yana me kama kunnuwansa, da hanunsa, alamar roƙo.
Murmushi tayi masa, haɗe da ɗan juya masa idanunta, duk da batajin daɗin jikinta, amma halin nata, nason ɗaukar hankalinsa na nan.
"Babu wani matsamin da ka ka keyi, kuma ma ae kawai kana sani nishaɗi ne!" tafaɗi haka tana ƙara faɗaɗa murmushinta, domin tunawa da daren su, na jiya da tayi, hakan kuwa yasa, taji wani sanyi a ranta.
Murmushi Dr.Sadeeq yayi, haɗe da kama dogon hancinta ya ɗan ja. "Nidai bansan yaushe, Zahrah na, ta zama haka ba, wannan shine nakoyar dake, kin fini iyawa!"
Fuskarta, ta cusa acikin ƙirjinsa, haɗe da ɗan muntsininsa kaɗan. cike da sabon shagwaɓa tace
"To bakaine, kasabarmin da hakan ba"
"Kuma kinajin daɗin hakan ko?" yatambayeta, yana me kafeta da beutyful eyes ɗinsa.
"Eh mana"
tabasa amsa ko kunya babu.
Murmushi kawai yayi, yana me mamakinta, lokaci ƙanƙani ta sauya, yanason haka ƙwarai, bayason macen da zatana nuna, tsananin kunyarta garesa, musamman idan akazo, wannan ɓangaren, wato ɓangaren (sex) gaskiya jiya, yaga salo iri iri, awajen Zahrah, har saida ya shiɗe mata.
"Tunanin mekake?" ta tambayesa tahanyar katse masa tunanin dayake.
"Ina tunanin yanda, zan karɓi abun daɗina anjima ne!" yafaɗa yana me kashe mata idanunsa ɗaya.
Haƙorinta ta sanya ta ɗan danne laɓɓanta na ƙasa kaɗan, kashe masa nata idon itama tayi.
Dariya yayi kawai, haɗe da miƙewa tsaye, yana cewa "Wayyo Hajiya, Zahrah zata lalata miki yaro!"
Dariya itama tayi, haɗe da maida kanta, cikin bargo.
Tsab yashirya kansa, cikin wani navy blue suit, me tsananin kyaun gaske, wanda taƙara bayyana hasken fatarsa, white parking shirt yasanya aciki, yayinda necktie ɗinsa yakasance, navy blue colour, ankuma ɗanyi masa ado da ɗigo ɗigon fari, italian bally shoe, masu kalan suit ɗinsa, yasanya aƙafarsa, take yasake fitowa ɗas dashi, agogo yake ƙoƙarin ɗaurawa, a tsintsiyar hanunsa, yajuyo da kallonsa gareta.
"Baby!!" yaƙira sunanta, cikin wani, slowly sound.
Zahrah da idanunta, ke lumshe ta amsa da "Ummm!" murya akasalance.
Takowa yayi, yaƙaraso jikin gadon, haɗe da ranƙwafo da kansa, dai dai saitin fuskarta, bakinsa ya ɗaura akan, kumatunta, haɗe da manna mata kiss, hanunta yakama yashiga murzawa a hankali.
Buɗe idanunta tayi, haɗe da sakar masa murmushi.
"I love you!!!" tafaɗa cikin murya me kama da raɗa.
"I love you too!!!" shima yamaida mata da amsa cikin muryar raɗa, kamar yanda tayi masa.
Zama yayi, yashiga shafa kanta, cikin mintuna kaɗan yaji, sauƙar numfashinta, na fita a hankali, alamar tayi bacci.
Gyara mata kwanciyan nata yayi, haɗe da rufe mata, jiki da blanket, kissing ɗinta yayi akan lips ɗinta, kana ya miƙe tsaye, wayarsa dakuma, jakar office ɗinsa, ya ɗauka, kana yafice daga cikin ɗakin.
Sabuwar motarsa, ƙiran 4matic, black colour yashiga, maigadi na buɗe masa gate, ya cilla motar kan titi, tafiya yake shikaɗai yana zuba murmushi, sosai yake tsananin son matarsa, yanajin kansa acikin farinciki, marar misaltuwa, aduk sanda yake tare da Zahrah, yasan yana son Zahrah, amma bai tabbatar da cewa ƙaunarta, tayi masa babban kamuba, saida ya aureta, jiyake idan babu Zahrah atare dashi, rayuwarsa, bazata taɓayi masa daɗi ba, son Zahrah ya mamaye gaba ɗaya, kusurwan jikinsa, yanakuma matuƙar sake jin daɗi, idan ya hango, soyayyarsa, dake kwance, acikin idanunta, yasan yanzu kam yasamu soyayyar matarsa, duk da haryau, yasan akwai wani abu, na soyayyar Zaid, dake shumfuɗe acikin zuciyarta, amma asannu komai zai washe, zai zamana shi kaɗaine, tauraron dake haskawa, acikin ruhinta.
*(Nasan har yanzu akwai wasu, dayawa daga cikin ku, waƴanda suke fatan Zahrah, ta koma ga Zaid, amma inaso kufahimci wani abu, ba komaine aduniya, idan kanaso, kake samu ba, ba komaine zai zamana, ace kasameshi ya zama naka ba, sannan kuma bakowace soyayya, bace take samun cikar burinta ba, haƙiƙa Zaid, SON SO yake yiwa Zahrah, haka kuma Zahrah itama tana son sa, amma kuma baizama dole ace sai sun mallaki juna ba, idan Zaid bai rasa Zahrah ba, taya kuke tunanin zai koyi sawa zuciyarsa dangana? idan bairasata ba, taya kuke tunnin zaidaina banzan tinƙahonsa, daya keyi ako da yaushe, nacewa baya neman abu ya rasa? rasa Zahrah yana ɗaya daga cikin ƙaddarorinsa, wanda Allah Ya tsara masa a rayuwarsa, zasu faru dashi, yace bazai taɓa iya rayuwa ba idan babu ita, amma kuma saigashi cikin ikon Allah, Duk jinyar da yayi Allah Bai ɗauki rayuwarsa ba, saboda kwanansa, bai ƙare ba, kada kace idan babu wani bazaka iya rayuwa ba, dayawan masoya, suna cewa, idan har suka rasa abun sonsu, to bazasu iya rayuwa ba, tabbas SO gaskiyane, amma kada ka/ki ce haka, mutum baya mutuwa har sai kwanansa ya ƙare, kuyi haƙuri team Zaid, nasan yanda kukeji, saidai kuma babu amfanin nuna son zuciya, idan nabawa Zaid auren Zahrah, haƙiƙa nayi babban son kai, da kuma na zuciya, shikansa Zaid, yafaɗa cewa, sam baidace da Zahrah ba, kada kumanta, da girma irin na aikata laifin fyaɗe, wanda yayi maka fyaɗe sam baidace da kaci gaba da rayuwa dashi ba, saboda yawanci son zuciya ne, ke jawo hakan, sannan kuma ako da yaushe, yin abun daya dace shine yafi, son zuciya dakuma bin umarninta, yana haifar da dana sani, Allah Yarabamu da aikata, abun da zamu zo, muyi dana sani Ameen.)*
*****
*ZAYD*
Gaba ɗaya ya sauya, yazama wani silent dashi, bayason hayaniya ko kaɗan, kwanansa biyu kenan, yau baya gida, yana can guest house ɗinsa, yana jinyar kai da zuciyarsa, sosai yake karatun Al'Qur'ani, babu dare ba rana, hakan kuwa sosai ya haifar masa da salama, acikin zuciyarsa, saidai kuma duk wani bugun numfashi dana zuciyarsa, tare suke tafiya da soyayyarta, ƙarya yake, shi yasani, ƙaryane, soyayyar Zahrah, tafita acikin zuciyarsa, lokaci guda, baisan wani irin kalan, zazzafar soyayya bace yakeyi mata.
Zaune yake akan kujera, ya lumshe kyawawan idanunsa, sallaman Abid ne ya karaɗe cikin falon, ahakali ya ware idanunsa, akan Abid.
Murmushi Abid, ya sakar masa, haɗe da ƙarasowa, wajen da Zaid ɗin ke zaune.
"Namijin duniya!" Abid yafaɗa yana me dafa kafaɗan Zaid.
(Namijin Duniya, na Aunty Mami, wacce bata karantaba, tayi missing)
Murmushin ƙarfin hali, Zaid yayi, haɗe dasa haƙori ya cije laɓɓansa, girgiza kansa kawai yayi, yana me tunano rayuwarsa ta baya.
"Yaushe kafara shan magani, batare da an tursasaka ba?" Abid yatambaya, yana me duba magungunan, dake zube akan wani table, dake aje gaban Zaid.
Murmushi Zaid yayi haɗe da duban Abid, cikin murya me sanyi yace.
"Please Abid, kasan banason yawan damuwa, ɗazufa kabar gidannan, yanzu kuma me yadawo da kai?"
Murmushi Abid yayi, haɗe da cewa
"Nazo ne, na maidaka gida, yajin ya isa haka, ka bar ƴar mutane, ita kaɗai, hakan kuma baidace ba"
"Zamana anan yafi min daɗi Abid, gaskiya banajin zan koma gidan nan" Zaid yafaɗi haka, da iyaka gaskiyarsa.
"Kada kace haka Zaid, bansan yakakeji acikin zuciyarka ba, amma tabbas nasan abun da kakeji bayayi maka daɗi, amma kuma, komawarka kusa da matarka, inaga zaifiyemaka wannan zaman kaɗaicin, da kakeyi"
"Banajin zan iya zama da wata Abid, Zahrah ce muradina, amma narasata" hanunsa yaɗauka, yakamo na Abid, ya ɗaura a dai-dai, saitin zuciyarsa, Cike da rauni yace.
"ji yanda zuciyata, take bugawa Abid, soyayyarta ne acikin ta, marar misaltuwa, inaso namanta da ita, amma nakasa, nakasa daina tunaninta, wallahi inasonta Abid, kataimakeni, inaso nadaina tunata, bazan iya jurewa ba, nasan kuma bazan taɓa samun madadinta ba!" tuni har ƙwalla suncika idanunsa.
Tsananin tausayin, abokinnasa ne yakamasa, haƙiƙa Zaid yana a zabtuwa, to amma haka tasa kalan ƙaddaran take, babu wani wanda ya isa sanja masa.
"Kayi haƙuri Zaid, kasaurari abun dazan faɗa maka, haƙiƙa soyayya na azabtar dakai, amma kaci gaba da daure zuciyarka, sannu a hankali, zaka manta ta, watarana, komai zai zama labari, inaso kayi ƙoƙarin mantawa da komai, ka je ga matarka, saboda itama tanada haƙƙi akanka, koba komai kai ɗin mijin tane, kuma Allah Zai kamaka da rashin, sauƙe mata haƙƙinta, tashi kaje kayi wanka kazo, nayi dropping ɗinka agida!" Abid yafaɗi haka cikin lallashi.
Babu musu Zaid yamiƙe, ya wuce cikin bedroom ɗinsa, dakansa ya haɗa ruwa yayi wanka, yana fitowa ya sanya, wasu riga da wando, masu kalan jinin kare, wato maroon colour, kayan suna da kyau, kasancewarsu, masu tsada, sosai kyawun sa yafito, acikin kayan, hmm ZAID, ZAID ne har yau, shiɗin na musammanne, irinsa basuda yawa, kuma wahalar samu garesu, shiɗin nadabanne, kyau dakuma ɗaukar hankali, yana a tattare dashi, Ajininsa hakan yake, wato burgewa, ga duk wanda yaganshi, duk da cewa yayi rama, amma kuma murɗaɗɗiyar surar jikinsa tananan, da turarensa me daɗin ƙamshi, ya feshe jikinsa, yana fitowa cikin falon, Abid yasaki murmushi, cikin sigar tsokana yace.
"Sabon ango kenan, sai ƙyallin amarci kake, gashi kuma kasha kyau"
Ƴar ƙaraman tsuka Zaid yayi, haɗe da wurgawa Abid harara.
"Nifa banason Iskanci, wallahi idan kasake ka kunnani, babu inda zani!" yaƙare maganar aɗan ƙufule.
"Sorry abokina, muje ko" Abid yafaɗi haka yana me tashi tsaye.
A motar Abid suka tafi, Abid ne ke jan motar, sai jan Zaid da hira yake, shi dai Zaid shiru yayi masa, haɗe da lumshe idanunsa, taya zai fassara abun dayakeji akanta?
Suna isa ƙofar katafaren gidan, Abid ya tsai da motarsa, haɗe da juyowa ga Zaid, hanunsa ya ɗaura akan na Zaid, cike da kulawa yace.
"Kamar yanda na faɗama tun a farko, tabbas saika daure, nasan kanajin ciwo, amma dan Allah karka cigaba da sanya, kanka acikin damuwa, basai na faɗa maka ba, nasan kasan cewa, akwai haƙƙi, da kuma alhakin Zahrah, dake bibiyarka, haka kuma idan har ka cutar da Afra, Allah Bazai barkaba, haka kuma haƙƙinta ma dake kanka, bazai barka, kayi rayuwa, me daɗi ba, please Zaid kayi controll ɗin kanka kaji!" cike da lallashi Abid ya faɗi maganar.
Ajiyar zuciya, Zaid ya sauƙe, haɗe da jinjina kansa, alamar yaji, buɗe murfin motar yayi ya fice, saida Abid yaga shigan Zaid gida, kafun ya tada motarsa yabar ƙofar gidan.
Tana zaune a falo, sanye take da riga da sket na kanti, gaba ɗaya tayi wani irin rama, duk da cewa dama tun asalinta, ba ƙiba gareta ba, haƙiƙa tana cikin damuwa, kwananta biyu kenan, bataji koda motsinsa bane, duk da cewa tana mejin tsoronsa, amma kuma tana buƙatar ganinsa, da sallama ɗauke a bakinsa, ya shigo cikin falon, Afrah najin sallamarsa, tayi saurin ɗago da kanta ta kalleshi, kallo ɗaya yayi mata ya kau da kansa.
Ƙarasowa cikin falon yayi, haɗe da zama akan kujera, cike da girmamawa, Afrah ta gaidasa, haɗe dayi masa sannu da zuwa.
Babu yabo ba fallasa, ya amsa mata, shiru ne yashiga tsakaninsu na ƴan sakanni.
Ƙirjinta na bugawa tace "Me za'a kawo maka?"
Kallonta yayi naɗan sakanni, da ƙyar ya iya buɗe bakinsa yace
"Kawomin Ruwa"
Jikin Afrah na tsuma, ta miƙe don kawo masa ruwa, kamar yanda ya buƙata.
Ruwan Faro takawo masa haɗe da ɗan ƙaramin glass cup, har ƙasa ta durƙusa ta aje masa ruwan, a gabansa.
Ɗaukan goran ruwan yayi yakai bakinsa, saida yasha fiye da rabin ruwan, kafun ya aje goran yana shirin miƙewa tsaye ne, yaji Afrah tasanya hanu ta kama ƙafansa, fuskarsa ɗauke da mamaki, ya juyo da kallonsa gareta, gani yayi fuskarta, tayi chaɓa chaɓa da hawaye.
"Dan Allah Kayi haƙuri, kada kajuyamin baya, inason nayi zaman aurena cikin salama, idan baka yafeminba, bazan taɓa jin daɗi ba, wallahi ƙaddarata ce tazo a haka!" kukane yaci ƙarfinta.
Wani irin tausayinta ne yakamashi, "Gwara taki ƙaddaran, tazo miki da sauƙi, akan tawa ƙaddaran" yafaɗi haka acikin zuciyarsa.
Hanunsa yasanya, ya kamo kafaɗunta, ya ta data tsaye.
"Ya isa haka, kidaina kukan nan banaso yana samin headache, kinci abinci ne?"
Kanta ta girgiza alamar "A'a"
"Okay, kinada abun da zakici ne ko kuwa?"
"Eh inadashi, na dafa abinci ɗazu"
"kici abinci!" yafaɗa ataƙaice, yana me nufar hanyar ɗakin sa.
Daɗine yakusa kashe Afra, sam bata tsammaci kulawa, har haka daga gareshi ba.
Zaid kuwa yana shiga cikin ɗaki, ya cire rigar dake jikinsa, ya wurga cikin wani dustbin, ɗin aje kayan wanki, yana shirin cire belt ɗin wandonsa ne, yaji anayi masa knockig ƙofarsa, wani irin haushine ya kamasa, a hasale ya nufi wajen ƙofar don ganin waye.
Yana buɗe ƙofar sukayi ido huɗu da Afrah, sai da taji gabanta ya faɗi, musamman da ta ganshi a tuɓe, amma kuma dolenta zata kau da tsoronta.
"Meye?" yatambaya yana me ƙare mata kallo.
"Ammm... dama abincine nakawo maka" tafaɗa tana me kallon plate ɗin dake riƙe a hanunta.
"Banaci!" yafaɗa ataƙaice yana me yunƙurin rufe ƙofar ɗakin nasa.
Dasauri ta kutsa kanta cikin ɗakin, cike da mamaki yake kallonta.
"Dan Allah kaci, kada kacemin a'a, Dan Allah!" tafaɗi haka tana me langwaɓar da kanta gefe, take idanunta sukayi rau rau dasu, da'alama kuka take son yi.
Ajiye abincin anan, yafaɗa yana me nuna mata kan sofa, cikin jin daɗi ta aje abincin, harta juya zata fita kuma, saita tsaya, haɗe da dawo da kallonta garesa. "Kayi haƙuri, ko badanni ba, kaci abincin" juyawa tayi tacigaba da tafiya, hartakai bakin ƙofar fita Zaid yace
"Afra"
Juyowa tayi garesa, ƙwalla yagani kwance acikin idanunta, da hanunsa yayi mata nuni alamar tazo, kanta aƙasa hartaƙaraso gareshi, domin gaba ɗaya, yacika mata idanu, sosai murɗaɗɗiyar surar jikinsa, ta ƙayatar da ita.
Bata tsammata ba saiji tayi, yasanya hanunsa, ya jawota jikinsa, rungumeta yayi, haɗe da ɗaura kansa akan kafaɗanta, ya lumshe idanunsa, jikinta ne gaba ɗaya yayi sanyi, hanunta duka biyu tasanya itama ta rungumesa, ƙam, haɗi da lumshe idanunta, wani irin shauƙi ke ratsata, ƙamshin sa mai matuƙar daɗi, shi yayi sanadiyar dulmiyata cikin wata duniya....
Yana rungume da ita amma kuma zancen zuci yake.
"Tabbas, abun da Abid yafaɗa masa, gaskiyane, Afra itace matar da Allah Ya zaɓa masa kuma daidai dashi, wannan zaɓin Allah Ne, bazaɓinsa ba, kuma zaɓin Allah Yafi zaɓinsa, saboda haka, dole zai karɓi Afra amatsayin matarsa, kuma zai yi ƙoƙari wajen ganin, ya yi mata adalci, bayajin sonta aransa, amma zaiyi iyaka, bakin ƙoƙarinsa wajen ganin, yazauna da ita lafiya , idan ya rabu da ita, baisan wace buɗaɗɗiyar zai kuma samu ba, shidai yasan irin Zahrah ita kaɗaice, kuma yariga daya rasata, saboda haka dole zaiyi haƙuri da Afrah, kodan son kyautata masa daya lura tanayi"
******
Zaune take akan kujera, ta ɗaura ƙafafunta, bisa kan wani table na glass, dake cikin falin, wata ƴar ficikan riga maroon colour ne, sanye ajikinta, saman wuyan rigan net ne, yayinda hanun rigan kuwa, ya kasance na vest, wato siririn hanu, tayi kyau sosai acikin shigar nata, hanunta riƙe yake da kofi, wanda ƙe ɗauke da Banana Smothie aciki, sai kaɗa kanta take da alama, taji daɗin Banana Smothie'n da take sha, duk da cewa, har yanzu bata wani jin daɗin jikinta, amma haka ta daure, take abu kamar me lafiya, miƙewa tayi daga zaunen da take, haɗe da ƙarasawa gaban tangamemen tv plasma'n dake aje cikin falon, remote ta ɗauka, ta ƙara volume ɗin tv, ta aje remote ɗin kenan, wutan nepa ta ɗauke, gashi magriba ta somayi, ɗakin babu wadataccen haske, babu zato ba kuma tsammani, taji an sanya hanu an rufe mata idanunta, wani irin ƙara tasake alokaci guda, sai kuma ta yanki jiki tafaɗi ƙasa, da hanzari Dr.Sadeeq wanda shi yayi mata haka, yasanya hanu ya tarota tafaɗa cikin jikinsa, wayarsa ya laluɓo ya kunna torchlight, daidai lokacin ne kuma wutan nepan ya kuma, dawowa haske ya baibaye ɗakin, amatuƙar razane yashiga girgizata, yana ƙiran sunanta, amma ina ko motsi batayi ba, hanunsa yakai kan hancinta, yaji babu alamar shiga da fitar numfashi, tsorone yakamasa, haɗe da ruɗewa, akiɗime yashiga jijjigata, amma bata motsaba, saboda babu numfashi ajikin ta.....
*13/February/2020*
*✅ote me on Wattpad*
@fatymasardauna
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Lovely Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain and motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*CHAPTER 110*
A matuƙar ruɗe yake girgizata, yana me ƙiran sunanta, sosai ya tsorita da al'amarinta, gaba ɗaya ya ruɗe, yama manta da cewa shi ɗin likita ne, sungumarta yayi acikin ƙirjinsa, direct sai cikin mota, a gidan baya yasakata, yafigi motar da wani irin gudu, saboda tsabar gudun da yakeyi, mintuna kaɗan, suka kawoshi, cikin asibitinsu, a ruɗe yaje wajan, abokin aikinsa Dr.Salim, yasanar masa abun dake faruwa, emergency aka wuce da ita direct, shikam Dr.Sadeeq kasa shiga cikin emergency room ɗin yayi, suke karɓan emergency patient idan aka kawo, amma kuma sai yau, gashi shine da kansa ya kawo, sai kaikawo yake tayi, aƙofar shiga emergency room ɗin, kwata kwata hankalinsa baya jikinsa..
Bayan Mintuna 30
Yana tsaye ajikin bango, idanunsa a lumshe suke, zuciyarsa kuwa, bugawa takeyi da ƙarfi, tamkar zata faso cikin ƙirjinsa, ta fito.
Dr.Salim da sauran doctors, ɗinne suka fito daga cikin ɗakin, har yanajin tuntuɓe, agarin saurin ƙarasawa inda suke.
"Salim ya ya take? tafarfaɗo ne? Meke damunta dan Allah? Allah Yasa tana lafiya?" Duka waƴannan tambayoyin, Dr.Sadeeq ya jerawa Dr.Salim su.
Murmushi Salim yayi, haɗe da sanya hanunsa, ya dafa kafaɗan Dr.Sadeeq.
"Haba Man, saikace ba doctor ba, duk kabi ka ruɗe, bawata babbar matsala bace bafa, kaida kanka ma zaka iya maganceta, amma duk karuɗa kanka"
Ajiyar zuciya me ƙarfi, Dr.Sadeeq ya sauƙe, sakamakon jin daɗin kalaman da Dr.Salim yayi.
"Masha Allah! kada kaga laifina, wallahi Salim, inasonta sosai ne, banason wani abu, ya sameta shiyasa" Dr.Sadeeq yafaɗi haka, yana me lumshe idanunsa.
Murmushi Salim yayi, haɗe da cewa. "Muje office"
Babu musu Dr.Sadeeq yabi bayan Salim, suka wuce office ɗin Salim ɗin.
Suna shiga suka zauna, su dukansu akan kujera ɗaya, murmushi Salim yayi haɗe da maida kallonsa ga Dr.Sadeeq, hanu yasa ya dafa kafaɗan Dr.Sadeeq ɗin, cikin son kwantar masa da hankali yace.
"Kada ka damu Sadeeq, ba wani abu bane, tsananin tsorone kawai, ya sata suma, amma bayan haka babu wani ciwo dake damunta, sai dai naga tana da hawan jini, amma kuma gaskiya abokina, ka iya aiki, wai ma watanku nawa da aure ne yanzu?"
Harara Dr.Sadeeq, ya jefawa Salim. "Wannan wani irin iskanci ne Salim? me ya haɗa ciwonta da tambayan watannin auren mu? yanzu ba lokacin wasa bane, ina tsananin son matata, bana ƙaunar naga wani abu yasameta, idan akwai wani abu bayan wannan, ka sanar dani, idan kuma kaƙi zan bincika da kaina, daɗin abun nima likita ne" Dr.Sadeeq yafaɗi haka, yana me ƙoƙarin miƙewa tsaye, sarai yasan iskancin Salim, iya shegensa yayi yawa, gwamma ma yaɗauki Zahrah'nsa, kawai su koma gida, inyaso shida kansa, zaiyi checking ɗinta agida, dama ruɗewan da yayine, yasanya ya kawota asibiti.
Hanunsa Salim ya riƙe haɗe da cewa.
"Meyayi zafi kuma? daga tambayar watannin aure, yanzu duk ba wannan ba, miye tukuicina wanda zaka ban, idan nafaɗama wata magana me daɗi?"
"Tukuici kuma? wace magana me daɗi kenan? nida matata bata da lafiya, har akwai wata magana da za'a faɗamin wacce zatayimini daɗi? nace maka kadaina min wasa ko Salim, yanzu ba lokacin wasa bane." Injicewar Dr.Sadeeq.
"Koma dai menene can maka, kuma tukuicina ne sai ka bani, ina tayaka murna, saboda madam ɗinka, tana ɗauke da ɗan ƙaramin ciki, na wata biyu!" Salim yaƙare maganar yana faɗaɗa fari'ar, dake kan fuskarsa.
Zama daɓas Dr.Sadeeq, yayi akan kujera, haɗe da sanya hanunsa, ya kama duka kafaɗun Salim, cike da tsananin farinciki yace "Dagaske kake Salim? Zahrah na ɗauke da ciki na ajikinta? Kafaɗamin gaskiya, dan Allah karka yaudareni!"
Dariya Salim yayi haɗe da cewa "Wallahi ba wasa nake maka ba Sadeeq, da gaske matarka, kuma Zahrah'n ka, tana ɗauke da ciki, sannan kuma yana da kyau, ka kiyaye ɓacin ranta, dakuma duk wani abu, da kasan zai sanya ta tsorita, saboda yawan tsorita zai iya haifar da zubewan cikin.."
Kafun ma Salim yaƙarisa zancensa tuni, Dr.Sadeeq ya sulale ƙasa yayi sujjada, na tsananin nuna godiyarsa ga ALLAH, Haƙiƙa ya matuƙar jin daɗin, wannan albishir ɗin da Salim yayi masa, rungume Salim yayi cike da farinciki.
"Thank you so much Salim, haƙiƙa yau kasani farinciki sosai, kuma kaima insha Allah, zan saka farinciki, ta hanyar baka tukuici, wanda zakaji matuƙar daɗinsa" yanakaiwa nan a zancensa ya sake Salim, haɗe da ficewa daga cikin office ɗin, direct ɗakin da aka kwantar da ita ya nufa.
Shigowarsa, yayi daidai, da buɗe idanunta, wani irin ƙawataccen murmushine, kwance akan fuskarsa, ƙarasowa yayi, kan gadon ya ɗagota, haɗe da rungumeta, tsam acikin ƙirjinsa, wani irin daɗi yakeji na musamman, kwanciya tayi luf acikin jikinsa, cikin muryan shagwaɓa tace.
"Hubby me mukeyi a asibiti?"
Sake matseta yayi, acikin jikinsa, haɗe da sanya hanunsa, yashiga shafa bayanta, cikin wata irin murya yace.
"Bansan dame zan iya biyanki ba Zahrah, haƙiƙa ke ta musammance, kinkawo min farinciki, na musamman, kinsani acikin wata duniya, me ɗauke da wasu surruka, wanda suke da wuyar mantawa, Inasonki My Wife! ina tsananin ƙaunarki, nagode miki sosai, Allah yayi miki albarka!" "Inaasoonki!!" yakuma faɗa, in a slow sound, yana me sumbatar goshinta.
Mamakinsa ne yacika Zahrah, ita sam bata gane me yake nufi ba, kyawawan fararen idanunta, ta zuba masa da'alamu tanason jin ƙarin bayani daga garesa.
Hanunsa yasa ya shafi gefen kumatunta, idanunsa ɗaya, ya kashe mata, haɗe da cewa.
"Verry soon, ni da ke, zamu zama parents!"
"Parents?" ta maimaita sunan abakinta, da ɗan mamaki.
"Yes, ni dake munkusa zama iyaye, saboda kina ɗauke da, ciki!" yafaɗi haka yana murmushi.
Waro manya manyan idanunta tayi, haɗe da sanya hanu ta shafi kan ɗakalallen cikinta.
"Ciki! inada ciki fa naji kace?"
"Eh kina ɗauke da cikina, yanzu haka ajikinki, saura lokaci ƙanƙani kizama mummy's boy"
Wani irin madaran farinciki ne, taji yana ratsa duk wani ƙofar sadarwa dake jikinta, ko kusa koda wasa bata taɓa, kawo hakan acikin tunaninta ba, rungumeshi ta sakeyi ƙam ƙam, haɗe da sakin wani irin murmushi, gaba ɗaya sai tanemi ciwon jikin nata ma ta rasa, "Ashe itama zata zama Mama? lallai ALLAH Abun godiya ne" tafaɗi haka acikin zuciyarta.
"Babyna mu koma gida ko?" yatambayeta, cike da tarairaya.
Dama ita uwar shagwaɓa ce, aikuwa tuni ta narke masa, haɗe da kaɗa masa kai, alamar
"Eh"
Karɓo musu takardan sallama yayi, haɗe da dawowa cikin ɗakin, ɗagata yayi caɗak, yasanyata acikin ƙirjinsa, haka yanufi ƙofar fita, daga cikin ɗakin, shagwaɓa tasakamai, akan cewa ya sauƙeta ƙasa, zata iya takawa da ƙafafunta, amma fir yaƙi, waishi bayasone ko kyakkyawan motsi tayi, bayaso tasha wahala, haka suka fito cikin asibitin, kowa sai kallonsu yake, abokan aikinsa kuwa, dariya kawai sukeyi masa, sam basuyi mamaki ba, domin kuwa duk wanda yasan Dr.Sadeeq, to yasan,cewa, yana matuƙar ƙaunar Zahrah'n shi, domin ko da yaushe sunanta, nanan raɗau acikin bakinsa.
A hankali yake tuƙa motar, tana manne ajikinsa, ji yake kamar ya maidata cikin jikinsa, wani irin sabon ƙaunarta, yakeji na huda fatarsa, yana shiga cikin jikinsa.
"Me zakici na saya miki my lovely na?" ya tambayeta, cike da kulawa.
Harshe tasanya, ta tanɗe bakinta, haɗe da cewa "Ni gurasa kawai nakeson ci, sai kuma shaka, amma gurasan, nafison wanda, aka yanka masa tomatoes, sosai asamansa" taƙare maganar tana haɗiye yawu.
Dariya sosai tabashi, yanayin yanda tayi maganar kaɗai, ya isa tabbatar maka cewa, cike take da kwaɗayin gurasan.
"Okay kome kikeso ni me samamikine, matuƙar a kwaishi acikin duniyar nan, ni dakaina kikeso nayi miki gurasan ko kuma, nemo miki zanyi a waje?"
Dariya tayi haɗe da dubansa cikin shagwaɓa tace "Kai ka iya gurasa ne?"
"Ko ban iyaba akanki ai zan koya" yafaɗi haka yana murmushi.
"Nidai banaka nakesoba, kawai ka nemomin, kuma ma ni nafison wanda akayi a gida, bawai wanda ake sayarwa a waje ba!" taƙare maganar tana me turo ɗan ƙaramin bakinta gaba.
"Wannan me sauƙi ne, yanzu kuwa zan kaiki, gidan da za'a miki gurasa" yafaɗi haka yana me karya akalan motar tasa, zuwa wani hanu daban.
(Wallahi nima kwaɗayin gurasan nake😋 batun yauba, ko ta wayane, kuturomin please.😥)
Mamakine yakamata, ganin sun tsaya agaban gidan Hajiya, kallonsa tayi haɗe da zaro idanunta
"Gidan Hajiya fa, ka kawo mu" tafaɗa tana wuƙi wuƙi da idanu.
"Eh mana, kinsan Hajiya, ƙwararriya ce, wajen iya sarrafa abinci, kuma ina databbacin cewa ta iya gurasa, taso mushiga" yafaɗi haka yana me miƙa mata hanunsa, alaman takama.
"A'a gaskiya nidai mukoma gida, yanzu idan ta tambayi, DALILINA nason cin gurasa, muce mata me?"
Murmushi yayi haɗe da cewa "Baza ma tatambaya ba, ai itama tasan watarana, mutum yakan jin son cin irin waƴannan abubuwan" Da haka Zahrah ta yarda suka shiga, cikin gidan.
Suna Sallama a falon, Hajiya dake zaune, tana duba wasu lace's, dake zube a gabanta, ta amsa musu, cike da fari'a, da kuma mamakin ganinsu da tayi, domin kuwa sam bata tsammaci ganinsu, nan kusa ba, saboda basu jima da zuwa ba.
Kan Zahrah a ƙasa, ta ƙaraso cikin falon, cike da ladabi ta durƙusa, akan guiwowinta, ta gaida Hajiya.
Cike da fari'a, Hajiya ta amsa mata, haɗe da kamo hanunta, ta zaunar da ita, akusa da ita.
"Batun yauba na faɗa miki, nima uwace, ki saki jikinki dani, zanfi jin daɗin haka!" Hajiya tafaɗi haka cikin son nunawa Zahrah ƙauna.
"Nidai yanzu agidannan, ba a wani damu dani ba, idan nazo ma ba a wani bani kulawa" abun da Dr.Sadeeq yafaɗa kenan, yanayin yanda yayi maganar kamar wani ƙaramin yaro.
Dariya sosai yabawa Zahrah, ta lura shidai shagwaɓaɓɓene na ƙarshe.
"Ai ni bana yayin tsoho, idan har nasamu sabo, dama ba ɗiya mace ƙarama nake da shiba, to Allah yabani sainace banaso? kariga daka zama goɗo goɗo dakai, me zanyi dakai, ko kinga ya dace na bashi kulawa ne Zahrah?" Hajiya ta tambayi Zahrah.
Kunyarsu ne su duka yakamata, amma kuma yazatayi, Hajiya nason janta ajiki, dole itama ta sake da ita.
"A'a Hajiya, idan kika basa kulawa, zai ƙara shagwaɓewa da yawa!" Zahrah tafaɗi haka, tana me satan kallonsa, ta gefen idanunta, tasakar masa gwalo.
"To kaji abun da matarka ma tace, saboda haka, sai kayi haƙuri" inji cewar Hajiya.
"To ya na'iya, idan banyi haƙuri ba, kuma tunda kikace haka, saina gayawa Hajiya komai" yafaɗi haka yana kallon Zahrah.
Wayyo Allah, Zahrah ina ƙasa ta ɓule tashige ciki, tsabar kunya, tasani, ƙaramin aikinsa ne, ya gayawa Hajiya, cewa ta nada ciki, amma ko daya kunyatata.
Kallon tuhuma, Hajiya tashigayi musu dukansu biyu.
"Me kuke ɓoyewa?" ta tambayesu.
"Hajiya waifa kwaɗayin gurasa take, kuma wai na gida takeso, shine na kawota ki mata" Dr.Sadeeq yafaɗi haka, yana me ƙara faɗaɗa fari'arsa.
Kallon Zahrah, Hajiya tashiga yi, na ƴan wasu sakanni, tsab tafahimci abun da take son fahimta, take wani irin farinciki, ya ɗarsu acikin zuciyarta, hakanan taji ƙaunar Zahrah, ta sake shiga zuciyarta.
"Alhamdulillah! Masha Allah!! aikuwa yanzu zakici gurasa, da kaina ma zanyi miki" Hajiya tafaɗi haka cike da tsananin jin daɗi. " Ashe dai akwai, tsananin rabo, dake tsakanin Dr.Sadeeq, da kuma Zahrah, yanzu da ace ta dage, ta kafe kai da fata, ta hanasu aure, shikenan kuma da wannan cikin, alayi za'a sameshi, daga nan kuma, ta ɓata sunan zuri'arta, domin kuwa aje azo yaro ko yarinyar da aka haifa wajensu zai dawo, tunda Sadeeq shine uban sa" Hajiya tafaɗi haka acikin zuciyarta.
Zama Zahrah tayi, acikin falon, tana me hararan Dr.Sadeeq ƙasa ƙasa, Allah ma yasota da bai ce ciki ne da ita ba, da itakam yagama kasheta, sam bata fahimci cewa Hajiya, ta gane hakan ba.
Bayan mintunan da basu da wani yawa sai ga Hajiya, hanunta ɗauke da plate, wanda ke shaƙe da gurasa, sosai yaji ƙuli, da kuma mangyaɗa, gashi an ƙawata samansa, da dangin su albasa da kuma tumatur, hadda kabeji, ga kuma cocumber, wayyo wannan gurasar fa tayi, tuni yawun Zahrah ya tsinke, haka ta shiga lasan bakinta, kamar wata mayya, ai Hajiya na aje plate ɗin gurasan, Zahrah ta jawo shi gabanta, sam tama manta da cewa Hajiya surukarta ce, hanu baka hanu ƙwarya, haka Zahrah kecin gurasan, abun daya yi matuƙar bawa, Dr.Sadeeq mamaki kenan, shidai yasanta, ita ba mutum bace, me cin abinci da yawa, hasalima idan zataci abinci, aɗan ƙaramin kwano take ɗebowa, amma yau gashi tana cin gurasa, tana wani lumshe idanunta, kamar bata taɓa, cin abinciba, haka takeyi, idanu kawai, ya zuba mata, aduk ko wani minti ɗaya ƙaunarta sake cika zuciyarsa take.
Sosai Zahrah, taci gurasan nan, sai da tajita ta ƙoshi nak, kamar tunbinta, zaiyi bindiga, kafun ta ɗauki, goran ruwan faro, takai bakinta, ajiyar zuciya tashiga sauƙewa, akai akai, kamar wacce tayi tsere.
"Sannu" Dr.Sadeeq, yafaɗa mata haka, cike da kulawa.
Murmushi tasakar masa haɗe da ɗan matsowa kusa dashi, dayake Hajiya bata falon.
"Naci gurasa saura shaka" taƙare maganar tana tanɗe ɗan ƙaramin bakinta.
Idanunsa ya zuba mata, haɗe da cewa.
"Wani irin baby ne haka na samiki, me masifar ci, da kuma kwaɗayi?"
Ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba haɗe da cewa.
"Wallahi inaji, idan bansha shaka ba, akwai matsala, batun yauba nake jin kwaɗayi matsananci, amma na yau ɗin dai yayi over, har inajin idan bansamu, abun da nakeso ba, bazan iya koda yin bacci ba " taƙare maganar tana me shagwaɓe fuska.
Murmushi yayi, haɗe da sanya hanu, yashafi kan kumatunta, cike da kulawa yace.
"Allah Yasauƙeki lafiya, My Acici na!"
Dariya suka saka, su dukansu biyun.
Hajiya dake tsaye, tana kallonsu, batare da saninsu ba, itama ta saki murmushi.
"Ashe da tahana Sadeeq auren Zahrah, ƙwarai da ta tauye, musu haƙƙinsu, Allah sarki, ashe suna son junansu har haka?"
Da wannan zancen zucin taƙaraso cikin falon.
"A'a Hajiyar gurasa, kin ƙoshine kodai a ƙaro miki?" Hajiya tatambayi Zahrah.
Ƙasa tayi da kanta, haɗe da cewa "Naƙoshi Hajiya, saidai zan tafi da sauran gida, saboda inaso naci kafun na kwanta"
"Wannan ai me sauƙi ne, na aje miki wani ma a kula, idan kin tashi saiki tafi dashi" Inji cewar Hajiya.
"Hajiya bakida Shaka acikin gidan nan ne? kinsanfa mutumiyar taki, kwaɗayi ta koya, yanzu kuma wai shaka take son sha" Dr.Sadeeq, ya tambayi Hajiyarsa.
"Ai kuwa akwai shaka, acikin fridge, domin kuwa jiya da dare, banajin daɗin bakina, shine na haɗa nasha, to akwai ragowan, yayi sanyi ma sosai, ae inaga" Hajiya tafaɗi haka tana me nufar wajen da fridge ɗinta ke aje.
Shaka'n ta ɗauko, ta kawowa Zahrah, wayyo Zahrah tasamu abun da takeso, gyara zama tayi daɓas, tashiga zuƙan shakanta abunta, daɗi kamar kunnenta zai fita haka takeji.
Hmmm Zahrah, dai basu bar gidan Hajiya ba, saida tayi ƙat, har guzuri, na gurasa, da kuma, kayan ƙwalama, Hajiya tayi mata, tatafi dashi, koda sukazo tafiya, Dr.Sadeeq ya keɓe da mahaifiyarsa, inda ya gayamata cewa, Zahrah na ɗauke da ciki, duk da tagane hakan, tun kafun ya faɗa mata, amma sai jin datayi daga bakinsa, yasanya taƙara jin daɗi, sosai, takuma ƙarfafa masa guiwa, akan cewa kome Zahrah takeso, yayi mata waya, ya sanar da ita, zatayi mata shi ko menene, ta bawa driver, yakai mata har gida, sosai yaji daɗin hakan...
Suna komawa gida, ta faɗa toilet, wanka tayi, kana ta ɗauro wani ɗan ƙaramin towel, wanda ya tsaya iyaka cinyarta, tafito, yana zaune akan gado, yana danna laptop ɗinsa, sanye yake da dogon wando, da kuma wata farar riga me shara shara, tana fitowa daga cikin toilet ɗin, ya sauƙe idanunsa akanta, murmushinsa dake, ƙarawa fuskarsa kyau, yayi mata, itama ta mayar masa da martani, duka hannayensa, ya buɗe mata, alamar ta taho garesa, da gangan ta yada towel ɗin, dake ɗaure ajikinta, tashiga takowa zuwa garesa, wani irin abu yaji yashiga cikinsa, take yaji wani irin sha'awarta, me tsanani ta kamasa, tana zuwa tafaɗa jikinsa, haɗe da haɗe ƙirjinsu waje guda, atare suka sauƙe ajiyar zuciya, rungumeshi tayi ƙam, haɗe da cusa kanta acikin ƙirjinsa, sosai ƙamshin turarensa, keyi mata daɗi fiye da da.
Bakinsa ya ɗaura akan wuyanta, haɗe da manna mata wani irin hot kiss, hanunsa yasanya duka biyu, yana shafa bayanta, cikin wata irin murya yace.
"Idan naganki da kaya, nakan rasa nutsuwata wani lokacin, yanzu kuma da kikazomin a haka, so kike na haukace miki ko Baby?" yaƙare maganar yana me sake cusa, kansa acikin wuyanta. Hanunta ta nutsa acikin gashin kansa, yayinda take ya mutsa gashin nasa a hankali, kansa ya maida kan ƙirjinta, inda ya sauƙe bakinsa atsakiyan ƙirjinta, wato tsakankanun breast ɗinta kenan, lasan wajen yakeyi a hankali, yana me shafa kan mararta, lumshe idanunta tayi haɗe da sake ƙanƙameshi, sosai takejin daɗin abun da yakeyi mata, hanu tasa ta zame masa riga haɗe da turasa kan gado, ta kwanta akansa, ƙasa yayi da kansa still zuwa ƙirjinta, yasan abin da tafiso kenan, wata ayi sucking breast ɗinta, yanda yake tsotson breast ɗinta, yana sucking ɗinsu, shine abun dayafi, komai ɗaga mata hankali, wani irin sha'awa me ƙarfine yashiga ratsa jikinta, jawo kansa tayi ta haɗe bakinsu waje ɗaya, sucking laɓɓan juna suke cike da ƙauna, jin laɓɓan nata yake tamkar anshafa sugar, lokaci ɗaya ya birkice mata, kwantar da ita yayi plat, haɗe da bin kowani kusurwa dake jikinta, da hot kiss, hanunsa yaɗaura akan breast ɗinta yana murzawa a hankali, yayinda yake sucking ɗinta daga ƙasanta, kamar koda yaushe shiɗewa take idan yana mata haka, amma nayau shiɗewan nata na musamman ne, har wani zillo takeyi masa, saboba ya cireta acikin hayyacinta, Zahrah da Doctor, sunyi nisa basajin ƙira, babu wani ƙyanƙyami, haka yake tsotse duk wani ruwa daya fito daga jikinta, idanunsa sun kaɗa sunyi jawur saboda tsabar jaraba, Zahrah kuwa kuka take amma bana wahala ba, haƙiƙa dole ta zauce, domin babu wata mace da za'ayiwa haka, tace bataji ajikinta ba, wani irin juyawa yaji kansa nayi masa alokacin da yagama shiga cikin jikinta, (kunsan daɗi ma nasawa, mutum yaji kamar, kansa baya jikinsa, lol) to haka Dr.Sadeeq, yakeji a kullum game da Zahrah'n sa, haƙiƙa Zahrah'nsa, ta da bance acikin mata, yau kam dai, sun haukacewa juna, domin dukansu suntafi wata duniya, me daɗin gaske, akullum jinsu suke kamar sabin haɗuwa, bakomai ke sashi yake liƙe mata ba, ako da yaushe, kamar daddaɗan ɗumin, da ke cikinta, wanda ke ratsashi yana sanyashi nishaɗi, yana acikin jikinta, ya ɗaura bakinsa akan nata bakin, harshenta yakama yashiga tsotsa a hankali, yana me ƙara shigewa can cikin jikinta, (hope kungane irin shigewan danake nufi🙈)
*18/february/2020*
*✅OTE me on Wattpad* @Fatymasardauna
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Associatiom*
_{United we stand and succeed; our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*CHAPTER 111*
A wannan rana Zahrah da Doctor da ƙyar suka iya barin juna, gaba ɗaya sun zautar da kansu, yayinda ƙarin ƙauna, yasake shiga cikin zuciyoyinsu, Zahrah batayi bacci ba saida tasake cin gurasa, tayi nak, haka ta kwanta tana ta sauƙe numfashi, kamar zata fashe haka takejinta, tsabar ƙoshi...
*** *** ***
*ZAID*
Kwance yake akan doguwar kujeran dake falon, kansa da komai nasa suna kallon sama, amma idanunsa a rufe suke, a yanzu yafison ya keɓe shi kaɗansa, batare da wani ko wata sun takura masa ba, shikaɗai yake zancen zucinsa.
"Bazaice baya tunata ba, haka kuma bazaice bata kwance acikin zuciyarsa ba, da sonta yake kwana, dashi yake tashi, duk da cewa ya tsaya yana ta addu'a, akan Allah Ya yaye masa ƙaunarta, balaifi yaɗanji sauƙi, amma kuma har yanzu akwai soyayyarta, a tattare dashi"
Afrah da tun ɗazu ke tsaye akansa, ta zuba masa idanu, haƙiƙa tana matuƙar ƙaunar Zaid, musamman yanzu da ya shayar da ita, wata zuma wanda babu wani namiji, daya shayar da ita kwatan kwacinta, ada tana ɗokin auren Zaid ne, saboda kyau da kuma kuɗinsa, amma yanzu shiɗin takeso, koda kuɗi ko babu, tana matuƙar ƙaunarsa, batason wani abu dazai ɓata ransa, tana yi masa tsananin biyayya.
"Dear!" taƙira sunansa murya a sanyaye.
Bai buɗe idanunsa ba, haka bai kuma amsa mata ba, duk da cewa yana jinta, hakan nan yaji bakinsa, yayi masa nauyi, yagaza amsa mata.
Ganin haka yasa ta ƙaraso zuwa inda yake kwance, durƙusawa tayi, a gabansa haɗe da sanya hanunta, akan wuyanshi, da sauri ta cire hanun na ta, sakamakon jin zazzaɓi da tayi ajikinsa.
Fuska ta marerece cike da kulawa tace "Dan Allah Dear kasha magani mana, tunjiya fa kake fama da zazzaɓin nan, meyasa kakeson ƙarawa kanka damuwa ne? haƙiƙa nasan cewa kana sonta, amma kuma tunda kasan ita yanzu ta haramta a gareka, miye amfanin tunaninta, bance kadaina sonta ba, amma inaganin tunaninta da kakeyima haramunne"
Sai alokacin yabuɗe idanunsa, da suka kaɗa sukai jajur dasu, wani irin murmushi yayi, me ɗauke da ma'anoni masu tarin yawa.
"Kawomin maganina insha" kawai yafaɗi haka, don bayason ta sake taso masa da mikinsa, don baijima da kwanciya ba, ɗazu ma har kuka yayi acikin toilet batare da kowa ya saniba, brain ɗinsa takan hautsinewa ne, idan yatuna cewa Zahrah tawani ce, yakanji kamar yayita kwarara ihu, idan yatuna irin cin zarafin da yayi mata, yakanji inama da ace suna tare, daya kyautata mata fiye da yanda zai kyautatawa kowa aduniya, ba tun yauba, yace da ana sauya ƙaddara, da tuni ya koma baya ya sauya tasa ƙaddaran, da yasani da tunfarkon ganinsa da ita, yabiya sadaki aka ɗaura musu aure shida ita.
Afrah ce takatsesa daga tunanin da yakeyi ta hanyar cewa.
"Ga maganin nakawo maka"
Karɓan magungunan yayi daga hanunta, haɗe da ɓallesu acikin gidansu, ya watsa acikin bakinsa, kana yabi da ruwa.
Zama Afrah tayi akusa dashi, har jikinsu na gogan na juna, hanunta tasanya ta kama nasa hanun, cike da lallashi tace "Inasonka Mijina, banason inaganinka acikin damuwa, dan Allah Ko badanni ba, kadaina sanya kanka acikin damuwa!" kafun ma ta ƙare maganar, tuni har idanunta sun kawo ƙwalla, tausayinsu takeji su duka biyun.
Murmushinsa me kyau, da kashe zuciya yayi mata, haɗe da jawota jikinsa, cikin wata irin murya yace. "Kada ki damu, komai watarana zai wuce, naso na daure amma kamar bazan iya ba, duk da haka amma bazan karaya ba, zanta jarrabawa, watarana sai labari"
Hawayen da suka cika cikin idanunta ne suka tsiyayo waje, "Inama ace wannan ƙaunar itace tasamu daga wajen Zaid" tafaɗi haka acikin zuciyarta.
Ganin tana hawaye yasanya hanunsa ya share mata, jawota yayi ya rungumeta acikin ƙirjinsa, acikin zuciyarsa yace "Zanyi ƙoƙari nasoki Afrah, zan yi ƙoƙari nasama miki gurbi acikin zuciyata, nagode da kulawarki agareni" abunda Zaid bai saniba shine, maganar da yayi, ba iyaka zuciyarsa ta tsayaba, harta fito fili.
Murmushi Afrah tayi haɗe da sake shigewa cikin jikinsa, hanu yasa ya ɗago haɓarta, suka jefa idanunsu acikin na juna, bakinsa ya ɗaura akan nata bakin, yashiga tsotson lips ɗinta a hankali, wani irin sanyin daɗi taji acikin ruhinta, kamo laɓɓansa itama tayi, ta shiga tsotsa, har mamaki takeyi idan tana tsotsan laɓɓansa, saboda laɓɓansa taushine dasu, kamar laɓɓan mace wacce tasan kanta.
Kissing ɗin juna sukeyi sosai, yayinda yasanya hanunsa a bayanta, ya zame mata zip ɗin rigar dake jikinta, bata da wani manyan breast amma tana rage masa zafi, yanda yake murza breast ɗinta cikin nutsuwa yana kuma tsotson lips ɗinta, shi yasanya taji gaba ɗaya jikinta yayi laƙwas, haƙiƙa Zaid yasan kan mace, yasan yanda zaiyi ya zautar da ita, a iya romance kaɗai, yana bata gamsuwa hundred percent, tuni ta cire masa rigan jikinsa, tashiga goga masa breast ɗinta akan chest ɗinsa, take yashiga fidda wani irin numfashi, daman tasan hakan shine logonsa, takaranceshi sosai, (Ko miji baya sonki, idan kika karanci halayyarsa, zakiji daɗin zama dashi, musamman idan kika fuskanci, abun da idan kikayi masa zaki ruɗasa, ko acikin sex ko romance, please ƴar uwa kada kiyi wasa da wannan daman) sosai suke kashe juna da salo, ɗaukarta yayi caɗak, yanufi bedroom da ita, akan gado ya shumfuɗeta, yashiga tsotseta.. Hmmm Zaid jarababbe Afrah jarababbiya, haka suka mannewa juna, duk da cewa Afrah ko farcen Zahrah bata kamo ba, amma balaifi itama tana da nata ni'iman, don dama ko wace mace da irin ni'imarta, sannan kuma baya ga haka, sosai yake samun gamsuwa a wajenta, domin itama ta iya romancing namiji, kuma sosai take gyara kanta, don Zaid yaji zam zam, lol. Amma kuma Zaid kam yasan daga kan Zahrah yagama jin wani zam zam, wanda zai gamsar dashi. (Kunsan muɗin na musammanne😉 idan kina da kishia me suna fatima, to kiji tausayin kanki🤣😜 saura kuma su o'o dan sunansu ba fatima bane, suce nayi ƙarya, namesake kuzo kufaɗamusu cewa maganata gaskia ce.🤗)
***
Tsaye yake acikin kitchine gaba ɗaya ya haɗa gumi, banda ƙonewan da yayi a hanunsa yafi sau biyar, yanzuma ƙonewa yayi a babbar yatsarsa, na hanun dama, ya tsaya yana hura wajen, kwanon soya ƙwaine ɗaure akan gas, yayinda hanunsa ke riƙe da cokali, gaba ɗaya gaban gas ɗin ya ɓaci da manja, gashi har gaban rigar sa manjan ya taɓa, waishinan wainar fulawa yakeyi (Hana baba tashi, mudai muke cemai anan, amma sauran garuruwa bansan me suke ƙiranshi ba, kunsan hana baba tashi akwai daɗi, musamman idan yaji yaji😋😂)
Ƙoƙarin juya wainar fulawan yake, amma yaƙi juyuwa, gaba ɗaya ya ƙona hannayensa, har wainarma tasoma ƙonewa, da ƙyar ya samu ya kwashe, kuma dama wanda ke cikin kaskon shine na ƙarshe, kashe gas ɗin yayi haɗe da ɗaukan tissue ya goge gumin dake tsastsafowa a goshinsa, plate ɗin wainar da kuma roban yaji yaɗauka ya nufi falo.
Tana zaune akan sofa, tayi piecess da ƙafafunta, sanye take da wata ƴar riga marar nauyi, itanan zaman jiransa take, yakawo mata wainar fulawanta taci. Yana shigowa cikin falon tasaki dariya, domin kuwa har kumatunsa manja ne.
Ganin haka yasanya sa ɓata fuska, haɗe da tsayawa yana jifanta da hararan wasa.
"Kaganka kuwa, chab aikuwa kayi dumu dumu da manja!" tafaɗi haka tana ƙoƙarin gimtse dariyarta.
Shagwaɓe fuska yayi kamar wani ƙaramin yaro, plate ɗin wainar yakawomata gabanta ya aje mata, haɗe da aje mata roban yaji, muƙut haka ta haɗiyi wani yawu tsabar kwaɗayi, tuni ya wunta ya tsinke, jawo plate ɗin gabanta tayi, haɗe da gutsuran wainar fulawan takai bakinta. Da sauri ta tofar da wainar fulawan sai kuma tashiga kelaya amai, babu ƙaƙƙautawa, amatuƙar ruɗe yayo kanta, shiya riƙeta harta gama yin aman, dakansa ya gyara wajen, zama yayi haɗe da jawota jikinsa cike da tausayinta, yashiga yi mata sannu.
Kwanciya tayi luf acikin ƙirjinsa tana me sauƙe ajiyar zuciya, sosai tagalabaita, amai ba wasa ba.
Bayanta yake shafawa a hankali, yana ɗan jijjigata, kamar wata jaririya.
"Abincinne ba daɗi, yasa kikayi amai?" yatambayeta.
Ya mutsa fuska tayi haɗe da ɗaga masa kai ashagwaɓe tace "Ƙauri haɗe da warin hayaƙi wainar fulawan keyi"
Narke fuska yayi haɗe da karya wuyansa gefe, "yanzu duk ƙoƙarin nan da yayi, yatashi a banza?" yatambayi kansa.
Ajiyar zuciya yayi haɗe da cewa "Kiyi haƙuri, bansan ya akayi yayi warin hayaƙi ba, yanzu to mezakici?" cike dakulawa ya kuma tambayanta.
Zahrah ƴar rigima da shagwaɓa, sake narke masa tayi, ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba, haɗe da cewa "Ni yanzu, Banana PineApple Smoothie kawai zan sha"
"Banana pineapple smoothie ba abincine wanda zai riƙeki ba, kifaɗamin yanzu me kike so bayan smoothie ɗin?"
"Gasashshen nama, wanda aka sa masa, sweet pepper dakuma onion" ta faɗi haka tana tanɗe baki.
Hanu yasanya yashafi gefen kumatunta, inda dogon suman kanta ya kwanta, "Wannan ba abun damuwa bane, kinaso muje mu sayone kokuma naje ni kaɗai?"
Tsulum tatashi zaune haɗe da cewa "muje tare"
Ɗaki suka koma shida kansa ya shiryata cikin, wani doguwar riga na lace, yanaɗe mata jikinta da wani vail marar nauyi, shima kayan jikinsa ya sauya, suka fita hanunsu sarƙe acikin na juna.
Wani haɗaɗɗen hotel suka nufa, hotel ɗin namusammanne, domin kuwa sai waƴanda suka amsa sunansu ne suke zuwa cin abinci wajen.
Yana riƙe da hanunta suka kutsa cikin hotel ɗin, awani ɓangare wanda babu yawan jama'a sosai suka zauna, suna zama wata waiter da jikinta ke sanye da uniform taƙaraso wajensu, cike da girmamawa ta basu menu, dan zaɓan abun da suke so, Zahrah ce takarɓi menu'n tazaɓi abun da takeso akawo mata, Dr.Sadeeq kam bai buƙaci komaiba, saboda a ƙoshe yake.
Mintuna kaɗan aka kawowa Zahrah abun da takeso, gyara zamanta tayi, haɗe da ɗaukan gasashshen namanta tasoma ci, harwani lumshe idanunta takeyi tsabar daɗi, ji take kamar bata taɓa cin wani nama me daɗin wannan ba, sosai taci naman, kana ta ɗaura banana pineapple smothie akai, shidai kallonta kawai yake, kome tayi burgesa take, kallonshi tayi da fararen idanunta, haɗe da ɗaukan tsokan nama guda ɗaya, takai bakinsa, babu musu yabuɗe bakinsa tasamai, ɗage masa giranta guda ɗaya tayi sama, haɗe da cewa "Yakaji naman, daɗi ko? hmm ai daga yau kullum anan zanna cin nama!" taƙare maganar tana jijjiga kanta, shidai murmushi kawai yaketa aika mata.
Harta gota, zata wuce, sai kuma tayi saurin dawowa da baya, sake ware idanunta tayi akan yarinyar, tabbas itace bazata manta fuskarta ba, kallon yarinyar tashigayi sosai, itakuma yarinyar sai dariya take tana kaɗa kanta, da'alama tana cikin farinciki. "Zahrah!" taƙira sunan yarinyar ahankali, yanda ita kaɗai da tayi maganar ne zataji me tace, "Itace wacce hotunanta suka cika jikin bangon ɗakin Zaid, kenan itace Zahrah'n Zaid? itace mafarki dakuma burinsa?" abun da Afrah ke faɗa kenan acikin zuciyarta, tsintar kanta tayi da tsayawa tana kallon ta, bawata babba bace bazata wuce 20 to 21 year ba, aƙalla tasan zata fita da 3 year, ita kanta yarinyar tayi mata kyau, domin kuwa tana da burgewa, kyawunta abayyane yake, "Hmmm idan dai har Zaid zaina mafarkin samun irin wannan tauraruwar, me zaiyi da irina?" Afrah ta tambayi kanta a bayyane.
"Mekikeyi a tsaye anan kuma?"
Muryar Zaid yakaraɗe cikin kunnuwanta, da sauri tajuyo tana kallonsa, sam ita tama manta da cewa tare suke.
Kallonta yayi naɗan sakanni, kafun ya raɓa ta gefenta ya wuce.
Ƙirjin Dr.Sadeeq ne ya buga, alokacin dayaga gilmawan Zaid ta bayan Zahrah, amma kuma da dukkan alamu shi Zaid ɗin bai lura dasu ba.
"Ya kamata mutafi ko princess, idan yaso saimu yi take away ɗin naman mutafi dashi gida, sai ki ƙarasa ci acan" Dr.Sadeeq yafaɗa a ƙagauce.
"Um um nidai Hubby kabarni please, nakusa nacinye fa" Zahrah tafaɗa a shagwaɓe.
Babu yanda ya iya, dole haka ya barta, taƙarasa cin namanta.
Tana kammalawa kuwa, yakama hanunta suka bar cikin hotel ɗin, ba gida suka nufa direct ba, saida suka biya wajen saida ice cream yasaimata, kana suka ɗauƙo hanyar gida.
Gaba ɗaya jin zuciyarsa yake a jagule, "Meyakawo Zaid wannan hotel ɗin? Kodai bibiyan matarsa yake?" tambayar da Dr.Sadeeq ke tayiwa kansa acikin zuciyarsa kenan, amma bayida wanda zai basa amsoshin tambayoyinsa. (😂 Doctor fa yana tsoron Baba Zaid yasin)
Suna isowa bakin gate ɗin gidannasu, me gadi ya wangale gate ɗin Doctor yatura hancin motarsa ciki.
Tana ganin shigarsu cikin gidan, tasaki wani irin murmushi, tun fitowarsu a hotel ɗin take biye dasu, acikin motarta, batare da tabari sun gane hakan ba.
"Zanyi muku zuwa na musamman" tafaɗi haka a bayyane. Haɗe dayin reverse ta juya akalar motarta zuwa gida...
(Zanfara yi muku 1 read more, saboda banason editing, wallahi wuya yake ban😥)
*20/february/2020*
*✔️OTE me on Wattpad*
@fatymasardauna
#Love
#Romance.......
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers }_
*https://www.facebook.com/kainuwawritersassociation*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Chapter 112*
Yana zaune acikin falon, taturo ƙofa tashigo bakinta ɗauke da sallama, cike da mamaki yake kallonta. "Bakije gidan Ƙawartaki bane?" ya tambayeta yana me tsareta da kyawawan idanunsa.
Murmushi tayi haɗe da ƙarasowa cikin falon, zama tayi gaf dashi, haɗe da ɗaukan hanunsa ta ɗaura akan cinyarta. "Naje nasamu batanan, kuma dama banaso nabarka kai kaɗai agida, shiyasa na dawo" tafaɗi haka tana me ƙara faɗaɗa murmushinta.
Kansa yajinjina haɗe da ɗaukan goran ruwan dake aje a gabansa, yakai bakinsa, kallonsa take tanaso tafaɗa masa abun dake cikin ranta, amma kuma tsoro takeji saboda batasan taya zai ɗauki maganar ba.
Matsewa kawai tayi haɗe da sanya hanunta ta saƙalo hanunsa, fuskarsa takafe da ido kana tace "Yau nahaɗu da Zahrah"
Da sauri ya ɗago kansa ya kalleta, cike da tsananin mamaki yace "Wace Zahrah?"
"Zahrah wacce kasani, wacce kuma tunaninta ke maƙale acikin zuciyarka, babu dare babu rana" ta bashi amsa.
"A ina kikasanta, har kikasan cewa itace Zahrah'n danake tunani akowani lokaci?" yajefomata tambaya yana me kafeta da idanunsa.
"Duk wanda yasanka dole zaisan Zahrah, mussamman ma ace wanda yake kusanci dakai, ko kamanta cewa har yanzu akwai hotonta acikin ɗakinka?"
Miƙewa yayi daga zaunen dayake haɗe da cusa hannayensa cikin aljihun wandonsa.
"Zahrah ɗaya na sani a rayuwata, kuma tajima da mutuwa, saboda haka ni bansan wata Zahrah ba" yanakaiwa nan azancensa yasakai yawuce cikin bedroom ɗinsa, ko waiwayenta baiyi ba.
Mamakine ya bayyana ƙarara akan fuskar Afrah, sakamakon jin kalaman Zaid da tayi, "Dare safe rana, bashida wani aiki sai tunaninta, tasha jinsa yana kuka a toilet, dukkuma akan Zahrah ɗinne, amma wai kuma yau da bakinsa yake cewa Zahrah ta mutu, anya kuwa Zaid yana lafiya?" Afrah ke magana da zuciyarta.
Murmushi tayi asakamakon tunawa da wani abu da tayi, tashi tayi tanufi ɗakin da Zaid yashiga.
Yana zaune agefen gadonsa hanunsa, riƙe da wani littafi da kuma biro, da'alama nazartan littafin yake, amma kuma idanunsa cike suke da ƙwalla, yanajin motsin shigowar Afrah, yayi sauri ya rufe littafin, ransa a ɓace, ya juyo gareta.
"Mekikazo ɗauka? Bana faɗa miki cewa bakoda yaushe ne, nake da buƙatarki ba, please get out!" yaƙare maganar yana meyi mata nuni da ƙofar fita daga cikin ɗakin.
Ajiyar zuciya ta sauƙe haɗe da takowa zuwa garesa, tana zuwa gabansa ta durƙusa haɗe da zube guiwowinta a ƙasa.
"Kagafarceni idan abun dana faɗa maka akan Zahrah ya ɓata maka rai, banyi haka donna ɓata maka ba, saidai kuma zanfaɗa maka koda zaka tsaneni ne, wallahi bazaka taɓa yin rayuwar farinciki ba, harsai kasamu Zahrah ka ƙara neman yafiyarta, nasan cewa kana da buƙatar Zahrah akusa dakai, fiye da yanda kake da buƙatar ko wace mace a duniya, amma kuma ƙaddara babu yanda bata juyawa bawa, dan Allah kayarda dani, akwai abunda zanyi wanda zaisa kusamu jituwa a tsakaninka da Zahrah, harma da mijinta"
Kallonta yayi da jajayen idanunsa haɗe da tashi, kawai yawuce cikin bathroom.
"Afrah bazata taɓa ganewa bane, shi kaɗai yasan irin zogi da kuma ciwon da zuciyarsa keyi masa, aduk sanda aka ambato masa sunan Zahrah, a yanzu so yake yasa aransa cewa, babu wata Zahrah, domin wacce yasani tajima da mutuwa, wanda yake gani a yanzu, wata Zahrah'nce daban kuma ta wani ce" tsaida zancen zucin nasa yayi, haɗe da cire rigar dake jikinsa, direct gaban shower ya nufa, tsayawa yayi haɗe da sanya hanunsa ɗaya, ya dafa jikin bango, ruwane keta dukan kansa dakuma bayansa, sauda dama idan yana acikin ƙunci, tsayawa yake gaban shower ruwa yaita dukansa, dahaka yake ɗan samun relief.
*** ***
Kwance take akan kujera, sanye take da wani dogon sket, wanda yake a tsuke daga sama har ƙasansa, sket ɗin irin roba ɗinnnan ne, rigarta kuwa wata ƴar vest ce marar nauyi, fara ƙal da ita, tunda ta samu cikin nan, bata rabo dajin zafi, hakan yasanya bata cika zama da kaya masu nauyi ba, wayartace rike a hanunta, kunnenta kuwa sanye suke duka da airpiece, waƙar film ɗin Sanam Teri Kasam takeji, harwani lumshe ido take, saboda tanason waƙoƙin film ɗin sosai, sweet ne abakinta tana ɗan tsotsa, gudun tara yawu, dayake bata ƙure volume ɗin waƙarba, hakan yasanya tajiyo bugun ƙofar da akeyi mata, da mamaki take kallon ƙofar falon, ita dai tasan batayi da kowa cewa yau zaizo wajenta ba, kuma yanzu ba lokacin dawowan Doctor bane, batajin zata iya tashi dan haka saita bawa me knocking door ɗin damar shigowa kai tsaye.
Da sallama ɗauke a bakinta, tashigo cikin falon. Kallon kallo suka shigayiwa juna ita da Zahrah, ita tana kallon Zahrah ne fuska ɗauke da murmushi, yayinda Zahrah kuwa ke ƙare mata kallo, saboda batasanta ba ma ita kwata kwata.
"Da dai anbani izinin shigowa, aida sai na shigo" takatse Zahrah daga kallon da take mata, ta hanyar faɗan haka.
Murmushi Zahrah tayi haɗe da tashi zaune tace "Bismillah, shigo"
Ƙarasowa tayi tsakiyar falon, haɗe da zama akan kujera.
"Sannu da gida" tace tana murmushi.
"Yauwa sannunki da zuwa" Zahrah tafaɗi haka itama tana murmushi. Miƙewa tayi da niyar takawo mata ruwa da lemo, da sauri tace. "A'a barshima basai kinkawomin komai ba, daga gida nake banajin ƙishi"
Kallonta kawai Zahrah tayi kana ta koma kan kujera ta zauna, cike da ƙosawa Zahrah tace. "Baiwar Allah Bangane wace ke ba fa"
Murmushi takumayi akaro na barkatai. "Sunana Afrah, dama nasan baki sanniba, amma ni nasanki, kiyi haƙuri bansaniba ko hakan danayi yaɓata miki rai, jiya naganki a hotel kinacin abinci keda wani, wanda nake kyautata zaton cewa mijinki ne, tunda naganki, naji kin kwantamin arai, kuma wallahi da zuciya ɗaya nake sonki, please idan bazan takuraki ba, inaso muzama ƙawayen juna"
Murmushi Zahrah tayi me sauti, haɗe da cewa "Nagode ƙwarai da ƙauna, amma kuma inaganin kamar akwai matsala, idan har muka fara ƙawance yanzu, dududu fa yau nafara ganinki, kinga dole kafun abota musan halin juna" inji cewar Zahrah.
"Da alamu bakida wata matsala nima kuma haka, kuma insha Allah bazakiyi danasanin ƙawancen mu ba" taƙara da cewa "Akan hanya nake, watarana zanyi miki zuwa na musamman amma kafun nan,please samin number'n wayarki" miƙawa Zahrah wayarta da ta cirota cikin jaka tayi.
Babu musu Zahrah ta amshi wayar tasanya mata number'nta aciki, kana ta miƙa mata abarta.
Murmushi tayi haɗe da miƙewa tsaye, "nagode sosai" tace kana ta nufi hanyar fita daga cikin falon, Zahrah na ganin ficewarta ta sauƙe ajiyar zuciya, haɗe da komawa ta kwanta, aranta tana addu'an neman tsari daga sharrin mugayen mutane, da kuma aljanu....
*** *** ***
Gaba ɗaya yau tatashi jikinta arikice, ganin haka yasa Dr.Sadeeq hana kansa zuwa office, yazauna tare da ita, yanata amsar shagwaɓanta, zuwa yanzu sosai shagwaɓanta yafi na da, tun da tasamu cikin wani sakalci da taɓara ya tsiro mata, shikuwa doctor biye mata yake, hakan yasa gaba ɗaya yanzu tazama wata, shagwaɓaɓɓiya da ita sai kace ƴar shekara 4.
Kwance take akan sofa yayinda kanta ke ɗaure bisa cinyarsa, minti irin me tsinkenan ne abakinta, tana tsotsa a hankali, yayinda shikuwa ke shafa sumar kanta a hankali.
_______
Mamakine ya matuƙar kashesa, ganin unguwa da kuma inda Afrah ta kawosa, ɗago idanunsa yayi ya watsamata su, "Inane nan?" yatambayeta still idanunsa na kanta.
Murmushi tayi masa haɗe da cewa "Unguwar su ƙawartawa da nake gaya maka ne, kuma ganan ma gidan nata" taƙare maganar tanayi masa nuni da gidan dake gefensu, bugawar zuciyarsa ne ya ƙara tsananta, take yaji kansa nayi masa wani irin sarawa.
"Kimaidani gida Afrah, tunkafun ranki ya ɓaci!" cikin yanayi na ɓacin rai yake maganar.
Dama tasan za ayi haka, hanunta ta ɗaura akan nasa cikin son ta rarrasheshi tace "Kayi haƙuri Dear, bazamu wuce 30 minute ba, nasan kasan gidan, kakuma san wacece acikin gidan, banyi haka donna ɓata maka ba, nayi hakane don kawai kasamu salama, ƙwarai nasan idan harta yafema kuma ayau idan kuka ga juna, tabbas komai zai wuce, duk da nasan sai ahankali, amma kuma dukanku zaku samu sassauci...."
"Kimaidani gida nace kona ɓaɓɓala ƙashinki gida biyu anan wajen!!" amatuƙar hasale yaƙare maganar.
Saida ta tsorita domin bata tsammaci wannan tsawan daga gareshi ba.
"Fita" yace da ita murya a dake.
Sumi sumi ta fice acikin motar, dan ta fuskanci sam babu alamar wasa a tattare dashi. Fita shima yayi daga cikin motar ya koma wajen zaman driver domin dama a wajen mai zaman banza yake dazama, itakuma tana wajen zaman driver.
Yana shiga yatada motar, kallon Afrah yayi fuska babu walwala, da sauri ta buɗe motar tashiga, da ƙarfi yaja motar sukabar ƙofar gidan.
Suna zuwa gida, ya wuce ɗakinsa kai tsaye, itama Afrah tayi nata ɗakin, sam bataso haka yakasance ba, taso ace abun da ta ƙudurta aranta shine ya faru.
Kayansa yashiga haɗawa acikin trolly ɗinsa, saida yatabbatar ya haɗa duk wani abun da yake buƙata, dama kuma jiya aka kawo masa visa'n su.
Tana tsaye agaban mirror daga ita sai wata ƴar fingilan riga, kallo ɗaya yayi mata ya ɗauke kansa, akwatinta ya ciro acikin drawer, kallonta yayi itaɗinma kallonsa take.
"Kishirya kayanki, 6 pm zamu tashi gobe insha Allah" yanakaiwa nan azancensa yasakai yafice daga cikin ɗakin.
Mamakine yakama Afrah, "dama ya shirya musu tafiya shine baisanar da'ita ba?" tambayar da tayiwa kanta kenan, ganin bata da wani wadataccen lokaci yasanya, tashiga shirya kayanta acikin trolly'n, da ya fito mata dashi.
Zama yayi akan gado haɗe da jawo diary ɗinsa ya buɗe, abun rubutu ya ɗauka yaɗanyi rubutu, kaɗan kana ya rufe diary'nnasa ya tura acikin wata ƴar ƙaramar jaka.
Washe gari
Kamar yanda ya faɗa ƙarfe 6 dai dai jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasar America, a wannan karon baya tunanin zai waiwayo Nigeria, so yake ya koma America da zama gaba ɗaya, wannan shine ƙudurinsa, sai dai idan Afrah tace zatazo Nigeria bazai hanata ba, shikam dai yasa aransa cewa bazai zoba, saidai ko wani babban dalili, me ƙarfi.
*** *** ***
Abuja University Gwagwalada.
Yau suke bikin kammala degree ɗinsu, saboda haka gaba ɗayansu sunacikin farinciki. Kowannensu yasha adonsa cikin shiga ta burgewa gwanin ban sha'awa.
Tsaye take ajikin wata bishiya tana waya, sanye take da baƙar tie abaya gown ajikinta, wacce daga hanunta zuwa ƙasanta aka mamayeta da ado na flowers masu kyaun gaske. Da babban mayafi tayi amfani wajen rufe jikinta, sai dai kuma duk da haka, saida cikinta ya bayyana kansa, sosai taƙara haske da kuma kyau, sai wani ɗaukar ido take, daganinta kaga me ciki, wacce take cikin jin daɗin, yanzu watannin cikinta huɗu kenan amma kuma tuni ya bayyana kansa, ita kanta har mamakin girman cikin nata take, don watanninsa basukai ace girmansa yakai har haka ba.
"Zakizo mu kammala pictures ɗinne kokuma zaki tsaya soyewa" Husnah dake tahowa ga Zahrah tafaɗi haka da ɗan ƙarfi. tayanda Zahrah'n zata jita.
Murmushi Zahrah tayi haɗe da kashe wayar, kana ta juyo da kallonta ga Husnah.
"Kinsan banagajiya da jin muryarsa ne, amma muje mukammala agurguje, saboda gida nakeson nakoma gaba ɗaya jina nake agajiye" Zahrah ta faɗi haka tana ɗan yamutsa fuskarta.
Murmushi Husnah tayi haɗe da cewa "Nima sauri nake saboda yau Man ɗina zai turo magabatansa gidanmu, kuma ayau za'a sa mana ranan aurenmu, nasankuma baza asa ranan da yawa ba, just ba zai wuce 1 month ba"
Dariya Zahrah tayi haɗe da cewa "Lallai Husnah aure kikeso sosai, ji yanda lokaci ɗaya kika falle."
Dariya sosai Husnah tayi haɗi da cewa "Laifine dan mace irina taso aure? nakai aure, nakuma cika mace me lafiya, kinga kuwa dole naso aure, ke nifa wallahi gaba ɗaya yanzu rayuwata, a daddafe nakeyinta, na ƙosa najini a ƙirjin mutumin, nima yakasheni da irin nasa salon" cikin yanayi na shauƙi ta ƙare zancen.
Dariya dukansu sukayi kana suka tafa.
Basu tsaya an kammala bikin dasu ba, kowaccensu ta nufi gida.
(Kuyi haƙuri, wallahi kwana biu narasa ganewa kainane, gaba ɗaya typing yafita araina, kuma kunsan abun yana aiki ne da zuciya dakuma ƙwaƙwalwa, wallahi dana fara kaina sai yanamin ciwo, saboda haka dole zan taƙaita muku labarin, insha Allah acikin satinnan zan kammala littafin, duk da bahaka naso ba, amma kuma abubuwa sunmin yawa, ina buƙatar hutu kusan na 1 month, idan na bari kuma banƙarisa ba, zan shiga haƙƙin masu karatu, kuyi manage da wannan, yau ko editing banyi ba, saboda ciwon kae, dan Allah kumin uzuri kunji, duk na naƙosa nagama labarin, saboda haka zanci gaba dayi muku shi a gurguje.)
*✔️OTE ME ON WATTPAD*
@fatymasardauna
#Love
#Romance
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI!!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*CHAPTER 113*
Kwance take akan gado, hanunta riƙe da littafin hausa, tana karantawa, sanye take da doguwar riga irin bubu gown ɗinnan, zuwa yanzu cikinta ya ƙara girma, har tsoro girman ke bata, ga yawan motsin da takeji acikin cikin nata.
Yajima a tsaye yana kallonta, sosai cikin ya ƙara mata kyau, gashi cikin ya bayyana kansa acikin rigar dake jikinta.
"Ƴan mata na!" yaƙira sunanta cikin wata murya me sanyi.
Da sauri ta dawo da kallonta garesa, murmushi tasakar masa, haɗe da tasowa daga kan gadon, da ɗan gudu gudu, tafaɗa cikin jikinsa ta rungumesa.
Hannuwansa yasanya duka biyu shima ya rungumeta, kiss ya manna mata akan wuyanta, haɗe da lumshe idanunsa, yana me shaƙan ƙamshin jikinta, sosai ƙamshin nata keyi masa daɗi.
"Nayi kewarki madam ɗina me ciki" yafaɗi haka yana me shafa cikin dake jinkinta.
Ashagwaɓe tace "Nima nayi kewarka sosai fa dear!"
"Dagaske kinyi kewata? keda ma kika hanani abun daɗina, two days fa kenan yau baki bani zumana ba!" cikin yanayi na ɗan karya murya yafaɗi haka, lokaci guda yana me marerece idanunsa.
Ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba, cike da shagwaɓa tace "To bakaineba saikanamin da ƙarfi, kuma Allah Hubby yanzu idan kajima kanayi sainaji kamar zan amar da kayan cikina, gashi tsoro nakeji idan kana fidda wannan sautin numfashin, kamarfa zaka sume haka kake"
Sake marerece fuska yayi haɗe da kwantar da kanta akan wuyansa, hanunsa ya ɗaura akan cikinta."Babyn Mama kaine kake wahalar min da mata ko? kuma kaine kake hanawa abani abun daɗi na ko? please my boy kabari yau abani ko kaɗanne, kuma ae balaifina bane, banasanin ma inayin kamar zan shiɗe, kuma ma ae daɗin kine yake da yawa ko Baby boy ɗina?" yatambayi yaron cikin?
Dariya ne yakamata ganin yana magana da cikin, "Kai Hubby ina ma zaijika, ko saninka fa baiyi ba, ni kaɗai ya sani" ta ƙare maganar tana dariya.
"Wayace miki baisanniba, lallai kam idan bai sanniba ae kuma shikenan magana ta ƙare, taya ma za'ace baisan wanda ke yawan aika masa gaisuwa ba? dan ma dai kwana biu...."
"Shiii! Ina roasted fish ɗina, da nace katahomin dashi?" taje fo masa tambayar ta hanyar katsesa daga maganan da yakeyi.
"Nakawo miki yana falo.."
Bata tsaya jin sauran zancenba, ta wuce falo cikin sauri.
Zama tayi akan sofa tashiga cin roasted fish ɗinta, sosai taji daɗin kifin, domin kuwa da ɗuminsa aka kawo mata, gashi yaji onion sauce. saida taci sosai kana ta ɗaura da lemon exotic.
Shikuwa tana fita acikin ɗakin, direct bathroom ya nufa, wanka yayi, domin dama agajiye yake sosai, kasancewar daga office ya dawo.
Fitowarsa daga cikin bathroom ɗin yayi daidai da shigowarta cikin ɗakin. Kallonsa tayi haɗe da sakar masa murmushi, shima murmushin yayi mata, kana yanufi gaban dressing mirror don kimtsa kansa. Doguwar riganta ta cire kana ta faɗa toilet.
Lokacin da tafito ɗaure da wani ɗan ƙaramin towel ajikinta, shikuma yana zaune akan gado, yana sipping fresh milk, a hankali. Kallon santala santalan cinyoyinta yayi, haɗe da haɗiye wani yawu, sosae yake missing matar tasa, musamman ma daddaɗan ɗumin dake cikin jikinta, wanda idan yajisa yake sanyasa cikin nishaɗi da kuma nutsuwa. Kasa haƙuri yayi alokacin da ta juya masa baya, mai take shafawa ajikinta, yayinda towel ɗin yaɗan zame daga kan ƙirjinta, har tsayayyun breast ɗinta suka ɗan bayyana kansu
Rungumeta yayi ta baya, haɗe da ɗaura kansa bisa wuyanta. Hancinsa yashiga gogawa akan wuyannata yana me busa mata numfashinsa me ɗan ɗumi akan fatarta, take taji tsikar jikinta na tashi, ɗago idanunta tayi ta kalleshi, shima idanunsa ya jefa acikin nata, wani irin kallo me matuƙar kashe jiki, yake jifanta dashi, bazata iya ɗauke idanunta, daga cikin nasa idanunba, haƙiƙa kyawun idanunsa, na matuƙar ɗaukar hankalinta, lumshe idanunta tayi, haɗe da sauƙe wani irin numfashi, sake jawota jikinsa yayi haɗe da ɗaura duka hannayensa, akan ƙugunta, matso da fuskarsa yayi daf da tata, har hancinsu na gogan najuna, still idanunta a rufe suke bata iya kuma buɗesu ba, ɗaura bakinsa yayi akan nata bakin, a hankali ya shiga tsotsan leɓenta na ƙasa, yayinda itama ke tsotson lip ɗinsa na sama, numfashi suka shiga sauƙewa a tare, harshenta yakama yana sha a hankali, yayinda yasanya hanunsa, ya warware towel ɗin dake ɗaure ajikinta, hakan yabawa towel ɗin daman faɗuwa ƙasa, ahankali yake shafa bayanta, zuwa gefe da gefen cikinta, sauƙar numfashinta ya tsananta, saboda sosai takejin daɗin abun da yakeyi mata. Harsaida tasamu kusan ɗaukewar numfashi, alokacin daya soma murza breast ɗinta, yanayin yanda yake mata ya matuƙar shiɗar da ita, ashe bashine kaɗai yayi missing ɗinta ba itama tayi kewarsa sosae. Hanu tasa ta zame rigar dake jikinsa, wani irin ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya suka sauƙe alokaci guda, sakamakon haɗuwar fatar jikinsu waje ɗaya,sosai hakan yasake basu wani shauƙi. Kasa jure yanda take goga masa tausassun breast ɗinta akan chest ɗinsa yayi, ɗagata yayi caɗak suka nufi kan bed.
Kwantar da ita yayi flat haɗe da bin ko ina najikinta da kiss, har izuwa kan breast ɗinta. Sosai yashiɗar da ita, yayinda shikuma ya zauce, ba abun dake tashi acikin ɗakin, sai sautin numfashinsu, dake fita a hankali..... Yau love fa yakawo wuta, domin kuwa gaba ɗaya Doctor ya manta, da kansa da kowa nasa, Zahrah'nsa tabasa zuma wanda samunsa ke da matuƙar wahala, musamman kuma daya kasance wannan zuman natane ita kaɗai, Allah yabata, sauran kuwa kowacce da irin tatabaiwar, sosai yau doctor ya tara mata gajiya, sai kukan shagwaɓa kawai takeyi masa, dakansa yayi mata wanka, bayan yayi nasa, kana ya naɗota a towel kamar wata ƴar baby, kwanatar da ita yayi akan gado, bayan yasanja bedsheet ɗin, domin wancan ya ɓaci da sperm ɗin Me daɗinsa, shi har mamakin yawan ruwa irinnata yake. Kwanciya yayi shima akan gadon kana yajawota jikinsa, luf tayi acikin jikinsa, tana me fesa masa iskan numfashinta, acikin ƙirjinsa. Bayanta yake shafawa a hankali, yana me sauƙe ajiyar zuciya akai akai. Ƙamshin turarensa dake tasowa yana shiga cikin hancinta, shine abun da ke neman hautsina mata ƙwaƙwalwa, domin kuwa, yana mata yanayi da wani ƙamshi wanda har abadan duniya bazata taɓa, mantawa da ƙamshin da kuma mai ƙamshin ba, take bugun zuciyarta ya tsananta, haka nan taji zuciyarta naneman karyewa, bazatace ta manta dashiba, domin kuwa aduk kwanan duniya yana maƙale acan ƙasar zuciyarta. "To tayama za'ayi ta manta dashi?" tambayar da tayiwa kanta kenan, lumshe idanunta tayi, alokacin da ta tuno da haɗuwarsu ta ƙarshe, alokacin daya kusanto zuwa gareta yana me neman yafiyarta, bazata taɓa mantawa da wannan ranan ba, kamar yanda bazata taɓa mantawa da ranan daya fyaɗeta ba, wani murmushine ya kuɓuce mata, batare da ta shiryawa hakan ba, azuciyarta tace "Lallai Zaid yayimini babban Illa, wanda har nakoma ga mahaliccina tabonsa bazaigoge ba, yayimin fyaɗe sannan kuma ya koyamin soyayyarsa" batasan da cewa hawaye sun fito daga cikin idanuntaba, saida taji ɗuminsu nabin kan kumatunta, da sauri tasanya hanu ta share gudun kada doctor ya gani. Ashe ta makaro domin kuwa idanunsa na kanta. Sake matseta yayi acikin ƙirjinsa, haɗe da kai bakinsa, kan nata yashiga tsotsa a hankali, ganin haka yasa takama harshensa tana tsotsa, kamar tasamu sweet, sosai takejin daɗi idan tana sucking tongue ɗinsa, har wani suga suga takeji akan harshen, wata ƙila hakan yana da nasaba, da yawan shan sweet da yakeyi, zaiyi wuya kaga bakinsa shiru babu sweet aciki, hakan ajininsa yake. (Kamar dai sweet and big bro ɗina, i miss you yayana😰) bedaina kissing ɗinta ba harsai dayaji sauƙar numfashinta, nafita slowly, alaman tayi bacci kenan, mintuna kaɗan shima bacci ya ɗaukesa....
*** *** ***
America.
Tunda sukaje America take ta fama da rashin lafiya, gaba ɗaya ta zafge ta rame sosai, ga Zaid daya sata agaba, kullum saiyayi sex da ita sama da sau biyu. Yanzuma durƙushe take aƙasan tiles tanata kwarara amai, ko kyakkyawan motsi takasa yi.
Shigowarsa gidan kenan, sosai yaƙara kyau da haske, ƙaƙarin amanta daya keji ne yasanya sa nufar ɗakinta da sauri. Tagama aman amma takasa tashi daga wajen domin gaba ɗaya jikinta yayi laushi.
Jawota yayi jikinsa ya ɗaurta akan cinyarsa, cike da kulawa yake shafa bayanta, sannu yaketa yi mata, don ko ba afaɗaba, kowa yaganta yasan tanashan jiki. Shida kansa ya gyara wajen, kana ya buɗe drawer'nta ya ɗauko mata mayafi, hanunta yakama suka fita daga cikin ɗakin, direct asibiti ya nufa da'ita.
Gwaje gwaje aka mata, kana akace su ɗan jira akawo musu result, babu jimawa kuwa, saiga result ɗinsu yafito. Bayan doctor James yaduba result ɗinne, yasaki murmushi haɗe da duban Zaid, cikin harshen turanci yace "Congratulation friend matarka tana ɗauke da ciki, na 9 weeks!"
Kamar sauƙan aradu haka Zaid yaji kalaman Dr.James acikin kunnuwansa, da sauri ya kallo Afrah wacce itama take cike da mamakin abun da Dr.James ɗin yafaɗa.
"Cikifa kace Doctor?matana tana ɗauke da cikina?" yatambaya cike da tsananin mamaki.
"Eh mana, ai bazanma wasa ba, dagaske matarka tana ɗauke da ciki, shiyasa take ta amai babu ƙaƙƙautawa" duk cikin harshen turanci irin nasu na America suke maganan.
Bazai taɓa misalta irin daɗin da yajiba, hakanan ya tsinci kansa da sakin murmushi, tashi yayi ya rungume Afrah, jiyake kamar ya ciro cikin aJikinta, yadawo dashi jikinsa, gani yake kamar zaifi kula da cikin. Agurguje yayi duk wani cike cike da zaiyi sukabar asibitin. suna isa cikin gida yayi parking motar, amaimakon yabarta tayi tafiya da ƙafanta, saiya ɗagata caɗak, wai yana gudun kada cikin ya jijjiga. Akan kujeran falo ya direta haɗe da zama daɓas agabanta, hannayenta yakamo duka biyu, cike da farinciki yace. "Nagode Afrah, nagode miki sosai, kin bani farincikin dana rasa, haƙiƙa Allah ne yadubeni yadawomin da farincikina ta hanyarki, please Afrah, kikulamin da ƴata dake cikin cikinki kinji, daga kan naira ɗaya har 100m zan iya mallakamiki, matuƙar zaki kulamin da ƴata dake cikinki, inasonta inasonta fiye da komai aduniya, Allah ne yadawomin da abuna, dama tawace bata kowa ba, please ki kulamin da cikin dake jikinki, namiki alƙawari zanbaki duk wani abu dakikeso"
Mamakine yakusan kashe Afrah, sam bata fahimci me kalamansa suke nufi ba, yace dama tasace bata kowa ba to wakenan? tambayar da take matuƙar so tasamu me amsa mata kenan. Ganin ya kafeta da idanunsa ne yasanya tasaki murmushi haɗe dacewa "Nima inason na haifamaka ɗa ko ƴa, kuma insha Allah Zan kula da cikin nan sosai, fiye ma da yanda zan kula da kaina, amma me yasa kaketa cewa ƴa, bamusan fa menene ba macece ko namiji Allahu a'alam"
Murmushi Zaid yayi haɗe da miƙewa tsaye "Mace zaki haifa insha Allahu, wannan bayin kaina ko yin wani bane, yin Allah ne, shiya hanani, yanzu kuma shiya bani, saboda haka bazan gajiya dayi masa godiya ba" yana kaiwa nan azancensa yawuce ɗakinsa. Haryanzu dai ita bata fahimci ina kalamansa suka dosa ba, kwanciya tayi akan kujera, minti kaɗan bacci ɓarawo yayi gaba da ita.
Shikuwa yana shiga cikin ɗakinsa, ɗan ƙaramin drawer ɗinsa ya buɗe wanda ciki yake aje diary'nsa, ɗauko diary,n yayi yasoma rubutu, yana kammalawa ya buɗe shafin farko na diary'n nasa, take wani hoto wanda ke ɗauke da kyakkyawar fuskarta ya bayyana, tayi kyau ƙwarai acikin hoton, gaɗan ƙaramin bakinta nan yasha lipstick, murmushi yayi alokacin daya kai hanu yashafi kan kumatunta, ahankali yace "Nasani dama zaki dawo gareni, kobata hanyar zama tawa ba, amma tabbas zaki dawo gareni, gashi kuma kindawo ta hanyar dayafi dacewa, nan bada jimawa ba zakizo amatsayin tawa ta har abada, duk wuya duk tsanani ke ɗin zaki kasance tawace, nine wanda bakida kamarshi acikin duniya, nine mutum guda ɗaya wanda zai kasance me matuƙar mahimmanci a wajenki, nine wanda bazaki taɓa samun irina ba har abada, ni ɗayane nake da wannan matsayin agareki, bayanni babu wani" wasu irin hawayene masu zafi suka gangaro daga cikin idanunsa, da sauri yarufe diary'n kana ya shiga toilet donyin wanka, jinsa yake acikin matsanancin farinciki, lallai Allah yamasa kyauta, wacce zata kasance mafi soyuwa agareshi.
(Wayaga Zaid da ƴa ko ɗa😜)
***
Wani irin kulawa na sadidan Zaid ke bawa Afrah, kome takeso adunia shiyake yi mata, zuwa yanzu harmamakinsa takeyi, irin yanda yake nunamata tsananin ƙauna, wani lokaci har kuka takeyi, itama tana matuƙar son cikin sosai, amma yanda Zaid ke ƙaunar cikin ba'a magana, tasani badon komai yake nuna mata wannan ƙaunarba saidon cikin dake jikinta, haka take rainon cikinta cike da ƙaunar abun dake cikinsa, wani lokaci tana mamakin yanda Zaid keta faɗan wasu irin maganganu wanda suke matuƙar ɗaure mata kai, daga zaran yataɓa cikin sai yafara cewa "Babyna kina lafiya ko, na ƙosa kidawo gareni, inakewarki sosai, kizo muyi rayuwarmu wacce bamuyita ba da, muyi rayuwa cikin farinciki, inasonki sosai babyna!" abun dayake faɗa kenan, hakan kuwa mamaki yake bata sosai, duk kuwa yanda taso fassara kalaman nasa, bata iyawa, hakanan take haƙura kawai ta share. Cikin nada wata huɗu Zaid ya ware wani ɗaki dake cikin bedroom ɗinsa, saida yacika ɗakin tam da kayan wasan yara, babu abun da babu nawasan yara acikin ɗakin, acewarsa ɗakin babynsa ne, itadai Afrah idanu kawai tazuba masa, saboda taga soyayyar dayakeyiwa abun dake cikinta naneman zautar dashi.
*** *** ***
Nigeria.
Masha Allah cikin Zahrah ya ƙara girma sosai domin kuwa yanzu yana wata na bakwai ne, sosai cikin yayi turtsetse dashi, zuwa yanzu batasanya wani kaya sai dogin ruguna, irin masu faɗin nan.
Tana zaune atsakiyar falon, yayinda ta tusa wani tray wanda ke ɗauke da kayan fruit agaba, gefe kuwa plate ɗin dambun nama ne wanda yaji albasa, sai kuma ɗan wake wanda yaji cabbage da cocumber ga tomatoes, yasha mai da yaji, wai duk wannan tulin kayan ciye ciyen Zahrah so take taci kowanne acikinsu.
Auntie Raliya ce tafito daga kitchine hanunta ɗauke da wani cup wanda cikinsa ke ɗauke da wani zuma, me magani aciki.
"Manya anata fama kenan" Inji cewar Auntie Raliya.
"Wallahi Auntie ni duk na rasa ma da wanne zan fara, inaga ɗanwakena kawai zanci sauran kuma nabari saina koma gida" Zahrah tafaɗi haka ga Auntie Raliya tana me jawo plate ɗin ɗanwaken ta.
Dariya Auntie Raliya tayi haɗe da zama kusa da Zahrah'n "Gaskia Bro bai iya ajiyaba, wannan wani irin ɗa ne haka yasa miki acikin cikinki, yaro ne zance ko yarinya, sai shegen ci"
Dariya Zahrah tayi sosai haɗe da kallon Auntie Raliya cikin dariya tace "Wallahi kuwa Auntie, dubeni fa yanda nayi ƙatuwa, nayi muni, shikuma duk kwanan duniya ƙara kyau yake, gaskia ni bazan yarda ba, auntie wayo kawai yamin"
Dariya Auntie Raliya tayi haɗe da miƙowa Zahrah kofin dake riƙe a hanunta. "Ungo amsa kishanye duka"
Zaro idanu Zahrah tayi, haɗe da kallon Auntie Raliya'n "Auntie kamar tsumi ne fa, acikin cup ɗin?"
"Ba kama bane, tsumine me kyau na mata, wanda yake matuƙar wujijjiga oga, amsa kisha banason gardama" Auntie Raliya tace tana ƙoƙarin kai kofin bakin Zahrah.
Kwaɓe fuska Zahrah tayi, haɗe da ɗan marerece ido. "Wallahi Auntie tsoro nake insha wani tsumi, a yanzun, kinsan kuwa yanda nake fama, doctor fa shiɗewa yake, nasha wannan kuma ae shikenan sumar dashi kikeso nayi"
Dariya sosai Auntie Raliya tayi, haɗe da ɗaukan tsuminta ta shanye "Shikenan to idan kin haihu na miki haɗi na musamman, matar doctor, ashe ba abanza ba, gaba ɗaya ƙanina ya sukurkuce akanki, wato kinsan me kikeyi masa" cewar Auntie Raliya.
Dariya Zahrah tayi haɗe da cigaba da cin ɗanwakenta, sai kaɗa kai take wai ɗan waken yayi daɗi, itakuwa Auntie Raliya saiyi mata hira take, sosai suka seta ita da ƴan uwan mijinta, ƙauna sadidan take samu daga wajen Hajiya, yayinda Auntie Raliya ma ke nuna mata so, sun saba sosai da Auntie Raliyan, harjinta take kamar ƴar uwarta tajini, don babu abun da take ɓoyewa Auntie Raliyan, dayake Auntie Raliyan ma irin wayayyun matan nanne, basu da nuƙu nuƙu, baruwanta dawani abu waishi surukanta, ta ɗauki Zahrah'nne kamar ƴar ƙaramar ƙanwarta, don har sirrin yanda ake kama me gida a hanu take faɗa mata..
Sunsha hira sosai da Auntie Raliya, sai bayan sallan Isha doctor Sadeeq yazo ya ɗauketa suka koma gida. Washe gari kuwa, tun 7 am tatafi gidansu amarya Husnah, don yau za'ayi kamunta, kuma itace best friend, don ma ciki yayi mata cikas.
Anyi kamu cikin kwanciyar hankali, yayinda kamun ya ƙawatar sosai, anyi ɓarin naira sosai baga gidansu ango ba baga gidan su amarya ba, naira tayi kuka don ankasheta a wannan ranan, kayan da amarya tasanya ma kaɗai kuɗinsu baƙaramin yawane dasu ba. Zahrah bata bar gidansu Amarya ba sai bayan magrib kusan 9 pm, haka ta koma gida agajiye. Washe gari kuma, aka rangaɗa walima, shima sosai yaƙayatar don anyi musu wa'azi me ratsa jiki, ranan friday kuma aka ɗaura auren Husnah da angonta, sosai dai akasha shagalin bikin Husnah, inda Zahrah tataka rawar gani sosai, wajen ganin tabawa ƙawartata kyauta, wacce zata burgeta. Ranan da aka kai Husnah ɗakin mijinta sosai Zahrah tayita mata tsiya, ita kuwa Husnah ko ajikinta, cewa ma tayi "Mijinta baifi ƙarfinta ba, bata wani jin tsoro, tsaf zata iya ɗauke buƙatarsa".....
***
Yana zaune akan kujera ita kuma tana zaune aƙasa, wani irin ciwo takejin cikinta nayi mata, tun ɗazu yake ankare da ita, amma dai baice da ita komaiba, ganin dayayi tana murƙususu waje ɗaya ne yasanya sa cewa "Baby yadai, akwai damuwa ne?" murmushin dole ta ƙaƙalo haɗe da dubansa ta mererece fuska. "Samad marata kemin ciwo da cikina" tafaɗi haka tana me cije laɓɓanta.
"Subahanallah to kodai naƙira Bro nafaɗa masa ne?" yatambayeta cike da damuwa.
Da sauri ta girgiza masa kae haɗe da cewa "A'a dan Allah Samad karka ƙirasa, banaso yatashi hankalinsa"
Murmushi kawai Samad yayi haɗe da cewa "Babe ƴar daɗi miji"
Harara ta aika masa haɗe da murguɗa masa baki tace "Eh ɗin"
Murmushi yakumayi yaci gaba da cin abincinsa, itakuwa sake matsewa tayi tana mejin ciwon naƙara ƙaruwa. (Kodai Babe haihuwa zatayine ? Chaiii wayaga Zahrah a Labour room🏃♀🏃♀)
(Bansan me na rubuta a chapter 66 kuma 112 ba😂 nasan nayi muku shirme lokacin wallahi ina yanayi ne😂 komai bibbiyu nake gani🤣 amma yanzu nadawo normal💃🏼 My Wattpadians ina ƙaunarku har acikin jinina, inamugun ganin mutumcinku, wallahi na rantse muku saboda ku kaɗai nake typing, inaji daku irin sosai ɗinanan fa, kucigaba da bani vote nikuma zan kawo muku wani labari me sugar, sai yafi Zaid daɗi💃🏼😂)
*26/February/2020*
*✅OTE ME ON WATTPAD*
@fatymasardauna
#Love
#Romance
#SON SO @ my only wattpad fans
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI!!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Chapter 114*
Har ya ƙare cin abincin tana nan zaune sai rumtse ido da cije baki take, ƙirjinta ne yasoma bugawa akai akai, sakamakon tunawa da tayi cewa akwai aiki babba agabanta. Miƙewa tayi daga zaunen da take, ahankali take taka ƙafanta data ɗan kumbura, harta shige cikin ɗakinta. Da kallo yabita har ta ɓacewa ganinsa, murmushi kawai yayi shima kana ya ɗauki wayarsa yafice daga cikin falon.
Tana shiga cikin ɗaki direct ta wuce bathroom wanka tayi da ruwan zafi, kana ta zo ta ɗauki magungunanta tasha. wata ƴar ƙaramar riga tasanya ajikinta, kana tabi lafiyar gado ta kwanta, minti shida tsakani bacci ya ɗauketa.
Kwanciya yayi luf abayanta bayan yacire rigar dake jikinsa, hanunsa yasanya ya ɓalle mata aninayen dake jere a gaban rigarta, lumshe kyawawan idanunsa yayi haɗe da sanya hanu ya shafi breast ɗinta. Saida ya sauƙe ajiyar zuciya me ƙarfi, kana ya sake rungumeta ajikinsa, kansa ya ɗaura akan wuyanta, haɗe da sanya harshensa, yashiga lasan fatar wuyanta, yayinda hanunsa ke kan breast ɗinta, yana murzawa a hankali. Kamar acikin mafarki takejin abun da yakeyi mata,ahankali ta buɗe idanunta, batakai ga kallonsa ba, daddaɗan ƙamshin turarensa, ya sanar da ita cewa shine, sake narke jikinta tayi acikin nasa, jin alamun cewa tafarka ne, yasanyasa juyo da ita suka zama suna fuskantar juna. Kallonsa tayi da idanunta, da suke cike da magagin bacci, murmushi tasakarmasa haɗe da sanya hanu ta shafi lallausan sajen fuskarsa. Idanunsa da suke cike da tarin sha'awarta ya watsa mata haɗe da matso da fuskarsa daf da tata, har numfashinsu na gauraya dana juna, yanayin irin yanda yake kallonta ne, yasanya taji gaba ɗaya jikinta yayi sanyi, wani irin ƙaunarsa me sanyi taji tana shiga cikin jikinta. Ranƙofowa yayi haɗe da yi mata rumfa da ƙirjinsa, baikai gayin romancing ɗinta ba, amma gaba ɗaya kallon daya keyi mata, ya gama kashe mata jiki, ahankali ta lumshe idanunta, sosai ƙamshinsa keyi mata daɗi. Kansa ya cusa acikin ƙirjinta dake tashin ƙamshi, ahankali yake goga mata lallausan sajensa akan breast ɗinta. Sake lumshe idanunta tayi, haɗe da sanya hanunta, a bayansa ahankali take shafawa, tana fidda wani irin numfashi. Slowly yake kissing ɗinta, tundaga ƙirjinta har zuwa kan bakinta, da kaɗan kaɗan yake tsotson pink lips ɗinta, yana me lumshe idanunsa, da suka koma kalar ja, baitaɓa mata irin wannan kissing ɗin me rikita tunani ba sai yau, sosai takejinta cikin wani irin yanayi na musamman, ajiyar zuciya me ƙarfi ta sauƙe, haɗe da buɗe bakinta, kamar zatace dashi wani abu, amma kuma babu wata kalma da zata iya fitowa daga bakinta, saboda gaba ɗaya ya shiɗar da ita. Ya ruɗata da salonsa, harshensa ya tura acikin bakinta, haɗe da soma kaɗa mata shi acikin bakin nata. Hanunsa yasanya ya zare ƴar rigan dake jikinta. ƙasa yayi da kansa yana sucking ɗinta, kamar kullum daya fara sucking ɗinta take saka masa kuka ta kuma shiɗe masa, yau ma hakance takasance, ganin numfashinta nashirin ƙwace mata ne, yasa ta janye kansa, haɗe da mirginawa gefe tana sauƙe wani irin numfashi, ji take kanta na juya mata, ga wani irin sha'awarsa dake fusgarta. Sake kwanciya yayi a bayanta, haɗe da cusa kansa cikin tulin gashin kanta. Numfashi shima yake fitarwa akai akai, burinsa ɗaya shine yaji wannan ɗumin nata, me zautar masa da tunani.
Juyowa tayi gareshi haɗe da hayewa saman ƙirjinsa, hanu tasanya tana shafa gashin kansa, yayinda taɗaura bakinta akan ƙirjinsa, tana sakar masa wasu irin kiss dake tada masa da tsikar jiki, lumshe idanunsa yayi yana me karɓan saƙonta, dama akunne yake matuƙa, gashi yanzu tana ƙara kunnasa. Ganin da yayi cewa zata haukatasa da yawa ne, yasanya sa dawo da ita ƙasansa yazamana shine a samanta. Kallon da yayi mata ne ya ƙara kashe mata jiki, haɗe bakinsu yayi waje ɗaya, lokacin da ɗumin jikinta ya ratsashi saida ya sauƙe wata ajiyar zuciya me ƙarfin gaske, take kuma ya fara manta awacce duniya yake, atare suke kissing ɗin juna, cike da wani irin so, sun matuƙar zautuwa, kowannensu yatafi wata duniyar ta daban, amma duk da haka bakinsu yana cikin na juna..........
*** *** ***
Bayan Wata Biyu.😜
Yanzu cikinta yana wata tara harda sati biyu, amma haihuwa shiru, zuwa yanzu ko tashi bata iyawa sai antaimaka mata, cikinta yayi wani irin girma, hakannema yasa Hajiya da kanta taje ta ɗaukota, ta dawo gidanta da zama, bahaka Dr.Sadeeq yasoba amma babu yanda ya iya, dolensa ya haƙura, kuma sosae yake kewar matartasa, wai donma yanasamu suna keɓewa, idan dare tayi, har hotel suke zuwa.
Kwance take akan doguwar kujeran dake falon Hajiya, green Apple ne riƙe a hanunta, ita bata ciba ita bata ajiye ba. Tun daran jiya take fama da wani irin ciwon mara dana baya, amma babu wanda ta faɗawa, gudun kada su tashi hankalinsu, yanzu kam abun yasoma fin ƙarfinta, don ciwon kamar zai zautar da ita haka takeji, zamowa tayi ƙasa daga kan kujeran da take, haɗe da durƙushewa aƙasan tiles, hanu tasanya takama gefe da gefen cikinta, tare da sakin wani ƙaran azaba, lokaci guda taji wani irin ciwo yataso mata gadan gadan. Fitowar Hajiya daga ɗaki, yayi daidai da shigowan Doctor Sadeeq cikin falon. Dukansu da sauri sukayi kanta.
"Innalillahi Hajiya, dama bata da lafiya ne?" Dr. Yatambayi Hajiya a matuƙar ruɗe. Kafun Hajiya takai ga cewa wani abu Zahrah ta fashe da kuka haɗe da faɗawa jikin Doctor ta ƙanƙameshi ƙam, gaba ɗaya ya ruɗe yarasa inda zai tsoma kansa, shima rungumeta yayi tuni idanunsa sun kawo ƙwalla.
Hajiya ce tafito daga ɗakin Zahrah'n hanunta ɗauke da Hijab, ita tasawa Zahrah'n hijab ɗin, kana tace doctor Sadeeq ɗin ya ɗauki Zahrah su wuce asibiti. Jikinsa na rawa haka ya ɗaga ta ca ɗak yasata a mota, Hajiya tashiga motar ta riƙeta, shikuma yaja suka nufi asibiti, gudu yake dasu kamar zaitashi sama, kanaganinsa kaga wanda baya cikin hayyacinsa, bayaso wani abu na wahala yasamu matarsa ko kaɗan, da ace zai yiwu to daya karɓa mata naƙudan, don baya ƙaunar ganinta cikin wahala da azaba har haka.
Suna shiga cikin asibitin direct aka wuce da Zahrah labour room. Wasu likitoti ne guda uku mata akanta, babu abun da take sai salati da cije baki, ita kaɗai tasan me takeji, ganin bazai iya jurewa ba, yasanya sa faɗawa cikin labour room ɗin, dayake dama asibitinsu ya kawota, yanazuwa gaban gadon, ya kama hanunta, buɗe wahalallun idanunta tayi ta kalleshi, atare wasu hawaye masu zafi suka fito daga cikin idanunsu, matsanancin tausayinta yakeji, fiye da tunanin me tunani, Hanunsa dake saman nata, takama ta matse, haɗe da girgiza masa kanta, cikin wata irin murya me ɗauke da tsananin ciwo tace.
"Kayafemin idan na mutu dan Allah!"
Kai ya girgiza mata da sauri haɗe da cewa. "Bazaki mutu ba Zahrah, zamu rayudake acikin duniyarnan insha Allah, zaki raini abun da zaki haifa ɗa hanunki, insha Allah!!" cike da tsananin rauni ya faɗi haka, sosai zuciyarsa ta karye, bata sake ce dashi komaiba, kawai ta ɗauke idanunta akansa, cigaba tayi da nishi haɗe da karanto addu'a, Doctor na riƙe da hanunta, yana tofa mata addu'a, haɗe da shafa kanta, ƙwalla ne kawai suke fita daga idanunsa. Wani irin yunƙuri haɗe da nishi tayi sai ga kukan jariri ya cika ɗakin. Laƙwas haka tayi akan gadon, lokaci guda komai nata ya tsaya, motsi da numfashinta, duk suka ɗauke, kumatunta yasoma bubbugawa yana ƙiran sunanta, hawaye kuwa akan fuskarsa wani na koran wani kamar an buɗe famfo.
Wata daga cikin likitoti matanne ta ɗauki yaron, takaishi wajen da ake aje jariri, kallon Dr.Sadeeq da yake hawaye tayi, tace
"Haba Sir, wannan fa ba wani abun damuwa bane kasani, yanzu zata farfaɗo insha Allah"
Hankalinsa ma baya wajenta balle yaji me take cewa, shigaba ɗaya ma basirarsa toshewa tayi, amaimakon yabata taimakon dayasan zai dawo da ita hayyacinta, saiya tsaya yana ƙiran sunanta, yana kuma jijjigata. Likitance tashiga bata taimako, wani ƙaƙƙarfan ajiyar zuciya Zahrah ta sauƙe, alaman ta farfaɗo, bayan kamar mintuna uku ta shiga buɗe idanunta a hankali, dashi tafara tozali ya tusata a gaba, sai kuka yake, hanunta ta miƙa masa, da sauri yataho yakama hanun, kissing ɗinta yayi akan goshinta, haɗe da rungumeta, atare suka shiga sauƙe ajiyar zuciya akai akai, sun kusan 8 minute ahaka, kafun taɗan janye jikinta daga nasa, murya a sanyaye tace "Ina Hajiya?" "Tana waje" yabata amasa a taƙaice, yana me binta da kallo me ɗauke da tsananin ƙauna, haɗe da tausayi me ruguza zuciya.
Wata daga cikin likitotinne tace "Sir yakamata a kimtsata, sai mukaita ɗakin hutu"
Juyowa yayi ya kalli likitan haɗe da cewa. "Babu buƙatar ɗaya daga cikinku sai ta kimtsata, nida kaina zan kimtsa abata"
"Sir tana buƙatar ɗinkifa, saboda ta ƙaru" likitan takuma faɗan haka.
Da sauri ya kalli Zahrah, take hawayen dake cike acikin idanunsa, suka gangaro kan ƙuncinsa, wani sabon tausayinta ne yasake kamasa, "Ina sam bazai iya mata ɗinki ba, bazai taɓa koda kwatantawa bane ma, dakansa da hanunsa ya huda Zahrah'nsa? wannan abun bamai yiwuwa bane" yafaɗi haka acikin ransa. Baice da likitotin komai ba, sai matsawa dayayi kusa da Zahrah, yasake sumbatarta akaro na biyu, wata allura ya ɗauko yayi mata a hanunta, tayanda yasan bazataji zafiba, kallonta yayi still hawaye yake, daƙyar ya iya jan ƙafansa yafice daga cikin ɗakin, abun mamaki kota kan jaririn baibiba, tun dama yafaɗo dunia bai kulasaba, yanata rabin ransa Zahrah.
Likitotinnan ne suka ɗinke ta tsab, saidai bata wani ji zafi sosai ba, domin alluran da Doctor yayi mata, allurace me ƙarfi dake hana jin zafi, suna gama ɗinketa, wata acikin likitotin takamata suka wuce bathroom, likitance ta haɗa mata ruwa tayi wanka, tana fitowa likitan tabata wata riga wacce takarɓo awajen Hajiya tasanya, miƙo mata jaririn likitan tayi, hanunta na rawa haka ta karɓi jaririn ɗan nata, tana karɓansa taji wani irin sanyi ya ratsa zuciyarta, fuskar Dr.Sadeeq ta kalla sak akan fuskar yaron nata, lokaci ɗaya taji wani irin so da ƙaunarsa sun cika mata zuciya, tana fitowa acikin labour room ɗin, Hajiya da Dr.Sadeeq sukayo kanta, daga ita har jaririn Hajiya ta haɗasu ta rungume, sai ga ƙwallan farinciki na zuba daga idon Hajiya, amsar yaron tayi daga hanun Zahrah haɗe da sanya sa acikin ƙirjinsa ta rungumesa, sosai takejin ƙaunar jikan nata, musamman dataga yana kama da ubansa, sai dai duk da haka akwai kamannin Zahrah a tattare dashi. Dr.Sadeeq kuwa ko kunyan Hajiya dake tsaye baiyiba yaje ya rungume matarsa, kyakkyawan kiss ya sauƙe mata akan ƙuncinta, haɗe da ɗaura kansa akan kafaɗanta.
Saurin tureshi tayi daga jikinta, ta haye gado ta kwanta, tana sauƙe numfashi, kawar da kanta gefe tayi, wasu irin siraran hawayene suka gangaro daga cikin idanunta, ita kaɗai tasan menene yasata wannan hawayen. Mintuna kaɗan bacci ɓarawo ya ɗauketa, dagani kuma kasan tanajin daɗin baccin.
Alokacin da Doctor yakarɓi jaririn ahanun Hajiya, kafesa yayi da manyan idanunsa, wani irin ƙaunar ɗan nasa ne ke fusgarsa, sosai yaron ke kama dashi, rungume ɗan yayi acikin ƙirjinsa, sai kawai ga hawaye nafita daga cikin idanunsa, kallonsa ya maida ga Zahrah wacce take bacci, wutar sonta ne ke ƙara ruruwa acikin zuciyarsa, lallai Zahrah tana da babban matsayi agareshi, ta basa farinciki me ɗorewa, tahaifa masa ɗa, tayi masa komai a duniyarnan, baisan damene zai saka mata ba.
Hajiya dakanta ta ƙira Inna tasanar mata maganan haihuwan, dama tuni Aunty Raliya kam ta tsofe a asibitin, koda su Inna sukaji cewa Zahrah ta haihu, ba ƙaramin farinciki sukayi ba, sunji daɗi sunyi murna sosai, ita da Baffa duka suka rankayo zuwa asibitin.
Ba ita tafarkaba sai bayan azahar, bathroom ɗin ɗakin da take ciki ta shiga, haɗe da sake tsabtace jikinta, tana fitowa kuwa tasamu Doctor ya karɓo musu takardan sallama. Gaba ɗaya likitotin asibitin babu wanda baitaya Dr.Sadeeq murnan samun ƙaruwan da yayi ba, har ɗaki suke zuwa su duba Zahrah, sukuma tayasu murna.
Hanyar da Hajiya taga ya miƙa ne yasanyata cewa.
"Wai ina zaka damu ne Sadeeq?"
Da compidence ɗinsa ya juyo gareta haɗe da cewa. "Gidana mana Hajiya"
"Gidanka? to ba gidanka zamuba, gidana zamuyi, hauka kake na ɗauki yarinya da ɗanyen jiki, na baka? wama zai tsaya ya kula da ita? maza juya akalar motarnan" Hajiya tafaɗi haka babu alamar wasa akan fuskarta.
Sam bahaka yasoba, amma babu yanda zaiyi, shikenan shi baza abarsa yaji ɗumin matarsa dana ɗansaba, haka yata ƙunƙuni acikin ransa shi kaɗai, har suka isa gidan Hajiya.
Abinci mai rai da lafiya Hajiya ta kawowa Zahrah, ga kuma gasashshen nama, bayan taci abincin Hajiya dakanta, tasakeyi mata wanka.
Zama tayi agaban mirror tashafe jikinta da manta me daɗin ƙamshi, powder tashafa afuskarta, bata tsaya nanba harda janbaki tashafawa laɓɓanta, ga kuma kwalli da ta sanyawa cikin idanunta, mascara ta ɗauko ta zizira akan eye lashes ɗinta, take fuskarta taƙarayin kyau. Wani riga da sket na material me tsada tasanya ajikinta, take takoma ƴar baby kamar yanda take da, dogon gashinta ta kanannaɗe a bayanta, haɗe da hayewa gado, zataci gaba da bacci, miƙo mata yaron Inna tayi haɗe da cewa "Wani kwanciya kuma zakiyi bayan baki bawa yaron nono ba?"
Shagwaɓe fuska Zahrah tayi haɗe da turo ɗan ƙaramin bakinta gaba, da ƙyar ta iya ciro nonon nata ta kai bakin yaron, yana kamawa ta runtse idanunta da ƙarfi, saboda wani zafi da taji, haka dai ta ɗan daure, shikuwa yaron sai zuƙeta yake, gajiya tayi dajin zafin ta cire nonon abakinsa, kwantar dashi tayi, itama kana ta kwanta agefensa, baccin gajiya ne ya kuma ɗaukarta...
Idan dai hartaji sauƙan numfashinsa akan wuyanta, to yazame mata dole ne farkawa daga baccin da take, yanzu ma sauƙan numfashin nasa taji adai dai saitin kunnenta, a hankali take ware idanunta harta sauƙesu akansa. Murmushi yasakar mata haɗe da ɗaura kansa akan ƙirjinta.
"INA SONKI!!!" yafaɗa murya a sanyaye....
*(Insha Allah gobe zanmuku update, yau naso nayi da yawa, to wallahi tsoron editing nake, amma Insha Allah gobe kujira sabon posting, maybe ma yanzu kullum zanna baku update saboda mugama book ɗin da wuri)*
*28/February/2020*
*✅OTE ME ON WATTPAD*
@fatymasardauna
#Love
#Romance
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasrdauna
*CHAPTER 115*
"NIMA INASONKA!"
Tafaɗa tana me lumshe idanunta. Iskan bakinsa ya hura mata akan fuskarta, haɗe da sake rungumeta, ɗayan hanunsa yasanya ya shafi kan jaririn nasa, dake ta bacci. Murmushi Zahrah tayi ganin yanda Dr.Sadeeq ya kafe yaron nasa da ido. Hajiya da Inna ne suka shigo cikin ɗakin atare, da sauri Zahrah ta janye jikinta daga na doctor, shima a kunyace ya sauƙa daga kan gadon yana sosa kai.
"Hmmm Allah yashirya, Inna kina gani ko, wai da ahakan yakeso na basa ita" inji cewar Hajiya.
Murmushi kawai Inna tayi batace komai ba. ( Su Inna anzama nitsaljin🤣) Kallon Doctor Hajiya tayi haɗe da cewa "Zo muje inason magana dakai" babu musu yabi bayanta suka fice daga cikin ɗakin.
Zama tayi akan kujera haɗe da maida hankalinta garesa.
"Me dame kake shiryawa sunan nanne? sannan kuma da wani suna kayiwa yaron huɗu ba?"
Murmushi ya ɗanyi haɗe da cewa "Ai nagama shirina tuntuni Hajiya, dama lokaci kawai muke jira, sannan kuma dama tuntuni sunan babanta nake son sawa yaron, dashi kuma nayi masa huɗu ba"
Hajiya tace "Masha Allah, To Allah Ubangiji ya rayasa, hakan da kayi kuma ka kyauta, tashi kaje dama maganan da zamuyi kenan"
Miƙewa yayi haɗe da yi mata sallama yafice daga cikin falon.
Lokacin da Husnah tazo ganin Baby kusan haukacewa tayi, sai santin yaron take wai yayi mata kyau sosai, komai nasa irin na babansa, ga idanunsa kyawawa, itadai Zahrah dariyanta kawai take, saboda itama Husnan tana ɗauke da ɗan ƙaramin ciki.
Akwatuna guda biyu Dr.Sadeeq ya kawo wa Zahrah, ɗaya nata ɗaya na baby'nsa wai kayan barka, kayane masu kyau da tsadar gaske sosai ya kashe kuɗi, wai ahakanma wasu kayan nanan zuwa.
Kulawa Zahrah take samu a wajen Hajiya sosai, idan kaganta ma kamar ba itace ta haihu ba, sosai jikinta ya murje, tasakeyin fresh, hasken fatarta ma sosai ya ƙaru, komai nata ya cika, taƙara kyau akan nada, shikansa Dr.Sadeeq idan yaganta, ko son ɗauke idanunsa akanta bayayi, saboda yanzu tasake zama wata mace ta musamman, duk inda ta zauna kuwa ƙamshi take rabawa.
Ranar suna yaro yaci sunan baban Zahrah wato Adam, za'ana ƙiransa da (Asad) lokacin da labarin sunan da aka sawa yaro yazo kunnen Zahrah sosai taji daɗi, wani irin farinciki taji acikin ranta, girman Doctor kuwa ya ƙaru acikin idanunta, ta tabbatar cewa shiɗin mai so da ƙaunarta ne.
Da sassafe meyi mata meckup tazo ta tsantsara mata ado, sosai fuskarta tasha kwalliya, wani haɗaɗɗen lace orange and milk colour tasanya ajikinta, wanda yaji ɗinkin riga da sket irin 12 piecess ɗin nan, sosai kayan sukayi mata kyau, domin sunja kuɗi wajen sayansu da ɗinkasu, kowa yaga Zahrah da babynta saiyace masha Allah. Saboda sunsha kyau sosai. Hidima sosai akayi tundaga kan abinci da abun sha, har izuwa abubuwan da za'a rabawa baƙi, akwati guda biyu Hajiya tayiwa Zahrah da ɗanta, haka Baffa ma akwati yayi mata Inna ma zagewa tayi tayiwa Zahrah akwati shaƙe da kaya, Auntie Raliya ma akwati ta mata, sosai Zahrah tasha kaya, har rasa inda zata sa kayan tayi, ana cikin haka saiga kayan Dr.Sadeeq sun iso, akwatuna huɗu, biyu natane shaƙe da kaya, sauran biyun kuwa na yarontane, bata gama mamakin irin dukiyar da Dr.Sadeeq yakashe mata ba, saiga Aunty Raliya tana rangaɗa guɗa, hanunta riƙe da key, danƙawa Zahrah key ɗin tayi ahanunta, haɗe da cewa "Ungo amsa kyautace ta musamman daga mijinki, ya baki kyautar gidansa dake cikin asokoro" mamakine ya kusan kashe Zahrah
"Gida kuma Aunty?" ta tambayi aunty Raliya don tayi tunanin ko kunnuwanta ne basu jiye mata da kyau ba.
"Ƙwarai kuwa gida, saima kinga gidan, don gidane me tsananin kyawun gaske, yafa kashe kuɗi sosai wajen ƙawata gidan" Inji cewar Aunty Raliya.
"A'a Aunty gaskiya nikam banaso, wani irin kyautane haka? hidimar da Doctor yakeyi dani tayi yawa, daga haihuwata zuwa yau yakashe kuɗi yafi 3 million fa Auntie, yanzu kuma yace yabani kyautar gida suku tum, inajin tausayinsa Aunti banason nazama rauni acikin arzikinsa" Zahrah tafaɗi haka da iyaka gaskiyarta.
Murmushi Auntie Raliya tayi haɗe da sanya hanu ta dafa duka kafaɗun Zahrah.
"Kada ki damu Zahrah, shi ɗinfa mijinki ne, kuma kome zaimiki aduniyarnan bazai biyaki ba, kamar yanda kema bazaki iya biyansa duk abun daya miki ba, saboda haka babu wani abun damuwa don yamiki wannan kyautar, kin cancanci hakanne agareshi, don haka amshi makullin gidanki, ke dai kawai kiyi masa godiya, irin wacce ta dace" Aunty Raliya ta faɗi haka tana me damƙawa Zahrah makullin gidan ahanunta.
Kuka Zahrah ta fashe dashi tana jin ƙarin ƙaunar mijinnata na huda mata zuciya, lallai yazama dole agareta taƙara ƙaimi wajen kyautata masa.
Yamma nayi aka haɗa walima me rai da lafiya, bayan malama tazo tagabatar da wa'azine akayi ciye ciye, aka kuma sha drinks, duk wanda yazo sunan kuwa babu wanda baisamu kyaututtuka ba, abun sai dai ace Alhamdulillah, kafun magriba tuni mutane sun watse, gida ya saura daga Hajiya sai Zahrah da kuma Aunty Raliya.
Wanka tasakeyi ta tsantsara ado cikin wani irin meterial me kyau da tsada, wanda yana cikin kayan da Doctor ya ɗinka mata don fitan suna, doguwar riga akayi mata wanda ya matuƙar kama jikinta sosai, dogon gashinta dayasha saloon ta kanannaɗe atsakiyar kanta, ba abun dake fita ajikinta sai ƙamshin humra dana body spray.
Zama tayi akan gado haɗe da ɗaukan wayarta tashiga kan whatsapp, yaronta kuwa tuni dama yana wajen su Hajiya dake zaune a falo suna hira, Sadiya me aikin Hajiya ce tashigo cikin ɗakin haɗe da sanarwa Zahrah cewa wai tayi baƙo yana falo.
Jitayi gabanta yaɗan faɗi, amma saita dake tace da Sadiyan tace da baƙon tana zuwa.
Mayafi ta ɗauka ta yafa ajikinta, kana ta zura flat shoe ɗinta, tafice daga cikin ɗakin.
Su Hajiya tasamu zaune afalon, sai kuma wani, wanda bata ma taɓa ganin fuskarsa ba. Kafun takai ga gaishesa, shiya ɗago mata gaisuwa, amsawa tayi tana ɗan murmushi, gyara tsayuwansa yayi haɗe da cewa..
"Saƙone dama akabani nakawo miki, yana waje, idan ba damuwa muje saiki gani"
Kallon tsoro tashiga yi masa, saboda batasansa ba balle tasan wanene ya aikosa.
"Badamuwa, Raliya rakata sai kuje kuga saƙon ko"
Hajiya tafaɗi haka, don ta lura da tarin tsoron daya bayyana akan fuskar Zahrah'n.
Hakan kuwa akayi tare suka fita da Aunty Raliya.
A compound ɗin gidan suka tsaya gaban wata haɗaɗɗiyar mota ƙirar mercedes maroon colour, mutuminne ya bubbuɗe ƙofofin motar, take kayan dake shaƙe acikin motar suka bayyana, ɗan makulli ya miƙowa Zahrah haɗe da cewa
"Ranki ya daɗe gashi ni nacika umarnin da aka bani, wannan kyautace daga megida na, yace na ce miki Allah ya raya"
Mamaki haɗe da al'ajabi ne suka kama Zahrah da Aunty Raliya.
"Kyauta daga me gidanka kuma? wayeshi to?" Zahrah tayi masa duka waƴannan tambayoyin cike da son jin amsa, haɗi da kuma mamaki, gani take kamar mutumin baida cikakken hankali.
Murmushi kawai ɗan aiken yayi haɗe da sake miƙo mata makullin motar yace
"Kiyi haƙuri bai bani damar sanar miki dashi ɗin kowaye ba, amma yace dan Allah ki karɓa"
Ta buɗe baki zatayi magana kenan motar Dr.Sadeeq ta kutso kai cikin gidan.
Kasa cewa komai tayi har Dr.Sadeeq yafito daga cikin motarsa, ya ƙaraso garesu, kallonsa Zahrah tayi shima kallonta yakeyi.
"Hajiya ga makullin ni zan wuce" wannan mutumin yafaɗi haka, yana sake miƙa mata ɗan makulli.
"Ko ma waye ya aikoka, kace masa banaso, don bana buƙata" tafaɗi haka tare da juyawa daniyar komawa inda ta fito.
"Zahrah!"
Sunanta da Dr.Sadeeq yaƙirane yasanyata tsayawa cak haɗe da juyowa tana kallonsa.
"Zoki amsa, ki kuma yi masa godiya" Dr.Sadeeq yafaɗi haka, yana me karantar yanayinta.
Cike da mamaki tace "Amma..."
"Banaso kice komai ki amsa kawai nace" yakatseta daga maganar da take ƙoƙarin yi.
Jiki asanyaye ta karɓi makullin motar.
Ciki ciki tace "Kace nagode"
"To" kawai ɗan aiken yace kana ya juya yafice daga cikin gidan.
"Wai meke faruwa ne, waye ya aikosa?" Aunty Raliya ta tambayi doctor, don ta lura kamar yana da masaniya akan wanda ya aiko motar da cikinta ke shaƙe da kaya.
Murmushi Doctor yayi haɗe da cewa "wani aminina ne dake zaune a Dubai, shine dana gaya masa ta haihu yayi mata wannan kyautar"
Dafe ƙirji Aunty Raliya tayi tare da cewa
"Lallai wannan koma wayeshi yanaji da naira, wannan motarfa zatakai 4million inma bata fi ba, ga kuma kayan dake cikinta, wanda suma kaɗai sun haura 1m, me kenan yake nufi?"
"Babu wani abun da yake nufi Aunty, haka dama shi yake kyautarsa, muje ciki ko" yaƙare maganar yana kallon Zahrah wacce ta daskare a wajen.
Cike da mamakin kyautar abokin Doctor ɗin Aunty Raliya taja ƙafanta takoma falon Hajiya, Zahrah ma jikinta a sanyaye tabi bayanta, shima falon yanufa, yanda yaga tana tafiya asanyaye ne yasanyasa yin murmushi kawai.
Bata tsaya a falon ba direct ɗakin dayake masauƙinta ta wuce, tsayawa tayi a gaban mirror zuciyarta cike da tarin tambayoyi kala kala, sam bataji zuciyarta ta aminta da kyautar nan da'akayi mata ba, kwata kwata batama yarda cewa wai abokin Doctor bane ya bata. Tana acikin tunanin, yaturo ƙofar ɗakin yashigo bakinsa ɗauke da sallama.
Amsa masa sallaman nasa tayi haɗe da zuba masa idanunta, dagani kai kasan tambayoyine cike a bakinta.
takowa yayi ya ƙaraso daf da ita, hanunsa yasanya ya jawota jikinsa, saida yashaƙi daddaɗan ƙamshin dake fita ajikinta, ya sauƙe ajiyar zuciya, kana yace.
"Kinyi kyau sosai"
Murmushi ta ƙaƙalo haɗe da cewa. "Nagode"
Cikinsa yashafa tare da cewa. "Yunwa nakeji sosai, nayi missing sweet cook ɗinki, please ko zaki kawomin abinci?"
"Meyasa kake barin kanka da yunwa? kasan banaso, yanzu me zakaci na kawo ma?" tatambayeshi cike da kulawa.
"Koma me idan kika kawomin ni mai iya ci ne" yafaɗi haka yana me zama a bakin gado.
Harta kusa fita daga cikin ɗakin sai kuma ta tsaya cak, haɗe da juyowa, idanunsu yafaɗa cikin na juna, domin dama shima kallonta yake.
"Waye ne yaturomin da mota? Nasan kasan ko waye, domin zuciyata tafaɗamin cewa, ba abokinka bane ya turo, kamar yanda kafaɗa a baya" tambayar da tayi masa kenan, cike da burin samun amsa agareshi.
"Baki yarda da abun dana faɗa ba kenan?" ya tambayeta yana me ƙara tsareta da manyan idanunsa.
Murya a sanyaye tace "Kayi haƙuri, bawai ina nufin kamin ƙarya bane, kawai dai naji zuciyata ce bata gamsu da amsar da ka bayar ga Aunty Raliya ba"
Murmushi yayi haɗe da cewa "Zuciyarki tafaɗa miki gaskiya, domin kuwa ba abokina bane yaturo kamar yanda na faɗa a baya"
Waro idanunta tayi, duk da zuciyarta ta raya mata cewa ba abokinnasa bane, amma kuma duk da haka bata tsammaci jin haka daga bakinsa ba.
"Waye?" tatambaya murya na rawa.
"ZAID" yabata amsa ataƙaice...
(Nagaji kuyi manage, idan nasha ruwa zan ɗora daga inda na tsaya)
*29/February/2020/*
*✔️OTE ME ON WATTPAD*
@fatymasardauna
#Love
#Romance
#One Love My Wattpadians
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Chapter 116*
"ZAID!" ta maimaita sunan abakinta cike da tsananin mamaki.
Yanda yaga jikinta na ɓari shine abun daya basa mamaki, zallan tsoro ya hango kwance akan fuskarta, yayinda cikin idanunta kuwa, suka bayyana soyayyar dake kwance acikinsu, wato soyayyar ZAID, shi yasani ba tun yauba, bakuma zai yaudari kansa ba, yasani ƙwarai Zahrah na son Zaid, so ba irin na wasaba, so matsananci, amma kuma babu yanda zaiyi, dayana da iko to daya cire mata son Zaid acikin zuciyarta, amma wannan banasa bane, na Allah Ne, yasan Zahrah tana sonsa, amma soyayyar da takewa Zaid ta dabance, da ace zai iya, to daya danne zuciyarsa, ya miƙata ga Zaid, yasan hakan zai samarmusu da farinciki, ita da Zaid, amma kuma yasan koda yayi hakan to ba mafita bane, domin ayanzu yasan dole idan baya tare da Zahrah tayi kewarsa, yana sane da cewa yakafa mata tutar son sa, wanda bazata ankara da hakan ba, har sai randa yazama baya tare da'ita, baya fatan wata ƙaddara ta rabasu, amma yasani ko mai daren daɗewa sai sun rabu, saboda akwai mutuwa, koshi ko ita, watarana ɗaya dole zai bar ɗaya, yau idan baya raye, baya fata Zahrah ta auri wani namiji idan ba Zaid ba, tunaninsa yayi nisa, baisan da cewa ta ƙaraso inda yake ba, saida yaga ta zube a gabansa, tana kuka, cikin muryar kukan takecewa.
"Kada kamin haka doctor, wallahi ni banason duk wata kyauta da zatafito daga garesa, namantasa acikin rayuwata, banaso kuma nasake tunasa, kamayar masa da kyautarsa, bana buƙata farincikin da kake bani kaɗai ya isheni"
Tunda tafara maganan yake kallonta, ajiyar zuciya yayi, haɗe da kamo hannayenta, cikin murya me sanyi yace. "Kinsani bakyau maida hanun kyauta baya, meyasa to zakiyi haka? mekike tunani akan Zaid?" ɗan dakatawa da maganar yayi, tare dayin wani murmushi, kana ya miƙe tsaye, daga zaunen da yake.
"Kyautace kawai ya miki, ai atunanina hakan ba wai yana nufin wani abubane, bazan tilasta miki ba, amma nasan abundake cikin zuciyarki, don gashi har a idanunki sun nuna, so ba ƙarya bane Zahrah, haka kuma ba laifi bane, don zuciya na dakon so, wannan ma wata ƙaddarace, wanda babu wani wanda ya isa ya kauce mata" yanakai ƙarshen zancen nasa yanufi hanyar fita daga ɗakin.
Da sauri taje ta faɗa jikinsa, kuka take sosai, durƙusawa tayi haɗe da zube guiwowinta a ƙasa, kana ta riƙe rigarsa, kanta tashiga girgizawa, tana kuka tace. "A da na sosa fiye da yanda naso kaina, amma ayanzu baya acikin zuciyata kamar yanda kake tunani, Inasonka da duka zuciyata, bana fatan wata ƙaddara tazo wacce zata rabani dakai, kabani farinciki, kajiyar dani daɗi, kashayar dani zuman soyayyarka, bazan iya watsa maka ƙasa idanunka ba, kai mijinane wanda bayan kai bani da wani tamkarka, nasan kai ɗin me sonane, amma meyasa kayi haka? mai yasa kai da kanka, zaka amince da na karɓi kyautar wanda yazama silar rugujewar rayuwata?"
Durƙusawa yayi agabanta, haɗe da sanya hanunsa ya share mata hawayen dake gudu akan fuskarta, cike da kulawa yace. "Banason kukanki Zahrah, keɗin wata babban jigo kuma mahaɗi ne acikin rayuwata, nasan Zaid ya cutar da rayuwarki, amma kuma hakan bazai hana ki amshi kyautarsa ba, ayanzu kowa yasan cewa ke matatace, saboda haka Zaid bazaiyi miki kyauta da wata manufa ba, kuma kafun ya miki kyautar saida ya tambayi amincewata tukunna, nakuma amince masa, nayarda da Zaid Zahrah, nasan idan duka mutanen duniya zasu taru su cutar dake, to Zaid bazaiyi hakan ba, haka kuma idan ni zan iya cutar dake, to ina tabbatar miki idan Zaid yasan da hakan, to bazai bari na cutar dake ba, Zaid ɗin da kikasani ada bashine wanda yake a yanzu ba, kada kiyi tunanin wai ko zanji haushi akan kyautar da Zaid yayi miki, niba jahili bane Zahrah, haka kuma halina ya banbanta da na wasu mazan, ni mutum ne me saurin fahimta, sannan kuma abune mawuyaci nayiwa wani na mummunan zato, agurin wasu mazan, hakan zai iya zama matsala, amma a wajena hakan ba komai bane, tunda nasan cewa keɗin tawace ni kaɗai, bakuma wai don bana kishinki bane yasa hakan tafaru ba a'a, ni kalan nawa kishin ba irin na wasu bane, inakishinki sosai, sai dai kuma kome acikin nutsuwa nakeyinsa, ke kinsan inasonki ina kuma kishinki " yaƙare maganar yana me lakace mata dogon hancinta.
Kukane yakuma ƙwace mata sai kawai tafaɗa jikinsa, ta rungumesa ƙam, shima rungumeta yayi yana shafa bayanta ahankali, haɗe da hura mata iskan bakinsa, acikin kunnenta.
Saida tayi kukanta sosai, kafun ta soma sauƙe ajiyar zuciya, cikin murya me sanyi tace.
"Kai na da banne Mijina, irinka basu da yawa acikin duniya, haƙiƙa nafi kowacce mace sa'a dana sameka, dakai kaɗai zan rayu har izuwa mutuwa ta, kaima ka rayu dani ni kaɗai kaji, bazan iya jure ganinka da wata mace ba bayanni, Ina maka son da bansan iyakarsa ba!"
Murmushinsa dake ƙara masa kyau yayi, haɗe da sanya iskan bakinsa ya hura mata fuska.
"Dake kaɗai Zan rayu Zahrah na, ni nakine ke kaɗai, amma idan kina kukan nan fa, dole zan ɗan yi ƙasa da idanuna, na hango wata, saina kawota ko wanke wanke ne tanayi mana ko, idan dare yayi kuma sai ina raba muku kwana ko..."
Bata bari yakai ƙarshen zancen nasa ba, ta muntsine sa aciki, saida yasaki wata ƴar ƙaramar ƙara, cike da shagwaɓa tace "Wallahi nidai babu ruwana dakai, idan dai har kace zakamin kishiya!"
Dariya yayi sosai haɗe da cusa kansa acikin ƙirjinta. "Ni na isa ma nayiwa ƴar sakalalliyar matata kishiya, amma bandai saniba wataƙila idan naga kin tsofe na miki!" yanzuma cikin zolaya yayi maganar.
Hannayenta tasanya acikin gashin kansa, tashiga ya mutsawa, hadda kai masa cizo a wuyansa. Sai da tayi masa buji buji da kayan jikinsa kafun ta ƙyalesa, gashin kansa ma gaba ɗaya ta hargitsa masa shi. Koda ta kawo masa abinci tare sukaci, yana kwance ajikinta itakuma tana bashi abincin abaki, ahaka har ya ƙoshi.
Kallonta yayi da idanunsa, dake tsumata kana yace "Namatsu abani ke Baby na, wallahi ina kewar ɗumin ki sosai, amma Hajiya gaba ɗaya ta kanenaye min ke, waidole saikinyi arba'in, Babyna kice tabarmu mu koma gidanmu kinji!" cikin yanayi na shagawaɓa ya faɗi haka.
Murmushi Zahrah tayi, haɗe da sanya hanu ta shafi kumatun sa, cike da ƙaunarsa tace "Kayi haƙuri Hubby, nima ina kewar sucking ɗinka, kuma ai bawai bazan dawo bane zan dawo fa" tafaɗi hakane don kawai ta kwantar masa da hankali.
Ya buɗe baki zaiyi magana kenan muryar Hajiya ta karaɗe kunnuwansu, inda take cewa.
"To iyayen rashin kunya, saika tashi katafi dare na ƙarayi, ke kuma miji daɗi, ga yaronki nan, abincinsa yakeso ki basa." kunyar Hajiya ne yakama Zahrah, haka ta amshi yaron kanta a ƙasa.
Doctor kuwa turawa Hajiya baki yayi, haɗe da cewa "Hajiya zantafi, amma kiɗanyi haƙuri ba yanzu ba mana"
Baki Hajiya ta sake tana kallonsa. "Sannu marar ta ido, wallahi saika tafi yanzu kuwa" Hajiya tafaɗi haka tana me kama hanunsa, haka yanaji yana gani ta fitar dashi daga ɗakin, Zahrah kam dariya taketa yi masa. Bayan ta shayar da yaron natane, tashiga toilet tayi wanka, doguwar rigan bacci tasanya, kana ta ɗauko diary'nta, rubutu tayi aciki, ta mayar dashi ma'ajinsa. Kwanciya tayi luf akan gado, cike da tunani kala kala bacci ya ɗauketa....
*** *** ***
Yau kwanansu 50 cif cif agidan Hajiya, sunƙara kwanaki 10 akan kwanakin gama wankansu, idan kaga Zahrah bazakace ita bace, sosai taƙara cika da kyau, fatarta ta ƙara haske, komai nata yasake cika, gwanin sha'awa, yau ne zata koma gidanta, tuni Dr.Sadeeq ya sanja mata kayan furnitures ɗinta, komai yasanya mata sabo, Hajiya kuwa tun tuni taketa ɗirka mata magunguna, haka Aunty Raliya ma ta dage sai bata wasu magunguna masu ƙarfi take, ita kuwa sha take abunta, wanda taji yanada bauri ne kawai take ajiyewa bata sha.
Wanka ta tsantsara cikin wata jar atamfa Super Exclusive, wacce taji ɗinkin riga da sket, sosai kayan ya amshi jikinta, zama tayi da kanta, ta tsantsarawa fuskarta kwalliya, sai gashi kuwa kyawunta ya ƙara bayyana, dogon gashinta dayasha gyara ta tubke da ribbon haɗe da kafa ɗaurin ɗan kwalinta me kyau, wani red ɗin takalmi tasanya aƙafanta me tsinin gaske, ɗan ƙaramin mayafi ja ta ɗauka ta rufe jikinta dashi, babu abun dake fita ajikinta, sai daddaɗan ƙamshi.
Yana tsaye ajikin motarsa dake fake a compound ɗin gidan, yaga fitowarta, kusan suman tsaye yayi. "Tabbas Zahrah me kyauce, tahaɗu tako ina, kullum ƙara kyau da cika take, lallai kuwa da yayi saken barin Zahrah, tabbas da yazama soko, marar rabo, samun mace kamar Zahrah, babban sa'ane daya samu a rayuwarsa" yafaɗi haka acikin zuciyarsa, yana hangame da baki wajen kallonta, baisan ma taƙaraso garesa ba, saida yaji ni'imtaccen ƙamshinta na ratsa cikin hancinsa.
Murmushinta me kyau tayi masa haɗe da kashe masa idanunta ɗaya. "Ya dai kwalliyar tayi maka ne" tafaɗi haka tana me juya masa bayanta. Alaman yaganta da kyau.
Yawu ya haɗiye, alokacin da idanunsa suka sauƙa akan hips ɗinta, baigama dawowa hayyacinsa ba, yakuma jefa idanunsa akan ƙirjinta, jikinsa na rawa ya jawota ya rungumeta.
Wani irin ajiyar zuciya suka sauƙe atare.
"I really Miss you Babyy!!" yafaɗi haka akasalance.
"Miss you too dear!" itama ta mayar masa da amsa cikin muryar raɗa.
Hajiya dake kallonsu ta window tasaki murmushi haɗe da komawa cikin falonta ta zauna, aranta tanayi musu fatan shiriya.
Saida suka biya ta JABI lAKE sukayi sayayya tukun kafun daga nan suka wuce gida.
Wanka ta sakeyi ta shirya kanta cikin wata irin fitinanniyar sleeping gown, wacce ta bayyana komai na surarta bata ɓoye komai ba, rigar doguwace har kusan ƙafa, amma kuma duk da haka itaɗin kamar babu take, kasancewarta shara shara. dogon gashinta ta sake a bayanta, haɗe da shafe jikinta da shu'umar Humra, wani sweet Lip Gloss tashafa akan leɓenta.
Yana zaune a falo yana danna laptop ɗinsa, ƙamshinta ne yafara kawo masa ziyara, lokacin daya sauƙe idanunsa, akanta sai da yaji wani irin shock ajikinsa, da sauri ya miƙe ya ƙarasa gareta. buɗe hannayensa yayi daniyar rungumeta, da sauri ta matsa gefe, tanayi masa dariya, haɗe da yin wata irin tsayuwa, wacce takusa zautar dashi.
Lumshe idanunsa yayi tare da sanya hanunsa ya jawota jikinsa. Ƙam ya rungumeta, sai gashi yana sauƙe ajiyar zuciya akai akai. Kallon juna suka shiga yi idanun ko wannensu ɗauke da tsananin sha'awar ɗan uwansa. Jikinsa na rawa ya kama lip ɗinta na ƙasa, yana tsotsa ahankali, jiyake kamar yanashan honey. da kanta ta zame rigar dake jikinta, ta faɗi ƙasa, take surarta ya bayyana, hmmm ba yau yafara ganinta ba, amma kuma ya zautu ƙwarai daganin surar jikinta, jiyake kamar ma baitaɓa kusantarta ba, sosai yayi missing ɗinta. Jikinsa na rawa ya ɗauketa suka wuce bedroom, tuni dama Asad yayi bacci, dama shi haka yake sam baida ƙiriniya, daya ƙoshi sai bacci, bakuma zai tashiba sai dai idan yanajin yunwa.
A yau ɗin ne suka sake tabbatar da cewa sunyi kewar juna, musamman ma Doctor Sadeeq da kusan cinyeta ne kawai baiyi ba, gaba ɗaya ya zauce, ya susuce, wasu maganganu yake wanda ita kanta batasan me yake cewa ba, saboda sun lula wata duniya ta musamman, wacce sukayi nisa acikinta basaji basa gani, kansu kawai suka sani. Aranan nan wata zuma suka shayar da junansu, wanda bazasu taɓa mantawa ba. Wannan ranan takasance rana ta biyu masu muhimmanci a garesu.
*** *** ***
Bayan wata 6........
America
Zufa ne keta ketowa ta goshinsa, gaba ɗaya baya cikin nutsuwarsa, kai komo yaketayi agaban labour room ɗin sama da 1 hour kenan yana abu ɗaya, jiyake kamar yasanya hanu akansa yaita ƙwala ihu. Ɗaya daga cikin Nurse ɗin dake kanta na fitowa ya nufi wajenta, da sauri idanunsa sunkaɗa sunyi jajur dasu. Murmushi Nurse ɗin tayi masa haɗe da cewa "Ina tayaka murna, matarka ta haihu, kasamu baby girl" wani irin sanyin daɗi yaji acikin ƙirjinsa, baisan lokacin dayayi sujja don nuna godiyarsa ga Allah ba.
Ana kaita ɗakin hutu, wata nurse tace yashigo ya karɓi babynsa, lokacin daya sanya hannayensa ya amshi babyn, wani irin kukane ya ƙwace masa, alokacin da idanunsa suka sauƙa akan kyakkyawar fuskarta kuwa, bugun zuciyarsa ne ya ƙaru, saboda kokaɗan yarinyar bata kama da mahaifiyarta, durƙushewa yayi aƙasa, riƙe da yarinyar tasa yana kuka, hakan kuwa sosai yabawa likitotin mamaki.
Bakomaine yasa sa yake kuka haka ba, face tsananin danasani na rayuwar da yayi abaya da yake. yakasance mazinaci, mashayin giya. "Yanzu idan ƴarsa mafi soyuwa agaresa, tataso taji labarin abun da ya aikata a baya, wani irin kunya zaiji? mezaice da'ita idan ta tambayesa, meyasa yazamo haka?" tambayar da yayiwa kansa kenan, amma kuma baida amsa, baida kuma me amsa masa.
Rungumeta ya sakeyi tsam, acikin ƙirjinsa, ahankali yace.
"Kindawo gareni Zahrah, Allah yadawomin dake, Inasonki Inasonki, inamiki so na musamman Allah ya albarkaceki ƴata!!!" kiss ya manna mata akan goshinta, kana yazuba mata idanu, bazaiyi mamakin kamannin daya gani akan fuskar ƴartasa ba, saboda yasan ba aja da ikon Allah, kuma hakan ma wata rahamace da Allah yayi masa, Allah ya hanasa Zahrah alokacin dayaso, yanzu yakuma basa Zahrah alokacin dayaso, hancinta bakinta duka kalan nasa ne, amma kuma idanunta tamkar idanun Zahrah aka ciro aka sanya mata, kallon farko da yarinyar tayi masa, saida yaji tsikar jikinsa ya tashi, saboda gani yayi tamkar Zahrah ce dakanta agabansa. yana rungume da yarinyar ya ƙarasa gaban Afrah dake kwance akan gado tana kallonsu, ranƙwafowa yayi ya manna mata kiss akan goshinta, hanu yasa yashafi kumatunta, haɗe da cewa "Nagode ƙwarai Afrah, Allah ya miki albarka, bazan manta da wannan ƙoƙarin da kikamin ba, Inasonki"
Karo na farko kenan arayuwarta da taji kalmar nan tafito daga bakinsa akanta, "Inasonki" ta maimaita kalmar abakinta cike da mamakinsa.
Kansa yajinjina mata haɗe da sakin murmushi.
"Ki kwanta ki huta, nasan kinsha wahala sosai" yafaɗi haka yana shafa kanta.
Lumshe idanunta kawai tayi saiga hawaye nabin kan fuskarta. Hanu ta miƙa masa ya bata yarinyar, ba iya mamaki ba hadda tsoro saida ya bayyana akan fuskar Afrah, sakamakon ganin fuskar yarinyar ɗago kanta tayi ta kalleshi da sauri.
Kamar yasan me take tunani, murmushi yayi mata haɗe da ɗaura hanunsa akan kafaɗanta. "Kada kidamu, Allah ne yayi ikonsa, Allah ne yadubeni yayimini rahama, sannan kuma ko da ace kowa zaiyi mamakin kamannin yarinyar ni bazanyi ba, saboda wacce take kama da ita, jinin jikinane, sannan kuma Allah yana da ikon yin komai"
Ajiyar zuciya kawai Afrah ta sauƙe haɗe da kafe yarinyar nata da ido, tabbas da badan taji ƙauna irinta uwa da ƴa akan yarinyarba, to tabbas da tace ba itace ta haifi yarinyar ba, Zahrah ce, shine aka sanja mata, aka ɗauki nata aka kaita wani gun, itakuma aka kawo mata wannar, a matsayin ƴarta. Rungume ƴar tata tayi, tanajin ƙaunarta aranta.
***
Suna komawa gida Zaid yayiwa Afrah kyautar zuƙeƙiyar mota, tare da kuɗi Naira Million 3 duk na murnan ta haifa masa baby ne, washe gari kuwa suka tarkato suka dawo Nigeria, abisa takurawan Mom ɗinsa. amma da anyi suna yace zasu koma. Aranan da aka haifa masa Zahrah aranan ya mallaka mata babban kamfaninsa na ƙera takalma, dake Italy, aranan kuma akasanjawa kamfanin suna zuwa sunan yarinyar, saɓanin da dayake sunan Zaid.
Tunda aka haifi Zahrah Zaid baibari kowa ya ɗauketa ba, inbanda uwarta, nan ma nono kaɗai take bata, idan yaɗauketa yashiga ɗakinsa da ita, kulle ƙofar yake da key gudun kada wani ya damesa, komai na duniya shiyake mata, wani irin so da ƙaunar yarinyar yake ji, wanda baitaɓa jin irin saba, akullum kallon Zahrah kawai yakeyiwa yarinyar. Irin soyayyar dayake yiwa yarinyar shike tsorita kowa.
Ranan suna kamar yanda ya alƙawartawa kansa cewa idan ya haifi ƴa mace sunan Zahrah zaisawa yarinyar, hakance takasance domin kuwa sunan nata yasaka, wato FATIMA ZAHRAH, koda Afrah taji sunan da ƴartata taci sai kawai tayi murmushi, ko kaɗan batayi fushi da faruwar hakan ba, saboda tasan albarkacin Zahrah itama zata samu soyayya ta musamman daga wajen Zaid ɗin, haka kuma albarkacin Zahrah ƴarta itama zata samu gagarumar soyayya daga wajen ubanta.
Nairori sunyi kuka a wannan rana, sosai Zaid yayi ɓarin kuɗi tundaga randa aka haifeta kawo yau dayake suna, dukiya kawai yake ɓararwa, tun abun nabawa Mom ɗinsa da Afrah mamaki, har suka daina mamaki, saboda zuwa yanzu sunsan soyayyar da Zaid keyiwa ƴarsa Zahrah ta wuce gaban kwatance, harta bacci akan ƙirjinsa takeyi.
(Sai haƙuri idan kunga typing error, Yau banyi editing ba, wai ina kukene masoyan Zaid, kwata kwata naga alama bakwa farinciki, ace matar Zaid ɗinku nada ciki, amma ku kasa nuna farincikinku, ashe soyayyar takuma, batakai zuci ba, haka team Doctor ma, kuma ashe soyayyar taku ta bogece, tunda anmasa haihuwa ko barka bakuje ba.....)
*✅OTE ME ON WATTPAD*
@fatymasardauna
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Godiya ta Musamman Agareku HASSAN ATK and HUSSAINI 80k haƙiƙa kuɗin kun cancanci babban yabo, ako da yaushe akullum kuma ina yaba ƙoƙarinku, Allah Yabiya muku baƙatunku na alkhairi. Dani da sauran marubuta muna godiya sosai agareku*
*NOTE* *Nasan daga fara book ɗinnan kawo yanzu na ɓata ran wasunku da yawa, amma inaso kusan cewa sam bahaka naso ba, wannan labarin me suna SHU'UMIN NAMIJI ƙirƙiransa nayi da kaina, ba wani ko wata bane suka bani labari ko shawaran nayi, sannan kuma inaso yawancinmu musan cewa yarda da ƙaddara yana daga cikin imani, balallaine kasamu abunda kakeso alokacin da kake soba, haka kuma balallaine akullum kazamo me nasara ba, haƙiƙa Nasara wani babban jigone da kowa keson samu acikin rayuwarsa, haka kuma rashin nasara ma wani jigo ne da ke sawa mutum ke gane kuskurensa awasu lokutan, idan da'ace komai muka nema zamu samu, to tabbas da ayanzu dayawanmu munshagala da bautar ALLAH Hakan kuma sam ba dai dai bane, arayuwa akwai abu biyu NASARA da kuma FAƊUWA, balallaine kazamo me sa'a ba ako da yaushe, dayawanku suna jin haushin abun da nayi, na hanawa Zaid auren Zahrah, inaso ku fahimceni, banhana Zaid auren Zahrah da gangan ba, ko wai don son zuciyata ba, a'a, inaso kufahimci cewa rashin Zahrah acikin rayuwarsa shine mafarin shiriyarsa, koda a gaskene ba wai a novels ba, idan kanemi abu baka samuba, kada kazargi wani abu, kada kuma kaga kamar ALLAH Baya sonka ne, ko kaɗan bahaka abun yake ba, bai zama lallai abun da kakeso yazamanto alkhairi agareka ba, haka kuma wani lokaci Allah Yakan jinkirta baka abun da kakeso koda kuwa abun alkhairi ne a gareka, kada kayi fushi domin hakan ma wata JARABAWA ce agareka, ALLAH'n daya haliccemu yafi kowa sonmu, shi ke bamu, shi kuma ke hanamu, kada ki/ka sa damuwa acikin zuciyarka, wai don waninka yasamu kai baka samu ba, kaima watarana zaka samu Insha Allah, sannan kowa aduniya baya wuce rabonsa, haka Idan ALLAH Maɗaukakin Sarki ya tsara abu, to babu wanda ya isa ya sauya, natsinci kainane kawai da fara typing ɗin wannan labarin batare da nayi tunanin komai ba, hakanan nafara rubutashi, cikin ikon Allah kuma yabani sa'a, kuka karɓeshi hanu bibbiyu, haƙiƙa labarin nan nice nake rubutasa, amma kuma bani ke da ikon abun da zai faru acikinsa ba ALLAH Ne, komai da ɗan Adam zaiyi acikin duniyarnan bashi keda ikon yinsaba ALLAH Ne kawai ke bashi dama, to haka ALLAH Yatsara cewa Zahrah ba matar Zaid bace, babu kuma wanda ya isa ya bawa Zaid ita sai ALLAH..... Kuyi haƙuri masoyana ina rubuta muku labarinne aduk yanda yazo kaina, nasan dayawa kunji ba daɗi, saboda bakwason Doctor, sai dai kuma babu yanda nidaku zamuyi dole sai haƙuri, wasu har yanzu suna ran cewa, Zahrah zata koma ga Zaid, sai dai ina mai baku haƙuri domin awannan labarin Zaid ba zai taɓa auren Zahrah ba, haka ƙaddaransa take, kuma duk musulmi yanada kyau ya yarda da ƙaddaransa walau mai kyau ko marar kyau.*
*CHAPTER 117*
Two years Later!
Acikin shekaru biyunnan da suka wuce abubuwa da yawa sun faru, ciki kuwa hadda haihuwan Husnah, da kuma ƙarin girman da akayiwa Doctor Sadeeq a wajen aiki, Zahrah kuwa tazama lecturer acikin jami'ar da tayi karatu. Abubuwa dayawa sun faru acikin waƴannan shekarun.
Tsaye take agaban wani babban table tana haɗa wasu takardu dake gabanta, ajikinta sanye take da Abaya gown, maroon colour, wanda jikinsa yaji adon duwatsu da kuma flowers masu kyau, yayinda Abaya Vail ɗin dake yafe saman kanta, ya sauƙo har zuwa ƙirjinta, babu wani kwalliya akan fuskarta, lipstick ne kawai sai kuma kwallin data sanya acikin ɗara ɗaran idanunta, sosai taƙara kyau, cika da kuma wayewa, duk da cewa a ƴan shekaru biyun da suka wuce itaɗin ba baya bace wajen kyau, amma ayanzu komai nata yaƙara ninkuwa akan nada, yanzu tana amsa sunanta na cikakkiyar mace. Kallonta ta maida kan agogon dake ɗaure akan tsintsiyar hanunta. "4:30 pm" ta faɗa tana ɗan waro idanunta, da sauri tacigaba da tattare takardun, wasu tasa acikin jakarta, wasu kuwa ta sanyasu acikin wata drawer dake cikin office ɗin. Wayarta da jakarta ta ɗauka, kana ta nufi hanyar fita daga office ɗin.
Motarta ƙiran Corolla LE tashiga haɗe da bata wuta, ta fice acikin jami'an.. Bata wani jima sosaiba ta isa sabon gidansu wanda suka koma babu jimawa.
Da sallama ɗauke abakinta ta kutsa kanta cikin falon, babu kowa afalon, sai TV Plasma ɗinsu dake ta aiki shikaɗai. Direct wani ɗaki dake cikin falon ta nufa, tsayawa tayi ajikin ƙofar ɗakin tana sakin murmushi, idanunta nakan wani yaro da shekarunsa na duniya bazasu wuce uku ba, ya nata ƙiriniyansa shi kaɗai, yaron kyakkyawane sosai, gashin kansa kuwa kamar na larabawa. Cikin sanɗa tashiga takawa harta ƙarasa wajen dayake zaune, murya a hankali tace.
"Babyy!" Jin muryar mahaifiyarsa acikin kunnuwansa yasashi juyowa da sauri, yana ganinta, ya tafi ya faɗa jikinta, yana dariya, itama dariyan tayi haɗe da manna masa kiss akan bakinsa, cike da kulawa haɗi da ƙaunarsa.
"Aunty Sannu da dawowa" cewar Haulat me yi mata rainon yaron, idan zata aiki.
"Yauwa Haulat sannu da gida" Zahrah ta amsa mata fuska a sake.
Ɗaukan yaronnata tayi suka fice daga ɗakin, direct sama ta haura inda anan bedroom ɗinta yake.
Aje yaron nata tayi akan gado haɗe da durƙusawa agabansa, chocolate irin marar zaƙi sosai ɗinnan ta ciro ajakarta, kana ta ɓare ta basa a hanunsa, da murna Asad ya karɓi Chocolate ɗin, matso da fuskarsa yayi daf da tata, kiss yayi mata akan kumatunta haɗe da cewa "Thank you Mummy!" yayi maganar ne cikin muryarsa dake ɗauke da tsananin yarinta.
Murmushi tayi kana taɗanja kumatunsa, miƙewa tayi ta wuce cikin bathroom acan ta cire kayan jikinta haɗe da sakarwa kanta shower.
Koda ta fito sama sama ta shafa mai domin yanayin garin ana ɗan busa zafi, wani dogon skin tight baƙi ta sanya, wanda yayi matuƙar bayyana surar jikinta, bama kamar hips ɗinta da suka sake cika, wata riga mai net tasanya, irin fitted ɗinnan, sosai rigan tayi mata kyau, ƙirjinta ne kawai yazamana a rufe, amma gaba ɗaya jikinta daga cikinta zuwa bayanta a bayyane suke, haka tsarin rigar yake.
Da Body Spray ɗinta me daɗin ƙamshi ta feshi jikinta, dogon gashinta dayasha kitson kalaba, ta kama ta ɗaureshi da ribbon, direct gaban ɗan madaidaicin fridge ɗin dake ɗakin ta nufa, buɗewa tayi ta ɗauko goran Yoghurt, buɗe murfin goran tayi tasoma sha ahankali.
Shigowarsa ɗakin kenan, amma kuma kokaɗan bataji motsin buɗe ƙofarsa ba, yana sanye da riga da wando na Suit navy blue colour masu kyaun gaske, tabbas ya sauya daga kamanninsa nada, yaƙara haske da kyau, ga lallausan sajensa da ya kwanta luf akan fuskarsa, yazama wani na musamman dashi, me tafiya da hankalin ƴan mata, yaƙara zama Handsome, dagani kai kasan kuɗi sun zauna masa..
Dariyan Asad da taji ne yasata waigowa ta kalli yaron, atunaninta ko ɓarna yakeyi mata, gani tayi idanunsa nakan ƙofar shigowa ɗakin, saboda haka itama ta maida idanunta wajen, da taga Asad ɗin na kallo.
Idanunsu ne suka sarƙe a cikin na juna, wani irin murmushine ya ƙwace mata, haɗe da lumshe idanunta, ta kuma buɗesu alokaci guda, shima murmushin yayi mata, kana ya buɗe duka hannayensa, alaman ta taho garesa, babu musu ta ƙarasa garesa, haɗe da faɗawa cikin jikinsa, atare suka rungume juna, tare da sauƙe ajiyar zuciya.
Hanunsa yasanya yashiga shafa bayanta, haɗe da soma hura mata iskan bakinsa, cikin kunnenta. Luf tayi acikin ƙirjinsa, tana mai jin daɗin abun da yakeyi mata, idan har tanajin iskan bakinsa acikin kunnenta, sosai take samun nutsuwa acikin ruhinta.
Sun kusan mintuna 10 a haka kafun tace dashi cikin sanyin murya. "Sannu da dawowa!"
Bai amsa mata ba, saima hannayensa daya ɗaura a gefe da gefen cikinta, yashiga shafawa a hankali, shiru tayi aƙirjinsa tana sauƙe numfashi. Ɗayan hanunsa yasanya ya ɗago haɓarta, suka jefa idanunsu acikin na juna, wani irin kasalane ya dirar mata alokaci guda, sakamakon tozali da kyawawan idanunsa da tayi. lumshe nata idanun tayi, tana sauƙe numfashi a hankali, matso da tasa fuskar yayi gaf da tata, harsuna iya jiyo hucin numfashin juna, bakinsa ya buɗe haɗe da kamo lip ɗinta na ƙasa, yasoma sucking a hankali, tsikar jikinta ne, ya shiga tashi, take wani shauƙi yasoma ratsa ta, kusan mintuna 6 yana sucking lip ɗinta, kafun ya tsagaita yashiga maida numfashi. Ganin haka yasanya ta sanya hanunta akan wuyansa, haɗe da sanya bakinta acikin nasa, ta laluɓo harshensa, tasoma masa shan sweet, yanda take sucking ɗinsa tausassun laɓɓanta na kai komo cikin bakinsa shine abun da ya ƙara hautsina tunaninsa, tsananin sha'awarta ne yasake ninkuwa acikin zuciya da jikinsa. Hannayensa yasanya yana ƙoƙarin buɗe gaban rigarta. Kukan Asad ne ya katsesu daga duniyar da suke ƙoƙarin faɗawa, gaba ɗaya su sunma manta da cewa yana ɗakin. shikuwa Asad chocolate ɗinsane yafaɗi ƙasa, shiyasa sa fashewa da kuka.
Da sauri Zahrah ta ƙarasa garesa haɗe da ɗaukan chocolate ɗin ta danƙamasa a hanunsa, dawo da kallonta tayi ga Doctor dake tsaye idanunsa sunyi ja. Murmushi tasakar masa, tare da takawa ta ƙarasa garesa, hanunsa ta kama ta zaunar dashi akan gado, kayan jikinsa tashiga rage mai, saida ya rage dagashi dai dogon wandon suit ɗin dake jikinsa. Bathroom tashiga ta haɗa masa ruwan wanka. saida taga shigansa wankan kafun ta ɗauki Asad suka fice daga cikin ɗakin, wajen Haulat tamaida Asad, itakuma ta wuce kitchine. Milk Shake tahaɗa masa, haɗe da ɗaukan wani tray na tangaran me kyau ta yayyanka kayan marmarin aciki. ɗaukan ɗan madaidaicin tray ɗin tayi, tare da cup ɗin da milk shake ɗin ke ciki, ta nufi ɗakinta.
Harya fito a wankan yana zaune akan gado, dagashi sai long jeans ajikinsa, tanashigowa cikin ɗakin, ya kafeta da tsumammun idanunsa, ɗan madaidaicin stool ta jawo ta ɗaura kayan hanunta akai, zama tayi akusa dashi. Da kanta tasoma bashi fruit ɗin abaki. Yanacin fruit ɗin amma gaba ɗaya hankalinsa na ga breast ɗinta da suka bayyana kansu ta saman rigar dake jikinta. Sarai ta kula da cewa hankalinsa naga breast ɗinta, hakan yasa da gangan ta kuma saɓule wuyar rigan don yagani da kyau. Tana kammala bashi fruit ɗin, aka soma ƙiran sallan Magriba, alwala yayi haɗe da ɗaura brown ɗin jallabiya akan wandon dake jikinsa yafita zuwa masallaci, itama alwalan tayi, ta gabatar da sallah, bata tashi akan sallayan ba har saida tayi sallan isha. Wanka takuma yi, yanzu kam wata fitinanniyar sleeping gown ta sanya wacce iyakarta guiwa, turarenta da tasan yana tafiya da imaninsa tashafa, haɗe da ɗaukan wani wanda ƙamshinsa ke haifar da kasala, tashafa aƙasan breast ɗinta dama duk wani lungu da saƙo na jikinta.
Tana tsaye agaban dressing mirror ɗin yashigo cikin ɗakin, dawowarsa daga masallaci kenan.
Lumshe idanunsa yayi haɗe da buɗewa, idan yabiyewa Zahrah zata zautar dashi ne kawai, gaba ɗaya yawani zama soko akanta, kullum ƙara kyau da cika take, sannan kuma duk kwanan duniya ƙara fito da wani sabon salo take, wanda take rikitasa da su, ga tarin soyayyarta dake ƙara wanzuwa acikin jini da jikinsa, shikansa baisan wani irin so yakeyi mata ba, amma yayi amanna da cewa, bayan Zahrah babu wata, ita kaɗaice bata da tamka, ita ta musammance acikin matan duniya. baisan wata mace ba aduniyarsa bayan ita, amma kuma yanaji ajikinsa cewa, yayi dace, yakuma samu gamdakatar wanda bayajin akwai wata wacce zata kama ƙafarta.
Ƙarasowa yayi gaban mirror ɗin ya rungumeta ta baya haɗe da kwantar da kansa abayanta, yana sauƙe ajiyar zuciya, iya ƙamshin dake fita ajikinta ma kaɗai, ya isa yasanya masa feeling, ina kuma ga ya taɓa lallausan fatar jikinta.
Hanu tasanya ta shafi gefen fuskarsa, haɗe da ɗan zame jikinta daga nasa. Hijab ɗin dake aje kan gado ta ɗauka, haɗe da zurawa ajikinta.
"Hubby Nasan Babyna yayi bacci, banaje na dubasa" tafaɗi haka tana me nufar hanyar fita daga ɗakin.
Bai iya ce mata komaiba harta fice.
Tanazuwa ɗakin Asad ɗinkuwa tasamu yayi bacci akan lallausan gadonsa, yayinda Haulat mai kula dashi itama tuni tayi bacci, zama tayi ta tofeshi da addu'a, haɗe da gyara masa kwanciyansa. Rage musu hasken wutan ɗakin tayi kana ta yi ficewarta.
Tana shiga tasamesa tsaye dagashi sai towel ɗaure a ƙugunsa, yayinda jikinsa ke ɗauke da danshin ruwa, da'alama ruwa ya watsa wa jikinsa. Cire hijab ɗin jikin nata tayi, ta nufo inda yake, atare suka sakarwa juna murmushi, jawota yayi haɗe da mannata da ƙirjinsa, hanunsa yasanya acikin gashin kanta, murya asanyaye yace.
"Nayi kewarki dear, muna gida ɗaya amma yau two days kenan banji ɗumin jikin ki ba!" yaƙare maganar yana me cusa kansa acikin wuyanta. Lokacin da sajensa ya taɓa fatar wuyanta, saida taji wani yarrrrrr ajikinta, hanunsa yakai kan cikinta, ya warware igiyan da tazamo mahaɗin rigar dake jikinta, aikuwa take rigar ta buɗe ta gaba, hannayensa duka yasa ya juyo da ita suka zamana suna fuskantar juna. kallon juna suka shigayi cike da shauƙi, hanunta ta ɗaura akan chest ɗinsa tana shafawa a hankali, lumshe idanunsa yayi haɗe da laluɓar fuskarta ya haɗe bakinsu waje ɗaya. A hankali suke sucking lips ɗin junansu, suna fidda wani irin numfashi mai sauti, cike da nutsuwa ya zame gaba ɗaya rigar jikinta, tayi ƙasa, hannayensa yaɗaura abayanta yashiga shafawa yana yawo dasu ahankali har ya gangaro zuwa kan ƙirjinta, still bakinsu na haɗe dana juna suna bawa kansu hot kiss. Saida sautin numfashinsu dukansu ya sauya, alokacin da hanunsa suka shiga yawo akan breast ɗinta, cire bakinsa yayi acikin nata kana ya gangaro da bakinnasa zuwa wuyanta, tsotseta yake son ransa, yana fidda wani irin numfashi dake nuna yana cikin tsananin mayen sha'awa dakuma sonta. ƙafafunsu ne suka soma gazawa wajen ɗaukarsu, tana acikin ƙirjinsa suka nufi kan bed. Maƙalewa tayi ajikinsa, ahankali take goga masa breast ɗinta akan chest ɗinsa, hakan kuwa sosai ya ruɗasa, tana kwance aƙasansa yayinda shikuma ya yi mata rumfa da faffaɗan ƙirjinsa, sukansu basusan awacce duniya suke ba, gaba ɗaya sun zauce, alokacin daya gama ratsa cikin jikinta, sai da wasu hawaye masu ɗumin gaske suka gangaro daga cikin idanunta, sam hawayen bana baƙinciki ko damuwa bane, wannan hawayen sukan fitane alokacin daya dace, lokacin da mutum yakasance baya acikin duniyarsa, irin wannan hawayen sukan fitane, alokacin da mutum wanda ke acikin tsananin magagin sha'awa da kuma so yasamu abun dayakeso a lokacin daya kusa zautuwa, wannan hawayen na musamman ne, wannan hawayen sukan fitane alokacin da mutum yasamu cikar muradinsa.
Yanayin da suka samu kansu aciki, yakasance me daɗi agaresu, gaba ɗaya daren sun ƙare shi ne cikin soyayya, yayinda Zahrah keta zuba masa shagwaɓa shikuma ya dage sai lallaɓata yake, koda sau ɗayane bayason abun dazai ɓata ranta. Gaba ɗaya yagama shagwaɓata, yamai da ita saikace wata ƴar 7 year. Yanzuma shagwaɓan tagama zuba masa, tana kwance luf acikin ƙirjinsa, yayinda shikuma ya kafeta da idanunsa, dake ɗauke da mayen sonta. Kissing ɗinta yayi akan goshinta, haɗe da maida duka hannayensa cikin ƙirjinta, har yau jinta yake kamar sabuwar budurwa, koda yaushe ƙara shiga zuciyarsa take, sannan babu wani abu na jikinta daya sauya daga mai kyau zuwa marar kyau, breast ɗinta har yau sunanan a yanda suke babu wani abu daya samesu, hakan nema yasa ako da yaushe yake nanuƙe mata, ya murzata son ransa, atunaninsa bacci take saboda haka yayi ƙasa da kansa zuwa ƙirjinta, wani numfashi ta sauƙe alokacin da taji hucin numfashinsa, na sauƙa akan ƙirjinta ahankali, dama baccinta baiyi nisa ba, duka hannayenta ta cusa acikin gashin kansa, tana yamutsawa slowly, ahaka har bacci ya ɗaukesu dukansu..
(Nima bacci nakeji, kuyi haƙuri typing ɗin dare nayi, yanzu nagama kuma dare yayi sosai, saboda haka da safe idan Allah Yakaimu zan sake muku shi. Please kubani Vote sosai a wannan page ɗin, Inason wannan page ɗin, da wanda zanyi gaba sufi kowanni page na baya yawan vote, next page na Zaidun mune.)
*✅OTE ME ON WATTPAD*
@fatymasardauna
#Love
#Romance
# SON SO @ my wattpadians.
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*SHU'UMIN NAMIJI !!*
*Written By*
Phatymasardauna
*Dedicated To My Brother KHABIER*
*🌈Kainuwa Writers Association*
*WATTPAD*
@fatymasardauna
*Godiya ta musamman agareka NAZEEFI YAREEMA (N YAREEMA) wannan fejin gaba ɗayansa kyautane agareka*
*Godiya mai tarin yawa ga duk wani ko wata, dake mini forwading novels ɗina, haƙiƙa kuna ƙaramin ƙarfin guiwa, kuma inajin daɗin hakan sosai, Allah Yabarmu tare*
*Bazan taɓa mantawa dakuba my lovely fans, haƙiƙa kuma kuntaka rawar gani sosai wajen sambaɗomini comment, ina alfahari daku aduk inda kuke masoyana, Allah yabar ƙauna maitarin yawa a tsakaninmu Ameen*
*Da bazarku nake taka rawa my Wattpadians, SON SO tare da SON ƘAUNA nakeyi muku, Inasonku irin sosai ɗinnan*
*CHAPTER 118*
*(END! END!! END!!!)*
Rayuwa tana tafiya ne da gudu gudu batare da wani mai rai ya ankara da hakan ba, akullum kwanan dunia shekarunmu ƙara ƙarewa suke, sannan ƙara girma muke, sake kusantar mutuwa muke. Daga kwana ɗaya anzarce kwanaki daga kwanaki anwuce satuttuka daga satuttuka anwuce watanni daga watanni anɗarawa shekaru. Haka yake ako da yaushe, acikin waƴannan kwanaki da shekarun kuma abubuwa ne masu yawa suke faruwa suke kuma shuɗewa, wani yasamu cigaba wani kuwa yasamu naƙasu, wani ransa yayi baƙi wani kuwa ransa yayi fari ƙal. To hakance takasance acikin labarin ZAID da ZAHRAH, shekaru sunja rayuwa ta haɓaka, shekaru sama da biyar kenan yanzu, har lau kuma rayuwa suke cike da farinciki....
"MY SOUL! MY SOUL!! MY SOUL!!!" muryarsa daketa kwaɗa ƙiran sunan MY SOUL ta ƙaraɗe ilahirin farfajiyan gidan, tundaga cikin katafaren falonsa, keta kwaɗa ƙiran har ya kawo compound ɗin gidan.
Sanye yake da wando track suit sai kuma wata farar t-shirt ƙafarsa sanye suke cikin wani takalmi mai igiyoyi. Tsayawa yayi haɗe da sanya hannayensa akan ƙugunsa yana fesar da numfashi, yayinda yaketa baza idanunsa, ko zai hango wacce yake nema. Babu wani abu daya sauya ajikinsa, sai ma kyau da hasken fata daya ƙara, ga wani haɗaɗɗen ƙasumba daya daɗa ƙawata kyakkyawar fuskarsa, lallai shiɗin namiji ne cikekke, wanda zai ɗauki hankalin duk wata mace data gansa, ya haɗu sosai da sosai, duk da cewa shekarunsa sun ƙaru akan nada, amma duk da haka yana nan ayanda yake, kyawunsa da kwarjininsa suna nan, haryanzu shiɗin mutum ne mai tsananin son gayu, sam bayason ƙazanta, komai nasa me ajine. ZAID kenan namijin dayazamo abun kwatance acikin sauran mazaje, namijin daya iya jure dakon soyayya me tsananin zafi, namijin daya zamanto sadauki, akan soyayya.
Sake gyara tsayuwarsa yayi, haɗe da ƙara furta ƙiran sunan
"MY SOUL"
Da gudun gaske wata kyakkyar yarinya wacce bazata wuce 6 year ba ta ƙaraso tsalle ɗaya tayi ta haye bayanshi, lumshe idanunsa yayi, alokacin dayaji an ɗale kan bayansa, yasan babu wani ko wata da zaiyi masa wannan aikin idan ba MY SOUL ɗinsa ba. Hanunsa yasanya ya jawota daga bayansa, zamewa yayi akan guiwowinsa haɗe da ɗaura duka hannayensa akan kafaɗunta.
"Maƙoshina saura kaɗan yafashe My Soul duk kuma akanki ne, kinaji inata ƙiranki shine kikaƙi ki amsa ko?" tamkar wani ƙaramin yaro shagwaɓaɓɓe haka ya faɗi maganar.
Dariya fara kyakkyawan yarinyar da yanayin fuskarsu ke shige da tata tayi, haɗe da sanya hanunta akan dogon hancinsa.
"I'am Sorry My Papa luv, ina cikin garden ne, kuma na amsa amma bakaji ba" yarinyar tafaɗa tana ɗan juya idanunta.
Murmushinsa mai kyau yayi mata haɗe da jawota jikinsa ya rungume.
"Bazaki daina juya idanunki idan kina magana ba ko?" yatambayeta yana me shafa bayanta ahankali.
"Papa luv banice fa nakeyin hakan da gangan ba, nima banasanin najuya idanuna idan ina magana!" tafaɗi haka a shagwaɓe hartana ɗan buga ƙafafunta a ƙasa.
Lumshe idanunsa kawai yayi yana maijin ƙarin ƙaunar ƴartasa na ratsa jini da tsokan sa, sosai yanayinta ke kama dana Zahrah babba, haka kuma ɗabi'ar Zahrah ne wani lokaci idan tana magana takan juya idanunta, to itama wannan haka ta keyi, sau da dama idan tana abu, kallon real Zahrah kawai yakeyi mata, domin kuwa yanzu da ta ƙara girma kamanninta da Zahrah sai ya sa ke fitowa, baisan wani irin soyayya yakeyiwa ZAHRAH ƴarsa ba, gaba ɗaya soyayyan da yayiwa Zahrah itace ta dawo kan yarinyar, wani irin so yake yi mata da baida misali, jinsonta yake ako ina na jikinsa, Zahrah ƴarsa itace rayuwarsa, itace Hasken sa, itace madubinsa, wacce idan ya duba ransa keyin sanyi, samunta yafiye masa komai aduniya, samunta wani alkhairi da ginshiƙi ne acikin rayuwarsa, domin kuwa tunda yasameta, arzikinsa suka yalwata akan nada, shikansa ayanzu baisan iya adadin dukiyarsa ba, itakanta yarinyar kamfanoni masu tarin yawa ya buɗe mata, sosai yake samun alkhairi adalilinta.
"Papa Luv!" yarinyar ta ƙirasa murya a sanyaye.
Buɗe idanunsa yayi ahankali haɗe da sauƙesu akan babyn ta sa "Na'am My Soul" ya amsa mata.
Ya mutse fuska tayi haɗe da cewa "Yunwa nakeji Papa Luv banyi breakfast ba"
Waro kyawawan idanunsa yayi haɗe da miƙewa tsaye ya sungumeta suka nufi inda zai sadasu da babban falon gidan.
Tana tsaye agaban dining area tana nunawa hause girl yanda zata shirya musu dining ɗin, tasha adonta cikin wani jan lace me kyau da burgewa, taƙara cika ta zama babbar mace, dagani kai kasan tana murza naira son ranta, domin wani haske ta ƙara tayi fat da ita. Shigowarsu cikin falon suna dariya yasanya ta maida hankalinsu gareta, batasan wannan wace irin soyayya bace ke tsakanin Zahrah da Babanta Zaid, soyyace irin ta bugawa a jarida.
Tana tsaye tana kallonsu suka ƙaraso dining area'n kujera yaja ya zauna akai kana ya ɗaura Zahrah akan kujeran dake gefensa na dama, dama kuma haka suke zama koda yaushe.
Murmushi Afrah tayi haɗe da cewa "Nashiga ɗakinka banganka ba ae, sainayi tunanin kana wajen yin gym, ashe ma kuna tare da Zahrah"
Murmushi kawai yayi haɗe da sanya hanu ya shafi kan Zahrah, baitankawa Afrah ba saima duban Zahrah da yayi cike da so yace "Me zan zuba miki?"
"Duk abunda zakaci Babana nima shi zanci!" Zahrah tafaɗi haka tana kashe masa idanunta ɗaya.
Dariya suka sanya atare haɗe da bata hanunsa suka tafa, abinci yasoma zuba musu da kansa, acikin plate ɗaya, dama kuma a yanzu baya taɓa cin abinci saida Zahrah, zaiƙi ci da kowa amma zaici da ita, kujera Afrah taja ta zauna itama, haɗe da soma yin serving ɗin kanta, don ta lura babu wani wanda yake ta ita, daga Zaid ɗin har Zahrah, su dama kansu kawai suka sani.
Shida kansa yaciyar da ƴartasa, itama haka ta dinga basa abincin abaki har ya ƙoshi, sama sama suke hira da Afrah, nan ma itace take jansu da hira, amma daba haka ba bazasu kulata ba, ita har mamakinsu ma take, Zahrah sam bata damu da ita ba, kamar ba itace ta haifeta ba, zancenta baya wuce mahaifinta dakuma Momyn Friend ɗinta, wanda suke makaranta ɗaya dashi.
Tana gama goge bakinta da tissue ta kalli Papa Luv ɗinnata ashagwaɓe tace. "Please Papa luv yau muje shan ice cream mana!"
"My Soul yau inada aiki, mubari sai gobe mana, kinga fa next week zamu koma U.S.A, akwai abubuwan danakeso nayi kuma kafun mu koma" yafaɗi haka bayan ya aje kofin tea ɗin dake riƙe ahanunsa.
Sake shagwaɓewa tare da narke fuskarta tayi, ɗan ƙaramin bakinta taturo gaba haɗe da cewa
"Ae Dan Allah Nace Papa Luv, inaso naje ne!"
"Shikenan zo muje na shiryaki" yafaɗi haka yana mai miƙo mata hanunsa.
Tsalle ta doka haɗe da faɗawa jikinsa ta rungumesa, cike da farinciki ta kai masa sunbata akan ƙuncinsa.
"Thank You Papa Luv"
Ɗagata yayi caɗak akan kafaɗunsa haɗe da sanya hanu ya kwashe wayoyinsa dake kan table, direct suka wuce ɓangarensa.
Kai kawai Afrah ta girgiza haɗe da cigaba da cin abincinta, sam abunsu baya damunta, tasaba da hakan, koda yaushe haka suke, kamar tip da taya basa rabuwa.
Shida kansa yayi mata wanka yashiryata cikin wasu riga da wando na jeans masu matuƙar kyaun gaske, naɗe mata dogon gashinta yayi a tsakiyar kanta, da wani babban ribbon, lokaci ɗaya kyawunta da tsananin kamaninta da Zahrah suka sake bayyana, shima wanka yayi kana ya shirya kansa, cikin wasu riga da wando masu kyaun gaske, sosai yayi kyau sai tashin ƙamshi yake, Little Zahrah dakanta saida tayaba kyawun da Papa Luv ɗinta yayi.
Yana riƙe da hanunta suka fito harzuwa falo, kallonsa ya maida ga Afrah wacce ta mato akan kallonsa.
"My Wife bazaki zo kirakamu bane?" ya tambaya.
Murmushi kawai tayi haɗe da lumshe idanunta, akasalance tace "Kuje kawai Dear nikam inanan, amma ku tahomin da nawa ice cream ɗin"
Hanu Zahrah ta ɗaga mata alaman bye bye kana suka fice daga cikin falon.
Barinta yayi awajen sayan kayan maƙulashe irinsu chocolate da sauransu shikuma ya nufi wajen turaruka. Tana tsaye ta ƙurawa wani babban ledan chocolate dake can sama idanu, so take ta ɗaukoshi ta sanya acikin kayanta amma kuma wane ita, ya ɗarawa tsayinta, jitayi anrufe mata idanu a hankali, a iya saninta mutum ɗayane keyi mata hakan, saboda haka yanzuma tasan cewa shiɗinne, dariyan farinciki tasaka haɗe da cewa "ASAD!"
Dariya yayi haɗe da sake mata fuska ta juyo zuwa garesa, kyakkyawan yarone wanda bazai wuce 7to8 year ba, yarone fari tas dashi tamkar ajinsin larabawa yafito, tsallen murna Zahrah tasanya haɗe da rungumesa, shima rungumeta yayi cike da jin daɗin ganin ƙawartasa wacce rabonsa da ita yau tsawon sati uku kenan, tun da aka basu hutun makaranta rabonsa da ita..
Cike da ɗokin ganinsa Zahrah tace. "Laaa Asad dama zanganka anan? kaida waye kukazo? nidai nida Papa Luv ɗina mukazo, aibansan zamu sameka anan ba da munzo tunda wuri"
Hanu yasanya ya ɗan murɗe bakinta cikin halayyarsu ta yara yace "Baki gajiyawa da Surutu Soul ina Papan naki?" yaƙare maganar yana me baza idanunsa.
"Asad me kakeyi anan, bacemin kayi chocolate zaka ɗauka kazo ba?"
Daga Asad har Zahrah atare suka juya suna kallon mai maganar. Kyakkyawar mace wacce ta amsa sunanta mace mai aji da kamala, sanye take da abaya gown black colour ta yane jikinta da mayafin abayar, komai nata na burgewa ne, kallo ɗaya zaka mata, kakuma son sakewa domin ba irin ƙananan matannan bane, duk da cewa bata da wani jiki, haka kuma bata wani sanja ba, har yanzu tana nan da kyawunta mai fusgar hankali.
"Itace Mamanka?" little Zahrah tafaɗi haka ƙasa ƙasa tana kallon Asad.
Kai Asad ya kaɗa mata alamar "Eh"
Da gudunta ta ƙarasa wajen Momyn Asad ta rungumeta, cikin surutunta daya zame mata sabo tace.
"Oyoyo Mom Asad, dama inataso mu haɗu dake, amma bakya zuwa school ɗinmu, Dad ɗin Asad ne kawai yake zuwa, ni da Asad abokaine sosai, kuma dan Allah kudawo U.S.A kunji, muma kunga can zamu koma" tunda little Zahrah tafara zuba bata tsagaitaba sai yanzu.
Hakanan Zahrah taji yarinyar ta burgeta, durƙusawa tayi agaban yarinyar haɗe da sanya hanu ta shafa fuskarta, hakanan taji bugun zuciyarta ya ƙaru, "Idanunta ne ke mata gizo kokuwa dagaske kamanninta take hangowa akan fuskar yarinyar?" tambayar da tayiwa kanta kenan, cike da son sanin amsa.
Murmushin da Little Zahrah tayiwa Mom Asad ne yayi sanadiyar kusan rugujewar zuciyarta. "ZAID" tafurta sunan acikin maƙoshinta da kuma kan laɓɓanta, sai dai kuma amon sauti baifito ba.
"My Soul"
Taji wata murya dabazata taɓa mantawa da ita ba tafaɗa.
Dagudu Little Zahrah takamo hanun Papa Luv ɗinta dake tsaye.
"Yauwa Papa zokaga Momyn Friend ɗina Asad, wacce nafaɗamaka tana da kirki, tana bawa Asad abun daɗi, shikuma yana bani."
Idanunsa ya sauƙe akan bayan wata mace dake durƙushe a ƙasa tabasa baya, cigaba da jansa little Zahrah tayi harzuwa inda Mom Asad ke durƙushe amma bata ɗago fuskarta ba.
"Momyn Asad, ga Papa Luv ɗina nima, tare dashi mukazo" little Zahrah tafaɗa cike da kauɗi.
Ahankali ta ɗago manya manyan idanunta ta ta kalli mutumin da Zahrah ke cewa shine Papa Luv ɗinta.
Atare bugun zuciyarsu suka tsananta, take wani irin abu ya tsarga jiki da jijiyoyinsu.
Da ƙyar ta'iya daure zuciyarta ta ƙaƙalo murmushi.
Shima murmushin yayi haɗe da sunkuyar da kansa ƙasa.
Hanun Asad ta kama jiki asaɓule ta juya daniyar barin wajen.
"Asad" taji muryar Zaid yaƙira sunan yaron.
Tsayawa sukayi cak amma ita bata juyo garesa ba, takowa yayi har inda suke ya durƙusa haɗe da kamo hanun Asad.
"My dear ya hutu?" yatambayi Asad.
"Lapiya" Asad yabashi amsa yana murmushi.
Kallonta yayi haɗe da cewa "Dama Asad ɗanki ne?"
Kanta kawai ta jinjina masa alamar "Eh" gaba ɗaya ta ƙosa subar wajen shikuma yakama Asad ya riƙe ƙam.
Murmushin dake ƙarawa fuskarsa kyau yayi haɗe da cewa "Fine boy, natayaki murnan samun wannan kyakkyawan yaron, amma kuma saidai inajin tsoron abunda zai faru anan gaba, Asad abokin Zahrah na ne, idan nan gaba yasan nayiwa mahaifiyarsa laifi mai girma yakike tunanin zai ɗauki abun?"
Kanta ta girgiza masa haɗe da ɗanyin murmushi. "Kada kace haka Zaid, abu idan ya wuce yana da kyau amantasa, afuskanci gaba, banafatan Asad yasan abun da ka aikata agareni" ɗan numfasawa tayi tare da kama hanun Asad. "Sauri nake zanwuce gida" kallonta ta mayar ga Little Zahrah da ta ƙura mata idanu tun ɗazu, murmushi Zahrah tayi mata, haɗe da shafa kanta, sosai taji son yarinyar acikin ranta.
"Allah ya albarkaci rayuwarki Rabin raina" Tana faɗan haka taja hanun Asad suka bar wajen.
Saida ta ɓacewa ganinsa kafun yasaki wani murmushi haɗe da cusa duka hannayensa acikin aljihun wandon jeans ɗin dake jikinsa. Little Zahrah ce tataho zuwa garesa haɗe da maƙalewa acikin jikinsa, murya asanyaye tace "Papa dama kasan Mommyn Friend ne?"
Murmushi yakumayi akaro na sau babu adadi, hanunta yakama suma suka bar wajen, batare daya bata amsar tambayar da tayi masa ba.
Tunda suka shiga mota batace da yaronnata ƙalaba, shima baitanka mata ba, domin dama shi hakanan yake ba mutum ne mai son yawan magana ba, yana da miskilanci wani lokaci. Ganin da yayi cewa kamar Momyn nasa na cikin damuwa ne yasanyashi gyara zama haɗe da cewa.
"Momy wani laifi ne Papan Friend yayi miki? naji kamar yace wai bayaso muji ko mu sanine oho"
Harara ta watsa masa, hakan yasashi yin gum da bakinsa, shidama gulmace ke cinsa, da yasani ma da baitambaya ba.
Tana isa gida tasamu Husnah da Areefa matar Asad, sunzo suna jiranta, sam basu sanar da ita zuwansu ba, batayi mamakin ganinsuba kamar yanda tayi mamakin ganin yanda aka sauya mata tsarin falonta, aka mamaye gaba ɗaya falon da decorations masu kyaun gaske, tsayawa tayi tana ƙarewa falon nata kallo.
"Happy Birth Day to you my dear Wife!!!"
muryar Dr.Sadeeq ta karaɗe ilahirin kunnuwanta, kallonta ta maida inda taji muryartasa na fitowa.
Fitowarsa daga ɗaki kenan yasha ado cikin riga da wando na jeans masu matuƙar kyau. Murmushi tasakar masa, gaba ɗaya ita tamanta da cewa yaune birth day ɗinta.
Hanunta yakama suka nufi wani ɗan keɓeɓɓen waje dake cikin falon, sosai aka ƙawata wajen da decoration's mai kyau, kusan suman tsaye tayi alokacin dataga irin hidiman da mijinnata ya shirya mata, manya manyan cake masu kyau da tsada yasa akayi mata har guda uku, ga kayan ciye ciye dana shaye shaye, tsananin farinciki da ƙaunarsa ne suka mamaye zuciyarta, juyawa garesa tayi ta rungumesa, haɗe da cusa kanta acikin ƙirjinsa tana shaƙan daddaɗan ƙamshin jikinsa.
"Thank you so much my lovely husband!!!" tafaɗa cikin sanyi yayinda ƙaunarsa ke ƙara ratsa zuciyarta.
"Babu godiya atsakaninmu My Wife kina da babban matsayi a wajena, keta musamnan ce, inasonki da duka zuciyata!" Dr.Sadeeq yafaɗi haka yana ƙara matseta acikin ƙirjinsa.
Kwantar dakanta tasakeyi ajikinsa cike da ƙaunarsa, haƙiƙa tasamu duk wani abu da takeso, farinciki, soyayya, da kuma zaman lafiya, sosai Doctor ke bata kulawa, bayason ɓacin ranta ko kaɗan, yana ƙaunarta har acikin jininsa, itama kuma tana ƙaunar mijinnata sosai, ayanzu yafiye mata kowa da komai, yabata farinciki haka kuma yabawa iyayenta, yamantar dasu komai na ɓacin rai da talauci, ya wadatasu da komai na rayuwa, bata da wani TAURARO sama da shi, shiɗin na musamman ne arayuwarta, koda sau ɗayane bata taɓa yin danasanin kasantuwarsa amatsayin mijinta ba, ko da kowa aduniya zai juya mata baya, tasan banda Mijinta Haskenta Abun Alfaharinta. Rayuwarta tayi mata daɗi akoda yaushe saidai tace ALHAMDULILLAH..
***
Yana tsaye agaban dressing mirror yayinda little Zahrah ke tsaye agefensa, tana shan chocolate, Afrah ce tashigo cikin ɗakin hanunta ɗauke da kofin coffee wanda take haɗamasa kullum daren duniya.
Miƙo masa kofin coffee ɗin tayi, ya amsa yana murmushi, aje kofin yayi haɗe dasanya hanu ya jawota jikinsa ya rungumeta, bakinsa ya kai dai dai saitin kunnenta, ahankali yace "Inasonki ƴar lukutar matata!"
Dariya Afrah tasanya haɗe da cewa "Nima inasonka ɗan lukutin mijina"
Murmushi kawai yayi haɗe da sanya hanu yashafi kumatunta.
"Nima inasonka Papa na!!" little Zahrah dake tsaye a gefensu tafaɗi haka da ƙarfi.
"SON SO nake miki farincikina, idan babuke acikin rayuwata, to babu wani haske dazan sake gani, Allah yarayamin ke na aurar dake ga miji na gari!!" yafaɗi haka yana dariya, acikin zuciyarsa kuwa, har yau tsananin danasanin yanda halayansa suka kasance a baya yake, yayi danasani sosai, har gobe kuma akan danasani yake, bazai kuma taɓa daina Istigfari ba har ƙarshen rayuwarsa.
Duk da Little Zahrah bata fahimci me maganganunsa ke nufi ba, amma tasan cewa mace da namiji suna aure, domin wancan satin daya wuce ma sunje auren ƙanwar momynta.
Dagudu taƙaraso ta rungumeshi, ƙasa ƙasa tace "Nidai ko zanyi aure bakowa zan auraba sai Friend, aishima yanasona ko Papa?"
Durƙusawa yayi agabanta cike da soyayyarta yace "Yanasonki mana, ai aduniya babu wani wanda zaiƙi me wannan kyakkyawar fuskar, ke ɗin ta musammance My Soul!"
Daɗine yakama Zahrah, sake rungume mahaifinnata tayi, aranta tana ƙara ƙaunar papan nata, domin adunia tasan bayan shi babu wani wanda zaiyi mata irin wannan soyayyar dayakeyi mata a yanzu......
*** *** ***
Duka ahali biyun rayuwarsu ta miƙa komai suna yinshine cikin farinciki da jin daɗi, akowacce rana ta duniya ƙara ƙaunar junansu suke, saidai muce MASHA ALLAH.
*Alhamdulillah anan nakawo ƙarshen labarin SHU'UMIN NAMIJI ina fatan zakuyi aiki da abun dayake dai dai aciki, inda nayi kuskure kuma Allah Ubangiji yayafemin, nagode sosai da sosai masoyana, haƙiƙa kunbani haɗin kai nakuma ji daɗin haka Allah Yabar Ƙauna, waƴanda na ɓatawa rai don Allah kuyi haƙuri, balaifina bane, haka labarin yake, haka kuma ƙaddaran ZAID da ZAHRAH yake, babu wanda ya isa sauya ƙaddaransa.
*Ku ci gaba da bibiyana Insha ALLAH Zakujini da labarai kala kala wanda ina da tabbacin zasuyi muku daɗi, Ina muku SON ƘAUNA!!! Insha ALLAH Ina zuwa muku da wani sabon labarin wanda zai ɗare ma Shu'umin Namiji, ina kuma da tabbacin cewa zaku ji daɗinsa sosai.*
*✔️OTE ME ON WATTPAD*
@fatymasardauna
*8/March/2020*
*Taku Ako da Yaushe*
fatymasardauna
No comments