Jin Dadi Sabo Complete Hausa Novel
[7/22, 1:08 PM] Sis Asma: BISMILLAH
Copy by ZAINAB BUTALAWA
🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
1
Official
By
AsmaBaffa
ALHMDLLH ina Godiya ga Allah da ya bani damar sake rubuta sabon Novel dina JIN DADI SABO. kamar yanda muka fara lfy Allah yasa mu gama lfy tare da masu karatu baki daya.
Ina godiya gareku fans dina makaranta novels dina yan groups.
Jinjina ga masu sharhi kunfi kowa birgeni wlh yanda kuke karantawa kuna bibiyar novels tun daga farko har karshe,ina addua Allah yasa mu Karu da juna, ina fata Allah yasa novel din yayi muku sweet ya fadakar ya kuma nishadantar Ameen.
Masu korafi musamman Wanda basa tsayawa su fara karatu daga farko kawai wajen dadi suke karantawa basu San ma ya novel din yake ba amma kuma akwai kawo korafi sai ka ganar dasu suce ai ba daga farko suka fara ba, Dan Allah inhar ba daga farko kika fara ba karki kawo korafi Sabo da korafi bazai karbu ba😅.nafi son masu bibiya filla filla.
Wajen reply na Sharhi fans a dan kara hakuri ko da zaku ga banyi reply ba ko banga na wata ba na tsallake ayi min afwa,da masu magana ta Pc,masu kira etc duk muyi hakuri da juna pls Sabo da dole sai anyiwa wasu ba dai dai ba.
Idan kunga wani abu da bai dace ba zaku iya gyara min fans tunda dole a kwai kuskuren da masu karatu kadai ne suke ganowa, Sharhi shi ke sawa novel ya tafi dai dai yanda ake so.
Duk wani tnx bana sonsa idan nayi posting a daina rubuta min tnx ko haka👍duk masu tnx bazan musu reply ba,masu sharhi zanyiwa😅.
Ban yarda ayi min Poster na Novel ba, a daina kwatanta min Stars dina ana sa pics.
Sharhi kawai nake bukata banda tnx etc.
Wannan Page din nakune Gaba daya masoyana makaranta Novels dina daku zan fara sabo da kune masu muhimmanci a wajena.
Birnin tarayya Abuja cikin wani katafaren makeken gida na gani na nunawa a Tv, gidane Wanda ya amsa sunansa babu abinda babu cikinsa,ga motoci maka maka iya shan kallonka babu ta kasa da million Goma, Cikin wakeken palon me dauke da kujeru yan gaske ko a gidan shugaban kasa sai haka, wata dattijuwa ce kyakyawa chocolate color amma mai duhu da ganinta kasan hutu, Naira da Jin dadi ya samu gindin zama a jikinta,Kwalliya da iya shiga ta zauna a jikinta hannunta rike da kafceciyar waya tana latsawa tana Jan tsaki kadan tare da karawa a kunnenta,ba sai an fada ba kasan wannan matar gogaggiyar yar boko ce,Cikin murya me dauke da fada tace Alklsm yaushe zaka dawo ne AHLEEF ? Ya kamata kazo ka karbi aikinka kasan na gaji ka bar min komai a hannuna daga cewa zaka je Saudiya da Paris hutawa har yanzu kaki dawowa,Abbanku baya kasar ka Sani, su Suhail kasan basa nan suna US Schl dinsu ba ayi hutu ba, ni kadai ce aikin yayi min yawa ya kamata ka dawo kaci Gaba da rike dukiyarka tafi karfina.
Dariya Ahleef yayi kadan a waya yace Momee zan dawo soon kiyi hakuri,Better cewar Momee gashi Niima ta gama University yanzu kaga sai mu fara shirin bikinku Ko ? Jin an ambaci matar daya fi so a duniya Niima yaji wani farin ciki a ransa ya kusa mallakar Niimarsa wacce yake ganin tafi ko wacce mace a duniya,duk mata mazaje ne a wajensa Sabo da Niima wacce kullum sai sunyi waya yaji muryarta yake iya bacci,Momee ko dan shirin biki ai dole na dawo am sorry Mum,Murmushi ta saki a rayuwarta babu Wanda take kauna sama da Ahleef ko yayanta da ta haifa Bata sonsu kamar yanda take son Ahleef a duniya.
Bayan sun gama waya da Ahleef cewar Next wk zai dawo gida.
Wata yar kyakyawace Chocolate me kyan diri zata kai 25yrs ta shigo Palon Momee tana faman yatsina fuska,sanye take Cikin wasu Arabian wears dark blue riga da skert masu tsada da kyau jakarta ta ajiye gefe tare da zama kusa da Momee,Momee na gaji yau nasha aiki a Office ga Meeting da mukayi sun kai kala uku,Cike da tausayi Momee tace sannu Niima ai haka aikin yake ba sauki,je kiyi wanka kici abinci sai ki samu ki huta Ko, Da sauri ta Mike ta nufi sama abinta,Yar karamar yarinyace ta shigo sanye cikin Uniform na Islamiyya Zata kai 15yrs tun daga waje take cewa Momee na dawo,yar fara ce yarinyar amma ba kar ba tana da dan Duhu kadan amma ba baka bace, Last Born Latifa kenan cewar Momee wuce ki cire Uniform ki kaiwa me muku wanki a wanke,Yess Momee ta wuce da gudu.
Bayan sati guda da zancen Ahleef zai dawo daga Paris Sabo da dokin auren Niima bai canja Date ba,yau Saturday yaune kuma suka tashi da girke girken tarbar babban bakonsu,Niima dai tana Murna itama sosai dan tayi missing kyakyawan saurayinta.
2pm jirginsu ya sauka a Abuja,Momee ce kawai taje tarboshi tace ita kadai zata je, Tare da escort suka jera motoci guda Takwas.
Janye da Trolley dinsa ya fito,Gaba daya kallo ya koma kansa mata da maza Sabo da tsananin kyawunsa hade da iya shiga,ya tsaru iya tsaruwa,Sumarsa kadai abin kallo ce da birgewa,dan gemun nan tare da dan saje kadan sai sheki sukeyi suna walwali,Fatarsa kadai abin birgewa ce sai ka rantse yanzu aka fito dashi daga cikin engine,ba sai an fadama ba kasan Naira da Hutu tare da Jin dadi Sun ratsashi,sanye yake Cikin kana nan kaya White and Grey color kamshin dadinsa gaba daya ya mamaye Airport din, Dogo ne Amma ba can ba, shi ba me kiba ba sannan ba siriri ba, idonsa dara dara suna lumshewa, fuskarsa tana da dan tsayi kuma tana da dan fadi normal, hancinsa dogo dan lcib baiyi tsini da yawa ba,bakinsa dan karami jajir dashi yana shining,Fatarsa fara ce amma ba irin kal kal ba,wata iri ce ta birgewa shi ba farin dan Africa ba, ba na larabawa ba kuma na bature ba,haka sumarsa ma take Unique ce kamar ruwa biyu haka yake,babu Wanda zai ganshi bai kara kallonshi ba ko maza ne bare mata,tafiyarsa kamar basarake ta maza masu ji da kansu sai shegen Iyayi a cikinsa da gani ba sai an fada ma ba, bazai wuce 31yrs ba yana ji da kuruciya a cikin lokacinsa yake,tun Kafin ya karasa Momee take zuba murmushin Jin dadi danta da tafi so fiye da yayanta na cikinta ya dawo kusa da ita,da sauri ya karaso tare da rungume Momee yana murna itama haka,Cike da ladabi ya gaisheta sai shagwaba yake mata yana narke mata gwanin sha'awa itama tana lallabashi.Momee tace Son lets go nafi so kaci abinci ka huta,cikin muryarsa me dadin gaske me tafiya da zuciyar yan mata cike da iyayi yace Sorry Mum muje,da kansa ya bude mata ta shiga shi kuma Escort suka bude masa ya zauna gefen Momee,suna gaishe shi yana amsa musu da sakin fuska ba wulakanci,Direct gida suka wuce,Latifa da Niima kawai fadawa sukayi jikinsa suna ta tsalle da murna,da kyar momee ta koresu daga jikinsa,shima da yake Shu'umi ne sai ya jawo budurwa r tasa Niima ya rungume kam a jikinsa,ba karamin kyau tayi masa ba,ga wani kamshi da takeyi,Yaji Albarkatun kirjinta male male bisa kirjinsa lokacin Momee ta shiga kitchen,ya wani lumshe ido yace uhmmmmm wannan mene haka kamar jinjirin mage Sabo da laushi,itama Niima tace dashen Allah kenan ni kaina ina ji dasu,dariya yayi ba karamin kyau dariyar tayi masa ba kamar kar ya daina,hakoransa kanana jere suka bayya,yace to maza San min kafin Momee ta fito yana wani shagwaba,Zatayi magana kenan sai Ji sukayi Momee tace ku kuma mene haka? Ban son iskanci ku kiyayeni fa, da sauri Niima ta gudu Bedroom dinta,shi kuma yace Momee Bari nayi wanka nazo naci me dadi kinsan I missed ur food.
Asalin Ahleef
ALHAJI AHMAD SALEES(ALHJ AMADU) Dan asalin kasar Niger ne,tun asalinsu kaf danginsu talakawa futuk, Amadu shi kadai iyayensa suka haifa a duniya, Bayan Amadu ya cika 25yrs iyayensa suka rasu Gaba daya sakamakon hatsarin mota sai yan uwa dangi,sanadin talauci yasa kusan zumuncin ma ba ayi da juna kowa yana bige bigen neman kudi,Amadu duk yafi su zumunci da hakuri tare da tawakali gashi da addini,hakan noma kawai yake danyi dashi yake ci yake sha,watarana yana gona ya hadu da SAUDAT wacce a yanzu take Hajiya Saudatu, yar asalin larabawan libiyace kyakyawa ce ta gasken gaske,fada ne na yan taadda ya barke a kasar tasu sukayi gudun Hijira zuwa Niger,Saudat kaf danginta an kashesu a yakin da akayi a kasarsu ita kadai ce ta tsira ta shige cikin Yan Hijira zuwa Niger,tunda tazo Niger take cikin gari a titi sai wanke wanke da shara da takeyi a wani gida ana biyanta,da haka take rufawa kanta asiri tana wannan gantalin Allah ya hada ta da Amadu a Gona,nan yaji sonta ya kamashi har ya kai ga yi mata magana,tas ta bashi labarinta na rayuwa kuma ya tausaya mata,tun daga ranar suka fara soyayya kullum suna haduwa a gona.
watansu biyu da haduwa ya sanarwa danginsa ya samu mata,sune suka tallafa akayi masa komai cikin talauci sosai akayi bikin,yan unguwar haka suka dinga surutu Amadu ya auri balarabiya yar gudun hijira ba a San asalinta ba etc,cikin bakin talauci na karshe suke Zaune lfy sai uwar soyayya da suke zubawa.
Sun kwashe kimanin shekaru goma sha biyar tare amma basu samu haihuwa ba, tun suna sa rai har suka hakura gashi basu da kudin zuwa asibiti ko maganin gargajiya haka suke ta addua.
Saudat sarkin hakuri, watarana tana zaune makociyarsu ta shigo tare da kawo mata Maganin sanyi Infection na gargajiya, tace Saudatu ga maganin sanyi ba a son mace ta zauna Bata shan maganin sanyi lokaci zuwa lokaci,Godiya tayi tare da karba,wata uku tayi tana amfani da maganin cikin ikon Allah sai ga Saudat da ciki murna ba a magana,har cikin ya cika wata tara ta haifi danta namiji kato kyakyawan gaske ajin karshe,ko ina zuwa akeyi kallon jaririn Sabo da kyansa,ranar suna yaro yaci suna Ahleef,Ko hakikar suna ba a yanka masa ba Sabo da talauci,bayan wata uku da haihuwa talauci ya kara zurfafa musu sai kawai sukayi shawara cewar gwara su koma Nigeria da zama garin kasuwanci ko Allah zai sa su samu aikin yi,basu tsaya ko ina ba sai Nigeria Cikin Kaduna state.
Cikin ikon Allah wani hamshakin me kudi ya dauki Amadu gadi a bakin gate tare da bashi daki da toilet a gidan yace ya kawo iyalinsa su zauna tare,Zama yayi zama Sun kusa shekara lokacin watan Ahleef bakwai Me kudin ya biyawa Saudatu da Amadu aikin hajji tare da jaririnsu,sannan ya siya musu katon rago aka yankawa jariri Ahleef na Hakika, bayan sun Dawo da wata biyu lokacin Ahleef ya cika 1yrs Allah yayiwa me gidan da suke aiki rasuwa,bayan rabon gado gidan ya tarwatse Gaba daya yaran Alhaji suka koresu gida ya zama na gado, Shine silar barin gidan gaba daya basu San inda suka nufa ba,ruwa,iska,rana sanyi duk ya kare a kansu har Allah yasa wani mutumi ya gansu ya tausaya ya basu wani dan karamin daki dake a kofar gida kamar na maza,anan suka raba suna zama, Ahj Amadu ya koma dako a kasuwa ita kuma tana wanki da guga.
watarana ta bar Ahleef a Daki ta shiga wani gida karbo ashana zata hura wuta a waje ma suke girki kowa a titi yana kallonsu,kuma bandaki daya suke shiga da wasu kartin maza samari hakan ma tausaya musu sukayi ganin basu da inda zasu shiga idan shiga bayi ya kamasu,Allah yasa Saudat me tsananin tsafta ce kullum toilet din samarin a wanke kal ita take wanke musu kuma suna jin dadi.
Tana shiga karbo ashana ashe wasu samari masu satar yara suna siyarwa matsafa suna fakonta a unguwar su biyu,jira dama suke su samu dama, Ranar ba kowa a layin kawai suka fada dakin tare da fesawa yaron Powder ta bacci suka sakashi cikin towel tare da fita da gudu suka fada motarsu sai birnin tarayya Abuja dama abinda ya kawosu Unguwar kenan.
Saudat tana fitowa neman duniya Bata ga Ahleef ba haka ta haukace Ko ina tana tambaya mutane Sun tausaya mata,Shi kanshi Amadu Kuka wiwi ya dinga yi da yaji cewar dansa da suka fi so a duniya an sace shi, Kullum cikin kunci suke gashi Saudat ta nace ita tasan danta yana raye,kuma idan an sace yara Kudu ake kaisu dan haka ita wai dole sai Sun bar arewa,haka ya lallabata ta hakura har suka kara samun wani ya dauki Amadu yake kula da flowers na gidansa,part guda ya basu suke zama lfy, har suka kwashe shekaru ashirin da biyar a gidan,Sai me gidan ya fara neman Saudatu yana so yayi lalata da ita ganinta kyakyawar gaske tafi matarsa,Amadu yana Jin labari ba yanda Amadu ya iya haka ya kwashi matarsa har zuwa Abuja City, Cikin sa'a kwanansu uku da zuwa suka samu wani attajiri Alhaji Dauda ya daukesu aikin gadi a gidansa, ita kuma Saudat zata dinga yiwa yaransu wanki, kaf iyalan Alhaji Dauda basu da tarbiya bare mutunci,shi kadai ne me dama dama, boysquaters ya basu a nan suke zaune,cin mutunci iri iri ake musu a gidan haka suke hakuri,ganin haka yasa Saudat ta fara Soya doya da kwai a bakin wata yar kasuwa kusa da wani katon mall na kece raini,Idan tayi wankin da takeyi da yamma sai ta tafi wajen sana'ar soya doyarta,dake ta iya sai take samun kudi sosai har masu kudi suna tsayawa su siya Sabo da tayi mugun iyawa kalarta daban ce kowa yaci sai ya kara,ta tsare mutuncinta normal.
Rayuwa kullum ja take dake dama basu samu haihuwa da wuri ba,Har aka kwashe shekaru 5yrs yanzu kenan yayinda Idan An hada da shekarun tun haihuwar Ahleef shekaru 31 kenan,har yau dansu Ahleef na ransu suna fatan ganinsa nan gaba, yanzu Idan kaga Ahleef kaga iyayensa baza kace su suka haifeshi ba, Sabo da Sun tsunfa Sun manyanta sai ka rantse kakaninsa ne tunda dama sai da suka manyanta sannan suka samu haihuwa,gasu kuma kullum a wahala suke da gwagwarmayar rayuwa shiko Ahleef yana cikin daula.
Bayan barayin Sun sace Ahleef suna ta sheka gudu a hanyar Abuja sojoji suna tsaida motoci ana dubawa Cikin sa'a aka kamasu tare da fito dasu su biyu daga motar,jaririn yana hannunsu suka fara dukan barayi tare da tambaya ina suka samoshi,Daya cikinsu sojojin yana rubuta komai a littafi,Cikin barayin suka ce wlh satoshi mukayi dama sana'ar muce mu Sato yara muna siyarwa da Matsafa, Wannan yaron ma sunansa Ahleef mun dade muna bibiyarsu har muka samu nasara,sunan yaron Ahleef min San iyayensa....kafin y'a karasa daya abokin satarsa ya rada masa Mu gudu fa daji,ba tare da tunani ba suka arce da uban gudu da niyyar su boye a daji,Sojoji suka fara Harbinsu ta ko ina nan take duk suka zube kasa matattu.
Bayan komai ya kammala suka dauki Jariri da sa hannun Gomnati aka fara cigiyar iyayensa a kafafe na Media Amma ba a dace ba yaro Ahleef har ya kwashe 1mnth a gidan raino.
Abba Alhaji Sulaiman Yahaya da Matarsa Hajiya Amina Momee Asalin yan Nasarawa lafiya ne gaba daya har Momee danginsu Suna can duk da cewa suna zumunci sosai da danginsu duk da cewa iyayensu Sun rasu tuni dama amma Momee Babanta yana raye can garinsu,suna yawan kai masa ziyara tunda sunyi sunyi ya dawo Abuja yaki.
Momee da Abba mutanen kirki ne masu hakuri ga tausayi,tunda sukayi aure Allah bai basu haihuwa ba har suka kwashe 8yrs haka,shine Momee ta bawa Abba shawara yaron Ahleef da suka gani a tv ana neman iyayensa ba a samu ba ita tana so suje ta karbi rainonsa yaron ya Bata tausayi gashi kuma Allah bai Bata Haihuwa ba, nan Abba ya Amince da sa hannun Gomnati aka basu yaro tunda anyi cigiya a Media iri iri amma Allah bai sa an samu iyayen jariri Ahleef ba.
Su Momee
Cikin so da Gata hade da Amana suka rike Ahleef,Momee bayan Ahleef ya cika shekara 6. Momee ta samu ciki ta haifi yarta Niima kyakyawa,Ahleef lokacin yana primary schl ta masu kudi,bayan 3yrs Momee ta Haifi yan biyu Salman da Suhail,Ahleef secondary schl da university gaba daya a London yayi su, cikin gata ya karanta Harkar kasuwanci har sai da ya gama Masters ya dawo Nigeria,Lokacin Sun shaku da Niima tana University amma a Nigeria tayi,Ita kuma Niima Bata wani son Ahleef Sabo da gani takeyi iyayenta sunfi sonsa kuma ba su suka haifeshi ba, sai take kishi da bakin ciki Sabo da Momee tafi sonsa Abba ma haka,su kuwa su Salman ba ruwansu suna kaunarsa kamar dan uwansu na jini,Dama tun Ahleef yana yaro su Momee basu boye masa ba yasan komai shi ba dansu bane.
Bayan Shekaru masu yawa Momee ta haifi autarta Latifa wacce yanzu take 14 to 15yrs,Ahleef yana gama secondary schl Abba ya bashi jari da Company har biyu kyauta tare da sa hannun lauyoyi da yan uwansa Sabo da halin rayuwa tunda yasan Bashi da gadonsa shi yasa ya bashi tun yana da rai.
yana juya Kudin da kula da Companies Kafin kace me sai ga Allah ya bunkasa abin ya zama Me dukiya na sosai yayi suna a duniya har yafi Daddy ma kudin,suma su Salman suna fara university aka basu nasu harkar,Niima ma haka,Momee ma haka,kowa a gidan da nasa na kansa yake amfani babu Wanda ya dogara da na wani sai Latifa yarinya,Duk gidan yan boko ne Abba kuwa dan Boko ne dan kasuwa kuma dan siyasa Wanda ya rike mukamai da dama manya yanzu haka shine Sakataran Gomnati na kasa baki daya,gidane Na Tarbiya basu da wata matsala har soyayya tayi zafi tsakanin Ahleef da Niima wacce ake tunanin aurensu kwanan nan.
Ahleef Yana da addini ga ilmi,bashi da wata matsala sai watarana yana da raini sama sama,ga Gadara da takama kuma yana fama da iyayi etc bashi da abokin da ya wuce Farhan,Farhan shima namiji ne kyakyawa halayyarsu daya da Ahleef yana da haske amma ba can ba,yafi Ahleef fara'a kawai,tun suna yara tare suka taso iyayensu masu kudi ne suma su Farhan, amma shi Lawyer ne.
ci gaban labari
Ahleef Zaune yake saman 3seater dake katafaren palon Momee suna hira sama sama,sai ga Niima ta shigo a fakaice ta watsawa Ahleef harara tana zaginsa a ranta dan Iska ya gama mallake musu iyaye,har ya zama shine me kudin ma, Inshaallah sai na jefashi a bakin cikin da zai bar gidanmu baki daya shege komai nasa me kyau kamar aljani to wlh duk kyansa bazan ji kaunarsa ba tunda ya mallake mana iyaye sunfi sonsa akan kowa.
Ahleef kuwa bai san ma tanayi ba, sai da Momee tace zauna mana kin tsaya masa a kai kamar me tunani,Ahleef cike da murna, wani sanyi ya mamaye masa zuciya ga Son Niima yana karuwa masa kullum,hannun ta ya jawo zauna yan mata ki huta,sannu,ya Office yana lallabata,ita kam aranta haushi kamar ya kashe ta,a fili kuma sai zuba murmushi takeyi.
Wata kyakyawar Budurwace yar 16yrs fara kwal kwal ga kyau kamar ita tayi kanta,komai nata ya kai karshe,duk inda kake neman kyakyawa ta karshe to kazo wajen wannan yar matashiya,dan lips dinta Pink shine abin birgewa, Girar nan me yawa, ga gashi yalo yalo ya kwanto a gaban goshinta har wani saje ne da ita yabi ta kasan kunnenta kadan,hancinta me kyau amma baiyi tsini da yawa ba,idonta dara dara masu kyau, abinda yafi tafiya da Imanin mutane shine Dirinta kyan sura ga Hips kamar an zana mata shi.
Faduwa tayi a kasa ta saki kuka me karfi tana shure shure da Burburwa,Wata Dattijuwa kyakyawa Ce cikin kidimewa tare da firgici tace Shukura? Budurwar tayi banza da mahaifiyar Tata taci Gaba da kukanta,Shukurata tashi zo ki fada min waye ya taba min ke ? Nan ma Shukura tayi mata banza sai kuka take,sai da tayi kukanta ta koshi sannan ta turo baki cike da shagwaba tace Inna.... Ba...ba.. Aishalle bace take min yanga akan ta siyo Tsire tana ci ni kuma baki bani Kudin na siya ba, Da sauri Inna ta Mike jikinta na rawa kamar uwarta ce tayi magana,Dari biyar ta dauko ta mikawa Shukura gashi maza yi shuru ki siyo kema kice,sai lokacin ta goge hawayenta kamar yarinyar yaye sannan ta saki murmushi tayi waje da sauri.
Misalin 15mnt Shakura ta dawo da tsirenta ta nemi waje can gefen rumfar dake gidan nan ta kwalawa Babatar kira Innaaa.....Inn...kafin ta rufe baki har Inna ta fito tana sauri,Shukura tace cike da Shagwaba Inna yi min fifita,Ba musu Inna ta fara yi mata fifita da mufici tana sannu ci a Hankali karki kone,Harshenta ta zaro waje tare da cewa yaji Inna fifita min Harshena,Inna tana murmushi tana kallon yarta abar kaunarta gashi tana fifita Harshe, Innaa.... Ruwa ki bani nasha, a randa ta ebo mata me sanyi,Inna bani abaki,ai kuwa ta Bata a baki ta sha,Dankwalinta ta cire ta jefar dashi,gashinta baki me santsi ya zubo a kafadarta Bata da tsayin gashi me yawa amma baza a kirata marar gashi ba, Bayan Inna ta gama mata komai ta koma tana aikinta sai ko Shukura tace Innaa... Zanyi wanka ruwan wankan ki dafa min, katuwar Budurwa amma kome sai an mata lafiyayya kuma,Baffanta ne ya dawo daga kiwon shanu,Da Shukura yayi arba nan ya fadada fara'arsa yace Autata ta kaina banga kin cakare ba ga Yamma lis tayi,tana Shagwaba tace Baffa sannu da zuwa,Inna nake jira ta kai min ruwan wankan, Da Sauri Baffa yace a kyale tuwon daren nan dan Allah azo a kula da yata yaran gari fes banda Yata,Inna ta fito ta hada ruwan wanka ta kai mata bayi,Bayan ta fito daga wanka ta shirya fes,tuwon dare ma tana ci ana mata fifita ko Inna ta Bata a baki taci Bata fiye cin abinci da kanta ba, Ko tsinke Bata daukewa a gidan kuma ta iya ko zata yi sai Inna tace a'a zata Bata jikinta,Idan Baffa yaga tana aiki to sai ya kwana ya yini yana masifa.
yau ma shukura ce ta nace sai ta dakawa Inna kayan miya,ta fara tana ta yi Sai Baffa ya kwada sallama,ganin Shukura na daka da masifa ya karasa shugowa haba Haba kashinta kike so ya karye ko kashi kike so ki buda mata, yarinya kamar Shukura nawa take da za a barta tayi daka,Inna tace nima bana son takeyi nayi nayi taki yarda,Shukura tace Inna na gaji zo ki karasa abinki dama idan da Sun kyaleta ma indai Shukurace sau biyu ma zata daka tace baza ta iya ba.
wacece Shukura ?labarin Auren Iyayen Shukura yayi kama dana Iyayen Ahleef nan gaba za muji.
AsmaBaffa
[7/22, 1:08 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
2
Official
By
AsmaBaffa
Dan Jin dadin AsmaBaffa fans club and Duk Inda ta Fadi Fans.
Washe gari da safe Shukura tana ganin Innarta tana aiki amma ko tsinke baza ta tayata daukewa ba sai dai komai ma ayi mata,sai lallaba ta akeyi ta shirya ta tafi makaranta amma taki sai wasa takeyi gata da kokari amma bata maida hankali,Baffanta yana da burin tayi karatu amma taki yarda sam,har coper yake dauko mata tana mata lesson ana biyansu kudi har ta fara jin dan turancinta ta koreta tace zarnin fitsari arniyar takeyi bata tsarki,tana ss3 ta kusa gama secondary schl dinta duk makarantar babu me kokarinta amma babu me wasa kamarta da tsokana ga Kuka da shagwaba sabo da gata yayi mata yawa sabo da haka ma mutane da yawa Yar Gata suke ce mata,gata da kyau amma duk kyan nan babu wanda ya taba cewa yana Sonta a duniya ko a kauye kowa gani yake tafi karfinsa,ga shegen kyau ga Shagwaba Da tabara kowa tsoronta yake ji,yan mata kawayenta har addua suke mata Allah ya kawo sanadin da wata ko wani zata ketawa Shukura mutunci wanda zai karya duk wani abinda take ji dashi,samarin Garin ma har Meeting suke hadawa a boye za a samu wasu mazaje suyiwa Shukura fyade sabo da su kawo karshenta suna mata hassada,babanta duk garin babu me kudi da dukiyarsa gata ya daya tilo har birni ake kai Shukura tana cin kayan dadi.
Alhj Umaru shine Mahaifin Shukura,Iyayensa sun haifi yara da yawa amma cikin ikon Allah duk sai sun Zama samari da yan mata suke rasuwa,Har Iyayensu suma suka rasu tun Umaru na matashi,sai yan Uwa da yayan yan Uwa,Umaru ne kadai Allah ya rayashi har ya girma ya gaji dukiyar Iyayensa na dabbobi shanu da Tumaki,kaf rigar fulanin dake can wani daji yankin Plateu Jos,wajen tafiya kiwo a nan ya hadu da Matar da ya Aura Haj Bilkisu wacce a daji suka hadu fada ya barke tsakanin arnan Jos da musulmi an harbe kowa nata ita kuma Allah ya taimaketa ta hadu da Umaru ya kaita rigarsu wajen yan Uwansa daga nan suka fara soyayya ya auri Bilkisu,tare ya biya musu aikin Hajji suka je yafi sau biyar, daga nan Allah yasa ta samu ciki ta Haifi yarta Mace zukekiyar gaske ranar suna taci Shukura,wacce ita kadai suka Haifa a duniya ga rashin iyaye da yan uwa sabo da wannan sai suka dauki son duniya suka tattara shi kan yarsu Tilo Shukura,tun tana yarinya haka ta taso komai tace shi za ayi mata,yanzu zai siyar da shanu ayi mata abinda take so,makaranta kuwa a kauyen da ba yanda zaiyi ne amma da Birni yace zai kaita Private amma basa son yarsu tayi nisa dasu wani abu ya sameta,shi yasa ya barta a ta garin Kauye sai yake dauko mata Igbo cikin masu Nysc ana mata lesson yana biya yana so yarsa ta iya turanci,aiko dake makarantar kauye ba karatu haka Shukura da taimakon lesson ta iya karatun Hausa da rubutu ta iya rubutun turanci sama sama kuma tana dan ji bada yawa ba,sai ta Zama kaf garin babu kamarta,ko baki akayi ma'aikatan Gomnati Shukura ake kira tana jagorantarsu wajen karatu da rubutu,yayin da take zuba shagwaba da tabara ga sangarta harda tayi yawa,kowa bata raga masa bata da kunya ko kadan komai girmanka ba ruwanta sabo da iyayenta basa mata fada sai abinda take so,iyakaci suce bari Shukura ko Allah ya kiyaye gaba,ko Allah kyauta,bata cas bata as,sai umarni ma da take bawa iyayenta kamar ita ta haifosu komai direct zatace Inna tashi ki min kaza,Baffa yi kaza kuma ba musu jiki na rawa zasuyi mata sabo da kaunarta da sukeyi,Shukura tana da kirki idan taga dama sai ka dauka wata me hankali ce,gata da fara'a yanzu ta wangale baki,indai ba shagwabar ce ta motsa mata ba to bata fushi a duniya,zai wahala ka gane fushinta ko ranta ya baci,duk aikin da Inna keyi Shukura tana gani kuma duk ta iya kawai yi ne baza tayi ba ta saba da hutu,Haka ga son jin dadi,bata fiye cin abincin gidan ba sai Nama,kifi,yogourt da sauran kayan dadi su take ci ko nawa ne iyayenta bata sukeyi wasa take da kudi a kauyen,gata da kyauta yanzu idan kuna mutunci zata baka kudi ko kayan sawa,Sabo da Babanta Sutura sosai suke mata kusan kayanta ma duk na Saudiyya ne sabo da iyayenta kusan duk shekara sai sunje Makkah kuma da Shukura ake tafiya tun tana shekara 10 ake zuwa Makkah da ita,gashi ta cika 18 zuwanta Makkah sau 7,shi yasa ta dan waye ba laifi baza kace daga kauye take ba,bata fiye sa Atamfa ba duk kayanta na kasar waje ne kana na da dogayen riguna masu kyau ,yanzu idan Shukura taga dama sai tace Baffa a kaini Birni zanyi Kallo kallo da gudu zai ajiye duk abinda yakeyi su tafi cikin garin Jos har Mall yake kaita iri iri sabo da Umaru ba bagidaje bane shi sam yasan ta duniya,Haka suke shiga Mall suyi kauyancinsu su fito,idan taga dama tace Aje Kano,katsina,kaduna kusan da yawa state din Nigeria Shukura taje ta cikin birni yawon bude ido Abuja ce yanzu burinta,so take Baffa ya kaita yace sai babbar Sallah tazo zasu je tana ta murna bata da buri sama da taje Abuja shine next target nata,A birni idan taga abu bata San sunanshi ba sai taga dan gayu na gaske ko yar gayu ta karshe sai ta tambayesu dan Allah ya sunan wannan?idan an fada mata tace mene Amfaninsa?a fada mata tace da turanci fa? Nan ma a fada mata haka takeyi a birni bata shuru da bakinta komai sai ta tambaya amma indai kai ba dan gayu bane to ko kallonka baza tayi ba kawai ita baka waye ba kuma ba dan birni bane,idan kuwa ka sake ta tambayeka baka Fada ba zaka ci masifa da jaraba ga gori kayi magana ta tara mutane sabo Da Kuka zata sa ta fara shure shure shi kanshi Baffa da kyar yake lallashinta,Baffa ma Har mall idan zasu shiga da sandarsa yake shiga ta kiwon shanu ayi ta musu dariya amma ko a jikinsu, wannan kenan.
Baffa ne zaune kusa da Inna yace Inna ya kamata kema ki shirya Wannan lokacin mu tafi dake sabo da tafiya ta taso min zuwa birni cikin Kano zan tafi da Shukura tayi kallo Kallo kema ya dace ki bude idonki,Tsalle Shukura ta shiga bugawa tana Murna zata je Kano wannan zai Zama zuwanta na biyu kenan Kano,tace Baffa zamu je Shopirayit wai (ShopRite) take nufi,Baffa yayi dariya yana jin dadi Shukuransa tana farin ciki yace Yar Shopirayit din bantan uba Saura muje ki damu mutanen birni,dariya sukayi gaba daya tace Ai Allah sai na tambayi yan gayu sun fada min Sunan jakin Baban gida da turanci,dama na dade ina so na tambayi sunan Jakin Baban gida da turanci ban sani ba aiko wlh wannan lokacin sai na tambayi yan Birni,Baffa yana dariya yace ai da kin bari sai munje Abuja birnin tarayya sai ki tambaya a nan ai sunfi yan gayu,sunfi ilmi ga boko,da sauri tayi tafi ai wlh Kano ma sai sun sani, kuturin uba kai kaga wasu yan gayu Inna baki gani ba yanda suke tafiya kwas kwas,baku ga wani Namiji ba Allah dana ganshi fatarsa santsinta yasin kamar na Gansa kuka sulub sulub.
Dariya sukayi gaba daya Shukura tace cab Inna kinga wani da muka gani yana cin Nama a bakin titi suna Shan lemo a tasha cikin tashar Unguwa Uku ai kadanba Sumarsu tayi Ukun takan Baba Sumar nan da kake tarawa kaima ashe Baffa kaima dan gayu ne hhh sukayi dariya,Shukura tunaninta Sumar Baffa ma ta yan gayu yake tarawa bata San irin kauyencin yan Fulani bane wacce suke tarawa duguzum ba gyara,haka kuma da taga wasu a birni a tasha yan iskan tasha ne masu sa mutane a mota amma dake na kauye daban da taga na birni sai ta gansu yan gayu ne ma bata San yan jagaliya bane hh,yan Wiwi ma kuwa,wanda kuma take cewa me santsin fata Wani ne kawai fari amma ba wani dan gayu bane kawai dai yayi dan wankansa.
Yau asabar yau tun safe suka shirya tafiya Kano Baffa an siyar da shanu za aje birni harda Kudin dan karamin Hotel da zasu kama daki daya su Uku dama haka yakeyi Su Baffa an waye.
Baffa anci rawani kamar dagaci ga Sanda katuwa,Inna kuwa duk Wanda ya ganta zai rantse mahaukaciya ce sabon Kamu a haka kuma taci gayu,Ita kuwa Shukura ansa doguwar riga Baka ta makkah katuwa da ita amma ko gyale bata yafa ba dankwali kawai ta daura a kanta sai faman kalle kalle takeyi,ana mota tuni Inna bacci ya kwasheta,Baffa ma haka,Shukura kuwa taki bacci wai kallon Hanya takeyi har aka zo kano sai da ta bawa mutanen motar dariya yanda ta zura hannunta ta window tana nuna Abu da yatsa,Inna tana bacci taji Shukura ta daketa a baya tas Inna tashi...tashi...ki Sha kallo,kin gani ...laaaa....Baffa...kalli...wan can zuwan Wallahi babu wannan,na rantse da Allah ba wannan abin,ikon Allah...laaaaaaaa...kaga Baffa.... Inna...kalli katon gida,Baffa yace Shashasha Banki ne wajen ajiyar kudi,Kudine a ciki mu shiga Baffa muyi kallo,ana jin Shukura ta rafka Salati kunga tallan Sabulu,Fati Muhammad ce yar Film gata a sabulu shi yasa ta kara fari nima sai na siyi irinsa,nan ma ta kalli katon Symbol Wallahi ga Sani Danja ta karanta tace An rubuta Glo yeeee tallan layi yakeyi na waya yasin na gane.
Driver da conductor ana ta dariya har suka sauka ta cika motar ita kadai, kyan Shukura yasa duk inda suka ratsa sai hankalin alumma ya dawo kansu ana kallon kyawunta. Shukura ta gigice,ana sauka a tasha sai taga wani Zabiya fari marar kyau,duk kuda na binsa,jikinsa yayi wani rodi rodi,ga Hakoransa yellow,hanci kato muni iya muni,ta kalli Zabiya (albino) ta kara kalonsa ta sheke da dariya kowa ya fara kallonta a tashar,hankalin kowa ya dawo kanta amma ko a jikinta,tana ta dariya sai kuma ta kalli Zabiya ta rufe idonta tare da cewa wayyo...Allah ni bazan so wannan ba,Baffa ai wlh gwara a yoni baka kamar bayan tukunyar Inna akan na Zama irin wannan,ashe farin ma akwai na muni,me za aci da kai ta furta tana kallon Zabiya,jikinka kamar nama ga kuda sai Binka yakeyi,Inna tace Allah kyauta miki,yo Allah na tuba ko Aishalle karshen muni a garinmu me zatayi da kai,zabiya dai bai kulata ba,tace anji kunya ana birni ba a goge baki da Brush,kalli hakora na farare wulluuuuuu...ta ware masa hakora,ai ko aka dinga dariya ana Shan kallo sai Baffa ne ya fisgi Hannunta suka tafi tare da hawa Napep,tana shiga Napep tace ko ni sai na iya tuka wannan yar motar,jibeta yar karama,me Napep ya tsaya daukan wata katuwar mata nan Shukura ta saka rigima ita ba wanda zai shigar musu wannan katuwar ta dannemu a ciki,Baffa da Inna sabo da sai abinda Shukura tace aiko suka ce baza a dauki wata ba Shukura bata so,Me napep yace sai kun kara min kudi fa,Shukura karaf tace kaine matsiyaci kaje ruga kaga shanunmu da awaki ehe.Mai Napep ya mata banza har suka isa Hotel ya saukesu,Baffa ya shiga da kansa ya kama musu daki daya tal su Uku,Baffa yace su shigo dama Shukura ta saba tun a Hanya ta cire takalminta sabo da karta bata musu Hotel gani takeyi kamar gida Ne,Inna ma ganin Shukura tayi haka itama sai ta zare takalmanta suka fara tafiya sadaf Sadaf kamar Barayi ka rantse wani Glass suke takawa a hankali.
Inna ta Rafka magana ganin alhazawa da mata masu kudi suna Hutawa tace gafaranku dai bayin Allah, Shukura wayayya tace ke Inna nan fa Kamar Makkah ne bakya ganin wajen me kyau, nan Inna ta kwala sallama da takalminsu a hannu,shuru ba Wanda ya kulasu,Shukura tace sai kinyi kalkala Inna irin na larabawa yan gayu, Shukura ta makale murya tayi Sallama aiko mutanen wajen suka sheke da Dariya tunaninsu almajirai ne suka zo bara har Hotel, Baffa yazo ya Fara Fada haba Haba Bilki kamar baki waye ba Ashe zuwa Makkah da kuke na banza Ne,Nan suka bishi har dakin da aka Kama, Shukura tace wlh kamar a Madina Baffa ta furta tare da fadawa gado tana shan AC.
Shukura ta fara shagwaba wanka Inna Baffa wanka zanyi,Haka suka rude suna lallashinta kowa ya shiga yayi wanka tare da Sallah.
Baffa yace to Alhmdllh amma baza muci abincin nan ba yayi tsada, Karaf Shukura tace ni kosai zanci da doya da kwai, Inna tace a siyomin Biredi da fanke me sugar.
Baffa ya fita ya siyo musu shi Kuma ya siyo gurasa da kuli, Bayan sunci sun koshi sai suka bazama kallon gari,wannan haske kamar a Makkah Cewar Inna,sai cikin dare suka koma masaukinsu,Inna da Baffa a kasa sukayi shimfida,Shukura kuma ita kadai a saman Bed sabo da gata.
washe gari Baffa yaje inda zai ga mutanen da zai gani dama shine dalilin zuwansa kano,Bayan ya dawo suka kuma bazama cikin gari yawo sune har countryMall,Shukura taga kofa wacce ake turawa ta Glass sai ta fara knocking Kwan... Kwan... Salamuakaikum a bude,ku bude min,a bude.sai da Ma'aikatan suka zo suka bude Mata,bayan sun gama yawonsu kaf tare da siyayya sai kawai Baffa ya Manta sunan Hotel da Address,suna ta shan wahala a cikin napep sai Baffa yace Shukura Dan ubanki baki rike Sunan ba?ke da kike yar Boko, Inna tace wlh kuwa kai mun gaji,baki Shukura ta turo yo Kai Baffa ni ina zan sani,kaine fa ka kawo mu,me Napep yace ya gaji shi tafiya zaiyi,nan ya saukesu ya kara gaba,Su Baffa dai bakinsu Kamar zai cire sabo da tambayar Hotel, Shukura ta zabura ta tare wani me Taxi yana tsayawa tace Dan Allah tambaya nake,yace ina ji,dan Allah malam kasan wani Otel me kyau jikinsa duk fulawoyi? Da bene sannan ga kamshi,yana ta kyalli...shuru tsagal Inna tace yaro da Kwan lantarki a ciki,harda Tv,Me taxi ya fara dariya ya gansu daga daji suke yayi mamaki ma da suke zancen Hotel shi bai gane ba yayi tafiyarsa.
Su Baffa sai a gindin wata bishiya suka kwana, Gari na wayewa sai Baffa ya tuna Sunan Hotel din,nan suka shiga Napep suka Koma suna zuwa sukayi wanka suka shirya suka fito da kayansu sai Tasha, Suka shiga mota sai kauyensu suna ta murna sunzo birni sunga Gari cikin mota sai ciye ciye suke.Shukura ta damu mutane da surutu har suka isa kauyensu lfy.
Kwance yake saman cinyar Momee shima Ahleef kusan irin Shukura ne yana son sa wani aiki yana kwance yana hutawa amma shi sai dai kannensa ba Manya ko iyayensa ba, in banda tunanin masoyiyarsa Niima ba abinda yakeyi son da yakewa Niima ko rabinsa Niima bata son Ahleef haka,sabo da shakuwa da kyau ga kudi shine yasa take son Ahleef sosai ba wai tayi zurfi bane, Shi kuwa Bashi da wacce ta fita a duniya.
Niima ce ta shigo daga aiki ta Dawo ido suka hada da Ahleef masoyinta ya kashe mata ido daya tare da furta sannu kamar bazaiyi magana ba,hannu ta daga masa tana zuba masa murmushinta me tafiya da zuciyarsa,sai kallonsa takeyi a ranta Tana jinjina kyau,kyan diri da kyan sura irin na Ahleef,a ranta ta ayyana dadin da zaiyi on bed take duk da cewa bata taba bin maza ba amma Tana kwadayin Ahleef wanda shi kuwa Son Niima yake tsakani da Allah ba Dan komai nata ba.
Muryarsa taji a nutse yace 5pm ki shirya zaki rakani gidan su Farhan,ok tace Tana fari da ido.
Misalin 5 na yamma taci uban wanka kamar a saceta cikin wani lace maroon color,
Hannunsa ta rike yasha azabar kyau kamar wankin engine haka yake tafiyarsa kamar wani Gomna,hannunsu rike cike da so kamar a sace su,Bayan sunje gidansu Farhan yawo suka wuce na shakatawa,Suna zaune suna shan Ice-cream sai ga wani frnd dinsa yazo zai wuce nan Ahleef ya Mike ya tafi wajensa suna tafawa suna Hira,Niima tana latsa waya sai ga motocin Gomna zuga guda sun shigo da Alama Meeting suka zo yi Abuja,Niima ta gigice kamar bakuwar kudi bayan gidansu ma sunfi Gomna kudi, sai gyara Riga takeyi tana karairaya,Ido hudu sukayi da Gomna tare da Manyan masu kudi da suke kusa da Gomna,tasan Gomna ne amma bata San Gomnan wanne state bane,Gomna shima yaga me Kyau yawunsa ya tsinke,ba bata lokaci yayiwa yaronsa magana,sai gashi Cikin Guard wani ya kawo mata card na Gomna yace gashi Inji me Girma Gomnan Taraba State Exelency Muhammad Aliyos,fit Niima ta cafke Card tare da jefawa a jaka tare da furta tnx, guard da sauri ya koma cikin tawagar Gomna,Niima kuwa wani Farin ciki da girman kai ne ya mamayeta lallai ta cika me kyau da farin jini har Gomna guda binta sukeyi, tace ahaf har wani kudi ne damu,ai kudin yan siyasa sune kudi kullum shigowa suke ta ko ina kamar banza,duk da Babana shima yana siyasa ai ba kamar Gomna ba kai zan yashi dollars fa zanyi abinda naga dama,tana wannan maganganun zucin kawai Ahleef ya dawo cikin takunsa ko ina ka duba kallonsa akeyi maza da mata,ita Kanta Niima a ranta tace Allah ya zuba baiwa a nan.
Ahleef kashe mata ido daya yayi yana murmushi sai wani lallaba ta yake yana mata shagwaba sai ta fara biye masa sai ta tuno samarinta yan siyasa masu kudi ciki harda Gomna Aliyos.
AsmaBaffa
[7/22, 1:09 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
3
Official
By
AsmaBaffa
Naku ne Fans na ko ina.
Hannun Niima ya kamo yana kare mata kallo,wani yarr taji a jikinta shima haka a hankali yace I love u Niima dan Allah ki rikeni amana karki barni duk da nasan bani da wani Asali iyayenku sune gata na dan Allah karki kyaleni ki taimaka min ta wannan hanyar kadai zan iya sakawa da Momee da alkhairi tare da Abba shine na aureki ina matukar Sonki Niima,hankalin Niima ne ya Tashi gaskiya ita yanzu bata son auren nan idan tayi aure shike nan Namiji daya tal zata dinga kulawa mijinta,ba samari duk masu kudin nan baza ta kula kowa ba, a hankali tace ina sonka nima ai baka da matsala Dani,Murna ta kamashi yace yanzu dai na fadawa Abba a sa mana Rana ko? Uhm Kawai tace tana wasi wasi a ranta,sai kallonsa takeyi kamar mayya ,Kalli mijinki da kyau Babyna,kunya ce ta kamata ta mike tsaye tare da cewa tashi mu tafi Hearty.
Soyayya sosai take nunawa Ahleef bata nuna masa akwai matsala,shi kuma ya gama sakin jiki da ita sai kashe mata kudi yakeyi sosai,so iya so tare da kulawa yake nuna mata,ita kuwa bata wani caring dinsa amma tana nuna tana sonsa,sai wahala yake a kanta,Har Abba ya dawo sukayi shawara da Momee suka yanke hukunci,nan Abba ya nemo danginsa Maza da mata,tare dana Momee suka yanke ranar aure nan da 4mnths,Wasu a dangi suna ta gulma za a aurawa Niima Marar asali Dan gidan raino dan tsuntuwa,Niima munafuka a gaban dangi sai ta zauna tare dasu a dasa gulmar Ahleef da ita, tace sam ita bata sonsa Abba da Momee ne suke so nanfa Zance ya zaga dangi ai auren dole za ayi mata Ahleef kadai ke sonta sabo da yaci dukiyarsu sabo da yasan bashi da gado,Haka Niima tabi itama kawayenta tana fada musu sai tsinewa Ahleef akeyi shi kuma bawan Allah bai san komai ba murna kawai yakeyi kamar me, Momee da Abba ma murna Sukeyi Sosai.
Shukura zaune take gefen Inna dake dama fura,Shukura tace Inna Sosa min bayana,Inna ta jawota tare da kwantar da ita a cinyarta kamar jaririya ta fara sosa mata baya,ita kuma tana Inna nan nan,Tana kwance tace Inna miko min Plate din can na cinye awarata,Inna ta dauko mata,sai da ta cinye sannan tace Bari nayi wanki Inna, Inna tace wanki? A'a kwanta ki huta zan wanke miki su,Shukura tace Allah bar min ke Inna, Tana kwance Inna taje ta wanke mata kaya tas, da yamma Inna na aikin tuwo Shukura tace kawo nayi miki tankade Inna, a'a Shukura zaki bata kayanki zauna ki Huta abinki,Shukura kuwa ta fice yawonta cikin kauyen.
Tun safe Shukura yau da period ta tashi tana shan wahalar ciwon Mara Dama idan tanayi Sai kuka takeyi harda shagwaba ma abin nata,Inna kuwa harda kuka tana tausayin yarta,Baffa kam yau ko kiwon shanu bai fita ba sha lele ba lfy,sun rufu a kanta sai addua suke mata har ta samu bacci ya kwasheta,da yamma kuwa ta tashi sosai taji sauki har ta fito Tana wanke kayan da Jinin ya bata tare da panties dinta,bayan ta wanke tace Inna...zo ki karba ki shanya minsu,da sauri ta karba ta shanya mata Kuwa,Baffa ne ya shigo da sauri ya manta ma da wata Sallama so yake yaji jikin Shukuransa.
Shukura tana so ta fadawa Baffa Pad dinta ta kare dama ita take zuwa cikin gari can jikin wani asibiti ta siyo abarta Sabo da kauye ma basu wani santa sosai ba Da tsumma suke kunzugu,sai tace Baffa kaje bakin asibiti kace a baka Biredin mata,Baffa ya washe baki ahh lallai sauki ya samu Shukurere ta har Biredi zaki ci,wanne kala?,murmushi Shukura tayi tace Baffa a bakin asibitin Ishu kawai ake samo shi,kace biredin mata zasu baka haka ake fada a kauyen,Baffa harda tuntube wajen sauri yana zuwa kuwa yace a bashi biredin Mata aka bashi ya biya kudin duk tunanin Baffa wani Bread ne Me dadi a ciki,ya kawo mata gashi Shukurere ta aci da yawa kinji tace to Baffa,yace wannan katon Bread ai sai da lemo Shukura, Inna tace kayi sauri ka siyo mata Maltina tunda tafi Sonta,nan ma jikin Baffa na rawa ya siyo mata Maltina me sanyi yace tasha da biredinta.
Sosai suke ji da Shukura gata sai wanda ta gani,kullum haka take a rayuwarta cikin gata da jin dadi sabo da haka kuma mutanen kauyen sai suka tsaneta sosai kowa burinsa ya zaiga Shukura ta tozarta ta wulakanta amma ba dama Allah ya riga ya bata masu hassada sai kallo.
Ahleef tare da Farhan suna garden sai shirye shiryen biki sukeyi sosai ganin saura 2mnths bikin sai matsowa yakeyi, Ahleef ya Kalli Farhan cike da iyayinsa da ya saba yace Man ina ganin Matsala a wajen Niima abin yana damuna,na tambayeta ko da matsala tace a'a,murmushi Farhan yayi shima da Iyayi yace kai dai tsoro Kake ji so yayi maka yawa,hmm baza ka gane ba sam ba caring yanzu wani shareni takeyi na rasa me nayi Mata gaisuwa ma yanzu sai taga dama,bata ma so mu hadu,kasan fa mata haka sukewa ango idan za ayi musu aure haushin angon suke ji,pls ka daina damuwa tunda har itace ta Amince idan bata sonka baza ta yarda ba, Kai wace ta isa taganka tace bata so ko baturiya yace ai tayi karya,Ahleef yayi murmushi yace haka Momee ma tace dana fada mata amma wlh kaji na rantse da matsala a wajen yarinyar nan sai dai kawai Addua.
suna zaune saiko ga Niima tazo tana tafka uban Selfie ita da kawayenta su biyu ta Kalli su Farhan shekeke tare da galla musu harara,sai suka matsa gefe kawayenta suna yaushe zamuje Government House dinne? Tace munyi waya execelency na yace Next wk yana nemana,sannan jibi Senator dina zaizo gida wajena ban San ya zanyi da wannan angon nawa ba, dariya yan matan sukayi tare da cewa ai ba a daura ba bare ya Hanaki kula wasu shegen angon naki sai shegen iyayi ga rainin hankali dan kawai yana da kyau da kudi, daya a ciki tace Niima Allah yayi Miki baiwa da miji kamar Ahleef amma kina so ki cuci bawan Allah,Niima ta turo baki tare da cewa ke kin san dai nima kyakyawa ce ga farin jini idan ma yatafi dubu zasu zo min mutimin da ba'a san asalinsa ba har wani kyansa za a gani,idan kuma kudi ne ga Manyan kusoshin Gomnati nan duk ina dasu kuma nima ina da kudin haka ubana Ma.
Su kansu kawayenta sunga haukar Niima tare da butulci.
Niima haka kullum burinta ta dinga gulmar Ahleef Tana aibatashi tana zaginsa cikin mutane har zancen ya Fara dawowa kunnen Momee amma tayi shuru taga gudun ruwan Niima yarta.
Shiko Ango kullum yabon Amaryarsa yakeyi sonta na karuwa a ransa kullum yana manne wajen Abba da Momee suna shawarar biki.
Kwanaki na ja biki saura 1wks ango ba zama Amarya kullum cikin bakin ciki take bata shirya aure ba za a tauye mata rayuwa,yanzu idan ta yarda da auren shike nan Alhazawanta sai mijinta kawai.
Shukura kwance take cikin dare Tana ta kwasar baccinta taji kamar hayaniya a hankali ta bude idonta ta kunna torchlight kenan taji ashar da zage zage,ai sai ta kashe torch ta leka ta window nan take ta hangame baki tare da fara Hawaye taga Baffanta da Innarta an dauresu ga wasu jibga jibgan arna sunkai su 15 dauke da bindigu,Baffa taga sun kafe da mari,da sauri ta bude kofa ta fito da gudu Tana kuka tana rokonsu su bar mata Baffanta itama mari suka zuba mata nan take ta sume sharaf a kasa Inna ta fasa Ihu sabo da rashin Imani wani yasa wuka yayi mata yankan rago,Baffa ya rafka salati tare da dafe zuciyarsa nan ya fadi matacce zuciyarsa ta buga.
Arnan dariya suka dinga Yi ta mugaye sannan suka kada shanu da dabbobin Baffa kaf suka tafi dasu,a garin basu kadai ba har sauran fulani da dama wasu an kashe su an tafi da dabbobinsu, Tunda Shukura ta suma bata farfado ba sai da gari yayi haske lokacin Mutane sun cika gidan taf,da kuka hade da salati ta farka Tana Ihun Baffa...Inna.... Wayyo...nan tayi arba da gawarwakin Inna da Baffa sai ta haukace gaba daya tana birgima da ihu tana na Shiga uku ina zan sa kaina na huta,gatana ya kare Inna... Baffa sambatu takeyi Kala kala sai da kowa ya tausaya mata harda masu kuka gaba daya ta haukace bata san inda kanta yake ba, har akayiwa Inna da Baffa sutura tare da kaisu makwancinsu ana ta zaman makoki,Shukura kuwa suman ta yafi sau goma tana farfadowa kamar zata sheka lahira,sai maza ne suka riketa aka shiga yi mata addua tare da Kiran Nasuru me Chemist yayi mata allurar bacci ya sa mata Drip nan bacci ya kwasheta,bata farka ba sai dare Ta dora daga inda ta tsaya ana mata nasiha amma abanza cewa take ni bazan Hakura ba, in Allah ya yarda kuma sai iyayenku sun mutu Allah yasa babanku da babarku su mutu suma,bazan ba kowa hakuri ba sabo da nima bazan hakura ba.
wata tsohuwa tukuf ta shigo gaisuwa gidan Shukura wacce ta gama rama sallolinta Tana kuka ta Kalli tsohuwar tace ai gwara da wannan ce ta mutu tunda ta tsufa bata da amfani mene amfaninki,wata ma cikin dangin Baffa na sallama tace ga wannan Ma shekara nawa kullum cuta takeyi ai da ita ta mutu,matar tace Allah sarki yar nan kowa na can ne lokaci nane baiyi ba.
Wasu yan mata su biyu sunzo gaisuwa Zaraf shukura tace ga Baban wannan Ma shanyashi ake a Rana sai an kwantar sai an tayar mene amfaninsa Ai ni wlh iyayena sunfi na kowa Amfani, ana mutuwa amma mutuwar su Baffa ta musamman ce..ba shiri Nasuru me Chemist yazo ya kara dannawa Shukura allurar bacci da Drip, bata farka ba sai washe gari,ba laifi ta dan dawo hankalinta amma sai taji masu zaman makoki dangin Baffa suna lissafa mutanen da arnan suka kashe a garin,nan Sai ko akaji Shukura ta kece da dariya tace Alhmdllh uban kowa ya mutu wlh tunda ubana ya mutu uwar kowa ta mutu tunda na rasa tawa,yanzu har Dantani Baban Aishalle ya mutu?kai Alhmdllh amma Allah na gode maka,yawwa gwara Kowa iyayensa su mutu duk mu zama daya,ai wlh bazan Kara jimamin mutuwa ba, Ni mutum ya sake yace min ubansa ko uwarsa ta rasu sai dai aga ina nishadi wlh.
Wani ne ya rafka sallama tare da cewa bayin Allah Ashe arnan Jos har rigar yan jalo suka je sunyi kashe kashe da yawa yafi na wannan kauyen namu,ayyiriri nanaye akaji Shukura tace yawwa su dandana suma suji Me naji.
Kwana uku kullum sai anyiwa Shukura Allurar bacci bata ci bata sha sai an mata Jan Ido har akayi Bakwai.
Kullum Shukura bata daina kuka tana Tuna iyayenta zata fashe da kuka,haka har aka kwashe 40days Dan abinda Baffa da Inna suka mallaka aka siyar gaba daya har gidan da Shukura ke ciki,dangin Baffa dama tunda akayi bakwai suka tafi da Shukura gidansu,haka aka raba gado yanda Allah yace aka bawa shukura kudi dubu Dari biyar kasancewar Kauye ne filaye da gonaki basa tsada,Shukura ba kunya ta karbe kudinta a ledar Viva tana kukan su Baffa.
nan ta samu Kudin nan ta Fara dagargazar dadi,ba irin shawarar da yan Uwa basu ba shukura ba yanda zatayi da kudinta ta Samu ci gaba amma tace a'a Sabo Da tun farko bata da mafadi sai abinda taga dama take yi ba a sata ba a hanata, gashi bata daukan ko tsinke a gidan dama sun San halinta ganin maraicin da take ciki suke daga mata kafa,ga shegen iyayi wajenta, kudinta ta sasu gaba tayi kyauta taci dadi,yauma da Yamma liss taga wani katon zabuwa Tana yawo tace nawa wannan Zanbon Goggo ko na uban waye zan siya a siyar min shi,Goggo ta tabe baki tare da cewa nawa ne kuma ni dubu biyu zan siyar,nan ta zaro 2k ta biya tasa yara suka Kama mata shi aka yanka Sabo da Kiwa ma wata budurwa ta bawa tace gyara naman nan ki soya min Zan baki Dari biyar,jiki na Rawa budurwa ta Karbe tayi yanda take so, ta karba tare da figawa mutanen gidan nasu sabo da bata da rowa,zama Tayi da Maltinarta a gefe tana ci tana kora Maltina sai kuma ta fashe da kuka ta tuno Baffanta da Inna yanda watarana ma abincin a baki suke bata ana lallabata taci,haka takeyi kullum barnar kudi ga Dunkuna tana faman yi iri Iri har shopping taje cikin garin Jos ta siyo cosmetics da turaruka masu kyau,abinda kawai take birge mutane dashi addini ne da ita sosai bata wasa da addini.
A kwana a tashi Dangin Baffa suka takura su ta ishesu tayi girma da yawa dole sai tayi aure ko su bata duk wanda suka ga dama,ita kuma tace ba wanda ya isa yayi mata dole,su kuma Suka ce baza ta ja musu abin kunya ba sai dai ta bar musu gida baza su iya da halinta ba, Kawunta ta samu tace Kawu kasan bana Zance bani da saurayi kuma ina so na cikawa Baffa burinsa na zuwa abuja nayi kallo kallo.
Takaici ya kama Kawu kawai ya jawo sanda ya fara zane Shukura Yana Karuwanci zaki shiga tsinanniya,sai da ya farfasa mata jiki abinda iyayenta ko zagi basu taba yi Mata ba, haka suka bi suka tsaneta a gidan da sauran dangi bata da ikon magana sai duka kuma yanzu aiki ake sata sosai a gidan kamar jaka lallai taga maraici, ko wanke wanke idan tayi To ranar da zazzabi zata kwana bata saba ba,Kwatsam sai Kawu sukayi shawara a junansu suka zabowa Shukura miji wani Me kiwon Shanu Halilu,Halilu Dan shaye shaye ga neman mata kaf garin an sanshi,Shukura bata da labari sai da bikinta ya rage saura 1wk taji ana kiranta da Amarya tana tambaya taji a garin ana ta mata dariya anga karshen iyayi da jin dadi.
Kukan Maraici Tayi tana tuna so da gatan da iyayenta ke nuna mata amma ga yanda ta koma dare daya,ragowar kudinta ta duba saura Dubu Saba'in kacal Duk ta kashesu a siyi banza siyi Wofi Trolley dinta ta jawo ta shirya kayanta a ciki kaf sauran da bata so ta barsu,Handbag dinta ta zuba kayan kwalliyarta ciki tare da kudinta ta shirya tsab,sai da ta Bari an shiga masallaci sallar asuba ta sadada cikin duhu ta bar Garin bata tsaya ko ina ba sai garin Jos ta zarce Tasha inda zata shiga motar Abuja,a Tashar tayi sallar asuba da Asuba,ta dauko Toothpaste dinta da Brush tayi da ruwa pure water,a tashar ta siyi kosai da biredi tare da shayi hadin kauri taci ta koshi sannan ta wanke fuskarta da sabulunta harda shafa powder da jan baki sama Sama,ji tayi Driver yana cewa shigo yan mata zamu wuce,da sauri ta shiga ta zauna mota ta tashi sai Abuja.
Bikin Ahleef saura kwana uku ango ba zama Sun gama gayyatar abokai,ba abinda ba a gama ba na shiri,sun narkar da kudi,Abba yana sama a dakinsa yaji ance yazo ga manyan danginsa sunzo Maza biyu da mata biyu,ya fito Sun gaisa kenan sai ga yayan Momee da kaninta tare da yayarta,abin ya basu mamaki,bayan an gaisa anci ansha,suka ce abinda yake tafe damu ba komai bane sai akan auren Niima,Gaskiya bamuji dadi ba Sam da ilminku da komai zakuyi mata auren dole,jiya taje mana Tana kuka ita bata so auren dole za ayi mata,Abba ne ya dakatar dasu yace ku bari Niima tazo shima Ahleef yazo, Nan Momee ta Kirasu a waya,5mnt dukkansu suka zo, Momee tace gata nan gashi kuji daga bakinsu,Ahleef suka kalla kai kaine da kanka kake son Niima tsakani da Allah?da Sauri Ahleef yace ae,Niima kefa?kinje kin Kai mana kukanki yanzu maimaita a gaban kowa,ai kuwa ba tsoro Niima tace uhmm... Ahmm..Ina sonsa amma bada aure ba,ni ban shirya aure ba, kuma ni bana...Mari taji Abba ya kifa mata shi,Tana kuka tace wlh ni bana son aurensa,Abba Hawaye suka gangaro masa,Momee kam dama zancen ya dade da zuwa kunnenta,a hankali tace Baban Suhail kyaleta,ai dai kin tabbatar bakya sonsa ko? Niima tace ae,Abba yace ni zaki wulakanta sai ki fada mana sabo da me? Tana kuka tace bashi da asali wa ya sani ko shege ne,Momee Kuka kawai take shekawa, Abba yana Jin haka yace Ahleef kayi tawakali kayi hakuri,Allah zai baka wacce ta fita,ke kuma baza muyi miki baki ba amma ki sani sai kinyi nadama,yan Uwansa ya kalla yace na gode kuje kawai,jiki ba kwari suka tafi,itama Niima ranta Fari kal ta koma dakinta tana bugawa samari da yanmata frnds nata waya Tana Murna suma haka.
shiko Ahleef ya mike kenan ya yanke jiki ya fadi kasa sumamme,
Momee da Abba da gudu sukayi kansa ana kiran Driver duk abinda za ayi masa anyi bai farfado ba da taimakon yan aiki aka kwasheshi zuwa Hospital,Private Hospital suka tafi amma duk likitoci sunyi iya yinsu sun kasa dawo dashi yaki farfadowa,Kwana daya bai farfado ba,Momee tare da Farhan ne ke kula dashi sai Abba dake sintiri,Kwana biyu bai farfado ba har dare yayi Momee ta damke hannunsa tana zubar da hawaye Tana masa addua cikin ikon Allah sai ya fara motsi,Momee ta rungumeshi tana Murna tare da godiya ga Allah, kamar ba Namiji ba taga yana Kuka sosai,Ahleef Momee ta kira sunansa,kuka kawai yakeyi Har Farhan ya shigo ya tausawa abokinsa duk dauriyarsa gashi yana kuka akan Mace,Momee ta Tallafo fuskarsa kayi Hakuri Son wlh mu kamar iyayenka ne,karka dauki maganar Niima kasa a ranka kaji na rantse munfi kaunarka fiye da yaran da muka haifa,kuma a yanzu Niima ko tace tana sonka bazan Bari ka aureta ba tunda Tayi Ma haka Allah sai ya baka wacce tafita komai da komai, Har abada Niima tayiwa kanta,kayi tawakali jarabtarkace,Farhan ya dora da cewa Maybe ma ba alkhairi bace a tare da kai shi yasa,kuma Allah zai ma sakayya dama can ba matarka bace,Momee da Farhan tare da Abba haka suka sa Ahleef a gaba da Nasiha iri Iri,Suhail da Salman Ma haka yar auta Latifa ma ba a barta a baya ba, ita kuwa Niima yau kwana 4 kenan suna asibiti amma ko dubiya bata leka ba,Momee da Abba duk sun daina kulata har su Salman.
ganin ba Wanda ke kulata a gidan tace zataje dubiya Momee tace karta soma ganin kafarta,Ahleef Sabo da Nasiha da kula da yake Samu yaji sauki ya dan warware amma ya daina magana da kowa sai ta zama dole baifi a Rana yayi manana sau uku ba, kullim fuska a cinkushe take shi kadai yasan irin kunci da baking cikin da yake ciki.
AsmaBaffa
[7/22, 1:09 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
4
Official
By
AsmaBaffa
Masu sharhi ina godiya wannan page naku Ne.
Tunda aka sallamosu yayi tozali da Niima Sonta ya dawo sabo ciwonsa ya tashi suka kara komawa asibiti,kwana daya aka sallamosu Duk ya kara fari ya rame,Niima sai harkarta takeyi ba ruwanta,Momee killum Nasiha da fada take masa yayi hakuri,Farhan shi ya dinga sanarwa cewa an dage bikin Ahleef sai nan gaba idan an sa Rana za a sanar mutane sunyi mamaki Wanda suka san labarin sun tsinewa Amarya ba adadi.
Ahleef ya zama kamar kurma fuska ba Rahma,Sai kallon hoton Niima kullum aikinsa Kenan,Momee tayi fadan har ta gaji,shima Abba haka,Har Saudiya Momee ta shirya musu ita da Abba tare da Ahleef suka tafi,sai da suka kwashe 3wks suka dawo Alhmdllh Ahleef ya samu afwa har kiba da kyau yayi sosai,sai rashin magana da fara'a ya dawo abin Tsoro,kwarjininsa ya Karu ya maida Hankalinsa wajen aikinsa Kawai,duk ranar da zaiga Niima to sai hankalinsa ya tashi ganin haka yasa Momee tace maza Niima ta shirya ta koma Kaduna wajen yayarta ta zauna kafin wani lokaci,Niima murna tayi zata ji dadin Shanawa da samarinta a can, Zata yi yawonta inda taga dama.
Ahleef ya riga da ya tabbatar bazai taba aure a duniya ba tunda ya rasa wacce yafi so Niima to bashi ba kara kula mata, kullum dare sai ya zubar da hawaye ya kasa hakura da Niima,har aka kwashe 3mnth a haka yake ba canji yana shan wahala.
Shukura ko da ta sauka a Abuja da yamma ta rasa ina zatayi kawai tayi zamanta a tasha a nan taci abinci har dare,sai kallonta akeyi gata da shegen kyau,a tashar nan ta kwana dake Abuja ne ba ruwan wani da wani ba wanda ya kulata,gidan wanka na mata ta shiga ta biya kudi Tayi wankanta Tayi brush tare da shiryawa tsaf ta fito ko vaseline bata shafa ba kaya kawai ta canja taja akwatinta Tayi gaba,tana fitowa gefen Titi taga wasu arnayen motoci guda biyar sun wuce da matsiyacin gudu sai ko daya daga cikin motocin suka kade wani dattijo nan take ya mutu,dattijon da dansa namiji abin tausayi yaron zai Kai 25yrs sai ihun kuka yake yayin da wannan motoci suka gangare gefen titi,mutanen suka fito,Ahleef yana motor dake tsakiya Duk escort dinsa ne,fuska ba rahma ya fito cikin takunsa kamar Sarki, Shukura dake gefe bata da burin da ya wuce taga baban wani ko babar wasu ta mutu sabo da nata Sun rasu,wajen gawar taja akwatinta bakinta har kunne sabo da Murna,yaron yana ta zunduma ihu Yoruba ne ko Hausa baya ji,Shukura ta kutsa ta cikin mutane har gaban yaron ta dinga tuntsira dariya,kowa yana kallonta gashi ko ba Dan Allah ba sai ka Kalli Shukura sabo da kyanta,Ahleef ya kalleta sau daya kirjinsa ya buga,Shukura tace amma Allah yayi muku albarka masu motoci gwara iyayen kowa su mutu a duniya nima nawa Sun mutu.
Kallonta mutane suka fara yi masu Jin Hausa suna Mamaki wasu na dariya, matashin Yoruba ya daura hannu aka yana rusa kuka yana Help me ooooo My Papa,Help me Jesus ,Oh..God Papa....yana ta sambatu Ahleef ya karasa da niyyar taba jikin Wanda suka bige da mota caraf yaji an rike masa Damtse,a fusace ya juyo da mamakinsa sai yaga Shukura ce duk da bai santa ba ya zuba mata Harara,kwarjininsa yasa tayi saurin sadda kanta kasa tana cewa Allah baza ka kaishi asibiti ba sai ya mutu shima tunda ubana ya mutu,Hannunsa ya fisge da karfi har sai da ta kusa faduwa kasa Bata hakura ba ta jawo rigarsa nan ma ya fisgeta yana bawa Guards dinsa Umarni a daukeshi zuwa Hospital,sanan aka kira Police suka shige mota suka bar Shukura da sauran mutane.
Itama akwatinta ta ja tayi gaba abinta ko ina zata je Oho. Ahleef kuwa ya cika da mamakin Irin rashin Imani na Shukura,Sunje Hospital anyi komai tare da Police,wanda ya mutu an kaishi gida tare da Tallafin kudade da kayan abinci,wanda kuma ya kade mutimin ba musulmi bane bare ace azumi ya kamashi.Abba da Momee ma duk sunje Sun kai musu tallafi,Yaron matashin ma Salman ya bashi aiki a Company nasa.
Shukura kuwa Hotels ta dinga zagawa sai da ta samu Me kwana daya dubu goma sha tara a Maitama,cikin gwarancin turancinta ta samu ta kama daki da kyar ma suka barta wai tayi yarinya,cikin dubu sabain dinta,taci abinci na dubu biyar, kamar wacce ta dawo daga kasar waje sai dai ana kallonta daga karkara tazo,kwana uku ta kwashe kudinta suka kare saura 3k Amma sai tace masu Hotel su kara mata 3days zata biya Idan ta shiga bank babu cash a hannunta kullum Bread take fita taci da ruwa ta dawo Hotel,ana haka 3days ta cika, masu Hotel gani suke kudi ne Da Shukura,da safe tayi wanka ta shirya tsaf cikin doguwar Riga silver color,tayi kyau kamar balarabiya kuma yar birni,akwatin kayanta ta ajiye a Room dinta ko Hand back Bata dauka ba sai kudinta dubu biyu ta fito tare da sanarwa ma'aikatan cewar ta tafi bank zata dawo yanzu kayanta har Handbag suna ciki yanzu zata dawo ta biya su.
Ganin har hakorin makka ne da ita guda daya Sun San ma Hajiya ce kuma sunga yanda take wasa da kudi,Shukura tana yin nesa da Hotel din tace ruwa ta sha ta shiga taxi tace ya kaita wani restaurant mutanen wajen dama Sun saba da Shakura tana zuwa tayi musu wasa da kudi farkon zuwanta Abuja da kudinta, suna ganinta suka fara washe baki, Ta zauna duk abinda takeso sai da tasa suka cika mata table da abinci,ta ware ciki taci ta koshi karshe ta duba ta zaro 2k sai ta mayar taja tsaki ta dauko Voter card dinta ta matseta a hannu yanda za a hango kamar Atm card ne sai tace bari naje nan Opposite Bank na ciro kudi just 2k ya rage a hannuna,mutanen duk arna ne musulmi yana musu kwarjini kuma suna ganin masu gaskiya ne most of them kawai suka ce taje ko gobe ma ta kawo,aiko da gwarancinta na turanci tace OK thanks ta fita Bata tsaya komai ba ta mike layin tana tafiya,alhazawa da manyan masu kudi sai kallonta akeyi Sabo da kyau Irin na Shukura,duk motar data wuce sai ta kalleta,Tafiya takeyi tana tunani wai ina zataje ? Ina zata kwana,wata dalleliyar motace tayi slow a gaban Shakura,da sauri ta kalli na cikin motar wani jibgegen Alhaji ne kamar zai fashe sabo da kiba kansa kuma dan karami Horn ya danna mata tare da yafitota tazo,bata San mazan Abuja ba sai ta je tare da gaisheshi tun a nan yasan Bata waye ba kuma bakuwa ce ya samu banza.
yace yan mata shigo muyi magana mana,ba musu ta shiga mota,shiko farin ciki ya kamashi,yace Hajiya na ganki ne kuma naji ina sonki,gaki kin hadu gaskiya kina da kyau irinki nake mafarkin samu,murmushi tayi kawai,yace ina ne gidanku na kaiki can ? Tace nima bakuwa ce kwana nan babanmu yaci dan Majalisar tarayya muka dawo nan da zama amma ni yar kauyen Jos ce fulanin daji,Alhaji dadi ya rufeshi ya samu yar gidan me kudi nan take yace a wanne Hotel zamu hadu ? nan ta gane me Alhajin ke nufi da ita,kawai sai tace karfe 12 na dare ai zaifi Ko ? Yace ashe dai kin gane gaskiya kin hadu ta ko ina.a boye ta maka masa Harara suna hada ido ta saki murmushi,tace hmm Muje kasan layin nan zanje wani Mall zan siyo waya sabuwa,Ki bari mu hadu a Hotel Idan mun gama Jin dadinmu sai na siya miki wacce kike so me tsada,nan taga fa baza ta samu sisi ba sai yayi lalata da ita sai tace to bari na koma gida sai mun hadu ltr, ta fice a motar yana washe baki zaiji dadi yau,sun rabu ya tafi itama ta kara Gaba tafiya take a kafa gashi Bata san ko ina ba a garin kawai tafiya take.
Momee Dalilin abinda Niima tayiwa Ahleef yasa Hawan jini me karfi ya kamata ta fara cuta me tsanani tun tana boyewa har ta kasa motsi gashi lokacin su Salman Sun koma Uk sai Latifa kawai, Ahleef kuma yanzu tunda abin ya faru Sam baya zama sosai a gidan yafi zama a katafaren wani gidansa daban can wata Unguwar da turawa suka fi zama ciki,ba ruwan wani da wani,kamar malaikan mutuwa haka ya koma ba fara'a ba komai ko magana sai ta kama wannan abin ne ya damu Momee har cuta ta kamata,Abba ma Yana Tunusia bai Sani ba boye masa takeyi,Ahleef ne ya shigo da safe gidan yaci uwar wanka Cikin wani yard hadadden gaske dinkin ya masa kyau sai kamshi yake zubawa,ga wani agogo malam abin kallo,Sumar nan tasa kyalli takeyi lips dinsa yana sheki jajur dasu.
Cikin takunsa na kasaita ya shiga bedroom din Momee yana bulbula kamshi,Subhanallah ya furta hangota yayi kwance ta dafe kirji tana tari tare da haki ta rame,da gudu ya karasa kusa da ita bai ma Bata lokacin yin magana ba cak ya dauketa ya sauka kasa cikin sarsarfa escort dinsa suka figi motoci sai wani katafaren asibiti Emergency,likitoci suka rufu kanta har aka samu ta farfado sai aka canja mata daki suka ce dole sai tayi 1wk Ko 2wks kafin a sallameta,Momee tana jin dan sauki tace kar Ahleef ya fadawa kowa sai ta warke,yace to Momee Tawa Allah baki lfy tace Ameen,Tunani yakeyi wacce mace zai dakko wacce zata iya kula masa da Momee.
Shukura yau titi ta yini tana yawo ga yunwa da take cinta,tana zaune jikin wata bishiya a zaune mararta ta murda ta fara ciwo sosai take ciwo da alama Period zata fara,ta Mike a hankali ciwo na cinta Bata kula ba ta tsallaka titi sai mota ta fyallo da gudu saura kadan ta maketa Allah ya taimaketa kadan ta dan bigi Kafarta sai ta fadi can gefe,dalleliyar motar ce tayi parking wani katon arne Igbo ya fito da sauri yaga jini na bin kafafunta tunaninsa motarce ta mata rauni haka bai san period take ba dama kuma ba pad jikinta,a motar ya sata ya figeta tana kuka za'a saceta,bai tsaya ko ina ba sai asibitin da aka kwantar da Momee tasu Ahleef, sai kuwa aka rasa dakin da za a kwantar da Shakura sai dakin da Momee ke ciki suka shiga neman izini tunda daki mutum daya ake bawa.
Ahleef na zaune gefen Momee suka shiga suka nemi izini tunda dakin da aka sa Momee na mutum biyu ne normal, Ahleef yace bai yarda ba, Momee tace Son kyale a taimaketa a kawota ba damuwa.
Shukura kukan Shagwaba kawai takeyi Wanda dama ta saba,jini na bin kafafunta aka turota Saman bed har dakin,duk ta cikawa mutane kunne.
Ahleef Sam bai ganeta ba,amma kamar ya santa amma ya manta a Ina,Momee tace sannu yarinya ko cikine daita tayi barinsa Allah Sarki gata kyakyawa Mashaallah,Likitoci sukace Ahleef ya fita zasuyi aiki yace wlh ba inda zaije me zai gani bayan sunsa wani labile Sun kare yarinyar,suna Jin Kukan Shukura tana kwarototo wayyo....Marata zata belle,meke damunki ? Kina da ciki ne ? Shukura ce tace ni Jinin Haila nakeyi ubanku ne yayi min Cikin ? Ai Dazu wani yace mu hadu a Hotel kuma banje ba wai ni zai yiwa wayo,kara ta kuma kwallawa tace wlh haka zaita zubowa haka yake min duk watan Allah, Innata ma Kafin ta mutu tace nafi wata me haihuwar ma wlh, yiiiii.... Taci Gaba da kuka nurses sai dariya sukeyi Wanda Suke Jin Hausa,Ahleef da Momee suna jinta sai dariya Momee takeyi kasa kasa,Ahleef yana ji ya daure fuska a yana wannan yarinya bata da sirri ta fiye surutu ga kukan tsiya yaja tsaki.
Anzo za ayi mata Allura ta fara tsandara kuka ita bata so,aka canja mata magani nan ma ta fara kuka ita Bata sha, Ahleef ta kaici yasa bai san sanda ya daka mata tsawa ba, Ta Cikin labile taji gaba daya ta firgita,ta kidime da sauri tace to ayi min Allurar,sai anzo za a tsira sai tace wash...ta fara guduwa Momee ce ta dan yiwa Ahleef magana Da ido wai ya kara mata magana,ba Wanda yasan fuskar kowa ta labile taji muryar dazu me shegen dadi amma ba alamar mutunci a cikinta ba shiri tace ayi min zan tsaya, sai da aka gama yi mata komai sukace taje tayi wanka,Igbon daya kadeta shine ya siyo mata doguwar Riga ta wani material me shegen kyau da tsada harda pad da parties kala biyar tunda ya basu,suka ce kwana uku zatayi a asibitin sai kafarta data ji rauni ta warke, kawai yace a bashi Bill zai biya sai da ya biya komai sannan ya samu wata Nurse ya Bata kudi kullum ana siyawa Shukura abinda takeso tana ci har a sallameta kuma su kula da ita sosai,sai ranar da za a Bata sallama zai dawo ya dauketa.
Shukura kuwa Wanka tayi ta shirya kanta ta wanke Wanda ta Bata sannan ta fito wow ba karamin kyau Material din yayi mata ba kamar a saceta,an gyara room din sai kamshi kawai ke tashi,an cire labilen da suka raba tsakaninsu da Momee,nurse ce ta shigo gashi baza ta iya tambaya da turanci ba ina zata shanya kayanta ?
Kawai sai ta kwanta Saman Bed dinta ta fashe da kuka,tana shure shure,Ahleef sai yanzu ya tuna da mutum fa a wancan bed din,Momee tace yan mata lfy ? cikin kuka tace ni ban... Iya...turanci ba...small small nakeji kuma so nake na tambaya wannan Nurse din ina zan shanya kayana nayi nayi na tuna sunan shanya da turanci na kasa,Momee tace to ai ba kuka zakiyi ba Nima na iya ga dana ma, Shukura sai ta Mike zaune tace tsohuwa dake yaushe kika koyi turanci ? Yanzu dama irinku kuna Jin turanci a birni ? Momee tayi dariya tace ae mana, Amma Gwaggo tun Jahiliya ke Babanki wayayyene, Tab niko Inna ta Allah yaji kanta tana dariya ta karasa da wlh kwakwalwarta a dinke aka yi mata ita kamar ansa zare da Allure a dinke ta,Ahleef dariya ta kamashi da kyar ya iya dannewa,Shukura taci gaba yanzu wannan baturen danki ne ? Momee tace ae mana shine yake jinyata,Uhm kawai Shukura tace har ta kwanta ta kara mikewa zaune tace Gwaggo wai dan Allah ya sunan jakin babangida da turanci dama tun Baffa yana da rai nake ta so muzo birni na tambayi yan gayu,Momee tace ke kin cika surutu ki kwanta ki huta Nurse ta kawo miki abinci kici,Shukura tayi dariya tare da cewa dan baku San wace ni ba,kaf garinmu babu kamata,miskila ce ni,shuru shuru bana magana yanzu ma dan ku yan gayu ne kawai shi yasa nake so na karu daku kafin na tafi.
tsaki Ahleef yaja ba shiri ta kwanta tayi luf,nurse da kanta ta shanya mata kayan ta Bayan room dinsu,an kawo mata abinci shinkafa da miya tare da yankan nama biyu, bude abincin Shukura tayi da sauri ta rufe tana ni bazanci wannan ba shinkafa da miya tsura sai gutun nama ina laifin ace da salat ma tare da Ko balangu ne daban Bazan iya cin wannan ba sai ta fara kuka tana da Baffa na yana da rai wlh saniya zai yanka min ma,Momee tace ikon Allah ki dinga hakuri da lamarin duniya tsaya a kawo min abinci sai kici,ba a fi 5mnt ba sai ga Driver me aikin Momee ta aiko da abinci iri iri.
Momee tace taso ki iba, Tana daga kwance tace dan gidan Gwaggo dan zubo min naci dama ta saba bawa iyayenta Umarni,ko kallonta baiyi ba waya yake latsawa,ba shiri ta mike har gaban Momee sannan tace sannu da jiki,Momee tace yawwa ebi ki tafi,nan fa ta fara kici kicin bude Flasks kowanne ta kasa budewa har nishi takeyi Momee tana ta dariya,sai da tayi ta gaji sannan tace kai ni na gaji gaskiya,Momee tasan Ahleef bazai bude mata ba sai tace bari na bude miki,jin Momee zata bawa kanta aiki kawai sai yace kwanta Momee ya fisgi flask daya ya bude,ya bude sauran ma wani kamshi ya daki hancinta,Shukura tace zanci wlh na gode,ta dauki plate ta ebi farfesu,ta ebi naman cikin miyar,sai ta ebi chips duk wani abin dadi shi ta iba, karshe ta kalli shinkafar fara ta zaro mata ido tare da cewa ke yar gidan kowa ce me za aci da ke in banda kisa mutum basir Bazan taba ibanki ba,Macaroni ma ta kalleshi tace ga kayan dadi wa yake ta kai me za aci da kai da wasu kofofinka kamar na hancin mutum.
Momee ta fara dariya, Ahleef a ransa yace wannan kawai yar iskar kauyece yana dariya a ransa, ita kuwa ko rufe flaks din batayi ba ta koma gefen gadonta ta fara ci, Ahleef cikin Isa yace wa zai rufe miki Flasks din ? Dan mitsitsin lips dinta ta turo zata yi kuka tsawa ya buga mata Idan kika Sani magana...kafin ya karasa har ta diro gaban kayan ta fara rufewa daya bayan daya da kyar, Momee tace Bata da lfy fa kana takura mata Son,Momee bari naje na dawo,ok kaini bakin toilet sai ka tafi,bayan ya kai momee tayi fitsari ya kara riketa ya kwantar da ita Saman Bed sannan ya fice abinsa.Shukura tana gama cin abincinta ta kwanta sai bacci ya kwasheta me karfi.
Bata tashi ba sai Cikin dare karfe 11pm tana bude ido Momee ta hango tana sallah saman sallaya Ahleef yana gefe saman Bed yaci uban wanka Cikin 3qtr da yar armless yana karanta jarida ya harde kafa daya kan daya,Shukura a ranta cewa take gaskiya ya hadu Ban taba ganin irinsa ba a duniya,a hankali ta Mike Bata Sani ba garin bacci pad ta goce ta Bata kayanta kadan Ahleef yana gani ya runtse idonsa yana Jan tsaki an kawo musu kazama daki a haka gata kamar me tsafta,sai da ta shiga toilet ta fara takaici Allah yasa dai dan Gwaggo bai gani ba, sai da ta gyara kanta tsaf ta fito tare da cewa Gwaggo dan san min turarenki,murmushi momee tayi ta mika mata kala uku ta shafa,Mikewa Ahleef yayi tare da cewa bari naje na kawo miki abincin zan aiko a kawo miki,Momee tace ga Shukura taji sauki tunda siyo min zakayi kuje tare Idan kun dawo sai ka Bata ta kawo, da sauri yace no Momee pls wannan kazamar ? Bata rai Momee tayi kawai da sauri yace am sorry Momee ke zo mu tafi,Shukura ta tsaya kallonsu suna birgeta yace kazama i'm talking to u da sauri ya fita cike da gadara,tabi bayansa da gudu gudu sauri sauri,jikin wata rantsatsiyar mota ta hangoshi ya bude side din Driver yashiga yau ba Escort da sauri cike da kauyanci ta zaga itama ta rasa ina zata bude kawai ta finciki murfin mota kamar zata balle shi, da kyar da kokawa ta bude gaban motar ta shige shima ya shiga yana dariyar kauyancinta a ransa yace mace har mace haka.
kalle kalle takeyi Ko gyale dama Bata dashi dan siririn dankwalin doguwar rigarta ta daura a kanta tare da zamge kanta da mayafin.
gudu yake sharawa a titi kamar zai tashi sama da ita,gidansa da yafi zama yanzu ciki ya fara zuwa ko kallonta baiyi ba taga ya fice ya barta a motar,tana ta karanta Address din gidan dake Manne a jiki har sai da ta haddace su tas,sai gashi ya fito da Latifa tana rike a hannunsa,ta shiga Baya sannan yaja motar suka tafi,Latifa akwai raina yan kauye,tace Yaya wannan budurwarka ce ? Tana da kyau sosai sai dai yar kauyece,bakin ciki ya kama Shukura,Latifa tace ai yarinyace ma wlh da kadan zata girmeni,daga wanne kauyen kike ? Shukura bata San Sanda ta juya da sauri ta zubawa Latifa rankwashi a kai tare da cewa dan uwarki sa'arki ce ni ? Latifa zafin rankwashi yasa ta shako Shukura ta baya,Shukura ta juya sosai suka fara kokawa suna doke doke da zage zage,Wani uban birki Ahleef ya taka kuuuu sai da suka tsorata ya buga musu tsawa sannan suka dawo normal,Shukura tace wlh duk ranar dana kamaki sai na lakada miki duka. Tsaki yaja yaci Gaga da Driving da sauri yayi parking a wani katafaren wurin cin abinci yayi take away,har cikin asibitin ya kaisu sannan ya mikawa Shukura ledojin Yana zuba mata uwar harara,karba tayi kawai zata kaiwa Momee,Latifa tana so taje ta duba jikin Momee amma ba yanda ta iya ya hanata wai gida zai maidata tunda Bata Jin magana tana ji tana gani sai hakura tayi,lokacin tuni Shukura ta wuce cikin Hospital din amma ta manta Hanyar da zata mayar da ita dakinsu,sai zaga Hospital takeyi tana duru duru sai faman bude rooms takeyi na mutane sai da Allah ya kawo wata nurse sannan ta dinga masifa marar lafiya da fita yawo ba tare da an sallameta ba haka dai ta nuna mata dakin nasu ta shige tana kunkuni.
AsmaBaffa
[7/22, 1:11 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
5
Official
By
AsmaBaffa
AsmaBaffa fans club Page dinku ne.
Da sallama Shukura ta shiga tace mun dawo tare da ajiyewa Momee ledojin a gabanta da Ladabi,Momee tana kallonta dauke da murmushi a fuskar ta,ta mikawa Shukura nata itama ta fara cin nata,Shukura dadin girki yasa ta fara surutu iri iri tana yiwa Momee tana shan dariya har suka gama ci amma momee na mamaki dangin Shukura basu zo ba kuma Igbo ne ya kawota sannan taga yarinyar ko a jikinta harkokinta takeyi, tayi niyyar tambayarta ina danginta sai ta fasa kawai ta share komai.Shukura i tace yau ta dinga taimakawa Momee idan zata je toilet momee tana sa mata albarka da godiya.
Washe gari da safe 8am sai ga Ahleef tare da Latifa wacce take sanye cikin Uniform da alama schl zata je, yau Ahleef ba karamin kyau yayi ba cikin shadda Grey sai sheki yakeyi ko kallon side din shukura baiyi ba ya gaisar da momee sannan ya ajiye mata abinci iri iri, Momee tace Allah yayi maka albarka Ahleef,Shukura a ranta tace Ahleef wannan sunan yan gayu ne, Latifa sai yanzu ta kula da Shukura hararar juna sukayi ko wanne ya dauke kai,Ahleef Jan Hannun Latifa yayi kinyi fa late lets go malama,Momee suka yiwa sallama suka wuce,yau kwanan Shukura Uku yau ne kuma za a sallameta maimakon murna sai ta fara bakin ciki yanzu Idan ta bar asibitin a ina zata ci abinci har ta samu wurin kwana,Lulluba tayi kawai take ta faman kuka a hankali ba tare da kowa ya gane ba,idonta yayi jajir tana dana sanin barin kauyensu yanzu ga halin da take ci,
abincin ma ta kasa ci, momee tayi mata magana har ta gaji Nurses ma sunzo Sam taki fitowa a Cikin blanket din sai gajiya akayi aka kyaleta, Igbo dai daya kade ta har yau bai zo ba Sabo da aiki ya rikeshi sai waya yayiwa Doctor cewar kawai tunda ya biya komai su sallameta a Bata 5k ta shiga taxi ta tafi gidansu tunda yaga zata iya komai,dama kuma Doctor din Abokin Igbo man ne, yanda yace haka Doctor ya aikata 5pm ya shigo still taki bude idonta,Ahleef yazo wajen Momee yana shan kallon ikon Allah, Da mutum ya kai Hannu zai cire bargon sai ta danne ko ina da kyar Doctor ya faki idonta ya cireshi tare da wulli dashi gefe,Da sauri ta mike zaune idonta Jajir dashi kamar me fuska takumbura ga Hawaye suna kwarara mata, tunanin kowa dama so take a sallameta zaman asibitin ne ya dameta shi yasa take kuka,Momee tace yi hakuri yata yanzu zai sallameki ki tafi gida Ko ? Ai sai aka ga ta kara volume din kukanta,Doctor yayi murmushi tare da leka fuskarta ya nuna mata takarda kinga da gaske takeyi ga takardar ma sallamar taki na gama komai inye yau zata ga Daddy dinta da Umma, yau zata ci abincin Mamanta kaga yan mata inyeeeeee....Shukura kuwa sai ta kara rafsewa da kuka tana tuna kayan dadin da take ci wajen Momee a banza har wani shidewa takeyi tana kuka,wani farfesu da kayan ciki da take ci kullum suka fado mata a rai,sai ta zamo kasa daga kan bed ta dinga rera kuka,Gasashiyar hanta take tunowa kullum a asibitin sai an raba musu sunci ga dadi Hawaye sababbi suka tawo sharrrrrr,Tunowa tayi Bata da wajen kwana tare da tunowa yanda kullum take karyawa da dankalin turawa,hannayenta biyu ta daura saman kai tana shesheka tana shidewa,Momee sai hakuri take Bata,Doctor ma na lallashi da kyar aka samu ta daina Kukan,likita ya Bata sallama da 5k,Momee tace gaskiya bai dace a Barta ta tafi gida ita kadai ba haka,Igbo ya kadeta bazai iya zuwa ya kaita gidansu ba, Ahleef dai danna wayarsa yake yi bai ce kala ba,Har Shukura ta mike zata tafi sai ta dawo taje gaban kayan abincin momee ta ebi duk Wanda take so taci ta koshi kamar zatayi amai haka ta cika cikinta wai taci na karshe,Gwaggo...Momee tace na hanaki kirana da wani gwaggo fa kin Sani, murmushi tayi kadan tace na manta ne Momee zan tafi ni Allah baki lfy, Momee tace ga number ta ko watarana zaki kawo min ziyara, karbar card din tayi ta fice Abinta kamar kwai ya fashe mata a ciki haka take tafiya har tayiwa asibitin nisa sosai.
sai data yi nisa sannan ta samu wata bishiya ta zauna tana hutawa,ko 2mnt batayi ba sai ga wasu mutane Sun koreta wai ba a zama a wajen,Shukura tace da a kauyene wa zai koreka ko a filin tsakar gidan Me unguwa ne sai yanda kaga dama zakayi,a hankali take tafiya ragowar 2k dinta Cikin Wanda Igbo yace nurse ta Bata suka zube a hanya,baya ta koma tana dubawa amma Bata gansu ba gashi kafafunta Sun gaji kawai sai ta fashe da kuka tana ci gaba da tafiya tana goge hawaye tare da cewa na Kawo kaina gashi ni dama ban iya komai ba zuciyata ta gama mutuwa Iyayena gata suka nuna min,ita kadai take maganarta har tazo dai dai inda Haj Saudatu take soya doya da kwanta me dan karen dadi, har ta wuce sai ta dawo Baya ta kafe Saudatu da mugun kallo a fili tace wlh tana kama da dan gidan Gwaggo Momee, Haj Saudatu ta kalli Shukura itama tana murmushi tace yan mata lfy ? Shukura tace wlh Inna kamarku daya da wani dan gayu baki ganshi ba idan kikayi dariya komai naku iri daya ne,Murmushi kawai Saudatu tayi tare da cewa ni kinga bani da yaro a zuci kuma tunanin danta abin sonta ya fado mata,Shukura tace Inna da zaki bani aiki sai na dinga tayaki ina miki wanke wanke kina bani dan Ladan aiki mu daga kauye muka dawo nan Abuja bamu samu aiki ba,Saudatu taji dadi dama tana neman me tayata aikin tana biyan lada, yarinya a ina iyayenki suke,Shukura gani takeyi idan ta fadi gaskiya za a hanata aikin sai tace daga kauyen Jos muke yankin Fulani,muka dawo nan neman aiki iyayena suna can Nyanya a nan Abuja gidanmu yake,Saudatu kuma ta tace muma yan Niger ne a Kaduna muka fara zama, sai muka dawo Abuja,mijina gadi yake a wani gida,nan muke Zaune hakan ma da kyar masu gidan suka barmu muke dan rabawa a gidansu basu da kirki.
Shukura a ranta tana Sa rai ko Saudatu Zata dauketa ta koma gidanta da zama ta samu wajen kwana sai taji Gaba daya ba harka, Shukura cikin karfin hali tace Inna idan zan kawo miki ziyara watarana fa ? Saudatu ta rike baki tare da cewa wuuuu yar nan rufa min asiri ai Ko baki basu bari muyi idan ma zaki zo sai jefi jefi kuma babu dadewa mu gaisa ki tafi gidanku in ba haka ba ki jawo mana masifa,Shukura taji ba wajen zama kawai tana tunani ga dare nayi to ina zata je ta kwana,jiki a sanyaye tace to Inna yaushe zan fara zuwa ina tayaki aikin ? Saudatu tace banda yau tunda kinga na kusa tashi dare yayi ki bari sai gobe kizo,yanzu maza ki tafi gida kar a nemeki,Shukura tace da na tayaki daukan kayan sai na rakaki gida,Saudatu tace na gode Allah miki albarka baza ki jawo min ba yar nan kiyi hakuri dan Allah ki barshi,Shukura Badan taso ba ta juya tana cewa sai goben zanzo, 3pm cewar Saudatu har ta zubawa Shukura doya da yawa a leda ta Bata kyauta.
Shukura ta rasa ina zata je har 8 na dare kawai sai ta tuna da Address din gidan Ahleef Wanda yanzu yafi rayuwa a cikinsa kawai taxi ta shiga ta bashi Address din gidan Ahleef,bayan me taxi ya kaita sai da ta tabbatar da gidan ne sai ta tsaya can farkon layin dan kar a ganta,ta juya wajen me taxi tace ita wlh kudinta Sun fadi yayi hakuri Bata da ko sisi amma yana binta bashi nan da 3days su hadu a wajen Saudatu me doya inda ya daukota,Me taxi ya dinga masifa har ya gaji karshe yace zaizo wajen Sauden nan da 3days din in dai ba a bashi kudinsa ba to wlh Ko Sauden ce kamata zaiyi,Godiya tayiwa Allah sannan ta fara dube dube sai da ta tabbatar ba Wanda ke ganinta sai tayi sauri ta zaga ta bayan katangar Ahleef inda babu security,Dalaf ta kama wata bishiya dake jikin katangar ta dane bishiyar ta gama kwalkoleta sannan ta lallaba ta taka dalaf ta dane saman katangar gidan Ahleef,Tayi sa'a a saitin garden ne sai ta kara tsalle kamar biri ta hau Saman wata bishiyar goba dake cikin garden din Sabo da katangar tayi stayi haurawa sai da dabara,ta kan bishiyar ta dirga a katafaren gidan nasa sannan ta fara tafiya cikin Sanda dan kar a ganta,ta kofar baya tabi sai gata a kitchen ta tura kofar a hankali,ta bi ta wuce ta fito ta wani katafaren palo tana son tayi kallo ba hali,da sauri tabi ta wasu wuraren har ta samu ta ga Steps taga wata Hanya ta kasan Benan da gudu ta shige tabi ta nan sai gata a wani part din guda ba abinda babu,wani katon wuri ta shiga Gaba daya kayan motsa kiki ne, ta wuce sai gata a wani kitchen din ba abinda babu, cikin inda kayan motsa jiki Suke a nan ta samu wani lungu Wanda idan mutum ya shiga ciki babu me iya ganinka a nan ta samu ta shimfida dankwalinta a kasa harda kashe Light ta kwanta sai bacci ya kwasheta.
Shukura Bata iya bacci lfy ba sai tayi birgima da shure shure taji gida me dadi sai juyi take tana bige bige har ta bige wani karfen motsa jiki kadan, Lokacin Ahleef ya dawo yayi shirin bacci cikin Fararen kayan baccinsa tunda ya shigo yau yake Jin kamar ana motsi a gidansa,kamar ba shi kadai bane,idan kuma ya kasa kunne sai yaji shuru,Yana Saman Bed yana latsa system sai yaji kamar abu yayi motsi,tsoro ya kamashi kawai dai ya dan daure ya Mike ya fara lallabawa yana sanda kamar sabon barawo,a haka ya duba ko ina na gidan sai yaga ba kowa,kawai sai yace ko kunne na ne ? Baki ya tabe tare da kashe Light na ko ina ya koma ya kwanta bacci.
Washe gari da safe ta lallaba ta fada wani bedroom wanda yasha kayan alatu masu kyau, Da sauri ta shige toilet din ciki,ta samu sabon brush da toothpaste tayi brush tare da wanka ta daura Alwala ta shirya cikin kayanta tsab sannan ta kara lallabawa ta fito inda take boyewa anan tayi sallar asuba tare da adduointa, sai 10am taji motsin Ahleef ya fito dakin da take zai motsa kiji,kara boyewa tayi sosai tare da leko da kanta tana kallonsa daga shi sai Boxers yana motsa jiki,shiko bai san da mutum ba,Yana ta motsa jiki,itako mamakin kyawu nasa takeyi ga kyan sura kasa dauke ido tayi a kansa kamar zata lasheshi,tana kallo ya hada zufa har ya gama sannan yayi wata mika sosai,Dariya ya Bata yanda yayi mikar saida ta murmusa,tana kallo ya juyo kamar yana facing nata da dan tight boxers din dake jikinsa Kamar tsirara haka yake Sabo da shape din komai ana gani,Shukura ta firgita ganin kato haka Bata San sanda tace kai..tab Amma sautin kadan ya fita baza ka gane maganace ko ba magana bace,a tsorace Ahleef ya fara waige waige yaga ba kowa,tsoro ne ya kamashi ya fita da gudu ya banke kofar,Abin dariya ya bawa Shakura namiji haka amma sai tsoro.
Sai da ya daina Jin tsoron sannan Kitchen dinsa ya shiga domin dafawa kansa Breakfast shi bai son girkin yan aiki,Chips and egg ya hada sai tea daya hada lafiyayye a cup,ya shirya komai a Dining,Shukura yunwa ta addabeta,ga kamshin girkin ya cika mata ciki,tana kallo Ahleef ya tafi bedroom din sa domun shiryawa sannan ya fito ya karya,da sauri ta fito tare da dauke Shayin ta balli Bread,Chips and egg duka ta dauke ta cinye tas da sauri ta ajiye masa empty komai sannan tabi ta inda ta shigo jiya gidan ta kara bi ta sama ta dirga ta waje can tayi sauri ta bar layin,Ahleef ya dau wanka yana zuba kamshi yazo dining ido ya zaro cike da tsoro jikinsa ya fara mazari ya ajiye komai ya shirya abinci amma yaga ba komai a wajen sai plate da cup,a tsorace ya fice da sauri tare da Umartar Driver dinsa ya kaishi Hospital wurin Momee,ganinsa da driver yayi a firgice tunaninsa Ko jikin Momee ne ya tashi Da sauri Driver yaja zukekiyar motar zuwa asibitin,Momee ma ta kasa gane kan Ahleef taga kamar a firgice yake ta tambayeshi ko lfy yace normal Sabo da abin kunya ne ya fada cewar kamarsa yana Tsoron Aljanun gidansa.
Shukura kuwa kowa ya kalleta yasan tana Cikin Nishadi yau tayi kwanan dadi,idan ta tuna yanda Ahleef ke firgita sai ta kwashe da dariya haka ta yini tana gantali a gari Bata da wajen zama,gashi kayanta Gaba daya suna Hotel ta barsu Bata da abinda zata canja kaya doguwar rigarce kullum a jikinta ko wanki Bata samu ba duk tayi dirty,lokaci yana cika 3pm ta wuce wajen Saudatu me Doya Zata fara aiki,gashi tunda ta cinyewa Ahleef abinci Bata kara cin komai ba, yunwa ta gama kwakwuleta.
Da murna ta karasa wajen Saudatu wacce ke hada kaskon suyarta,Sallama tayi tare da gaishe ta cike da ladabi,Saudatu tace yata Kinzo Akan lokaci kuwa haka nake so,Inna ai Bazan Bata lokaci ba bari na fere miki doyar,Nan Saudatu ta shiga koya mata yanda ake komai tana yi ba laifi ta iya duk da cewa Bata saba da aikin ba amma tayi kokari,sabo da kyan Shukura yau cinikinsu yafi na kullum,doya taci ta koshi har ta gode Allah,bayan 6pm suka siyar da komai,Saudatu ta bata Dubu daya kudin aikinta tace gashi ki shiga taxi da dari biyar,biyar kuma ladanki na aiki,Shukura murna kamar tayi Hauka tana ta godiya ta raka Saudatu bakin gate din gidan da suke aiki sannan ta tafi gidan Ahleef itama kamar gidan ubanta, a hanya taga wani wajen shan Ice cream tace yee wlh yau sai na sha,nayi niyyar tara Kudin amma dadina kawai zanci, ubanwa wahala ta kashe ? ,Allah ya hore, kawai ta shiga ciki taji ice cream tsada babu na kudinta,daga na 2k sai sama,Wani matashin me kudi ta gani yana ta jidarsu da yawa,tace sannu malam,dan Allah kaga kudina dari biyar gareni dan Allah cika min dubu daya da dari biyar zan sha ina so,yawuna ya tsinke,raina ya biya,kaga kuma ido guba ne,Matashin saida ta bashi dariya ya dauki roba guda ya bata,ta shiga gode masa ba adadi.
maimakon ta boye kudinta tana fitowa taga wajen da ake siyarda Shawurma taji Kudin sunyi yawa amma sai da ta siyi wata Samosa da akeyi a wajen guda biyu dari biyar, dari biyar din kuma ta shiga taxi drop babu ko neman sauki,yau ma ta sama tabi ta dirga cikin gidan Ahleef kamar jiya har zuwa makwancinta,ta cire kayan jikinka sai dankwalin rigar ta daura ta shige toilet ta wanke tas ta shanyata a toilet din cike da tsoro kar me gidan ya kamata,Ice cream dinta tasha da samosa dinta har lumshe ido takeyi.
Ahleef yana bacci amma sai ya dinga ji kamar motsin mutum yau ma haka ya duba ko ina baiga komai ba.sai da safe rigarta da inner wears dinta suka bushe, bayan tayi wanka fes tare da brush harda wanke gashi tana kamshi ta ko ina ta samu soap me tsada,Bayan ta saka kayanta Da suka bushe sai ta wanke gyalen shima ta shanya shi ta fito tare da kara boyewa, tana kallonsa yau ma ya motsa jikinsa, yau indomie ya dafa da kwai bai tafi wanka ba ya cinye abarsa sannan ya Haura samansa,yana tafiya ta fada kitchen din da sauri ta shiga dube dube nan taga ruwan zafi a flask ta hada tea me shegen kauri har yayi yawa ma, ta kwashi snacks a fridge ta fito da sauri ta koma wajenta na boyo,tana fita yana saukowa kasa yana latsa waya sanye Cikin fitted jallabiya fara yana kamshi kamar balarabe,Cikin palon ya zauna tare da daukan remote ya kunna TV tashar kwallon kafa yana kora lemo lafiyayye da Alama yau sunday ba inda zai fita,Shukura kuwa taci ta koshi,garin labe laben ganin ko yana palo ta fadi a kasa,ta mike da sauri tare da kwashewa da gudu ta koma wajen boyonta,Ahleef yaji kamar abu ya fadi harda yar kara,wani tsalle ya buga a tsorace ya haura sama da gudu ya buya a bedroom dinsa shima yana tunanin to mene a gidansa haka,ko dai barin gidan zaiyi ? Ko bakin aljanine a gidan.
Shukura kuwa yau itama ba inda zata sai 3pm zata je aikinta Sabo da haka ma ta lallaba ta shige daya kitchen din na daya bangarenta, duk wani abin ci da sha idan ta gani sai da ta dandana shi taji irinsa.
Kullum haka Shakura takeyi a gidan Har ta kwashe sati daya a gidan Ahleef tana buya ba tare da ya Sani ba,idan baya gida ma har girke girke takeyi ta wanke komai ta mayar inda yake yanda bazai gane ba, kudin aikinta kuwa kullum Saudatu zata Bata dubu daya ko dari takwas amma kafin taje gida ta siyi kayan ciye ciye da Kudin, watarana ko Na taxi Bata bari sai dai tayi ta rokon me taxi ko ta dinga tare lift, ta kara wani uban kyau da haske tare da kiba Sabo da yanda take ciye ciye a gidan Ahleef,har yau bai Ankara cewar kayan abinci suna ta karewa ba kuma bashi yaci ba, wasu abin ma ko farka kwalin baiyi ba amma Shukura duk ta farke su tana ta kwaba girkinta tana ci. Wani abin ma bata san mene ba,dama kuma ba wani iya girki tayi ba, dama dama na gargajiya ma.yanzu babu girkin da tayi mugun iyawa sama da doya da kwai,ta koya wajen Saudatu,sai Dambu,danwake,tuwo,fate,da sauran abincin kauye ta iya kadan tun iyayenta suna da rai.
yau ma Saturday Ahleef ba inda zai fita,haka Shukura ma Saudatu tace yau da gobe baza suyi abin siyarwa ba me gidansu zai yi baki zata taya masu aikin girke girke etc.
Tun safe Ahleef yake Jin kamshin girki a gidansa na musamman yana tashi,ya rasa a ina yake jinsa,ya duba baiga komai ba, yasan kuma shi kadai ne a gidansa,tunani ya shiga yi jimm Kadan ya tuna wani abu, a fili yayi dariya yace Oh makwafta ne, kaiii... amma Sun iya girki sai kawai ya koma palo yaci Gaga da kallon ball dinsa,ita kuwa Shukura tana ta suyar doya da kwai a daya kitchen din wanda Ahleef baya shiga, Sabo da Shirmen ta bata taba tunanin za aji kamshin girkin ba ai nan wai buya tayi tana girkinta a boye,chanel ya canja ya tare da kure Vol na kidan turawa me dadi,Shukura ta jiyo dadin kida bata ma san sanda ta fara rawa tana juya doya a kasko ba.
AsmaBaffa
[7/22, 1:12 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
6
Official
By
AsmaBaffa
JIN DADI SABO FANS GROUP ga page naku aci Gaba Sharhi.
Soye soyenta takeyi har ta gama tare da gyara kitchen fes ta dauki abincinta ta koma inda ta saba boyewa taci ta koshi abinta ta kawo ragowar Doyar ta ajiye a Kitchen ta koma da sauri kar me gidan ya kamata, Gaba daya Ahleef a tsorace yake a gidan shi yasa yake Jin kamar motsi,a hankali yabi inda yake jin motsin har kitchen din da tayi girkin ya shiga yaji kamshin girkin dazu ya bigi hancinsa Gaga daya kamshim ba a makwafta Bane,tsoro ne ya kamashi bai gama firgita ba saida ya hango ragowar Doya soyayya a plate, Kara ya saki tare da dauko wani Dogon Spoon idan ya taba plate din sai yayi tsalle ya kwalla kara yana ja da baya,Shikura tana labe tana kallonsa sai dariya takeyi a boye,Tana kallo ya leka dustbin ya kara suman tsaye ganin kwalaye da ledoji iri iri a ciki harda robobin Ice Cream,mopper ya gani a jike alamar anyi amfani da ita,da sauri ya fita tare da daukan key din mota ya bar gidan a firgice, Shukura Saida ta tabbatar ya fita sannan ta fito karo na farko da ta fara yiwa gidan kallon tsab,ta dinga yawo tana shan kallon haduwa har ta shiga Bedroom dinsa na Alfarma kamar me ya hadu komai White.
Har toilet ta leka a fili tace ba ruwansu da tunanin mutuwa,Saman Bed din ne ya birgeta kawai ta haye Sannan ta dinga tsalle tsalle wai dadi ta kara kwanciya tare da bajewa Bata ma san sanda bacci ya kwashe ta ba sai da ta kwashe fiye da Hour daya sannan ta farka a gurguje ta sace Wasu Boxers dinsa,Dogon jean pencil kala biyu, ta kara bude wasu bangaren ta kwashi Singlet kala biyu wai zata dinga bacci dasu,Jallabiya kala Uku fitted har kala uku ta dauke masa,har Zata fita taga wasu biscuits manya masu tsada dasu chewgum iri iri ta ebo wasu da yawa ta fito tare da komawa wajenta na boyo,Tana fita Shi kuma Ahleef ya shigo tare da manyan Malamai har su goma kowanne rike da katon Qurani,babu Bata lokaci suka dinga zuba karatu ana korar shedanu har suka gama ya basu kudi masu yawa suka tafi tare da tabbatar masa an kori Aljanu dama rashin addua ne yasa suka mai da gidansa kamar dakinsu,Babban malamin yace Ahleef wato Allah ya taimakeka ka fada mana da wuri,da tuni Sun nakasa ka,ido ya zaro,Malam yace ae fa ai gidanka kasuwar Aljanu ce guda ta duniya,a nan kasa kasa suke zuwa siye da siyarwa amma yanzu mun koresu,Ahleef yace malam ka tabbata babu ko jaririnsu basu tafi Sun bari ba ? Malam ya karkace gemu tare da cewa ko tsinke basu bari ba ka godewa Allah,Godiya Ahleef yayi yana murna har ya rakasu ya dawo gidansa ya kara bajewa saman kujera shi a dole an kori aljanu,Lokacin Shukura har tayi wanka ta saka Jean dinsa fari tare dafarar Jallabiyarsa fitted duk da cewa Sun mata yawa sai tayi masifar kyau tare da yafa gyalenta na doguwar rigarta tayi Rolling sannan tace bari ta fita yawo ganin gari,ta Saman bishiya zuwa katanga tabi ta fita abinta,Shima Ahleef ya kira escort dinsa zasu kaishi wurin Momee yau za a sallameta,kuma Abba dasu Salman sunzo duba ta suna gari,cikin motocinsa na Alfarma suka jero kamar Gomna motar da yake ciki tana tsakiya,Shukura kuwa wahalalliya tana tafiya a gefen titin da jallabiyarsa a jikinta tayi kyau, white color,Jallabiyar Ahleef Unique ce yana ganinsu yasan nasa ne,sabo da kalarsu daban ake dinka masa a turkysh har wasu tambari ne dasu Wanda shi kadai ya zabi abinsa ake masa.
Motarsa tazo wucewa ta saitin Shukura dake tafiya ko layin Bata bari ba, Tunda Ahleef yaga irin tambarin Jallabiyar a jikin mace ya cika da mamaki gashi Ko wace tayi kyau kuma da gani ta maza ce amma sai yaga kamar ya santa ma,kuma wannan ai tafi waccen kyau da kiba tare da gogewa,ta window din motarsa yake ta faman kallonta ya kasa gano ta, Baki ya tabe a fili yace dama a duniya dole sai ka samu abu me irin Naka.
Yana Shiga Hospital yayi arba da Niima tazo itama yau,kirjinsa ne ya buga ganin yanda ta kara wani kyau da kiba gashi ta sha kyau,Nan take Tsohon ciwonsa ya motsa ji yake kamar ya rungumeta,ita kuwa Niima wani kallo ma take masa na wulakanci ita tunaninta kyau shine so,ganin tana da kyau yasa sai yanda taga damar juya maza,sai kallonta yakeyi kamar ya hadiyeta zuciyarsa tayi rauni Hawaye ke shirin zubo masa shi kadai yasan azabar da yakeji a kirjinsa.Momee ta gano hakan ranta ya kara jagulewa tana son Ahleef fiye da kowa,Abba ma bakin cikin Niima yake ta gama Bata masa rai,haka su Suhail,Abba ne yayi magana Ahleef an sallameta fa muje gida,Momee Hannunsa ta riko Cikin kasa da murya tace My Dear Son ya akayi ne ? Kayi hakuri kaci gaba da addua kaji,ka daina damun kanka zaka sa ciwona ya dawo,murmushin karfin Hali yayi kawai yace to Momee ba damuwa lets Go, har Abba sai da ya murmusa ganin yanda Momee da Ahleef suke magana a hankali babu me jinsu,Suhail yace Bro ko sannu da zuwa baka yi mana ba, Salman yace nayi fushi ni suna ta dariya Gaba daya banda Niima dake taunar chewgum ta wani hade rai,Ahleef ya kalleta dan kar Momee taga kamar ya tsani yarta yace yan mata ba magana ? Kamar gimbiya da kyar tace sannu ya kk ? Yace Hmm Kawai ya shareta,ba karya Niima satar kallonsa takeyi yanda ya gaji da haduwa ga kyansa ba a magana kullum karuwa yake,tabe baki tayi tare da cewa can da matsalarsa.
Momee tasan idan tace Ahleef sai ya dawo gida da zama ta shiga hakkinsa Sabo da Niima ce bai son ta zauna a ransa shi yasa yayi dan nesa dasu gwara ta kyaleshi ya samu Nutsuwa,suna Komawa gida tace Son tashi ka tafi gidanka ka huta naga ka gaji jeka gobe ka dawo jeka huta,dama Kadan yake jira Sabo da Niima tana ta faman shige da fice hankalinsa yana tashi soyayya tana matsa masa,sallama yayiwa kowa ya wuce zuwa gidansa zuciyarsa a jagule,lokacin Shukura ta dade da dawowa gidan tuni.sai yanzu Yaga Bedroom dinsa an lalata masa shi kamar wani ya kwanta,kayansa kuma kamar an taba su, sai yayi tunanin idonsa ne ke masa gizo Amma gobe zai fadawa masu gyara gidan su kara gyara gidan,kudinsa ya duba ya gansu yanda suke ba a taba ba, shakira halayenta ba sata a ciki,ko nawa zata gani komai talaucinta baza ta dauki abinda ba nata ba bare kudi.
Bayan yayi shirin bacci sai ya fito zai duba gidansa tare da kashe Light lokacin Shukura ta shiga kitchen dinsa ta kwaso su Apple da sauran kayan Fruits tana wucewa shi kuma ya fito yaji kamar an rufe kofa da gudu yabi bayanta amma kafin ya kamata tuni ta boye shi kuma gani yakeyi kamar mutum kamar ya gani,a hankali yace lallai aljanu ne a gidan nan masu yawan gaske,amma akan na koma gida da zama gwara nayi rayuwa da Aljanu Sabo da Niima ta dawo gida yanzu,bazai iya canja gida ba Sabo da yafi son gidan da yake ciki, to ko Security camera zansa koma mene ai zan gani,to ai aljanu ne kuma ba a ganinsu idan kuma ya gansu zai tsorata,motsi yaji kamar an bigi wani karfe da sauri ya juya baya fara gudu gudu sauri sauri ya kulle kansa a Bedroom tare da kudundunewa cikin bargo yana addua iri iri har bacci ya kwashe shi,Shukura tana kallonsa tana ta dariya kasa kasa lallai wannan matsoraci ne na gaske.
Saudatu yau Alhajin da suke aiki a gidansa zaiyi baki zasuyi Meeting na business Ogansa me gidansa tare da Dansa zai kawo masa ziyara gidansa a nan zasuyi Meeting Sabo da Alhaji Dauda abokin Abba ne kuma suna Business da Ahleef yana ta musu mitar sunki zuwa gidansa,gaba daya gidan yan mata da samari tare da iyayen duk Sun rude Sun gigice sai kwalliya Suke zubawa kamar zasu je ganin sarki Sabo da Dan Abba yace yana sonsu,Mama Cewa take yawwa yan matana kuyi kyau sosai so nake Ahleef ya zabi daya a cikinku ya aureku burina ku auri me kudi irin babanku Wanda zai dinga kaini Makkah da kasashen turawa,wanda zai dinga siyo min super England ba wanda zai siya min Nichem ba,gidan da zaku huta gidan Naira,Ko Abban ne yace yana Son daya dole na bashi komai tsufansa,Yan mata suna dariya tare da cewa ai sai Mama Allah bar mana ke, Wani Saurayi zai kai shekarun Ahleef Mubaraq yace ni kaina da Abban yana da budurwa lallabawa zanyi nayi Auren jari da ita,Karaf Mama tace tana nan sunanta Niima har Company gareta ban San me yasa aka fasa aurenta da wani ba ban San kan lbr ba Amma tana nan batayi aure ba kaje kayi duk yanda zakayi ta soka dama gaka kyakyawa da kai duk yarana babu me kyanka,duk abinda suke fada Saudatu tana goge goge tana jinsu sai da gabanta ya fadi da taji an ambaci Ahleef me sunan jaririnta Amma tasan shekaru 31 ba wasa ba, tuni ta hakura tasan danta yan mafiya Sun yankashi tuni,Har so take a duniya ta ga waye wannan me sunan danta daya bace gashi sai rubibinsa akeyi Sabo da yana da kyau da kudi.aranta tace ai kuwa sai ta labe ta ga waye wannan baza tayi nisa ba.
tsawa taji wata budurwa ta buga mata me suna Hafsy,Hafsy itace budurwa Babba a gidan kuma tana da dan kyau kadan shi yasa Momee tace lallai ta makalewa Ahleef har ya aureta,gashi kuma duk gidan ita ke wulakanta Saudatu fiye da kowa, watarana har marin Saudatu ta taba yi, tafi kowa fitsara,daga ita sai Mubaraq a rashin mutunci,sai kanwarta Zahra sauran suma ba tarbiya amma mutum uku sune kan gaba, Mama kuwa itama haka take har Alhaji Dauda amma bai fiye wulakanci ba shi sai kadan kadan.Hafsy ce ta watsawa Saudatu Harara dalla malama wuce inda kika fito sai sa ido,Mama tace hmm kuma dai kwa fada suka sheke da dariya gaba daya,Saudatu ta riga ta saba kawai sai ta wuce abinta a ranta tace duniya ce, tazo zata wuce ta kofa Zahra ta bangajeta ta wuce abinta.
Yamma 5pm kowanne dake gidan yaci kwalliya yana jiran manyan baki suzo,Hafsy sai kwarkwasa akeyi,5:30pm motoci laba laba Sun kai 6 ne sukayi parking a cikin gidan,Yan mata fa ansha kyau,Guards ne suka fara Budewa Abba ya fito sai Salman da Suhail Sun dau wanka suna zuba Kamshi,Wata rantsatsiyar mota suka sake budewa sai ga Ahleef yaci uwar uban Wanka kamar baza a mutu ba,cikin manyan kaya farar Shadda kal tasha dinki fitted ta samarin Abuja, sai kyalli da sheki yakeyi,Yana uban taku kamar Sarki yana basarwa ga kyau kamar wankin Engine,kamshinsa duk ya cika gidan,yan mata sai leke suke ta Window,Hafsy tace wai...wai... Zahra na riga ki wannan me farar shaddar nake so,Zahra ta hayayyako da masifa wlh na rigaki shine nawa,ai wlh baki Isa ba,Babba sai babba,yaro kuwa na yaro ne, Jamila wacce suke kira Jamcy itama tace Ahleef take so suna leke ta window,Nan fa fada ya kaure a tsakaninsu sai da Mama ta raba su da kyar, Mama tace ku nuna min akan Wanda kuke fada naga kyan nasa da kuke fada,Zahra tace leka ki gani Mama gashi can da Farar Shadda tunda muke bamu taba ganin me kyau irinsa ba a duniya,Mama ta leka nan take ta hangame baki tare da cewa ina ma ana tariyo baya nima na dawo yarinya Akan wannan wlh sai nayi kisan kai,Dama sun San Mama akwai budurwar zuciya duk harkar charting baya wuceta,Mama ta wuce tace na tafi tarbar baki anjima kuzo ku gaisheshi.
Alhaji Dauda yana tare dasu a katafaren Palonsa suna ta Hira daga nan suka fada harkar Business,Mama ce itama ansha wanka taje suka gaisa taci kitson attach kamar arniya tana zaune a palon kusa da mijinta,bayan 30mt sai ga su Hafsy suna ta layin gaishesu suna karairaya,daga nan Mama tace suzo aci abinci,Ahleef kawai waya yake dannawa Ko kallo basu isheshi ba,babu wacce ya amsawa gaisuwa sai Mama kawai,su Salman kuwa harkar gabansu sukeyi suma,Jikin yan matan yayi sanyi amma basu hakura ba.
Bayan nan Ahaji Dauda yasa aka kawo musu abinci a nan Palon ba sai anje Dining ba,duk Sun zagaye ciki harda Zahra da Hafsy, Mubaraq yana ciki sai Mama da Jamcy.
Yan aiki aka bawa Umarnin kawo abinci ciki harda Saudatu sabo sunfi yarda da tsabtarta,Saudatu ta kawo katon Flask ta ajiye a saitin Ahleef cikin Nutsuwa tana Tsoro karta yi ba dai dai ba, tsaki Hafsy taja tare da cewa dan Allah madam ki ajiye ki tafi ke kullum baki San aikinki ba,Zahra ta kara Jan dogon tsaki uwar kinibibi tsohuwa dake,Mama maimakon tayi fada sai tace hmm Saudatu kenan Uwar Iya,Alhaji Dauda ne yace ku fa bakwa kyautawa Allah kyauta abinda yace kenan,Mubaraq ya shekawa Saudatu harara.
Abba dama shi ya dade da sanin gidan abokinsa ba tarbiya baiyi mamaki ba, yana Allah wadai da halayensu,Salman suma mamaki ya kamasu dattijuwa kamar wannan ana zaginta,Ahleef kam da sauri ya kalli matar da akayiwa tsaki dattijuwa sosai irin wannan ita kuwa ta bar aikin mana idan ba son kudi ba, ana zaginka kana zaune,Su Hafsy yaji ya kara tsanarsu yanzu sosai,Saudatu ya gani ta kawo wasu cups,Mama ta daka mata tsawa zubawa baki abinci mana,su duk ganinsu birgewa sukeyi su masu kudi.
Saudatu jiki na bari ta fara zubawa Su Abba,zata zubawa su Salman yace no na koshi ni,Suhail ma yace bazai ci ba ruwa zai sha kawai,Saudatu da fara'a ta kalli Ahleef tare da cewa kai fa Alhaji me za a zuba maka ? Ahleef ya kalleta aiko sai ya saki murmushi kamar ya santa yace Umma wanne kika dafa da hannunki ? Ta nuna masa kala uku harda Zobo Drink me dadi tace wannan nayi da kaina,yace zuba min su zan ci ni,Ita dai Saudatu sai tana ganin kamar ta San Ahleef amma ta kasa ganewa,Mama kuma da Su Hafsy sai kallon Ahleef sukeyi suna kallon Saudatu sai suka ga kamarsu daya har tayi yawa ma, komai nasu har hakoran kusan iri daya,Bayan ta zuba masa ya karba da kansa, har zata bar wajen Ahleef yace zauna mana Umma idan na gama sai mu tafi na jirasu a waje,Tsoro ya kama Saudatu tasan yau tata ta kare a gidan,tana zaune ya gama cin abincinta me shegen dadi sannan ya Mike Saudatu tabi bayansa suka fita har waje,yace Umma haka kuke rayuwa ke yar aiki ce ? Saudatu tace ae wlh rayuwa kenan,Ahleef yace ke da mijinki duk nan kuke aiki Saudatu tace ae a takaice ta bashi labarin irin zaman da suke a gidan,da wulakancin da suke fuskanta ita da mijinta,Ahleef ya tausaya musu yace watarana idan na samu time zan daukeki ki dinga dafa min abinci ina biyanki albashi Kin yarda? Murna ta kama Saudatu ta dinga godiya harda durkusawa har kasa,yace mijinki kuma sai na kaishi Office dina yana min goge goge ina biyansa,Zan baku wajen zama a gidana zan dawo na daukeki nan da 3wks.
Godiya kawai Saudatu keyi masa,yace haba Umma ki daina godiya haka ya zaro 10k ya Bata.
Abba ya fito tare da yan gidan suka rakasu suka tafi,Mama lokacin suka rufarwa Saudatu da balai da masifa iri iri suka ce gobe sai Sun bar musu gida,Asiri take wa bakinsu kowa yana sonta,tana mallake musu masu kudi,sai kace wata budurwa ita me zatayi da wasu maza masu kudi Saudatu ta furta a ranta, Babu hakurin da Bata basu ba har mijinta da suka sa masa dan dako Sam suka ce dole gobe su bar musu gida.
Tunda Shukura taga Ahleef ya bar gidan ta fito ta gyara gidan Neat har samansa yana ta kamshi ko ina ta canja tsarin gidan yayi Masifar kyau, tayi girkinta taci ta koshi ta dauki remote tana ta danne danne har Allah ya taimaketa ta kunna TV ta kamo tashar American film tana ta kallo har ta gaji ta mike ta shige bedroom din Ahleef toilet dinsa ta shiga tace dole na dana,ta fesa wankanta da kayan wankansa,ta fito ta shafa Body lotion dinsa,kayan gyara gashinsa da su ta gyara nata yana kamshi, Cikin sip dinsa ta bude ta duba cikin wankakkun shaddojinsa ta zabi wata ruwan toka ta dauki iya rigarsa wata yar fitted hannun links ne ta sa abarta shar tayi kyau kuwa,bata sa da wandon ba, turarensa iri iri ta fesa sannan ta kara gyara masa komai na dakin ta fito ta baje a palo tana kallon film tana shan lemo abinta,Ahleef har ya dawo Bata Sani ba, sai ji tayi ana kokarin bude kofa da gudu ta kashe TV ta arce inda ta saba buya,tun daga waje Ahleef ke Jin karar TV amma abin mamaki yana shugowa yaga TV a kashe,sai kwalin lemo,gashi shi yasan bai sa a gyara masa gida ba amma yaga gida sai kyalli yakeyi da sabon kamshi,tsoro ya kamashi ya haura sama yasha mamaki kalar gyaran dakin na musamman har Bedsheet an sake masa,Ya fito ya duba gidan kaf ko ina yasha gyara, ya tambayi security ko wani ya shigo ? Yace shi ba Wanda ya shigo,ya dawo ciki a fili yace wlh idan na kara ganin abin Tsoro guduwa zanyi na bar gidan.
Kwana uku tsakani kullum sai Shukura taje wajen da suke soya doya amma ba Saudatu ba labarinta,ta tambaya amma babu Wanda ya San inda Suke,har gidan Da Saudatu ke aiki taje amma akace an koresu daga aiki har kuka Shukura tayi sannan ta dawo gidan Ahleef taci Gaga da buyanta.
Yau Misalin 12 na dare Ahleef yana gida,Shukura ta sa rigar Shaddarsa wata Milk color Garin labe labenta ta daki wani karfen motsa jiki ta fadi Tim a kasa,kafarta ta dauje Jini yana fita,Kuka ta fashe dashi sosai ta manta Sam da za a kamata Bata kaunar ganin jini na fita sai ta fara kuka,kuka ta shiga rerawa,Ahleef Tsoro kamar ya sume,ya dauki katuwar kujerar Mirror yana lallabawa da niyyar duk Wanda ya gani ko aljanine fasa masa kai zaiyi,yana lallabawa a tsorace har ya bude kofar inda yake Jin kukan na fitowa a hankali ya Shiga,Yaga Gashin mace ai ba shiri ya jefar da kujera zai gudu regarsa ta makale a kujera ya fasa kara,Shukura kuka ya dauke dif tasan asirinta ya tonu shike nan korarta zaiyi kwanan kan titi ya ganta,Fuskarta ta dago suka hada ido da Ahleef yana kokarin guduwa rigarsa ta makale,Cak ya tsaya da yaga kamar yarinyar da suka kwanta a Hospital da Momee,kuma wacce ya gani sanye da Jallabiya irin tasa,tabbas itace ashe dama Kusan 2wks kenan tana gidansa ashe itace take sawa yana tunanin Aljanunee,wani bakin ciki ya kamashi,tana jira taji saukar duka sai taji cikin fushi yace Amma kin zalunceni kin cutar dani,all ths While ashe kece,why baza ki fada min ba ki rokeni na baki inda ya dace dake,hawaye ya kwararo mata na tsoro cikin rawar murya tace uhmm..tsoro...tsoro naji karka koreni wlh zan baka labarina ni marainiya ce,Hey...u better stop tht nonsense ina ruwana da maraicinki Who even care,Mikewa tayi ya kare mata kallo wato kayana ma kike sawa Sabo da kin rainani,ashe duk abincin nan kece kike cinyewa,shuru tayi ta wani turo lips Gaba,tace Allah baka hakuri, dan Allah kayi hakuri bari na bar ma gidanka,ta kwaso kayansa sunkai kala bakwai da take ta sawa tace ga kayanka,mamaki ya cikashi ashe barnar har ta kai haka ji yake kamar ya kasheta,rokonsa tayi dan Allah ka taima kamin da wajen kwana kafin na samu kudi,Kin San da haka me yasa baki rokeni ba tun wuri,har Ya juya zai tafi ya dawo yace sai kiyi ta zama Mayya,ya Leka lungun da take boyewa tana bacci yace hmmm tare da bude Bedroom din da take shiga toilet din ciki tana wanka yace ga daki nan kuma wlh kina min shirme sai kin bar gidan nan tunda bana ubanki bane,Murna ta kamata ashe haka yake da mutunci, bata taba zato ba gashi ya bata daki ma tsantsarere, kallonsa tayi baki a washe tace ashe mutunci ne da kai haka na gode,Allah yaji kan magabata,Allah kara budi da arziki ya biyama bukatunka na alkhairi yasa Aljanna makoma,Baki ya tabe tare da cewa yar Maula,Shuru tayi murna ta isheta Bata ma ta ciwon da taji tace ba dadewa zanyi ba ina samun wasu kudi zan bar ma gidan,ina sa rai da wasu kudade naji a jikina zanyi kudi kwanan nan sai na barma gidanka karka damu saura kadan.tsaki yaja yayi gaba abinsa yana cewa sai kinyi kudi ma zaki barmin gida? Ba rana kenan ya barta a wajen tana murna harda tsalle.
AsmaBaffa
[7/22, 1:12 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
7
Official
By
AsmaBaffa
ZAMA NA AMANA 2 FACEBOOK wannan page naku ne,na gode Allah ya bar kauna.
FLOWER jinjina gareki wajen Sharhi ba daga kafa tnx alot.
Fans bana son tnx fa Sharhi nake bukata ni.
Bedroom din daya Bata ta fada ciki tare da kwanciya saman Bed tana faman murna,yau ba wani tsoron Aljanu yayi bacci sosai shi kanshi washe gari yayi mamakin baccin daya kwasa ya nisa tare da cewa amma yarinyar nan ta cuceni wlh yaushe rabon da nayi bacci haka,ko gidansu zai maidata wajen Momee ina shi ina kwana gida daya daga shi sai budurwa ina bazai iya ba, wani tunani ne ya fado masa sai kuma yace no Momee zata kwasheta tace zata zauna a wajenta har abada shi kuma bai Son kwashe kwashe kawai ta gama kwanakinta ta bar masa gida shike nan,Saudatu ce ta fado masa a rai yace dama dawo dasu yayi gidan suka fara aikinsu kawai yace da yamma zai tura Driver ya dauko masa su.
Saudatu kuwa tunda aka koresu basu da wajen zama sai can karkashin gada suka koma suna kwana ita da Alhaji Amadu,ruwa,iska komai a kansu yake karewa suna Cikin yan cirani suna fadi tashi,Babu wurin kwana ina wata sana'a idan ma Sun bar gari to basu da wajen zuwa, Ahleef yana ranta Sabo da yace zai daukesu aiki dan haka Kullum Saudatu da mijinta sai sunzo kofar gidan Alhaji Dauda Sun yini Ko zasu ga Ahleef yazo daukansu,Saudatu da ta gaji da wahala Duk dauriyarta Yanzu kuka takeyi sosai wai su me yasa tuntuni rayuwarsu a wahala suke ne,yau ma suna nesa da gidan Alhaji Dauda ta tsuguna a kasa Bata San sanda ta fara hawaye ba, shi kuwa Alhj Amadu kusa da ita ya zauna yana tausaya wa kansu matarsa balarabiya talaucinsa yasa duk ta tsufa, da yasan hakane da bazai aure ta ba, tunda yasan talauci a jininsu yake gashi har yau ya jawowa masoyiyarsa ma, Lallashinta ya fara suka samu wurin inuwa suka zauna Kafadarsa ya miko mata tare da cewa kwanta Saudat ki huta,ita kuwa dama dake balarabiyace ko a jikinta ba ruwanta da mutane ta lafe a kafadar Alhj Amadunta.
Haka yauma suka karaci zamansu har dare ba Ahleef ba alamarsa suka hakura suka koma Karkashin gadarsu inda yan cirani ke taruwa su kwana mata da maza babu iya shegen da ba ayi a wajen sai dai ka sharesu kawai.
Yau da safe da wuri sai ga Shukura da shishigi har kitchen din Ahleef anan ta soya doyarta da kwai Irin yanda Saudatu keyi,ta dafa tea yasha kayan kamshi ta ajiye a Dining ta wuce dakinta domin yin Wanka, Ahleef ya fito cikin Shirinsa na fita Office yaga an shirya abu a Dining,budewa yayi yaga doya ta soya yanka biyar ta cikin mutum daya,wato kanta kadai ta Sani, sai ya zauna yasha tea dinsa tare da cinye doyar tata tas bai bar ko kwallo ba
Ya Mike ya koma Bedroom dinsa yana amfani da System Kafin ya fita,Shukura Ansa jallabiyar Ahleef Milk ta fito zata kwashi girki ta bude plate wayam ba komai,tace to ko shine ya cinye min? Bari naje na tambayeshi naji aiko idan me gadi ne wlh sai ya gane kurensa kuji karfin hali,Saman Ahleef ta nufa sai taji tsoro tasan baya daukan raini,sai da ya fito cikin shirinsa tana palo lokaci da saura ta tsuguna har kasa jikinta na rawa tace ina kwana, baki kawai ya tabe,ta maza tayi tace uhm...Kawu na kaine ka matsar min da abincin dana dafa,wai wayo tayi masa ya matsar mata kar tace ya cinye mata, Shuru yayi mata tace Kawu dan Allah nace Ko kaine ka boye min wata doya a plate? Na sanka da kirki shi yasa nace ko kaine ka boye min ita, ya ganeta tsab, sai yace ban gane ba au har girki kikeyi dama? Au ba kai ka cinye ba ? harara ya zuba mata yayi gaba tare da cewa ni gidana tare da Aljanu nake rayuwa maybe sune.sai yaga ita ko a jikinta Bata wani Jin tsoron Aljanu Mamaki ya kamashi yar yarinya karama da ita Amma Bata Tsoro lallai girman kauye ce.
Sabon shiri ya sake kamar baza a mutu ba, ya fito ya iske Shukura sanye da Jallabiyarsa Milk sabuwa dal ta saka masa ta wani jera girkinta a gabanta harda Fruits cikin karin safenta hhh kuma abinda ya bashi dariya da yaga danwake a gefe da safe haka,ita Bata iya girke girke ba sai na gargajiya sai doyar da ta koya wajen Saudatu shike nan,suma na gargajiyar kadan ta iya,duk Bata San illar zama daga ita sai namiji a gida daya ba,sabo da iyayenta basu nuna mata komai ba kawai abinda taga dama shi takeyi. iyaye Irin wannan ke jawowa kaga yaran wasu kamar dabbobi haka suke a cikin alumma.
Tsawa ya mata kadan keee...tayi mugun tsorata ita Bata saba ba,ba a yi mata tsawa, sai tagigice kawai ta fashe da kuka, Kuka take kamar ana mata azaba,lallai zaki bar gidan nan kuwa dan iskanci daga miki magana,kayan maza kike sawa baki da ilmi babu kyau mace nasa kayan da Akayi su domin Maza haka ma maza,Allah ya tsinewa mace me kamanceceniya da da Namiji, haka Namiji ma,sai kina shigar min Bedroom baki da hankali kina ebo min kaya.
Shukura wacce tayi mukus taji ance zata bar gidan,Ta turo baki cike da shagwaba kamar zata narke tace to ai lalurace tasa,kayana suna Hotel na gudu kudina ya kare,kuma bani da kaya shine na ranci naka ka daina masifa pls kudi Sun kusa zauna min kwana nan zasu zo zan biyaka abinka, kuma sai na siye gidan nan idan nayi kudi ya zama nawa gaskiya yayi min.
Dariya ma ta bashi daga taimako shine zata siye masa gida idan tayi kudi,mazewa yayi yace to karki kara taba min kayan sawa ta ya isheki haka,in ba haka ba wlh bulala zan siyo a gidan nan,Dariya tayi ya kalleta suka hada ido ya bata rai Irin karfa a rainashi,wayarsa ce tayi kara ya dauka Hello Momee gani nan Airport din zan zo yanzu,da sauri ya dauki hanyar barin Palon yace ke taso muje na siya miki kaya karki kara taba min kaya,da Karfi tace Allah da gaske kake? Kace wallahi tallahi? taga bazai kulata ba kuma yayi Gaba abinsa,Da gudu ta kwashe kayan abincinta ta kai Kitchen ta figi dan gyalenta ta yafa a saman kanta sanye da jallabiyarsa ta fito da gudunta,Jallabiya ta tadeta ta fadi tasan jiranta yakeyi amma sai ta fara kuka a wajen yanda ta saba yi a gidansu gaban iyayenta,ko kulata baiyi ba da Alama ba driver zai tafi shine a mazaunin Driver,da sauri ta kara mikewa a rude ta bude Bayan mota ta zauna maimakon ta zauna yanda ake zaman mota duk ta rude sai ta zauna takalli bayan motar saitin Boot kamar biri,kafafunta ta lankwashesu ta zubawa bayan titi ido ba gabansa ba,Ahleef bai san sanda dariya ta kamashi ba kawai bai kulata ba dan mugunta yaja mota a haka,sai dariya akeyi Sabo da duk motar daya wuce to sai Sun kalli fuskar Shukura ana ta dariya,Yana Sani ya fisgi motar tayo luuu ji kake guf ta bige keyarta da bayan kujerar gaba me zaman banza tunda dama baya take kallo.
Har airport yaje yayi parking sannan ya fito ya Shiga bayan motar kusa da Shukura,wata Igiya doguwa ya dauko,yace oya kwanta,a tsorace ta kwanta tunaninta saceta zaiyi ko dan yankan kaine dama Bata Sani ba ta kawo kanta.
Hannayenta ya hada biyu ya daure tam,Kamshinsa duk ya cika mata hanci Har hanci take kara budewa,Kafafunta suma ya hade ya daure sannan ya fita ya kulle motar yayi gaba wajen su momee.
Suhail su zasu koma Us schl,sunyi shirin barin kasar,Momee kuwa Abba yayi fushi matarsa tayi jinya an boye masa shi yasa yace da ita zai tafi yanzu yafi kula da abarsa sai nan da 2mnths zasu dawo kasar, Latifa da Niima kawai za a bari,sai Ahleef dake can gidansa,Sallama sukayi da juna a gurguje an fara screening ma, Shukura tana mota da kyar ta Samu ta Mike Zaune tana hango Momee suna magana Ahleef Sun kebe,wayyo taso Ace Ahleef bai daureta ba da sai taje wajen Momee ta gaisheta Amma ba damar hakan, Niima tana Airport din can gefe tare da sabon saurayinta Yazo wai zai yiwa iyayenta a dawo lfy, kishi ya kama Ahleef yasan dan ta kona masa rai ne yasa ta kira saurayinta,kuma kishinsa ya motsa da kyar ya danne Har su Momee suka tashi sannan ya bar wajen a fusace,yana zuwa fuska ba Rahma ya kwance daurin da ya yiwa Shukura yace fito ki koma gaba, lokacin da Shukura ta fito har zata shiga gaban mota akan idon Niima,kamar kiftawar ido sai ga Niima taja rigar Shukura da karfi ta fisgota baya,Shukura ga saurin zuciya da daukan Hukunci Bata tsaya sanin wace ko waye ba yar karama da ita amma ji kake Tasss ta kwashe Niima da mari me mugun Zafi Wanda saida marin ya jawo hankalin kowa aka fara kallonsu,Ashar Niima ta dura kafin tayi wani motsi tuni Shukura ta shige mota ta rufe tare da sauke Glass tana cewa ki kiyayi ranar da zamu kara haduwa wlh sai na miki Illa ba irina akewa wannan a kwana lfy ba ba a takani duk inda muke da mutum, kaf Abuja birnin tarayya kinga Wanda ya Isa dani ta furta tana Nuna Ahleef,shi kadai ne zai iya Sani ya hanani,shine me fada aji shi kadai zan iya kyalewa sai wasu Dattijai mata su biyu,(momee da Saudatu) Amma bayan wannan to babu Wanda ya Isa ya min na kyaleshi bare ke banza a banza gaja,kazama,yar Kauye dake ana birni amma an kasa wayewa ban hakura ba duk ranar da muka kara Huduwa wlh sai kin fada,me kai kamar murhu.Niima ta Sandare a jikin motar tana mamakin wannan yar yarinyar da Bata fi mate din Latifa ba Amma take ci mata mutunci haka ta window cikin mota take aiko mata da zagi haka,Shukura ta tsinke mata tunani da cewa da Allah ki dinga sallah akan lokaci ko kyayi kwarjinin musulunci gashi Sabo da baki da kwarjini kamata na kare miki zagi da gani addininki bai cika ba, kinga kawu Ahleef shi ko kallon banza ban Isa na iya yi masa ba,ke kuwa har mari kika sha to ki kiyayeni yarinya dan ba sanda a kusa ne da wlh sai na sumar dake da ita,wani farin ciki ya lullube Ahleef yau Shukura ta gama masa komai a duniya bai san sanda ma ya fara dariya ba dama yana neman wanda zai goge Niima shi idan yayi mata girmansa ya zube kuma ko Sabo da Momee tare da Abba baici ace yayiwa jininsu wani abu ba.
Niima ta girgiza da ganin me mugun kyau haka,dama ana samun irin wannan a kasar nan, To a ina Ahleef ya samota kyau irin na Ahleef Amma yarinyar kamar ma ta Fishi ita bata taba ganin me kyawun Shukura ba a duniya sai ko Ahleef,nan take Haushin Shukura ya kamata taji ta tsaneta Sabo da ta fita komai da komai,ita Niima Allah ya zuba mata Hassada Bata kauna wani ya fita,a ranta tace sai na gano yarinyar nan yar uban wace,kuma tana bakin ciki Ahleef ya samu me kyau irin wannan tafi so taga ya auri mummuna dan kawai kar ya ji dadin duniya,bata so ta Ganshi yana farin ciki shi yasa ma Bata damu sosai ba akan cin mutuncin da Shukura tayi mata,.
Ahleef ganin Niima ta koma wajen saurayinta cike da kunyar marin da Shukura tayi mata,sai ta tsaya tana nade borin kunya da hauka tana zubawa Saurayin Murmushi tare da rike hannunsa suna soyayya, Ahleef yaji haushi a kan titi ba mijinta ba saurayi kawai Amma Niima ta tsaya a bainar mutane yana tattabata harda su kiss,yana kallo yar Momeensa guda Zata lalace ba damar magana kawai yaja motarsa bai tsaya ko ina ba Sai wani Mall kato inda Saudatu ke Soya doya da kwai har wasu Sun fara siyar da Fruits a wajen, Shukura sai kallon wajen takeyi,Ahleef duk ransa ya jagule bama ya Jin zai iya komai,kawai Kudi masu yawa ya mikawa Shukura tare da cewa shiga nan ki siyo kayan sawa, Shukura ta fita dukkan mutanen data Sani saida ta fara tsayawa suna ta gaisawa ana wasa da dariya sama sama,Ahleef yana cikin mota yana kallonta yanda take Faran faran da mutane yana mamaki duk ina ta sansu haka,Sai tambayarta akeyi ina Saudatu? Shukura tace ta canja unguwa ne, Haka ta shiga Mall din abin haushin tana yin layin kayan ci da sha da kayan girki sai ta manta da kayan sawa yace ta siyo, chocolate,Biscuits su snacks iri iri kayan zaki ta kwaso,tayi layin kayan dafawa Ko Bata sanshi ba indai ya birgeta sai ta siya,ko idan taga Hoton tukunya a jikin ledar, Ice Cream iri iri, taga yogourt tace laaa bamu da irin wannan a fridge dinmu nan ma ta kwasa,harda su markadaddiyar gyadar gongoni tace wannan da gani zatayi dadi da Bread, side din Drinks taje nan ma taga wata katuwar kwalaba tunaninta lemo ne ashe giya ce duk tsadarta Sabo da kwadayi da son dadi saida ta siya,karshe taga wani wajen Shawurma da ake yi a ciki ta siyo abinta,sai data kashe kudin wajen kayan ciye ciye sannan taje side na kayan kwalliya ta kwaso iri iri babu duhun kai duk abinda Bata gane ba sai ta tambaya an wayar mata da Kai,Sai data gama sannan ta tuna me akace ta siya,a fili tace ai wlh gwara kayan dadi abinda zanji dadi akan wasu kayan sawa,ai da ragowar kudin bari na siyi kala biyu sun isheni kafin nayi kudi ai na kusa zama me kudi.
doguwar Riga ta dauka da Riga da skert Engliish wears sai panties guda biyar,da wani 3qutr tight legins,sai flat shoe kala biyu tace Sun isheni zaman duniya bana kiyama ba taja kayanta takai ta biya Kudin sai dubu uku ce ta ragu change,tace kai bani abin dadi na sauran Canjin babu Awara da kwai a nan ne wai ? Dariya me auna kaya yayi sosai yace babu Hajiya,tace to Kantu me sugar fa ko na gwangwani babu ? Yace sai Snail da frog na gwangwani abincin yan China ne,ido ta zaro tace kwado da dodon kodi ? yace ae,musulmi suna ci ? Ya halatta ? Yace sosai ma ai abin ruwa ya halatta,tace da dadi ? Yace sosai ma, tace to bani Snail kawai banda kwado bana sonsa,yace kin San dadi yafi dadi musamman kika hada shi da vegetables yasha miya me kyau,tace ka hado da ganyan miyar,Mutumi dai ya bata snail da wani ganye kala uku na turawa da suke girki dashi,Ahleef yaga ana ta fito da ledoji kawai boot ya bude aka zuba komai sannan ta zaga ta shiga suka tafi sai murna takeyi kamar zata tashi sama.
tsoro ne ya shigeta ganin yanda yake tuki ransa a bace kamar an aiko masa da mutuwa sai tsaki yake ja,shuru tayi itama Bata ce komai ba,tunaninta ma ko ita tayi masa laifi a hankali tace ko Budurwarka ce na mareta ban Sani ba ? Shuru bai kulata ba,to ko kanwarka ce ? Da kyar yace Budurwa tace,baki ta bude tace Allahhhhh.... Sarki yi hakuri ungo kumatuna rama mata marinta,Dariya ta bashi sosai,tace ka rama mata mutum yana ci da kai ya baka wajen kwana,Sutura ka Isa ka Bata masa maza dalle ni da mari,dariya ya shiga yi nan take Ya koma normal cikin farin cikin da ya dade rabon da ya samu,tace gaskiya Budurwarka Bata Sonka kana gani sai kula wani takeyi yana yi mata abin cikin Film din turawa amma kayi shuru gaskiya mijin tace ne kai,mijin Hajiya ka bada maza, murmushi yayi kawai, Kallonsa takeyi yanda yake me mugun kyau kamar Saudatu musamman idan yayi dariya, yee...wlh irinku daya da wata Tsohuwa me saida doya,juyowa yayi ya dan kalleta ta kwalla da karfi Yeee wlh Saudatu ce kai, Dan kara yin dariya mu gani ? Yaki yi,Shagwaba ta fara dan Allah kayi kaji Kawu Ahleef,har kwakwalwarsa saida tayi wani dumm yanda tayi shagwabar, Yana tuki ta bigi kafadarsa kadan ya sake juyowa suka hada ido ta kyalkyale da dariya tace Saudatu ce wlh, baki ya tabe tare da cewa ki daina hadani da wata yar tasha me doya kinma rainani ki rasa wacce zaki ce muna kama sai me soya doya a titi,Kai wlh ba yar tasha bace mutuniyar kirki ce mace ta gari kuma kyakyawa balarabiya baka ji larabcin da takeyi ba, Ahleef yace koma me takeyi ina ruwana,Dan Allah karka ciwa Inna Saudatu mutunci wlh yanzu nafi sonta a duniya bani da kamarta,ina ma zan ganta da a gidan dadi take wajenta zan koma ta rikeni,Oh sai gidan dadi ke kike so ? Wlh kuwa to bakina ya saba da dandano taya zan so wahala ai sai dole.uhmm kawai yace Jin yanda yar karama da ita ta iya zance haka.suna zuwa gida yayi parking yace to Saudatu muje,Dariya tayi tace suna na yafi na Saudatu dadi wannan na tsofaffi ne, Saida ta kwashe komai ta shigar dashi zata boye yace kawo sai naga me kika siyo nan fa kuma tayi miki miki tana zare ido tace ni dan Allah tunda Sabo da Allah ka taimakeni basai ka gani ba, U are Crazy dalla miko na gani a tsawace ya furta,da Sauri ta dauko komai ta jera a gabansa ya shiga Dubawa,mamaki ya cika shi ganin kayan da suke cikin ko wacce leda,bai San sanda ya kama kunnenta ya murde ba cike da bacin rai kara ta saki sosai ya murde da karfi,ya zuba mata rankwashi yafi biyar masu zafi sannan ya saketa tare da tureta gefe saida ta fadi kasa,Kuka ta zauna tana ta yi a wajen tana ni nafi son kayan dadi kawai kace kayan sawa zan siya, kuma ai kala biyu Sun isheni,Kwalbar giyar ya dauke yace wannan fa Alcohol ce kika siyo,Shuru tayi tana kallo tace to meyasa suke siyarwa idan ba tsinannu ba ni na Zata abin dadi ne ma,giyar kawai ya dauke yace kwashe tarkacenki ki bar min palo,tace nima ai yar gidance palonmu zaka ce abinda na kusa siye gidan ma baki daya,ki cire wannan hakorin makkah naki na karya,wlh bana karya bane kuma ba Makkah zaka ce ba Makoki zaka ce Sabo da zuwana makkah sau bakwai ba daya ba kaga ya wuce Makkah sai makoki, nifa yar me kudi ce ka daina ganin kai wani me kudi ne, Babu me kudin babana a garinmu.Harara ya watsa mata yayi Gaba abinsa ya haura sama tare da zubar da Alcohol din ya jefa kwalabar a Dustbin.
Saudatu har yau kullum sai taje kofar gidan Alhj Dauda tana Jiran Ahleef amma Shuru bai zo ba har ma ta cire rai yau katsam tana zaune ita da mijinta sai ga Ahleef cikin zugar motocinsa tare da Escort Sun bashi tausayi ganinsu a rakube gefen bishiya da sauri ya fito daga motar katsam Saudatu ta Ganshi Murna kamar me haka Alhj Amadu sai yau ya fara ganin Ahleef Shi kanshi sai yaga suna kama da Matarsa Saudatu kadan amma bai kawo komai ba Sabo da ya manta ma Sun taba Haihuwa, Cike da ladabi Ahleef ya gaishesu tare da cewa ya na ganku a kofar gida? Saudatu tace ai tun ranar da kuka tafi suka Sallamemu nan ta labarta masa komai,Ahleef yace ku shiga mota muje kawai,Bayan Sun shiga mota yayi tunanin ya kai Dattijuwar da yake kira da Umma gidansa su zauna tare da Shukura sai yayi tunanin ai kwanan nan Shukura zata tafi ba wani zama zata yi ba, sannan baya son Zargi kar Umma da mijinta taga Shukura budurwa ta dauka ko karuwarsa ce yana kare mutuncinsa a ko ina,Momee dama tana neman me dafa abinci dattujuwa Sabo da Latifa tare da Niima Me musu girki tayi aure ta bar gidan Momee kuma Bata gari,Alhj Amadu kuma da yasa masa suna Baba zai dinga share masa Office da gogewa etc,Gidan Momee kawai ya wuce dasu,sannan ya bugawa Momee da Abba waya ya sanar musu da komai,Part guda karami komai akwai a ciki har kayan sawa dama Ahleef ya tanadar musu babu wani abu da zasu nema su rasa na amfani a bangarensu,Duk ya nunawa ma'aikata su sannan ya daga darajarsu fiye da ko wanne ma'aikaci dake aiki karkashinsa cewarsa su tsofaffi ne baza suyi aikin wahala ba, Latifa ma Ahleef ya hadata dasu Saudatu, ba laifi ta mutuntasu,Niima ma bai fasa ba sai da yace ga me dafa musu abinci,Alhj Amadu kuma a Office dinsa zaiyi aiki.
Ganin Ahleef yana son su Saudatu kuma ya daga darajarsu yasa ita kuma ta tsanesu zasu kara mallake musu iyaye da dukiya,gashi ma taga Saudatu da mijinta suna yanayi da Ahleef sannan mutanen kirki ne kowa Sonsu yake kawai sai ta tsiri wulakantasu,duk wulakancin Niima rabin kafar su Hafcy Bata kama ba, Sai Saudatu take ganin ma ita ai me kirki ce akan su Hafcy Amma duk da haka Bata kaunar Niima a ranta duk da Wulakancin su Hafcy haka kawai sai taji gwara mata Hafcy akan Niima,Ahleef yana gidansa amma yana yawan zuwa ya tambayi Saudatu ko Amadu idan Sun hadu a office ko suna da matsala Ko wani yana yi musu wani abun sai suce ba komai wlh lfy suke.
Shukura tunda ta siyo kayan zaki su kawai take ci kullum Bata dora tukunya dama Bata iya girki ba,tunda Ahleef ya murde mata kunne bai sake ganinta ba a daki take zama yawanci,sai yau ta fito 8pm yana palon kasa yana kallon American film,can nesa ta zauna tana nuku nuku sannan tace Sannu Kawu,Dan Allah Kawu Ahleef....ki daina ce min Kawu nifa ba dan kauye bane kuma ba Tsoho ba,to General Ahleef...yace Soja ne ni ? to Alhaji,yace No,to Sir ? Sir Ahleef ya kaji ? dama dama ya furta yana tabe baki,to dan Allah dan bani rancen dari biyar,Ba musu ya zaro Ya mika mata ta Mike da sauri tare da cewa ina yin kudi zan baka kaji? to kawai yace mata tunda yaga Kuruciya ce ke damunta baka fita Ko ina ba kana kwance kudin zasu sameta.
fita tayi me gadi da kyar ya bude mata shi tunaninsa ma kanwar Ahleef ce yanda take nunawa kamar gidanta.
always pad dinta ta siyo guda daya ragowar canjin ta siyo Bounty chocolate ta dawo tayi Sallama ta wuce shi,shi bai kulata ba Computer yake latsawa.
muryarsa taji yace kawo ledar mu gani ba tare da ya kalleta ba, ba musu ta mika masa,ya duba ya gani yace karba abinki.
AsmaBaffa
[7/22, 1:12 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
8
Official
By
AsmaBaffa
MAMAN FATEE and MADINA ALIYOU wannan page naku ne Sabo da Jin dadinku.
Tana karba ta wuce Bedroom abinta bata fi 15mnt ba sai gata ta fito again tana so itama tayi kallo,Romantic film yake kallo yana ganin ta zauna a Palon tana ta shan Bounty Chocolate dinta sai ya canja Channel ya mayar bangaren News kawai, bata ce komai ba taci gaba da harkarta yana tasa Shima,Wayarsa tana kusa da ita ta fara ruri kallon Screen din tayi taga Farhan,hannu ya mika mata ta bashi wayar,mika masa tayi ya daga tare da sallama cike da shegen iyayi dinsa yace How Far ? Farhan ta waya yace baka da kirki wlh ace na dawo ina kasar amma ko ka shigo Ko Mamma ai kazo ka gaisar amma shuru tace tunda na tafi Qatar baka zo ba,am so sorry ina busy ne wlh ka Sani,ok kana gida yanzu zan shigo kuma kwana zanyi,gaban Ahleef ya fadi kar Farhan yaga Shukura me zai ce masa, Da sauri yace da daren nan Almost 9pm ka bari sai gobe,Ok Allah kaimu gobe cewar Farhan.
Ajiyar zuciya ya sauke sannan sukayi Sallama sai yanzu yaga Shukura Bacci ya kwasheta tuni saman Kujera a zaune, Har ya gama aikinsa Bata tashi ba,zuwa yayi da niyyar tashinta sai yanzu ya kare mata kallo gaskiya ta hadu ya furta a hankali, gashinta ya kalla Wanda ya kwanta a goshinta,kafa yasa ya bigi tata kafar kadan Shuru taki tashi yayi ta tashinta amma sai dai ta turo baki taci Gaba da baccinta,kyaleta yayi shi bazai iya daukanta ba gaskiya kawai ya kashe light yayi tafiyarsa ya barta nan zaune tana bacci abinta,wanka yayi tare da shirin bacci har ya kwanta ya tuna a zaune take bacci,Yana tsaki ya sake sakkowa kasa tare da kunna Light ya dauketa kamar jaririya yana kallon fuskarta yaji Bata da nauyi ko kadan,Bedroom dinta ya Shiga komai tsab Neat amma ko ina Sweet ne a zube,saman Bed din ya tsaya maimakon ya kwantarta sai ya cillata saman gadon da karfi kamar wata Bag,Amma ido kawai ta bude a hankali ta rufe taci gaba da baccinta,Sweet din da sauran kayan zakin ya kwashe kaf ya fita dasu ya boye a Bedroom dinsa ya kwanta tare da addua sai bacci.
Hafcy da gaske Son Ahleef ya kamata me zurfi,bata da aiki sai tunaninsa duk ta fita daga Hayyacinta,Tun tana boyewa har abin ya gagara,Zahra ma hakan take domin ita har wata rama tayi ta daban,Number din Ahleef ta sata a wayar babansu ta shiga Dialing ringing din duniya tayi amma baya daga ko wacce number sai yana da business da kai,haka ta zage ta rubuta masa text kamar haka
Hlo Handsome Hafcy ce yar gidan Alhaji Dauda pls idan kana da time ina so muyi magana,Ahleef yana ganin text din ya goge komai,Hafcy ana jiran Ko kira ko feedback amma Shuru kake ki, Zahra ma haka tayi masa amma ba labari,Hafcy ta gaji kawai ta sanarwa Babansu,Alhj Dauda yace ta bari sai Abba ya dawo daga tafiya zaije da kansa a hada su aure da Ahleef dole,Sabo da haka sai Hafcy ta samu kwanciyar hankali,Zahra tana Jin lbr tace Sam ita ke sonsa nanfa fada ya kacame tsakanin Hafcy da Zahra,Babu irin sasancin da iyayen basuyi ba amma sunki dainawa har suka kulla gaba me tsanani tsakanin Zahra da Hafcy,Mama tun abin baya damunta har yazo ya dameta haka Alhj Dauda ma hankalinsa ya tashi Jin Hafcy ta dauki wuka zata kashe Zahra Allah yasa aka kwace da kyar.
Gaba daya gidan yanzu basa zaman lfy sai fada duk akan Ahleef dan Saudatu.
Niima dawowarta kenan daga Office amma tun daga waje take kwalawa Saudatu kira ba wani mutuntuwa Saude...Saude kawai take cewa,Saudatu ta fito cikin nutsuwa tare da cewa Hajiya gani dai dai lokacin Ahleef ya Dauko Shukura Sun taho tare yana so ya cusawa Niima haushi sai kuma suka iske tana yiwa Saudatu rashin mutunci, tsayawa kawai sukayi a baya,Shukura Bata gane Saudatu ba Sabo da ta juya bayanta kuma tayi kiba da kyau sosai Alamar Saudatu tana Jin dadin gidan, Niima tace ke Saude me kika dafa Allah yasa dai ba irin naku abincin na mutan kauye kika yi min ba, tsawa ta buga mata dake nake fa,jikin Saudatu ya dauki Mazari tace Je ki duba Hajiya idan baiyi ba sai a sake Sabo,Tsaki taja tare da cewa naje fa kikace Common dalla je ki kawo,Kitchen ta shiga ta fito dauke da katon tire lemon Niima ta Dauka tare da watsawa Saudatu a fuskarta tare da furta Stupid,lokacin Shukura ta tabbatar Saudatun tace ai kafin kiftawar ido ta kwashe Niima da maruka har biyu karo na biyu, zuciya tazo mata iya wuya an wulakanta Saudatu Bata San ta ina tayi karfi haka ba nan ta Kwashe kafafun Niima ta fadi kasa tim,kanta ya kwalu da tiles jikake kwal ta kuma haye saman Niima ta rufe ta da duka ta ko ina,yakushi Da cizo Saudatu tana jawo Shukura wai ta bari,Ina ai dayan lemon ta dauka ta juyewa Niima a jikinta,ta dauki dukkan stew din Allah yasa ma ba zafi ta juye mata a kirji,Bata hakura ba ta ja rigar Niima ta yagata gida hudu sai bra dinta ce ta bayyana, da kyar Saudatu ta janye Shukura daga jikin Niima wacce a yanzu kamanninta Sun sauya Sabo da yakushi da cizo ,Ahleef yana kallo harda harde hannaye yau Shukura tafi kullum birgeshi bai ma san kyautar da zaiyi mata ba, Waya ya zaro tare da Kiran Momee ya sanar da ita iya abinda yaga Niima tana yiwa Saudatu,Momee taji Haushi ranta ya baci,Abba ta sanarwa,lokacin Niima tana ta ihu da zage zage tace saita salwantar da rayuwar Shukura sannan ta fada Bedroom da kyar,Momee da Abba ne suka kira Niima a waya suka mata tatas,Abba yace idan har kika kara Niima zan cireki daga jerin yarana,hakuri ta bawa Abba da Momee kamar gaske ta daina.
Shukura ta rike Saudatu tace Sannu Inna kina hakuri,Sir ga Saudatun dana ke baka labarinta, Inna kinga dan uwana na ne wannan a gidanshi ma nake zaune yanzu,ko zaki zo mu koma can da zama? Kiyi hakuri da abinda wannan tayi miki,Ahleef dai yana kallonsu Har Saudatu ta sanarwa Shukura irin taimakon da Ahleef yayi musu kaf, Ita kuwa Shukura tace dama dan uwanta ne,yanzu kin daina doyar ? Saudatu tace yaron kirki Ahleef yace ba sai na wahalar da kaina ba, Nan sukayi ta hirar bayan rabuwa,Ahleef yace Momee ta tsawatar inshaallah ba abinda zai kara faruwa,Saudatu tana murmushi tace ba damuwa Allah ya saka maka da Aljanna, yaji kan mahaifa,Shukura dai hakuri ta kara bawa Saudatu akan abinda ya faru dazu, Saudatu sai albarka take sawa Shukura da Ahleef,Shukura ta kalli Ahleef ta kalli Saudatu haka takeyi wai kama sukeyi sosai,gefe taja Ahleef tace ko na dawo nan da zama? No baki Isa ba ki gama kwanakin ki bar min gida kawai,lets go bazan rikeki ba idan ma kika dameni korarki zanyi baki daya,Baki taja ta tsuke tace Inna zan dinga kawo miki ziyara duk Wanda ya tabaki ki fada min zan gyara musu zama,Dariya Sukayi gaba daya harda Ahleef ya murmusa.
Sallama suka yiwa Saudatu Ahleef yace daga yau kin daina aiki a gidan Umma ki koma part dinku da zama akwai komai a part din na abinci ki dinga yi ke da Baba kawai shine zaman lfy mun gama magana ni da Momee tasan komai kuma duk abinda ya faru karki ce zaki bar gidan ki sanar min zan canja muku wajen zama,Saudatu tayi Godiya ta wuce part dinsu ta iske Mijinta yana hutawa ta sanar masa komai shima addua ya shiga Zubawa su Ahleef.
Shukura tana tsaye ya kalleta fuskarsa dauke da Nishadi marar misaltuwa,Shi yasan bazai iya yiwa jinin Momee komai ba amma ga Shukura tana masa abinda ya dace ba tare da ta San komai kansa ba, kuma tana birgeshi wajen daraja dan Adam koya yake kuwa.
Kanta ta dago a hankali suka hada ido ta dauke kanta kana ta kara kallonsa suka hada ido again da sauri ta sadda kanta kasa ta kara dagowa nan ma idonsu ya sarke dana juna murmushi suka sakarwa juna sannan ya riko hannunta karo na farko, tun daga Palon yace yau fadi duk abinda kike so na baki shi,Shuru tayi ta nutsu sannan tace indai na fada zaka min ? Yace ae tace to daukeni ka shillani sama ka cafe dama na dade ina so na samu me karfin da zai min,Baffana ne ke yi min tun ina yarinya har na girma yanzu kuma ya rasu na dade ban samu anyi min ba...ba zato taji Ahleef yayi sama da ita kamar tsinke yayi mata yanda ake shilla yara ana cafewa kadan sannan ya direta a kasa,sai ga Shukura tana dariya tana hawaye wai ta tuna da Baffanta da Innanta da suka rasu,tun tanayi kamar wasa sai ta koma kuka gaba daya sosai take shesheka,ya danji tausayinta amma nata da sauki tunda taga gawarsu,shi kuwa bai san nasa ba ko daya.
kasa ce mata komai yayi har tayi kukanta ta gama sannan yace muje to,wani haushinsa taji wato shi bai iya lallashi ba,mota suka shiga suka dauki hanyar gida.
yau wani nishadi yake ji Shukura tayi masa abinda ya dace yayi Wanda bazai Iya Sabo da Momee da Abba,kida ya kunna me masifar dadi Shukura ta kama abin rigarta wani zare tasa a baki tana wasa dashi,Muryarsa taji yace me zaki ci yau ya fuskanci Bata wani iya girki ba kullum kayan zaki take ci,juyowa tayi ta kalleshi cike da murna, ba kara min kyau tayi ba, shi kanshi saida yayiwa Allah tasbihi,da sauri tace komai nake so na fada ? Yace yes, tace Allah ? Rantse kace Allah,ba zan rantse ba ni yaro ne ko dan Kauye ne cewar Ahleef, Shawarma da Pizza sai Madara me kwakwa,idan da chips and Egg ma zanci,yawwa na tuna fried rice da kaza itama kafin na kwanta zanci kaji ? Duk Wannan gurmin a cikinki zaki hada su yau ke kadai? To Bazan siya ba, shagwaba ta fara masa kaifa kace na fadi abinda nake so kuma na fada zaka ce a'a kawai ku dama yan boko haka kuke Alkawarinku ba cikawa sai dai ayi ta turanci,dariya ta bashi sosai Murmushi yayi yace Oho miki Bazan siya miki ba, kala daya zan siya ke ko lafiyarki bakya tunani,yana magana tana kallon lips dinsa tare da hakoransa,har ya gama ta tsura masa ido har sai da ya bigi sitiyari kadan sannan tace Allah kamar Saudatu ne kai, Harararta yayi kadan ke kuma me kama da Musa Driver na,Dariya tayi tace Allah ya kiyashe ni harda da yin maganar fulani hodi Jam wannan Driver naka me suffar yan ruwa,Murmushi yayi kadan shi zan aura miki ai nan gaba shine dai dai ke, glass dinsa ta dauka a wani waje cikin motar ta manna a fuska sai ya mata mugun kyau abinka da farar fata,ko da yazo inda zasu siya abinci haka ta fito da glass dinta sai kallonta akeyi yanda tayi kyau ka rantse yar wani Hamshaki ce,hannunsa ta rike Sabo da Bata taba ganin hadadden waje iri wannan ba sai taji tsoro ma, Mutane suna jinta tana wlh kamar a London,Sir kalli can naga irinsa a Makkah,ta daga kanta sama tace laaa ha ila kaga irin na film din nan wajen da akayi naushi aka Harbe yaran Boss irin saman wajen ne,wasu da yawa nan suka gane Shukura daga kauye aka zo amma a jikinta babu me ganewa,Ahleef ya take mata kafa da tasa tayi kara yace idan kika kara magana baza ki koma gidana ba a nan zan barki, Shuru tayi Bata kuma cewa komai ba har suka fito ta hango wani Building na Makeup cikin rada wai kar ta disgashi a mutane ta fara yafito shi da hannu wai ya sunkuyo zata yi maganar sirri,Ya dan duko kadan tare da mika mata kunne daya duk da haka saida ta dage kafafu sannan bakinta ya kai kusa da kunnen sa tace dan Allah can wajen ai gidan kwalliya ne ko ? Gashi nan Ansa Make up,Makeup kuma da hausa ai kwalliya kenan,ae kawai yace tare da mika ma plate din yace ta zabi abinda zata ci a zuba mata,ta dinga nunawa komai sai da ta nuna ana zubawa a gefe sannan yace tazo suje su zauna,Sama suka hau inda aka tanada na zama aci abinci,sai ta kalli plate dinta taga kalar abincin Ahleef daban da ya ebo babu shi a plate dinta,to ya akayi ita Bata ga wannan kalar ba gaskiya ita baza ta yarda ba kuma nasa zaifi nata dadi,Lemo ma kalar nata daban data zaba,kallon plate dinta tayi ta kalli na Ahleef,yana satar kallonta dama yana Sani yasa aka bashi special Wanda ba a wajen yake ba a kasa suke ajiyesu sai in ka karanta Menu nasu zaka San dasu,tana kalle kalle aka zuba masa Bata Sani ba.
sai kallon plate dinsa takeyi taki cin nata,yayi kamar bai ganta ba, ta fara cin nata sai ta tabe baki tana yatsina fuska,ta ja tsaki tana cakalkalashi a bakinta tace naka da dadi ? Yace kamar kunne zai cire,tace to ni nawa ba dadi dandana kaji,baki ya tabe ke kika zaba, to ni ya akayi banga irin wannan ba? Shuru ya mata yana jinjina kwadayinta,lemonta ta dauka ta kurba nan ma ta tabe baki tace baka ji ba kamar fitsarin jaka Allah basu iya komai ba, Shuru ya mata yana dariya a ransa,ta kalleshi ta kalli plate dinsa tace kaci a hankali ni ba ci maka naka zanyi ba, Murmushi yayi kawai yaci Gaba da cin nasa itama tana dan cakalar nata,taga da gaske cinye nasa zaiyi ba tare da ta dandanashi ba,Nata ta ebo kadan a Spoon tace dandana kaji to nawa,kai ya girgiza baya so,Ina Brush fa Allah kullum sau Uku kalli hakorana,na Sani ya furta,tace to San min naka naji kalarsa,plate din ya tura mata da ragowar kadan a ciki, ta cinye tas sannan ta kara jawo nata kalar ta cinye abinta,Lemo yake korawa tace sai ya San mata nasa taji irinsa,da kansa ya daura mata a saman lips wai tasha kadan.ta zuga da karfi zuuuuuuu har ta kusa zukeshi ya fisgo abinsa daga bakinta yaci gaba da sha.sai da suka gama sannan suka dauki hanyar gida abinsu.
Kwanaki kadan ba laifi tsakanin Shukura da Ahleef suna dan hira sama sama idan ta kama, yau ma 5pm Cikin kana nan kaya black jean da top Brown ya gaji da haduwa ya shigo a gajiye daga Office ya dawo,yana bude palo wani kamshi da sanyi ya dakeshi bai san sanda ya lumshe ido ba,Samansa ya Haura anan yaga gyara iya gyara yasan Shukura ce tayi,wanka yayi ya shirya Cikin 3qtr da riga Armless ya sakko kasa a gurguje nan ya iske Farhan har ya iso cikin shigarsa ta alfarma na Light blue Shadda,ya wani baje saman 3seater Remote a hannunsa yana chanja Channel na tv,Ahleef ya mika masa Hannu suka kashe sannan shi kuma ya dauki Remote na ac ya karo karfinta,Farhan ne yayi magana Cikin salonsu Guy kana hutawa fa wannan gida naka kamar me mata komai na daban,Murmushi kawai Ahleef yayi yana tunanin idan Shukura ta fito Farhan ya ganta taya zai wanke kansa duk da yasan Shukura yarinya ce me zaiyi da ita shi sai yar 25 zuwa sama kuma Farhan yasan da hakan.
kitchen Farhan ya shiga ya ebo kayan ci snacks da sha sannan ya dawo ya zauna suka fara hira irin ta zaratan abokai masu ji da kai, 15mnt tsakani sai ga Shukura ta bude kofa ta side dinta ta shigo Palon sanye da rigar Shaddar Ahleef ruwan toka Bata sa wandon ba sai rigar tazo mata har kasa tayi Rolling da bakin gyalenta na doguwar riga dan siriri,da gani wanka tayi ta shafa powder kawai da lipgloss,sallama tayi musu tare da gaisar da Farhan,cike da mamaki ya amsa,Ahleef kuwa tuni ya runtse ido yana tunanin amsar da zai bawa Farhan,saitin kafar Ahleef ta zauna a kasa zata yi magana sai taga Farhan yana ta faman kallonsu,sai ta fasa tace pls 2mnt zan ganka ta fada kasa kasa,Ahleef ya dan duko da kansa saitin nata yace fada min bazan iya tashi ba, Cikin rada tace 1k zaka ranta min,yau ma baice komai ba ya zaro ya bata,ta mike suna gani ta bude kofar tayi waje da Alama wani wajen zata je.
Farhan yace kutmar kai dan uwarka yaushe ka koma haka? Ina ka samota kaf dangin Momee da Abba ba irin wannan, kai kuma baka ma san iyayenka ba bare wasu danginka to ina ka samo ta, Harara Ahleef ya aika masa tare da cewa nasan haka zaka ce dama amma kafi kowa sanin halina wlh ba abinda ke tsakani na da ita,nan Ahleef ya bawa Farhan labari tun farkon ganinsa da Shukura har zuwa yau bai boye masa ba, to tunda kace iyayenta Sun rasu why not Muje kauyensu kawai ayi muku aure kaga wannan tafi Niima nesa ba kusa ba,da Alama kana sonta,wani bala'i da masifa Ahleef ya shiga yi shi ba soyayya Allah kiyaye masa daga ya taimaketa to takusa bar masa gida ma, Farhan yana dariya yace to tana birgeka Ko ?Naga ma kayanka take chakarewa a ciki wow.. Nan ma ya fara masifa. Farhan yace zuki amma fa karshe ce wajen haduwa kamar ba India wlh,kun mugun dacewa me kyau da me kyau, Tsaki Ahleef yaja yayi shuru yana latsa waya, Shawara Idan ba so kake shedan yayi tasiri watarana a kanku ba ka dauke yarinyar nan idan zaka taimaka mata ka kaita gidanku can wurin Momee wlh Amma nan irin wannan balarabiya haka shedan zai iya galaba watarana,kuma a addinance bai dace ba,babu ma tsari Sam cewar Farhan, Ae ai zan sallameta next wk gaba daya ma ko Bata da wajen zuwa ba ruwana dole ta bar min gida.
Farhan yace a'a gwara a maidata kauyensu idan ka koreta baka kyauta ba tunda Bata da wajen zuwa,tunda baka sonta ni ina sonta sai na kaita wajen Momee nasan zata rike min ita tunda Sun San juna,baki Ahleef ya tabe yayi shuru bai ce komai ba.
20mnt sai gata ta dawo da take away na jullof rice taji hadi ta wuce Bedroom taci abinta ta fito hannayenta biyu sanye cikin aljihun rigar yanda maza sukeyi haka tayi itama ta fara yin irin tafiyar Ahleef kamar wani Sarki har gabansa tazo ta fito da 200 Naira canjinsa ta zaro tare da mika masa,Dariya ce ta kwacewa Farhan yace ya sunanki? Tace Shukura ban taba ganin abokinsa ba sai yau,Farhan me saurin Sabo sai gashi har suna yar hira da Shukura sama sama ta zauna a palon,Ahleef yace kasan anyi bikin Yazeed kuwa? Ae naje gidan sa ma na masa murna,matar tasa ce Sam Bata da kirki Bata iya muamula da mutane ba,Shukura ba da ita ake zance ba Zaraf tace Marinka tayi? Farhan yace sai da kumatuna ya kumbura,tab amma babba da kai sai ka tsaya baka karyata ba? Tafi karfina cewar Farhan,tayi Murmushi tare da cewa yan boko basu da karfi ai dama,amma da agarinmu ne kaga Shatu dai Bata da karfi Ko to sai ta zane irinku yan Birni,Dariya Farhan yayi yaji shirmen kuruciya Bata fuskanci me yake nufi ba.
Ahleef yace Shukura... karo na farko, sai da taji wani yarrrr a jikinta,da kyar ta iya cewa Naam, yace ga Frnd dina nan idan zaki aureshi yana sonki,yaushe zakiyi aure ? Shukura kunya ta kamata ta tace da dai Inna tana da rai ne sai aje a tambayeta yaushe zasu yi min aure,ta furta tare da rufe ido tana murmushi,Ahleef ma murmushi ya saki yace to idan kin shirya aure ga abokina yace kina da kyau kin masa,idan zai dinga siya min kayan dadi to zan aureshi ta Mike ta bar wajen da sauri ta koma Bedroom dinta wai kunya.
Farhan ransa idan yayi dubu to ya baci abinda Ahleef yayi masa a gaban yarinya,a ransa yace amma tunda yayi masa haka shi kuma yanzu zai karbi soyayyar nan da gaske kuma wlh indai tana sonsa auranta zaiyi tunda yayi masa haka,a fili yace Good for u, ni zaka yiwa haka a gaban yarinya zaka zubar min da mutunci,ko sonta nakeyi haka zan fada mata direct? Idan kaine zanyi maka haka? Fine ni kuma da gaske zan fara soyayya da ita ka jira gobe ta shirya zanzo zance,Ahleef ya kalleshi yana murmushi yace kaifa kace kana sonta ni kuma na hadaku shine nayi laifi dama dan ka sota ka aureta na hadaku,tunda kace kana sonta gida bai koshi ba za a kaiwa dawa ba,Kullum ma kazo zance kuma zan kai maka ita gidan Momee ta rike maka ita ka aura,Farhan yace to dan Uwarka ka kaita ka gani kuma ina nan zaka zo kasameni banza dan iska, Ahleef yace kaine dan Iska daga ganin fara me kyau shike nan mayen mata,ni kasan yanzu ba abinda zanyi da mace ko a kafa aka daura min ita sai dai na kaita bola,Girgiza kai Farhan yayi yana dariya dan abin dariya ya bashi,Ahleef da baya surutu sosai amma shine daga zance daya akan yar magana ya hakikice haka lallai zai koya masa hankali.
tashi ka tafi malam dare yayi,korata kakeyi ma yau kenan to dama kwana zanyi ina kallon Matata tana zirga zirga, dariya Ahleef yayi yace ga bedrooms ka zaba Wanda kake so me mata na Shukura ikon Allah, Kallonsa Farhan yayi kawai ya Mike ya fita bako sallama ya bar gidan.
AsmaBaffa
[7/22, 1:12 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
9
Official
By
AsmaBaffa
Pls Wanda sukayi Sharhi suka ga banyi reply ba SMS nasu waiting yasa min ayi min hakuri da Uzuri kuma aci Gaba da Sharhi dan Allah fans.
ZAINAB ATIKU SALAMA, AUTA and MAMAN MEENAL this page is for u Sabo da Jin dadin Sharhinku.
KHADIJA A HAMZA da JANNAT jinjina da godiya me yawa.
Washe gari da safe Sunday Ahleef yana gida,Shukura taki yarda ta fito karma ya ganta wai kunya take ji akan maganar Aure da yayi mata tun jiya,tana so ta fito amma ta kasa gashi yana Palon,Leko da kanta takeyi sai ta koma da sauri tana yarfe hannu ita ya za ayi yau ta kalli Ahleef, yau ji take baza ta iya yini a gidan ba, gwara ta fice yawonta har sai dare ta dawo, fuskarta ta rufe da gyale yana Palon sai gani yayi Shukura ta fice da gudu tayi waje,ya tsorata domin kamar wacce Aljanu suka tasar mata,tana fita kamar yanda take yawonta da haka ta dinga yawo a kafa tana hutawa har Dare yayi,ta dauki hanyar komawa,tana kusa da layin sai ga Farhan ya shararo motarsa zaije wajen Ahleef, kallo daya yayi mata ya gane itace,slow yayi tare da sauke glass ya danna mata Horn ta juyo,sai da ta kalleshi ta gane kuwa shine kawai sai ta rufe fuska, yace tazo ta shiga mota taki yarda sai ma sauri data kara tana tafiya yana binta a mota,babu rokon da baiyi mata ba amma taki shiga sai da kyar ya samu ta Shiga, Ahleef kuma yana gida hankalinsa ya tashi yaga tun safe ta fice da gudu kuma har dare babu labarinta karfa Ko wani abu ya sameta,yana samansa jikin window kawai compound yake kallo, Farhan aka budewa gate ya shararo motarsa ciki,Shukura ya fara gani ta fito daga motar, ajiyar zuciya ya sauke sannan ya fito zai tarbi abokinsa, Ahleef yasan dole a hanya Farhan zai hadu da Shukura,Farhan kuma abinda yasa ya nace sai ya dauki Shukura Sabo da ya batawa Ahleef rai dole sai ya gano gaskiyar Ahleef ko son Shukura yakeyi yasan halinsa da zurfin ciki,cike da kunya ta shigo Farhan yana gabanta kamar Saurayi da budurwa, Shakura da Ahleef suka hada ido dake Ahleef maye ne da ido ya mata magana ina taje dake itama yar duniyace ba wuya ta gane sai ta mayar masa da ido Cikin kankanin lokaci,Farhan bai san me akeyi ba,bai taba tunanin zasuyi haka ba da idonsu zai kalla, sai yaga kawai Shukura ta wuce abinta,Farhan ne ya dameshi shi ya bashi abinci yunwa yake ji,so yake wai yaga Ko Shukura ke masa girki, idan itace yasan dole zai sata tayi yau fa sai ya kuresu,Ahleef yace sai dai kasan kaci Indomie,to kasa Babyna tayi mana me dadi mana, Ahleef dariya yake a ransa Sabo da ya harbo jirgin Farhan,Sai ya shiga kitchen da kansa ya iske Shukura ciki tana dafawa kanta abinci wai tuwo zatayi miyar taushe,Ta yanka kabewa kawai ta cika tukunya da ita ruwan cikin katuwar tukunya har baki, har tayi hadinta gaba daya komai ta zuba har Allayyahu du a ciki kuma tukunyar ko tafasa batayi ba, Gashi sai yanzu ma ake gyara nama za a zuba, naman ne karshe,Ahleef kallonta kawai yakeyi duk tayi kaca kaca da kitchen din,ko ina kwanikan aikinta ne ake ta yi,duk ta firgita kanta Bata gane me Ahleef yakeyi ta cikinta takeyi tun safe Bata ci komai ba, Ahleef gefe guda yake nasa,duk kamshin jikinsa ya kara gigita Shukura,Tukunyarta katuwa data dora ya bude kamar Wanda yaji kamshi ya wani lumshe ido tare da cewa uhmmmm... Kaji irin na manyan mata,mata fa suna girki anan yanzu naga girki anan Amma dai za a sammana wannan kamshi haka,Dadi Shukura taji an yabi girkinta ta Washe dan bakinta tace zan San muku ka daina budewa kar miyar ta lalace,Dariya ta cikawa Ahleef ciki,yace lallai zaiyi dadi kam ayi sauri a gama muna jira,me kake dafawa kai? Yace uhmm Indomie da kwai zamu ci kafin ki gama naki,kawai sai yaga ta kashe gas tace ni bana son girkina naku zanci ga me kwai ai yafi dadi wa zai hada abinda aka dafa da kwai da kuma tuwo,Ahleef yace sai kin mana tuwon sannan ki San mana nima na baki namu,baki ta turo tana kunkuni ta kunna gas taci gaba da girki,kawo na tayaki nima sai na koya Ko,tace to zo ka tayani wanke kwanikan nan,suka fara wanke wanke Shima ya fuskanci Bata iya sosai ba, sai labari ta fara bashi,Sai ga Farhan ya shigo shima ganin kwakwaf,Shukura ta fara labarinta tace Sanda Inna da Baffa suna da rai ko, Farhan yace uhmm muna ji,tace kai baka tsayawa kaji lbr sai surutu ka bari mana kaji abin tausayi sai kayi kuka,Inna ce dai Inna ce watarana da karanbaninta wai ta danawa bera tarko a karkashin gado zata kamashi Sabo da yana dauke mata soyayyen namanta, kwana daya biyu ta manta ashe tasawa bera tarko sai ta tura hannunta kasan gado wai zata ebo naman sai tarko ya saki ji kake bas ya danewa Inna Hannu ya kamota, ta fito dashi...tun wajen Suka fara tuntsira dariya Bama kamar Farhan,tace wai ku ance ku tsaya mana kuji to,Ahleef yana dariya yace muna ji, taci Gaba Inna dai da tarkonta a hannu ta kasa cirewa gashi ni na tafi yawo na,Baffa kuma yana kiwo gashi ba mayafi a jikinta baza ta iya fita haka ba,sai ta tsaya jikin katanga ta fara kwalawa mutane kira babu Wanda yaji dama muryarta kamar ta tsuntsu haka take idan tana magana Volume baya daduwa baya raguwa,kuma wai sai dai tace mutane...mutane kuzo baza tace jama'a a taimaka ba,Baffa ne ya shigo ya Cire mata Allah sarki hannunta ya kumbura Inna babba ce fa amma ta kama kuka,kaiiiii ta bani tausayi, Farhan suka dinga dariya,karshe ya tabe baki yace to shine me ? Shike nan labarin ? Ahleef yace kai amma akwai tausayi gaskiya,Allah sarki Inna,Shukura tace Kaji me Imani amma banda kai ta nuna Farhan Wanda ya fice daga kitchen,Tukunyarta har yau Bata tafasa ba, Amma ta bude sai juyawa take tana dandanawa,Ahleef yace muna jira fa, zuciya tayi wai tukunyar ta bata haushi akan me Bata tafasa ba, shine ta kwala murfin da kasa tace na gaji wlh ni bazanyi ba, Kin girma da iyayenki me yasa du baki iya girki ba,gyaran gida kawai kika iya taya zaki rike mijinki idan kinyi aure,kicin kicin tayi da fuska tace kai in dai ba me kiba bane tsab zan iya rikeshi wlh ina da karfi fa kalli damtse na ta dago hannu, Ahleef ya dinga dariya,tace yar gata ce ni fa a gida bana komai ko zanyi Iyayena hanawa sukeyi,gyaran gida nafi iyawa Sabo da kullum idan Bata nan inayi,Kai ya jinjina tare da cewa to gashi yanzu Sun rasu Sun barki ya za ayi ke nan, to ba sai ka koyamin ba tunda ka iya, Bani da time ni kinma kusa bar min gida kiyi shiri Next wk,gabanta ne ya fadi tace dan Allah kayi hakuri ka kara min ko wata goma ne ina yin kudi zan tafi kuma na kusa saura kadan.
Indomie ya juye a plate Uku kowanne da kwai biyu ciki dafaffe,plate guda ya mika mata,ya dauki nasa dana Farhan yayi waje,a kitchen din ta cinye nata sannan ta gyara kitchen din tas ta zubar da miyarta da takeyi ta wanke tukunyar sannan ta wuce palon wajen su Ahleef, Inner wears ta gani sababbi latest an kawo na maza da yawan gaske Ahleef ya zaba Farhan ma ya kwashi nasa,Shukura ta koma kusa da Ahleef ta zauna tana ta kallon kayan, Farhan yana kallonsu yanda Ahleef ya Bata rai sosai dan kar ma Shukura tace zata taba kayan,mikewa Farhan yayi tare da cewa saida safe ya,ka fasa kwanan ? Ahleef ya tambaya,Ae Bazan kwana ba a cika min ciki da Indomie Budurwata sai da safe,Shukura Kunya ta rufeta da kyar tace Allah tashe mu lfy,Ka gaida Mama zan shugo gobe cewar Ahleef.
Shukura ta kalli Ahleef a hankali tace tace Dan Allah bani guda biyu ina so Harara ya watsa mata,bata kara cewa komai ba ta Mike tayi Dakinta.
Shukura an gama Shiri ana murna taji cewar Ahleef gidan Momee zai kaita ta zauna can wurin Inna Saudatu,cikin Shiri ya fito yana zuba kamshi yasha wani yadi me tsada da kyau, Kayanta suna leda tabi bayansa har mota sanye take cikin doguwar rigarta Pink, yauma Driving zaiyi da kansa,tana shiga yaja motar,Sai gani tayi ya tsaya a wani katon gida Farhan ya fito da trolley har biyu manya ya saka musu a bayan mota,Ahleef yace bazan shiga ba ka gaisar da Mama,gidan su Farhan kenan,Shukura a ranta tace dole kuyi wulakanci wannan irin kudi haka,Shagon dinki suka tsaya na mata taga nan ma an sa musu katuwar Ghana Must go a bayan mota,Ahleef ya ja mota suka tafi,bai tsaya ko ina ba sai wata schl me Arabic da boko ba nisa da gidan Momee ya shiga yayi mata registration da komai,makaranta ce me tsada Sabo da a kauye tayi makaranta yace a sata a ss1 a dawo da ita baya.
Bayan ya gama yace ga makarantar da zaki dinga zuwa an gama komai Uniform dinki yana Cikin kayanki akwai komai a ciki,Shukura Bata kaunar zuwa schl dama tun asali Gata da basira amma tun iyayenta na da rai sai da kyar take zuwa, wata waya me kyau da tsada amma yar Nokia ce Bata WhatsApp kawai ta kira ce yace gashi akwai number ta a ciki ko me ya faru ki sanar dani,kuka ta fara yi yanzu kullum sai taje makaranta,mene kike kuka? Tace ni tsoron yan birni nakeyi kuma kullum sai naje makaranta,kin fi so a barki cikin jahilci kina yiwa mutane kauyanci baki iya komai ba? Shuru tayi a mota tana shesheka har suka je gidan,ta fito Cikin yan aiki wasu suka shigar mata da kayanta kaf na Boot part din Saudatu,Tana mamaki ashe duk kayanta ne haka aka zuba,Ahleef yace jeki ciki zan wuce Office Sauri nakeyi,Murmushi tayi tace na gode Allah kara arziki sai kuma ta fara hawaye,lfy ? Tace shike nan na daina ganinka kullum kullum waye zai siyo min kayan dadi? Dan Allah ka maidani gidanka mu zauna tare ni nafi sonka yanzu akan Saudatu,dariya ta bashi yace indai akan kayan dadine Saudatu ma zata baki kici,ai ita tsohuwa ce irin naku na yan boko nake So,to jeki idan kina so ki kira wayata,yanzu baza ka dinga zuwa ba shike nan ? Yace da Momee tana nan kullum sai kin ganni,Amma to ai ga Inna Saudatu ko,a'a akanta ni bazan zo ba kullum to budurwarka fa wacce nake zanewa ? Ko dan ita kazo mana, yace a'a ba haka nake soyayyata ba ni kullum sai naga budurwata,to yanzu idan ta dukeni fa ko ta zagi Inna ? Ahleef yace na baki wuka da nama ki mata duk abinda kikaga dama, Shukura da kuri tace Allah ballata zanyi ba ruwana,mota ya shiga tana daga masa hannu ya bar gidan yana dariya, duk abinda sukeyi kan idon Niima,tace Alhmdllh dama tazo har gida da zan kassara rayuwar yarinya matsiyaciya.
Shukura da gudu ta shiga part dinsu wajen Inna Saudatu tare da rungumeta ta baya,ba Zato Saudatu taji Shukura ta fada a jikinta tana murna,Saudatu dama tasan da dawowar Shukura Ahleef ya sanar dasu,kallon part din Shukura tayi komai me kyau ne daki biyu da toilet ko Wanne da palo sai kitchen kamar bangaren Amarya haka wajen yake, Bayan Sun gaisa suna hira Saudatu ta yarda lallai Shukura yar uwar Ahleef ce tunda ba Momee ce ta haifi Ahleef ba, sannan taji yan aiki suna cewa Ahleef dan uwan Momee ne ta raineshi.
Trolley Shukura ta bude kayan sawa ne na mata babu kalar da Babu ciki, har Bra duk ya siya mata kamar yasan size dinta,komai dai dai ita,haka dinkuna dake Ghana mustgo laces ne Atampopi,Shadda dasu materials iri iri masu tsada da kyau dinkin kuma dai dai ita kamar an aunata na zamani iri iri, sai mayafai takalma da jakankuna, Uniform dinta kala hudu Har Sandals da schl bags kala uku da littatafai komai an hada ba abinda zata nema.
Inna tace Mashaallah gaskiya Dan uwanki yana ji dake wannan kaya haka kamar lefe,murmushi Shukura tayi ta kwanta tana latsa wayarta,sabo da Baffanta yana da waya tun tuni tana dauka shi yasa bata Bata wahala ba ta gano kanta,Tana Kwance Inna tace tashi mu kara gyara gidan nan sai muyi girki,Shukura ba musu ta Mike Sabo da tuntuni tasan Fadan Inna idan tace ayi ka zauna wasa masifa zaka sha Bata daukan raini kuma Bata bada kofar da zaa rainata sai irin su Hafcy da Niima marasa Tarbiya.
Shukura ta zage akayi gyaran duk inda baiyi dai dai ba sai Umma Saudatu tasa ta tisa wajen ta iya dole,Duk ta gaji likis,Umma Bata bari ta huta ba tace girki zasu yi yanzu, suna girki Umma taga Shukura Bata iya ba, haka ta dinga fada sai da ta koya mata dole sannan tace tayi girkin a gabanta tana Guiding nata,tanayi Umma na koya mata,ta kusa gamawa ta dauki waya ta latso Number Ahleef,tayi Ringing me tatsawo sannan ya dauka Sabo da yayi saving Number din nata,yana dagawa ta kwalla da karfi tace girki nake ta yi kai tun dazu,dariya ta bashi sosai da kyar ya danne yace Dan Allah fa? Na rantse baka ji kamshin bala'i ba Allah ta furta cike da murna, murmushi ya saki yana rubutu a Office dinsa yace to ya da dadi? Ban Sani ba Umma ta hanani dandanawa tace ba a dandanawa wai sai anjima,yace wow Har miyau na ya tsinke ya zubo,dariya ta kyalkyale da ita tare da cewa yau ga Babana wajen kwadayi,Bari idan Umma ta barni na Dandana to zan kiraka na fada ma irin dadinsa Ko kasa Driver yazo na zuba ma ya kawo maka Office ai dai ni ba kazama bace zaka ci,to yace kawai ta dinga Murna zaici girkinta karshe tace ka fadawa Abokinka na manta sunansa me suna kamar za ace Fari,Oh Farhan ? yawwa ae shi kace na iya girki ina ta yi,Dariya Ahleef ya saki ba tare da ya shirya ba yace Ok zan fada masa yazo yaci girkin Amaryarsa,cike da Shagwaba tace kaifa ka iya sa mutum kunya Allah ai tunda Baffa ya rasu to ni wa zai daura min aure,yace danginki mana,baki ta tabe Auren dole zasu min fa na tsere ka bari watarana zan baka lbr kaci dariyar kawunmu yanda na siyar masa da Akuya naci dadi da Kudin.to Allah kaimu yanzu jeki wajen girkin idan ya kone bazan ci ba,kashe wayar tayi,Umma tace keda Yayan naki ne ? tace ae mana lbr na bashi na iya girki,Dariya Umma tayi sosai,Shukura ta kafeta da Ido tare da cewa Umma wlh kama kukeyi da Yaya sosai,Umma tace rufa min asiri Tsohuwa da ni kina hadani da me kyau haka,Baba ne ya dawo daga Office ya gama aikinsa har Ahleef ya sallameshi ya dawo gida ya Iske Shukura da Saudatu suna girkinsu,Umma tace gafa Shukura yar Uwar Alhaji Ahleef ce wacce nake baka lbr ashe yarinyar nan yar uwarsa ce amma take zuwa muna soya doya a titi,Baba yayi dariya Shukura ta tsura masa ido tace yeee... Baba ma Irin yaya Ahleef ne kalli wlh Dimple dinku iri daya har hancin kamar wa da kani,Baba yace haka ake ta fada a Office kuma kama haka take yanzu idan za aje Turai sai kikaga mai kama dake Shukura ai duk Dan Adam ne yan uwane shi yasa ake samun wani yayi kama da wani, suna ma wani iri daya,Shukura tace hakane nima sanda muka je makka naga me kama dani Balarabiya,Baba yace gaskiya yayanki mutumin kirki ne,Shukura tasan karya tayi tace uhmm kawai tare da canja zancen tace Baba harfa Muryarka da tasa wlh iri daya,Umma cikin wasa tace ke kin damemu da kama kama fa, Sun dade suna Hira har suka gama girkinsu.
Lafiyayyar Fried rice tasha kayan hadi iri iri, ga hadin Couslow sai soyayyar kaji,kunun Aya sukayi da lafiyayyan zobo, duk Umma yau ta koyawa Shukura su sunyi tare.
Umma tace to Shukura kinga yanzu mun gama girki sai Yayanki kije bangaren su Momee Ki karbo foodflask da za a zuba masa kinga mu flask dinmu duk da masu kyau ne amma irin nasu na daban ne,kije ko yan aiki, ko Niima ko kuma Latifa su baki kizo a hada a bawa Driver ya kai masa.
Tsoro ya shigi Shukura yanzu fa ta dawo gidansu da zama,gashi ta daki Latifa watarana ga abinda tayiwa Niima rannan wai wai Yau ya zatayi.Shukura ta kware wajen satar Hanya ta shiga waje ba tare da kowa ya ganta ba ko Bata San hanyar shiga ba sai ta nemo ta da kanta,haka tabi ta barauniyar hanya ta hanyar Garden har ta samu nasarar shiga cikin Palon ba kowa,ta lalubi kitchen ta shige da sauri ta tarkato duk abinda take so,har zata fita ta bude fridge dinsu na kayan sha,ta dauki wani hadin lemo da Niima ta zauna ta Bata lokaci wurin hadashi Sabo da zatayi bako,yayi masifar dadi kuwa cikin wani juck na roba me kyau, Shukura ta bude juck din robar karami dashi ta kurba taji dadi,kawai ta kafa kai ta shanyeshi tas ta Ebo ruwa ta cika juck din ta mayar inda ta dauka, wani flask ta gani hadadde karami an shirya abubuwa kusa dashi a saman tire,sai ta bude a hankali tayi arba da farfesun Hanta da Koda kawai sai ta fara ci taji dadi ta dinga ci tana cewa nasan na wannan yan iskan ne,da Momee tana gidan bazan ci ba tare da na fada mata ba, amma tunda su Niima ne kadan zan rage,dama Shukura Bata ci komai ba,jira take sai tayi sallah sai taci Wanda suka dafa da Umma to yanzu ta fasa cin nasu sai zuwa dare yau Allah ya ciyar da ita nasu Latifa,baifi Guda Shida ta rage hantar ba duk tacinye,romon ma bata barshi ba sai da ta yagi bread a kitchen taci dashi kadan ta maida komai inda yake ta dauki kwanikanta ta kara bi ta barauniyar hanya ta koma Part dinsu,Niima tana daki sai kwalliya take zubawa,taji motsi tunaninta yan aiki ne suke zirga zirga, Latifa ma yau Sunday tana gida tana jin karar kwanika a kitchen amma tayi tunanin Niima ce.
Bakon Niima yazo taci uban wanka kamar zata je Dinner, sai da taje ta shigar dashi palon baki sannan ta dawo kitchen domin kai masa abinci,bata duba flask din da hantar ke ciki ba kawai ta dauki katon tire din data jera komai a kai,juck din kuma Shukura ta cikashi da ruwa nan ma Bata duba ba ta daura saman tire komai da komai taje wajen babban bako tare da ajiye masa a gabansa tana karairaya, saurayi yace yau zanci dai girkin Amaryata da ake ta fada min a waya za ayi min. Murmushi ta saki tace yau gaka gashi sai ka manta hularka, yayi dariya baki da dama Amarya ta shi yasa yau ba yanda Mama batayi dani ba kan naci abinci wlh naki ci Sabo da nasan me Amaryata zata shirya min.
Niima tayi wani fari sannan ta dauki plate da spoon bari na zuba maka kar yunwa ta illata min kai,tana Bude flask wayam sai yanka shida rak a ciki roman kuwa babu ma,Rudewa Niima tayi kunya ta kamata ta rude gumi ya fara feso mata ta shiga tunani,yace Lfy Sweetyna? Da Ina ina tace kaga wlh nayi na....a... Jiye..amma kalli babu a ciki to ko Aljanune? Dariya yayi yace wanne Aljanu ko dai bakiyi ba karya kikayi nasan yan matan yanzu da karya Ko kuma yan gidanku Sun cinye ? Wlh daga ni sai Latifa masu aikin ma basu taba yi mana haka ba kuma yanzu babu wacce ke shigar mana kitchen Momee ta hana tace sai dai muyi girki da kanmu,tace bari na zuba ma lemon kasha kayi hakuri idan ka dawo next zan sake maka, yace Ok ba damuwa,ta fara tiltilo lemo tsiiiiiii sai farin ruwa shaaaaa ya cika cup,dariya ya kwashe da ita tare da cewa amma Kin iya rainin hankali wannan ne girkin da kike ta yi min kuri ? Kin hanani cin na uwata,haushi Niima taji ya kasa fahimtarta,tace karfa ka raina min hankali kasan dai nan gidan munfi karfin karya idan kudine gidansa kazo ya zaka zo ka dinga fada min magana,kune Matsiyata wlh ba mu ba,Saurayi ya saki baki tare da cewa ashe baki da tarbiya dabba Ce ke? Fada ya kaure sukayi kaca kaca yaja motarsa ya bar gidan yana godewa Allah da ya gano Niima Bata da tarbiya.
Sabo da bakin ciki sai da Niima tayi kuka tana bawa Latifa labari,latifa ta dinga salati tace naji motsin kwanika dazu tunanina yan aiki ne,nima haka cewar Niima,Suna ta tunani to waye yayi musu haka,kaf yan aikin gidan sai da suka tara su aka tambayi kowa,amma suka rantse basu dauka ba,Niima tace duk ranar da na kama Wanda yayi wlh sai ya bar gidan.
Shukura kuwa tana komawa tace Umma yau kamshin girki ya cika min ciki sai dare zanci nawa,Umma tace to zubawa yayan naki, nan Shukura ta shirya komai daban daban kalar yan gayu,aka zubawa Driver a mota ya tafi kai masa.
Ahleef yayi mamakin ganin girki lafiyayye Haka lallai Shukura ta samu uwa ta kirki Saudatu Zata koya mata komai, abinci ya zuba ya fara ci wani shegen dadi Wanda bai taba cin girki irinsa ba me dadi haka yana cikin ci yana santi Shukura ta kira wayarsa,ya dauka tace Yaya ya kaji ? Yace na nadaki sarauniyar iya girki ta Africa,ta dinga dariyar Jin dadi,Yace yau nasan sai na manta hanyar gidana nan ma ta tuntsire da dariya an yabi girkinta,ya cika baki da abinci da kyar yake magana yana Sani yayi haka dan taji dadi ba kyau ayi maka abin gwaninta ka kasa yabawa,yace yar kauye tafi yan birni iya girki tazo ta kwace musu bokonsu na iya girki,Tace kai Sir to gobe ma zanyi maka wani,yace dolenki ma ai naga waje,an nunawa kurciya baka,yanzu zan fadawa saurayinki shima yazo yaci,Shukura tace to idan yaci anjima da dare ka kirani ka bani labarin irin santinsa,yayi mata ta yara yace tam tare da kashe wayar.
Ahleef ya biyewa Shukura ya takurawa Farhan lallai sai yazo Office yaci abincin Amaryarsa wai dole Farhan yazo.
AsmaBaffa.
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
10
official
By
AsmaBaffa
Kuyi Hakuri readers kwana biyu ina Busy ne shi yasa baku jini ba.
Ina matukar godiya ga masu Sharhi Allah ya biya ku,karku gaji pls aci gaba ina gani kuma zanyi kokarin ganin kowa na masa reply.
ASYCOOL,DIYAR KATIBI, HAFSAT KHAIRAN and ZEEMAMA wannan page din naku ne Sabo da Kauna.
Farhan yana shiga Office din yace na Niima ba.. Kafin ya karasa Ahleef yaja wani mugun tsaki Wanda bai taba yi ba, me zanyi da ita Allah ya kiyaye, Farhan yace Niimar taka ? Dama sai yanzu na gane wlh ba so Bane kawai Shakuwa ce ta zama waje daya da kuma son kyautatawa Momee da Abba,Kallonsa kawai Farhan yake yana mamaki,dama ba so bane kace ? Kwarai kuwa Allah ya taimakeni Bata aureni ba ni sai yanzu ma nake kara sonta kuma ta birgeni wajen taimaka min da tayi ban aure ta ba, Farhan ya fara dariya tare da cewa kaifa kace tafi matan duniya kyau, Lokacin ban gane ba amma Ko yar yarinyar nan Shukura ai ta linka ta sau dubu saba'in na tsaya ina batawa kaina lokaci,Uhm yanzu Shukura ta fita kenan ? Farhan ya tambaya,Nesa ba kusa bama budurwarka ta fita kyau, Ashar Farhan ya dura masa tare da cewa munafikin banza zakayi bayani,sai kazo kana fakewa dani budurwata budurwata munafuncin banza,Dariya Ahleef yayi tare da cewa Kasan Allah ba wani so tsakaninmu kawai taimako ne,ni me zanyi da mace yanzu babu class dina fata nake ma ka aureta wlh, harara Farhan ya watsa masa tare da cewa Allah kiyayeni kazo kana bibiyarmin mata,nan Gaba zaka yi bayani,baki Ahleef ya tabe baka ganewa wlh malam ga abincin nan ci ka tafi,Farhan yaci abinci shima yana zuba santi iri iri.
Da dare Ahleef sai yaga gidan yayi masa fadi,ba dadi shi kadai kamar maye gaskiya yayi missing Shukura, haka yayi shirin bacci ya kwanta 12am ya tuna bari ya kira Shukura ya bata labarin santin Saurayinta Farhan lokacin da yaci girkinta,Har yayi Dialing ya tuna dare yayi ya kashe ganin gobe Zata fara zuwa schl.
Washe gari da sassafe Umma Saudatu ta tashi Shukura, dake Shukura haka kawai Allah ya sa mata tsoron Saudatu da wuri ta tashi tayi shirin makaranta Uniform White and Green din yayi mata kyau Hijab dinta iya mazaunanta,Schl bag dinta ta shirya tsab sannan tayi break fast tare da mikewa taje har dakin Baba ta gaida shi da labadi,yace Shukura makaranta za aje tace ae Baba, to Allah bada sa'a ya zaro dari biyu ya Bata kudin makaranta,tayi Godiya ta amsa cike da murna ta rataya jakarta tare da musu Sallama ta fito,tana fitowa motocin Ahleef Suna shigowa gidan wasu sababbi dal dal guda shida tare da escorts nasa,Shukura ya hango tayi kyau cikin Uniform dinta,Guard ya bude masa motar ya kara 5mnt bai fito ba Sabo da Izza sai daga bisani ya zuro kafafunsa abin kallo yana fitowa Kamshinsa ya gauraye wajen,Yasha uban kyau cikin kana nan kayansa.
Direct wurin Umma ya nufa suka gaisa,Sai da sukayi Mintuna suna hira da Baba sannan ya musu sallama ya fito cikin takunsa na birgewa,Shukura ta rusuna tare da cewa Ina kwana Yaya,kin tashi lfy kawai yace sannan yace muje pls zakiyi Late,abinda bai Sani ba Shukura tafi son tayi late Sabo da bata son makaranta a rayuwarta, saida ta shiga Mota kusa da Ahleef gefensa sannan tace au nayi mantuwa ina zuwa ta bude ta fice tana tafiya kamar marar lfy wai dan tayi Late Bata so taje kan lokaci tafi so taje makaranta an kusa fita daga first period, cikin dakinta ta buya dan kar Umma ta ganeta,sai da ta dan dade sannan ta fito tana tafiyarta cikin sangaya har ta shiga mota,yace as from today Driver ne zai kaiki kullum, Baki ta turo tare da cewa ai makarantar ba nisa da kafa ma zan iya zuwa daga yau ni a kafa zan na zuwa ta furta dan kawai kar ta dinga zuwa schl akan lokaci,bata San makaratun birni dana kauye daban ba, shima bai ce mata komai kawai satar kallonta yayi kadan ta gefen ido,Kuruciyar tata tayi yawa Sabo da iyayenta Sam basu koya mata komai ba.
Jarida yake karantawa har Sukayi parking a Compound na schl din,wajen Principal ya kaita da kansa aka sa wata Senior student Namiji ya rakata Ss1 class dinsu tana tsoro tsoro yanda taji ana feso turanci ta ko ina. Ahleef ta kalla shima ita yake kallo, Hannu ya Mika mata Sukayi Handshake sannan yace jeki to bye,baki ta turo tare da cewa ya naji ana cewa Ss1 za a kaini ni fa a Ss3 nake repeating din yayi yawa,Baza ki gane ba sai nan gaba jeki class ya furta yana daga mata hannu, itama ta daga masa hannu tana kashe masa ido daya,dariya yayi kawai ta wuce.
Zata Shiga Class din malamar dake ciki tana koya darasi ta kalli Shukura tare da cewa Beautiful Lady can I Help u? Shukura tace Help ? Help...Help ta ci gaba itama ta tambayi malamar tare da cewa to Help me wiz Money or Wiz Meat, Chocolate,Ice Cream,Shawarma? Ta tambaya tana washe baki,yan Class har malamar suka kwashe da dariya wannan akwai son Dadi ga turancinta na Tsofaffin Hausawa Baza suce With ba sai wiz,Zey etc.
Malamar tace go and sit down,ta wuce sumi sumi ta zauna ita kadai can karshen baya,Maza da mata kallon Shukura akeyi ana gulmar kyanta kamar ita tayi kanta.
Tunanin yan class Shukura Bata da wani kokari tunda sunji kalar turancinta duk kyanta sai suka rainata,Period din Malama ta kare wani malamin Biology ya shigo,ya fara yiwa yan aji tambayoyi what is kaza what is kaza etc,yana yin tambayar farko ba Wanda ya daga hannu sai Shukura,shi kanshi ya girgiza da kyanta yace ta fada,ta Mike ta bada amsa dai dai kuma kawai turancinne idan anji an San Bata kware ba, Malamin yasa aka dinga tafa mata,ya kuma jefo ta biyu Shukura ta kara daga hannu tare da wasu yan aji ya kara nunata ta fada nan ma ta bada amsa dai dai Kafin ya bar ajin saida ta amsa questions hudu.
Wani ma ya shigo haka ta dinga kokari gaba daya sai gashi ta kankaro mutuncinta kowa yasan me kokari ce sai ga students mata da maza Sun fara mata magana dake ita Shukura zai wahala kaga tayi fushi ko ta Bata rai haka suka dan saba kadan ta saki jiki sama sama.
2pm suka tashi ta fito bakin Gate,Drivern Ahleef ta gani Yana jiranta ta shiga suka tafi gida,Yau ma tare da Umma sukayi abincin dare suka gama komai.
Washe Gari Driver ne zai kaita amma tace ita da kafa zata je,ta fito kenan Latifa ma ta fito Sabo da Niima ta bawa Latifa labarin cewa an kawo wata yarinya gidansu Bata da kunya an sata a schl ma Sabo da haka Zata yi mata transfer zuwa makarantar su Shukura domin hana Shukura karatu da Jin dadin schl baki daya,Sannan Niima ce zata dinga shirya komai yanda zai tafi dai dai,Niima tace Latifa ta shirya yau ita Zata fara kaita schl ma, Latifa da bata yarda zatayi ba Sabo da bata San wace ba, Sun fito Compound tayi arba da Shukura ta ganeta sai ta bawa Niima Labarin fadansu da Shukura a motar Ahleef sannan tace Alhmdllh dama na tsaneta tunda itace wlh sai inda karfina na ya kare sai karatu ya gagareta, Niima taji dadi suka tafi a mota,Shukura tana kallonsu ta fice ta tafi a kafa tana ta bata lokaci har first period Zata fita sannan taje schl.
Tana zuwa gate taga Niima tare da wasu malamai da kuma seniors baki daya tana fada musu cewar Shukura kanwarta ce,bata son karatu ne shi yasa aka yi mata Transfer zuwa wannan makaranta Sabo da Sun iya ladabtar da Soudent,kuma a kula Shukura barauniya ce,sannan tana zagin iyayenta kar a raga mata a schl din Sun kawota ne domin a hukuntata idan tayi laifi, PC yace ai yayanku ne ya kawota kuma baice musu haka ba, Niima ta zaro takarda ta mika masa tace gashi babansu su ne ya bayar a kawo kan halayen Shukura yana so schl su tayashi tarbiyantar da ita,pc ya karba kuma ya gamsu haka sauran malamai ma, ta kara miko takarda tace inji yayansu Ahleef yana bada Umarnin hukunta Shukura idan tayi laifi dama haka take ta damesu a gida Bata ji,karshe ta zaro kudi masu yawan gaske ta bawa malamai har senior student,kudin da ta bawa PC na daban ne nan Take suka gigice suna godewa Niima ta juya ta shige motarta ta bar schl din.
Lokacin kuma Shukura ta shigo gate din PC yace lallai gaskiya ne ga zahiri dan Iskanci tana New student sai yanzu Zata zo schl period daya ta fita salon ta lalata musu schl, to baza su yarda ba wlh dole su dauki mataki ba ruwansu da New student ce,Bulala PC yace a kawo masa,yace Shukura tayi kamun kunne,tun kafin tayi ta fara Kuka,haka ya sata kamun kunne, tsallen kwado sannan ya sa wasu malamai biyu suka zanewa Shukura jiki sai da suka fasa mata fata jikinta yayi rudu rudu,An daki sarkin Shagwaba,su kansu malaman sai da suka ce basu taba ganin yar shagwaba irinta ba daru take iri iri ana kallonta,idonta yayi jajir Sabo da kuka haka ta Shiga Class,tasan dama tunda taga Latifa tare da Niima a schl din dole tasan sai wani abu ya sameta.
Bayan anyi musu Break Latifa Har tayi frnds masu kudi yan wulakanci ta sanar musu Shukura yar aikin gidansu ce daga kauye aka kawo ta gashi kuma su a Ss2 suke seniors ne,Shukura tana gaban me Yogourt ta karba ta bar wajen taji kawai an shako Hijab dinta ta baya sai da ya yage ta wuyanta kafin tace komai wata ta fisge yogourt din me kankara,Ido Hudu sukayi da Latifa,Shukura a ranta tace bashi kika ci,Tana kallonsu wajen su Shidda suka dinga dungure mata kai suna mata dariya tare da wulakanci iri iri Student suna ta kallo masu dariya na yi masu Tausayin Shukura suna ji,Shukura kuwa Sun mata yawa mukus tayi kanta a kasa har suka gama suka tafi sannan taja kafarta da take dingisawa da kyar Sabo da tsallen kwadon da tayi ya tashi Tsohon rauninta da Igbo Man Wanda ya taba bige ta a mota ya ja mata. Motocin Ahleef ne suka keto cikin Schl din tare da Escorts Latifa ya fara hangowa cikin kawayenta marasa kunya,kallo ya koma kansa Gaba daya,Fitowa yayi cikin shiga ta Alfarma duk Wanda ya kalli Ahleef sai yasan lallai Allah Sarki daya ne,yan mata ko kyafta ido basa yi kansa,Latifa ta fara iyayi ga yayanta suka rankaya zasu kwasar gaisuwa,Ahleef da mamaki yace ke kuma me ya dawo dake wannan schl din ? Ko iyayin ne ya motsa ? Latifa tace nafi sonta Yaya,baki ya tabe tare da cewa taki schl din tafi wannan komai fa,anyway je ki Ss1 ki kira min Shukura,Munafuka Latifa sai ta nuna Sam Bata gane wa yake nufi ba sai da ya mata kwatance sannan wata ciki tace ta gane ta suka tafi jiki na rawa suka samu Shukura ta kwanta saman Sit tana tunani iri iri,Duka Latifa ta dada mata a cinya tare da cewa kije inji Wanda ya kawoki nan,tasan Wa take nufi,ta dauki jakarta suka fisge tare da zazzage komai na ciki a kasa sukayi tafiyarsu,Shukura abar tausayi ta sunkuya tare da kwashe komai ta mayar cikin bag sannan ta fita tana dingishi amma a ranta Dadi take ji na zuwan Ahleef Sabo da yanzu ganinsa takeyi kamar dan uwanta na jini.
Yana cikin mota yana shan AC ya hangota a birkice idonta Jajir kuma ba fara ar daya saba gani a fuskarta,sannan Uniform dinta duk sunyi Dirty bayan ya santa da tsabta.
karasowa tayi jikin motar daya ke ciki ana ta kallonsu,Murmushin dole tayi ta leka kanta ta Glass din tare da cewa Sannu da Zuwa Yaya,ba tare da ya kalleta ba yana latsa wayarsa cikin iyayinsa tare da murya me dadin sauraro yace me ya samu kafarki ? Kuka kikayi ? Uniform kuma sunyi Dirty,gefen yatsanki kamar shatin bulala,Rau rau tayi Zata fara kuka da kyar ta danne tace ba komai dazu ne aka ce yan class sunyi laifi shine aka zane mu duka tare da tsallen kwado,Kuka ta fashe masa dashi tace shi yasa nace ma wlh bana son yan birni mugaye ne saura kadan su kasheni dazu Allah ne ya kiyaye malaikan daukan rai bai karaso ba, dan Allah Sir bana son karatun ni na hakura wlh.
Ba kya son zama likita ko Lawyer,teacher etc ? Shuru tayi tace ni Soja nake son zama Sabo da na rama dukan da aka yi min yau ko Roadsafety wlh duk sai na kama motocin Malaman nan da sauran duk Wanda ya Bata min,Murmushi yayi tare da mika mata Wata ledar abinci da ya yi mata take away yace jeki to class,Murna ta lullubeta wannan kadai ya yaye mata bakin cikinta,godiya tayi tana murmushi, ko kallonta baiyi ba yace Farhan ne saurayinki yace a kawo miki, Allah sarki kayi Masa godiya ko ka bani number dinsa kawai pls? Zai baki da kansa nan gaba tafi class bye suka ja motocinsa, Class taje ta baje abinta kowa na kallo babu Wanda ta kula tunda Bata da kawaye haka ta cinye Namanta da sauran tarkacen ciye ciye dana sha,Students ana ta hadiyar yawu.
Bayan 1wk kuwa Latifa lallabawa tayi ajin su Shukura lokacin ta fita anyi Break ta Saci Dubu biyar wata a cikin jaka ta zuge bag din Shukura ta saka mata dubu biyar inda baza ta gani ba ta bar class din.
Bayan an dawo daga Break yarinya ta nemi dubu biyar finta ta rasa kuma aikenta akayi a gidansu after schl Zata kaiwa telansu,ta sanar a class duk Wanda ya dauki kudinta ya dawo mata Dashi class kowa yace bai dauka ba,aka ce ayi caje aka fara caje jiki da jaka a gaban Malamin da ya shigo shima yana taimakawa,sai aka samo dubu biyar cas a jakar Shukura aka fara ihu Thief...Thief.... aka fito da Shukura Waje Malamin yayi mata bulala goma yace dama yayarta tace barauniya ce ita haka a gida ma take sace kudin iyayenta,Hakan ma wai ya raga mata Sabo da New Student ce,Shukura Bata saba ba ta barke da kuka tana cewa wlh Sharri aka yi mata amma ba wanda ya saurareta sai ma dariya da yan Class suke mata,ita kanta Bata San waye ya kulla mata sharri haka ba, amma ta barwa Allah, Tun daga wannan rana Shukura ta daina zuwa late,ta fara taka tsan tsan da jakarta Sabo da kar a kuma kala mata sharri,bata kula kowa daga mata har maza Bata kulasu Sabo da Sun Bata Haushi da suka kala mata sata,duk Wasu doka na schl ta kiyayesu sai wani Masifar kokari da take tashen yi ba a magana turancinta kullum gyaruwa yakeyi ga kyau ga diri data kara.
Latifa ta Sanarwa Niima komai da Shukura ke ciki,Niima tace tana da saurin fushi kiyi mata wulakancin da Zata ji Haushi kuyi kokawa kice ta dakeki a gyara ta a schl din.
Latifa yau a dai dai gate ta jira Shukura da Sassafe ,Shukura Bata San da mutum ba tadan bigeta,Latifa taci kwalar Shukura ta fara zagin iyayenta,Shukura an zagar mata Iyaye yau ta gaji da hakuri, tunda tasan su Niima basu da mutunci ta daina shiga sabgarsu kuma kawar Latifa ta zago ta bawa Shukura labarin tuggun da suka hada mata iri iri, Shi yasa Shukura tayi zuciya suka fara kokawa ta zaro biro kawai ta cakawa Latifa a gefen kanta Wajen kawai ya tsille jini ya fara tsartuwa ta kafar,Nan fa schl ta hargitse malamai suka yo kansu tare da cewa a rufe gate kar kowa ya fita,Shukura ta kama katanga ta dane ta haure ta arce sai gida,Latifa kuma akayi asibiti da ita,Niima har taje tana ta kuka,Ahleef ma an fada masa,yana zuwa ya samu ba wata matsala har anyi wa wajen dinki an sallamesu,Gidan ya wuce Direct ya duba Latifa ta tsara masa karya da gaskiya amma yasan Sune da Laifi tunda yaga Latifa a schl din yasan Shukura zasu tsokana dole,Bai ce komai ba ya nufi part din Umma Saudatu kai tsaye yayi Sallama Shukura tana Sallar La'asar, Baba kuwa yana masallaci,Umma a zaune take tana gyara Garin Alkamar da zatayi tuwo.
gaisawa sukayi Umma tace kazo Jin rigimar da kanwarka ta kwaso ko,Murmushi yayi yace ai Bata ji ne Umma,Umma tace ta bani labarin komai gaskiya sune da laifi bari ta idar da Sallah tayi maka bayani 'yata Bata da laifi, suna hira sama sama Shukura ta Idar Umma kuma ta wuce kitchen.
gabansa Shukura ta zauna kasan kafafunsa ta kalleshi fuskarsa ba Rahma,a hankali ta gaisheshi,Me ya hadaku da Latifa dama fada na kaiki ki koya ? Shukura Bata Ce komai ba sai Shirin Kuka ma zatayi da kyar ta kwashe komai ta sanar masa har yanda Niima take bada kudi tana zuga malamai da Latifa,Ahleef ya jinjina lamarin,tace ka yarda dani Yaya bari na nuna ma sheda ka gani ta zare Hijab dinta abin mamaki sai yaga t-shirt dinsa a jikinta ta daura Skert a kasa,Damtsemta ya kalla ko ina shatin bulala,rigar ta janye kadan tare da juya baya tace kalla bayanta rudu rudu shima,Hijab dinta ta maida tace sannan kuma Last nazo gate taci kwalata ya ake so nayi,taya bazan tsille mata kai ba ko yar uban wace wlh Bata Isa ba,na baya ma hakuri nayi Sabo da Dan Adam ba komai za ayi maka ba kace lallai sai ka rama dole kayi hakuri.
Lallai sai yau Ahleef yasan Shukura tana da hankali ashe.
Kamar bazai ce komai ba yace gaskiya idan Saurayinki yaji Bazai ji dadi ba ana Dukar masa mata haka,Shukura ta turo baki cike da Shagwaba dan Allah Yaya ni ka daina ta furta tare da fadawa saman kujera kusa da shi,Kansa ya dauke daya barin tace juyo mu gani Sir, yaki juyowa ta koma can barin, gwiwoyinta suna kasa ta kifa cikinta saman kujera tana so wai dole sai tagani yana dariya ya daina fushi da ita,kansa ya Maida can barin,ta Mike tsaye tana dire diren kafafu wai sai ya tsaya shi kuma yaki yarda,hannayenta tasa biyu ta rike kan kam a saitin fuskarta tace to muga hakoranka,ido ya kafeta dashi tare da bude mata kuwa yana murmushi tace irin na Umma sai kuma taji kunyarsa ta.sakeshi da sauri,Umma ce ta kwala mata kira a kitchen,tana shiga tace haka ake saukar bako ? Tire ta nuna mata kai masa,a gabansa ta ajiye tire tare da zama a kasa kamar ita Zata ci,ta tsiyaya masa lemo ta Mika masa yace bazai sha ba shi ruwa zai sha,Shukura tace ni kuwa ina sha ta shanye lemon, ta bashi ruwa,Abincin kuma jullop Spaghetti ce taji hadi yace ta zuba masa dama yunwa yake ji, Umma fa ta gama yadda Shukura da Ahleef yan uwa ne sai ta bar musu Part din Gaba daya su samu suyi hirar zumunci,Ahleef hankali kwance yake cin abincinsa me dadi sosai,Shukura tana zaune kusa dashi ta zura masa ido kawai birgeta yakeyi a duniya ga komai nasa me kyau ne,shi kuwa yasan tana kallonsa kawai muryarsa taji yace Saurayinki zaki na kalla haka yace Sunday ma zaizo zance gobe kenan fa.
share zancen tayi tace amma ranar Monday kai zaka kaini schl din ? Indai naje ni kadai to kawai ku tanaji makara da likkafani, gaskiya Makarantun Birni basu da Imani a kauye kuwa ni kadai ce me kokari sai abinda nace,amma a nan shegu sai kokari kowa me kokari nice jakar ajinmu fa Yaya, dariya yayi yace jaka kuma ? Tace bakar ma kuwa irin marar mangala din nan, sai dai kayi hakuri nasan ta karshe zanzo yo wannan manyan kwari haka.
murmushinsa ya yi me tsada tare da cewa da bulala zanzo ranar karbar result kuwa,Zama tayi a gabansa kamar me daukan darasi tace kai yan gayu ne a makarantar mu kaga yanda suke tafiya wani dos dos ga daukan wanka,Kema sai ki koya ai,Ina nan zan fara kuwa amma ba a schl ba, yanzu Yaya inda kake me kyau haka ai sai me kyau akwai wata a class Dinmu sunanta Islam kyakyawa ce da zaka yarda da ka aureta kun dace,da ta ganka kazo wajena nace musu yayana ne, Sabo da Sonka fa yanzu take kulani kawata ce sosai har karatu take koya min Sabo da Sonka tayi ta siya min abubuwa,kuma tace gidansu Auren wuri ake musu kaga da tana gama secondary schl sai ka aureta wlh tana sonka tace dan Allah na hadaku,Ina da budurwa fa ni kin Sani karma ki soma a kai kasuwa,karki kuskura ki kara yi min zancen wata Mind ur Business bana sonta ya furta a fusace,Shukura tace Islam din ? Tsaki yaja ya mike tare da cewa Sai Sunday gobe zamu zo da Farhan zasu gaisa da Umma,har zai fita Shukura tace Yaya ga abu kamar ya makalema a hakori kawo na cire ma, Toothpick ta dauko,shi kuma ya zauna,tace mu gani ya bude kyawawan hakoransa tasa tsinken ta cire abin nama tare da cewa kalla ? kamar wani danta tana kula dashi,Zai Mike tace baka taje gashinka da gemunba, dariya yayi kadan yace dama ido kike sa min Ko,ya zaro Cumb dinsa da wani dan mitsitsin turaren gemu na gashi,da gudu ta dauko masa mudubi karami ta karasa masa a fuska yana kallo ya taje gashin da gemun tare da shafa masa turare yana sheki sannan ta matsar da mudubin tace Allah kaika lfy,yace Ameen ya wuce abinsa ba tare da ya kalle ta ba.
Zahra kuma kanwar Hafcy Babansu yace dole su jira har Abba ya dawo daga tafiya amma dole cikin su biyu wacce Ahleef yake so to ita za a hada su aure,Nan Suka fada neman mafita gwara tun yanzu ko wacce ta shigar da kanta gareshi Ko zai zabe ta, Hafcy tayi bincike sai da tasan yanda tayi ta nemi Niima suka zama frnds Sabo da ta hanyar Niima Zata dinga ganin Ahleef,sannan Niima ita kuma ta fada mata Ahleef ba a San asalinsa ba a gidan raino aka daukoshi ba dan Sunna bane, Sharri iri iri Niima ta kullawa Ahleef karshe tace shi yasa ma Bata aureshi ba,Hafcy tabe baki tayi tare da cewa Amma kin tafka asara irin wannan namiji haka to ni ko daga sama ya fado karewar rashin asali nasan Allah ne ya Halicce shi inasonsa,ko dan kudinsa da kyansa ai a so wannan gwarzon gwaraza, kawai ki tallafa min, nima idan kina neman wani abu zan ba abinda bazan miki ba, Niima kuma tasan Hafcy ta fita iya shege a kasar nan shi yasa sai ta yarda domin akwai wani mummunan kudirinta Wanda idan da Hafcy zai tafi dai dai,Ita kuma Hafcy ta sanarwa Mubaraq cewa ya zama ready Niima yanzu kawarta ce damarsa tazo shima,Murna kawai yakeyi ta fadi gasassa.
Zahra kuma bincikenta sai ya nuna mata Shukura yar uwar Ahleef ce da yafi so Sabo da haka idan tana tare da Shukura to zatayi Nasarar samun Ahleef cikin sauki,dama Service Zata fara sai kawai ta nemi a Bata teaching a makarantar su Shukura ta zama Malamarsu kuma tayi nasara an Bata yanzu kawai dole fa sai ta zama kawar Shukura ta gaske.
Islam kuma ganin Shukura kamar taki hadata da Ahleef sai ta koma barin Latifa domin hanata sakewa sannan Latifa ta hada ta da Ahleef.
Maman Su Hafcy akwai son kudi so takeyi Lallai Ahleef ya auri daya cikin yaranta sannan Mubaraq ya auri Niima yanzu itama jira kawai take Momee ta dawo daga tafiya ta koma kawarta sosai ta kwantar da kai yanda Zata ji dadin harka da ita,Shi kuwa Baban su Hafcy tsakani da Allah yake so Ahleef ya auri yarsa daya Sabo da burin yayansa ya cika shi duk abinda matarsa da yaransa ke so to dai dai ne kawai.
Oga Ahleef kuma Yanzu gani yake babu wacce ta Isa ya so ta a duniya,kuma Farhan yake so ya auri Shukura Sabo da yasan zai riketa da Amana,Shukura kuma so take Ahleef ya auri Islam tunda Islam kawarta ce Bata San cewar tuni Islam ta koma wajen Latifa ba.
Asm[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
11-15
Official
By
AsmaBaffa
Yau Sunday yau Ahleef yace zasu zo da Farhan,Shukura cikin Zumudin ganin Ahleef ta damu Umma sai sunyi girkin da yafi wanne dadi,Umma ma biye mata tayi Sabo da Ahleef abin a kyautata masa ne,Girki suka Shirya kala biyu da kayan sha,Shukura ta kara gyaran part din Yasha turaren wuta ko ina kamshi ke tashi na daban,tana yin sallar laasar ta shiga wanka ta tsiri shafe shafen da bata yi ma,cikin mayukanta Masu kamshi Wanda duk cikin kayan Ahleef ne da ya siya mata,tana gama shafawa ta bude kayan da gaba daya Ahleef ya siya mata su,ta zabi wata atamfa Green and black Riga da skert ta sa yar Bra dinta,dinkin das a jikinta ta cika skert din fam kamar a sace ta,Bata iya kwalliya ba sai ta shafa powder da jambaki Red kawai tasa kwallinta,tayi masifar kyau tana bulla kamshi abinta ta fito palo ta zauna tare da daukan littafi tana dubawa irin ba dan kowa tayi kwalliyarta ba wai dama haka take.
Umma ta kalleta kawai tayi murmushi tare da cewa Mashaallah duk Wannan kwalliyar ta Yayan ce ? Murmushi Shukura tayi tare da cewa Umma ai ni badan su nayi ba,Umma Bata ce komai ba tace to yan matanci ne ya motsa ashe ta furta tare da cewa bari na watsa ruwa ta shiga dakinta.
Umma na shiga Su Ahleef suka shugo bakinsu dauke da Sallama,Shukura ta amsa tare da cewa Oyoyo Yaya fuskarta dauke da fara'a,Farhan ma ya shigo yana karewa Shukura kallo ba kyafta ido yanda ta gaji da haduwa abin ba acewa komai,Ahleef kuwa yayi mamakin dama haka take da girma ko ina a cike amma sai yayi kamar bai ganta ba, ita kuma so take taga yana kallonta a nan Zata San lallai tayi kyau idan har Ahleef yana nacewa kallonta,amma ina Sam bai nuna ba ko kallonta baya yi,Farhan ne ya koma kamar yaga Tv, ta gaishesu tare da sanar musu Umma Zata fito yanzu ta shiga wanka,Kitchen ta mike ta shiga,Farhan yabi bayanta da kallo Ahleef yace mene haka kuma ? Sai kace maye a gaban yarinya dan Allah ni bana son haka so ya dinga masifa ba ji ba gani karshe yace a haka kake so na aura maka ita ni bana son ka jawo mana raini kaja mutuncinka aikin banza yau ka fara ganin mace? Farhan yace amma anyi dan iska wannan masifar fa ni da Babyna dan na kalleta sai nayi laifi ? Da ganin yanda kake masifa ma kishi kake ji,Ahleef yace sharrin da zaka min kenan ? Farhan yace nifa malam dalla rufe min baki wlh bazan taba son wannan na aureta ba kazo kana fakewa dani Kaje da abarka sai abu yayi nisa kazo kana Gaba dani kuje ku karata, Baka sonta fa kace,kamar Shukura zaka ce baka sonta a hasale ya furta,bafa nufina bana sonta ba No bada aure ba tafi karfina sai dai kai,Tsaki Ahleef yaja ni bana bukata wlh kaf mata babu wacce zan iya aura.
Murmushi Farhan yayi tare da cewa to Allah kyauta,idan so kake ka aurar da ita to ga Muhseen kasan bazai wuce tayinka ba,Har Ahleef zaiyi magana sai ga Umma ta fito suka gaisa tare da hira,Shima Farhan yasha mamaki Me kama da abokinsa,Baba ya dawo daga Masallaci ya zauna shima suka sha hira,Shukura kuma ta cika musu Gaba da kayan abinci,sannan ta koma gefen Farhan ta zauna kusa da shi,Babane ya mike ya shiga Bedroom Umma ta bi bayansa,Farhan kwakwalwarsa ta tsaya da aiki Sabo da kamar Baba da Ahleef haka Umma ma, Ahleef ne yace kawo min schl Bag dinki na gani,Wai dan karta zauna kusa da Farhan,taje ta kawo sai ya nuna mata gefensa tare da cewa Zauna mu duba books din,Farhan kuwa kallonsu yayi kawai yayi murmushi ya fara cin abinda aka kawo musu,Books dinta ya dinga tambayar abubuwa a ciki yaji duk ta iya, yaji dadi kuma ya jinjina mata, wani Assignment na English ta dakko masa tare da cewa Yah na kasa wannan wlh tun jiya,Sai da ya karba ya gani ba zato taji Saukar biro a kanta ya rankwala mata shi,wajen ta dafe tare da sakin yar kara Muryar Shagwaba tayi Yah da zafi fa,Koya mata yayi har ta iya sannan Shima yaci abinda zai iya sannan Umma ta fito suka mata sallama suka tafi tare da mikawa Shukura wata katuwar leda wai inji Farhan saurayinta kuma Ahleef ne ya siya komai,Farhan yace ka gama gulmarka.
yau Monday yaune kuma Zahra ta fara teaching dinta a makarantar su Shukura, Yau second period ta shiga ajin su Shukura,kamar abin kirki ta gama teaching dinta sai ta bada Test tare da cewa wace Shukura ? Shukura ta daga hannu,Zahra ta girgiza da ganin me kyau haka kamar ba mutum ba,tace a gidan su Ahleef kike ? Shukura tace ae,Murmushi Zahra tayi tare da cewa duk wanda ya gama ya bawa Shukura ta hada ta kawo mata ta fita abinta. Har Office Shukura ta samu Zahra da Test,Zahra ta kalleta da Fara'a tace Shukura kina da kyau,tnx Shukura tace itama tana murmushi,Idan Baza ki damu ba zanso mu zama frnds duk da na girmeki amma ni wlh kawai kina birgeni,Shukura ganin yar gayu irin Zahra kuma me kudi gashi tace tana sonta da kawa gaskiya mutuniyar kirki ce Zahra bata da wulakanci ai dole ma ta zama kawarta,a fili Shukura tace nima ina Sonki ba damuwa,Shukura ta dade suna Hira da Zahra har suka fara sabawa sannan ta koma class,Zahra kuma Shukura na fita ta tabe baki tare da cewa ina samun shiga wajen yayanki zan raba ku kema bazan so me kyau irinki ta rabeshi ba.
Allah sarki Shukura Bata da kawa murna takeyi Allah ya Bata kawa malama guda, Babba kuma yar gayu,Su Latifa Yanzu suna Jin tsoron Shukura tunda ta tsillewa Latifa kai suka rage yi mata abu, kullum yanzu idan anyi Break suna tare da Zahra suna hira Amma Bata yarda ta fada mata sirrinta, Zahra kuwa buri takeyi taga ranar da Ahleef zaizo wajen Shukura kuma taki nunawa tasan wani Ahleef ma,Hafcy kuwa kusan kullum tana gidan su Niima ko Zata ga Ahleef yazo amma Shuru ba labarinsa,Niima tace ta shirya suje har Office dinsa ranar Manday akwai wasu takardu da Momee tace a bawa Ahleef zai mata Posting dinsu zuwa Jordan,sun samu hanyar ganinsa ba tare da ajinsu ya zube ba,Hafcy Murna wajenta kamar zatayi Hauka ranar Monday wankan da bata taba yi ba shi tayi har gidan makeup taje kamar Amarya haka ta fito.
Shukura Sun samu Free period dab da za a tashe su,Zahra ta nemota Office suna hira har aka tashesu Zahra tace tazo ta kaita gida a motarta,Fitowarsu kenan sai ga Ahleef a wata mota sabuwa gal ta gaske fara kal kayansa ma shadda fara komai White ba karamin kyau yayi ba,Zahra ce ta fara Ankara dashi Ji take kamar ta dira tsalle sabo da murna,Shukura sai gani tayi kawai Zahra ta canja tafiya tana lankwashewa,Ahleef bai gane Zahra ba ko kadan Shukura ya dannawa Horn,laaaaa Yayana yazo yau shi zai daukeni Kawata kalleshi can,Wani kishi ne ya tokarewa Zahra a boye ta makawa Shukura Harara a fili kuma ta washe baki suka tafi har motar Ahleef,ta Window ta leka side dinsa tare da cewa ranka ya dade yaya fit ta zagaya da murna ta shige gaban mota sannan ta dagawa Zahra hannu bye Aunty kawas,Zahra tayi dariyar dole ta daga mata hannu tare da cewa Ina yini tana leka Motar kallon Up and down yayi mata da kyar ya iya cewa lfy, sai da tayi magana ma ya gane ta,Wani kallo da ya mata ya dauke kai sai da ta raina kanta jikinta yayi sanyi,yaja mota suka bar schl din direct Office dinsa ya nufa,Yaya Ina zamuje kuma ? Umma kar taga na dade wlh fada ne Da ita sosai idan anyi laifi Shukura ta furta kamar zatayi kuka,kallonta yayi kadan tare da cewa ashe kina da tsoro?ina kika samo kawa? Shukura tace malamar mu ce Aunty Zahra tana so na nima haka baka ga yanda takeso na ba, Hmm ki dai bi a hankali da kawaye musamman irinsu Ahleef ya rasa furta.
Shuru ta masa tana tsoron Umma ita dai, muryarsa ta tsinta yace naje gidan dazu Ai na fada mata sarkin tsoro,Murmushi tayi tare da cewa tsakanin ni da kai wa yafi tsoro kai,Dariya yayi lokacin ya tuno da Aljanun gidansa,katafaren Building dinsa yayi parking ma'aikata sai gaisuwa suke kwasa,Har Shukura ake gaisarwa Oga yazo da kanwarsa,Office dinsa ya bude suna shiga tare da ita sai kallon tsaruwa da haduwa Take sai kamshi tare da sanyi ke tashi, saman wata 2seater lafiyayya ta fada kai tare da kwanciya,Abinci yayi Order a kawo a katafaren wani eatery na manyan Masu kudi,Shukura gajiyar schl tasa Bata surutu Yah Ina toilet ya nuna mata can ciki ta dauki schl bag dinta yace toilet din zaki tafi da wata schl bag kuma,Ajiyewa tayi sannan ta bude ta cikin Hijab ta dauki pad dinta zaraf ta boye ta tafi toilet abinta,Dariya kawai Ahleef yayi kadan dama ya ganeta tun a mota Sabo da shi yana iya gane mata shi yasa yace kar ta shiga da bag Sabo da ganin kwakwaf.
tana shiga taga toilet neat sai ta sa key ta kulle tayi wankanta tas tare da maida kayan jikinta ta shirya Kanta,kafin ta fito kuma su Niima sukayi knocking Sabo da an santa shi yasa aka kyaleta ta wuce Direct wurin Boss,come in Ahleef ya furta cikin daddadar Muryarsa,Hafcy ce a gaba tana baza kamshi sai Niima,yana ganin Hafcy ya kara tsuke fuska,zama sukayi babu wata gaisuwa sai Sannu da aiki suka ce masa bai ko amsa ba yana ta rubuce rubucensa tare da daga waya ko kallonsu bai sake yi ba,Hafcy kuwa sai gyara kirji akeyi ana rangwada,Niima tace takardun Momee na kawo,ba tare da ya dago ba yace ajiye a table,tana daukowa Shukura ta bude toilet tare da fitowa daga ciki sanye da uniform dinta amma kowa ya kalleta yasan tayi wanka yanzu,Kallonsu tayi kawai duk Sun tare sit din zaman sai kawai ta zagaya kusa da Ahleef tana wata shagwaba kamar yarinyar Yah a ina zan zauna ni ? Da murmushi ya kalleta yasa hannu ya jawota ta bayansa sannan ya mike yace zauna a kujerata ki karasa aikin,takardun ya Nuna mata anan zakiyi ta Marking da biro tace na gane,Kallon Niima yayi tare da cewa bata documents din tasan me Zata yi.Shukura kuma kamar gaske sai jujjuyawa take a kujerar tana musu wani kallo tana aikinta da ya nuna mata, kamar hoto haka suka zama, shi kuma ya shige toilet zaiyi Alwala.
Gyaran Murya Shukura tayi tare da cewa keep it On the table cant u hear a simple English,ta kalli Hafcy tare da yin muryar Wanda ba bahaushe ba ko turanshi (turanci) babu? Nace a ajiye min a Table,Niima ranta ya gama jagulewa Ahleef ya yarfa ta a gaban frnd dinta Hafcy ma haka ranta ya konu ashe Niima aikin banza ce a wajensa amma ta Bata lokacinta,Shukura ta karo karfin AC taci Gaba da abinda takeyi ba tare da ta kallesu ba tace pls zaku iya tafiya i have done with u guys,Ahleef yana jinta yana ta dariya a toilet,Chewgum ta bare ta jefa a bakinta sannan ta jawo wardrope tare da ebo kudi 20k ta mikawa Niima take ths i know shi kuka zo nema Ko? Niima ce ta fara Mikewa a fusace Zata mari Shukura Ahleef ya fito tare da buga mata tsawa are u crazy kizo har Office dinta zaki Mareta Who the Hell are u, How Dear u,Niima tace Amma kasan kudin ubanmu ne ba naka ba,da bazar mu kake rawa,da ba a San asalin ka bane sai kace zaka bude mana ido,kai har kana da bakin magana marar asali tsintacce kayiwa iyayenmu asiri ka mallakesu harda kawo mana karuwarka gida ashe anan kuke sheke ayarku, bari su Momee su dawo wlh sai ka bar mana dukiyar mu,Hafcy tace ke Niima iya bakinki wannan yafi karfinki kuma ni a haka nake sonsa shine dalilin kulaki da nayi amma ni nafi karfin kawance dake wlh zaki zageshi shi yace a bashi dukiyar,Shukura ce tace Enough ku bar mana Office, Baraki ma ai iyawa ne wasu basu da darajar da zaiyi dasu, kun bada mata wlh get lost, Hafcy ce ta nuna Shukura da yatsa zamu hadu dake zaki maimaita kalamanki, ae din anji badai ya Sonki kuma bazai so ki ba Shegen kai kamar kwallon goruba, Kwafa Niima tayi Suka fita kuwa ba tare da sunce komai ba, Kujera Ahleef ya fada zuciyarsa tana masa radadi,Shukura ta fahimci hakan sai ta dawo kusa dashi,tana Bashi hakuri duk da Bata san labarinsa ba amma sai taji tausayinsa.
Yaya ta furta a hankali,kallonta yayi yana murmushin karfin hali yace dauko abinci gashi can kici,kafada ta makale ni tare zamu ci, lafiyayyun abincin ta bude tace dole suci tare haka suka ci abincin tare tana masa surutu har ya nemi damuwarsa ya rasa karshe ya karasa aikinsa ya sauketa a gida Bayan ya siya mata abubuwan ci iri iri, tana fita tace Yaya Bye banda tunani pls, I will try my Best inshaallah ya furta yana murmushi.
Hafcy tunawa da tayi da bukatar dan uwanta Mubaraq shi yasa taki yarda suyi fada Da Niima,kwanaki na ja Shukura yanzu ta kara gogewa tare da wayewa kuma hankali takeyi sosai Sabo da kulawar da su Umma ke kokarin yi akanta,ta iya kwalliya tare da girke girke abin ba a cewa komai, Ahleef kullum sai dai ya fake da Farhan yace Shine saurayinta.
Yau Momee da Abba zasu dawo Nigeria,gaba daya Sun tafi Airport Ahleef shine gaba kowa murna yakeyi,Alhmdllh Sun sauka lfy ana ta murna da ganin juna,Tattarawa sukayi aka tafi gida gaba daya,Washe gari Ahleef da kansa ya gabatar Umma, Baba da Shukura wajen Momee da Abba,Momee da fara'a cikin mutuntuwa ta amshesu Abba ma haka dama Momee tasan Shukura sabo da haka hira ta dinga janta dashi,abu daya ne ke damun Momee yanda taga tsantsar kamar Ahleef dasu Umma.
Sati biyu da dawowar su Alhji Baban su Hafcy ya samu Abba a Office kan maganar Auren Ahleef da Hafcy ko Zahra, Abba ya tuno rashin tarbiyar yaran sai yace ba damuwa indai Ahleef yana so shi bashi da Matsala amma bazai masa dole ba, zai tambayeshi yaji.
Yau Maman su Hafcy taje gida wajen Momee suna ta hira kamar abin arziki sai kuma ta fara kawo mata gulmace gulmacen Ahleef tana so taji ya suke da Momee Amma Momee Bata yarda tace komai ba duk kuwa da yawan zuwan da takeyi gidan.
Mubaraq yau shine ya kawo Hafcy wajen Niima,Sai da Hafcy ta gama abinda zatayi sannan ta fito zasu tafi Niima ta rakata har mota,Mubaraq a hankali yake dan janta da Hira Hafcy tana dariyar da ita kadai tasan nufinta tare da cewa Sister ga yayana da alama yana ciki a kular min dashi, Mubaraq dan gayu ne sosai ya iya wanka,Niima taji yana birgeta sosai Bata wani ja masa aji ba ta amshi soyayyar sa hannu biyu sukayi exchange na phone Number,suna Hira Shukura ta fito daga part dinsu Zata shiga wajen Momee tasha wankanta,Mubaraq ya ganta Gaba daya ya rude a ransa yana so ace ta zama matarsa,Niima na gabansa amma hankalinsa na kan Shukura Niima sai ta ji haushi kamar ita ba mace bace tana gabansa yana kallon wata can,da kyar ta danne fushinta har suka tafi,yau kuma Ahleef ya dawo gidan da zama Sabo da Abba ya matsa akan lallaai ya dawo gida..
Kullum yanzu Niina sai ta kai karar Ahleef da Shukura wajen Momee,ta kulla sharri tace Sun mata wani abu, tun Momee bata yarda har ta fara yarda ganin yanda Ahleef yake share Niima,shi ya jawo yanzu ta fara ja baya da Ahleef, Shukura kuwa kiri kiri yanzu Momee take nuna mata rashin Kauna,sabo da Me mutane suna cin arzikinsu suna zaune lfy Sabo da samun waje sai su dinga wulakanta Masu gida ita Baza ta yarda da wannan ba.
Tunda Ahleef ya dawo Shukura ke gyara masa daki,Haka abinci ma sai jefi jefi yake cin na Momee Umma ke dafawa dashi ta bawa Shukura ta kawo watarana har su Momee suna Ci Sabo da Umma karshe ce wajen iya girki,Shi yasa take kara Jin haushi kuma ta gaji to abun bazai yi kyau ba.
Tun safe yau Shukura tana farkawa tayi mika tare da cewa yau mugunta nake ji duk Wanda tsautsayi ya fada masa shi zanyi wa ba ruwana.
AsmaBaffa
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
16-20
Official
By
AsmaBaffa
MAMAN FAHAD and HADIZA MUKTAR ga page naku ina Godiya.
MARCYCOOL jinjina me tarin yawa.
Shukura tuni tayi Sallar asuba wanka tayi ta fara kalailatar Shiryawa kamar Zata je party,Umma tana palo tana kallo Ahleef ya shigo da sallama dauke a bakinsa,a'a sannu da zuwa karaso mana ka zauna,murmushi dauke a fuskarsa sai da ya duka har kasa cike da girmamawa ya gaishe da ita kana ya zauna suna hira jefi jefi,jira yake yaga ta ina Shukura Zata fito,sai gata ta fito sanye da Arabian Gown fitted black me duwatsu tayi kyau sosai musamman da tayi acuci tare da tayi Rolling mayafin,ido biyu sukayi da Ahleef ta saki murmushi ya kashe mata ido daya, tana so itama ta kashe nata bata iya ba sai fari tayi farrr da ido, murmushi yayi tare da dauke kansa daga gareta, Umma ce ta kawo masa abin ci da sha,wata yar aiki ta bangaren Momee ta shigo tare da Cewa Saudatu kizo inji Momee,Haka kawai sai Ahleef yaji haushi da yar aikin ta kira ta da Saudatu kai tsaye Ko ba komai ai dattijuwa ce da an dan sakaya sunan.
Tsam Umma ta yafa mayafinta ta wuce part din Momee.
Shukura tace zanbi Umma wajen Momee gaskiya ban yarda da Kiran nan ba is better ayi komai a idona Sabo da Momee ta canja mana fuska kwana biyu Niima ta gama zugata, Hmm kina da gaskiya muje to,tare suka jera kamar ango da Amarya, a palo suka iske Niima,Momee,latifa tare da Abba,har Baba yana wajen.
Ahleef tare da Shukura suma waje suka nema tare da zama,Momee Bata Jin haushin kowa sai Shukura Akan yanda Niima take Bata labarin cewar kwadayi ne ya kawo Shukura gidansu,Momee kuma ta tuna tun a asibiti tasan Shukura da kwadayin abinci maybe har kudi ma shi yasa tasan yanda zatayi dole ta dawo gidansu da zama ta hanyar ahleef, Gashi Ahleef yana wulakanta yayanta akan Shukura wacce a duniya suka tsince ta,sannan ta fuskanci Ahleef yanzu yafi damuwa da Saudatu fiye da ita Wanda kwanan nan suka shigo gidansu gwara ayita ta kare kawai.
Abba ne ya fara magana Alhmdllh gaba daya gashi mun hadu,Ahleef kaine babba ta dalilinka kuma abubuwa suke faruwa a gidan nan marasa dadi Wanda bamu gane gaskiyar faruwan hakan ba, ke Niima gamu baki daya a nan fada mana abinda ke faruwa,Momee cikin fushi tace Abban Latifa ba haka za ayi ba gwara farko kowa yasan waye Ahleef a wajenmu har Wanda yake fifitawa akanmu su Sani ni bazan lamunci haka ba, nan fa Momee ta refe baki ta fara kwararo labari tun farkon batan sa har zuwa dalilin da yasa suka je gidan raino suka dauko shi har jarin da Abba ya bashi ya zama me kudi zuwa yanzu komai saida ta fada, Cikin fushi Abba yace Haba Momeen Yara ina hankalinki yake,mene na bayyana jarin da na bashi,wannan gori kika yi masa kuma shi ma danki ne kuma sai da kowa ya sheda kinfi sonsa da yaranki na cikinki,kuma jari dana bashi ki Sani kyauta ne halak malak ba bashi lauyoyi Sun sheda Sabo da irin wannan ranar dama nayi haka,nasan ku mata tunaninku kadan ne abinda zuciyarku ta baku sai ku aikata, ke ai abin kunya ne aji wannan a bakinki,halayen Niima waye bai sansu ba amma kin kasa fahimta.
Ahleef yace kuyi hakuri Abba da Momee Idan na Bata muku kuma bari na fada muku dalilin da yasa bana saurarar Niima da kuma haduwata da Shukura,Haka ya basu labarin Irin wulakanci da cin mutuncin da Niima ke masa da Wanda tayiwa Shukura iri iri, sannan ya basu labarin Haduwarsa da Shukura har zuwa yau, sai ya bada labarin haduwarsu da su Umma har Baba Bayan ya gama ya kara bawa Momee hakuri.
Saudatu tare da Baba Kuka suka fara yi,Abba yace kuyi hakuri wannan ba abin kuka Bane,Momee tace sayi Shuru tunda sunzo zasu dasa mana rashin zaman lafiya a gida musamman wannan kodaddiyar ta furta tana nuna Shukura, Shukura tayi murmushi Sabo da ita Bata wani fushi sai tace kodaddiya kamar Tsohuwar atamfa fa Momee...Babane ya Katse ta da cewar wannan Ahleef dai danmu ne na jini wlh,na dade ina bincike a kansa sabo da yanda mutane ke cewa kamarmu daya,ban fadawa kowa ba Sabo da kar ace karya nakeyi, bari nayi lokaci yayi na furta yau Allah yayi,Momee tace tanan kuka Bullo kuma ? Baba shima ya bada labarinsa dana Saudatu kaf bai boye komai ba har sace Ahleef,sannan yace abokin Ahleef Farhan shine ya sameni ya sanar dani tarihin Ahleef kaf anan na gane danmu ne, karshe Baba yayiwa su Momee Addua da godiya na rike dansu da Amana, Saudatu kukan Murna takeyi kawai,Abba yace tabbas biri yayi kama da mutum Yanzu muje asibiti ayi gwajin DNA kowa ya fita daga Zargi, Momee ta zabgawa Shukura harara sannan tace muje a duba amma wlh wannan Tunda Bata neman zaman lfy Baza ta zauna a gidan nan ba, kuma Ahleef indai har ni na raineka na Isa da kai sai dai ta koma kauyensu tunda babu dangi tsakani taje can inda ta fito kuma kar naji ka kaita wani waje ka ajiyeta wlh.
Shukura batayi fushi ba duk da taji haushi sai tayi murmushi tare da cewa Momee zan tafi dama amma dan Allah kiyi tunani akan Niima ki daina yarda da zancenta karya ta shirya miki,wani murmushin mugunta Niima tayi taci nasara akan Momee an kori Shukura,Abba yace Kiyi hakuri yarinya ki koma gaban danginki kawai yafi miki mutunci, Shukura tace inshaallah Abba ba damuwa amma bari na baku lbr na,Momee tace ba sai kin fada ba bama bukatar ji,iyayenki Sun rasu mun Sani thats all, Niima tace hakane kawai ya ishemu,Abba ya harareta tayi Shuru.
Ahleef tausayin Shukura ya cikashi ransa ya baci sosai ji yake dama shi aka kora,Da fara'a Shukura tayi musu Sallama ta fita daga palon da sauri Sabo da dab take da tayi kuka,Ahleef ya mike da sauri zai bi bayanta,Momee ta daka masa tsawa dawo ka zauna, Saudatu tace kayi biyayya itama kamar mahaifiyarka ce ta fimu iko da kai a halin yanzu,Baba ma haka yace daga nan suka dunguma zuwa asibiti,kafin su tafi saida Umma ta jadaddawa Shukura ta zauna ta jirasu kar ta tafi, tunda Momee ta kori Shukura batayi adalci ba Sam ta nuna son kai suma bar mata gidanta zasuyi su tafi da Shukura,ita kuma Shukura tasan me Umma ke shirin yi dan karta kara raba da da iyaye kawai ta shirya kayanta kala biyar da komai ta dauki kudin break dinta da Ahleef ya Bata ta ajiye a hannunta dubu goma ta zuba a jaka ta dauki katuwar Yogourt me kauri tare da soyayyun naman kaji Zata dinga sha a hanya ta ta sadada ta fito kenan suka hadu da Niima Zata fita da car key a hannunta, dariya tayiwa Shukura tare da cewa ba a ja dani yarinya, Dutse kato Shukura ta dauka tayi kan Niima dashi ta rotse mata kai,Kara Niima ta saki ta fadi sumammiya jini na zuba a kanta, Shukura tace dama na fada duk ranar da zan bar gidan nan dole sai wata ta tafi gadon asibiti, na yarda zan bar gida amma dole kema kiyi gadon asibiti.
ruwan cikinta Shukura ta taka da karfi tare da tsallakewa tayi tafiyarta ta bar gidan kawai tana goge hawayenta yanzu ta daina ganin Yayanta Ahleef,Niima kuma yan aiki Sun taru a kanta ba abinda basuyi mata ba amma Bata farfado ba,Momee suka bugawa waya,Momee ta fashe da kuka a asibiti tana ka gani ko Ahleef abinda ka jawo mana gashi nan ta kashe min yarinya,Wayar Ahleef ya karba yace a kawo Niima asibiti itama, Abba yace Good yarinya tayi daidai nasan Niima ce ta tsokaneta ai hakan yayi kyau ina ma ta karyata gida uku da kowa ya huta.
Likita yayi gwaji ya tabbatar Ahleef dane ga Umma da Baba Saudatu da Amadu kowa yayi farin ciki musamman Ahleef Farhan ma yana asibitin Ahleef yace yayi sauri yaje ya dauki Shukura kar ta tafi kafin su dawo gida.
sai da Shukura ta shiga taxi sannan ta fara tunanin ina Zata je, kawai tace a kaita tasha tana zuwa ba Bata lokaci ta shige motar Kaduna state motar Bata cika ba Baza ta tashi da wuri ba Shukura ce dama farkon Shiga motar,Lokacin Farhan kuma yaci uban birki a gidan security yace ai ta bar gidan tuni, da sauri Ya kira Ahleef a waya yana sanar masa,da Sauri Ahleef ya bar su Momee gaba daya tare da fadawa motarsa ya fusgi mota a gigice Bai tsaya ko ina ba tashoshi ya dinga bi har ya je tashar da Shukura ta shiga mota saura mutum biyu motar ta cika Ahleef yayi parking motarsa ya shiga tambayar Masu mota yana bada kamannin Shukura,Wani dattijo yace ina tunanin tana waccan yellow Bus din indai kyakyawar nan ce,Ahleef ya je motar har jikin motar ta Window ya hango Shukura ciki tana shan Yogourt dinta tana hawaye,Murmushin da bai shirya ba ya saki ta Window ba zato tana waigowa ta ganshi a tsaye,tunaninta gizo yake mata sai taga da gaske ne,Murmushi tayi masa sabon hawaye ya shararo mata,alama ya mata da hannu ta fito sai ta makale kafada,dariya yayi yana yafitota da hannu ta sakko amma sai ta makale kafada, ga Hadari ya hada gab ake da fara ruwa,Driver yayiwa magana Shukura Zata fita,tace Ni Bazan fita ba Driver,Ahleef ya zaro kudi wanda bai san nawa Bane ya bawa Driver kan ya sauke Shukura,Conductor yaga kudi a banza yace kowa ya fito dole sai Shukura ta fito ta karfi,Ahleef yace duk Wanda yake motar ma an biya masa kudin mota zuwa inda zaije ya fito da wasu kudin ya kara bawa Driver,da sauri passengers suka sauka sai Shukura a ciki taki fitowa gashi an fara yayyafi,Ahleef ganin Baza ta fito ba ya shiga da kansa ya fara miko kayanta kasa conductor ya kai jikin motar Ahleef ana dariya ana shan kallonsu,hannun rigarsa ya nade ya daukota a nutse cikin dabara suka sauko kasa,Ruwa ya tsuge kamar da bakin kwarya passengers suka koma motarsu,ita kuwa Shukura wutsil wutsil takeyi har ta kwace a hannun Ahleef yana Damkota tana kwacewa mutane suna kallo, Shukura ta fara ihu tans zan tara ma mutane ka kyaleni wayyo jama'a a taimakeni barawo ga dan mafiya, Ahleef shima yace kuyi hakuri kanwata ce jiya aka sallameta daga asibitin Mahaukata,tana da tabin kwakwalwa,mutane suka fara Allah bada lfy ai ga alama ma ta nuna Allah sawwake yarinya Allah baki lfy kinji.
jawota yayi jikinsa har yogourt na zubo masa kadan a rigarsa kamar zai maidata cikisa ga ruwa ana shimfidawa,daukanta yayi cak amma ta fara kokawa dashi tana wutsil wutsil ruwa na dukansu,wasu da suka fake a shaguna ta glass din Windows suke ta kallonsu suna dariya,da kyar ta kwace kanta har ta zura da uban gudu cikin zafin nama ya damkota yana dariya ita kuwa ta maida abin da gaske ta wani hade fuska,jawota yayi sosai ta fada kirjinsa ya rungumeta tsam a jikinsa wani irin yanayi suka tsinci kansu ciki musamman Ahleef bai taba Jin irinsa ba sai a jikin Shukura, a kirjinsa ta lafe tayi shuru tana shakar kamshinsa ta daina Wutsil wutsil, ruwa ya kara tsugewa a hankali ta dago da fuskarta tare da zuba masa kallo na musamman Wanda dole sai mutum yaji a jikinsa,Hannunta yarike tare da furta Muje mota duk yayaninsa ya canja,kwar jini ya mata nan take ta kasa yi masa musu ta bishi suka shiga mota,sun jike sharkaf da ruwa,motar yaja zuwa gidan su Farhan, Shukura sai fushi takeyi tana share Hawaye har suka karasa gidan su Farhan.
su Umma dasu Momee saida suka je har gidan Raino aka tabbatar da komai gaskiya ne sannan suka wuce gida,Momee ta zauna tana Jinyar Niima.
a bakin gate ya tsaya tare da Kiran Farhan ta waya,Farhan yana fitowa key ya mika masa yana tsokanar Shukura ta gudu ba sallama,wani dan karamin gida Ahleef ya kai Shukura me dauke da bedroom biyu da palo sai kitchen,ba abinda babu a gidan,gidan yasha gyara Neat dashi,kayan abinci ne kawai sai an siyo,zaki iya zama a nan ? kafada ta makale tare da cewa ai tsoro zanji ka dawo dasu Umma mu zauna tare dasu,Idan har zaku Zauna tare to Umma da Baba sunfi karfin wannan gidan sai a canja muku,baki har kunne Sabo da murna zata zauna tare dasu Umma.
har mamaki Ahleef yakeyi yanda Shukura ke kaunar iyayensa sai yaji ta birgeshi ya kara wani sonta, Daukan Shukura yayi a mota tare da kiran Farhan yaje gidan Momee ya kwaso kayan Umma,Shukura tare dana Baba ya kai can guess House nasa da suka taba zama tare da Shukura,Farhan yayi duk abinda Ahleef yace har Umma da Baba ya kaisu gidan, Momee tana gani har sallama sunyi da Saudatu amma Bata ce su zauna kar su tafi ba, Ahleef tare da Shukura suka Isa gidan,Baba Murna Umma ma haka wai Ahleef dansu ne,a palo suka zauna gaba dayansu,Babane ya fara magana Alhmdllh mun godewa Allah sannan ya bude da Addua,Yau Allah ya nuna mana ranar da muka hadu da danmu na jini,Nasiha Baba yayi sosai,Umma ma Sabo da murna kasa magana tayi,Shukura tayi Murmushi tare da cewa dama na fada miki Umma kuna kama da wani kikace kar na dameki to gashi Umma Allah kin iya Haihuwar me kyau,Dariya sukayi gaba daya har Ahleef, Ahleef yace Baba daga yau Baza ku kara aikin komai ba, Ku huta kawai,Shukura tace Yaya har girki Baza ayi mana muci dadi ba? Gaskiya Umma sai tayi girki,idan naje schl in dawo naga gida rafai wannan ai ba shawara bace,to ai banda aikin gida akace ko cewar Baba,Umma ta furta kyale ja'ira sai kin fada min ta ina kuka hadu da Ahleef da kika mana karya dan uwanki ne,dama ke yar uwarmu ce ashe bamu Sani ba fada mana muji,Dariya Shukura tayi taji kunya tace ai to boye sirrina nayi shi yasa na fadi haka Umma.Hira sukayi sosai karshe Ahleef yace zai tafi zaina zuwa kullum akwai komai a gidan na amfani,Shukura Bedroom dinta ta zaba,Umma da Baba ma haka,Baba shi kam har ya fita wurin abokansa da suke zama can Zone 11,Umma da Shukura basu huta ba sai da suka kara gyara gidan sosai duk da ba Dirty sannan suka Daura girkinsu.
Washe gari da wuri ta Isa makaranta,Latifa tayi mamakin ganin Shukura tunaninta ta koma kauye Bata da gidan zama, Kallon kallo suka yiwa juna Shukura yanzu tace ta daina raga musu ko kadan dama dan Umma take kyalewa yanzu kuma Umma ta zubar da girmanta a wajenta, Sai da ta tabbatar Su Latifa ba teacher a ajinsu ta shiga ajin da gadara,Latifa na zaune Bata san Shukura ta shigo ba suna ta surutu kawai taji anci kwalarta tare da tsarge Hijab dinta gida biyu,kafin Latifa tace komai ta wanketa da gigitaccen marin da kowa sai da hankalinsa ya dawo kansu,Shukura Bata kyaleta ba ta dauki jakar Lateefa ta zazzage komai a kasa tare da Nuna latifa da yatsa Dama na fada miki bashi kika ci,Kawayen Latifa suka taso da niyyar dukanta Latifa tace kar Wanda ya taba ta Ina zuwa ta fita da sauri Hijab din na hannunta,Wajen PC taje tare da fada masa karya da gaskiya,sabo da yana karbar cin hanci wajen Niima Yace ta bari zai dauki mataki mummuna,Nan yasa aka yi sabon Assembly, kowa na schl ya hallara yace Shukura Mohd ta fito,ba Bata lokaci ta fito ta tsaya ya zayyane abinda Latifa ta fada masa sannan yace yau zaiyi maganinta ya samu bulala ya fara tafkar Shukura sai da bulalar ta kare sannan ya mikawa malamai kowa yayi mata guda biyar biyar,Shukura tace a tsaya tana da magana,kowa yayi shuru ana jiran wata maganar kirki sai suka ji tace PC dan Allah ka kara min ko guda ashirince,banza ya mata,ya fara tafiya kenan ta kwala masa kira sir ?ya juyo kuwa sai ta zaro harshe tayi masa gwalo,Pc yace stupid Mad girl, malamai Sun gama nasu sannan yace sai tayi wankin toilet har na 1wk shine Funishment nata, Bayan ya sallami Student Shukura tace wlh sai tayi maganin Latifa da pc itama.
Bayan komai ya lafa,Shukura ce ta samu wata garkamemiyar Kusa ta lallaba wajen motar PC tana Jan murfin ya bude dama bai cika rufe wa ba idan a schl ne,mazaunin Driver ta samu tare da fasa kujerar ta zira kusar kanta ya dago sama inda mutum na zama Zata coke masa Mazaunai,bayan ta gama da sauri ta bar wajen,ana tashi PC ya fito zai tafi gida ya fada motar tare da zama a kai,kara ya kwalla tare da mikewa da sauri ya fito yana danne Mazaunansa da hannu jina ya dan fito har ya nuna a rigarsa,Shukura tana labe tana kallo sai dariya take yi,bayan motarsa ya kalla nan take ya zaro ido ganin an jiketa sharkaf da ruwa da Yogourt a saman kujera,ya tambaya ko anga Wanda yayi masa haka,kowa yace Bai Sani ba.
Latifa tana zuwa gida ta fadawa Momee komai daya faru,Momee tace lallai Ahleef ya raina ni zaizo ya sameni,Niima tace Momee ki daina bata lokaci sonta fa yakeyi zai aureta.
Dalla rufe min baki ai duk ke kika jawo da kin aureshi da hakan Bata faru ba cewar Momee amma bari yazo kafin ya fara son Shukura dole zai Auri Hafcy ko Zahra,Ke kuma ya kuka kare da Mubaraq din?baki Niima ta tabe sannan tace nifa bana sonsa Momee,Allah ya shiryeki cewar Momee.
Niima wani kyakyawan yaro wanda kwanan nan ya shiga 20yrs bai dade da gama secondary schl ba, yaro dan gayu amma dan talakawa ne futuk,Niima ta nace masa taga me kyau tana sonsa sai kashe masa kudi takeyi,sutura Masu tsada, waya me tsada,yanzu mota take son siya masa Ga kudi da take bashi ko yaushe,tun yaron baya kulata sosai ganin kudi yake kulata,yanzu kullum tana yawo dashi a gaban motarta,shi yasan ta girmeshi da wajen shekaru takwas Amma Sabo da kudinta yace zai aureta sai soyayya suke zubawa abinsu,ita tana sonsa don kyansa da iya Shiga shi kuma don kudinta,Ahleef ya linkashi a kyau da komai sau yafi dubu amma Sabo da iyayenta Sun nuna suna sonsa kuma ya fisu kudi duk ta silar iyayensu Shine yasa Bata sonsa tana masa bakin ciki da hassada amma tasan Ahleef samun irinsu sai jefi jefi.tana son yaron Abdullah amma tasan da kyar idan Momee da Abba zasu yarda ta aureshi ita kuma shi take so,yaro kuma bashi da sisin aurenta tana batawa kanta lokaci,kaf dangin yaron Haneef Sun San Niima Sabo da tana kai musu ziyara tana musu wasa da kudi kowa gani yake mutuniyar kirki ce kuma me hankali,
Momee ce ta matsawa Abba lallai yayiwa Ahleef aure ba tare da ya zabo mace da kansa ba, Abba ganin Momee tafi son Ahleef akan kowa yace to yanzu wa kika zaba masa Zahra ko Hafcy ? Momee tace gwara Hafcy itace babba kuma tana da hankali tunda kusan kullum sai tazo gaishe da ni kuma ta tabbata Ahleef bazai tsallake zabinsu ba, Abba yace Kece baki San yaran ba amma ni na Sansu basu da tarbiya ko kadan, Momee tace tunda kace haka to a kyale su ga Islam kawar Latifa,Hmm wannan yarinyar nasan Mahaifinta Sam basu da hankali suma ga asiri da bin malamai,Momee tace to ni dai bazai auri wata Shukura ba kawai ni zan zabo Masa cikin dangina,Abba yace ki dinga tunani Wlh Sabo da abinda zaije yazo,kinyi abin alheri kin rike yaro da Amana amma kina so ki rushe ladanki,gashi kin jawo har Su Saudatun Sun bar gidan,zansa Securities su gano min inda ya maida su su dawo gidan mu zauna tare amma ni Shukura Baza ta dawo ba tunda Bata neman zaman lfy kuma Baza ta auri yarona ba,kai Abba ya girgiza kawai,Yanzu ma yau ta dukar min latifa ta yaga mata uniform,Abba yace tayi dai dai sanda ita Latifan tayi mata ai sharewa kikayi ko ita Bata da daraja ? Ko ba mutum bace ? Da ai na kowa ne kuma bar ganin kamar Bata da gata itama da baiwar da Allah yayi mata,Maganar aure ni ban yarda da zabinki ba ki zabo wata indai basu da halin banza zan daura Auren yanda kike so,Momee tace ga yar kawata Hajiya Binta kasan tana da budurwa mate din Niima,ae to dama dama su amma itama yar Tata ai ba wata ta kirki bace,kullum yarinya gantali itace yawo kasa kasa amma tunda kina so zamuje ayi tambaya asa ranar biki duk abinda ya biyo baya kiyi kuka da kanki,Momee tace na yarda hakan,Sunan yarinyar Nafeesa sai ka sanarwa Ahleef Umarni ne ba shawara ba Nima idan yazo zan fada masa da kaina.
murmushin takaici Abba yayi kawai ya fita,Momee kuma ta sa Securities su gano mata inda Shukura dasu Umma Suke zama,su dawo dasu Saudatu gidanta amma Shukura su saceta su kaita wata State din kawai su barta a can yanda kafin ta dawo ko Ahleef ya ganta an daura aure shike nan dole su hakura da juna.
Bell aka buga ta tashin yan schl,Shukura ta fito kenan taga Niima ta fito daga mota Zata je staffroom da Sauri Shukura ta tafi da gudu ta yiwa Niima wata wawar bangaza sai da takalminta me tsini ya Gurde ta, ta fadi kasa kashin Niima ya goce ihu ta fasa kafin kace me Shukura tace na rama nima ta fice daga schl din da gudu,tana fita Securities da Momee tasa suka damke Shukura tare da dannata a mota ta karfi tana kuka da zullo,Ahleef ya zo shima a motarsa tun daga nesa ya hango yanda aka kakaba Shukura a mota ta karfi amma kamar Masu aiki guards din Momee,kafin ya gama tunaninsa motar ta bacewa ganinsa tuni,yabi bayansu amma ina bai kamasu ba tuni Sun bace,kamar zaiyi hauka haka yaje schl aka tabbatar yanzu ta make Niima ta fita da gudu,Latifa tana kuka ta kama masifa wannan tsinanniyar kake nema kalli yanda tayiwa Auntyna,Ahleef bai san sanda ya kwadawa Latifa mari ba tare da cewa ni sa'anki ne ko Shukura saarki ce da zaki zageta,tsaki yaja ya bar schl din zuwa wajen Momee Direct.
Yana shiga ya iske Baba da Umma har an dawo dasu part dinsu na da, Yasan ma Momee ce itace tasa aka sace Shukura kenan.
Shukura kuma tana mota Suna zuga uban gudu da ita,ta kalli Wanda ke kusa da ita tace nasan hanya ai idan birnin sin zaku kaini zan dawo ne, Kai Driver karo karfin ac nan Sabo da naji dadin kallon garuruwa a hanya,Daya a cikinsu ya mika mata Maltina gashi ance kar mu barki da yunwa,karba tayi tare da cewa lallai tafiyar nan zatayi dadi musamman ma idan kun siyo min tsire ina ci,a hanya suka tsaya aka siya mata su tsire da sauransu,tana washe baki tace yawwa, Driver yace amma Yarinya kina da kwadayi wlh, kyaleni naci kunga ko da na mutu sai a kaini kabari da Nauyina ba a kanjame ba, naje lahira bulbul dani,dariya sukayi Gaba daya.
wai ku wannan dalilin ne ya sa zaku saceni ? Me nayi ? Ina zaku kaini ? Ni wlh Ahleef dina Nake son gani,dan Allah ku kaini muyi Sallama,yanzu hankalinsa zai tashi,ga Umma da Baba kuma na bar wayata a gida sai ta fashe da kuka har ta basu tausayi ma,suka kara Siya mata kayan dadi amma Sabo da ba kwanciyar hankali kasa ci tayi duk zalamarta tunanin Ahleef kawai takeyi har bacci ya kwasheta.
AsmaBaffa
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
21-25
Official
By
AsmaBaffa
JIN DADI SABO FANS ga page naku again ina godiya.
Basu tsaya da Shukura ko ina ba sai wani kauye can Cikin Igbo Land dake Anambra state,tana Bacci dan rashin tausayi suka shafa mata wata powder Wanda ko ta tashi Baza ta iya tuna daga ina take ba sai bayan 1mnth ko wks lokacin kuma tuni anyi Auren Ahleef shike nan ko ta dawo a banza,su kansu sunji tausayin Shukura,daya cikinsu yace gaskiya ban yarda da garin nan ba rashin imanin yayi yawa is better mu kaita kasar Hausawa tunda idan ta tashi Baza ta iya tuna komai ba, wasu ciki sukace a kyaleta kawai haka sukayi tafiyarsu zuciyoyinsu cike da ta tausayin Shukura dake kwance gefen titi,kasar arna ba me taimako Ko kulata basuyi ba kowa harkar gabansa yakeyi,har dare yayi sai da 9pm tayi sannan ta farka,ta kasa tuna Komai,yunwa ke cinta kawai sai ta fashe da kuka ta rasa daga ina take ina take yanzu.
Kusan Ko yaushe yankin can kudu ruwan sama ake musu,yanzu ma ruwane ya tsuge baka ganin komai sai yan gidajensu tsalli tsalli kowa yana gidansa,zagaye suke da gonakinsu duk ko ina abin tsoro,ruwa ke dukanta sosai gwanin tausayi,kuruciyar Shukura sai ta zauna wai wanka takeyi a ciki kowa sai yayi tunanin Hauka ce ta mata sabon kamu,sai da ta gaji ta nufi wani gida kusa da ita taje ta dinga rafka sallama,wani murjejen kato ne wani dunkulelen gardi ya fito dauke da kafceciyar addarsa kugunsa daure da wani bante ba Riga, yaren igbo yayi mata cewar lfy ? Daga ina take tayi saurin bashi amsa kafin ya yanke mata kunne daya, Shukura kuma ba ajin yaren sai turanci shi kuma a kauye yake bai iya turanci ba,zancen kurame tayi masa ya bata wajen kwanciya da kyar ya gane,sai ga wata narkekiyar dattujuwa da daure kirji ta fito tare da tambaya lfy, Mijin nata ya bata labari,tace to kwana daya tal Zata yi ta bar musu gida,da zancen kurame suka fada mata,ta bisu cikin akurkin dakinsu matar ta bata zani da wata t-shirt ta canja kaya,na jikinta kuma ta shanya su,Sannan ta dan dunkule gefen wata tabarmar kaba,ta kwanta,mutanen Sun San ba bacci takeyi ba kiri kiri suka kama baje harka Shukura sai Nishi take ji da gwalangwalan dinsu,ita Bata gane me sukeyi ba.
Haka Shukura Ta kwana da yunwa,da sassafe matar tace to gari ya waye ta bar musu gida Idan ta Gama,Alwala da sallah shukura tayi tare da adduoi sannan ta duba taga matar ta fita kawai ta bude wata tukunya da taga matar tayi girki, ta samu egusi soup da sakwara taci ta koshi Ta gama kenan sai ga matar ta shigo ta tarfa Shukura tana cinye musu abinci,da gudu ta fita sai gata Sun dawo da mijinta tare da wasu narka narkan Maza kowanne dauke da Adda,Suna cewa Sun kama barawo dodo zasu kaiwa jininta,da gudu Shukura ta fita tare da banke na kofar tayi Gaba da matsiyacin gudu,su kuma suka rufa mata Baya da addarsu Allah yasa ta maida kayanta jikinta,har bakin titi suka rakata amma Sun kasa kamata sai hakura sukayi dole.
Ahleef bedroom din Momee ya shiga tare da sallama Gaba daya a firgice yake,Murmushi Momee tayi tare da cewa Son lfy na ganka haka ? Cike da girmamawa ya samu waje ya zauna sannan cikin tausasa kalamai Momee ina Shukura ? Momee nasan ke kika sa akayi kidnapping nata,pls Momee Idan bakyaso na kulata wlh na hakura ki dawo da ita kar rayuwarta ta cutu tana ya mace yarinya kamar wannan, nasan Halayenki Momee uwace ke ta gari wacce tasan darajar dan Adam,Murmushi Momee tayi Bata boye masa ba ta sanar dashi abinda tasa ayiwa Shukura,Karshe kuma tace kaje gidan Hajiya Binta Kawata ka nemi yarta Nafeesa ku daidaita ko 1mnth baza ayi ba za ayi bikinku,Abbanku ma ya Sani zai fada ma, kuma zan sanarwa Saudatu da Baba,wannan yarinya kwadayayya wacce Bata kaunar zaman lfy, ina kaunarka Ahleef baza ka auri waccar yarinyar ba, wlh Momee ba sonta nake ba kawai taimaka mata nayi,zan yarda ku aura min ko wace amma pls Momee ki dawo da ita ko wajen danginta a maidata,ko ki fada min State din da kika sa aka kaita,Tabe baki Momee tayi karshe tace wlh Baza ta fada ba kuma Baza a dawo da ita ba kuma ka sake naji zancen wurin Abbanku sai ranka ya baci.
Momee ya kyale kawai ya fita da sauri bai zarce ko ina ba sai wajen su Saudatu da Baba ya sanar musu komai,Umma ta shafa sumarsa tare da cewa yanzu Sun fimu iko da kai kayi halacci kayi musu biyayya da shi kadai zaka saka musu sannan ka dage da addua kawai.
Godiya yayi musu ya wuce wajen Farhan tare da bashi labarin komai Farhan ma nasiha yayi masa kan yayi biyayya kawai,amma banji dadi ba a rasa wacce za a baka sai Nafeesa yarinyar da kullum tana titi yau wannan kasa gobe ma waccan kasa tana barikinta Momee batayi tunani ba,yanzu zancen da nake maka saurayinta wani dan china ya dauketa Sun tafi Korea idan ta dawo kuma ta fake da Business,Wlh ni ko Bed bazan iya hadawa da ita ba cewar Ahleef, Farhan sai dariya yake masa.bayan kwana biyu Ahleef ya tambayi securities na Momee wanne state suka kaita ? Amma sai suka ki fada Momee ta hanasu wai,dole ya hakura ya koma addua.
Ahleef bai taba tunanin haka ya damu da Shukura sai yanzu, ba wai So ba kawai birgeshi takeyi sannan da tausayinta da yake ji shi yasa ma ya shiga wani hali a kanta,kwanaki kadan kowa yasan Alheef yana da damuwa,Komai gagararsa yake yi har Office ma komai a hanun Secretary ya barshi,baya murmushi Ko Kadan ya gama fita a hayyacinsa,bashi da aiki sai tunanin Shukuransa yana tuna yanda suka zauna tare gida daya tana masa kuruciya iri iri,haka ma yake tuna murmushinta tare da dariyarta,bata fushi Sam,watarana idan ya tuna yanzu tana can maybe rayuwarta ma ta lalace har kwalla yakeyi,ga Auren Nafeesa da Momee tace dole ne domin Abba har sunje sunyi tambaya tare da sa ranar aure nan da 1mnths,Abba baiyi da ka ba saida ya tambayi Ahleef idan baya so Baza ayi masa dole ba, ganin Momee tana so kawai sai yace yana so,amma Momee anan tayi son kai,lokacin da Niima taki yarda da Auren Ahleef ai Bata yi mata dole ba, gashi kullum a kawo samari take amma bata ce komai ba, shi kuma Ahleef ganin tun yana jariri ta raineshi tasan bazai mata musu ba tunda bashi da gata sai su shine ta nuna son kai akan Shukura tayi fada Da yaranta,Tana son Ahleef amma akan Shukura ta jefashi wani hali kuma babu alamar fasawa.
Hafcy kuma sunji Ahleef zaiyi aure bakin ciki ba Wanda basuyi ba karshe ko wacce tace Baza ta hakura ba sai Sun tabbatar an fasa wannan aure sai Sun tarwatsa komai,Mubaraq bai samu shiga wajen Niima ba, wani yaro take so Wanda da Auren wuri tayi sai ta haifi kamarsa.
Baba da Umma suna zamansu lfy da Momee ba wata matsala tana kyautata musu sunyi kyau tare da murjewa. Sunji ba dadi da za ayiwa Ahleef Auren dole amma basu da iko a kansa dole sai dai kallo gudun kar su yi butulci shi yasa suka sa ido.
Amarya Nafeesa kuwa tunda taji Ahleef Zata aura take sheka uban murna kamar ta zunguro lokacin, Ango ko zance baije ba baibi ta kanta ba.
Makarantar su Shukura sunji labarin barin gida da tayi Latifa ta Baza cewar ta tafi yawon karuwanci.
Kamar Kullum Ahleef kwance yake saman lafiyayyan Bed dinsa yana faman tunanin Shukura bai ma san ya fara hawaye ba, Momee ce ta turo kofar a hankali,da sauri ya goge ido tare da fara baccin karya,Momee ta juya tuna ninta Bacci yakeyi.Tana barin dakin yaci gaba da tunaninsa wanda kullum karuwa yakeyi baya sauki,Harkar bikinsa kuwa Farhan da sauran frnds su suke komai.
Shukura tunda arna suka kifota da Adduna Bata tsaya ba sai da taje jikin wani gida shima a kauyen,Wani dattijon iyamuri yayi mata turanci Hey! Young Lady where are you going ? Whats Happening ? Shukura tana haki tace i need a help,wasu ne suka saceta amma ta manta inane garinsu,mutumin yace ta suje gidansu yana da mata sai ta zauna zuwa kwana biyu dodon tsafinsu zai fadi garinsu,Matarma me kirki ce ta bawa Shukura wajen kwana da abinci kalar nasu,tace amma da Snail tayi miyar,Shukura tace ko bera ne a ciki Zata ci haka bare wani snail, dare ya tsala gari tsit Mutumin ya sadada a hankali ya kwanta a bayan Shukura kamar matarsa yana mata goge,tana farkawa ta tsala ihu yatashi a guje zai koma wajen matarsa,matar kuma taji ihu ta fito a guje sukayi karo da kai gwaraf,sai Ihu suka koma daki Gaba daya,matar dama tasan halin mijinta, Washe gari kuwa da sassafe matar tace Shukura ta bar mata gida Zata kwace mata miji.
tafiya Shukura ta dingayi a hanya har ta hadu da wani matashi tace ya taimaketa ita yar arewa ce, nan take ya kaita inda Zata hau mota,Ba Bata lokaci ya sata a motar Anambra City tare da fada mata yanda zatayi,ya biya mata kudin motar sannan ya bata 3k,ta dinga zuba masa gidiya sannan suka wuce tana mamakin ashe a ko ina akwai mutanen kirki.
Me taxi ne ya sata a Motar Kaduna state da kyar ma suka dauketa kudinta bai kai ba, wani bahaushe dan cirani Wanda shima Kaduna zaije shine ya cika mata kudin motar.
sun sha tafiya sai cikin dare suka sauka a Kaduna lfy,Matashin yace to shifa kauye zaije a kauye yake,Shukura tace dan Allah ya taimaka ya tafi da ita gidansu can kauyen kaduna saceta akayi kafin ta gane gidansu sai ta tafi,Matashin yace ba damuwa muje,taji dadi tace ya sunanka ? Yace Jamilu ke kuma fa ? Shukura ta furta sannan suka shiga motar kauyen.
Jamilu neman kudi yake zuwa Anambra dan cirani ne,iyayensa Sun rasu kakanninsa suna raye su suka rikeshi har ya girma suke tare gida daya,baiyi karatu ba Sabo da rashin Gata shi yasa yake tafiya neman kudi.
Dattijon me Suna Malam Hari zaune yake kusa da matarsa Rahina suna hira a tsakar gida sai ga Jamilu da Shukura Sun shigo da sallama,Ko zama Jamilu baiyi ba ya sanar dasu abinda Shukura ta fada masa a kanta,babu wani damuwa suka tarbeta a mutunce,Tun Bata saba dasu ba har suka saba da juna ci sha da komai suke Bata duk da cewar na kauye ne Shukura Bata Jin dadinsa Sabo da ita ko a kauyensu ma cimarta dabance, sati daya Kakan Jamilu wato Hari yace tunda har tana iya tuna garinsu a kauyen Jos to zai Bata dubu uku kudin mota,baza su iya riketa ba dan Adam abin tsoro ne,Rahina ma tace wannan gaskiya ne ta tafi wurin danginta amma a kyaleta zuwa sati biyu ko uku.
Sati biyu tsakani Shukura ta koma Normal ta tuna Ahleef da Abuja da komai ma,ta dawo Hayyacinta,matsalarta daya tunanin Ahleef daya addabi ranta ba dare ba rana,yanzu ta tabbata Son Ahleef Ya kamata sosai,tun bata yarda ba har ta yarda,tana tsaye cikin daddazon mutane a kauyen mata da maza ana wasannin gargajiya,sai kallonta akeyi a kauyen anga kyakyawa,tunawa tayi yau rabonta da Abuja 3wks kenan karfa Ahleef yaje ya manta da ita ya auri wata,kara ta saki kowa sai da ya firgita ana kallonta ta dafe bakinta da hannu tare da tsayawa cak,sai ji akayi tace Ahleef zai so wata,sai ta fara falfala sauri kafin kace me ta koma gidansu Su Jamilu tace Zata tafi ita gida, Rahina tace ta bari sai gobe amma fafur Shukura tace tafiya zatayi, kakan Jamilu ma ya hanata tafiya yace ta bari wani satin zai kaita Abuja da kansa,ba damar tayi musu kuka kawai ta fashe musu dashi.Shukura Bata san ma bikin Ahleef saura kwana bakwai ba.
Kullum Shukura kuka takeyi ba ji ba gani Bata iya cin komai ita sai ta tafi tun Su Jamilu Suna Bata baki har suka kyaleta,Malam yace 'yar nan kudi nake jira na samu sai mu tafi,Cikin sheshekar kuka Shukura tace ni a kyaleni a gani ko ba sisi sai na koma Abuja ko da Allazi wahidin ne,dariya su kaka suka dinga yi, Shukura tace kaka wajen mijin da zan aura fa zanje, So kuke yayi sabuwar budurwa ina nan,Rahina tace oh yaran yanzu ba kunya,Shukura tace yo ke kaka me kuka iya a soyayya, Kin taba zama kamar yini daya kinyi tunanin Malam Hari? Rahina tace mu da ake mana Auren zumunci tun muna yara ina muka San wani tunani yar nan,.
Shukura tace tab wlh an cuceku ni kuwa ina yin tunaninsa kullum kullum,harfa tunaninsa nakeyi yana min dariya,Malam yace ya sunansa yar nan ? Ahleef sunan larabawa ne baku ganshi ba kyakyawa cewar Shukura, to wai kai malam ka taba siyawa Kaka kayan dadi ? Malam yace bazan iya tunawa ba, ni kuwa kullum sai ya siya min,muje yawo dan Allah kaka mu tafi gobe,Kaka yace sai kudi sunzo,Shukura tace sai kace mutum haka zasu zo su sameka da kafarsu?
Washe gari da safe Shukura dasu Malam suna zaune ta kalli buhunan masara,gero,dawa etc tace kaka kuna da wannan amma bakwa cin dadi,ku siyar dasu mana mu a yanka mana zabbi sai ku zauna kullum kuna cin tuwo,Kaka yace sarkin kwadayi kenan ke dole sai anji dadi, ba wai kullum ba Kaka amma idan akwai sai aci,idan babu an san babu sai a hakura, Kuka ta kara fashewa dashi sai an siyar da buhun masara Sun tafi Abuja,Hari da son kudi yace Baza ta sabu ba bindiga a ruwa, Shukura tace to bani bashi muje Ahleef zai biya me kudi ne,Malam yace bada ni ba yar nan. Jamilu yana son Shukura amma yasan tafi karfinsa matar manya ce shi yasa ma bai damu kansa ba.
Ahleef kuwa ya rame ya kara haske kullum tunanin Shukura yakeyi shine dalilin da yasa aka ce ba party ba komai kawai aure za a daura a kai Amarya,bangaren Amare ma sunyi shiri tsab an kashe kudi duk da cewar ango bai taba zuwa zance ba,itace take binsa Office baya saurarta ko kallon arziki Bata samu,Amarya kuma da iyayenta laifin Momee suke gani,Nafeesa taci alwashin tana Auren Ahleef Zata mallakeshi sai abinda tace,Momee sai ta koma abin kyama wajen Ahleef.
Umma da Baba su nasiha da addua kawai sukewa Ahleef.
Kwanci tashi yau ne daurin Auren Ahleef 12pm za a daura, mutane kasa kasa suke sauka,yaune kuma Baba, Jamilu tare da Shukura suka shiga motar dake tashi 7:30am na safe,mota ta tashi Sun fara tafiya duk inda Shukura taga mutane sai ta leko da kanta ta Window din motar ta kwala magana da karfi Sai Abuja ko da kafar katako Masu dariya suyi,murna takeyi kamar zatayi hauka.11:30am suna Abuja Sun shiga taxi tiryan tiryan Shukura ta fadi Adress gidan Momee a kofar gidan ta hango mazaje sunsha wankan Shadda da alama biki akeyi gabanta ya fadi,Baba ta hango ya dau wanka ya fito,da gudu Shukura ta karasa wajensa ta kyale Jamilu da kaka a mota,Baba ya dinga murna Shukura ta dawo,Shukura tace Baba ina yaya ? a takaice Baba ya Bata labarin komai,Shukura sai kuka,cikin kuka ta dan bawa Baba labarin komai na saceta da akayi.
Baba kaga Wanda suka dawo dani dan Allah shiga mota Baba muje wajen daurin Auren, Baba yace yar nan kina mace ina ke ina zuwa wajen daurin aure,Baza ka gane ba Baba akwai matsala babba Baba dole muje kafin a daura aure,haka Shukura tayiwa Baba wayo shima ya gigice ya fada motarsu taxi suka bi bayan motar su Salman, Malam da Jamilu sai kallon masu kudi sukeyi ashe Shukura gaskiya ta fada masu kudi ne Ahleef.
can Nesa sukayi parking,Shukura so take kawai taga Ahleef amma mutane sunyi yawa,har an fara khudubar daurin aure kowa naji,Shukura ta runtse ido tana hawaye da addua, Baba ma da Kaka har Jamilu sun karasa wajen,Ahleef da dasu Abba suna cikin masallacin,Baban Nafeesa da yan uwansu ne suka ce a dakata kar Wanda ya daura aure,Shuru akayi ana sauraronsu,Yace sunyi bincike an sanar dasu Ahleef baida asali, bashi da iyaye a gidan raino aka dauko shi,shi yasa suka fasa aurawa Niima shi dake yarsu ce shine aka kulla za a cucesu shine za suce yarsu ta aureshi to Allah ya taimakesu ba'a daura ba, kuma Baza ayi da tasu ba karshe yace zamu dawo da kaya tare da kudade da aka kawo amma aure a daura da yar wani ba tasu ba.
A bin Haushin ga yan jarida haka Abba cikin bacin rai ya Mike ya bada tarihinsu dana Ahleef har na Saudatu da Baba,kowa sai da ya tausaya gashi anyi tonon silili a bainar mutane,su kansu iyayen Nafeesa sai jiki yayi sanyi suka ce to Sun yarda a daura,Abba ya rantse sau uku bazai daura ba wlh shima bazai daura da Ahleef ba su bawa yarsu me asali ba dai Ahleef ba, Shukura tana Jin komai tar a kunnenta tsalle ta buga tare da cewa yessss Alhmdllh. Da kanta ta fara keta dubban mazaje ana kallon ikon Allah ta Isa har inda Baba, Kaka da Jamilu suke da sauri ta jawosu gefe can tace Baba da Kaka ku zama waliyai na dan Allah kuce a daura da Shukura Muhammad, Wani farin ciki ya lullube Baba,yace yan uwanki fa ? Ba matsala ? Cike da kunya tace Baba kun San tarihina fa, idan komai ya lafa zamuje kauyen.
Da sauri Su Baba suka rankaya tare da kaka suka kirawo Abba gefe suka labarta masa komai murna wajen Abba ba a magana,yace ayiwa Shukura godiya ta fitar dasu kunya,farko Niima ce ta tozarta su aka fasa yau ma again kai Alhmdllh.Abba ne yace aci Gaba da Khuduba,Ahleef dai wani takaici ne ya kara ziyartarsa tunaninsa daidaitawa akayi da iyayen Nafeesa za a daura auren,idonsa yayi jajir Sabo da bacin rai,Baba da Kaka sune na Shukura,Abba da Yayan Momee kuma na Ahleef, nan take aka Naura Auren Ahleef da Shukura kan Sadaki dubu dari,Abba shi ya biya sadaki,Maroka Masu kade kade ana ta yi.
Ana ta kara Sanarwa da daurin aure ya dauru,mutane Sun sheda, Shukura saida tayi Sujjada ta godewa Allah,sannan ta karbi biro hannun wani ta rubuta short note a jikin yagin kwalin taba data tsinta a kasa.
Baba ka fadawa Ahleef da sauran Masu sona na tafi gidan kawata a Apo qrts cikin Abuja ina nan zan dawo gobe.wani saurayi ta bawa tace idan yaga Baba ko Ahleef ango ko Abba ya bashi,taxi ta shiga tayi tafiyarta cike da farin ciki.
Ahleef kuwa yaji dadin daura aure da Shukura duk da ba soyayya Suke ba,amma taya za a daura aure kuma Sun San Shukura ta bace ? Amma kuma wani irin farin ciki yake ji marar misaltuwa.Farhan da sauran abokai ma haka,labari tuni ya kai kunnen Momee amma taji haushi dole sai da aka daura da jarababba Shukura Ai gwara a kyale Ahleef ba aure akan a bashi Shukura.
Su Niima,Hafcy,Islam etc basu ji dadin lamarin ba, Zahra kuwa tace sai ta raba Auren sannu a hankali.
kowa da abinda yake furtawa har akayi hotuna da komai mutane suka watse sai ango da abokanansa shakikai suna guess house dinsa ana ta tsokanarsa musamamman da Baba ya bashi dan Note din da Shukura ta rubuta.Kaka da Jamilu an kaisu masauki can gidansu Farhan aka kaisu Sabo da matsalar Momee.
Angwaye Suna zaune sai tsokanar Ahleef Sukeyi dan gatan Amarya da kanta tazo wajen ta bada Umarni a daura da ita,Shukura ta birge mutane ta fitar da ango kunya tayi halacci ana ta mata addua,Nafeesa kusan haukacewa tayi da taji ba da ita aka daura ba, laifin iyayenta take gani,fushi tayi tace wlh kuma baraki yanzu ta soma tunda su suka jawo ba a daura da ita ba.
Su Niima Dasu Momee Sai tuge kwalliyarsu sukayi tunda da shukura aka daura to baza suyi kwalliyar bikin ba.
Shukura kuma gidan wata Fauziyya yar makarantarsu taje Suna dan shiri da ita kuma Fauziyya nutsatsiyace ga kirki da wayewa gata ta Iya kwalliya, abinda yasa Shukura taje can Sabo da Momee sannan tafi so ango ya ganta Amarya kamar kowacce.
Ango ya rude kawai shi Shukura yake son gani,ba wai dan tana Amaryarsa ba Dan ya dade bai ganta ba, kuma yana so yaji ina aka kaita wacce rayuwa ta tsinci kanta,yana son ganin lafiyarta.
AsmaBaffa
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
26-30
Official
By
AsmaBaffa
JANNAT,MAMAN MEENAT, QUEEN KK da BBY LUV
Page nakune.
Fauziyya ta damu Shukura da zancen ina kika tafi ana ta cewa karuwanci kika tafi tafi,Shukura tace nasan Latifa ce ta fada bani da lokacin wannan ni yanzu ma da kika Sani Amarya ce wlh so nake ki karbo min rancen Dubu talatin tunda gidanku Masu kudi ne gobe zan baki, so nake na fito a amarya ta kamar kowacce,mamaki Fauziyya tayi ace kamar yar Shukura da aure abin mamaki,a fili tace to Mama ta bani dubu hamsim zan kai mata bank,zan cire talatin ciki na baki zuwa gobe lallai ki karbo wurin ango a sa mata kudinta ba tare da ta gane ba,Shukura tace Inshaallah,yanzu ta Ina za a fara yamma nayi,gidan gyaran jiki zamuje Masu sauki ayi miki na rana daya Kafin ango yazo ya bada kudin na 3mnths,Fauziyya Mamansu ta fadawa komai na iya bikin Shukura,Mama tace kuje gidan sady me gyara tayi mata kyauta ni zan biya,da murna suka tafi driver ya kaisu,Sady tace yanzu za ayi miki gobe ma haka,idan Miji kuma ya yarda sai kiyi ta zuwa har tsawon 2-3mths,kaf jikinta aka yiwa gyaran, sai kuma gashinta yasha uban gyara sai kyalli da sheki.
Lalle aka Zana mata na Amare,da yake Fara ce sai kaji kamar ka saceta tsabar kyau,sai 8pm suka gama sannan,Maman Fauziyya tace saura tsumi kuje gidan Hajiya Mariya itace me tsuma Amare yanda ya dace,basu koma gida ba sai da suka je karbo maganin kala kala Wanda ya dace da Amarya wacce bata taba aure ba tayi amfani dasu,a gajiye suka koma gida, Maman Fauziyya tausayin Shukura takeyi shi yasa bata bari ta kashe kudinta ba albarkacin kawar yarta ce yasa tayi mata,Sabo da haka sai kawai suka siyo ready Made wata Riga ta dubu goma wata yar ubansu,Takalmi da jaka,Sai lace da suka siyo dan dubu goma suka bawa tela Emergency zasu karba gobe da safe komai Sun tsarashi Ahleef ji yake kamar ya zunguro gobe tayi yaga Shukura, da kyar bacci ya saceshi sabo da Murna.
Washe gari da sassafe suka koma gyaran jiki aka yi mata etc.
Sai 5pm Shukura zata ta nemi inda Ahleef yake ba tare da ta koma gidan Momee ba.
Ahleef da wuri ya tashi yana ta duba agogo ko zaiga Shukura,har Bakin gate yake fitowa ya tsaya amma Shuru ya koma Bedroom ta Window kawai yake kalon kofar har 2pm ta wuce sunyi Sallah ana hira amma banda Ahleef ya kasa cin abinci,4pm yana yin Sallah ya fada toilet yayi wanka yasa wata Shadda fara kar dinkin zamani,ba karamin kyau yayi ba sumarsa tasha gyara kamshi kawai yakeyi da sheki,yau harda coka hula baka a gaban goshi,yasa Bakin takalmi,kowa yasan ba karya ya hadu karshen karshe,da sauri ya sakko kasa da niyyar zuwa ya binciko Shukura duk inda take,Farhan da sauran Frnds suka kulle kofar da key zasu tsokane shi,ai kuwa ya dinga masifa suka ki budewa har 5:44pm sannan suka bude suna masa dariya,tsaki yaja tare da ficewa.
Yana fitowa inda motocinsu suke,Sai ga Fauziyya taci uban wanka dake itama me kyau ce fara amma ba kar ba, Sai wata budurwa makwaftan su Fauziyya itama tasha wanka tace sai ta bisu taga bikin Masu kyau da kudi Zeenat kenan, Shukura ce ke binsu a baya tasha doguwar rigar material black and White kamar tasan Ahleef shima Black and White yasa, dinkin irin na Amare ba karamin kyau ta tsula ba, Bata Sa gogoro ba, Dan siririn gyalen Rigar sharara ta yana a saman kanta, ba kowa zai gane Shukura ba zai rantse bakuwar balarabiya ce ko yar India.
takalminta me dan tudu black dai dai tana tafiya dos dos har pose din ta black,Ahleef kallo daya ya mata ya gane abarsa.
Tsayawa yayi jikin motar tare da kafeta da kallo kana ya sakar mata murmushi me kayatarwa,Shukura kunya ta kamata kawai sai ta sadda kai kasa tana tafiya,Su Fauziyya dariya ma ta basu,wani farin ciki ya lullubesu gaba daya kowannensu yana ji kamar ya hadiya dan uwansa,Dago kanta tayi a hankali tana murmushi idanunsu suka sarke da juna,kafin ta karaso shima ya taka yaje har inda take,Su Fauziyya suka gaisar da shi ya amsa,yace su dan jirashi a garden,hannun Shukura ya rike kawai ya jata suka nufi daya Part din,Shukura kuma cewa take Yaya ayi party mu gaskiya,yace yau da kafa daya zanyi rawa cewar Ahleef,dariya tayi tare da cewa kana rawa da kafa daya ni kuma ina dariya da hakori daya,muje muyi wata magana ya furta.
a palo ya zauna saman kujera itama ta samu one Seater, bani lbr me ya faru Bayan sun saceki ? Tiryan tiryan ta bashi labarin komai shi kuma ya kafeta da ido,zuciyarsa cike da tausayinta,waya ya zaro tare da kiran Abba ya sanar masa ya za ayi da Amarya kar Momee ta bada matsala, Abba yace karka damu dole za a kaita gidanka yanzu so nake jibi mu shirya da kai tare da Shukura, Baba da Ummanka muje kauyen yarinyar a sanar musu sannan ta zauna kamar 2wks sai danginta su kawota gidanka kamar ko wacce Amarya,Momee fa Abba ? Kyaleta wannan zanyi maganinta karka damu,bayan ya gama wayar Shukura tayi bacci ashe,a hankali ya taka zuwa gabanta yana kare mata kallo tun daga sama zuwa kasa,lallenta ne ya tafi da hankalinsa ya shiga kallo yana yabawa a zuciyarsa,Kasa daurewa yayi har saida ya rike hannunta yana shafawa,rigarta ya yaye kadan ya shiga kallon Zanen lallen dake kafarta,yafi 10mnt yana kallonta farin ciki yana ratsashi.
Farhan ya kira a waya yaje wajen su Fauziyya ya kaisu gida wajen Umma, shi anjima zai taho da Shukura ta samesu a can.
Yasa an masa take away na abinci yasan tana tashi sai tace abinci Zata ci,sai wuraren magrib ta farka lokacin Ahleef tuni Sun fita Masallaci,bakinta ta wanke yau Bata sallah shi yasa ta zauna tana jiran Ango ya dawo ita kuma ta tafi,
Ahleef ya dan jima sannan ya dawo direct wurin Shukura ya nufa,a Zaune ya isketa,tana ganin ya shigo tace Yaya yunwa,ba tare da yayi magana ba ya nuna mata ledar abunci,a nutse ta zauna taci abinta a hankali har ta gama yana kallonta kasa kasa,Toilet ta shiga tare da wanke hannayenta ta gyara kwalliyarta sannan ta fito,muje na kaiki wurin kawayenki can Wurin Umma suke,bata yi musu ba suka jera kamar ka sace su, kayan jikinsu kamar anko sukayi dama,Escort dinsa ne da motoci Sun kai takwas suka shiga,Ango da Amarya suna Bayan mota Sun lafe abinsu,Sauran Frnds nasa da suka ga Shukura sai mamaki suke dama haka take me kyau,lallai Ahleef yayi dace.
Parking sukayi yan biki hankalin kowa ya koma kansu,Part din Momee suka fara zuwa,tana tsakiya cikin yan uwanta suna hira taga Ahleef tare da Shukura,Shukura har kasa ta gaidasu,amma Momee Bata amsa ba sai ma harara da take aikawa Shukura,Ahleef yana gaishe ta sai ta amsa da fara'a.Shukura a ranta tace kyayi kya gama duk abinda Allah yayi to Dan Adam sai kallo, Hannunta Ahleef ya rike suka nufi part din Saudatu,Momee kuma tana can suna gulmar Shukura.
Umma taga Shukura murna a wajenta ba kama hannun yaro ga kuma danta ya auri Shukura.
Fauziyya da kawarta mikewa sukayi tare da yi musu sallama.
Ahleef ma da sauri ya bar part din Sabo da ya kyale frnds nasa su kawai.
Washe gari aka gama komai mutane duk Sun watse komai ya dawo Normal,Abba da kansa yace Shukura ta shirya jibi za a kaita kauyensu za tayi sati biyu sannan dangi su kawota da kansu, baya son Gutsiri tsoma sannan sai da yayiwa Momee nasiha sosai shine tace to a kai Amarya amma duk abinda ya faru kar Wanda ya kawo min kara,kuma ni bazan shiga harkarta ba taje can tayi rayuwarta da Ahleef tunda ita an raina ta bata Isa tayi magana ba sai ace Bata kyauta ba, shi dai Abba bai ce komai ba yace nan da sati biyu za a kai masa Amarya bayan sunje kauyen su Shukura Sun dawo,baki Momee ta tabe tace a dawo lfy ni dai ko kofar gida bazanje ba akan yarinyar nan kodaddiya.
Washe gari da safe Shukura Shirin makaranta tayi abinta,Umma tace ki bari mijinki ya dawo ki tambayeshi idan ya barki sai kije dan Allah Umma ni zan koma kinga fa na dade ban je,Baba ne ya fito ke shirya ki tafi makarantarki,an gama biki me kuma ya rage,idan yazo zance ni nace kije,Cike da kunya Shukura ta karbi kudin Break dinta ta kara gaba,yau Driver tasa ya kaita har ta bude Zata shiga Momee dake saman bene ta buga mata tsawa,karki kuskura ki shigar mana mota,motocin mijinki basa gidan nan,Shukura Bata ce komai ba ta rufe motar ta fita haka a kafa taje ta makara sosai,Latifa ce me taren yan makara,tana ganin Shukura ta saki dariyar mugunta,sai da tayiwa Shukura bulala goma masu zafi sannan tace wato ke ga Amarya harda Lille kika zo,ubanwa zaki birge ? Shukura tace Ubanki,kawai sai fada ya kaure tsakaninsu,Latifa ta ciji Shukura a kunne kamar Zata cireshi,Shukura kuma ta dankara mata cizo a kumatu,teachers da kyar suka Iya raba fadan amma sai suka daurawa Shukura laifi me yasa tazo da Lalle kuma ta makara,ga laifin dukan senior dinta,ruwa suka Bata da wani ruwa daban suka ce ta dirje mata lallan,Kuka tayi sosai har aka tashesu Shukura aiki takeyi da suka Sata,Ahleef bai san ta tafi schl ba yazo suka gaisa da Umma da Baba anan yaji ta tafi schl, abin ya bata masa rai amma ya danne,taya za ace jiya a daura aure washe gari Amarya ta fita ita ba exam ba Bare ace dole,Mota kawai ya fada kamar zai tashi sama haka ya Isa makarantar.
Shukura sai shara da wanke toilet take faman yi tana kuka Sabo da ta gaji likis, idonta yayi jajir,kamar ance ta juyo sai taga motar Ahleef shima ya gane itace,tsintsiyar ta jefar ta nufo wurin Ahleef tana kuka,ba zato ta fada a kirjinsa tana Kuka wiwi hade shagwaba tace Yaya ta kara fashe masa da uka, hannuta ya kalla sai yaga lallen daya fiso har ya lalace,what ? Ya furta kana yace me ya samu lallen?labari ta bashi sannan tace sai da na fada maka ni bana son makarantar amma kaki yarda dani, Ahleef yaji haushin abinda aka yiwa Shukura,Office din pc ya nufa ya dinga masifa sannan yace schl zai canja mata daga yau.Shukura Murna kawai takeyi da sauri ta yi wurin motarsa yazo zai bude ya shiga,da sauri ta zagaya tare da bude masa tana cikin nishadi za a canja mata schl, murmushi ya saki wanda ke rikitawa yan mata tunani,Shukura tace sai ni matar me kudi wlh wa ya isa yaja Da ni ko lecturer ne dan ubansa,wlh Badan yar gidanku bace sai nayi sharia da ita a kotun koli,kotin daga ita sai Allah ya Isa.
Dariya ta kama Ahleef ,kai gani kake wasa nakeyi hmm,na tuna ma Yaya ana bina kudin lalle da wasu kaya dana siya,da hannu ya nuna mata inda yake ajiye kudi ta dauka ta vile 30k ta maida sauran, idan basu isheki ba kara,sun Isheni Allah ya kara budi na gode dan Umma.
Ya fara driving ba tare da ya kalleta ba yace mene ne aure Shukura ? Yanzu ka rasa tambayar da zaka yi min sai ta aure,aure waye bai sanshi ba bare ni da nake katotuwa, ba surutu nace kiyi min ba,tambayarki nayi mene aure ? Shukura ta kalli saman cikin motar ta tafi dogon tunani sannan tace Kaga idan kayi aurenka to shike nan kayi aure,sai mace ta dinga girkinta me dadin tsiya Tana cinyewa,sai kaga tayi kiba da haske,sannan kuma idan kayi aure Inna tace sai a dinga tararrayar mijin,ni yanzu yaya taya zan iya tarairayarka kayi girma da yawa sai dai na goyaka,Gaskiya ne Amarya cewar Ahleef,sai kuma me ? Uhmm ayi wanka da kwalliya,Ahleef yayi dariya tare da cewa zero baki ci ba tunda baki San mene aure,Allah na fada dai dai kaine dae baka Sani ba,tunda haka kace to bari na sake Sabo, ai dai ance mace ta dinga....sai ta rufe idonta wai kunya a hankali tace tana yiwa mijinta wanka tana silleshi da sabulu,haka aka koya mana a schl, yanda Shukura ke fada masa ya gane Bata ma san mene aure ba,a fili yace ai kuwa kin cinye Gaba daya,murmushi ta saki tare da cewa dama na fada maka ina ja,kwakwalwata na ja,babban kai ne dani,Dariyar da bai shirya ba ya shiga yi,baki ta turo gaba tana Shagwaba Haba Yaya dan Allah shike nan na daina fadama ai,Sorry na daina fada min inji.Shuru tayi wai tayi fushi,saida ya biya ta gidansu Fauziyya aka basu kudin data ranta sannan suka wuce har Maman Fauziyya ya gaisar tare da bawa Fauziyya 20k kauta.
Hafcy tun tana bin Niima har ta gano da kanta gwara ta nemi hanya da kanta,ita kuma Zahra tunda ta samu labarin da Shukura aka daura ta rantse Baza ta kara kula Shukura ba har abada. Malam Hari da Jamilu Bayan anyi musu sha tara ta arziki suka koma kauyensu, Shukura ta basu tabbacin Zata zo watara. Umma kuwa ganin Shukura Bata da gata sai ta fara gyara Shukura da tsumi masu inganci da kuma yanda Zata kula da mijinta sannan kullum Shukura ma tana zuwa wurin gyaran fata,Ahleef kullum sai ya shiga wajen Umma wai lafiyarsu yake dubawa.
4:30pm ya dawo daga Office a gurguje ya shirya Momee tana palo tare da Niima ya wuce da sauri yana tafiya yana sannu da hutawa Momee,tabe baki Momee tayi tare da cewa ga sallamamme an gama shanyeshi wlh da Abba baya kasar nan korarsu zanyi baki daya kawai ka sha wahalar rainon yaro sai yanzu za a nuna min iko,Niima tace ki bari idan Abban yayi tafiya Ahleef ma Sai ki kirkiri kasar da zaki turashi kafin ya dawo an gama komai.
Harara Momee ta bugawa Niima tare da cewa aike kika jawo tunda kika fasa aurenshi,na rike yaro a hannuna za a nuna min iko a kansa.
Ahleef direct part din Umma ya nufa cikin tafiyarsa me matukar birgewa,Door Bell ya danna Umma ce ta bude taga danta wai ita kunyarsa take ji, shi kuma Ahleef kunyarta yake ji lokacin da take ce masa Alhaji tana gaidashi ashe uwarsa ce guda,,Umma ce ta katse masa tunani da cewa shigo mana,cikin Ladabi ya durkusa tare da gaisheta,ta amsa da sakin Fuska sannan ta nuna masa bedroom din da Shukura ke ciki,ya nufi dakin ya kwankwasa Shuru kawai ya murda Handle din kwance ya ganta saman Bed tana sheka baccinta hankali kwance,sanye take cikin wata yar guntuwar Vest iya rabin cinyarta dark blue tayi mugun kyau cinyoyin kukuta lukuta gasu farare kar suna sheki,bai taba ganin Shukura haka ba.a hankali ta bude idonta fes a kansa yana tsaye sai kare mata kallo yakeyi,mikewa tayi ta zauna Gefen bed kafafunta suna lilo a kasa,Hannunta ta daura saman bed gefenta ta dan bubbuga kadan wai ya zauna,ita Shukura fa Bata San ana wani abu ba idan anyi aure ko tsoro Bata ji,sabo da bata da frnds tun asali, gefenta ya zauna.yana shakar kamshinta, itama haka,sai Mutsu mutsu takeyi kunya ta gama rufeta yana kallonta da guntayen kaya a jikinta.
Tana so ta mike domin dakko zani ta kare jikinta amma tana kunya ya kalle mata Mazaune subu subu wanda suke Masu matukar kyau kamar an zana mata su, shi kuma gogan ya ganeta sai gyarawa takeyi ta duburbuce amma sai ma kwanciya yayi abinsa saman Bed, Shuru tayi masa sai wasa take da yatsunta, shi dai kallonta yakeyi kawai,Kamar Baza tayi magana ba sai kuma tace bari naje na dawo,Ok kawai yace da sauri ta dakko Hijab kato har kasa ta saka, a ransa yace aiki ya sameki, 5mt ta dawa dauke da katon tire na abinci,ta jikin kofar tace dan bude min pls, yana budewa ya ganta da tire kato ta shugo a ransa yaji dadi kamar tasan yunwa yake ji sosai,so yake su hada ido amma taki Yarda,zuba masa tayi komai sannan tace gashi,ta bashi mamaki bai San tana da hankali haka ba sai yau abincinsa ya shiga ci ita kuma ta shiga wanka abinta.
Yana gamawa ya Gaji da jiranta bata fito daga wanka ba,sai ya koma dakin Umma, Baba ma yana nan suka shiga hirarsu ,Shukura kwalliya taci kamar Zata je biki,cikin wata atamfa me tsada dakyau fitowa tayi tana kamshinta.
Ya fito zai tafi Shukura kuma zata shiga,sai da numfashin Ahleef ya dauke na wasu lokuta sabo da kyan data yi, Murmushinta ta sakar masa me gigita maza,a hankali yace 11pm ki kawo min tea banda madara,Shukura tayi rau rau Zata fara kuka tace da dare haka part din Momee fa Allah ni dukana zasuyi bare naje har part dinka kai maka abu, ki kawo ba abinda zai faru, shagwaba ta fara kamar yar jaririya Allah ni...ni... Kunya... nakeji zafa ace min dadi miji tun ba a kaini ba ina bin miji,wani bala'in birge Ahleef tayi da wannan shagwabar tata,a ransa yace wai meke damuna ne yarinya karama Zata hallakani abinfa nema yake ya fi karfina,shike nan zan kasa Control,a fili yace
Ni nace kizo baki da tsoro nasani kawai kizo.
Shukuru tace tam zanzo amma wlh indai shegiyar Niimar nan ta tsokaneni sai na wanke mata kumatu fes da maruka Momee kawai zan kyale,amma Latifa kam ai sai na balla mata hannu, Ahleef dariya ya saki kadan,kuma Innata tace indan akayi aure to kar mace ta sake a taka mata birki wajen kula da mijinta,Ahleef yana Murmushi yace gaskiya ne, to ka gani ai dole ma na ci mutuncin duk wanda ke kokarin hanani tarairayar mai gida, Ahleef yace ashe zanji dadi na, Shukura tana murmushi tace kai Ni Allah ya gani bazan iya goyaka ba bare tarairaya, Akwai wata kawarmu a kauye aka yi mata Aure wai muka je ganin Amarya in baka lbr me zamu gani murjejen kato wai ya kwanta a cinyar matar,kuma idan ka ganta wata yar tatsitsiya da ita,Ahleef ya dinga dariya yanda take labarin, baka ganshi ba kamar ya hadiyeta sabo da girmansa ai idan nice Yaya kayi min haka wullarka zanyi.
Ahleef yace zaki kasheni da dariya My lollypop,Fari tayi da ido tace alawar yarace wannan ai haka kawai kace min wata lollypop alawar tsinke ,Alawar yara fa kenan yaya sai kace wani maye.Hmm yace na tafi sai kinzo zaki bani labari me dadi,Shukura tace tab yo ni me kake so na zama shike nan bazan ja aji ba?,zanzo amma ina baka zan gudu,Ahleef a ransa yace ina zamana ma zaki bani labarin ya wuce a binsa yana dariya da Nishadin daya dade bai samu ba, ita kuma ta kunna kallo abinta,Bayan kamar 10mnt sai ga Hafcy,Zahra tare da Niima harda Momee sun banko kofa kamar zasu ballata.
🥰😘🥰😘
Fans kuyi hakuri kwana biyu baku jini ba,ina busy ne,ba halina bane rashin typing akan lokaci kun san in dai baku jini ba to akwai dalili Inshallah baza ta sake faruwa ba.
YAU NA AJIYE TYPING SAI BAYAN SALLAH INSHAALLAH,ZAN TA SAMBADO MUKU BA TSAYAWA SAI ANGAMA.
AYI MIN UZURI FANS.
THANKS ALOT FANS.
LOVE U ALL. 🥰😘😍
AsmaBaff
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
31-35
Official
By
AsmaBaffa
ASMABAFFA FANS CLUB GA NAKU PAGE SABO DA KAUNA,ACI GABA DA SHARHI PLS.
Momee ce ta kalli Saudatu kallon wulakanci tare da nunata da yatsa tana kumfar baki kunyi kadan wlh kunyi tsararo inci kashin yaro,inci fitsarinsa sannan sama ta kai kuzo ku ruguza min farin ciki ,ku rabani da farin ciki to wlh karyarku tasha karya dai dai lokacin Ahleef ya manta wayarsa a dakin Shukura yazo zai dauka yaji abinda Momee ke fada, Momee kuwa taci gaba wa ya sani ma ko ba dan halak bane dan shegene kuka jefar ko kuka siyarwa da yan mafiya Allah yasa aka damke yan mafiyan,na raini yaro a hannuna kuzo zaku nuna min Isa Akan kawai kun haifeshi, da can me yasa baku nemeshi ba, sai yanzu,baku san cinsa ba bare shansa har zaku zo da wannan gantalalliyar yarinyar wacce aka haifeta a gona kan titi, me shegan hadama da son abin duniya an baro kauye an tattare to wlh bari kuji Ahleef ko gware kukayi kuka zo duniya to wlh sai ya sakeki verysoon,idan ma bai sakeki ba to Auren kuwa sai ya kara da Hafcy ko Zahra yanda na rike Ahleef wlh idan na tsine masa sai ta bishi.
Niima tace Momee na fada miki fa Ahleef ba irinda yake ba, yanzu neman mata yakeyi Akan naki aurensa,cikin shege yayi mata fa shine suka hada plan aka daura musu aure, Hafcy wacce jikinta ya fara mazari jin cewar Saudatu da dan dako sune iyayen Ahleef nan take cikinta ya duri ruwa sabo da tunano yanda take cin mutuncinsu,yau gashi dansu take so kamar ta mutu,taya zasu sota a matsayin suruka,shi yasa a duniya wulaknci ba abin yi bane akan kafi wani shima yana da baiwarsa ta musamman, Allah bai halicci dolo ko wawa marar amfani ko wanne akwai nasa baiwar.
Cikin karfin hali Hafcy tace Momee ni kadai zan iya gyara musu zama, ta kalli Shukura data kafesu da ido cike da fitsara,Hafcy tace munafuka saida kika jawo yayi miki ciki kika aureshi mayya dan aci dukiya,Niima ta kara da cewa anji kunya bariki tayi riba harda ciki, Shukura murmushi tayi tace wa yaki karuwa?an samu karuwa ai abin dadine tashin farko yayi min ciki da wuri uwar wata ko saida ta tsufa ta samu da kyar kinga ni abin na godewa Allah ne,kuma...Ahleef ne ya shigo a fusace tare da kwashe Shukura da maruka har biyu,Momee zaki fadawa magana haka,are u Mad? Saudatu da Baba basu ce komai ba kawai suka zauna suna shan kallo,Niima da Hafcy suka kyakyace da dariya,Momee ta kalli Shukura tace ki taka a sannu yarinya yanzu a baki takarda fara kal,u better watch ur tongue.
Wayarsa ya dauka ya fita a fusace zuciyarsa na zafi da jin maganganun su Momee sannan ya mari best frnd dinsa Shukura taya zai iya lallashin sarkin shagwaba kuma yasan gaskiyar komai amma ya take ya hukuntata,su Momee ma suka koma part dinta cikin tsananin farin ciki,Shukura ta kame a tsaye dafe da kumatunta,sai kuma ta fashe da kuka wiwi ta fadi a kasa yi take ba ji ba gani Saudatu sunyi lallashi har sun hakura.
Idonta ya kumbura har 11pm tayi yana jira ta kawo masa tea din da yace amma Shuru, a waya ya kirata bata fasa dagawa ba tace hello!ina tea din? Ya furta ransa a bace,Shukura ga zuciya ga tsoro, haka ta dafa tare da hada komai a tire,Umma tace haka zakije wajen mijin?da sauri ta fada Bedroom wanka tayi ta danyi kwalliya sama sama yanda Umma ke koya mata,Umma tace ki canja kayan bacci,haka dole ta shafa turaruka tasa katon Hijab har kasa ta fito kamar Zata fashe sabo da bacin rai,Umma tace ki tabbatar kin bashi hakuri kinyi laifi, baki ta turo tace kawai dan dankine shine ake nuna min banbanci kawai,dariya ma ta bawa Umma tace ae naji dan dana ne jeki maza dare nayi.
Shukura tana isa part din taci karo da Latifa tana karatu,ajiye tiren tayi gefe cikin sanda ba zato Latifa taji wawan dundu a bayanta har guda uku, bata zaci Shukura bace tunaninta Aljanune kawai ta kwashe da gudu tare da fadawa dakin Momee.Na rama nima cewar Shukuru ta dauki tire dinta har part dinsa,knocking biyu ya bude fuskarsa cike da farin ciki,a gabansa ta ajiye zata fita ya jawo Hijab dinta tare da dawo da ita ciki,burburwa ta fara masa zata kwace sabo da haushinsa take ji sannan gashi daga shi sai Boxers a jikinsa,surarsa me matukar kyau da birgewa a bayyane Bata Saba gani ba, kunnenta ya daura dan lips dinsa me taushi ya furta Ki tsaya ko nayi maganinki kin San ban son musu
ko so kike na kai kararki wurin Umma? wani yarrrr taji bata san sanda ta lumshe ido ba tana shakar kamshinsa,a kunne ya kara rada mata Shuk...kafin yace komai Shukura tace wayyo Allah wash kamar wacce aka cakawa Allura,shi kansa yaji tsoro,again a dai
kunnenta ya sake cewa lfy? noke kunnenta tayi tare da cewa dan Allah ka daina wani iri nakeji ba dadi ni gaskiya zan fadawa Umma,Murmushi yayi tare da rike hannunta zuwa Bedroom dinsa na alfarma wanda ya kai karshe a haduwa..
tsakiyar gadon ya hau yace bani tea baki ta turo irin ta gaji ita haka ta hado masa a cup tare da mika masa ta tsaya masa akai,Zauna mana, kafada ta makale tare da cewa ni fa bacci nakeji tafiya zanyi,Tea dinsa ya kurba kadan ya fara latsa wayarsa,da sauri tace laaaa dan kamo min game dama ita mayyar game ce ko a kauye haka take kwace wayar Baffa tayi ta yi,saman Bed din ta hau ta manta fushi take dashi tana leka cikin wayar taga chat yakeyi a whatsapp kara matsowa yayi jikinsu na gugar juna, Ahleef jininsa ya amsa sosai wani zirzir yake ji, Shukura ma hakan take kuma ta kasa tafiya,game ya kamo mata da kyar Sabo da jikinsa ke mazari,zallar shaawarta yake ji tana taso masa.
Tea dinsa ya shanye ya kasa samun nutsuwa,Shukura kuma ko a gyalenta,Wai baza ki cire hijab dinba?kai ta daga tana game dinta,a hankali ya daga hijab din ya shige ciki yana shakar kamshinta,tana jinsa tace pls ka fito,bai saurareta ba tana game dinta ba ji ba gani haka ta fisge kanta ta karfi tana ungo wayarka indai akanta ne kake min leke leke ga abinka kai Yaya sai kana abu kamar zaka cinyeni ni karbi wayarka nayi tafiyata,Murmushin da bai shirya bane ya subuce masa yace na bar miki wayar cire sim dina ki bani,Baki ta tabe tare da cewa bana so ka kyaleni da yar nokia ta idan nayi kudi na siya ina sa rai da wasu kudade kwanan nan, kana min leke Akan na ari wayarka ina ga kyauta kabani.idan ma ba rashin zuciya irin tawa ba,me zai sa na kulaka bayan ka zabga min Mari.
Kallonta yake cikin nutsuwa yace bakya mantuwa I'm so sorry ban kyauta ba na mari best frnd dita, da sauri tace kana rage min mukami da matsayi matar me kudi zaka ce ina matarka kana lika Min frnd kai wasa kakeyi da auren nan,cike da nishadi yace ai ke kika sa aka daura....kafin ya karasa tace kuma ya dauri hakkina na kanka baja baja kuma sai kasa na zama me kudi idan ba haka ba walakiri kai zai jibga lokacin ni na tsufa a aljanna.
Kwanta kiyi bacci kina ta surutu gashi har Umma ta rufe part dinsu,light ya kashe duf ba haske ya kwanta can gefe rigima ta fara masa sai ya rakata part dinsu ko kulata baiyi ba,haka ta gaji itama ta kwanta can gefe,juyowa yayi tare da matsowa fuskarta saitin tasa cikin salon rada yace Best Frnd kiss me, Zaro ido tayi tare da cewa irin na american film ai kake so?kai ya daga mata wai ae, tab banfa iya ba idan nayi kaji ba dadi fa ba ruwana ka tambayi kanka sai ka miko lips din ai na gwada,dariya ce taci karfin Ahleef,Shukura daga wanne dajin take ne, lips dinsa ya daura saman nata tace wai zaki ake ji ne? Kai ya daga mata tace uhm ai mu duk inda zaki da maiko yake muna nan, a hankali ta wani refato lips dinsa na kasa ta wani zuka kamar tasa a bakin robar lemo,dariya ta kamashi tayiwa na sama ma haka ta jinjina kai tace kai malam banji zakinba sai kamshin alawa nakeji,janyewa yayi yace bari na shiga toilet,wata wardrope ya bude ba tare da ta sani ba, tunda duhu yayi yawa,sai ya jefa sweet a bakinsa ya shafawa lipa dinsa ruwan zuma sama da kasa,ya dawo yace yawwa to ki lashe sosai yanzu zakiji zakin ya zugo miki,Shukura ta kara dallaro harshenta ta lashi lips dinsa kadan taji zaki,yace ya kika ji? Tace cakwai cakwai amma tsaya kyam sai na shanye na yau,Shukura tuni bata san ma ta iya ba haka ta dinga tsotse masa lips ciki kuma taji zaki da kamshin sweet duk da cewa tana jin wani iri a jikinta,a hankali jikinta ya mutu tana jin wani dadi na shigarta,har ya zare mata Hijab bata sani ba, tana ji ya zare mata riga amma ta kasa hanawa,da kyar tace bafa kyau gaskiya, jikinta ya shiga sosai daga ita sai Pant da vest shi ma haka,yana ta kissing dinta tana shafa masa sumarsa,wuyanta ya shiga lasa har ya gangaro kirjinta wanda suke madaidaita dasu a cike sumul sumul,Hannayensa ya daura saman Boobs dinta a tare suka saki ajiyar zuciya,ya shiga latsa su yana murzasu son ransa,Shukura ta fara zame jikinta ni dai ban gane ba gaskiya, ai Bata ida zaucewa ba saida ya fara shansu kamar jariri,Shukura wacce ta gama tafiya tayi wet, amma duk da haka sai da tace kai Yaya sai kace Jariri wai baka jin kunyata nifa ba Umma bace shekaru nawa da yayeka? amma yanzu baka manta ba ka dawo kaina na shayar da kai ai yaci ace ka manta yanzu Kai ba yaron yaye ba, yana jinta yaci gaba da bata salo tana fuskewa har ta kasa ta shiga tayashi itama,jinsa tayi ba komai a jikinsa ya cire boxers dinma sai kawai ta fara masa kuka wai yayi mata ciki ita ya zatayi,Pant din ya cire mata jikinsa na karkarwa idonsa ya rufe,wani Salon sucking down ya shiga gabatar mata dashi,ita kanta yanzu bata san a ina take ba, Sai kukan dadi sukeyi an rasa na wa za a saurara a cikinsu,ba tare da yayi mata komai ba ya samu nutsuwa itama haka,amma sai da ta dawo hankalinta tace ni bana so gaskiya ta fashe da kuka tare da cewa yaya shike nan ba akai Amarya ba kayimin ciki a gida yanzu ya zanyi da abin kunya, sai da ya huta tare da kara karfin ac yace bafa haka akeyin ciki ba.
Shukura taki yarda yace romancing ne tace Allah baza ta yarda ba, yace to zan kaiki asibiti gobe a cire cikin, sai lokacin hankalinta ya kwanta tana ajiyar zuciya zata maida kayanta ya kwacesu ya zubesu a kasa ya shigar da ita jikinsa sosai cikin blanket baci me dadi ya kwashesu amma duk sanda ya farka ko motsi yayi ko tayi sai ya tambayeta lfy? Me ya faru yana murza albarkatun kirjinta.ita ma bata san sanda take shagwaba ba iri iri, cikin tsakiyar dare yace zai kara Romancing dinta taki yarda wai zata samu cikin yan biyu,gaf da asuba da kyar ya shawo kanta ta yarda suka kara murje juna,saida ta gama Jin dadinta ta ajiye Masa kuka iri iri ya Kara mata ciki zata haifi Yan biyu.
Bayan sunyi Sallah tare da azkhar suka koma baccinsu me dadi, har 11am basu tashi ba,Momee tana so ya fito yayi break amma shuru, har sun gaji da jiransa,bayan kuma sun san yana riga kowa tashi a gidan,Latifa tace Momee lfy yake kuwa, Momee tace bari naje na tasoshi,Tabe baki Niima tayi tare da cewa iyayi ne kawai so yake yaje wajen uwarsa yaci,uwar kinibibi tana jiransa shi yasa yaki fitowa yanzu sai mun gama munafukai,Momee tace ya isa ma wlh babu wanda ya isa na sha wahalarsa yace zai min iko dashi.
Knocking kofar tayi tare da murda handle a kulle tajita karon farko kenan da ya sawa dakinsa key,Shukura ce ta farka gabanta na faduwa za a kamata a dakin miji ba tare da ankai Amarya ba.
Jallabiya ya zura tare da bude kofar kadan ya leko da kansa Alamar bashi da gaskiya,Tsaki Momee taja tare da cewa baka da gaskiya, anyway breakfast is ready,Ok kawai yace ta juya ta tafi, wanka yayi ya shirya cikin wasu kana nan kaya,masu uban kyau da tsada,Shukura ma da sauri tayi wanka sannan ta shirya cikin rigar shaddarsa me kyau,kuma tayi tsananim kyau ta yafa dan wani gyalenta na abaya data daura a kanta jiya,turarukansa ta fesa tare da kara gyara dakin neat,hannunta ya rike zasu fito tace wlh kunyar Momee nake ji bazan iya fita ba, Kina matar tawa mene abin kunya?zasu ce ni nake bibiyarka,to sai me kuma common lets go ya figi hannunta suka sauka kasa tare,Gaba daya Momee suka saki salati kamar sunga mutuwa da sauri Shukura ta kwace hannunta ta fece da gudu zuwa part dinsu,Baki Momee ta rike tana kallon Ahleef kamar wanda yayi sata kana ta daure fuska tace haka kuma ka koma lalacewar taka ta kai haka kwafa tayi tace zan yi maganin abin,sumarsa ya Sosa cikin kunyar Momee din yayi shuru ya zauna tare da fara cin abincin,dan kadan yaci ya mike yace Momee na fita,Hmm Office ko kuma wajen waccen tsohuwar karuwar zaka je?
Tunda Mommee ke masa abubuwa bai taba Jin zafin kamar na yau ba,matarsa ta sunna zata kira da karuwa,ko a fuska Momee tasan ransa ya baci,amma sai tace bace min da gani sallamamme wacce ta raineka ka mai dani ba komai ba,dama matsalar rike dan wani kenan watarana sai ya ganka yace uwar banza to ni dai Allah ya gani nayi iya abinda zan iya.
Ahleef baice mata komai ba ya fita abinsa fuskarsa har ja takeyi sabo da bacin Rai,bai tsaya ko ina ba sai part din Umma,Umma na kallonsa ta gane yana cikin damuwa,bayan sun gaisa tace kaifa lfy? Lfy kawai yace,Mikewa tayi ta shiga dakin Shukura a nutse tace mijinki Yana cikin damuwa yata kiyi yanda zai samu farin ciki,na koya Miki komai karki bari ya fita da bacin Rai,Kunya ta kama Shukura da kyar tace to Umma,fita tayi daga dakin yana zaune cikin tunani ya tsinci Muryar Umma tana cewa shiga ciki tana Nan,ba sai na ganta ba Umma Office zan tafi wai shi kunya,Umma ta ganeshi sai tace A'a bana son musu kaje ka sameta Mikewa yayi ya nufi dakin.
a hankali ya tura kofar ya shiga da sallama,bayan labile ta boye,ba zato yaji hannunta cikin nasa,jikinsa ne ya dauki wani shock yarrr... da kyar ya iya dannewa,gabansa ta dawo da sauri tare da kura masa Ido,lips dinsa ya tsuke irin kallon ya isheshi haka,Ya naganka kamar kana da damuwa,gira daya ya dage mata I'm ok me kika gani? Nothing kawai dan na tambayi best frnd dina laifi nayi?yau baza kaje Office? Ango fa nake kin manta sai ayi min dariya ai a samu abin fada,kema baza kije schl ba sai nan da 3wks yana furtawa ya haye lafiyayyen bed dinta ko safarsa bai cire ba kuma yau zafi akeyi, bed ne me kyau wanda yasha gyara haka bedroom dinma Umma ta gyara mata da safe sai kamshi ke tashi.
Ac ta kunna masa tare da Dan karo karfinta kadan, gefen kafafunsa ta zauna a hankali ta cire masa safar kafafunsa,har zata kwanta sai ta fasa tunawa tayi da Umma kunya bai dace ba sai ma yaga bata da kunya kawai sai ta fita tare da rufe kofar a hankali,dama lumshe idonsa yayi ba bacci yakeyi ba,murmushi ya saki me kayatarwa wani dadi ya lullubeshi sabo da yanda yaga tana lallabashi tana ji dashi abin har mamaki ta bashi yar mitsilar yarinya da iya kula da miji.
Umma na Palo taga Shukura ta fito a kunyace ta zauna kusa da ita, bata Rai Umma tayi tare da cewa ya kika dawo Nan me zakiyi ga mijinki can yana cikin wani hali?haka na koya Miki? tashi ki bani wuri tunda ba kya ji,da sauri Shukura ta mike tace to Umma yayi fa bacci,Lallai zamu bata dake tunda abinda zakiyi kenan kin sanni Shukura ki kiyayeni.
Da sauri tace am so sorry Umma ta koma da sauri dakin,Murmushi kawai Umma tayi tare da cewa yaran zamani da haka ake kwace muku miji ko sure fada neman matan banza wai ku Jan aji.
Shukura kuwa a hankali ta shiga dakin ta rasa me zatayi shi kuma ya fara bacci tunani ta farayi to me zatayi masa kuma,kallon fuskarsa tayi a fili tace yafi mace kyau mutumin Nan zankadi Allah me baiwa,still gani tayi yana zufa kamar ma mafarki yakeyi me wahala,yana cewa no...karki tafi...tana tsaye ya farka a tsorace ya hada zufa,kusa dashi ta karasa kana tace sannu mafarki kayi ko,kallonta yakeyi tare da Mikewa zaune da kyar, yace ae scary Dream nayi,Hmmm kawai tace wace kar ta tafi ?naji kana furtawa a mafarki, watace ya bata amsa, wani kishi taji Nan take bata San sanda tace kyakyawace? kallonta yayi da sauri Yana nazarinta sannan yayi Dan guntun Murmushi tare da cewa ae She is so Beautiful,Baki ta tabe tare da cewa hmmm tana da kyau,to ni fa? Yace kema me kyau ce mana Yana leka fuskarta Yana zuba Murmushi,ban yarda ba sai dai ka zabi daya,yace ai kece du ta mafarkin,ba wani Nan zaka ce nice ta mike da niyyar tafiya abinta.
Da sauri ya riko hannunta ya jawota saman Bed din kusa dashi ta fada kwanciya yayi itama ya jawota jikinsa ya manne kirjinta da nasa tare da zame dankwalin kanta ya shiga shafa gashinta me dadin kamshi a hankali,zuciyarta ce ta shiga bugawa fat fat da karfi,a hankali yace mene kike Jin tsoro just relax,da kyar tace ba tsoro nake ji ba,yace gashi Nan zuciyarki na bugawa,ni din? Oh tambaya kike? Yes a Ina kaga tana bugawa,na nuna Miki ne? Bata San nufinsa tace yeah.
Dan matsawa yayi ya raba tsakajinsu tare da daura hannunsa saman kirjinta ya lumshe Ido ya bude har sun koma red idonsa,da sauri ta zame jikinta gefe ni Dan Allah kar na haifi Yan uku jiya Yan biyu ne a cikina yau zaka Kara yawwa na tuna muje asibitin pls a duba idan nayi ciki a cireshi kar abin kunya ya samu a gidan Nan,gani yayi tsakani da Allah take maganar sai ta bashi dariya da mamaki,Lallabashi ta shiga yi sai anje asibiti jiya yayi mata ciki kuma Yan biyu,da kyar ya lallabata ita Amarya ce ta bari sai jibi zasu je.
Momee kuwa sai da ta turo Niima ta Kira mata Ahleef wai me yakeyi bazai tafi Office ba idan bazai je office ba to yazo tana nemansa.
Haka Yana son zama tare da Frnd dinsa ya tafi,Yana zuwa Momee ta fara masifa wanne naci da rashin kunya ne ya tare a gindin Amarya daga aure,to ka shirya jibi zan aikeka Qatar tunda gobe Abba zai tafi ya samu Kiran gaggawa daga British,kai jibi zaka Ka tafi,Shukura kuma Nan da kwana uku zan kaita kauyensu idan ka dawo sai Shirin tarewarta,Ahleef har ga Allah bai so hakan ba,amma idan kana zaune gidan wani kuma akace rikeka akeyi tofa sai hakuri domin dole kayi biyayyar da baka yi niyya ba,kuma dole kayi biyayyar dole baka da yanci sai abinda akace tunda ba gidan ubanka bane.
Dole ya amsa ba tare da ya nuna komai a fuska ba.
Momee ta Kafa ta tsare ta hanashi sakewa shi da Shukura baza ta bari Shukura tazo wajensa ba,idan kuma yaje minti biyar za ta dinga masa aike yazo zai mata kaza,Saudatu ta kasa gane kan abin,ta bawa Baba lbr yace su kara hakuri a gani tukun,ranar da Ahleef zai tafi sallama Momee bata bari yaje yiwa Saudatu da Baba bare Matarsa Shukura,Shukura taci kwalliya zasuyi sallama ta fito da sauri wurin motar amma Momee na ganin haka ta bawa Driver Umarni su tafi airport dake tana motar wai sai ta rakashi,Shukura da Ahleef sai hangen juna ta window Yana kallon hawayenta da kyar ya danne nasa ya daga mata hannu itama ta daga masa,da Kai ya nuna mata ta daina kuka zai dawo,Duk Wanda ke wajen sai yaji tausayin Shukura sabo da Momee ta gama takura ta sosai ba sakewa,ita kuma tafi su iya shege idan so take ta karya komai nasu Dan tafi kowa iya satar hanya,tanayin biyayya wa Momee sabo da Ahleef kuma gashi a gidansu take zaune,idan tayi wani Abu taga Ahleef bai son a Raina Momee da zuriyarsu bata manta sanda ya zuba mata Mari akan Momee shi yasa ta hakura.
Saudatu ce tayi ta faman kwantarwa da Shukura hankali,Momee na dawowa daga airport sai ta tasa Shukura a gaba ta bata Address din kauyensu da Yan uwan babanta dana babarta,washe gari da wuri Momee tace Shukura ta shirya kayanta kaf,ta shirya harda Saudatu da Baba tunaninsu za aje a sanarwa da danginta aurenta da Ahleef, Momee tace Umma ai ba daku zamu tafi ba,ku koma ni na isa wakilci ga Niima da Kawarta Hafcy zamuje,Ba Shukura ba har Saudatu da Baba sai da suka tabbatar ba alkhairi su Momee zasu Kulla ba,har Baba zaiyi magana Shukura tace karkace komai Baba,idan Ahleef ya dawo ga Address Dina Nan idan Yana so na na tabbata zai nemeni komai dadewa,Umma na gode da rikeni da kukayi idan da rabo zamu sake haduwa Umma karku damu,ki fadawa Ahleef kar ya nemi wayata Momee ta kwaceta tun jiya,Nan sukayi sallama Ana hawaye ta fita tare da shiga mota.
Niima taja tsaki tace dole ayi kuka za a koma kauye cin miyar daddawa,Shukura itama ta tunzura tace daddawa kuma kitchin din me dirty dankwali ma akwai Ashe bamu kadai ke ci ba,da ba asan asalin ungulu ba da sai ace daga masar take,Hafcy tayi cagal rufemana Baki ko wlh ki gane kurenki,tsaki Shukura taja tace banza a banza man Kare ke har mutum ce dama,Hafcy haushi ya isheta tace dadin abin dai farin an Kara da mai,Shukura tace ke kuma ya shafa Baki kamar na tsuntsuwa chilikowa.
Momee ce ta buga musu tsawa tace ku kyaleta taji da haushin komawa kauye ga kuma rabuwa da Dana da za ayi dole uwar naki wlh. Shukura Bata Ce komai ba har suka je kauyensu ita ta nunawa Driver ma gidan kawunsu,Niima tace Lallai dole azo karuwanci Abuja,Hafcy tace a kauyen ma wannan kauye ne wai tab,Yara sunyi cincirun do Ana kallon mota da kuma Yan birni,da kyar dattijai da Yan uwan suka gane cewar Shukura ce Maji dadi yar Mirgayi,Nan aka dinga layin kallonta Maza da mata Shukura Maji dadi ta dawo daga karuwanci dama kauye tuni sunce karuwanci ta tafi birni,Yan uwan Baffa suka ce Shukura baza ta shigar musu gida ba yarinya taki aure ta gudu karuwanci wlh baza su laminta ba.
Murmushi Momee tayi tasa aka fito da kayan Shukura tas tace to Bayin Allah kuyi Hakuri ku karbeta gata Nan cikin shege tayi kwanan Nan aka gano a asibiti sati uku Nan gaba zaku ga ya girma,tazo ta likawa Dana Dan ya aureta ni kuma bazan yarda ba,sabo da kar na koreta Allah ya kamani yasa na dawo da ita garinsu kune Yan uwanta kune dolenta ni ba abinda ya hadamu da ita.
Tuni Hawaye ya jikewa Shukura Mayafinta ga tozarci gaban Yan uwan da alummar gari,gashi tasan Ahleef rannan yayi mata cikin Yan biyu yanzu idan ya girma zasu ce cikin shege ne tayi,tana Kuka tace Momee kiji tsoron Allah kazafi kika min,kuma wlh cikin Ahleef ne ya min rannan yasan da maganar ku tambayeshi sai da nace ya kaini asibiti a duba yace zamuje Nan da 2days kuma yayi tafiya,ta juya gaban danginta tace wlh wlh da aurena Kawu ku yarda Dani,Kawu sabo da takaicin Shukura ta bata musu zuriya ya samu ya masgeta da katuwar Sanda Nan take ta sume a wajen,Momee,Niima da Hafcy kansu ya kulle tam Jin Shukura tace Ahleef yayi mata ciki,kuma aurensu ko sati ba ayi ba,kenan dama Ahleef ciki yayiwa Shukura shi yasa suka hada dabara wajen daurin aure aka daura aurensu Dan kar asirinsu ya tonu,Nan Fa suka shiga mota suna ta Muhawara Ana saka da warwara,Momee tana ta tunani dama so take dole tasa ya auri Niima ko Hafcy tunda Ahleef lalataccene to sai dai ko Hafcy ta aureshi idan tana so amma baza ta aurawa yarta Niima Lalatacce ba,baza ta aurawa yarta mazinaci ba,Ashe abinda suka aikatawa kenan shi yasa Ahleef yake haba haba da Shukura,Maimakon Momee ta rufawa Ahleef asiri suna dawowa gida ta fesawa Saudatu da Baba,Saudatu su sun San gaskiya shirmen Shukura ne kawai ko ajikinsu,daga Nan Momee ta dinga fadawa Kawayenta da wasu cikin Yan uwan,Niima kuwa dama kadan take jira kowa daya shafeta ya sani,Hafcy ta fadawa mamansu dasu Zahra,Mama tace ba komai Hafcy ta dage ta aura haka zasu samu kudi ba matsala,Zahra tace ta fasa aurensa wlh duk da tasan itama ba budurwa ba ce Amma baza ta auri namiji me neman mata ba,Hafcy dai kafarta daya na ciki daya na waje.
Ahleef Yana can bai San me akeyi ba Yana ta gwada wayar Shukura Shuru Umma da Baba kuma sai dai suce masa Shukura tana Nan cikin koshin lfy kar ya damu,abin ya fara damunsa.
AsmaBaffa
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
36-40
Official
By
AsmaBaffa
Sabo da Jin dadinku masu Sharhi na baku wannan....kuna birgeni tnx all.
Shukura kwance kasa ta sume,alummar kauye Ana kallonta dangin Innarta dana Baffa babu Wanda ya tausaya mata ko ya tsaya ya saurareta kowannensu ji suke kamar su kashe kowa ya huta da wannan abin kunya,wani Dan matashi ne cikin dangin Rabe ya kwara mata ruwa ta farfado tana zare Ido tana kallonsu tare da Kara tsanar danginta na rashin Zumuncinsu tare da nuna mata kiyayya sabo da iyayenta basa Raye,Nan Mutuwar iyayenta ta dawo mata sabuwa ta fara zubar da Hawaye masu dumi, su kuma manya da Yara mata da maza suna Kanta a tsaye suna mamakin ganin yanda Shukura ta goge ta Kara kyau da Haske,cikinsu wata tsohuwa tace ta tababbata juna biyu gareta gashi duk sai kyalli take.
Wata yar budurwa ta fashe da kuka tace shike Nan ta jawo Mana Babu Wanda zai auremu a garin Nan tayi Mana tambarin da bazai gogu ba,yanzu Ja'e nasan fasa aure na zaiyi yace muma bamu da tarbiya, kawu Babban banza yace share hawayenki ko da suratul Yusufa sai kin samu me sonki kuma yau zan fara rubuta Miki kina shanyewa maganin farin jini haka suka dinga cakaki akan Shukura har suka fara tafiya gidajensu Ana Allah wadai da Shukura,a hankali ta mike ta nufi gidan Kawu da niyyar shiga,Kawu yace Ahir dinki aradu kina tako kasar gidana zan karya Miki kafafu,tasan Halinsa ba Imani,sai ta nufi gidan wani Shima ya biyota da sanda,haka ta dinga zagawa kowa na korarta ta rasa Ina zata shiga,da kyar ta roki Megari ta zauna a gidansa zuwa wani lokaci Amma Megari guda yaki yarda yace saidai ta kwana a yar bukkarsa ta kofar gida ya bata Amma ba a gidansaba, haka ta hakura ta shiga dakin kofar gida kowa Yana kallonta. Matar Megari Talliya tace yo Kai Malam ai kawai ta dawo cikin gida da zama kaga na samu yar aiki,yo me zaisa mu Bata wajen kwana da abinci kyauta a banza tazo ta dinga min aikin gida Ana Bata wajen kwana da abinci
Megari yace Talliya kin kawo Shawara ga dakin cikin gida a Bata ta dawo,haka Liman yasa ta shugo da kayanta akwatuna, har Biyu,Talliya tace oh amma Shukura a barikin masu kudi kike harkalla dasu? Irin wannan Kaya haka ga kyau kin Kara,Shukura takaicin ya rufeta tace da aurena fa ni ba bariki nayi ba,mijina Yana Nan,Talliya tabe Baki tayi tare da cewa ke kika sani ni Dalla tashi ki Kai min Nika,ki dawo kuma aikace aikace na jiranki ba hutu kikazo yi ba abinci da wajen kwana fa zamu Baki duk lalacewarki danginki kaf sun gujeki Amma mu muka dauko wa kanmu,da can sanda iyayenki suna da Rai wanne irin iyayi ne bakiyi a garin Nan ba da tabara ke ga yar gata,to yanzu Ina gatan?
Shuru Shukura tayi tasan yanda Yan kauyen suke mata hassada tun asali sabo da ta fisu, karshe dai cike da bakin ciki ta fito Kai Nika,sai nuna ta akeyi a kauyen tayi cikin shege ta dawo daga bariki,ko bako ya shigo kauyen sai ya ji labarin, bayan Shukura ta kawo Nika ita tayi abincin gidan me gari ga uban yawa kamar na gidan biki ba karamar azaba Tasha ba,bayan ta gama sai da tayi wasu ayyukan a Daren sannan ta samu Talliya ta barta tayi wanka tare da sallah karshe aka Bata tuwon taci Wanda Babu dadi sabo da yawansa kuma ba kayan Hadi ne a cikin miyar ba,Amma duk da haka ranar da kyar aka samu miyar dumamen safe ta ragu kadan sabo da dadin girkin Shukura kowa yaji dadinshi.
Ko da Shukura ta kwanta in Banda tunanin mijinta Ahleef Babu abinda takeyi Nan ta tuno irin Jin dadin da sukayi ranar da suka kwana tare,Nan take ta lumshe Ido tare da dakko rigarsa jallabiya cikin kayanta tasa abarta ta kwanta tana tunaninsa Nan bakin cikinta ya yaye Baki daya duk da frnd dinta ne tana muradin kasancewa dashi har karshen rayuwarta.
Washe gari tun da asuba Talliya ta tasota a masife ta damawa Yan gidan Koko ga Yara kana na har da almajirai a gidan birjik, megari bayan yasha miyar jiya yaji kamar ya tsinke yatsansa sabo da dadi yau ma ya kurbi Koko a fili ya firta shegiya bariki badan ba abune me kyau ba ai da ka tura matarka ko Dan ta koyi girki,Harara Talliya ta watsa Masa tare da cewa to me kake nufi? Murmushi yayi tare da cewa ja'irar yarinya da ita Amma ta iya girki haka duk shagwabarta Ashe ta iya girki gaskiya ki koya,tsaki Talliya tayi ta bar dakin fuuuu a fusace.
Da Rana Shukura duk ta gama aikin da aka sata,sai rike kugu take ta gaji sosai tana rokon Allah kar cikin Ahleef ya zube, Amma Talliya ba Imani tace daura girkin Rana kiyi Mana dafadukan shinkafa da manja, Shukura ta gingima tukunya ga itace hayaki ga Rana haka ta kwaciba girkin,tana sani tayishi yanda bazai dadi bama, Ana zubawa me gari da almajirai da sauran yaran gida haba kowa Santi yake zubawa har ita kanta Talliyan,Shukura ta kasa cin abincin sabo da ba dadi Amma su a haka yafi na Talliya sau dubu,Megari sai washe Baki yakeyi,mamaki ya kama Shukura tana cikin haka ta fada tunanin Ahleef dinta Wanda ya fiye mata komai ita kadai sai gashi tun tana Murmushi ta koma sheka dariya, dukkan yaran gidan da Me gari kansa kowa kallonta ya koma yi Baki bude, wani cikin yaran yace Wlh wannan me kyau ce, Me gari yace ke Lfy?shuru Shukura tayi Nisa har kanta take girgizawa tana dariya,Talliya Baki bude tace ke Dan Uwarki ba dake ake ba iyeeee ta zabga mata duka a baya, da sauri ta dafe wajen tana sosawa cike da Shagwabarta tace wayyo Mijina,Talliya tayi zaton da Megari take ta kirashi da mijinta, tace karuwa uban waye Mijinkin?
Nan take Shukura ta saki sabon Murmushi kamar ka saceta sabo da kyau sannan ta kalli Talliya tare da turo mata Yan lips dinta jajaye tace Mijina fa can kin San sunansa ma abin so ne,Ahleef,kyakyawa,duk kyauna ya fini,Babu abinda nafi so a jikinsa irin idonsa,da Murmushinsa wlh Anty Talliya idan kika ganshi sai kin kusa Suma,ga kudi,ga ilmi,ga addini,ga hankali,ga nutsuwa,ga iya soyayya ni kadai naji me naji dole na haukace ko....Dalla rufe Mana baki Lallai Babban bariki kika buga,Shukura tace wlh mijine na sunna, Me gari yace Ke karki Raina mana hankali fa yanzu Kya bar Mana gida.kinje Karuwanci ae kinyi ki Mana shuru kawai ki ajiye iskancinki gefe can.
Shukura yau tayi sati guda a gidan Me gari Amma kullum aiki take kamar jaka a gidan, komai an sakar mata,duk tayi duhu ta rame kadan,ga tunanin Mijinta da ya addabeta,yanzu duk kayanta akwati Biyu manya Bata sawa sai Jallabiyar Ahleef da kuma wata rigar shaddarsa light blue,duk inda zata a garin a haka take fita sai dai ba kazanta zaka ganta fes kullum sabo da Megari Yana Bata kudin sabulun Dan ma watarana idan son dadi ya motsa sai ta siyi kifi soyayye da kudin taci abinci dasu.
Shukura ta koma wajen dangin mahaifinta Dana Innarta ko zasu karbe ta Amma sunki yarda taje yafi a irga Amma sunkiya,sai wahala take Sha gidan Megari da girki, gashi Me gari yaji dadin girkin ta baya so kowa yayi Masa girki sai Shukura,bashi da aiki sai yabon Shukura da iya girkinta Yana cewa kuma badan bariki ba ai tana da hali me kyau,kullum maganarsa Bata wuce ta Shukura a gaban abokansa,Liman ma abokinsa ne kawai sai ya bashi Shawara ya auri Shukura kawai,Me gari yace wuuuu tafi karfina wannan kaji yanda take bariki a gidana yanda Kiri Kiri take bamu labarin farkanta,yanda take sonsa kullum har mun gaji da ji,abin ya Kai kaga tana sheka dariya ita kadai idan ta motsa ma kuka zaka ga tanayi tana magana da turanci ko me take cewa oho,ni kuma kasan Liman ni mutum ne me tsananin kishi.
Liman dai ya karfafawa me gari Lallai ya auri Shukura ko ta wanne hali ne tunda shine me fada aji a garin,Da kwarin gwiwa Me gari ya dawo gida Nan ya iske masoyiyar tasa Shukura tana kwance saman wata Tsohuwar tabarma gindin bishiyar dake cikin gidan,Tana Hawaye sannan tana Dan Allah kazo gareni My Ahleef,Ina jiranka nasan zaka zo,Mijina I really missed u,my best frnd my Everything pls am waiting....sai maganganu take a fili kamar me aljanu,kishi ne ya soki zuciyar Dattijo MeGari Nan take zuciyarsa ta baci a fusace ya buga mata tsawa keee wai wannan turancin da kike me kike nufi ne idan zagin sauran Masoyanki kike yau kina fifita Farkanki a kan sauran to ki sanar min wlh naje har can na kwade shege da sanda mene amfaninsa.
Shukura kallon Me gari ta fara ba shiri ko dai ya haukace ne?ita Bata Fahimci me yake nufi ba Sam, amma duk da haka tace nufina nayi kewarsa,shi nake jira yazo gareni ya daukeni mu tafi,Me gari yace uban wa? Mijina Mana.
Talliya ce ta fado gidan gabanta ya yanke ya Fadi ganin Me gari gaban Shukura kamar me rokon Gafara,Salati ta saki tare da cewa da mutuncinka?wlh tashi maza kafin na Tara muku jama'ar gari ki bar min gida,har abada Baki Kara ko 1hr a gidan Nan,Megari zaiyi magana Amma Talliya tace na rantse da sarkin dake busa min numfashi kayi magana ko ka hanata tafiya sai na Tara ma jama'ar gari kaf nayi Maka sharrin da baka zato, Tabarya Talliya ta dauka a Haukace tayi kan Shukura da gudu Shukura ta fada dakin da take kwana,ta fito da kayanta dake akwatuna fit tayi waje Hawaye Suna shararo mata yanzu Ina ta nufa,Talliya kuwa cewa take daga sati daya har an fara zagayowa Nan ta ingiza keyar Megari ta kulleshi a daki Dan karma ya fita ya taimaki Shukura.
Shukura kuwa hadiye kukanta tayi ta ta fara bugar kirjinta tace Shukura Hadiye kukanki ki zama me zuciya,kinje birnin tarayya ma kinyi abinda kika ga dama bare kauye gidan kwana ya gagareki?kamar bake ce kika iya satar shiga gida ba komai kyansa da lalacewarsa, a fili ta furta kalamanta a ranta tana cewa zan iya canja gari ko state ma Amma Nan garin kadai Ahleef zai San Ina Nan,Nan zai zo ya daukeni mu tafi muji dadinmu.da murna har tana rera wakarta ta ja akwatunanta sai Gidan Aishalle wacce akayi mata aure tun suna Yara basa shiri da Shukura Amma Shukura yau ta yarda Aishalle tafi Yan uwanta kawai ta kwada sallama a gidan,Mijin Aishalle ya ganeta to shi Allah ya bashi hakuri shi yasa ya kasa korarta akwai Kara da alkunya a tare dashi,Shukura ta gaisheshi tare da cewa dan Allah kar gabanka ya Fadi ba wajen kwana na zo nema ba,yar Iskar matarka zaka Kira min na Bata ajiya,Sai ga Aishalle ta fito daga Bayi ta kalli Shukura sannan tayi Murmushi tare da cewa kina Nan dai da halinki to Dan Uwarki kawo ajiyar ki tafi kin San dai ko sanda kina garin Nan zaneki nakeyi,Mijin Aishalle ya kallesu yayi dariya ya tabbata kaf dinsu kuruciya ce ke taba su basuyi hankali ba tunda Yara ne har yanzu.
Kafin ya gama tunaninsa Shukura tace ke ja can da muninki Amma ni Baki ga Mijina ba wlh duk ranar da yazo garin Nan na tabbata sai kun sume inda kika San aljani kin San bana karya zaku gani kuma kyau ne ya auri kyau ba irinki ba Muni ya auri kyau,Mijin dai dariya yake suna ta zagin juna karshe Shukura ta bada ajiyar akwatunanta tayi gaba,tana fitowa sai da ta zage gidajen danginta kaf Bata kuma yiwa kowa magana zata fito abinta, ko ma ka kulata baza ta kulaka ba,gidan Kawu ne na karshe Matar sa ta gama miyar ta tare da tsame Naman kaza ta ajiye kazar a gefe tana gyara miyarta,Shukura ta shigo idonta ya sauka kan kwanon da kazar guda take ci har murfin kwanon ba ya iya rufe kwanon sabo da kazar ta tokare ko Ina, Alhmdllh Shukura ta furta tare da cewa an Dade ba a hadu ba, Kawu na gefe a zaune Yana jira a kawo kaza, Shukura ta tuno rashin mutuncin da Kawu ya mata kawai ta dauke kwanon kazar ta koma kofar gida abinta ta zauna gefe ta rike kazar Nan da hannu biyu tana yaga a nutse tana ci,sai da taci tafi rabi,Kawu da Matarsa tare da yaran gida duk Baki bude suke jira suga Shukura ko zata dawo da Kazar Amma shuru,har Kawu ya kasa Hakuri ya zari katuwar sandarsa ya fita neman Shukura sabo da kazar ma Bata da lafiya da kyar ya bari aka yankata Dan yaga zata mutu ne Amma shine tazo a banza to wlh sai ta biyashi kudin kazar indai taci.yana fita ya iske Shukura tana yagar kaza,tana ganin Kawu ta mike tsaye kuma tana ci gaba da yaga tana uhmmmm dadi wlh Kawu gaskiya nagodewa Allah da Kaine Dan uwan Babana na jini,kayan wa mutum ya Isa ya taba idan bana Dan uwansa ba,shi yasa nake Alfahari da samun Uba kamarka.
Kawu ji yake kamar ya hadiya zuciya har wani cije Hakora yake Sabo da masifa,Ki nemi ubanki,ni ba ubanki bane bana fatan ki zama yata ko wata yar uwata,kuma wlh tunda kika Ci kazar Nan ban yafe Miki ba ko yanzu kika mutu sai munyi sharia dake a gaban Allah sabo da Baki da gadona, Shukura ta fara yar dariya tana ja da baya gudun kar Kawu ya kamata tasan kawai ta mutu,ta yagi kaza tace ka Fadi kudinta naci bashi idan Mijina yazo zai biya,ba kunya Kawu ya dinga tsine tsine akan kaza sabo da son abin duniyarsa, Shukura tace za a biyaka Kawu relax calm down Ok,Kawu yace kin zagi Uwarki ta kabari ba ni ba,kuma tunda kika zageni da turanci wlh sai Naga bayanki a garin Nan,sai na tabbatar Miki barikin naki bai je ko Ina ba,yaja kwafa ya shige gida,Amma Shukura sai ta tabe Baki ta mayar da ragowar cikin kwanon ta rufe ta shiga har gaban Matar Kawu ta ajiya da sauri tace a rabawa Yara su maida yawu ni kuci na baku kyauta,ku Yan uwan nane na siyi kazar wurin Kawu, wata yar Budurwa wacce Kawu yace zai fara Bata rubutu Tasha, tace talaka Ina kika ga sisi? Me kikayiwa kanki bare wani,Shukura tace na tabbatar Miki ki bani lokaci kadan sai na siye garin kaf na bar muku kyauta ku zauna Zaki gani, Da ace ke ba yar uwata bace to siyenki zanyi ki koma baiwata Amma kinci darajar zumunci,Kawu ta kalla tace da sannu duk mutanen garin Nan sai sunyi nadama indai Allah ya bamu Rai da Lfy tana gama fadin haka ta Kara gaba abinta.
Gidan yar Uwar Innarta Yafendo take kallo daga nesa tana tsara yanda zata dinga shiga gidan ba tare da an gane ba, masifaffiya ce ta gaske gashi komai ita ta iya wani bai iya ba,tana da zaratan samarinta guda biyu suna zamansu a gida daya tare da matayensu,Yafendo akwai Tsafta da komai ita ta sani wani bai iya ba. Shukura ta zabi zama a gidan sabo da gidan Kato ne baza a gano ta ba, har dare tana can bakin Rafi tayi sallar Isha sannan ta karaso gidan dama su katangar Kara ce kawai ta Buda yar kofa dai dai ita ta baya ta shige gidan ta gyara musu katangarsu yanda take ta bi ta jikin rumbu ta buya a bayansa tana kallonsu suka Gama hirarsu da cin tuwonsu kowa ya tafi ya kwanta gida yayi Shuru, Yafendo tuni tayi bacci a kan Dan gadonta,Shukura cikin duhu ta lallaba sabo da ganganci ta shiga dakin Yafendo ta sadada ta shige karkashin gadonta dake gadon karfe ne me rumfa tun irin na zamanin da,Ko Ina a Tsaftace Shukura ta shaki baccinta har gari ya waye, Yafendo ta fita tana shararta da ta Saba har kofar gida take Sharewa Shukura ta fito a sace ta ebi ruwa a botiki da buta ta shige Bayin Tsohuwa da sabulunta tayi wanka da Alwala tare da maida kayanta da sauri ta koma dakin,tayi sallar asuba Yafendo Ana can Ana share share sarakan Tsafta,Surukar Yafendo Indo ita ta shigo dakin lokacin tuni Shukura ta koma karkashin gadon tana gani ta ajiye Koko da fanke me sugar,sai ga daya Surukar ma Gaje ta ajiye kosai da Kunun tsamiya yasha Nono lafiyayye a samansa,suna fita Shukura ta janyo Kunun da kosai sai ta dakko sabon ludanyin Yafendo Tasha dashi yanda take so ta mayar ta rufe komai ka rantse ba a taba komai ba haka aka kawo yanda taci da dabara ta mayar ta ajiye komai yanda aka kawo,haka ta jawo fanke ma taci guda uku ta mayar,Ludayin Yafendo kuma ta boyeshi can gefe cikin kasan gado.
Yafendo kuwa tana gama aikinta tayi wanka sannan ta dawo dakin tana masifa mata Basu iya abin duniya ba haba Ina rayuwa zata tafi a haka,ba tare da ta kalli kasan gadon ba ta zura hannu ta jawo kwandon kayan kwalliyarta ta shafa Mai ta shirya ta mayar ta tura,ta Kara zura hannu ta jawo a kwati ta sa kayanta ta tura ta mayar, Shukura na gefe can a kwance tana kallonta.
Yafendo ta bude kunu da kosai tace A'a yau kuma rowarce ta motsa aka kawo Dan wannan ba a ciko kwano ba,Baki ta tabe tare da kurba tace hmmm ai da akayi kunu ba irin na yaran yanzu ba,idan Dane wa zai Sha wannan kunu,Kosai ta bude da sauri ta bude Baki ta dafe kirji na shigesu sai kace jariri ne zaici Lallai Gaje ta fara canja hali Amma zata ci ubanta sai na yi maganinta a gidan Nan.
Shukura tana ji tana kunshe dariyarta,haka dai Yafendo ta Sha Kunu,ta Bude Koko taga Koko da yawa tace Allah sarki Indo mutuniyar kirki matsalarta daya ita kuma Koko Babu kauri a tsinka Masa ruwa yanzu mu a zamaninmu ka kaiwa me gida wannan ba sai kayi kwanan gidan ubanka ba ranar,Amma Allah sarki Iro na Yana hakuri,ludayi tasa ta ebo Koko ta sakeshi a kwanon tsiiiiiii tace ashasha kalli harda burbushin tokar Kara a ciki sabo da kazanta duk sai na gyara muku zama.Shukura a ranta tace Yafendo ba a iya mata Allah kyauta.
Shukura tana so ta fita Amma ba dama sabo da Yafendo ta share dakinta ta kwanta tana Jin radio su Gaje kuma suna wajensu suna girki,mazajensu Iro da Yahaya suna kiwo,wani yaro ya shigo da katon buhun mangoro a kansa jajaye nunannu Wanda yanzu aka tsinko su a sama,gaban Yafendo ya ajiye yace gashi inji Yahaya can wajen Kiwo ya bani na kawo miki, Godiya Yafendo tayi tace Kai yaro ka dinga sa takalmi a kafarka gashi Nan kazanta tasa duk ta tsatsatsage ina uwarka take da zata barka Haka,yaro dai yayi waje Yana Jin haushi,tsaki taja sannan ta raba ta bawa su Indo tasu ta ebi wata ta wanke ta zauna tana Sha sauran kuma a buhun ta tura kasan gado.
Dama Shukura yunwa ta fara cinta Yafendo ta fita wanke Mangwaro tayi sauri ta bude buhun ta ebo kusan guda goma,ta fito ta bude randar dakin ta kamfaci ruwa a wata roba me Fadi ta koma kasan gado,dake kusan komai har kayan kwanikan Yafendo suna kasan gado a wanke a shirye,a hankali Shukura take wanke magoronta tana Sha a hankali,idan Yafendo ta fita sai tayi taunarta yanda take so idan ta dawo kuma sai tayi a hankali,Yafendo taso taji kamar motsi a kasan gadon Amma sai tace Kai wannan bera da naci yake ya dameni tun rannan a kasan gado kwana Nan zan kawo Mage gidan Nan kowa ya huta.
Da Rana Shukura Bata samu taci abinci ba sabo da a tsakar gida Yafendo ta fita ci,Sai yamma ta samu ta fito daga gidan Baki daya,gidan Aishalle taje ta dauki toothpaste da brush dinta tayi sannan ta karbi rancen dari biyu wajen Aishalle wai sai Mijinta Ahleef yazo zata biya ta fice abinta da su ta siya danwake da dafaffen kwai guda biyu taci a garin sannan ta tafi can lambu inda ta Saba zuwa hutawa sai dare ta dawo gidan Yafendo,sai da ta shiga kitchen dinsu taci tuwo da Miya sannan ta shige dakin Yafendo kasan gado, sai da su Indo suka zo zasuyi Dumamen tuwo suka ga ba malmala daya,Gaje tace watakil almajirai suka sata kin San yanzu Haka sukeyi,da sunga baka kusa sai su sace ma abinci.
Kullum Shukura haka takeyi har ta kwashe sati biyu a haka Allah bai sa an kamata ba,bashi kuwa yanzu ta karfi take kwatar kudi tace ta ranta sai Mijinta yazo zata biya,haka masu shaguna ma duk taci bashin sabulan wanka da wanki da wasu abubuwa duk tace sai Mijinta yazo,Haka bangaren masu abincin siyarwa,masu tsire da kifi,har chemist taci bashin paracetamol da maganin ciwon ciki,bashin always pad ma haka,kuma ba roka take a Bata bashi ba kawai shiga zatayi ta faki Ido ta kwashi abin ta fice tace kana Bina bashi sai Mijina yazo,idan kayi magana tace zata siyeka ka koma bawanta ko kuma ta siye shagon naka.
Kwana daya tsakani Yafendo da sassafe tace yau Kwalimar karkashin gadon ta zatayi ta gaji da Jin beraye na motsi gwara taga ko mene a ciki,Katuwar sandarta ta dakko da nufin idan taga bera ta buge shi,ta bude gado sukayi Ido biyu da Shukura,Yafendo tayi mugun tsorata tunaninta gamo da aljana tayi ta fito da gudu tana Kiran Iro da Yahaya,suka raho da gudu da saddunansu,tana nuna musu kasan gado suka dage har katifar da komai sai ga Shukura Shar Shar dake tayi wata kiba da kyau sabo da ciye ciye kuma Bata aikin komai sai tunanin Ahleef dake damunta.
Yahaya yace Yafendo ai Shukura ce,zo kuga masifa wajen Yafendo kamar zata ari Baki,zagi kuwa ba Wanda Bata yiwa Shukura ba sannan tace fada min tun yaushe kike a dakin Nan,Shukura ta zauna sosai ta Basu labari kaf kan gidan Megari da dalilin da yasa har take shugowa tana kwana,Iro yaji tausayin Shukura ko ba komai yar uwarsu ce ai Amma duk gari da dangi an ki ta an kyamaceta bayan Bata da kowa sai su,Nan Iro ya roki Yafendo a barta taci gaba da zama a gidan kafin Nan gaba aga me Allah zaiyi, Duk Masifar Yafendo tana tunawa da yar uwarta Inna tace to ta yarda Shukura ta zauna a gidan su dinga kwana tare Amma sai dai ta kwana a kasa kan karamar katifarta dake gefe.
Dadi ya kama Shukura ta dinga zuba Godiya sannan taje ta kwaso kayanta na wajen Aishalle ta dawo dasu gidan Yafendo, ta fara Taya Yafendo sukayi kwalimar tare Yafendo na Masifa ta Bata mata kasan gado da kazanta duk kwallon magoro,ga ludaya duk ansha Koko da fura a zube, duk aikin da Shukura keyi Yafendo cewa take Bata iya ba ita tafi kowa iyawa.
Da dare Tare da Shukura su Indo sukayi girki a gidan na dare,Ana tsakar gida Ana ci sai Yafendo tace sanata Elrufai an bashi zaben Gomna yanzu a kaduna ko? Shukura tace ai ba Senator bane Yafendo dama Gomna ne ya Kara ci,Nan Yafendo ta ce to yar karya wa Zaki gayawa to sanata ne yanzu yaci Gomna, da shine shugaban majalisar dattijai a Abuja,Shukura tace bafa haka bane,Nan Musu yakacame tsakanin Yafendo da Shukura,Duk su Iro suka ce Zancen Shukura ne gaskiya,Yafendo kuma ba a Isa ance an fita sani ba Nan ta fusata tace to ai na Dade da sanin Gwamna ne har za a Gaya min shi Gomna ne,Ganduje na Kano ma ba ya koma ba ta dole bai ci ba aka kwace dole,kasar Nan ba wani me gaskiya duk karya sukeyi sai yanzu nake nadamar guri'a ta Dana sawa Buhari.
Baki Shukura ta tabe tace tab ni kuwa Ina Buhari sabo da shi Mijina yake so,Ahleef shi yake so,Yafendo ta durma mata dundu a baya Dan ubanki Ina kika ga auren?a Ina Mijin yake Nan aka ce ciki kikayi aka dawo dake shine Zaki ishemu dama Kawu yace Alfahari kike tayi da Kwarton ki na birni kina sonsa tir da halinki,Iro yace Haba Yafendo kufa daina Zurfafawa wlh baku sani ba ni Ina gani kamar tana da gaskiya,Yahaya ma yace a dai bi a hankali lokaci Dole zai nuna.
Megari ya Dade Yana fama da ciwon son Shukura har yanzu bai hakura ba sai ya auri Shukura indai Yana Raye liman sai zuga shi yakeyi,yayin da Shukura ta kame kanta yanzu kullum tana gida ko fita Bata yi a garin sabo da ko Ina taci bashi,kuma gashi tana tsarewa Ahleef igiyoyinsa ko ba komai ita da auranta tasan idan Ahleef Yana Nan bazai bari a dinga kalle Masa mata ba shi yasa take tayashi.
Labarin Ahleef kuwa su Yafendo har sun gaji daji a bakin Shukura Kai kaf garin Babu Wanda bai San labarin Ahleef ba Mijin Shukura na bariki,manya da Yara sun sani har dattijai in kaji yanda ake tsara kyawunsa Ana dariya suna ganin Shukura karya take, akwai wani da yazo daga Birni garin yasha dinkin Shadda Shukura tana gani cikin bainar mutane tace irin style din Ahleef na wata farar shaddarsa,tana Nan a cikin kayana nazo da ita,,shike Nan samarin garin suke layin karbar aronta wajen Shukura Ana yi musu irin dinki kusan kowa a garin kana cewa Ayi Maka dinkin Ahleef kowa yasan mene har telolin wasu kauyukan kana ce musu ayi min dinkin Ahleef style to za ayi Maka,yanzu dinkin shi ke tashe a kauyukan, Shukura ita kanta tana mamaki kowa yasan Ahleef a Baki,Ahleef style.
Kuma abinda yasa suka Kara yarda cewa Shukura da gaske take Ahleef ko dai Mijinta ko farkanta ne yanda suka ga tana sa dinkunan maza iri iri har jallabiya tabbas na Namiji ne kuma da gani mutumin me kudi ne shi yasa hankalinsu ya kwanta suna ganin Shukura zata biya su bashin da taci da gaske take.
Shukura zaman hakuri kawai take da Yafendo sabo da fadanta kuma komai baka iya ba Babu abinda zakayi ka birgeta bare ta yaba.
Ahleef kuwa tun bayan tafiyarsa yake fama da son kasancewa da Shukuransa,ya kasa komai sai tunaninta,gashi ko a waya ba ita ba labarinta kuma harda Umma sun kasa fada Masa gaskiya,Idan ya gama wa Momee komai zai dawo sai Momee ta Kara tura shi wata kasar ba tare da ta bari ya tako Nigeria ba,gaba daya ya fita daga tunaninsa ya kasa gane wa Momee,Matarsa yake son kasancewa da ita,yanzu ya tabbatar tsananin son Shukura yake ba kadan ba,Momee kam tuni ta sanarwa Abba cewar Ahleef ya tafi wani aiki kasashe,Amma Matarsa ta zabi tafiya garinsu ta zauna da Yan uwanta kafin ya dawo sabo da ta gudu ta Bata musu rai Dole zata wanke kanta wajensu,Abba yace ahlmdllh yarinyar tayi tunani,Momee tayi Murmushi tare da cewa ai tana da tunani da kaina muka je na kaita sannan akayi musu bayanin aurenta nace Nan gaba ma zakuje dasu Baba shi mahaifin Mijin nata,wlh masu mutunci sun karramamu,Abba dadi ya kamashi yace sai Ahleef ya dawo kasar idan za a dakkota sai mu taru muje gaba daya aga juna ayi abinda ya dace Allah yayi Miki albarka kema,Momee ta waya tace na gode mijina,Abba hankali ya kwanta tunaninsa abinda Momee tace gaskiya ne kuma da sanin Ahleef.
Saudatu da Baba yanzu sunga Momee ta daina musu magana Sam tsakaninta dasu sai Harara da kallon banza,ganin haka suka yanke sanarwa Ahleef zasu bar musu gida,tunda Matar gidan da alama Bata kaunar zamansu yanzu.
AsmaBaffa
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
41-45
Official
By
Asmabaffa
Saudatu da Baba da kansu suka sanarwa Ahleef sufa sun gode da taimakonsa Amma zasu bar gida ga abinda Momee ke Musu sannan suka bashi labarin abinda ya faru na tafiyar Shukura,Ran Ahleef idan yayi dubu to ya baci kamar zaiyi hauka,Farhan ya Kira a waya ya bashi Umarnin ya kwashe su Umma da kayansu ya kaisu can Wani sabon gidansa daya siya kwana Nan me shegen kyau ba abinda Babu a gidan na rayuwa. Farhan ba Bata lokaci yaje ya kwashe kayan sawarsu ya Kai can gidan,ya zuba kayan abinci da komai sannan ya kawo masu aiki mata su biyar da maza sabo da su Umma suji dadin rayuwa a gidan girki kawai Umma zatayi ba abinda zatayi.
Sun Sha mamaki da murna suna sawa dansu albarka Babu adadi,Momee kuwa tunda taga Farhan ne ya dauke su tasan Umarnin Ahleef ne tace Umma ta gaida aisha Haka kawai tsofaffi sunzo sun rikita min gida baku San wahalar yaro ba kuce zaku Sha dadinsa.
Mubaraq yayan su Hafcy ya nacewa Niima har sai da ta fara kulashi ta karfi,tun Bata damu dashi ba har ta fara sonsa,Mama tafi kowa Murna zasu ci kudin su Momee tace saura ku Hafcy ko ke ko Zahra ku dage Ahleef ya auri daya ko zamu samu kudin da yawa sabo da shine me kudin, ko mata dari yayiwa ciki suka haife Babu ruwanmu ku aureshi kudi muke nema ba wani tarbiya ba.
Hafcy tace nima Dana yi tunani Haka na gani kawai ayi asan abin yi, tunda mun sallami shegiyar matar tasa.
Ahleef ne ya Kira Momee yace ya gama komai da Company din nasu dake kasar Japan gida zai dawo gobe, Momee cikin fada tace idan baka son aikin Nan Dana ke saka Ahleef ka fada min,gaba daya ka damu ka dawo Nigeria uban me zakayi a kasar ga aiki a Nan kaca kaca,Dan kaga bani da manyan Yara irinka shine kake min Haka, Allah sarki Ahleef baya son yaga Momee tayi fushi dashi ko ace shi ya Bata mata Rai sai kawai ya rude ya shiga Bata hakuri Yana lallaba ta sabo da halaccin rikeshi ta raineshi fiye da yaranta data haifa, Afwan Momeena what Next kuma? Wasu Kaya zaka je north Korea ka turo minsu zan bude shagon butique, da mamaki yace Momee sai na kwashe more than 2mnth a garin kin sani kuma yanzu akwai nauyi da hakkin Shukura a kaina, Salati Momee ta saki yanzu Shukura ta fini?akanta kake so dama ka dawo?
Momee Bata San Umma ta sanarwa Ahleef komai ba sai tace yarinyar kana tafiya ta tattara kayanta ta shiga duniya ba a San inda take ba,ai Abba yace kin fada Masa kin maidata kauyensu kafin na dawo,Momee tace Kai da kanta ta gudu kawai fada Masa nayi Dan hankalinsa ya kwanta,Kai wai me zaka yi da wannan yarinyar ne?Ahleef tuni ya gane Momee Bata da gaskiya ransa yayi Mummu Nan baci daba Dan kar tace ya hada ta fada da Abba ba da sai ya sanarwa Abba komai,a fili yace Momee wlh I do really love my wife,Dan Allah na dawo ko 2wks nayi sai na koma nayi Miki aikin? Momee tace Sam baka Isa ba ta datse Kiran ma Baki daya.
Baba da Umma dai suna can hankalinsu kwance Farhan ke musu komai da Umarnin Ahleef.
Shukura yau ta kwashe wata daya kenan a kauyensu kullum cikin sa Rai take zata ga Ahleef yazo Amma Shuru ,Nan kuma Megari ya samu Dangin Shukura ciki harda Kawu da Yafendo zai auri Shukura karya take Bata da wani Miji a birni,Kawu haushi ya kamashi ganinsa idan Shukura ta auri Megari taci gaba kaf garin ta ciri tuta,shi ga yarsa zata auri talaka Amma Shukura me gari Guda me fada aji me mulki, sai yace Kai Megari da girmanka da hankalinka zaka auri Karuwa? Megari yace ko a gidan Karuwai take na ganta zan aure ta Haka,Yafendo kuwa Murna takeyi ai Shukura ta ci gaba Megari Guda, Kawu yace to ya zakayi da yaron cikinta?Megari yace karya ce ba wani ciki,tana da ciki zaka ganta haka?kawai maganar mutam kauyece, Yafendo tace Bata da wani ciki Shukura fa shirmenta kawai takeyi sabo da kuruciya ko rannan tayi alada.
Megari ya washe hakoransa na cin goro.
Bayan sati biyu tuni dangi sun Gama komai za a daurawa Shukura aure da megari, zance ya baza gari,ance kar a fada mata sai an daura ta ji daga baya, Ana saura kwana Uku a daura aure Shukura taje gidan Aishalle,Aishalle tace ke kuma da kike auren me kyau a birni ya naji za a daura Miki aure da Megari,Shukura tace aure kuma? Ban gane ba kefa kin cika hauka,Dariya Aishalle tayi tace to wlh boye Miki akeyi kaf garin da Yan uwanki sun sani Amma ance kar a fada miki yau saura kwana Uku ki zama Amaryar me gari,gashi can Talliya Matarsa tayi yaji ta bar gidan ma,idan Baki yarda ki tambaya kiji,Yafendo tasan komai,har an Kai kudin aure wajen Kawu,idan kin San kina da auren wani wlh ki San abinyi tun wuri.
Ai Shukura ko Gama ji batayi ba ta fito sai gida wajen Yafendo ta fado da gudu tana Hawaye tace Yafendo me nake ji wai za ayi min aure da Megari? Yafendo tace yo tsayawa zamuyi mu kalleki ko me,kinzo sai karya kike Mijinki zaizo Yana Ina?Baki da sheda,Wanda suka kawoki sunce karuwanci kike Zaki likawa wani Dan ya aureki Kinga sun tabbatar Mana Baki da aure kuma aure kamar anyi.
Ga Dubu goma Megari ya kawo sune kudin lefenki, da Sauri Shukura ta karbi Kudin lefen dubu goma,har Yafendo tana dariya tunaninta ta yarda da auren,Sai taga Shukura ta tattara kayanta a akwatuna tas ta fito ta kalli Yafendo tace wannan dubu goman ki fadawa Megari na ranceta zanzo tare da Mijina na biyashi kudin Lefensa,da sadaki ya kawo bazan ranta ba Amma tunda kudin Lefe ne na ranta na bar muku garinku wlh Akan na auri Megari gwara na koma ga Allah banyi aure ba.
Tasa Kai ta fice sanye da hijab tana Jan akwatunanta tana tunanin Ina zata je inda Ahleef zai San tana nan.
Tana cikin tafiya sai ga Megari a saman wani tsurar machine dinsa da ciyawar tumaki a bayansa ya dawo daga gona,kallo daya ya gane barin gari zatayi,ai da sauri yaci uban birki ya dirgo daga Machine ya rike hannun Shukura Kam,tunawa da tayi tana da aure wani bakin ciki ya kamata ta dage iya karfinta ta warware Megari da Mari,idonta cike da kwalla tace Ina da igiyar wani a kaina baku da hankali ko jahilci na damunku.
Megari yaja baya dafe da kumatu Yana mamaki,tace kaja mutuncinka Ina ganin mutuncinka,ta ja kayanta taci gaba da tafiya abinta ta bar Megari da jimami duk girmansa da mutuncinsa ga mulki babu Wanda ya taba ko Masa magana marar dadi Amma wannan so ya jawo Masa yasha Mari,Allah ya taimakeshi ba a gaban talakawansa bane da yaji kunya.
Shukura Machine ta hau Bata tsaya ko Ina ba sai wani Kauye me Dan Nisa gaban kauyensu,Suma Yan Fulani ne wai Dan kar tayi Nisa da garinsu sabo da zuwan Ahleef.
Rashin sani Shi kuma Ahleef yace Umma ta bawa Farhan Address din kauyen su Shukura su Shirya tare da Baba da Umma Farhan ya kaisu garin su dauko Masa Matarsa a dawo da ita kafin ya dawo, washe gari da Sassafe suka dauki wanka musamman Farhan daya ke ji da kansa,Umma kuwa kowa ya ganta yasan Balarabiyace Tasha lace tayi Masifar kyau gashi dama tayi kiba haskenta ya Kara fitowa,Baba ma yasha Shadda me tsada yayi kyau,Farhan a wata arniyar motarsa yazo driver na jansa,Umma suka shiga suma,Sai wata dalleliyar mota da escort din Ahleef a motoci biyu suna binsu a baya suka dau hanyar Jos.
Sunje garin Jos suka tsaya Suka ci abinci da sallah sannan suka dauki Hanyar Kauyen su Shukura,sun Sha tafiya me nisa kafin sannan suka Isa garin,tun a farkon garin Yara ke bin motar suna motoci ne motocine,sulluwa ce wlh har guda uku,Farhan ne ya sauke Glass yace gidan su Shukura yake nema,Suka ce Shukura Maji dadi ai jiya ta gudu ta bar gari Akan za a ayi Mata aure da Megari,Farhan gabansa ya Fadi yace to a wanne gida ta zauna? suka nuna musu gidan Yafendo.
Bayan sunyi parking Nan fa gari ya dauka Mijin Shukura bature yazo daga birni Ashe gaskiya Shukura ta fada,Mata har da masu leke ta katanga kallon Mijin Shukura,kafin kace me kofar gidan Yafendo ya cika dam da Yara da manya maza da Mata harda matan aure za aga Ahleef.
Farhan Yana fitowa kamshi ya turare wajen,Samari suka fara Kaine Ahleef Mijin Shukura? Farhan yayi Murmushi yace Ashe kun San Ahleef kuma? Nan suka dinga bashi labarin Ahleef yanda Shukura ta fada musu har dinkinsa da ake yayi a garin,Farhan yasha mamaki yau,yace bani bane Ahleef ni abokinsa ne,Ahleef Yana America,zuwa mukayi muga Shukura mu dauketa wannan sune iyayen Ahleef.
Yafendo ce tace babbar magana Ashe yarinyar da gaskiyarta to ku shugo ayi maganar a nutse,Yafendo tayi musu saukar mutunci sannan ta Kira manya cikin dangin uban Shukura da kuma manya cikin na Inna aka zauna,bayan an gaisa da addua,Baba ya zube musu zance tiryan tiryan ya Basu labari haka Umma ma ta bada Wanda Baba ya manta,
Yafendo tace to Wanda suka kawo Shukura kuma su waye? Nan Umma ta Basu tarihinsu,Dana Ahleef harda na Momee ta Basu kaf sannan tace wannan kuma Dan sabani aka samu shi yasa ta dawo da Shukura har ta furta munana Nan kalamai a kanta.
Nan fa kowa ya shiga zare Ido kunya ta kamashi yanda suka dinga wulakanta Shukura,Suma sai suka Basu labari yanda Shukura Tasha wahala a garin kowa ya gujeta,da auren da za ayi mata da Megari har ta gudu ta bar garin yanzu ba a San Ina take ba,Baba da Farhan tausayin Shukura ya kamasu,Umma har da kuka tace shi yasa ake son bincike Akan abu,gaskiya baku kyauta ba,Shukura yarinyar kirki ce wlh me yasa kuka kasa ganewa kuna Yan uwanta, Farhan waje ya fita can gefe ya Kira Ahleef, ring daya Ahleef ya daga tare da cewa dalla Malam bawa matata waya naji muryarta na lallasheta, Farhan kansa Ahleef ya bashi tausayin Amma Haka ya daure ya bashi labarin komai.
Son Shukura ne sabo ya Kara sukan Ahleef hawayen tausayinta ya zubo Masa duk a kan aurensa Shukura ta Sha wahala haka, Ahleef yace Farhan Amma Allah ya tsinewa Megari shi ya cuceni ya jawo min masifa matata ta bace wlh idan na dawo kasar Nan ba a ganta ba wlh sai yayi prison,Farhan Yana ta bashi hakuri Yana Lallabashi tare da kwantar Masa da hankali.
Umma tace ku tashi mu tafi to me zamu jira,Farhan yace Addua zamu ci gaba da Yi Ana bincikenta Allah ya bayyana Mana ita.
Farhan ya yiwa mutanen garin kyauta da yawan gaske sai murna akeyi har suka musu sallama suka bar garin, Koda suka koma gida tuni Ahleef ya bada sanarwa a kafafen gidan radio da tv anyi ko Ina idan Shukura taji ko wani da ya santa a sanar Mata ta koma Abuja da Address din gidan su Umma Amma Shuru tana can wani Kauye Wanda yafi nasu ma harkar shanu kawai akeyi na Kiwo a garin.
a garin kuma Shukura tunda ta sauka Allah ya hadata da wani Dattijo da Matarsa su kadai a gidansu Basu da yaro ko daya suka ce Shukura ta zauna tare dasu ba damuwa abinda Shukura Bata sani ba tsofaffin mugayen Yan fashi ne dasu ake hada Baki Ana tare hanya,su suke yiwa Yan fashi waya,Shukura tsakar dare sai taji sun fita suna ta waya, ita Bata San me sukeyi ba,Bata da burin da ya wuce ganin Ahleef yanzu yakai kullum aikin kuka take ba dare ba rannan har ta kwashe sati biyu tare da wannan tsofaffin, wata ranar asabar katsam sai taga Yan sanda sun cika gidan tab sunzo mota mota tare da damke Dattijo da Matarsa an gane cewar yan fashi ne,Zasu hada da Shukura ta fashe da kuka tace Wlh ni bakuwa ce sati na biyu da zuwa garin,Yan sanda suka tambayi Yan gari aka tabbatar musu sannan suka kyaleta,sai gashi an samu bindigu sunfi ashirin a dakin dattijo Nan akayi gaba dasu.
Shukura Tasha mamaki tace Lallai mutum mugun ice Ina ta bacci dasu da gudu ta kwaso akwatunanta ta hau Machine tayi hanyar kauyensu da ta gudu, dai dai lokacin kuma Ahleef yazo Nigeria ba tare da sanin kowa ba,escort dinsa kawai yayiwa waya suka sameshi da sababbin motocinsa sunfi goma a Hotel din da yake ya fito cikin shiri yace a kaishi kauyen su Shukura tunda wasu daga ciki Farhan yaje dasu.
Wanka iya wanka yasha kamar baza a mutu ba,sanye yake cikin wata dakakkiyar Shadda Yar gasken gaske light blue,fitted dinkinsa links,sumar Nan ta Kara yawa an kwashe gefe da gefe kadan taci kudi sai kyalli take hade da Dan sajensa zuwa Dan gemunsa na matasa yasha gyara luf luf sai ya Kara kawata fuskar tasa abinka da farar fata ba a cewa komai,Agogonsa Gucci me tsananin tsada,ga wani takalminsa kalar shaddar irin na sarakai flat half shoe sai kamshi take ta ko Ina,cikin tafiyarsa ta kasaita ya shiga mota suka Ware wuta sai Jos,duk inda suka wulga sai anbi motocin da kallo sabo da kyawunsu.
cikin garin Jos suka ci abinci da sallah kana suka dauki Hanyar Kauyen suma, suna shigowa hanyar, Machine da Shukura ke Kai ya yanko Shima fiiiii Hijab dinta na tashi Yana gefen motocin sun jera suna tafiya, Ahleef Sam bai kula dasu ba sabo da motarsa tana tsakiya,Shukura kuma Bata taba zato ba tunaninta bazai zoba sabo da ta cire Rai da ganin Ahleef,kuma wannan kalar motocin Bata sansu ba Sam,tunaninta ma ko Gomna zasu Kai ziyara kauye,kamar suna tsere da motocin,ga akwatunanta a gaban me Machine filfila wuta kawai suke Suma.
sunzo garin dai dai Yar kasuwar kauyen karama dai dai jikin wani container me charji suka tsaya Machine ya lalace,Shukura tace nazo gida ni bari na sallameka na karasa a kafa,ta sauke kayanta tana lalubo kudi ga rugugin kidan da me chaji ke sawa ya cika kasuwar Baki daya,Sai da su Ahleef suka shugo garin ya bude Ido ya fara kallon gefensa dai dai inda kida ke tashi kamar ance ya kalla itama Shukura ta bawa me Machine kudi kenan ta juyo sukayi Ido biyu ta glass dinsa na mota,ai da sauri ya sauke Glass don ya tabbatar, itama ta kafeshi da kallo wai kuwa shine Anya? Motocin ya bawa Umarni su tsaya, Shukura tayi Masa zuru da Ido har ya bude mota da sauri ya fito a nutse kamshi ya cika wajen kaf, Shukura ta tabbatar shine Bata San sanda ta washe Baki ba kawai sai da ta bi kidan me chaji tayi girgiza da rawa duk mutanen da suke kasuwar da wajen suna kallo hankalinsu ya Kara dawowa wajen sunga Shukura tana rawa,Ahleef ya harde hannaye a kirji Yana zuba Murmushi Yana kallo Shukura tasa kafa ta daki akwatunanta suka watse tace kun zama old version, Ahleef ya Kara sakin dariya ba shiri tare da takowa wajenta itama ta taho da gudu kamar wata yar basketball Haka ta daka tsalle ta makalkaleshi, da badan me karfi bane da sai sun zube a kasa,Kara kankameta yayi Yana manna Mata kiss a ko Ina na jikinta,mutane kuwa sun taru kamar Ana kallon wasan dambe kowa ya zura Ido Ana mamakin ina Shukura tasan wannan Baturen me kudin?ko shine Mijin nata?ko kuma kwartonta ne,wasu kuma suna jinjina rashin kunya da bariki irin na Shukura da wannan saurayi,wasu ma sai rufe Ido sukayi wai baza su iya gani ba kunya suke ji.
Sun dauki Lokaci me tsawo kafi su rabu da juna,Shukura taja gefe tace uhmm kayi kiba da kyau kafi da kana can ka manta Dani,ke kuma kin Kara girma kalli yanda kikayi tsayi let's go muyi magana later.
Mutanen wajen Shukura ta kalla tace wannan ne Mijina Ahleef ku sanar duk me Bina bashi yazo kofar gidan Yafendo ya karbi kudinsa,Ahleef ya dinga dariya wato bashi aka ci Masa haka,da kansa ya bude Mata mota ta shiga Shima ya shiga guard ya rude suka karasa cikin garin kofar gidan Yafendo,kafin kace Me mutane kowa har matan aure an fito ganin Ahleef,masu bin bashi sun cika damkan suma,Iro da Yahaya ne suka fara arba da Ahleef,Shukura tace to ga Mijin,Iro yayi dariya tace bayan kin bar gari abokinsa da iyayensa sunzo,Nan Iro ya Bata labarin zuwan Farhan dasu Baba tare da alkhairin da sukayi musu.
Shukura tace ikon Allah kenan, Ahleef ya rike hannun Shukuransa kakam.
Yafendo tuni an tattaro kan Yan uwa harda kalan dangi sunzo ganin Ahleef me kudi kamar Dan Shugaban kasa shine Mijin Shukura,ga kyau kamar aljani,Kawu saida ya firgita,dangi suka fara Nadama harda bawa Shukura hakuri,Shukura a fili tace yanzu ba da aka ga Naira,da kuwa ai Mahaukaci ya fini mutunci,me zaku Gaya min,wlh kawai kuna Yan uwana Amma bazan ga mutuncinku ba dama dama Yafendo da yaranta.
Ahleef ne ya Dan matse hannunta wai tayi Shuru,tace baka San wacce wahala Nasha ba kawai ka kyaleni,Yanzu kowa ya yarda Ina da aure,kuma ga Mijina,sannan zan iya siye garin Nan kaf,zan iya maida wasu Bayi,Ba danginta ba har Yan garin sai suka fara bawa Shukura hakuri kar ta siye garin,Ahleef ne ya kwantar musu hankali da wasa take muku fa,Yafendo ta gabatar da kowa wajen Ahleef haka kawu sai waazi da Nasiha yake musu,cikin masu ganin Ahleef harda Megari da Liman, Megari a ransa sai Allah ya Isa da tsunuwa yake jawa Ahleef tafi dubu.
Bayan an Gama gaisawa Ahleef yayi musu ruwan kudi, Shukura Bata so ya bawa danginta ko kwandala ba irin abinda suka yi Mata,
Sai fushi takeyi,karshe tace Ina masu bashi,Nan suka cunkuso ciki Suma aka fara da Megari dubu goma,Ahleef ya bada,tace Ina me tsire dubu biyu ne nasa,Ahleef yace nasan za a Rina,tace me balangu da me kifi dubu daya daya,Aishalle adari biyu Amma Bata dubu goma kyauta,Me chemist kudin paracetamol da pad,Ahleef ya bude mota kawai kudi yake irgawa Yana mikowa Ana ta biyan bashi mutane masu yawan gaske,da ya gaji ma kawai wajen kudin ya bude Mata ta karasa da kanta,Wanda zata yiwa kyauta tayi Masu bashi a biyasu har ta Gama kaf,dariya ta bashi sosai yanda ta kware wajen cin bashi sabo da tana da shi tasan zai biya.
Ahleef yanaji Ana Zancen Dinki Ahleef style dama Farhan ya bashi lbr kawai dariya yake a ransa abinsa,har ta Gama tace kazo muje ko zaka ga garin?Ni pls ki shigo mu tafi Abuja dare fa zaiyi Bae ya furta cike da Shagwaba, Murmushi tayi Shagwabar tayi Masa kyau, tace to Dan jira Ni pls ta shiga gidan Yafendo,Bata tsaya jiran komai ba ta fada wanka,bayan tayi wanka ta fito ta canja atamfa cikin kayanta wata sabuwa sau daya ta sata tunda tazo da kayan garin,wata black and blue ce dinkin Riga da skert sun kamata das ba karamin kyau tayi ba,mayafi Baki ta dauka da wani flat shoe baki me tsada duk dama ta sako su cikin kayanta Amma Bata Sa ba sai yau,kamar ka sace ta,yau wankan da kwalliyarta ta dabance,sai gashi ta fito a Yan matan Abuja masu ji da kansu, Yafendo anji kudi Har ta fita ta harhadowa Shukura magungunan tsumi iri iri ta karanta Mata yanda ake amfani dasu ta Bata Leda guda, Shukura sukayi sallama tace watarana zata zo ta daukesu suga gidanta.
Duk ta Dan yiwa dangi sallama an yafi juna,Kawu ma an biyashi kudin kazarsa da ta cinye musu.
Ahleef yaga yanda Shukura ta dau kyau gaba daya ta Kara wani kyau gashi ta sake girma komai ya Kara cikowa sosai sabo da Shan madarar shanu kullum tayi wani fresh kamar ba a kauye take ba.
Bodyspray din Yafendo ta fesa me dadin kamshi,Ahleef ji yake kamar yayi tsuntsu ya gansu a Abuja masau kinsa Hotel,suna tafiya a mota kasa kyale Shukura yayi sai da ya fara kissing din lips dinta Yana lasar Mata wuya,ita kuma tana hanashi wai kunyar Driver pls ka Bari,wani wuri ya Danna kawai sai ga labile masu kyau sun sakko suuuu kasa ya raba tsakaninsu da driver.
Ko Ina ya rufe saisu kadai a bayan mota,jikinsa ya jawota ta kwanta,Shukura tace wai har yau Yaya baka canja halinka na lashe lashe ba?,Murmushi yayi tare da cewa ai ke za a tambaya har yau Baki canja halinki ba kin San mene aure me akeyi,wai ma Ina ciki na Dana yi Miki? Kunya ce ta kama Shukura tace ai yanzu fa watansa biyu da sati Uku bai Isa fitowa ba ,bakiyi period ba? Nayi Mana ai matar Iro tace wasu idan suna da ciki basa daina period itama haka takeyi idan tana da ciki,kaga maybe nima Haka ne.
Ahleef yace uhm gaskiya ne to ki lallaba min Babyna Allah yasa ki haifo min mace,Shukura ta boye fuskarta a kirjinsa tana dariya kasa kasa tace nima nafi so na haifo Mace ta,Sabo da me kike son mace ya tambaya yana kallon fuskarta cike da zallan so,tace Sabo da na dinga yi Mata kitso,Ina shafa Mata Jan Baki, Ahleef yace to ki dage ki haifo ta tunda har nayi Miki cikin,Shukura tayi Murmushi tace tam,wannan kuruciyar ta Shukura nishadi take bashi.
Dankwali ta ya zame ya shiga Shafa gashinta me ssantsi yace Farhan ya bani labarin yanayin da kika shiga I'm really sorry ban sani ba,Bakinsa ta rufe Masa da tafin hannunta tace never mind nasani shi yasa na jiraka a kauye nasan zaka zo,Nan ta bashi labarin abinda bai sani ba harda rayuwarta a gidan Yan fashi, suna ta dariya Shukura na matashi da bindiga a cikin pillow Bata sani ba.
Sai wurin Magrib suka Isa Abuja Hotel din daya sauka suka tsaya,Shukura tace ban gane ba Ummafa da Baba Ni nake son gani Dan Allah a kaini wajensu Kai sai ka zauna a Nan pls, u are not serious yaja hannunta suka shiga ciki bayan yayi musu order abinci, Room din suka shiga Shukura taga akwatunansa guda Hudu manya a ciki tace nifa bani da kayan sawa na bayar da nawa a kauye,na ba matar Iro data Yahaya kyauta.
Akwai kayanki a Nan karki damu.
Asmabaffa
[7/22, 1:13 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
46-50
Official
By
AsmaBaffa
Baki Shukura ta turo Masa tana wata Shagwaba me gigita hankalin me gida ni dai Umma nake son gani, ran Ahleef ne ya baci shi Bata sonsa Bata son ganinsa sai su Umma,yazo tun daga wata kasar sabo da ita,yaje ya dakko ta amma tana maganar wai su Umma take son gani,it a ya kaita can shi ya zauna a Nan, a fusace ya kalleta,kallo daya ta tsorata tasan Lallai ransa ya baci da kalamanta,sai yanzu taga ita ma fa Bata kyauta ba, batayi Masa adalci ba, Baki ta bude da niyyar magana kafin tace komai ya shige Toilet abinsa.
Fushin nasa har mamaki ya Bata, tana Nan tsaye ya Dade ya fito daga wanka ya isketa bai ko kalleta ba, itama kasa magana tayi sabo da tsoro taji kar ya masge ta,toilet din ta shiga itama tayi wanka,kasa daura towel tayi sai skert dinta ta maida tare da jawo shi sama kamar tayi daura kirji ta yafa Mayafinta sannan ta fito lokacin ya Gama shirinsa cikin kayan bacci ya daura jallabiya ya tayar da sallah abinsa.
lotion dinsa ta shafa me kamshi ,gashinta ta busar tayi amfani da wasu mayukan gashin nasa ta gyarashi sosai,sannan ta dakko powder dinta da ta shiga mota da ita ta Dan shafa sama sama ta shafa lipgloss sannan ta maida kayanta itama ta fara sallolinta, bayan ya idar tare da adduoinsa abinci ya fita ya karbo Wanda yayi order, fuskarsa ba rahma ya dawo lokacin ta idar da sallah kawai ya ajiye Mata nata ledar abincin ba tare da yace komai ba.
Shukura kamar zatayi kuka ta kalleshi Amma bai ko bi ta kanta ba,tana gani ya zare jallabiyarsa kayan baccinsa masu kyau suka bayyana 3qtr wando da Riga armless farare ba karamin kyau yayi ba,sai kamshi yake fesarwa.
Laptop dinsa ya kunna ya fara aiki a ciki Yana cin abincinsa hankalinsa kwance Amma hankalinsa Yana kanta kawai dai fuskewa yakeyi Dan ya nuna Mata kuskurenta.
Shukura taki taba ko ledar abincin duk kwadayinta,tana zaune bisa sallaya tayi Shuru,Yana kallonta ta gefen Ido har ta gaji ta bude abincin duk dadinsa Bata iya ci da yawa ba,ta mayar ledar ta mike tayi brush ta fito ta koma inda ta Bari ta ci gaba da zama tanaso tace ya Bata Kaya ta canja tana Jin tsoronsa, tana kallo ya Gama Shima yayi brush ya dawo da niyyar kashe light zai kwanta.
a hankali Shukura ta iya furta Dan Allah Ina kayan nawa zan canja,da yatsa ba tare da yayi magana ba ya nuna Mata wasu akwatuna har uku,mamaki da murna ya kasheta Bata San sanda ta saki Murmushi ba,wato tsarabarta ce tunda daga kasar waje ya dawo,kamar tayi tsalle ta rungumeshi Amma ba hali idan ma tayi yanzu zai ce saboda kayan daya Bata ne, sai kawai ta share ta jawo karamar ta bude taci sa'a inner wears ne da kayan bacci a ciki, tunawa tayi ta taba ji Yan schl dinsu Mata suna hirar idan anyi aure kayan bacci na Jan hankali ake sawa,masu kalar nuna tsiraici ko fushi me gida yakeyi da Kai sai ya daina,yau ga Mijinta na fushi da ita ya kamata ta gwada ta gani.
Wata light pink ta zabo da kadan ta Dan sauka tudun mazaunanta shara shara, hannunta siriri kamar net Haka take tana wani sheki da kyalkyali Wal Wal ta hadu karshe me tsada ce ta gaske.
Ahleef bai kashe light ba da yaji ta tambayeshi Kaya zata canja sai ya bar Mata hasken ya koma saman bed yana zaune ya jingina da fuskar gadon Yana Shan Jinger tea Yana latsa waya ta wani bangaren Yana satar kallon Amarya.
Mayafinta ta daura a jikinta ta cire atamfar tare da linkewa sai kuma ta saci kallon Angon nata sai ta ka kalli rigar tana so ta samu wajen da zata buya ta sa kayan, Yana kallonta kawai sai ya kwanta tare da kashe wayarsa ya lumshe Ido kamar bacci ne ya kwashe shi,a hankali tazo jikin gadon Dan ta tabbatar yayi bacci sai ta ja yatsan kafarsa a hankali taga ko motsi baiyi ba,har zata rufa Masa bargo sai taji tsoro kar ya farka ya zaneta dama cikin fushi yake.
Zip din rigar ta zuge ta saka abarta saman gyalen data daura sannan ta janye gyalen ta gyara zaman rigar a jikinta,subhannallah kamar a jikinta aka Dinka,ba karamin kyau tayi ba kamar wata baturiya,hips din Nan kamar zai Fado,Haka kirjinta a cike taf,cinyoyin lukuta lukuta suna sheki, lallabawa tayi zuwa jikin Mirror ta kalli kanta ita kanta sai da ta kalli kanta ta Kara tare da godewa Allah sannan ta saki gashinta ta Kara tajeshi wai yau sai ta koma Baturiya, sai ta tsaya a mudubi tayi ta kallon kanta tana juye juye, kirjinta ta kalla a fili tace kuci gaba da jiran jariri a haifo shi,Ahleef Wanda ke kallonta Yana jinta bai San sanda ya danne Bakinsa ba sabo da dariya data kamashi a ransa yace ga Baban jariri Yana ta jira an hanashi shi da abinsa.
Juyowa tayi da niyyar lallabawa ta kashe light kawi sai taga Ahleef a zaune yanda yake dazu Yana Danna wayarsa kamar baima San me take ba,mamaki ya cikata yaushe ya tashi to Bata sani ba,kunya ta lullubeta,Amma ta tuno maganar Yan class dinsu kuma gashi ma yasan tasa kayan Amma ko kallo Bata isheshi ba gwara ta Bari ya gani sosai ko zai sakko.
Sabo da Haka sai ta maze kawai taje ta dauki kayan data cire ta daura saman kujera,ta dawo ta wuce ta gabansa ta dauki ledar abincinta ta dakko ruwa ta Sha ta ajiye,ita Bata sani ba ta Gama nakasa Ahleef sabo da Yana kallonta ta kasan wayar ba waya yake kallo ba,ita kuma haushi har ya kamata taga bai ma San tanayi ba.
A hankali ta tako har gabansa ta tsuguna a kasan bed din sannan a hankali tace kayi hakuri dazu baka ji dadin kalamai na ba,kayi hakuri Naga sai kumbure kumbure kakeyi daga Yar magana,kuma ma ai gani nayi idan nace Ina son Umma kamar Kaine tunda sune suka haifeka sai gashi Kai fushi kayi ma,kayi hakuri to na janye maganata ta dazu bana son na ga Umma da Baba Ahleef nake so na gani tunda Kai kishin ma harda su Umma yi kakeyi.
Farin ciki ne ya kamashi Amma sai ya kanne yace,Gobe zan koma inda na fito Ni ki kwantar da hankalinki,kuma Wajen Umma zakije tunda kina so,Ni duk abinda kike so zan Miki inshallah gobe can wuce ke kuma ki zauna da Ummanki dama kunfi kusa tare na ganku.
Gaban Shukura ne ya Fadi yanzu tafiya zaiyi daga haduwa yau,sai kawai ta rushe da Kuka ta kafa Kai a jikin bed tana ta yi abin tausayi,taji dai ce komai ba,kawai sai ta wuntsila tayi flat tana ta birgima da Shure Shure tana kukanta tana Ni baza ka tafi ba.
Dariya yayi ba shiri yace to tashi naji,taki dainawa,yace wasa fa nake miki na isa na tafi ai sai da yardarki muna tare,Sai lokacin ta mike zaune tana Murmushi tana goge hawayenta, da kansa ya sakko ya dauketa sannan ya zauna saman bed tana saman cinyarsa ya Bata ruwa Tasha tana ajiyar zuciya,sai kalle Mata jiki yake sabo da komai Ana gani gaba daya ya rude ta Gama zautar dashi da shigar ta, dama so yake su shirya kawai,light ya kashe musu sannan ya daura ta saman bed din Shima ya kwanta a gefenta kowannensu Yana kamshi.
Shuru tayi a saman bed ba tare da tace komai ba, a hankali ta juyo Dan ta gani bacci yake ko me, tana juyowa fuskarsu sai da ta gogi ta juna,Hancinta ya hade da nasa, Ido suka lumshe a tare,Wani iri suke ji a jininsu bazai misaltu ba,kasa matsawa kowannensu yayi, a nutse ya daura lips dinsa saman nata tare da komawa samanta tana kasa,hannayensa ya dafesu a saman katifar,Magana tayi me...me...zaka..yi? da kyar ya gane me tace, bakinsu ya hade wuri daya ya kamo harshenta da nasa Yana tsotsa kamar zai cinye Mata Baki,tun tana Jin kunya tayi Shuru har ta kasa ta rike saitin sagensa da tafukan hannunta tana shafawa a hankali zuwa gemunsa tana Kara kissing dinsa sosai,Kirjinsu ya hade waje daya tare da gangarowa wuyanta Yana lasarta, a hankali ya zuge zip din rigarta, Jin hannayensa a saman dukiyar Fulaninta yasa ta rude tare da shiga wani hali.
Harshensa taji saman na shanunta wani shidewa ta fara yi har Bata San sanda ma take nuna tana Jin dadin abun ba kunyar Tata duk ta gudu ba tare da ta sani ba, Ahleef yayi niyyar shigarta Amma sai ya fasa sabo da tunaninsa Bata sonsa sai ya koya Mata sonsa,zai iya hakura Yana Dan Romancing nata suna rage zafi kafin Shukura ta kamu da sonsa sosai yanda zaiyi abinsa ba tare da tunanin komai ba,sabo da Haka kawai Romancing dinta yayi suka samu nutsuwa sosai sannan ya kyaleta,a haukar Shukura ba ayin komai dama iya abinda akeyi kenan a aure. Sai da suka huta sannan yace tazo suyi wanka,tace A'a Ni kunya nakeji kaje kayi idan ka fito zanyi,Murmushi kawai ya sakar Mata Wanda ke kashe Mata jiki sannan ya shige bayi abinsa.
Yana tafiya ta kwanta a saman bed din tana zuba Murmushi tana tuno irin dadin da suka jiyar da juna,da kuma nuna Mata so da yayi zalla..tana kwance taji kamshinsa ya fito daure da guntun wani towel fari da Dan karami Yana tsane jikinsa,Ido suka hada ai da sauri ta kulle idonta tare da fadawa toilet cike da kunya,shi dariya ma ta bashi lokacin da suke romancing Sam dadi ya Hana taji kunyar sosai ta zage Amma sai yanzu take Jin kunyarsa
Kafin ta fito ya shirya tare da gyara bed din neat,da kyar ta daure ta iya shirya kanta a dakin sabo da kunya,sai da ta Gama sannan ta haura saman bed din kusa dashi tana kunya ya kashe musu light, jinka ya shigar da ita a kunnenta ya Rada Mata Unique u are so sweet,mun godewa Allah da ya halatta aure,da ba'a halatta Mana aure ba ya zamuyi kenan? Dariya kadan Shukura tayi kana tace hmm ai ko ba a Halatta ba sai anyi aure,akeyin Zina ma,ko ba aure da aka Halatta yin abinmu zamuyi mu Dan Adam,Dariya yayi ke Baby, itama dariya tayi tace Ana Jin wannan dadin za ace baza ayi aure ba ai mutane yin abinsu zasuyi, Boobs dinta ya shafa wannan sun Kara girma me kike Basu just 2mnths bamu hadu ba Amma naji sun Kara cikowa,Shuru tayi wai kunya ta kamata,tana jinsa Yana ta faman yi Mata tabe tabe a jiki har bacci yayi gaba dasu.
Washe gari har makara sukayi sai wurin 8am Shukura ce ta fara farkawa cike da farin ciki tare da tsatsan nishadi,yau Allah ya amsa adduarta gata ga mijinta kwance gado daya itakam komai yayi zam zam a hankali ta furta Allah dawwamar damu a Haka har abada.
Fuskarsa ta tsurawa Ido tana kallonsa tana Murmushi tare da yaba halitarsa a zuciyarta, gemunsa ta Dan taba a hankali, ai kamar ta taba wuta Haka ta janye hannunta Dan kar ya farka ya kureta, a ranta tace laushi da santsin gashinsa yafi nawa,tana wannan tunanin ya farka a hankali ya bude idonsa kyawawa masu matukar haske, Ido suka hada sai tayi sauri ta boye fuskarta kan pillow,Dariya ma ta bashi ya danyi Murmushi kana ya mike Yana cewa munfa makara bamuyi sallah ba ki tashi, kanta ta Kara cusawa cikin pillow tace kaje in ka fito zanyi ni., Hmm ya furta Yana Murmushinsa me sumar da yan Mata ya shiga toilet.
Ya dauki lokaci me Dan tsawo kafin ya fito daure da towel yana goge ruwan jikinsa,yanda Ya bar Shukura haka ya dawo ya iske ta, yau fa zan maida ke schl ki tashi ki shirya, da sauri ta mike zaune tace idan Su Niima suka ganni fa?suje su fadawa Momee tasa ayi min wani abu ta Karasa cikin Shagwabarta data Saba, ido ya zuba Mata yanda tayi wani kyau kamar kar ya daina kallonta da kyar ya saita kansa sannan yace ke dai bakya son schl tuntuni so kike ki zauna a Haka? Baza kiyi ilmi ki waye ba? Kana so ka fada min ban waye ba kenan? Yanda tayi tambayar zai nuna Lallai taji zafin kalamansa,yasan Saurin zuciyarta sai yace ba Haka nake nufi ba, I mean ki Kara ilmi kan Wanda kike da shi yanda kike ai anga wayayya ta karshe.
Murmushi tayi me kayatarwa ta mike tare da shiga toilet tayi wanka,brush da Alwala,ko da ta fito iskeshi tayi saman Sallaya ya idar da sallah Yana Azkhar, da sauri ta Sa jallabiyarsa da Hijab tayi sallah tare da adduointa bayan ta idar ta mike kawai ta fada saman bed din sabo da bacci ne ya cika Mata Ido, Ahleef Yana karatun Qurani sai da ya Gama sannan ya zare kayan jikinsa daga shi sai boxers ya haura saman bed din Nan ya iske har tayi bacci abinta, jallabiyar dake jikinta ya lallaba a hankali ya zare Mata daga ita sai pant ya lullubesu da bargonsu me laushi suka ci gaba da baccinsu Manne da juna kamshinsu ya mamaye su suna Shaka cike da kwanciyar hankali tare da Shauki.
Basu tashi ba sai misalin karfe 11am,wanka kowannensu yayi,creazy Jean fari yasa tare da t-shirt purpple ba karamin kyau yayi ba karshe,Yana fesa turarukansa masu Dan Karan dadin kamshi Shukura ta fito daga wanka daure da towel guntu,wani kuma ta daure gashinta dashi tana tsane ruwan, ta Mudubi suka hada Ido tare da sakarwa juna Murmushi me tsada, sai kunya take ji da kyar ta iya Shafa Mai a hakan ma sai da ta rufe jikinta da bargo, da kansa ya duba kayan tsarabarta ya zabo Mata wata fitted gown Ready made Golden color me dogon hannu,tayi matukar kyau a ciki kamar a sace Shukura,Ita kanta tayi mamaki, a Mirror ta kalli kanta tace Yaya ban taba sanin Ina da kyau ba sai yau, dariya yayi yace to ai ba a yabon Kai,Ni ya dace na yaba,Dole ne na yabi kaina kuma na godewa Allah cewar Shukura tana dariya.
Gashinta ta gyara sosai sai sheki da kamshi yake fitarwa,Wata top ya dauko Mata black me budadden gaba adon Gold da baki ta daura saman rigar tsayinta ya Kai gwiwa wata pencil ce sai ta fito kamar wata sarauniya, gashinta tayiwa acuci sannan ta Yana siriri gyale black, takalminta Black me Dan tudu tare da tsadarjiyar bag dinta du black.
Powder kawai ta shafa da Vaseline a lips dinta.
Ahleef ne ya tako har gabanta ta baya ya rungomota jikinsa ya Rada Mata a kunnenta kinyi kyau Baby, Amma Ni Ina son Jambaki ki shafa kadan, cike da Shagwaba tace ai sai naci abinci zan shafa,kafada ya makale kamar yaro Shima da Shagwaba yace uhm...uhmm nidai a shafa min yanzu idan ya goge a kara mene amfanin kayan kwalliyar Dana yi dakonsa zuwa kasar Nan, a hankali ta zare jikinta ta juya suna facing juna,rungumeshi tayi tare da kwantar da kanta a saman kirjinsa sannan ta Mika Masa Jambaki Red ta furta shafa min.
a hankali Yana wani Murmushi me kayatarwa ya dago da kanta da hannu biyu tare da shafa Mata kadan Yana kare Mata kallo ji yake kamar ya lashe ta ya huta, knocking suka ji,ya Dan bude kofar kadan ya karbi abincin da yayi Order, Zama yayi tare da jawota jikinsa ya fara ciyar da ita Shima Yana ci har suka Gama cike da shauki, shiri suka Kara yi sun dau kyau ya rike hannunta suka fito, dalleliyar sabuwar motarsa Tasha wanki tana kyalli ya fara bude Mata ta shiga Shima ya shiga yaja su suka tafi.
Momee rike da waya hannunta tana faman Kiran number Ahleef ta kasar waje Amma sai wani bature ya daga Wanda kuma ba turanci yakeyi ba wani yare yake faman shekowa a cikin wayar, idan zata Kira sau Dubu yaren Nan take ji, Niima ta matso kusa da Momee tana har yanzu Baki samu Ya Ahleef din ba? Momee tace hmm Na rasa me ya sameshi yau kwana biyu kenan wannan yaren nake ji Haka suka yini suna gwadawa Amma sai yare.
Yau da Safe Latifa ta fito cikin Shirin schl sai tace Anty Niima ki saukeni a schl pls Driver yaje kauye kuma Ina da Test, Niima tace da zamu fita Hafcy da Zahra kanwarta muna da wani Uzuri Amma muje sai mu saukeki.
Hafcy da Zahra Driver ya saukesu gidan su Niima suka shiga motar Niima gaba dayansu suka tafi Zasu fara sauke Latifa, Sunyi Parking kenan Dalleliyar motar Ahleef da Basu San da ita ba tayi parking, yasha kana Nan Kaya harda pcap,Shukura kuma sanye cikin Ready made dinta tasha kyau kamar Queen,Ahleef da kansa ya bude Mata ta fito,Allah yasa su Niima Basu ga fuskarsa ba, shi kuma ya gansu Yana sani yayi yanda baza su ganshi ba,Shukura ma ta gansu Sarai ta fito,Hafcy tace Kai kun gani kamar Ahleef da Shukura,Zahra tace ke Ahleef Yana turai fa Farhan ne kin San fa rannan yaje kauyen shine ya dauko shegiya,tabe Baki Niima tayi tare da furta dama kunsan suna yanayi da Ahleef,Da alama Amanarsa yake ci suna iskancinsu shi kuma yana waje,,Ihu Latifa ta kurma tace wlh Farhan ne suke iskancinsu kalli ya rungumeta suna ta yiwa juna Rada.
Salati Zahra ta saki tare da cewa kunga suna ta kiss ko kunya Yana cin Amanar abokinsa,Niima tace Alhmdllh mun samu hanyar da Ahleef zai Mata saki uku ba tare da wahala ba,Nan take Niima ta dakko waya ta danno Camera ta fito daga motar cikin sanda ta bayan motar take ta faman kyasta Shukura da Ahleef suna rungume rungume sannan suka shige schl din hannunsu cikin na juna,Hafcy harda daukan Video.maimakon su bisu su tabbatar da gaskiya sai suka tsaya jiransu a waje,Shukura sai dariya takeyi ta kalli Ahleef tace wai Nan fa du sharri za a Kulla min,shi yasa na hugging naka da hujja suji dadin dauka,Tabe Baki Ahleef yayi kana yace Basu da aikin yi ne.
Suna jira har suka fito Ahleef ya Kara boye fuskarsa cikin pcap ya dukar da Kai suka koma mota ba tare da sun gane ba Farhan bane,yaja mota suka bar wajen yana tafiya suka turawa Ahleef ta WhatsApp dinsa sannan suka ajiye Latifa suka bar wajen cike da farin ciki harda Kure vol na radio suna Jin kida, Niima tace mu bisu muga inane masaukinsu,Nan fa ta rike wuta tana ta faman Bin bayan motar su Ahleef sai sunga Ina Farhan zai Kai Shukura,Suna ganin Hotel din suka kaure da shewa sannan suka juya kan motarsu suka nufi inda zasu,Ahleef da Shukura kuwa suna kallonsu abin ya Basu dariya.
Room dinsu suka shiga Shukura sai dariya take ta kasa tsayawa,Rungumeta taji Ahleef yayi ta baya ya shigar da ita jikinsa gaba daya Yana sinsinar wuyanta, Mood dinsa ya fara canjawa yaja ta saman Bed suka fada.
AsmaBaffa
Kuyi Hakuri fans wannan Typing din ina busy ne sosai shi yasa bakwa samu yanda ya dace,kuyi min afwa sannan bakwa min Sharhi bare naji dadin typing kawai Ina yi ne ba dadi.
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
51-56
Official
By
Asmabaffa
Gaskiya Kuna birgeni masu Sharhi.
JIDDER ZARIA ga page naki.
Baki Shukura ta Tsuke Bata kawo komai a ranta ta kwanta sosai Saman Bed,Ahleef ji yayi Sam ya kasa jurewa kawai sai yace tashi muyi Nafila,Shukura tace ban gane Nafeela da Rana ba yo ko sabon Aure ne ai sai dare akeyi,Fuska ya Bata ba wasa yace Nafila to zamuyi Allah ya albarkaci aurenmu oya get up pls don't waste my time,kallonsa tayi sosai taga ba alamar wasa tace Uztaz me tsanani ka koma kuma haka a turai? Babu alamar wasa yace ae, Baki ta tabe ba tare da ta gano ko mene ba kawai ta fada toilet tayi wanka tare da Alwala, Shima ya shiga a gurguje yayi wanka da Alwala Yana fitowa ta bude Mai zata shafa kenan ta tsinci muryarsa yace karki shafa min Mai a jikin komai.
Shukura ta bude Baki tana Jin ikon Allah turaruka ta shafa na jiki sun Kai kala uku,ta dauko na feshi yazo ya kwace tare da cewa Sunyi yawa so kike na Sha Chemical a cikina,Shukura tace A'a sai kace wacce na fesa ma a drink? Riga ya zura yace sa Hijab ki bini sallah,ba musu tasa tace yau Naga addine ne ya motsa to Dan Allah kar aja doguwar sura bacci nake ji,Bai kulata ba ya tada sallah, mamaki ne ya kama Shukura ganin sai da suka zo rakaar kashe Ahleef Yayi rafkannuwa Maimakon Sallama sai ya mike ya daura sallarsa, Shukura tace Nafeela ba gyara sai Farilla Malam ka sake,Ahleef ya Kara tayarwa Yanzu kuma Yana yin raka'a daya kawai sai ya zauna yayi tahiya da sallama,Shukura ta sheke da dariya tace wai lfy?
Tsaki yayi kadan yace sorry Bari mu sake,Ahleef ya Kara sakewa anci sa'a yayi ta dai dai bayan sun idar yayi adduoi ya dafa kanta,bayan ya Gama yace kina Jin yunwa?tace a'a sai anjima, ya Bata fresh milk me yawa ya dinga dura Mata sai da tace ta koshi,Shima yasha,Daga Nan yace mu kwanta mu danyi bacci sai yamma zamu fita,Shukura tace Yaya kamar kasan baccin nake ji ta furta tana me hayewa saman bed, Shi Ahleef kuma bai son ya lallaba ta taki yarda shi yasa Shima ya haura saman Bed din Yana binta da mayen kallo idonsa yayi ja har wani kyalli cikin kwayar idonsa keyi.
Ganin baiyi fara'a ba Shukura a tunaninta ko laifi tayi Masa ransa ya baci sai ta dawo ta shige jikinsa ta lafe,Gashinta ya fara shafa Mata a hankali cike da nutsuwa sai ko yaga idonta ya rufe zatayi bacci sai ya daina shafa gashin ya Dan cijeta a kunne kadan ba shiri ta bude idonta tare da sakin Yar Kara kadan,Murmushi yayi Wanda ya Kara masa kyau.
Wuyanta ya shiga murzawa ya gangaro kirjinta Wanda dama bra da pant ne kawai a jikinta sai hijab din da tayi sallah a hankali ya zare Hijab din daga jikinta,Nan take ya susuce ganin dukiyar Fulaninta cike tamjam a tsaye,gefensu ya fara shafowa Shukura ta fara amsar sako tayi wani luf, daga shi sai Boxers ya balle Bra din ta,ya rungumeta sosai suna Jin kaunar junansu na Kara ratsa su, bakinta ya laluba da nasa suka shiga tsotse tsotsensu, Shukura ta shiga lailaya Masa jiki Bata San Kara haukata Ahleef take ba,cike da rawar jiki ya fara tsotsar boobs dinta Yana shafesu har ya gangaro cibinta Yana shafawa Yana lasarta, a kunne ya Rada Mata in cire pant din kina Jin dadi? da wata iriyar Muryar da tasa Shukura dauke wutar kanta na wucin lokaci dummm sabo da yanda taji jininta Yana wani zuuuuu sabo da abinda takeji na dadi a jikinta.
Ta saman Pant ya fara Shafa down nata sai ga Shukura tana sakin numfashi sosai tana Jin kunya Amma ba yanda ta iya da hallitar Allah Dole take nuna Jin dadinta a fili,tana Kara kankame sahibinta tana shafa Masa Kai kamar jaririnta,wani lokaci kuma tana shafo Masa nipple nasa Wanda Ahleef ya gama kaiwa karshen makura sabo da Shukuran tasa itama one ce, Sai numfashi yake ja da kyar.
Da kanta ta taimaka ya cire Mata pant,ya fara wasa da Down dinta Yana tsotsa,Shukura k awai kunya ta gudu abinda taga dama fada takeyi,sai labarin irin son da take Masa take ta bashi tun lokacin data fara sonsa har halin data shiga Akan sonsa a kauye,shi dai ji yake kawai Amma baya fahimta Shima,
Sanda yayiwa Shukura wani kalar salo cikin sarkewar murya me kalar kuka kuka tace Allah ya tsinewa Wanda.... yake raba mu ko ....wane.
a hankali Ahleef yace Baby yau zan karbi hakkina,Shukura Nan take tace kayi dai dai Dan Autana karbi abinka wajen duk Wanda ya danne ma hakki, karka sake wani ya danne ma hakki, can ta wani shidewa kamar Ana zare Mata Rai saida ta farfado ta Kara cewa a Office ne aka danne ma hakki ko a turai ko Momee ce?
Ahleef dariya ta zo Masa da kyar ya maidata Yana kallon ikon Allah sai dadinta take ji Amma bai hanata labari ba,shi abinda ma yafi bashi dariya yanda takeyi kamar me jinya a gadon asibiti irin tana Suma tana farfadowa,bai San Amaryar tasa jarababbiya bace sai yau duk kunyar ta yau ta gudu fes take kallonsa Abubuwa,harda kiransa da Dan Auta.
Aikinsa yaci gaba da yi Mata sannan a hankali ya fara shigarta ta fara Jin radadi kadan a gabanta,ba yaso kuma ya Mata ta karfi a hankali ya fara shigarta Amma Shukura tana jin zafi zafi jiki na rawa ta kwace jikinta da mugun sauri tayiwa Ahleef bazata bai taba tunanin zatayi yunkurin kwacewa ba.can gefe ta matsa ta dunkule jikinta tace Ni na gaji haka ma ya isheni.
Ahleef bai San sanda yace kee what?...ai kinyi kadan yarinya wlh gwara ma ki tsaya na Miki a hankali,Shukura ta ja Hijab ta saka ta mike tsaye saman bed zata gudu, Ahleef ya mike shima saman Bed Babu komai a jikinsa, Hajiya Babba gata Nan tayi bake bake....Kunya ta kama Shukura ta fara kokarin dira kasa,ya tare hanyar ta koma daya side din ya tare Nan ma,ta dawo tayi matukar firgita sai mazari jikinta yake, ta fara rokonsa Ya Ahleef in kana yiwa Muhammadu Manzon Allah kayi hakuri Dan darajar Allah,Dan girman ya rasulillahi,dan zatin Allah Dan Allah Ni wlh zafi wayyo uwata Ni na shiga uku tana yarfe hannu,tace dama Yaya Haka akeyi ne wai,Ashe da gaske mata sukeyi naji labari nace ban yarda ba,Yanzu ko kunyata baka ji? Dariya yayi yace wlh kika sake na kamaki Baki zo da kanki ba Allah sai na Miki da zafin gaske Wanda sai kin Suma.
Shukura ta makale kafada suna tsaye saman bed,Wai Dan Allah kasa kayanka jiba fa Ina kallonka yanzu Ko tausayina baka ji Yar jaririyata, yace ki Bari ki gani Mana yazo zai kamata ta dirga kasa ya jawo Hijab dinta ta kwalla Kara a rikice sai da Yan Hotel suka ji Kara,kowa ya firgita a Ina ne karfa ayi kisan Kai,Nan Maaikata suka fara bincika dakuna Dan tabbatar da zaman lfy a Hotel din,Da gudu suka fara zaga room din,Shukura dai ta koma saman bed ta tsaya tana haki, kamata yayi tare da fige hijab din ya jefar ya samu kamar a filin wrestling Ahleef ya kwarfe kafafun Shukura ta Fadi ragwaf saman Bed dama yace ba mutunci idan ya kamata, Shukura sai da taga da gaske yake zai yagalgalata Sam baya cikin hankalinsa Jarabarsa ta Gama tashi, kuka ta fara rerowa ko saurararta baiyi ba ya fara kissing dinta da zafi tana Jin radadi Hawaye Yana shararo Mata Yana hadawa da hawayen duka ya shanye, dukiyar Fulaninta ya shiga matsawa da yamutsawa sosai da sosai ga zafi takeji, Bata ce komai ba Yana ta Mata mugunta iri iri a ranta ta yarda Ahleef baya wani Sonta ita take haukarta, ya kusa shigarta kawai Securities din Hotel suka kwankwasa kofa,tsaki yaja,ya Sa Mata Hijab dinta shi kuma ya Sa boxers ya bude kofar a fusace, Security sai da ya tsorata yace I'm sorry sir Ina duba dakuna ko lfy dazu munji Ana ta Kara bama so matsala ya faru ne kasan duniya,Da kyar Ahleef yace ba Nan bane ya banke kofarsa ya koma Yana zuwa Shukura tana Nan inda take tana kukanta,ba mutunci ya daura daga inda ya tsaya ta isheshi da kuka Wanda har ransa Yana damunsa bai son yaganta cikin damuwa tsaki yaja tare da tureta gefe yace kinci sa'a na hakura kuma kamar inda Nasa dazu kika ji dadi sai kinmin yanzu nima naji ki biyani abuna, Shukura lokacin tayi dariya ta daina kuka tace Abu me sauki zan biyaka kayan tsiyarka, kin rainani Shukura Ni kike cewa kayan tsiyata,Ya hakuri to ba Haka nake nufi ba, to ai Kaine ka jawo na rainaka dazu ka tsaya a gaba na ba kaya,.
Shiiiiit yace Wai tayi Shuru, fara aikinki, Nan Shukura ta tattaro basirarta ta fara zubewa Ahleef tana sarrafashi mamaki ta bashi da ta iya komai yanda yake so,sai gurnani yakeyi da kalamai masu dadi yake fada Mata shima ya Gama fallasa son da yake mata, bai Gama Shan mamaki ba sai da Shukura ta fara Masa wasu kalar abu kamar a film,ka rantse makarantar koyon hakan da Romancing taje, gaba daya ya zauce sai yaji zaima fi XXX din Sweet,Shukura Bata tsaya ba sai da ta saita Ahleef tas yaji dadi marar misali ya gamsu ta samu nutsuwa tare da releasing sannan ta zube saman bed tana hutawa,Jikinsa ya jawota ya rungumeta yau ta Gama biyashi sai albarka yake Sa Mata, lokacin ita kuma Shaawa ta Kara motsa Mata sabo da Abubuwa da tayi Masa ba tare da yayi Mata ba,Bayan Sunyi wanka sun huta tare da Sallar Azahar yayi musu Order din abinci suka ci.
Shukura dai a daddafe take komai kawai Shaawarta ce ta dameta sai Ahleef take so kuma,gashi Bata so ya ganeta ga kunya,kuma ta kasa dannewa,sai kallonsa takeyi da taga hakan bazai fisheta ba sai dabara ta Fado Mata ta rike mararta ta fashe da kuka ka rantse gaske ne,Ahleef ya gigice yace asibiti My Heart karki mutu idan kika mutu bazan rayu ba,Shukura ta rungumeshi Kam sai goga jikinta take a nasa yace sai anje asibiti ko ya Kira doctor Shukura tace ai Haka nakeyi watarana da kansa yake warkewa wataran idan ya rage saura 1wk na fara period,Hannu yasa Yana shafa mararta Shukura tace cire min kayana Ya sun dameni ko zanji sauki wash....wayyo....Ahleef yayi Mata sintir Dan munafurci sai tace kunyarka nakeji ni,Murmushi yayi duk ya rude ga Dukiyar Fulaninta suna tsole Masa Ido,tana ta faman makaleshi shima tuni ya dawo ruwa tsundum Shaawa ta Masa yawa Yana shafa Mata Mara ta wani Ware cinyoyinta Ahleef ya kalli abinda ya gani na gudana sai tana ta gigitashi da Abu iri iri,Ahleef Yana shafa Mara ya daina ya koma Na shanunta, Shukura tace bani fa da lfy ka fiye naci da son abun Nan,yace pls kadan tace to kadan zakayi kaji Dan na fara Jin sauki ne da bazan yarda ba.
Zagewa tayi suka murje juna sannan suka sake wanka tare da Sallar laasar, yace ta shirya su fita yawo kadan.
5:30pm suka dau wankan Sugar suka fita.
Momee tana zaune Niima ta Fado Palon da sauri ta fada kusa da Momee tace Albishirinki yau Munga Shukura da Farhan suna ta iskanci shi da Shukura matar Ahleef,Kalli pics nasu,Wayar Momee ta karba tace Kai Wannan ai kamar Ahleef? Niima tace wlh Farhan ne mufa mun ganshi Kiri kiri Yana kasa da Kai suna Shan love,Momee tace baku da hankali wannan Ahleef ne nifa na raineshi da kaina,Niima ta fara rantsuwa Itafa Farhan Ne,musu ya kaure tsakaninta da Momee,Momee karshe tace da dare Zaki kaini Hotel din zan tarfa Dan iska kuma Ni na fada miki Ahleef ne,baku kula bane,Ni zai rainawa hankali wani ya dinga daga waya Ashe Yana Nigeria,ai kuwa bai nemi zaman lfy ba wlh indai muka hadu yau zan gwada Masa bashi da wayo Alhmdllh Abba ba ya kasar zanyi maganinsa.
Ahleef ya fara shirye shirye zasu bar kasar tare da Shukura, 11pm Ahleef ya shararo mota cikin Hotel din Shukura an kame a gaban mota suna ta dariya suna Hira cikin so da kauna ba zato suka ga Momee da Niima katsam a gabansu. Jikinsa yayi sanyi Amma sai ya fuske ba tsoro ya fito ya budewa Shukura ta fito sannan ya rike hannunta tare da ledojin da suka yi Shopping.
Momee ta matso gabansa kafin yayi magana ta kwashe shi da Mari,da sauri Shukura ta daura tafin hannunta saman kumatunsa tana shafa Masa tana sannu My Hero,never mind ok, Kai ya dagawa Shukura irin yaji din Nan,Momee tace munafiki sallamamme,Dan iska,butulu Wanda bai San mutunci ba,ai dama an fada rike dan wani masifa ne, irinku ne masu kashe Wanda suka raineku,to ai dukiyar da kake gadara da ita Bata ubanka bace jinin matsiyata,gadon tsiya da talauci,karfa ka manta ko uwarka doya take siyarwa a titi,marar asali Butulu,nafi karfin ka wulakantani, ai Mijina ya baka dukiyar da kake juyawa komai namu ne karka yi tunanin Dan anyi yarjejeniya da Lauya shike Nan,wlh ko mutuwa Abba yayi zamu iya cewa bamu yarda da kyautar ba Dole a kwato kudin a bawa masu gado,Kuma ka sani sai da yardata aka baka kudin,Dan Haka yanzu ma bata baci ba daga yau zuwa gobe ka kawo min duk abinda ke hannunka na kudinmu,ka zauna da Shukura kuci talauci tunda ita ka zaba, hakuri ya fara Bata shi bai son Fushin Momee kuma baya ganin laifinta Amma tuni taja Niima tana tafiya tana masifa ka sire min na tsaneka wlh haka suka fada mota sai gida,Ahleef a waje ya tsuguna tare da dafe kansa yaji haushin lafazin Momee,Shukura tausayin Mijinta ya kamata hawaye ya shararo Mata itama ta tsuguna kusa dashi tana ta kuka Babu Wanda yacewa kowa komai.Ahleef ne ya danne zuciyarsa yace muje ciki My Queen Yana Jan hannunta ta mike ta bishi har room dinsu,tana Hawaye,gefen Bed suka zauna ya daura ta saman cinyarsa yace kiyi Shuru komai me wucewa ne Dame kike so naji,mene abin duniya ba komai rayuwa ce Haka take kowa da kaddararsa,Kaddarar muce haka ok? Ta daga Masa Kai ya Sa harshe ya shanye Mata hawayenta.
Shuru tayi suna haka sai ga Kiran Abba a waya,Ahleef ya daga,yace Abba suka gaisa,Abba yace Ahleef ku samu a Addua gamu Muna cikin jirgi Amma jirgi ya makale a sama yaki gaba yaki baya Ina ji a jikina Mutuwa zanyi,na sanarwa Momee ma irin halin da nake ciki, ga Kudi Nan Basu da yawa million Hamsim ne na baka su halak malak kuma bance ka fadawa kowa ba wannan sirrinmu ne,in ka tashi kaje USA wurin George ka karba a hannunsa.
Idan Momee ko Niima Sun bukaci Dukiyarka daka Tara ta sanadin kudina ka Basu kawai kaje ka karbi wancen bana son ku samu sabani akan kudi,Akwai wasu takaddun gidaje da filaye etc duk George zai baku,abinda yasa nayi haka Naga Momeenku ta canja Hali Allah ya shiryeta,Allah ya sawa rayuwarku albarka,Ka rike matarka da Amana, iyayenka......kit waya ta tsinke Ashe jirgin ne ya fada kasa kafin yaje kasa ya tararratse a jikin katon Tsauni Babu Wanda ya tsira Abba ya rasu,Nan take news ya baza ko Ina,Ahleef kuwa kuka,Shukura da taji komai na wayarsu itama kuka tana gefe,News ya kunna sai ko ga labarai ansa live,Momee dasu Niima kusan haukacewa sukayi da suka ji labarin.
Nan aka fara zaman makoki Har Baba da Umma Saudatu suna gidan Momee,Ahleef da Shukura Ana ta zaman makoki an cika dam kasa kasa da mutanen fadin Nigeria du Ana ta zuwa taaziya,Shukura dasu Saudatu Kam hakuri kawai sukeyi da Momee hantara da zagi tare da Harara take musu hakanma Dan Mutuwa ce da sai ta koresu,duk Mutuwar da akayi musu Basu ji digon Nadama ba kan Shukura dasu Umma.
Anayin sadakar Bakwai Momee ta Kira Lauya tace an soke kyautar da Abba yayiwa Ahleef zai maido Mana da abarmu,Lauya yace A'a Momee tace wlh zata daureshi ko tasa a koreshi daga aiki,shi kuma yasan halin masu kudi a kasar nan zai rasa aikinsa, Ahleef cikin bawa Momee hakuri yake ko yaushe, yau ma ya damka Mata komai Wanda Abba ya bashi kaf Dukiyarsa har wacce ya Tara komai ya Basu,tare da yardar Lauya,ba a ja da masu kudi a kasar Nan yanzu zasu tarwatsa rayuwar mutum cewar Lauya, Momee ta karbe dukiya tace Ni zaka mayar Yar iska Kai ga me kudi ko can gasu gada, tafi wajen Iyayenka kuci talaucinku Wanda basusan mutunci ba,bai ce komai ba Shukura rike a hannunsa suka fita, Farhan ma yasan komai yayi tir da halin Momee da yaranta,duk Wanda yaji abinda Momee tayi sai yasha mamaki daga Mutuwar mutum sai tattara dukiya.
Momee yanzu Bata da Wanda take gani a gabanta sai Mubaraq yayan su Hafcy,sabo da Niima tana sonsa Yana zuwa da wata suffa ta mutumin kirki gaba daya iyalan su Adamu sun shige jikin Momee sosai dasu take harka komai sai dasu,Maman su Hafcy kuwa itace babbar kawar Momee yanzu sai zuga Momee sukeyi komai sai Momee tayi Shawara da Mama ko Hafcy ko kuma Mubaraq,itama Niima Haka sabo da son Mubaraq da take sosai kamar ranta,sai abinda yace shi zatayi,ko unguwa zata fita sai ta nemi Izini a wajensa kamar anyi auren sai yaga dama zaice taje ko kar taje, sai so take ya turo manya suyi aure Amma sai ya kawo Uzuri yace wani gini yake so yayi Nisa sannan ya turo,ko yafi so idan ya Gama gininsa ayi aure sharp sharp cikin wata daya kacal,Niima ta yarda dashi baya karya.
Shukura kuka ta rataya Jakarta suka tafi har motocinsa ya Basu du,Farhan ya kwashe su Umma da Ahleef tare da Shukura ya kaisu wani Dan gidansa daya gina na hutawa me kyau sosai.ba abinda Babu daga Me gadi sai wata Yar aiki Hajiyayye matashiya zata Kai 25yrs ta taba aure Bazawara ce ita ke gyara cikin part din da yiwa Farhan girki idan Yana bukata, Ahleef ma ya Santa sosai sabo da tare suke zuwa gidan suna Hutawa, Hajiyayye ba abinda take kauna sama da Ahleef so take ya sota ya aureta ko bazai aureta ba to yayi sex da ita bukatarta ta biya Amma shi Ahleef Sam bai San tana yiba.
Tunda taga Ahleef ya shugo take kallonsa kamar Mayya,tana ganin Shukura rike da hannunsa,Nan take taji ta tsaneta.
Shukura kuma Haushin Hajiyayye taji da taga tana yiwa Ahleef wani kallo tana gaida shi, Bayan sun nutsu kowa ya dauki Room din da yake so,Umma da Shukura Suna Palo suna tattaunawa akan matsalar data taso, Baba Da Ahleef ne tare da Farhan suka yi sallama sun dawo daga masallaci, a Palon suka ya da zango Suma,Farhan ne ya fara magana, Alhmdllh kowa yaga abinda ya faru wannan Mu daukeshi a matsayin kaddara, Ahleef yayi dariyar karfin Hali yace sannu Sheik Dalla yi Mana Shuru,A'a ai gaskiya ya fada yaron kirki ci gaba cewar Baba,Umma tace kunfi kusa ai ja'iri.
Ahleef yace Umma zamu ci gaba da zama anan tare kafin naje USA Nan ya Basu labarin wayarsu da Abba,Umma tace to baza mu rufe ba Dole a fadawa Magada wato su Momee da yaranta idan sun Amince da wasiya shike Nan kaje turai ka karba idan Basu Amince ba a hakura Allah ya baka naka,Baba yace wannan Haka ne abin duniya bana Kiyama ba bazai rufe Mana Ido ba Dole abi doka Dole a sanarwa magadansa,Ahleef yace to ba damuwa,Farhan yace wannan gaskiya ne,idan Basu yarda ba suje su karbi abinsu Ni kuma zan yiwa Daddy na magana zai bawa Ahleef jari ko nawa ne,Ahleef inshallah bazai tabe ba kuma in Allah bazai tozarta ba zanyi iya kokarina.
Godiya Umma da Baba suka dinga yi suna sawa Farhan Albarka,Shukura Ita a Dole me Miji tace Haka kawai sun Sa bawan Allah a damuwa sun hanamu zaman lfy Akan son Kai da son duniya,shima Ahleef din da suka rikeshi ai Allah ne ya kaishi gidan lokacin Yana jariri,wannan ai ba dai dai bane ace Dole sai abinda kake so zaiyi ko ya Saba shariya, ai Allah zai saka Mana ne Allah kuma ya shiryesu yasa su gane.
Baba yace Ameen yata Allah Miki albarka,Ahleef da sauri ya amsa da Ameen kamar shi aka sawa Albarka,Umma tace to marar kunya,harda Saurin amsawa sabo da Matarsa ce cewar Farhan ,Ai Kai kaki kawo Mana matar taka cewar Umma, Farhan ya Sosa Kai yace ai na kusa Umma a tayamu da addua Allah kawo ta gari suka amsa da Ameen.
Shukura tace Ya Farhan wannan Yar aikin a Ina ka samota? Farhan yace a wajen Mamata takewa aiki nace ta bani ita tana min girki idan nazo Nan ko Ina bukata lfy dai ko? Shukura tace lfy Lau Amma Ni bana son yar aiki tayi min girki da aikin gida du zanyi ni daya ka maidata wajen Mama Mana in ba damuwa,Nan take kowa ya harbo jirgin Shukura Bata so mijinta ya kalli wata budurwa,dariya Farhan yayi yace to zan maidata yau yau ma kuwa,Umma tace ikon Allah Sannu Shukura da kokari.
Ahleef kuwa dadi kawai ya lullubeshi Shukura na kishinsa,Sallama Farhan ya musu suka fita tare da Ahleef sai yaga motoci har biyu sababbi fil masu tsada anyi parking nasu,Farhan yace ga motoci Daddy yace a kawo maka,Ahleef yace haba abin ai yayi yawa, ko kulashi Farhan baiyi ba ya hau motarsa ya bar gidan,su Umma duk sunji dadi sosai ganin motocin Ahleef dinsu bazai tabe ba,Shukura sai murna take.
Hannun Shukura Ahleef ya kama yace muje bedroom mu Dan huta ya Rada Mata wata magana a kunne Shukura ta rufe Ido tana Murmushi Wai kunya, yanzu za a dauko Mana kayanmu na Hotel Honey, Bedroom suka shige harda sa key sabo da tsaro.
Momee kuwa tana karbar dukiyar Ahleef kaf sai ta kirawo Mubaraq ganinta Dole ma zai auri Niima ai sun Zama daya sai ta dorashi a kansu Wai yaci gaba da juya komai,Sannan sirrinsu na kudi da kadara Mubaraq ya San komai kaf ta wajen Niima, Mama dasu Hafcy ihu da murna sukeyi suna jinjinawa Mubaraq. Alhj Adamu bai San me sukeyi ba Mama ta Hana a fada Masa komai.
Ina Godiya masu Sharhi.
Asmabaffa
AsmaBaffa
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
57-60
Official
By
AsmaBaffa
HOUSE OF HAUSA NOVELS Ina Godiya da Sharhi.
ASMABAFFA FANS CLUB Kuna Raina.
JIN DADI SABO FANS jinjina me tarin yawa tare da sauran Gps 😍😍
Na gode da Sharhi fans.
Suna shiga ciki Shukura ta zame Hannunta dake rike Dana Ahleef ta Sigar Shagwaba ta furta Baka Jin kunyar Umma da Baba, Ido ya zuba Mata sabo da ba karamin kyau tayi ba, kumatunta ya nufa da niyyar kissing nata ta matsa da sauri tana Murmushi zaka fara ko,je kayi wanka to ka fito,Maganarta ya kwaikwaya sai dai muyi tare,kyalkyalewa tayi da dariya ka iya irin maganar tawa kuwa,Ni kunyarka nakeji bazan iya, mene Baki sani nawa ba?nima nasan naki,ai Lada Zaki samu?
Kai ta girgiza Ni dai a'a hannu yakai da niyyar kamota da sauri ta zille Masa tana dariya, binta yayi suna zaga dakin shi Dole sai Sunyi wanka ita kuma taki yarda, ya samu nasarar kamata ba tare da Bata lokaci ba cak ya dauke ta tana wutsil wutsil bai tsaya ba sai Toilet tana kukanta na Shagwaba,bai taba kallon Surar Shukura kamar yau ba sai gaba daya ya zauce, da kyar ya daure suka yi wanka da Alwala sannan ya daura musu towel tare da dakkota, Mai kuwa itace ta shafa Masa, akwatunansu tuni har an kawo Musu daga Hotel,kofa Umma ta kwankwasa musu Ahleef ya bude,tace ga kayanku an kawo zo ka shigar muku dashi ciki, Bayan ya kawosu daki wani yard milk color me Masifar kyau da tsada marasa Nauyi Shukura ta zabo Masa, shi kuma ya dakko Mata wata doguwar Riga ruwan kasa me kyan gaske sama ta Dame tayi mata das kasa Kuma ta Dan bude sunsha kyau, Ido ya zuba Mata duk motsin da tayi Yana binta da Ido,Hannunta ta saka ciki cikin nasa, Ahleef a hankali ya shiga murza yatsunta,kungunsa ta rungumo sannan ta kwantar da kanta saman kirjinsa tausayi yake Bata sosai.
Ji yayi Yana neman canja salo ya daure da kyar daga bisani yace Magrib tayi Bari na wuce masallaci kema sai kiyi sallah sannan kin manta kin Kori me girki sai kije kitchen, dariya tayi tana boye fuskarta a kirjinsa.
Tare suka fito Ahleef da Baba suka wuce masallaci Shukura har kofar shigowa part din ta raka Ahleef, sai ta leka ta kofar tana daga Masa hannu suna magana da Ido,Har Baba ya bar gidan Ahleef bai sani ba.
Niima ce taci kwalliya Mubaraq yazo sai rawar kafa takeyi zasu fita tare,da sauri ta fito wajensa a compound yasha kyau cikin manyan kaya kamar wani mutumin kirki,Niima cikin takunta ta fito Yana Kare Mata kallo Yana hadiyar Miyau,tun kafin ta karaso ya sauko daga saman mota tana zuwa ya rungumeta tsam a jikinsa a hankali ta dago kanta tare da hade bakinsu wuri daya suna kissing ba ji ba gani su a Dole wayayyu Yan zamani, Mubaraq ya Gama rudewa murya na rawa yace Beb shiga mota ki muje ki kalli gidan Dana Gina kwanan nan.
Ba musu ta shiga gaba yaja suka bar gidan zuwa wani katafaren gida na gani na fada,duk da kudin su Niima ya siyi wannan gidan karya ya sheko Mara yace shi ya Gina Bata San kudi yasa ya siya ba.
Niima Murna tana ta faman wow tana kalle kallen haduwar, yace shugo Mana sweetheart,Haka ta shiga suka dinga zaga ko Ina,Bayan sun Gama ya jata har Bedroom suna shiga kamar Dan akuya ya shiga romancing nata,da kyar ta kwaci kanta,sai ya fara fushi Bakya so na ko? Ya zaka ce haka? Niima ta furta,gashi Nan dan abu kalilan kin Hana,a Haka zamu ji dadi idan munyi auren? Baki iya komai ba,nafi so na auri wacce ta iya Bedding gaskiya idan baza ki koya ba akwai matsala,ai tun a waje ake koya sabo da idan kayi aure dama ka iya.
Ki daina yarda da maganar Mata ta wani Dole sai kakai budurci gidan miji,Duk duniya ta yarda Virgin Bata da dadi Amma gaskiya gwara ma ki mike tsaye ki koya,nima fa ba dan iska bane kawai gani nayi Baki iya komai ba kuma ya dace ki koya,Amma tunda Bakya so ni wlh zamuyi fada mu Bata bana son auren wacce Bata waye ba,Niima taga ran sahibi Mubaraq ya baci gashi Yana ambata rabuwa,ita baza ta iya rabuwa dashi ba,shi yasa Dole tace na yarda to Amma kayi min a hankali , ta tabbatar zai aureta shi yasa ta yarda.
Mubaraq dadi ya lullubeshi ya samu nasara, Nan ya fara murzar Niima itama tana tayashi tuni ya zare musu kayan jikinsu suna tsotse da lashe lashe duk sun gigice suna murzar juna kafin daga bisani ya shigeta,to dama ta saba da romancing duk maza sun yi fingering palace din shi yasa ko zaffi Bata wani ji ba sai ma dadi suna ta iface ifacensu,Mubaraq kamar namijin Zaki mayunwaci sai gurnaninsa yake ba dadin ji.
Bayan sun samu nutsuwa Niima ko Dana sani Bata yi ba gani take in dai akan Mubaraq ne ba abinda baza ta iya ba a duniya ko sabon Allah ne akan Mubaraq dinta yayi fushi da ita gwara ta aikata, Mubaraq yaji mugun dadin da bai taba jinsa a jikin matansa na bariki ba sabo da Niima kullum cikin cin kayan itatuwa take tana kula da kanta Amma duk ya tashi a banza ta bada dadin a waje ta aikata sabo Babba Wanda yanzu abin ya Zama ruwan dare wurin Yan Mata da Samari sabo da so sai mace ta bawa Namiji kanta,gani sukeyi wannan shine so kuma zai auresu, wasu Kuma sabo da son Abin duniya.
Yan Mata a kula so ya daina rufe Mana Ido Ana tafka sabon Allah Akan a batawa saurayi muzo muna Dana sani marar amfani.
Niima ranta fess ta farantawa sahibinta Rai yau,shima sai wangale Baki yakeyi ya samu nasarar abinda ya Dade Yana kwadayi a jikin Niima, wanka sukayi tare wa iyazubillah lallabata yayi suka yi wanka tare kafin su Gama wankan ya lallabata suka sake second round a toilet, Bayan ta gasa kanta sosai ya Bata wasu kwayoyi na Hana daukan ciki ta Sha, har dare suna baccin gajiya sannan suka shige mota ya kaita Shopping tare da maidata gida.
Momee Bata wani damu ba tace ya Naga kin Dade har dare Haka,Baki Niima ta tabe tana Mika da hamma ta gajiya sannan tace Momee na biya Office daga Nan muka danje cenema kallon wani American film daga Nan muka je Shan Ice cream,Murmushi Momee tayi tare da cewa Ina ruwan Mubaraq yaron kirki to Ina na Latifa?ledoji Niima ta mikawa Momee gashi Mubaraq yace a baki,karba Momee tayi tace yaron kirki Allah Masa Albarka,Shi yasa na yarda dashi sosai kamar Dan cikina Haka nake jinsa that's why na damka Masa dukiyar Ahleef ya juya Mana ita mu kuma muji da sauran.
Latifa ce ta shigo da sauri ta karbi ice cream dinta da tarkacen Zaki tace Kai Sister kin Dade wlh yau fa 8days da Mutuwar Abba Amma har kika samu sukunin fita yawo? Momee tace Wanda ya mutu ya rigada ya tafi bazai dawo ba sai a tsaya baza ayi komai ba,Dariya Latifa tayi tace to Ni tunda zan Sha kaso na mene nawa a ciki ma tayi gaba.
Tunda Abba ya rasu Su Momee suka mallaki komai na dukiya shike Nan Momee ta Kara lalacewa ta maida kanta karamar yarinya, Attachment take sawa sosai a kanta tayi damammun dinkuna sabo da kudi sun lalata ta yanzu ta shige sahun Yara kana kana,Dan siririn gyale take yafawa ta fice tana tafiya da kyar sabo dinkuna na rashin mutunci da take sawa, kawai kashe kudi take har Dana hauka,itace yawo kasashe kasashe da manyan matan kasar Nan hajiyoyin Gomnoni etc, gata yanzu duk Yan Film na Hausa da Yan Nollywood dasu take harka kullum suna tare suna zugata suna tatse Mata dukiya,Yanzu duk inda zata shiga sai kaga wasu daga cikin Yan film daban daban da Mata Yan duniya,sabo da yanzu idan mutum ya Isa wani a kasar Nan to da wasu daga yan Film zaka ga Yana muamula tare da mawaka celebrities aikin kenan suna cin kudin mutum domin wasu basa harka da talaka sai me kudi Wanda zasu tatsi rabonsu.
Ba a Nan Momee ta tsaya ba Yanzu ta Zama babbar kawaliyar Gomnoni,Senatoci,Yan Majalisa Da wasu kusoshi na kasar Nan ita ke Kai musu yaran Mata kyawawa suna Masha a dasu sabo da so take a Bata Babban mukami a Gomnati yanda zatayi suna a duniya kowa ya santa,Haka Mata masu kudi Wanda suke neman Mazaje Yan Shila Momee ke Kai musu ta Gama lalacewa kudi kawai take hauka dasu,Niima ma haka,Latifa yanzu ta waye kullum tana club tana Shan kayan maye,Suhail da Sultan Suna Us suka samu labari har kukan takaici sukayi,takanas suka taho Dan suyiwa Momee fada Amma sai suka ga abin ya taazzara Mata Yan duniya a gidansu wajen Momee,su kansu da suka kalli uwarsu har wasu farcen roba take zokalawa a hannayenta sai da suka zubar da Hawaye,kayanta wasu cibinta a waje Amma a Haka take Yawo a gari,sabo da giyar kudi an mutu an bar Mata dukiya, Mazan banza sai shige da fice sukeyi, Sunyi Mata fada tace ba Wanda ya Isa ya hanata warwasawa idan suka Kara Mata magana Allah ya isanta,Sun nemi Ahleef wajen Farhan, Farhan yace ai Ahleef ya dauki Matarsa sun bar Abuja fafur yaki fada musu inda Ahleef yake,Kawai sai suka koma USA dinsu da rayuwa tunda Allah yasa Abba ya mallaka musu Dukiyarsu Basu damu da gado ba Tunda Momee taki yarda ayi rabon gado tace ai duk yaranta ne Kuma abin yaranta ai nata ne.
Dangi da Yan uwa Sunyi Mata fada Amma taki ji shi yasa duk suka fita daga harkarta abinda taga dama takeyi.
Niima da Mubaraq sun koma kamar miji da Mata yanzu sun tare a wannan gidan nasa kusan kullum suna tare suna masha'a, rayuwa Kenan,wani lokacin da ya dace ya saduda da duniya sai kaga lokacin yake lalacewa ma,Allah yasa mu dace ya kiyashe mu da canja Hali daga me kyau zuwa na banza,Allah yasa na banzar da mukeyi mu canja ya koma Na kirki.
Ahleef ne yayi parking Motarsa cikin shiga ta alfarma, Shukura tana kitchen tana tsantsara girkinta masu dadi saura kadan ma ta gama, taji dirin motar Ahleef, ita kadai taji wani sanyi a ranta Nan take ta saki Murmushi me kyau sannan ta Kara gyara English wear din dake jikinta Riga da skert masu shegen kyau ta fito kamar Yar Baturiya a ciki,ta window ta leka ta hango shi Yana fitowa daga mota Yana kwaso ledoji, ji take kamar ta zura da gudu ta rungumeshi sannan ta karbo kayan dake hannunsa Amma kunyar Umma da Baba karsu ganta yasa ta fasa,duk da tasan Baba ya fita wajen abokansa Umma Kuma tana dakinta Amma gudun kar a samu akasi yasa taji tsoron aikata hakan.
Kasa jurewa tayi a hankali ta leko Palo ba kowa sai kamshi da sanyi ne ke tashi,Sadaf Sadaf ta fito tabi ta Bayan labile Wai kar a ganta,Umma tana kallonta lokacin ta fita garden ta Ciro na'a Na'a tana shigowa taga Shukura tana tafiya ta cikin labile dariya ma ta bawa Umma,da sauri Umma ta wuce daki Dan kar ma Shukura ta ganta taji kunya.
Shukura ta bude kofar Palon a hankali ta leka kanta wajen Compound ta tabbatar ba kowa sai Ahleef da ya tsaya jikin mota Yana waya,Dan siririn gyalenta ta gyara dake saman kanta, kallonta Ahleef yayi Yana waya ta tsaya taki karasawa sai hannu take daga Masa tana jikin kofar palon kamar tana bada hannu a round na titi, wani sanyi da nishadi ya shigi Ahleef tare da kaunar matar tasa ya Kara sukansa a kahon zuciyarsa bai San sanda ya fara Murmushi ba Yana waya da Farhan, Farhan yace Dalla Malam dariyar uban me kakeyi,Shuru Ahleef hankalinsa Yana kan Shukura,Farhan ya fara zage zage Jin Ahleef yaki amsa Masa sai wani kunkunin dariya yake,Sai gajiya yayi shima ya yanke waya Yana zage zagensa irin na abokai,cikin takunsa me kyau na Isa da nunan Mazantaka ya karaso har gaban Shukura a kasa ya zube ledojin na Shopping Kafin tayi Motsi ya rungumeta Kam Kam sannan ya dagata sama ya Shilla ta dama gata Yar Caras ba Nauyi,dariya sukayi gaba daya,a kunyace tace Sannu da zuwa My Hero karo na farko kenan data canja Masa suna,Da sauri yace me kika ce? da sauri ta kwashi kayan ledojin ta tafi da gudu gudun ta tana cewa so kake Baba ko Umma su kama Ni naji kunya.
Tana shiga Palo taga Umma zaune tana kallo,kunya ta rufe Shukura tana wani noke noke,Umma ko ta kanta Bata bi ba sai kallonta takeyi,Sum sum Shukura ta shige Bedroom ta ajiye ledoji,Ahleef ya Shigo Bakinsa dauke da sallama,Umma tace Sannu da hanya,Yawwa ya furta tare da zama kusa da ita yace Umma barka da yamma,Fuskarta dauke da Murmushi ta amsa,Shukura ta fito ta wuce kitchen ko kulashi Bata yi ba Wai Dan kar Umma ta ganota,tana shiga kitchen ta dauko lemonta na kwakwa data hada ya dau sanyi ga dadi,Sai ta dauki wayarta ta tura Masa text
Dan shigo kitchen kaga wani Abu,Umma tana kallonsa ya karanta Yana wani Murmushi me Kara Masa kyau,tsam taga ya mike yayi kitchen, Kai kawai ta girgiza tana Jin dadin yanda Shukura ke kula da danta gashi ba raini ta daukesu kamar iyayenta,Bata Bari Umma tayi wani aiki etc.
Ahleef Yana shiga kitchen din ta baya taji ya rungumeta tare da daura kansa saman dokin wuyanta Yana Jin wani shaukinta,itama Haka,Nan ta juyo suna Facing juna ta dauki lemon a karamin glasscup me kyau ta daura Masa a Bakinsa da kanta ta bashi ya shanye yaji dadi ga sanyi,yace a karo harda bude bakin Yana jira ta Kara Masa yace one More pls,ta Kara Masa ya shanye,yace More Baki ta bude ta Sigar wasa tace no bazan Kara ma ba ya Isa cikinka ya cika,Kai ya girgiza tace to anki din ta maida katon glass juck dinta fridge ta wanke karamin cup din ta maida.
Damunta yayi da tabe tabe a kitchen din ya hanata ta karasa,da kanta tace je kayi wanka taja hannusa ta turashi waje tana Masa dariya shima Yana dariya Umma taga ya fito Kuma yaki dainawa,Umma tace iceko ciwon hauka ne ya kamaka bamu sani ba? Sai lokacin ya nutsu ya wuce Bedroom a kunyace.
Bayan ta Gama girkinta ta shirya Dining ta shiga Room dinsu sai ta hango Ahleef baiyi wankan ba ya daura Towel kawai yayi zamansa,Yana ganinta ya mike tare da cewa dama jiranki nakeyi ki min wanka Honey, dama baka yi ba tun dazu Nan ta fara kukan Shagwaba tana dire diren kafafu Allah akwai wahala nafa gaji Amma baza ka rage min aiki ba kullum kullum Ni nake maka wanka.
Kallonta ya tsaya yi wani so sexy ta Zama da tana Shagwabar hakurinsa ya kusa karewa da kallon Shukura da yakeyi kullum sai Romancing sukeyi taki yarda daya fara tun kafin ya shiga zata ki yarda Amma ya kusa maganinta.
Gani tayi ya kafeta da Ido bai ce komai Bata so ta Bata Masa Rai sai tace Wasa fa nakeyi ban gaji ba muje nayi maka,Aiko ya mike tare da furta kin taimaki kanki da yau kin gane kurenki,dariya sukayi tayi Masa wankansa yanda yake so ita kuma taki yarda ya Mata wayo tayi sabo da Yana kallonta zai birkice Mata shi yasa taki yarda saida ya fita sannan tayi nata ta Kara wanke toilet neat ta fito, ai yanda ta Masa wanka Haka ta tadda shi Wai jira yake ta shafa Masa Mai tare da Sa Masa Kaya, tana zuwa da Dan guntun towel dinta karami kuma ta nadeshi a kanta tana tsane ruwa,Cinyoyinta ya bi kallo wow ko Ina lukwi lukwi dashi skin nata na sheki da kyalli lumi lumi jajir, kugu ta rike da hannu biyo a gabansa ta dafe goshi tace baka ji wlh taja gemunsa kadan da Wasa sannan ta ja kumatunsa da hannayenta da Wasa,dariya ce ta kamashi Yana tunani a ransa idan ba aure ba me zaisa kamar Yar yarinya Shukura ta dinga Masa haka kamar jaririnta Kuma Yana biye Mata shi wani birgeshi takeyi ma, har baya so ya rabu da ita ko na second daya sai Dole, wace ta Isa tayi Masa Haka idan ba Shukura ba, hannunsa data kamo shi ya katse Masa tunaninsa ta kaishi gaban Mirror kenan,
Ba zato ya faki idonta ya balle Mata towel da sauri ta Kai hannu zata dauko ya dauke ya rike taja taja ta kasa kwata,tace Allah sai na kwance naka yace Haka nake so maza,tasan abinda zai Mata gashi tayi alwalarta Magrib ta kusa tace Dan Allah kayi hakuri wlh nayi Alwala ban so ta karye,a kunne ta Rada Masa sai dare zan ma wani Abu da ban taba yi maka ba,zaka ji dadi idan aka sake sai Umma ko Baba sunjiyo ihunka,dariya yayi tare da cewa Ni Zaki ma wayo,Shukura tace ba wayo da gaske pls kaji Dan Autan, da kansa ya daura Mata abinta suka shirya ita tasa atamfa Riga da skert na atamfa me kyau ya kamata tayi matukar kyau,shi kuma jallabiya ruwan toka yasa fitted me tsada da kyau, a gurguje ya Mata sallama tare da kissing dinta a tafin hannu da goshinta sannan ya tafi masallaci,Itama Hijab tasa lokaci nayi tayi sallarta da azkar tana zaune tana adduointa har akayi Isha ta mike tayi sannan ta fita Palo,ta karasa shirya Dining ta kawo Drinks etc,tana Haka Umma ta fito tana sannu Shukura Bakya gajiya,Murmushi tayi tace ba komai Umma, kinyi kyau sai kace zakije biki Shukura,Dariya Shukura tayi tace Kai Umma tana kasa da Kai. Umma a ranta tace yaran zamani Wai yanzu kamar Shukura sun iya kula da miji haka.
Zama Umma tayi a Dining Dama Baba yace bazai dawo da wuri ba sai 11 na dare karsu jirashi,Shukura ma Zama tayi suna Hira da Umma har Ahleef ya Shigo shima yaja kujera ya zauna Yana facing Shukura sai magana yake Mata da Ido tana sani taki ko kallonsa kar ya Bata kunya, Umma tana kallon abinda yakeyi tayi kamar Bata gani ba Shukura tayi Serving dinta abincinta tana ci kawai.
Zuba Masa nasa Shukura tayi ta tura Masa gabansa da lemo ta zubawa kanta itama ta fara ci sai kafarsa yake goga Mata da kafarsa, tayi kamar Bata ji ba, sai dai in sun hada Ido su sakarwa Juna Murmushi.
Bayan sun Gama ta kwashe komai tare da gyara wajen suka koma Palo gaba daya suna kallon News har Umma tana tsakiyarsu Ahleef na gefe Shukura na gefe sai sako suke turawa juna ta waya suna chat,Wani sako Shukura ta tura Masa sai yayi Murmushi me Sauti, Shima ya tura Mata tana gani ta karanta tana dariya kasa kasa ta sake tura Masa,ta Bayan Umma ya leko da kansa suka hada ido,suka danyi magana da Ido suka ci gaba,Umma ta gaji da halinsu tace Kai ku tashi ku bani waje, Baba ne ya Shigo dauke da sallama,suka Amsa tare da gaidashi suna Masa sannu da zuwa,Umma tace to ku San nayi ku bani waje, Sum sum suka mike suka tafi Baba Yana dariya yace me sukayi Miki ne Haka? Tace baza ka gane ba,Ahleef Sam bashi da ta Ido turai ta Gama lalatashi,Yarinya me kunya duk ya takura Mata,Baba yace ke Ina ruwanki dasu to ke lokacinki waye ya Sa Miki Ido? Murmushi Umma tayi ta mike ta dakko abincinsa suka nufi Bedroom Bayan ta kashe kayan wuta.
Shukura a tsorace take da Ahleef taga yau da kyar idan zai iya kyaleta,shi kanshi ya kudurce bazai tausaya Mata ya kyaleta ba a halin daya ke jin kansa ba.
Asma baffa
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
61-65
Official
By
AsmaBaffa
Masu Sharhi kuyi hakuri wannan Novel din baku wani samu kyautar page ba, bani da lokaci ne kwana Nan shi yasa da kyar kuke samu nake iya typing, sai a Next Novel Inshallah.
Shukura Zama gefen Bed tayi wani Shuru kamar ba ita ba, gani tayi Kallon da yake Mata ya shiga da tsoro ko idonsa baya iya daukewa daga kanta duk tabi ta rude ita kadai duk ac din dake room din Amma zufa ke keto Mata ta ko Ina, kusa da ita ya zauna a hankali, da sauri ta matsa har jikinta ya fara rawa,Ahleef ya kalleta kawai ya basar tare da cewa ki kwantar da hankali ba abinda zanyi Miki ni, tunda Bakya so ai ba a Dole je kiyi Shirin bacci ki kwanta sannan ki kwantar da hankalinki Yan Mata,da Hira yake janta har ta saki ranta suna hirarsu tare gwanin Sha'awa.
Wanka tayi sabo da ta Riga ta Saba Dole kafin ta kwanta sai tayi wanka,Shirinta tayi tsab tare da yin Nafeela lokacin Ahleef ya Shiga wanka, Bayan ya fito yabi jikinsa da turaruka sannan ya zauna gefen Bed da laptop dinsa Yana aiki,Mikewa Shukura tayi Bayan ta idar da Hijab dinta ta fita kitchen Coffee ta Hado Masa ta ajiye gefensa a hankali, Ido suka hada Murmushi yayi tare da furta tnx Wifey shi yasa nake Kara sonki kin iya caring, Murmushi kawai tayi ba tare da tace Masa komai ba ta zauna gefensa kafadarsu na gugan ta juna, Coffee dinsa yake Sha itama yana Bata tana Sha, bacci ta fara ji 10:40pm, muryarsa taji yace kwanta mana kiyi baccin ki,Kai nake jira,Kai ya girgiza sai nazo ki fara min kuka kawai Bakya so na yanzu da wacce take so nace ko Suma zata yi sai ta yarda ta bani hakkina,Amma ke kullum kuka kina baccinki Ni idan na Gama abinda nake Palo zan koma Na kwanta.
Dariya tayi tace ai in kaje Umma da Baba zasu ganka suce fada mukeyi,Hmm gaskiya zan fada musu abinda kike hanani Kuma kin San zan iya ba kunyarsu nake ji ba,Shukura ta bude Baki a tsorace tace Dan Allah karka fada musu ai abin kunya ne Ni kunya zanji pls,gobe zafa ki koma schl, sabuwa ka canja min ko waccen? Ahleef yace waccen tsohuwarki can Zaki koma, Shukura tace tam yanzu so take ta gyarawa su Latifa Zama shi yasa Bata so ma a canja Mata schl ba tare da ta kuntatawa sun Latifa ba.
Laptop dinsa ya kashe tare da wayoyinsa sannan ya kashe musu light suka kwanta cikin blanket, Shafarta ya shiga yi son ransa Yana sarrafata,itama Haka sabo da yanzu ta saba, Babu abinda kake ji sai nishinsu, gaba daya sun zauce Ahleef ko Ina tsotsensa yake da lashe lashe itama haka, Dukiyar Fulaninta yana Bakinsa daya Yana Wasa dashi, Salon yau da yake yiwa Shukura na daban ne Bata taba Jin dadi irin yau ba kalar sa daban,jikinta ya Gama macewa da kyar take Motsi, Down nata ya tafi Yana Mata wasu Abubuwa masu nauyin furtawa, kafin kace me Shukura sai kukan dadi take sama sama,a hankali cike da nutsuwa ya karanta adduar saduwa da iyali sannan ya shigeta Amma yasha Yar wahala kasancewa ta yarinya, Kuka Shukura ta sake Masa tana furta da zafi...wash...zafi Ahleef yayi Nisa baya ma jinta abinda yaga dama yi yake sai sambatu na sweet words yake Mata masu dadi, ya Dade Yana Abu daya, yaji dadin da bai taba ji ba a duniya, ya samu gamsuwa sosai da sosai, kamkameshi Shukura tayi sabo da zafin yayi Mata yawa, Ahleef harda hawayen dadi bayan ya zare jikinsa a nata,nutsuwa tazo masa,Shukura kukanta ya tsaya ba karfi tayi wani lakwas a gefe.
Sai da ya huta sannan ya dawo gare ta cike da so da kauna,ga nishadi da yakeji,bai San Ma Dame zai sakawa Shukura ba,Lallashinta ya fara yana sa Mata albarka Yana Bata hakuri, Baki ta rufe Masa da hannu tare da furta ka daina gode min kana bani hakuri tunda ka samu gamsuwa ai Alhmdllh,ba abinda bazan baka a duniya bare wannan da yake hakkinka, kawai taimaka min ka mikani toilet na gasa jikina.
Daukanta yayi kamar jaririya har Toilet,ya hada ruwa me zafi da gishiri,liquid sabulun muski ya zuba ciki ta shiga tana Zama da kyar tana tashi sabo da zafin ruwan Haka har ta zauna daram ciki,sai da tayi Haka tana zubar da ruwan ya canja Mata wani har tayi sau uku sannan yayi Mata wankan tsarki Dana sabulun,shima yayi nasa suka fito,a hankali take tafiya tale tale kamar Yar kaciya, cikin rigar bacci suka shirya,ya cire bedsheed tare da canja wani sannan suka kwanta Manne da juna sai bacci me dadi ya tafi dasu, Ahleef ya Dade rabon da yayi bacci me dadin na yau har mamakin dadin Shukura yakeji dama haka akeji ko matar tasa ce haka a ransa sai godewa Allah yakeyi.
Basu farkaba sai da asuba suka yi sallah da azkhar suka sake komawa bacci,Shukura ,7am ta farka tare da zare jikinta a hankali daga na Ahleef ta fita sai kitchen kafin kace me tayi soye soyenta,da wasu abubuwan na Breakfast ta shirya a Dining yanda ta Saba sannan ta gyara kitchen ta koma daki a hankali take tafiya tana tale kafa, wanka ta sheko tare da gasa jikinta, ta shafa Mai ta Gama komai,cikin ledojin da Ahleef ya Shigo dasu jiya ta dakko sababbin Uniform dinta Nan take ta gogeshi ta saka ta Kara wani kyau,komai sabo har schl bag da komai,biscuits da sweet masu dadi da tsada ta kwasa ta zuba a schl bag dinta ta shirya littafanta da komai, a gefen Ahleef ta zauna tana ja Masa yatsa da kyar ya bude idonsa a kanta,yasha mamaki ganin har ta shirya tayi wani kyau,tashi pls Hero zan makara 8am ta kusa,Baki ci komai ba Zaki tafi schl? Baki ta turo Masa Ni dai Dan Allah ka tashi nafa Gama Breakfast,mamaki ya kamashi har yaushe ta mike tayi wannan aikin?sai ta Kara birgeshi yaji sonta ya Karu a ransa, toilet zai shiga tace Ni dai karka yi wanka pls ka kaini schl sai ka dawo kayi wankan,shirinka dadewa, gefen Bed ta zauna tana jiransa ya sake yin Brush ya wanke face dinsa sai buga Masa kofa take Ka fito pls zan makara ta ciki yace zo ki min wanka,wlh abazan iya ba gwara ma ka fito ko na tafi a taxi,ko na tafi a kafa.
Dariya yayi sannan ya fito da sauri ya Sa 3qrt wando Blue da t-shirt fara gashinsa ya taje tare da fesa turare ka rantse wanka ya sheka abinka da farin mutum, tare suka fita, Su Umma Basu fito ba,Zama sukayi a Dining taci abinda take so shi bai Saba karyawa da safe ba,Tea yasha kawai ya mike,tace na zauna nayi gurkin Nan Amma sai kasha tea kawai ka mike, Kin manta sai 9am nake karyawa shima sabo da Fita Office ne da sai 11am.
tana gamawa tace muje mu gaisar dasu Umma sai mu tafi,Knocking sukayi tace ki shigo Mana, Umma tana linke Kaya suka duka tare da gaisheta ta amsa da faraa, Baba Kuma Yana ta Jan carbinsa a gefen Bed suka gaisa yace an koma makarantar ne Shukura,tace ae Baba,to Allah ya taimaka,tace Ameen Umma Breakfast Yana dining,mamaki da kaunar Shukura ne ya Kara kama Umma har ta Gama abinci ga makaranta Amma bai hanata aiki ba,tace to a dawo lfy Allah muku albarka Shukura Bakya gajiya.
Fitowa sukayi Ahleef sai kallon tafiyar Shukura yakeyi Yana boye dariyarsa, sai ya tsaya a bayanta bazai jera da ita ba Dan yasha kallon tafiyarta, juyowa tayi ta kamashi Yana Mata dariya,Harara ta watsa Masa taci gaba da tafiyarta Yana bayanta yace wannan tolo tolo ce ko agwagwa, ba tare data juyo ba tace a'a Yar kaciya ce, jikin motar taje ta tsaya tana Jin zafi kawai daurewa takeyi, bude mata yayi ta shiga ya rufe Yana tsokanarta sannan ya zagaya ya shiga shima suka tafi zuwa schl.
Har cikin makarantar ya shiga da hadaddiyar motarsa yayi parking sannan ya fito da sauri ya budewa Shukura ta fito a hankali Lokacin Latifa tazo suna bakin gate suna taren makara, suna tunanin zasu ga Ahleef a talauce sai suka ganshi Shar Shar sai ma kiba da kyau ya Kara,Shukura ma tayi kyau ta Kara kiba, Wani kallon Banza Shukura ta jefawa Latifa hannunta cikin na Ahleef suka wuce staffroom wurin PC bayan sun Gama magana har aji Ss2 Ahleef ya Kai Shukura sannan ya Bata 1k kudin Break, ta karba tana Jin kamar kar ya tafi,a kunne ya Rada Mata zanyi missing naki,kiyi karatu da kyau,zan dawo na daukeki ok? Kai ta daga kamar zatayi kuka tace to sai ka dawo,a kunne ya sake Rada Mata I love u Honey,Me too i do love u Hero, tafiya yayi suna dagawa juna hannu,Sai kallonsu students sukeyi sun birge kowa, Shukura sun ma kusa komawa Yan Ss3 su Latifa Waec zasu fara zanawa.
Ahleef motarsa ya shiga sai gida ya koma yayi wanka a nutse ya karya sannan ya fita Farhan sai kiransa yake a waya Yana jiransa,Su Umma yayiwa sallama ya wuce abinsa.
Shukura suna fitowa a Break ta shiga turawa Ahleef Messages Yana Mata replying suna ta faman chat kamar Haka:
Sweet Husband mun fito Break, Missing u Badly. tura Masa tayi suna tare da Farhan locin text din ya fada wayarsa Yana ganin Honey jiki na rawa ya bude ya karanta Yana Murmushi shima ya rubuta Mata Haka:
You have this incredible way of making my heart happy, Honey Sometimes I wonder if love is worth fighting for. Then I look at you. I'm ready for war.
tana karantawa itama ta tura Masa again:
Wow When you need someone to be there for you, I'll be right there by your side always! I love u My Hero, haka suka dinga chat iri iri ko wannensu na jin nishadi har sukayi sallama ta koma class.,Ahleef Yana ganin yafi ko wanne Namiji sa'ar samun mace itama Haka take gani tafi ko wacce mace dacen miji.
Shukura yau har tayi kawa Fatima me hankali da Nutsuwa,ga ilmi gata Yar gayu wayayya kyakyawa light chocolate tana da kyau ba laifi, itama sabuwar kawowa ce, tayi mamaki da taji Yar Shukura tana da aure kuma mijinta Bata taba ganin Dan gayu me kyau kamarsa ba Tunda take a duniya sai yau data ga ya kawo Shukura har class.
Shukura Bata kula kowa sai yanzu data yarda da nutsuwar Fatima, yau Latifa takaici bai Bari ko break ta fito ba Dan kar ma taga yanda Shukura tayi kyau.
Mutanen Unguwa da Wanda suka San Ahleef suka samu labarin abinda Momee tayi sun jajanta lamarin sai zagi Momee take Sha wasu Kuma Yan bakin ciki Allah ya Kara sukewa Ahleef, wasu Matasa masu Zama a Majalisa suna Hira sai gulma sukeyi ta gida gida har suka Fado kan Ahleef ai gwara ma da aka kwace,uban iyayi yanzu zamuga Dame zaiyi gadara,shi a Dole me kudi, wani cikinsu yace baku da labari ai kunya ta koreshi daga unguwa ko motar Hawa ta gagareshi duk an kwace,Wani makaryaci ya Kara da ai har kayan sawarsa Suka karbe ko gajeren wando basu bar Masa ba,mace ta raine ka tun kana yaro Amma ka zageta har kana ikararin Marinta,wani yace haba abin har ya Kai Haka? Tab ai labari sai Wanda kaji, wani Kuma yace gaskiya Ni yanda naji labarin Momee ce da laifi ta takurawa rayuwarsa, ku daina daukan jita jita da zance ya shiga gari sai kaji ya koma iri iri,gaskiya nima yanda naji Wacce ta raineshi ce me laifi Amma shi ai mutumin kirki ne Amma gaskiya zatayi halinta ai.
Momee zaune Cikin katafaren Palon ta cikin shiga ta alfarma,Hannunta rike da waya tana latsawa kana ta Kara a kunnenta alamar Kira tayi,Ana dagawa tace Excellency Naga kiranka, jam'iya ta Baki Babban mukami ki Duba News yau da dare Zaki ji,sannan kwanan Nan Zan Baki Babban mukami a state Dina,Murna Momee ta shiga yi,Yanzu zata yi suna a duniya itama ta Kara shiga sahun manyan kasar nan, sai bukawa frnds nata waya take tana sanar musu a tayata murna ta Zama Woman Leader ta jam'iya ta kasa Baki daya,Niima da Latifa sai Murna,Sultan su basu yi murna ba Sam da suka ji labari sai haushi ma da suka ji.
Niima da Mubaraq sai abinda ya Kara gaba tayi tayi ya aure ta sai yace ta jira tukun sai ta Gama koyar style iri iri na sex sai asha biki ita kuma Bata ganewa kullum suna Manne suna aikata Zina ba ruwansu daular kudi na eban su an mutu an bar musu dukiya sai hauka,da yawa Mutane suna Haka idan sun samu kudin gado sai a lalace Kuma Hajiya ta Zama tantiriya Yara Kuma suna Abubuwa Marasa kyau,Allah yasa mu Dace kudi su daina rudarmu suna halakar damu.
Tunda Mubaraq ya karbi dukiyar Ahleef da Momee ta damka Masa shike Nan su Hafcy gaba daya suka dauke kafarsu da zuwa gidan wata Momee,Mubaraq ma yanzu ya Dan fara rage haduwa da Niima sai tayi ta nemansa da kyar yake samu yace tazo su hadu a gidansa inda a Nan zai Kara lallaba ta ya kwashi gara,maganin Hana daukan ciki kuwa dankararsu kawai takeyi sabo da Mubaraq yace sam baya Jin dadin xxx idan yasa Condom.
2pm aka tashi su Shukura daga schl, sun fito suna Hira Fatima kawar Shukura ta kalleta sosai tace sai Naga kamar kina tafiya wani iri kamar Yar koyo ko rauni kika ji a kafar, Murmushin karfin Hali Shukura tayi sannan tace bugewa nayi a gwiwa ta sosai,Latifa sai Harara take zubawa Shukura ganin tana ci gaba.
Fitowarsu kenan sai ga Ahleef yasha Boyal dark Brown yasha kyau har ya gaji Shukura tana ganin motar Ahleef tace Fatima Mijina yazo dauka ta sai gobe na tafi,Fatima itama driver dinsu ne yazo ta shiga motarsu suka tafi tana dagawa Shukura Hannu.
Ahleef Yana daga cikin mota mazaunin Driver Shukura ta bude Bayan mota ta jefa Jakarta ta dawo gaba ta bude tare da shiga cikin motar bakinta dauke da sallama,amsa Mata yayi kawai ba fara'a a fuskarsa,Shukura ta kalleshi taga kamar Yana cikin damuwa,ko me ya faru dashi oho, tunda ta shiga mota taga Yana tunani ko motar ya kasa matsawa bare su tafi gida, a hankali ta kamo hannunsa tare da furta lfy Sweet heart? a hankali ya kalleta ya Dan saki Murmushi sannan yaja Motar suka tafi,suna kan hanyarsu taji muryarsa yace ya jikin? Kallonsa kawai tayi tace da sauki amma Me yake damunka? Kamar kana cikin damuwa, yace hmm Honey Dad din Farhan ne ya Bata Mana Rai Ni da Farhan,anjima zamuyi maganar. Sai hakuri cewar Shukura.
Bayan sun koma gida Umma tuni ta Gama komai da komai gidan a gyare tsab Yana kamshi abinci ma du tayi ta Gama, Umma tace Sannu da zuwa suka Amsa suna gaida Umma suka wuce Bedroom, tare sukayi wanka tare da shiryawa sannan suka fito Dining, Shukura tace Umma Ina Baba? ya fita wurin abokansa tsofaffi irinsu can unguwar su Hafcy inda mukayi aiki da,Baba Yana son zuwa wurin mutanan Nan,Ai an Saba ne da juna can cewar Umma, Ahleef yace Haka ne,Shukura ce ta zuba Musu abinda suke so a plate daya suke ci tare,lemo ma a cup daya suka zuba suna Sha cike da shauki,Umma tana kitchen tana aiki.
10pm Sunyi Shirin bacci suna saman Bed Ahleef Yana rungume da Shukuransa Yana shafa gashinta,Shukura cike da Shagwaba da shauki tace My Hero baka bani labari ba me Dad din Farhan yayi muku? Hmm Honey Wai Munje yace zai bani jari Amma karki ga fadan daya shiga yi min wai na tabbatar na biyashi kudinsa Nan da 1yr dama mu Yara mun Saba barnatar da kudi maganganu iri iri banji dadin kalamansa ba,yanzu har Ni zai fadawa tattali,ko iya Business sabo da zai bani rancen kudi kafin na biyashi sabo da yanzu yaga bani da shi.
Kirjinsa Shukura take shafawa a hankali tace Kayi hakuri Haka rayuwa take,ka daina damuwa kaji mijina ai Dad dinku ne,idan Kuma kaga da matsala ka bar Masa kudinsa kawai Allah ya baka naka, Honey harfa da cewa Wai idan kudinsa ya salwanta sai ya daure Ni har Farhan zai daure yace, Shukura tace to bar Masa kudinsa kawai Amma muyi Shawara da Baba ko Umma muji me zasuce, Allah ya kaimu gobe sai na sanar musu muji cewar Ahleef, Zancen su ne ya canja salo zuwa na soyayya Nan suka shiga farantawa juna Rai ba tare da yayi Xxx ba sabo da Shukuransa Bata warke ba.
AsmaBaffa
Ayi min afwa fans bana baku kullum Busy nake tnx all😍😍😍.
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
66-70
Official
By
AsmaBaffa
Washe gari da safe sabo da makaranta da wuri Shukura ta fada kitchen zata fara girki kenan Umma ta isketa suka gaisa,Umma tace kiyi iya cikinki da safe Kinga mu bama karyawa da Sassafe ke Kuma ga makaranta,Murmushi Shukura tayi tare da cewa to Umma ba matsala,Nan Shukura ta hada chips and Egg sai tea,tana Gama ci ta Shiga wanka,Bayan ta fito ta tashi Ahleef ya kaita schl, da sauri ya shirya suka yiwa Baba da Umma sallama suka wuce.
Bayan Ahleef ya dawo ya samu Umma da Baba ya sanar musu yanda sukayi da Dad din Farhan,Umma tace Shawara daya karka karba kawai bar Masa kudinsa,Baba ma yace hakane kawai kace ya barshi ka samu wasu sun Isheka,Farhan yace to sannan ya mike ya koma Bedroom dinsu kawai yaji gidan ya Masa zafi ba Shukura tunaninta ya addabe shi,ita kawai yake son gani suyi Hira, wanka yayi ya shirya tare da Fita ko karyawa bai yi ba,Umma tace yaci yace a koshe yake,Take away ya tsaya yayi na lafiyayyen Fried rice and chicken tare da Drinks ya wuce Schl din su Shukura yaga an kusa yi musu Break ma.
Yana zuwa lokacin sun fito Break tare da Fatima Kawarta suna Hira Shukura ta hango kamar Motar Ahleef, laa Fatima Kinga Mijina yazo nasan ma shine Maybe abinci ya kawo min,Murmushi Fatima tayi tare da cewa Lallai Yana ji dake,Fari Shukura tayi da Ido kana tace sosai yake Sona nima Ina mugun kaunar abina,Kirji ta dafe tana Allah sarki Dan Mijina muje na ganshi naji sanyi sanyi a Raina,Dariya Fatima tayi tace sai dai kije ke kadai Ni bazan je ba kunyarsa nake ji,Naga baya dariya ga kowa sai ke kadai yake yima,inje ya min kallon Tara saura quarter, ke kika sani cewar Shukura ta bar Fatima tsaye ta wuce wurin Mijinta.
A hankali take takunta cikin nutsuwa har takarasa tare da bude gaban motar ta Shiga tana dauke da sallama a bakinta, amsa Mata yayi sannan yace ya karatu?Yana Mai sakar Mata Murmushinsa Wanda ke Kara Masa kyau, Alhmdllh ta furta tare da cewa My Hero abinci ka kawo min? Dariya yayi sarkin Kwadayi ba abinda na kawo,Cike da Shagwaba ta kwabe fuska kamar zatayi kuka to kaje Ka siyo min Mana yanzu idan kana da kudi,Wai naga kamar bakayi Breakfast ba Baby? Ledar take away ya Mika Mata, ta karba cike da murna tana godiya,daya ledar ya dago Mata Kinga nawa,Murmushi ta saki tam Sweetheart ka cika cikinka dam idan na dawo Naga kaci kadan dure zan maka, dariya yayi kadan kana ya rungumeta tare da kissing din lips nata ya Mata sallama ta koma ajinsu shi kuma ya tafi,tare da Fatima suka ci abincin tas suka Sha ruwansu da lemo sannan suka koma aji, Ana tashinsu lokacin Ahleef suna tare da Farhan neman Mafita, ya Duba agogon hannunsa zumbur ya mike yace an tashi Su Honey zan dakko ta a schl,Farhan ya bude Baki sannan yace ka bari nasa Driver na ya dakko maka ita sai mu Gama maganar mu,A',a ni ban yarda ba da kaina zan dakko ta,Driver yayi min gudun ganganci da matata ba zai yuwu ba da kaina zan dakko ta,Dariya Farhan yayi yace Allah kiyaye hanya da yamma nazo gidan,Ahleef yace Allah ya kaimu yayi gaba.
Yana zuwa Already Shukura tana bakin gate tana jiransa, aiko ya dauko abarsa.
Yamma Liss Farhan yazo suna tare da Ahleef suna tattauna ya za ayi Ahleef ya samu Jari masu yawa,Farhan Yace Man kyale kudin Dad kar ya hanamu sakewa sabo da Dad shima akwai son Kudi, Gidana Na Lagos Dana Gina kasan yanzu zai kar Million dari kawai a siyar dashi kaci gaba da harkokinka,Ahleef yace no idan anyi Haka ai baka da kadarar da ta Kai wannan kudi ai kuma na takuraka,Masifa Farhan ya Shiga yi kamar zai tashi sama,To kudin Dana yi waye yamin silar samunsu idan ba Kai ba,Ni jarin nawa ka bani har na Zama abinda na Zama,Ko Dad bai min abinda kayi min ba a duniya duk abinda na Samu ta silarka ne Sannan yanzu Dan na baka Abu shine zaka min iyayi,Ni duk abinda na mallaka wlh zan iya mallaka maka shi Amma kana Fuck up,Ahleef zaiyi magana Farhan ya mike a fusace zai fita dai dai lokacin Shukura ta shigo dauke da tire na kayan Sha Dana ci, tace ah Ina zaka je Haka Kuma? Murmushi Farhan yayi mijinki ya Bata min Rai.
Murmushi Shukura tayi tace Dan kace Zaka bashi jari ko? Ya fada min jiya nace ya karba Amma karka saurareshi ka kawo kudin Ni zan karba Kuma Dole ya karba,ko ka tura min a accnt Dina zanyi maganinsa Ni da kaina,Dariya sukayi gaba daya Har Ahleef yanda Shukura tayi maganar kamar Babarsa, Farhan ya koma ya zauna tare da cewa to kaji abinda tace Mijin tace, Ahleef Yana dariya yace Totally Surrender abinda yace an Gama Yana dagawa Shukura gira daya,ta ajiye abincin ta zuba ta mikawa Ahleef nasa tace Gwauro Kuma ya zubawa kansa,Farhan yace na kusa daina zuwa gidan Nan tunda Ware Ni akeyi Ana min Gori.
Shukura tana Murmushi ta bar dakin suna ta hirarsu akan Business din da Ahleef zaiyi da kudin Farhan daya bashi.
Bayan wata daya kudin su Momi Sunyi kasa sosai ga Business baya tafiya kudi sai Bata sukeyi basa gaba,Mubaraq ya Gama tatike su kullum baya kasar Momee so take ma ta ganshi ta tambayeshi ya kudi suke Bata da Masifar yawa Haka,Amma Mubaraq Sam yaki yarda ma su San inda yake,Idan Niima ta tambayi Hafcy ko Mamansu basa fada sai suce su Basu San ma Mubaraq Yana juya musu kudi ba,Basu San inda yake ba,kudi Kuma da kadarori sai Bata suke wasu kadarorin ma suna tambaya za ace ai tuni an siyar da su.
Niima kuma sai cuta takeyi Ga Amai da tofar da yawu,Momee ta kaita asibiti aka ce ciki gareta har na 3mnths,Momee kuka sosai takeyi,Ga Latifa kullum sai Shan kwayoyi da giya tana club kullum, Women Leader ma da aka bawa Momee tuni an Kai sukar cewar ba Yar siyasa bace sabo da Haka Dole sai labari taji an tsigeta an Sa Yar siyasa.
Momee duniya ta fara Mata zafi musamman idan ta kalli Niima da Latifa sai ta zubar da Hawaye,A waya ta Kira Sultan da Suhail ta sanar musu halin da suke ciki,Sultan yace Momee lokacin da muka fada muku maganar gaskiya laifinmu ma kika gani,gashi yanzu kin Kai yaran wasu an lalata su,Kinga Dole ayiwa naki yaran,Haka Matar ya Ahleef kika Mata kazafi yanzu Kuma gashi Dole kina daukan karatun Duniya,dama idan baka ji nasihar mutane ba to duniya da kanta zata yi maka Kuma Dole ka ji nata, Momee tana Hawaye tace Ni dai kuzo a San yanda za ayi da Niima,Sultan yace wlh ba ruwanmu Kuna zubar da ciki kunyi kisan Kai again,Kuma kika Bata da danginki kaf Momee Akan abin duniya dare daya kika canja hali.
Visa Momee tayi ta nufi USA da niyyar ta karbe kudi da kadarar da Abba ya barwa Ahleef kyauta.
Tana zuwa mutumin yace bazai bayar ba sabo da Amana Abba ya bashi yace Kar ya bawa kowa kudin sai Ahleef yazo da kansa,Kuma da court din us akayi komai,tana takura Masa zaisa a daure ta,ba shiri Momee ta dawo gida ta dauki Niima zuwa asibiti Wai a cire ciki, Bayan aune aune aka gano Niima ta Gama kashe mahaifarta da Shan kwayoyin Hana daukan ciki,sabo da Haka ciki bazai zubu ba,idan aka cire to zata rasa ranta dolensu suka dawo gida suka ci gaba da rayuwa Kullum Kuma kadara da kudi suna karewa,Momee da kyar ta lallaba ta kwashe wasu kudaden masu yawa ta canja account sannan kadarar da ba a siyar ba ta siyar ta hada kan kudin kaf ta ajiye a accnt.
Ahleef Bayan kwana Hudu ya Gama dagawa Shukura kafa,kamar kullum yau da dare ya dawo gida,Shukura tana kwance a jikinsa suna kallo.
Wani mayen kallo yake binta da shi,Shukura ta tsorata gaba daya,a wayance tace Bari naje wajen Umma na karbo sako, Ahleef ya kalleta tare da cewa da Daren Nan? Wanne dare Kuma just 9:30 kace dare yayi,yanzu zan dawo pls ba musu yace alright da kansa ya mikar da ita tsaye tasa hijab tayi waje tana fita ta tsaya a Palo tana sauke numfashin tsoro tare da dafe kirji Wanda ke bugawa sabo da tsoro Tasha wahala first night yanzu Kuma taga take taken Ahleef.
Ta Dade a tsaye taki komawa sai ga Umma ta fito da niyyar zuwa kitchen zata hadawa Baba tea, Shukura tana ganinta ta buya Amma Umma ta rigada ta ganta,Muryar Umma kawai taji tace lfy ke Kuma? Dole ta fito fili tana Ina..Ina...dama..uhmm...kitchen zanje zan dafa Indomie ....au tea zan hada, Murmushi kawai Umma tayi tace to dama Nima Babanku zan hadawa zo sai na dafa daku,Shukura ba shiri tabi Bayan Umma har kitchen.
Fridge Umma ta bude ta dauko wani tsumi na mata tace ungo shanye yanzu,Shukura ta kalli abin tace Umma du kalli fa da yawa,ban son surutu na gyaran jiki ne ki shanye ki bani rubber ta,Shukura ta daga Kai ta kwankwade shi ta mikawa Umma robar, kafin Umma ta Gama dafa tea tuni magani ya fara aiki,Shukura duk taji ta Zama wet ga wata Yar Shaawa na kamata kadan taji ba Wanda take bukata sai Ahleef, ta rasa dalili,so take ma tayi sauri ta koma room dinsu,Umma na Gama dafa tea Shukura ta karba tace sai da safe Umma, to kin manta sugar din cewar Umma,da sauri ta dauki Sugar tayi gaba,Umma tace Spoon fa Baki dauka ba Wai meke damunki ne,da sauri ta Kara dawowa bula bula da Hijab dinta ta dauki spoon,Umma tace cups fa? Nan ma ba magana ta sura tayi gaba abinta.
Ahleef kuwa ya gaji da jira har ya mike zai je ya daukota sai yaga ta banko kofa bata kulashi ba tace ga tea Nan Bari nayi wanka,ta fada toilet tayi wanka da brush,tana fitowa ta shirya tana zuba kamshi cikin kayan bacci masu daukan hankali, Ahleef tunda ya Shiga yaki fitowa daga wankan da wuri,dama shi wankansa sai ya Dade sosai,Shukura taje jikin kofar tace Ni zanyi baccina Kuma idan na kwanta bazan tashi na hada ma tea ba,karma ka tasheni,Wai wayo ta hada Nan,Ahleef Bai gane ba yace no karkiyi bacci pls shugo toilet din ki jira Ni, naki Ni bazan shugo ba ta furta da Shagwaba,Yana fitowa ta zuba Masa idonta tana Kare wa halittarsa kallo tana dauke Kai Dan kar ya gano ta,Yana shiryawa yace bini muyi nafeela,Shukura tace Ni dai yau Allah bazan iya ba,bacci nake ji,sai dai kayi Kai kadai Kuma bazan jiraka ba zanyi bacci na kana tayar da sallah zanyi bacci abina, yau Sallar ma baza ki Bari ayi ba.
Ni Bari nayi tawa Ni kadai,zai tayar kenan Shukura taje tayi tsalle ta bayansa ta daneshi du ta makalkaleshi tana dariya tace Allah baza kayi ba kaima kazo ka fini samun Lada,fafur taki sauka Dole ya hakura da sallar, tea ta hada Masa ta Mika masa Yana gefen Bed ya kunna tv ya kamo tashar ball Yana kallo Yana Shan tea dinsa Shukura tayi matashi da cinyarsa, yace Bari mu kallon match din Nan sai mu kwanta ko?
Shukura tace sam wannan tsinanniyar ball za a kalla Ni bana gane me sukeyi,a rasa abinda za a kalla sai ball,wancen Dan iskan Messi din me Ido kamar na tururuwa su zamu kalla ta Danna remote ta kashe tv,ta karbe tea din dake hannun Ahleef yasha rabi kawai ta kwankwade Rabin tare cewa sai yanga kake kwanta bacci to za ayi Kuma karka tasheni, ta kwanta abinta Ahleef Yana Murmushi ya kwanta suna facing din juna,Bai taba ta ba sabo da tunaninsa zata Hana ta kama kukan da ta Saba,sai ko hugging baiyi ba Yana tunanin Taya zai bullo Mata,Shukura ta kashe light tare da rufe Ido Wai tayi bacci ita, a hankali Ahleef ya dawo da ita jikinsa sai ko yaga ta Kara makaleshi Bata ce komai ba, gashinta me tsayi da santsi ya warware ya nutsa yatsunsa ciki Yana shafa Mata a hankali cikin salon kwarewa.
Shukura idonta ta lumshe da kanta ta fara kissing dinsa tun tanayin kadan ta koma so Deep,sai Rada take Masa a kunne tana Masa wasanni a kunne da harshenta,Ahleef ya rude Basu San sanda suka zarewa juna Kaya ba,kowannensu cikin kwarewa da salon bajinta yake sarrafa Dan uwansa suna jiyar da juna dadi,sosai Shukura ta ba da hadin Kai duk da yauma taji zafi Amma ba sosai ba, Ahleef yau sabo da sweet din Shukura sai da yayi hawayen dadi,Hawaye sosai, Bayan sun tsarkake jikinsu bacci me karfi ya kwashesu, 2:30am Ahleef ya farka da Jarabarsa sallar dare ya Saba Yana yi tare da Shukura Amma wannan karon Yana tashinta yace yau ba sunnar Nafeela za ayi ba, Shukura da Tasha tsumin Umma Haka ta bada hadin Kai suka Kara darje juna, da Asuba ma Haka suka sake sabo Shukura tana Jin zafi Amma sabo da maita mukus takeyi Bata kin yarda sai dai tana cin uban gashi kamar zata Kone wajen da ruwan zafi,Ahleef kuwa kawai kwasar harkoki yake abinsa, ranar ko schl Shukura Bata je ba,Kuma tunda suka fito suka gaida Umma da Baba suka koma dakinsu abinci ma sai dai Ahleef yaje ya ebo musu ya dawo, a room suka yini sai yamma Bayan Sallar laasar suka fito,Baba sai fada yakewa Ahleef yau Bai samu jam'i ba ko daya, Shukura tace ai yanzu Baba zaije Magrib da Isha dazu ma kansa ne yake ta ciwo tun jiya sai yanzu yaji sauki,Baba yace Kash Allah ya sawwake kasha magani ko asibiti zaka je? Ido suka hada da Shukura suka yiwa juna signa sannan yace ai dazu Naga maganin a jakata na Sha shine ma na Samu sauki, Shukura tace da har zanzo na fada muku Baba yace Wai kar na fada tun jiya yasha wahala gaskiya,Umma ita kanta ta yarda da Shukura tace idan ba sakarci irin naku ba mutum ya kwana Yana ciwon Kai baza ki fada ba,Dazu kazo ka ebi abinci safe da Rana wa yaci?
Ahleef yace tun jiya take ta faman kuka sabo da ina ciwon Kai taki cin komai shine Dana ji sauki sauki nazo na ebar mata, Umma tace eyya to Allah bada lfy, Suka ce Ameen,Ahleef yace Bari zanje wurin Farhan anjima zan dawo,Hannun Shukura ya kamo yace ko Zaki je? Umma tace ba inda zata je jiya kunce bakuyi bacci ba kana cuta yanzu ai gwara ta huta,Shukura tace Umma Dan Allah zanje pls Kinga fa na Dade ban fita ba,Ke da idonki tunda Zaki iya sai kuje,da sauri taje ta shirya cikin wani arnen lace dinta milk da ratsin Orange takalmi da jaka tare da mayafi Orange tayi Masifar kyau, Ahleef kuwa cikin Milk shadda me tsada Tasha dinkin zamani na Matasa Yan gayu, sai kamshi sukeyi suka yiwa su Baba sallama suka fita hannunsu rike da juna,Ahleef yace dama ba wajen Farhan zanje bafa yawo zamuyi a kafa muga unguwar Nan, Umma idan ta sani maybe tace baza kije ba,Shukura tace Amma naji dadi, weather me dadi suna tafiya a hankali suna hirarsu ta masoya suna kwasar fresh air abinsu dake Abuja ne ba ruwan wani da wani kowa ya gansu sai sun birge, suna shaukinsu Sai ga Farhan da mota zaije gidansu ya wuce ya dawo baya tare da sauke Glass kasa Yana dariya yace Allah ya shiryeka Dan Iska, hannu Ahleef ya Mika Masa suka tafa,Shukura ma ta gaidashi,yace to kuzo mu koma dama gidanku zanje,Ahleef yace wlh baza mu koma ba sai dai kaje ka jira mu a gida sai sanda muka dawo ko ka tafi gobe ka dawo ko Nazo amma baka Isa mun koma ba,yawo muka fito da Honey,Farhan yace zaka sani ne Nima wlh indai nayi aure sai na Rama suna dariya yaja mota ya tafi gidan su Ahleef,Umma da Baba basusan a kafa suka fita yawo ba sai Farhan ne ya tona su.
Wata sabuwa Bayan kwananki kadan Ciwon Koda me tsanani ya kama Momee,kullum suna hanyar asibiti Ana cinye wannan dukiya,samari da wasu Yan film tare da karuwai sunga Momee kudi Babu ga ciwo ya kamata suka zare jikinsu ko dubiya ba wacce ta leko,Haka dangin Momee sunji labari Amma ko leke,Niima tayi kuka har ta godewa Allah,Latifa kuwa ba ruwanta kullum tana yawonta,Niima da katon ciki Haka take kula da Momee,Yan aiki duk Babu sun arce, Ahleef kuwa bai da labari sabo da tunda ya tafi bai sake leko su ba
Bayan wasu watanni Ahleef Alhmdllh ya sake Zama wani Hamshakin me kudi na gasken gaske,Haka Allah yayi shi komai ya taba sai yayi albarka, tuni ya Gina musu rantsatsen gidan da Babu irinsa, Kuma gidan da Farhan ya siyar ya bashi tuni yaje ya siyawa Farhan Wanda ya fishi kyauta, yanzu duk inda Ahleef yake sai kaga Shukura a gefensa yawancin meeting ko wani abu da ita yake zuwa,Kuma duk takardun da zai cike Yana rubuta ta a Itace magajiyarsa Next of kin, Shukura ta Kara wani wayewa ta goge sosai,sun kusa zana waec da Neco, Ana yawan Nuna Ahleef a gidan Tv ko radio yanda yake bawa kasa gudun mawa Yana taimakawa Marasa karfi.
Bayan Shukura sun gama ssce exam Visa Ahleef yayiwa Shukura tare da shi zuwa London,Umma da Baba Kuma ya biya misu Saudiya, Bai San wanne Hali su Momee ke ciki ba suka dage zuwa London,Suna cikin jirgi Shukura ta lafe a jikinsa tana bacci abinta cikin kwanciyar hankali sai wani lallabata Ahleef keyi,da dare misalin 8pm suka Isa London,mota suka shiga zuwa masaukinsu wani katafaren Hotel,tun a taxi Ahleef ya tsaya yasiyawa Shukura Lemo me shegen dadi da wani snacks, Shukura tunda suka sauka taji Niima a garin ga wani dadin sanyi,kasa kamar aljannar duniya,tana kora lemo tace My Hero Allah wadai da halin shugabanninmu ,dariya Ahleef ya dingayi yace Babu kyau fa zagin shugaba kin sani,me suka Miki? Shukura ta Kara daga lemo ta zuka sannan tace Nigeria baza mu taba ci gaba ba har Kiyama ta tsaya,gamu da kudi Amma gaba daya da shugaban nin da mu Yan kasar Babu na gari sai dai dai,yanzu jibi kasar Nan kamshinta ma daban ne,kalli Amma mu sai dai a sace kudin kasar,na kasa ma ko tallafi shugaba ya bada a raba kafin yazo hannun talakawa duk sun cinye kudin.
Ahleef ya kafeta da kallo tana ta ciye ciyenta Yana Kara Jin wani sonta da shaawarta na ratsashi, ba tare da ta kalleshi ba tace kallonfa na mene,rungumeta yayi a jikinsa gaba daya tare da Rada Mata I Love u Honey, Murmushi ta saki tace me too Sweety.
Suna zuwa Hotel dama tuni ya musu booking da karamar trolley dinsu suka wuce ciki.
Momee kwance a gadon asibiti Niima da Dan karamin cikinta tana aikin jinya sai masifa take zazzagawa Momee, Dan Allah Momee Ni ki karbi magani Kisha sai wahalar Dani kike duk kokarin da nake Bakya gani,Hawaye ya zubowa Momee tace Wai Ni kikewa tsawa Haka Niima? Cikin radadin ciwo Hawaye ya zubo wa Momee,da kyar tace Ina...na...na....Latifa?
Tsaki Niima taja kadan sannan tace tana yawon iskancinta can ai kin sani, Momee da kyar tace Ina zamana lfy na lalata halina,na dauki mutanen banza na cusasu a jikina,gashi yanzu ko arzikin dubiya ban samu ba,Maman su Hafcy ma Wai itace ta kasa ko leko Ni sabo da yanzu bamu da kudi,Niima tace sai yanzu nake Nadama Momee Dana ki aurar Ahleef,ga kyau,ga Kudi,ga kyan Hali,karshe naje naso Mubaraq Wanda shine ya lalata min rayuwata Niima ta fashe da kuka tare da durkushewa a kasa tana na cuci kaina,kema Momee duk ke kika jawo mana.
Momee dake saman Bed ta zuro hannu ta zubawa Niima rankwashi tare da cewa ke dai kika cuci kanki marar mutunci ,Latifa ce ta shugo ta dawo daga yawonta ta iske su Niima da Momee kowannensu Yana Hawaye cike da Nadama,Itama tsugunawa tayi a wajen ta fara kalar nata kukan tace Momee kece du kika jawo Mana,Momee tace Dan ubanki wacce tarbiya ce ban baku ba? Ai sai daga baya shedan ya rudeni na canja hali akan son duniya,yanzu sai mu fara istigifari ko Allah ya taimakemu,su Momee yau sunyi Nadama,sunji karatun Duniya Dole uwar naki,Nan take suka fara istigifari suna tuba,Baji ba gani,Niima tace sai mu nemi Ahleef ya yafe Mana,Latifa tace shegiya bariki gashi da kaina naji wahala na tuba,Allah dai ya karbi tubanmu,Shukura ma munyi Mata kazafi,Momee kinyi silar lalacewar dubban alumma shi yasa Allah ya Rama musu akan yaranki,nayi shaye shaye da duniyanci Ina karamata,ga Niima itama an Rama akanta tayi ciki,da Baki sa an lalata yaran wasu ba wlh da muma Allah bazai Bari mu lalace ba,ga kudin gado duk ya Kare yanzu ko kin warke bamu San ya zamu Kare da talauci ba, naje Neman Ahleef wajen Farhan yace ai Ahleef yayi kudin da yafi na da,Kuma ya dauki Matarsa sun koma London,Haka Su Umma Saudatu basa kasar,nayi nayi ya bani number din Ahleef wlh yaki bani..yanzu Kuma talauci ne kawai zamu karba a jikinmu matukar Ahleef Bai zo ba, Niima da sauri tace wlh rannan a tv Naga Ana nuna shi tare da Shukura Kinga yanda suka dawo kuwa kamar turawa nayiwa kaina nayi asara,duk nice na dinga zuga Umma har na cusa Mata kiyayyar Ahleef,gashi mun kwace dukiyar da take halak dinsa har mukace ya daina zuwa gidanmu,gashi Allah yayoshi ba talaka ba ya sake yin new Money.
Momee tace to a Ina ya samu kudin da zai juya? Latifa tace hanyar Allah ko Kuma Farhan ne,Niima tace Allah ya nuna Mana Ahleef na bashi hakuri sannan Kuma na Masa tayin kaina ko zai aureni,wlh sai yanzu naji sonsa Yana ratsani,Dan Allah Momee idan ya dawo ki nemi Alfarma ko zai aureni Bayan na haihu ya Kara ta biyu Dani,kin San Yana jin kunyarki Kuma Yana sonki,baya manta alkhairi idan kin Sa Baki da wuri zai aureni.
Momee tace Allah yasa zanfi kowa farin ciki.
Latifa tace Ni Kuma Farhan nake so Momee,Momee tayi Dan Murmushi tace Allah nuna Mana zan nema muku Alfarma.
Latifa da Niima su sukaci gaba da kula da Momee da Dan ragowar kudin da ya rage musu,har aka samu akayiwa Momee aiki aka cire Mata Koda daya data lalace sannan ta samu sauki sosai sun Dade a asibiti har ta warke sannan aka sallamesu ammafa kudinsu sun Kare karaf sabo da Mubaraq ya Gama kwashe komai ya bar kasar abinsa ba a San inda yake ba.
Mama dasu Hafcy ma kansu Mubaraq ya gujesu Basu San inda yake ba,duk murnar da suke zasu Shana da kudi a banza domin ya gujesu,Alhj Adamu Bai San komai ba sai aikin neman Mubaraq yake, Mama Sai kuka kullum danta ya bace, Su Hafcy kuwa sai tsinewa Mubaraq sukeyi yayi kudi ya gujesu sun taimaka Masa Amma karshe abinda ya musu kenan, Momee bayan ta warke report ta kaiwa Yan sanda Mubaraq ya gudu da kudinsu,su kansu Yan sanda ganin ba wata sheda kwakwara sannan Momee Basu da kudi sai suka share Zancen kawai suka sallamesu bayan Dan karamin bincike da sukayi.
A kwana a tashi yau abincin da su Momee zasu ci gagararsu yakeyi sun tsiyace sai katon gida ba ko sisi a ciki, Momee tace Dole mu saida wannan gida mu koma cikin talakawa mu siyi karami ko zamu samu na cin abincin,Momee suka daga tallan gida ba Wanda ya Taya,sai Momee ce da kanta taje wajen Farhan kan ya taimakesu ya samo musu Mai siyan gidan,Nan take Farhan ya bugawa Hamshakin me kudi waya ya siyi gidan su Momee suka siyi karami can unguwar talakawa suka zauna,sauran kudin kuma suka siyi kayan abinci etc.
London
Ahleef suna Bedroom dinsu ko hutawa basuyi ba ya cirewa Shukura kayanta tare da nasa suka Shiga wanka, damunta yayi da tabe tabe tare da tsotsar inda yaga dama, ganin ya fara susucewa cike da Shagwaba tace pls ka Bari sai dare Mana kamar zata narke Haka tayi maganar, wani nataccen kallon so yake aika Mata, a hankali ta rungumeshi tana me bashi hakuri sai dare can,kafada ya makale shi bai yarda ba sam,Dole ta hakura taba da amanna suka farantawa juna rai sannan sukayi wanka suka fito da kanta ta shirya sannan ta shirya Ahleef dinta tana Gama taje Masa gashi tace to oya karbo Mana abinci yunwa nake ji, fita yayi Yana tsokanarta Wai ciki gareta tunda yanzu tafi cin abinci.
15mns ya dawo dauke da ledoji Niki Niki,da sauri Shukura tace sannu da zuwa ta karbi kayan tana wani farin ciki kamar yau ta sanshi, abinci ya siyo musu da Kuma kayan sawa hadaddun gaske,Shukura sai Murna takeyi tace Allah ya Kara budi, Ameen yace Yana kashe Mata Ido daya, Hero gaskiya Ni ka daina min irin kallon Nan nafa San me kake nufi, ta furta cikin tsantsar shagwaba, da sangarta tana cuno Masa Dan bakinta,wani birgeshi takeyi idan tana Shagwabarta har cikin jininsa yake Jin wani yarrr..
Murmushi ya saki me kayatarwa kana ya jawota jikinsa ta Fado saman cinyarsa zuwa kirjinsa Fuskarta ta dago tana kallonsa sannan tana Wasa da yatsunsa, Harshensa taji cikin bakinta a nutse Yana tsotsa kamar alawa baya gajiya da Shukuransa,ga Tsafta tana kula da jikinta sosai ko ina kamshi zaka ji,itama a ranta tana mamakin Tsafta da gayu irin na Ahleef kullum neat ko wacce gaba ta jikinsa kamshi take lungu da sako, ci gaba yayi da Shafarta ba tare da Bata lokaci ba Shukura ta rude jikinta Yana rawa daukan ta yayi zuwa saman bed Wasa ya canja salo sai da suka Raya sunna abinsu,Bayan sun samu nutsuwar,Ahleef ya kankameta a jikinsa kamar za a kwace Masa ita ya furta kullum Honey sweet kike karawa, you are too sweet har ban San me zan ce ba, Fuskarta ta fara goga Masa a tasa cikin kunnensa tace Kaine kake bani abinci da yawa Ina cinyewa yanzu zaka kaga na haihu ai ance idan mutum Yana ci Yana koshi ba yunwa a gidan mijinta to yanzu zan ta sullubo yara.
Dariya ta kama Ahleef sosai Yana ta yi Yana Kara kankame Shukuransa yace ai ban sani ba dama haka abin yake? Da sauri Shukura ta ae kwarai to Alhaji gidanka ba yunwa ni Naga na Dade ma kamata yayi ace na haihu tuni,Ahleef ya Kara kyalkyalewa da dariya, fushi tayi ta turo Baki Wai sai dariya kake min na daina kulaka ma sakar min jiki tunda Haka kake,sorry Bae na daina kin kusa Haihuwa saura kadan ai mace kike so ko Namiji? tab me zanyi da Namiji nafi son mace Yar yarinya ta na dinga Mata lalle da kitso,idan ta girma na dinga aikenta,tana min girki da aikin gida, na daka Mata tsawa nace je ki gyara room din Dad Hero Dina,Ahleef Yana dariya kasa kasa yace to Yar taki Zaki cewa Hero dinkin a gabanta ba kunya,Kai nifa ba ruwa na da wata kunya Baturiya ce ni,gidan turawa ne mu ba ruwanmu ko? Ahleef yace gaskiya gidan Yan gayu ma kuwa,Shukura tace da su Momee Basu raba mu ba ai da tuni na haihu,Amma na koma kauye yunwa zata karasani Taya zan haihu da wuri kuwa, Me gari da Matarsa sun Gama azabtar Dani, Wai Ni yake so in baka lbr ya dinga kallona idonsa kamar na aljanu, Ahleef Nan take ya Bata rai, kishinsa ya motsa yace kyale maganar karki jawo nasa a kamo min Me gari na kaishi prison.
Murmushi tayi tare da furta calm down Hero,abinci ya jawo suka ci tare abinsu Yana Bata a Baki da kansa tana ta bashi dariya da hirar kuruciyar ta, Bayan sun Gama, shiri sukayi sun dau wanka kamar baza a mutu ba suka fita yawon zaga gari abinsu gwanin Sha'awa da birgewa.
Ayi min hakuri Fans wannan Novel din bana bada page da wuri wasu Abubuwa ne suka rikeni in busy ne sosai,Dan Allah kuyi min hakuri da afwa da kyar nake samun time na typing.
AsmaBaffa
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
71-75
Official
By
AsmaBaffa
Ahleef Yan London sun kwashe 2wks a garin suna zuba amarci kafin suka tafi Russia sun kwashe 1wk sannan suka wuce Saudi nan suka Iske Baba da Umma Sunyi Ibada sosai,sai kyau da haske da suka Kara tare da Yar kiba kowa ya gansu yasan suna Jin dadi,Shukura tana ta siyayya Ahleef Yana kashe Mata kudi sai abinda take so, Bayan sun Gama aikin hajji Su Umma suka dage zuwa Nigeria,Ahleef kuwa Shukura ya dauka suka wuce Dubai abinsu, Baba da Umma suna hutawa suka tafi Niger a jirgi wurin dangin Baba sada zumunci,can ma Sunyi Mamakin ganin Baba,domin tunaninsu baya Raye sai gashi ya kawo Musu ziyara tare da kyautuka na alheri, sunji dadi sannan Ya Basu labari dansa Ahleef, satinsu biyu sannan suka dawo Abuja cike da murnar ganin Yan Uwa.
Bayan 3weaks Su Shukura jirginsu ya sauka a Nigeria,Murna take faman yi zata ga su Umma, escort din Ahleef ne suka dauko su daga Airport zuwa gida, Umma da Baba ma murna suke sosai da dawowar yaran nasu,Shukura jikin Umma ta lafe sun Dade suna Hira har Ahleef tare da cin abincin Umma me Dan Karan dadi sannan suka wuce hadadden part dinsu cike da kaunar juna.
Niima ciki ya Kara girma sai fama take da laulayi, Momee kullum sai ta zubar da hawaye musamman yanzu da suke cikin talauci kudi ya Kare karaf,abincin da suka siya ma sun cinye Babu sai kadan,kudin cefane Babu shi kullum shinkafa fara da Mai suke ci abinda ya rage musu kenan, tuni suka daina girki da Gas sai itace ko coal,kamar kullum yau sun tashi sisi babu ko na Koko Basu samu ba sai taliya suka dafa suka ci da Mai,duk sun rame Sunyi Baki lalacewar tayi yawa ma,Babu Wanda yake taimaka musu,tunaninsu don sun tuba ga Allah shike Nan baza a jarab cesu ba sai gashi sunga ba Haka bane, wahalar tayi musu yawa yau Momee da kanta ta shirya tace Niima ku kula da gidan Bari naje wajen Farhan ko zan samu tallafi,Latifa tace Allah yasa a Dace Amma da na biki ko zanga Farhan naji sanyi, Momee tace to zo mu tafi,a gurguje ta gyara Fuskarta tare da yafa mayafi tabi Momee suka Shiga Napep suka nufi gidan Su Farhan.
Suna Shiga lokacin Farhan ya fito yaci wanka zai fita,Yayi mamakin ganin Momee da kanta,ya kallesu duk yaga sun lalace sun fita daga hayyacinsu da gani suna cikin wahala.
da sauri ya Isa wajen Momee tare da gaishe ta kamar yanda ya Saba, ta amsa fuska cike da annuri sannan ta fara karanto Masa matsalarsu ta Kara bashi hakuri sannan tace Dan Allah ka hadani da Ahleef ko ba komai zamu roki gafararsa tare da Matarsa.
Farhan ya tabbatar su Momee Sunyi Nadama,Latifa tana gefe ta wani rakube a bango kamar munafuka sai kallon Farhan take ba ko kyafta ido, Farhan Yana kallonta ya lura da abinda take suna hada Ido ya zabga Mata Harara tare da Jan tsuka kadan ya turo Dan lips dinsa gaba kamar yanda Mata sukeyi,Latifa tana gani sai ko ta bangale da dariya tana yaye Baki, fuska ya Kara tamkewa.
Farhan Yana kokarin bawa Momee Number din Ahleef sai ga Ahleef tare da escort dinsa sun shigo da motoci gidan,Momee Baki ta bude ganin motocin da Bata taba gani ba masu shegen kyau da tsada,Latifa kuwa ta ma manta a Ina take kamar Yar kauye Haka tabi motocin da kallo.
Da sauri suka budewa Ahleef mota ya fito cikin Shiga ta alfarma,tuni kamshi ya cika gidan,Yana fitowa ya Mika hannu tare da fito da Shukuransa cikin rantsatsiyar Shiga kamar zasu je gidan shugaban kasa,sun wani Kara ja da kyau,Momee da kyar ta ganesu,Haka Latifa ma Baki bude take kallonsu,Ahleef kuwa Bai kula dasu ba tunaninsa Yan maula ne.
Momee da sauri tace Dana Ahleef, Latifa tace ya Ahleef da karfi, Jin Muryar da ya sani da sauri ya juyo kallo daya ya ganesu, kafin yayi wani taku Momee tazo ta durkusa tana bashi hakuri harda kuka, Latifa ma Haka, Nan Momee ta fara bashi labarin duk halin da suke ciki da abinda Mubaraq ya musu etc.
Ahleef yace ba komai Momee Ni baku min komai ba Allah yafe Mana Baki daya,Shukura tana gefen Ahleef ta kankameshi Haka ta gaida Momee a ladabce, Momee ta kalleta da Faraa sannan tace ki yafe Mana Shukura mun zalunce ku,Shukura ta kalli Ahleef sannan tace Ni dama na yafe muku tuni ban rikeku a Raina ba,Ahleef yace kije Gida Momee zanzo anjima,Latifa tayi sauri ta bashi address din gidan da suke sannan suka tafi gida gwanin tausayi,har Sunyi Nisa Shukura tace kasa a kaisu gida a motarka,Nan ya bada Umarni driver dinsa daya yaja mota ya dauki su Momee ya maidasu gida,sai murna suke tare da bawa Niima labari itama sai dadi take ji zai aureta kwana Nan.
Shukura wurin Maman Farhan ta wuce,Ahleef Kuma ya tsaya tare da abokinsa suna tattauna magana kan su Momee, Farhan ya bashi labarin halin da suke ciki, Kuma gidan Dana maka waya ka siya shine nasu Momee, Ahleef ya tausaya musu kuma yasha mamakin karewar dukiya me tarin yawa Haka.haka Hukuncin Allah yake ko nawa ka Tara a duniya sai Allah yaso zasu zauna,komai kudin mutum idan Allah yaso ka talauce Dole su Kare Babu abinda ya gagari Allah har kaji mutane suna ai wane shi da talauci har abada,sai idan Allah baiga dama ba.
Wurin magrib Shukura tana wajen Maman Farhan tare sukayi girki suna hira,Mama tana Kara koya Mata dabarun rike me gida da yanda zata gyara kanta sosai,wasu Tsumin ta bawa Shukura iri iri da yanda zata dinga amfani dasu,har sukayi Sallar Isha Ahleef Bai dawo ba sun fita tare da Farhan.
Faskekiyar wayarta Shukura ta dauka tare da Kiran Ahleef, bugu daya ya dauka can kitchen ta shige sabo da tana kunyar Maman Farhan, kashe murya tayi tare da narkewa a hankali tana Shagwaba tace My Hero na gaji kazo mu tafi gida pls, wani yarrr yaji jikinsa ya amsa sabo da yanda tayi maganar,cike da so yace sorry Honey I wll be on my way soon, minti nawa zan baka? 10mnt Zaki ganni ok? Kai ta daga kamar Yana ganinta sannan tace to Allah kawo min Kai lfy sannan ta kashe wayar,har tazo bakin kofa zata bar kitchen din,Ahleef ya kirata back,ta daga taji me zai ce, tana dagawa yace na manta ban fada Miki ba? Tace mene fa? Albishirinki? Tace goro Fari Kar,tana jira taji sai yace I LOVE U SO MUCH, wani sanyi da sonsa ya Kara ratsata tayi Murmushi cike da farin ciki tace Love u much more, u are my World and u make me complete, sannan ya kashe wayar,sai ta sake kiransa again yayi picking tace missed u missed ur everything,Ur hand fit in mine just wanna sleep on ur chest sweety, Honey Zaki sa na kasa driving kina kashe min jiki, dariya sukayi gaba daya,Farhan Yana gefe Yana jinsa lokacin Kuma Niima da Dan cikinta tirtsitsi tana motar zasu kaita gidansu, su Momee tuni Ahleef ya musu kyautar gidansu back dama shi ya siye gidan.
Niima kamar tayi kuka taga yanda Ahleef suke ta diga love da Shukura baya kallon ko wacce mace sai Shukura, a ranta taji tsanar Shukura marar adadi ta kamata,Latifa da Umma su tuni Driver ya maidasu gidansu tare da kayansu.
Bayan sun ajiye Niima a kofar gidan suka juya sai gidan su Farhan,Maman Farhan tana mamakin Shukura yanda ta kasa zaune ta kasa tsaye ita mijinta ta Matsu ta gani kusa da ita, Dan yanzu Shukura tafi sabawa da Ahleef ko yini cikakke Bata iyawa ba tare da ta ganshi ba.
Tana Jin karar motar ta yafa gyalenta, sai gasu sun shigo,Maman Farhan tace Kun dawo kenan, wannan duk ta kasa sakewa baka Nan,Murmushi Ahleef yayi Yana kallon Shukura ta kasan Ido, a fili yace Haka takeyi ai da a Office nake ma da tuni taje, Farhan yace ki daina yarda Mama munafuki ne shima shine Dan anace Baya iya yini sai yasa an daukota, dariya Mama tayi tace to Dan sa Ido,Shukura tayi luf Wai kunya takeji,kallonta Ahleef yayi tare da cewa tashi mu wuce Madam,ta kwashi kayanta da Mama ta Bata sukayi musu sallama sannan suka fita,Shukura tace Ina escorts? Na sallamesu Ni zanyi Driving idan Kuma kina bukatarsu ranki ya Dade sai a kirasu sai abinda kike so, hararar Wasa ta watsa Masa suna nishadi suka wuce gida.
Suna Isa gida Umma tace Kun Dade yau,Ahleef da Shukura suka nemi wuri suka zauna a Palon Umma, Baba ma Yana nan, Ahleef ya kwashe komai da ya sani game dasu Momee ya sanar dasu sannan yace Umma yanzu Niima tana Nan da cikinta, gidan ma Allah yasa Ni na siya yanzu na bar musu shi kyauta,sannan kudin da Abba ya bani Wanda suke Usa an hanasu to nayi waya dasu nace a Basu na bar musu kyauta tunda Allah yasa sun iya business tun farko suja jari su juya kudin suna Samun na cin abinci,Sannan Niima Na Sa za a Bata aikin Gomnati su dinga yi tunda Ina da hanya Kinga ya Isa su rike kansu, Sai Latifa a nema Mata University taci gaba.
Albarka su Baba da Umma suka dinga sawa Ahleef yayi kokari da wani ne manta alkhairi zaiyi yaki tallafa musu, Ba komai Umma ai ko ba komai Momee uwata ce,ta rikeni Amana da Abba ko sabo da wannan ai bazan watsar dasu ba,har abada Ina ganin mutuncinta,dama Niima da Latifa sune suka Bata komai to Suma ga inda ta Kare musu. Allah ya kyauta yanzu idan Niima ta haihu sai Kuma tayi aure idan taga zatayi cewar Umma, Ahleef yace ai Momee tace aurarsu zatayi Baki daya Bayan ta haihu tayi istibrai, Farhan ma ya samu matar da zai aura Fatima kawar Shukura ce schl dinsu daya,Amma Wai wajen babansu yaje Kai Masa sako anan ya ganta,manya har sun Shiga zancen,Shukura ta kwalla ihun murna tace Fatima tawa dai Dana sani? Ahleef yace ae itace,yau Munje wajenta kawai naga Ashe itace ma, Umma tace Alhmdllh, Baba ma Haka yace Kinga kawa da kawa ga aboki da aboki,dariya sukayi Baki daya,Shukura sai murna take.
Umma tace Amma zaka dinga zuwa wajen Momee din taka kana gaisheta kamar da,Ae Mana, tace zata zo Wai har gida ta baku hakuri ma, sannan Niima zata zo Wai tayi sati daya anan gidan sabo da karfafa Zumunci,Umma tace Wlh mu ba komai mun yafe tuni ai.
Nan take Shukura ta hade fuska tunowa da tayi ai Tsohuwar budurwar Ahleef ce zai iya komawa yaso Abarsa,Kuma ance indai son farko ne ba a mantawa ko mutum ya tsufa soyayya zata iya tashi.
Kishi ya kama Shukura ta kasa Control a fusace ta mike ta nufi part dinsu,mamaki ya kama Umma da Ahleef,Baba Murmushin manya yayi yaje gano tuni,yace jeka Ahleef matar taka fa tayi fushi,Ahleef yace to me akayi Mata,Umma tace jeka wlh ka lallasar min yarinya ta.
Hankalin Ahleef ya tashi Shukura tayi fushi Bai San me akayi Mata ba,da sauri yabi bayanta,tun kafin ta Isa part dinsu ta fara rusa kuka, bedroom dinta ta shige tare da Sa key ta zauna dabar a kasa irin zaman Yan bori tana ta kukanta,Ahleef ya karaso da sauri ya Murda Handle Amma kofa Gam Gam,yace ki bude me ya faru,ko Baki da lfy Dan Allah ki bude Honey duk ya tashi hankalinsa.
Taki yin magana Kuma Bata bude ba kukanta take rerawa, magiya da rokonta ya Shiga yi idan baza ki bude ba to ki fada min me yake faruwa? tana shesheka tace Bayan kishiya kace zaka yi min, Ahleef Baki bude yace Ni din? Yaushe nace Haka? Yana mamaki tace ae ai Naga take takenka kuma wlh Allah indai kace Haka Ni Kuma sai ka sake Ni,Haka kawai za a kawo min jaraba gida a Jaja min cuta,Dariya ma abin ya bawa Ahleef Bai gane kan Zancen ba, yace Wai meke damun kanki ne? Ae kace Haka Mana ka zageni kaji dadi ai Dole kace min Haka tunda kaga wacce ta fini Kuma wlh baza ka dauko cuta a jikinta ka shafa min ba.
Salati Ahleef yaja shi bai San kan zancenta ba,tace idan shegiyar Nan tazo part dina wlh Allah da Kai da ita sai na yanka ku, Ahleef sai yanzu ya gane Niima take nufi ya Shiga sheka dariya yace to bude dai ki fito muyi zancen, da kyar ya roketa ta bude tare da fitowa, yasha mamaki ganin Fuskarta kamar an watsa mata yaji tayi jajir ga Hawaye ta ko Ina duk ac din dake gidan ta hada zufa.
Hannunta ya ruko ke yanzu Akan wata Niima kika Bata fuskarki Haka? Hawaye ya Kara shararo Mata tace gashi Nan yanda kake fadar sunan ma da dadi kake tsarawa kace NIIMA Mana Amma sai kayi iyayi kasa kalkala,Ahleef ya danne dariyarsa ya kumbura murya da Bakinsa yace to NI'IMA tace ai dai baka birgeni ba Tunda sai Dana fada kayi,yace muje nayi Miki wanka jiba yanda kike zufa Akan kishin banza,ai kinfi karfin kiyi kishi da Niima kucaka,Dariya Shukura tayi tana share Hawaye Wai taji dadi yace Mata kucaka.
Ya zura Mata Ido ya hango yanda take murna,Murmushi yayi tare da daura ta a cinyarsa yace to me zanci da wata Niima me katon goshi Bayan ga Shukura Balarabiya,Shukura ta Kara wani shigewa jikinsa tana Jin dadi Yana ta kushe Niima itace a sama, yace Shugabar Matana na aljanna Hurul ein,a aljanna ma sai abinda kika ce, Shukura tayi dariya tace Idan na Shiga Aljanna shuuma zan zama,Ahleef ya fara dariya,tace kasurgumar Yar giya zan Zama a aljanna kullum Nasha nayi tatul, Dariya Shidai Ahleef kawai yake na labarin Shukura sai da ya gaji sannan ya dauketa sukayi wanka suka kwanta suna hirarsu ta masoya bacci ya kwashesu me dadi.
Bayan sati biyu su Momee komai ya Dan fara gyaruwa suna Dan Jin dadi komai ya fara zamar musu Normal Ahleef ya gama musu komai Kuma Yana zuwa akan lokaci, yaune Kuma Niima ta hada kayanta ta nufi unguwar su Ahleef, da kyar masu gadi suka barta ta Shiga sai da ta Kira Ahleef a waya sannan ta samu aka bude Mata kofa, wani maaikaci ne ya rakata part din Shukura,Ahleef Yana Office Amma ya kusa dawowa Shukura tana Bed room ta Gama tsantsara masa girke girke masu dadi, tayi wanka tana tsane ruwan jikinta taji Sallamar Niima, Jin mace ce sai ta sakko daga sama daure da guntun Towel Fari ga karami a hannunta tana tsane ruwan gashinta, lekowa ta fara yi kadan ta hango Niima zaune, karasa sakkowa tayi tana tamke fuska Amma ta danne kishinta da Faraa ta tarbeta suka gaisa, Niima sai kishi take na Shukura tana wani Shan kamshi,Shukura ta Dan zauna kadan sannan ta kawo Mata kayan ci Dana sha.
Tana zuba Mata juice Ahleef ya Danna Door bell ya dawo, cike da Shauki tace Hero ne? Yace yeah Honey I'm Back, kofar ta bude a hankali cikin takunta na Jan hankali, Bai San anyi bakuwa ba ya daga Shukura sama tana Masa Oyoyo ajiyeta yayi tare da rungumeta a jikinsa suka fara kissing din juna sunkai 5mnt sannan Shukura tace muje ciki Mine.
Zai zame Mata towel tace akwai fa bakuwa a Palon Nan baka ganta ba,sai lokacin yayi tozali da Niima tana kallonsu kamar Mayya ko kyafta ido Bata yi,kishi ji take kamar ta kashe Shukura ta huta.
Da kyar ta iya gaida Ahleef,ba tare da ya kalleta ba ya amsa sannan ba kunya ya tsuguna yace Honey hau muje ki min wanka, bayansa Shukura ta haye kamar yarinyar yaye tana Wasa da gashinsa tana cewa Unique I love u, ta juyo ta kalli Niima dake Shirin kuka sabo da kishi, Shukura tace Bari mu sakko pls baza mu Dade ba wanka kawai zan masa.
Niima kanta ta dauke gefe tare da goge kwalla a boye su kuwa tuni ma sun bace Basu San tanayi ba,Niima tana Palon tun tana sa ran ganin zasu sakko Shuru kamar an shuka dusa, saida suka Gama Raya sunna sannan suka sake wanka tare da shiri ka rantse party zasu je suka sakko kasa, Allah sarki Niima sai gyangyadi take yi bakinta cike da yawu na laulayi HHH.
Ahleef ya kalleta kadan baya Jin tausayinta ko kadan gashi ta Sa Yar Jakarta a gaba, Shukura tace sannu mun barki kina jira, Baki cike da yawu Sautin maganarta baya fita sosai tace Bha..Bha...komai,Bhani...yedha( Leda) idan kina dha yita(ita) Shukura tace ai yawu Zaki Tara a ciki? Niima ta daga kai, No Ni Mijina abinci zai ci tsakani da Allah kyankyami gareshi bazai iya cin abinci Yana hangoki kina Tara yawu a Leda ba,Ina laifin ki na Shiga toilet, tsaya a raka ki wajen Umma ita zata Miki dabarunsu na Mata sai kiga yawun ma ya daina taruwa.
Ahleef waya yake dannawa baice komai ba, Shukura ta Kira Me aiki tace Barira kaita wajen Umma,Niima tace ai Ni a Nan zan zauna ba wajen Umma nazo ba,Harara Ahleef ya zabga Mata ba shiri yace to ita Umman ba gida daya muke ba,ko Shukura kawarki ce?, a Dalilin me Zaki zo wajena Ni, salon ki takura mu motsi bazanyi ba kina kallonmu, tsawa Ahleef ya daka Mata ba shiri ta mike tabi Barira wajen Umma zuciyarta na tafasa tana Kara Jin tsanar Shukura.
Ahleef yace bazan iya cin abinci yanzu ba Bari sai anjima yawun Nan nata ya daga min hankali,dama yawunki ne ko Sha zan iya Amma wannan Abu ba kyan gani, Shukura taji dadi Ahleef ya Kori Niima tasan badan Allah tazo musu ba, kallon American film suka fara Shukura tana jikinsa Yana Wasa da Dukiyar Fulaninta etc.
Da dare wurin 8pm Niima tayi wanka harda kwalliya ga ciki a gaba kurtsitsi dashi Wai a Haka take so ta birge Ahleef, harda Sa damammun Kaya ciki ya fito, ga mazaunai sun wani shamule kamar babu ba karamin Muni tayi ba,Amma Haka tace Umma zanje wajen Shukura muyi Hira,Umma ta tabbatar wajen Ahleef tazo badan Allah tazo musu ba, amma Bata ce komai ba tace a dawo lfy, Shukura suna Palon sama Babu kayan kirki a jikinsu suna ta zuba love sun zauce, dai dai wannan lokacin Niima taga basa Palon kasa kawai ta tafi sama tana ta kwada sallama Basu San tana yi ba, kawai sai ji sukayi an wangale labule an shugo tana sallama, Ahleef ya ganta ransa yayi mugun baci, Shukura tace kut..mene Haka Zaki afkowa mutane daki ba sallama ko Nan huruminkine, jahilar Ina ce ke?, Hijab Shukura ta lalubo zata sa Ahleef ya rike yace ta Saba gani ai kyale ta zauna ayi a gabanki ki gani idan zan fasa shegiya Mayyar Karuwa, dabba, Shukura ya jawo tunda akwai night wear a jikinsu Allah yasa, kawai yaci gaba da abinda yake,ba shiri Niima ta sauka da gudu kasa,sai da ta Gama kukanta sannan ta lallaba ta koma part din Umma tare da shigewa Room din da aka sauketa , kusan kwana tayi tana kuka tana tsinewa Mubaraq.
Da safe da wuri ta Kira Momee ta sanar Mata abinda Ahleef ke Mata,sannan tace Shukura ce a gabansa ta Gama shanyeshi,Momee tace ai Ni danaji Shuru na zata kun daidaita dashi ma Bayan kin haihu zai aureki, Amma ki gwada fada Masa idan yaki Ni zan Masa dabarar da Dole zai Amince kin San Yana ganin girmana.
Tun farko ke kika jawo,Nan Momee ta Kara Mata salon da zatayi Ahleef ya dawo sonta har ya amince zai aureta.
Da safe ya fito cikin kana Nan Kaya yayi azabar kyau,Shukura ta rakoshi cikin Shiga ta alfarma suna kamshi, Niima ta saman bene ta hango su suna ta soyewa a cikin mota,da sauri ta Sa hijab har kasa ta nufo su itama, har kasa ta tsuguna tare da gaida Ahleef, lfy kawai yace yaci gaba da magana da Shukura dake gefensa, ta maza Niima tayi tace Dan Allah Yaya Ahleef kayi hakuri ka yafe min abubuwan da nayi maka a rayuwa sharrin shedan ne, bazan sake ba,Dan Allah ka bani lokaci anjima idan ka dawo zan Gaya maka wata magana sako ne kawai zan fada.
Bai ce komai ba Shukura tace ance an yafe Miki har sau nawa Zaki nemi yafiya ya yafe Miki, a wayance Niima ta harari Shukura ba tare da kowa ya gani ba,Ahleef yace time da zan Baki kuyi magana da Honey idan ta Amince sai ta bani time na saurareki.
Niima zatayi magana kenan yawu ya ciko Mata Baki har Yana tahowa kamar zai zubo gwanin kazanta,ba shiri tace uhm...ohmm....sai ta mike tayi baya da gudu kafin kace me yuuut sai gata jikin bishiya wurin flowers tana kyara Amai, Shukura ta zaro Ido waje tana kallon Ahleef dake dariya,tace Dan Allah ka daina Mata dariya Kar ka jawo Allah ya jarabceni da laulayi irin nata,Allah ma baya Sa ba ya Kara kyalkyalewa da dariya tare da cewa duniya kenan.
Latifa yau ta dau wankan Sugar zata tafi Office din Farhan an rambada Powder da jambaki, Momee tace ai gidan Make up Zaki je Nan ta zaro kudin kwalliya ta bawa Latifa daga can zata wuce Office din.
Zamu ji ya Latifa za a Kare oho.😅😅😅😂😂😂🤣 Nafi yiwa Niima dariya wallah, magana ga yawu cike da baki hhhhh....
Up...up...Ni
AsmaBaffa.
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
76-80
Official
By
AsmaBaffa
Farhan Yana Office hankali kwance Yana waya da Fatimansa wacce zai Aura sai zuba love suke yarinya Yar mutunci ga tarbiya ga wayewa gata itama kyakyawa da ita.
Latifa taci kwalliya ta Sha kyau itama, Office din Farhan tayi knocking,kafin ya Bata damar Shiga sai da ta gyara tare da kallon Fuskarta a mudubi, come in yace sannan yaci gaba da wayarsa ta soyayya, Yana ganin Latifa ce ya canja fuska Amma sai ya danne yace I will call u back later ya datse Kiran, sannan yace zauna, Latifa sai da ta wani karairaye sannan ta zauna tana fari da Ido tana juya kafada.
Farhan ya girgiza Kai wani haushi ma ta bashi yace fadi meke tafe dake Ina sauri akwai aiki a gaba na,Latifa tayi fari sannan tayi wani murmushin Jan hankali sannan tace zuwa nayi na maka Godiya Akan abubuwan da kayi mana, yace no Need ai ba damuwa,Murmushi tayi tace ok tare da Mikewa tsaye tana juyawa Dan ya gani,sai taci gaba da magana tana juya idanu baka da wani aiki da zanyi maka sabo da abinda kayi mana Ina so nima na saka maka da alkhairi kaima,Farhan ya zaro Ido yace Dan Allah nayi bana bukatar a saka min.
Latifa ta kalli Office din tana kashe Masa Ido tare da cewa Naga kamar yayi dirty ai da ko shara da mopping nayi maka,yace no na gode jeki kawai, Dan Allah Ina so na fada maka magana Amma tamin nauyin fada, biro ta dauka da paper a saman table dinsa kana ta Rubuta Masa I love u a jikin paper sannan ta Mika masa,ya karanta takaici ya kamashi ba aji ba komai direct, a fili yace Ina da matar da zan aura kiyi hakuri, Latifa takaici ya kamata dama Bata fiye kunya ba sai ta hayayyako Masa da masifa Kar ka Soni din sai me Dan nace Ina sonka ko Kai kadai ne Namiji mtswwww taja tsaki tare da bude Kofa ta fice a fusace.
Tsaki yaja ya Danna Kiran Fatimansa suka dora daga inda suka tsaya, Momee ta bawa labarin abinda ya faru tsakaninta da Farhan harda Hawaye,Momee tace Kinga kin nuna Masa Baki da tarbiya bazai taba sonki ba,Haka na koya Miki kiyi? Nan Momee tayi ta masifa.
Niima dai dai Lokacin data San Ahleef Yana dawowa daga Office lokacin taci kwalliya yau dai tayi kyau ba laifi,Compound ta fito tana jikin wata bishiya dake facing din inda ake parking cars yanda Dole Ahleef ya ganta, Bata Dade da Zama ba sai ga Motocin Ahleef sun shararo cikin gidan,ya fito da sauri sabo da Burinsa yayi sauri yaga Shukuransa,Bai kula ma akwai wata Niima a gefe ba tuni hankalinsa yayi wajen Matarsa,jikin kofar Kuma Shukura tana Nan ta kyafe cikin kwalliya da Shiga ta gaske Wanda kowa ya kalleta sai ya Kara,Niima sai gani tayi Shukura ta sakalkale mijinta cike da Shauki tayi ciki dashi tare da banko kofa.
Nan suka barta tayi tagumi tana sake saken duniya a ranta tana neman Mafita yanzu ta fara tunanin Ahleef ya Mata Nisa yafi karfinta, sai dai Shukura abin ba a cewa komai sai du'a'i kawai.
Hankalinta tashe tayi cikin gida bangaren Umma kwalla cike a idonta,Zazzabin son Ahleef ya lullubeta sai yanzu Allah ya jarabceta da matukar kaunar Ahleef,ji take kamar ranta zai fita sabo da sonsa, idan ta kalli cikin Mubaraq dake jikinta sai kuka ya Kara kwace Mata tare da Nadama, Umma ita kanta tausayin Niima ya fara kamata Kuma ta gane Ahleef take so.
Niima ta iske tayi tagumi Hawaye na zararo Mata masu dauke da sinadarin dafin son Ahleef a cikinsu🤣
Lallashi tare da Nasiha Umma ta Shiga yiwa Niima,Kuma Niima taji sanyi a ranta, na gode Umma Dan Allah Umma kisa Baki Ahleef ya aureni Nan gaba,Umma tayi Shuru sannan tace zan gwada rokarsa Amma idan yaki bazan Masa Dole ba,matar mutum kabarinsa Dole idan mijinki ne sai ya aureki,idan ba shi bane idan duniya zata taru a kansa wlh bazai aureki ba,kiyi Addua Allah Baki na gari me kaunarki.
Niima tace na gode Umma tana share hawayenta.
Da dare Ahleef yazo wurin Baba suna Hira Umma ta shigo itama ta zauna,sai da suka nutsu sannan ta kawo bukatarta na Ahleef ya taimaka ya auri Niima Nan gaba,Baba zaraf yace Saudatu ki fita daga idona,ke ko kunya bakya ji Zaki sa ayiwa Shukuran taki kishiya da kanki,Allah ne ya halatta,Amma Ana so mutum ya nemi yarinya ta gari ba irin Niima ba,mene Bata yiwa Ahleef ba,sai yanzu da bukatar ta ce sannan zata damu Mutane,lokacin da shi ya Shiga wani Hali a kanta ta tausaya Masa?to wlh ko ba Raina ban yarda ya aureta ba.
Umma a sanyaye tace Mene abin fada anan tunda kace Haka ai shike Nan Nima ba cewa nayi Dole ba,idan yaga zai iya nace,to bazai Aureta ba cewar Baba Kuma kika takura wlh da kaina zan koreta daga Nan gidan.
Ahleef ba karamin dadin Maganar Baba yaji ba,dama shi ko me za ayi bashi da Burin karawa Shukurnsa kishiya bare ya auri wata Niima.
Shukura ce ta shugo part din Umma kenan ta Dan tsinci Zancen kadan Amma Bata Gama Jin me ainihin Zancen ke nufi ba,share zancen tayi kawai tare da gaida su Umma ta nemi wuri ta zauna itama sannan ta ajiyewa Umma wani flask me kyau, me Kuma kika dafa na kwadayi yau? Umma ta furta, Murmushi Shukura tayi tare da cewa Baba Naga Yana son danwake shine nayi Masa,da Tsantsan Jin dadi Baba yace oh Yata na gode Allah ya muku albarka, Umma tace Ameen, kwalliyar da Shukura ta sheka itace ta tafi da hankalin Ahleef sai binta yake da kallo ya kasa dauke idonsa a kanta, Shukura tana kallonsa ta gefen Ido Kuma taji dadi tasan kwalliyarta tayi,Mikewa tayi ta wuce part dinsu Kar Ahleef ya kunyatata sabo da taga sai wani magana yake mata da idonsa daya tana tafiya yayiwa Su Umma sallama yabi bayan Shukuransa.
A kitchen ya isketa tana dube dube sai ji tayi ya rungumeta ta baya tare da Rada Mata sallama a kunne,Jikin Shukura har ya harba wani bukatar Mijin nata ya taso mata tana a jikinsa ta juyo suna Facing juna,hannayenta biyu tasa ta tallafi fuskarsa tana kallonsa a hankali in a sexy way tace kana da kyau Hero I love u,kissing din lips dinsa ta farayi a hankali,shima Yana yi har suka koma da zafi zafi kamar zasu cinye kansu Yana cewa I love u to the bone Bae.
Daukanta yayi cak suna kissing juna ta ko Ina haka suka fito zuwa Bedroom, tun kafin su Karasa sun cire kayan jikinsu, Nan suka Shiga baje harkoki Baji ba gani abin nasu sai Wanda ya gani, Ahleef ya susuce sai kalamai yake ratartakowa Shukura Mata itama Haka daga Nan ya Shiga zuba Mata adduoi Wanda bai ma San me yake cewa ba, sai Bayan sun nutsu tare da tsarkake jikinsu Yana zaune ya mike kafafu saman bed bayansa ya jingina da fuskar bed din.
Sanye take cikin wani mini skert da Yar Riga ko cibi Bata Kai ba me siririn hannu tayi kwalliya sosai tayi kyau,tsakiyar kafafunsa ta zauna itama Yana Danna system ta lafe a jikinsa,hannunta dauke da glass cup na fresh milk tana Sha tana bashi shima Yana Sha Yana aikinsa.
Ba tare da ya kalleta ba yace Honey gist me,Murmushin da tasan Yana tafiya da imanin sa ta saki, cike da Shagwaba tace Hero makaranta fa University ga result dinmu ya fito yaushe zaka sani, Zancen ya share, kukan Shagwaba ta fara masa, mene Kuma? ya tambaya, ba Kaine ba Ina ma maganar schl sai kana shareni baka son zancen ma, a hankali ya lankwaso da kansa tare da daura Mata kiss a lips dinta itama ta Kara turo Masa Dan lips nata tare da sakalo hannunta daya ta wuyansa ya Shiga kissing nata sai da ya gaji sannan yace ina sane da schl Dinki Baby,bana son kina barin gida kullum bazan jure ba Amma Dole inshallah Zaki je schl ki jirani.
Murna ta kama Shukura bata San sanda ta rungumeshi ba tana kissing dinsa ta ko ina zata yi University itama a daina Mata iyayi, dariya Ahleef yake sabo da yanda shukura take murna kamar zai sata Aljanna.
Niima ganin ba fuska wajen Ahleef kawai sai ta tattara nata ta dawo gida wurin Momee, ta waya Momee ta Kira Farhan da Ahleef suzo tana son ganinsa cikin gaggawa tare da Farhan, Babu komai a ransu suka yi parking compound na Momee kana suka Shiga bakinsu dauke da Sallama,Latifa ta labe jikin kofa tana leken Farhan,Niima Kuma Ana can ana cancada kwalliya.
Momee da farin ciki ta tarbesu tana murna suka gaisheta cike da ladabi,Ahleef yace Momee gamu da fatan dai lfy, Baki washe tace wlh lfy Lau,wata alfarma nake nema a wajenku,nasan nafi karfin komai a wajenku musamman Kai Ahleef Umarni ma idan na baka nasa zaka yarda, Ahleef yace Haka ne Momee ai har yau uwarmu ce har abada ma, Baki Momee ta Kara washewa sannan tace Ina so Ahleef Dan Allah ka rufa Mana asiri ka auri Niima idan ta haihu,Farhan Kuma ka rufa min asiri ka auri Latifa,kafin Momee ta Gama zancenta Gumi ya jike Ahleef duk da ac dake Palon,Farhan kuwa ko a gefen rigarsa yace Momee kiyi hakuri wlh Ina da wacce nake so na rigada na fitar da matar aure saura 3mnths biki ma,Allah ya Bata miji na gari Wanda ya fini,Kuma na gode sosai da Babban tayi da kika min,Dukul Momee taji a ranta,a fili tace ba damuwa Farhan na gode Allah bada zaman lfy yace Ameen.
Latifa Dake labe hawayen kauna ya kwararo mata tasan ta rasa Farhan shike Nan.
Saura Kai Ahleef me ka gani? Ahleef yace kiyi hakuri Momee bazan iya auren Niima ba wlh sabo da Shukura baza ta iya Zama da kishiya ba,baya ga Haka ma yanzu Niima Bata Raina ko kadan,Momee ta jinjina Kai sannan tace kaje kayi tunani Ahleef tukun Nan da 1wk sai muyi maganar again.
Ahleef yace Momee bazan boye Miki ba ko nayi tunani amsa daya ce, da naso Niima kin sani itace ta yaudareni, ban yarda ba Ahleef na baka time kayi tunani cewar Momee,ganin Momee taki yarda yace to zanyi tunani Momee tunda kince,Murmushi Momee tayi tare da cewa yawwa na gode,Mikewa sukayi sai gida.
Shukura taga Ahleef ya shugo dauke da damuwa a fuskarsa tare da sassan jikinsa da gani ransa a bace yake, cikin nutsuwa Tasha kwalliya ta gaske tana walwali tare da kamshi ta rungumeshi tare da kwantar da kanta a saman lafiyayyen Kirjinsa, Kam Kam ya Kara kankameta a jikinsa Yana shakar Kamshinta,Jin Bai ce komai ba sannan ya Saba fada Mata zafafan kalamai da kisses Amma yanzu ko daya baiyi ba sai rungumeta da yayi a jikinsa Yana sauke ajiyar zuciya.
Saman lumtsumemiyar 3seater ta jashi suka zauna tana saman cinyarsa a zaune hannayenta ta sarkafosu ta wuyansa suna Facing juna,Bai son kallonta ma Dan kar ta gane Yana damuwa,amma tuni ta rigada ta ganoshi,sansanyar muryarta tace lfy My Heart? me ya sameka?waye ya Bata ma Rai?waye ya taba min Mijina? Murmushin karfin Hali yayi sannan yace Honey bana boye Miki komai wannan ma bazan iya boye Miki ba, Nan ya Bata labarin abinda Momee tace na auren Niima,kafin ya gama labarin Shukura tuni Hawaye sun wanke Mata fuska,yace kinji abinda tace min,a hargitse ta mike daga jikinsa,Yana riketa tana kwacewa,sai kokawa suka fara tukuru tana kuka,Yana rirriketa tana zillewa,da kyar ta samu ta kwace kanta ta nufi Bedroom dinta da sauri ta zura Hijab dinta sannan ta fito zata bar gidan, ya riketa Nan ma suka ci gaba da kokawa tana kuka da Nishi, Ina zakije daga fada Miki magana ko nace Miki zan aureta, tana Haki tace gashi ka fada min kawai kace kana son abarka zaka Raina min hankali kace wata Momee waye ai na San halinku maza,Ni bazan zauna da Kai ba ka sakeni kawai ko ka barni nayi tafiyata bazan zauna da Kai ba ta Kara fashewa da Kuka.
Yayi lallashin duniya har ya gaji ya saketa ai kuwa ta Sa Hijab dinta tayi waje kamar zata tashi sama,tunaninsa Wasa take ko wajen Umma zata je,Ashe tuni ita ta bar gidan ma,da sauri yabi bayanta wajen Umma.
Yana Shiga Umma ta tsorata yanda yake a hargitse a gurguje ya labartawa Umma komai,Umma tace maza bi bayan yarinya ta ka dawo da ita Kaine da shirme ta ya zaka fada Mata wannan magana Kai tsaye,Baba da dawowarsa kenan daga unguwa yace sai Naga kamar Shukura tana tare taxi Zata Shiga,da sauri Ahleef ya fita tare da fisgar mota yabi bayanta, Allah ya taimakeshi Bata samu taxi ba,sai kuka take a gefen titi tana tafiya, Horn ya Danna Mata tana tabbatarwa Ahleef ne sai ta Kara sauri zata tsallaka titi saura kadan mota ta bigeta, ransa ya mugun baci,parking ya gyara ya fito da sauri tare da jawota daga titi tana kokawar kwacewa ya wanke ta da gigitaccen Mari,kafin tayi magana ya Kara Mata wani sabon Marin sannan ya finciketa ya jefa ta a mota yasa lock kana ya Shiga shima tare da Jan motar suka koma gida tana dafe da kumatunta Wanda yasha Mari yayi jajir dashi.
Yana parking niyyarsa ya kaita wajen Umma ta lallasar Masa ita,amma Yana parking tana kukanta ta balle murfin motar ta fice tayi part dinsu da sauri, kansa ya daura saman sitiyari duk abin duniya ya Masa zafi,ya rasa meke Masa dadi a duniya sai daya gaji da Zama sannan yaje wurin Umma tare da cewa Umma Dan Allah kizo ki lallasheta ta hakura,Murmushi Umma tayi tace ba ruwana wa yace ka fada Mata,kaje ka shawo kanta tun wuri.
Fita yayi ya kyale Umma Yana Jin haushi taki zuwa ta shawo Masa kan Shukura,Shukura kuwa bedroom dinta ta shige Bata leko ba,yayi yayi ta bude Amma taki Haka ya hakura shi kadai ya kwana har gari ya waye da kyar yayi bacci Shukura ma Haka sun rigada sun Saba kwana tare suna manne da juna.
Bata fasa ayyukanta ba ta fito tayi komai har breakfast ta shirya kamar yanda ta Saba sai dai tana yi tana hawayen kishiya,tana tsaka da shirya Dining Ahleef ya fito sanye cikin jallabiya,suna hada Ido yaga har yau kukanta takeyi,mamaki da dariya a bin ya bashi,wani dadi ma yake ji duk a kansa ake wannan kuka Lallai Ana sonsa sai ya godewa Allah.
Kallonta yake Yana sakar Mata Murmushinsa ita Kuma tana harararsa ga Hawaye nabin kumatunta, Ahleef yace sannu da aiki Honey har kinsa naji yunwa wannan kamshi Haka,Banza ta Masa.
Tsokanarta yayi yace da Zaki hakura ma ai da na Baki kyautar gida da mota sannan na kaiki Makka,ai kafin ya rufe Baki tace bana so ko duniya ce ka rike abarka,me zanci dasu tana Harara tare da ajiyar zuciya, dariya yayi sosai yaci gaba da tsokanarta ke da Zaki ma huta da aiki idan na kawo Miki Amarya tana tayaki, Jin ya Fadi Haka a ranta tace Lallai da gaske ne abin Sai ko ta Kara barkewa da kuka sosai take rerawa, Ahleef Baki bude yake kallonta ta shige Bedroom ta dakko takarda da biro tace sai ya Rubuta Mata saki, Bai kulata ba yace Ni ai Ina sonki tare dake nake so na rayu kima daina tunanin wani rabuwa, wucewa tayi zata koma dakinta Bai hanata ba ta Shiga ranar Haka ya yini ba dadi har aka kwashe 3days Shukura taki sakkowa ta hakura, shiryawa yayi ya fita Bai tsaya ko Ina ba sai Gidan Momee.
Bayan sun gaisa ya zauna gefenta sannan yace Momee kiyi hakuri wlh alfarmarki baza ta samu ba,matata baza ta iya Zama da wata ba, Allah ya Bata Wanda ya fini Amma bazan iya auren Niima ba,Momee Bata takura ba tace babu damuwa Ahleef Nima sai yanzu naga Niima Bata Dace da Kai ba sai yaushe zaka kawo min Shukura mu gaisa ko sai nazo? Ahleef yace soon zan kawo Miki ita Momee,Bayan sun Dan taba Hira Ahleef ya dawo gida Bayan ya tsaya yayi musu take away na kayan tande tande.
Hakimar tasa Shukura taci Uwar kwalliya kamar zata je Dinner sanye take da gown me karamin hannu gefe da gefe tsaga ce har cinya rigar readymade ta fito Mata da surarta sosai kamar ka sace ta sai kamshi take zubabawa bakinta da alawa tana tsotsa a hankali tana kallon Tv abinta a Palo.
Sallama dauke a Bakinsa ya shigo da kyar ta amsa Masa tana basarwa ko sannu da zuwa Bata Masa ba,kawai tv dinta take kallo,kamar Bata San da mutum ba, abin duk ya dameshi,sai yaji ba dadi,kusa da ita ya zauna jikinsu na gugan juna,gaba dayansu wani Yar suke ji a jikinsu sunyi 3days ba tare ba, ji suke kamar sun shekara rabonsu da juna, Bata ce Masa komai ba ya fara magana cikin Muryar sa me dadin saurare, wato Shukura Haka zamuyi dake ko? na yarda dake nazo bana boye Miki komai Ina sanar dake Amma baza ki tsaya ki Fahimci abinda nace ba sai ki dauki zafi kina gaba Dani daga maganar da Baki San wani tushenta ba wacce ba gaskiya bace,to na rigada na fada ma Momee bazan aure ta ba,Kuma an kashe maganar ma,Son da nake miki ya wuce na hadaki da wata sabo da bazan iya adalci ba,Amma idan Baki yarda kiyi ta fushinki ke kika sani, ki sani dai bana Miki karya, sannan rayuwar nawa take,zan iya Mutuwa ko yaushe,Kinga dai yanda maza ke Mutuwa,sai mutum ya mutu mata su kama kukan banza komai na duniya hakuri akeyi.
Jikin Shukura yayi sanyi musamman da taji yace mutuwa Kuma tasan baya karya a zancensa,sai taji tausayinsa,tasan Bata kyauta ba,Mikewa yayi zai bar Mata wajen,da sauri ta ruko hannunsa da nufin ya zauna Amma yaki ya fara tafiya,da sauri ta mike tare da Shan gabansa ba zato yaji ta hade bakinsu waje daya da zafi zafi tana tsotsa kamar ta samu alawa, tun Yana jinta ita kadai shima ya tallafi fukarta da tafukan hannayensa masu laushi ya Shiga tsotsar bakinta da sauri sauri an Dade ba a hadu ba,Yana kissing nata itama Haka tana I'm so sorry My Hero,tana Haki kamar wacce sukayi tsere.
A wajen ya fara rabata da kayan jikinta ta wani lumshe Ido tare da taimaka Masa,Kasa karasawa sukayi sama Bedroom a palonsu suka ci gaba da shakatawa da juna,Shukura I missed u kawai take iya furtawa,mazarkwailar Ahleef ta gusar Mata da hankali Baki daya,Shi kanshi ji yake yau tafi ko yaushe mazarkwaila domin yaji kamar ma yau first night ya Gama haukace Mata,Bai San Umma tana tsuma Masa Shukuransa ba shi yasa take Kara mazarkwaila, sun Dade suna gwangwaje juna da zumarsu kafin su samu nutsuwa tare da tsarkake jikinsu,Sai lokacin ta Kara gyara Palon neat sannan suka koma bedroom tare da lumtsuma a saman bed,ita Kuma tana jikinsa tana Wasa da yatsunsa masu daukan hankali, a hankali yace Ki saurareni kiji Honey ke bakya tsayawa ki fuskanci mutum sai ki yanke hukunci,da sauri ta rufe Masa Baki da tafin hannunta me matukar laushi da kamshi kana tace bana bukatar wani magana na hakura ka aureta ai Allah yace ku Kara wlh na hakura tunda sunna ce, Ina sonka zan zauna Haka,tana Gama furtawa Hawaye suka shararo Mata,Dariya Ahleef ya Shiga yi Mata.
Haba ya rike tare da zura Mata Ido kamar zai Shiga cikin Fuskarta,ita kuma Hawaye na zubowa tana kokarin Sharewa Amma sun kasa daina zubowa karshe ma sai ta rushe da Kuka sosai ta fada jikinsa tare da rungumeshi tana ta faman shesheka.
Bayanta zuwa gashinta yake shafawa a hankali alamar lallashi har tayi Shuru sannan yace ki kwantar da hankalinki Zumata wlh kinji na rantse ba aure zanyi ba,bazan iya Miki kishiya ba sai kaddara wacce bana fata,naje gidan Momee na fada Mata gaskiya kinji na rantse kin San bazan Miki karya ba,Dan Allah ki daina kuka kina damun kanki 3days har kin rame.
Lallashi tare da dadan kalamai ya dinga fada Mata Yana nuna Mata yanda yake sonta,sai gashi ta yarda har ta saki ranta suna kyakyata dariya.
Farin ciki ya lullubeshi Ahleef Shukuransa ta daina fushi.ranar kwana sukayi suna farantawa juna rai.
Bayan Yan watanni ansha bikin Farhan da Fatima,Shukura babbar kawar Amarya,Ahleef a barin Ango sosai bikin ya kayatar.
Niima da Latifa suna gaban Momee,Sultan da Suhail Wanda jiya suka sauka a kasar suka shugo Suma suka nemi wuri suka zauna kusa da Momee, Sultan yace Momee munfa samu matan aure tunda muna da wadata aure zamuyi,Suhail tasa sunanta Basma Yar Kano ce suka hadu a schl,Ni Kuma Islam ce Yar Gombe ce yanzu sunce mu tura manya,Momee murna ta kamata tace Alhmdllh tunda dama kun dawo Nigeria Baki daya me ya rage kawai sai aure,Niima da cikinta Kato tace Hmm Bros na tayaku murna,Latifa tace Allah muma ya bamu sai a hada bikin,kowa yace Ameen daga Nan suka Mata sallama sun wuce gidan Ahleef zasu Kai Masa ziyara daga nan shima su sanar Masa sun samu matan aure.
Mubaraq dai har yau ba labarinsa tun Ana nemansa har an gaji an hakura,Mama Bata da aiki sai kuka sabo da duk cikin yaranta tafi son Mubaraq,Hafcy dasu Zahra su kansu abin Yana damunsu yanzu gidansu duk ya tarwatse Mama da Daddy Basu da nutsuwa,Alhaji Adamu yana cikin damuwa Wanda Dalilin Haka ya haifar Masa da ciwon Hawan jini,gashi Kuma wani Masifar Ashe Alhaji Adamu Baban su Hafcy manemin Mata ne kamar Dan akuya Haka yake,Koda ciwon Hawan jinin sa ya tashi Bayan yaje asibiti aka yi masa test iri iri Nan aka gano Yana dauke da cutar Hiv, Mama Basu sani ba ya boye mata,
Bayan wasu watanni Niima ciki ya tsufa sosai tana ja da kyar haihuwa ko yau ko gobe, da safe da wuri yau nakuda ta kama Niima Momee da Latifa suka tattara sai Asibiti,Latifa sai kuka takeyi sabo da yanda Niima ke azabtuwa da nakuda, Momee hankalinta ya tashi,su Sultan du suna asibiti,Ahleef Yana kitchen manne a jikin Shukura tana soye soyenta wayarsa tayi Kara ya dauka ganin Suhail ne ya Kira shi, hankali tashe ya fada Masa Niima na asibiti zata Haihu Rai a hannun Allah,da sauri ya datse wayar Yana sanarwa Shukura ta hade Rai tare da turo Dan lips dinta me shekin Pink color ta furta to Kuma ba sai ayi Mata Addua ba Kai mene naka ciki ko Kaine angwazoma din da zaka karbi haihuwar, haihuwar ma ta cikin shege har murna akeyi sabo da duniya tazo karshe to wlh sai dai mu tafi tare duk motsinka Ina gani bare ayi ma signa da Ido, gas ta kashe tare da wanke hannunta a sink da sauri tace muje na shirya mu tafi, dariya ma ta bawa Ahleef da wannan mitar Tata,wani farin ciki na ratsa shi Shukura na kaunarsa da yawa shi Kam ya godewa Allah Yana son yaga Ana kishinsa.
Tare suka wuce Bedroom ta Sa katon Hijab har kasa Amma duk da Haka tayi kyau,shi Kuma da 3qtr da Riga me shegen tsada da kyau,Shukura ta dauko jallabiya tace sa wannan so kake a kalle maka fata Ana hadiyar yawu, Murmushi ya saki me sashi sumar da mace ya manna Mata kiss a kumatu sannan yace I love u my wife,me too cewar Shukura ta fara tube Masa Riga sannan ta zura Masa Jallabiya akan wandon tace muje to,Bai Musa Mata ba ya bita tana rike da hannunsa,har Mota driver ya jasu sai asibitin da Niima ke nakuda.
Niima an Gama galabaita kamar zata mutu tuni su Shukura suna asibiti Kam Kam ta rike mijinta ta window ta leka ta dawo,Amma ta mutunta Momee sosai itama Momee haka,Su Sultan Suna ta tsokanarta saura ita Nan gaba tana dariya cike da kunya,Ahleef ya Rada Mata a kunne gaskiya ya kamata muma mu dage a samo Mana Baby, a hankali ta Dan dakeshi kadan da Wasa, Niima har ta fara barin wasiya iri iri tana kuka Allah ya taimaketa ta santalo yarta mace katuwar gaske zukekiya me kama da Mubaraq, Babu Wanda yayi Murna sai Niima ita taji tana kaunar yarta a ranta fiye da kowa.
Bayan ta samu sauki an gyarata tare da Baby Haka Su Ahleef suka dauketa ba tare da kyama ba aka dinga zuba Mata adduoi iri iri, a ranar aka sallamesu Bayan komai ya Lafa makwafta da Yan uwa sai tsegumi da gulma akeyi Dan ma a Haka Abuja ne ba ruwan wani da wani da arewa ne sai dai Niima ta koma kauye,Momee har gida taje ta sanarwa Alhaji Adamu da Mama Niima ta haifi Yar cikin Mubaraq, daga Mama,da Baban Mubaraq har su Hafcy ba Wanda bai zub da Hawaye ba,Amma Haka Dole suka je da Sha Tara ta arziki suka ga jaririya sak Mubaraq,Mama duk an fara saduda da Duniya sabo da balain da suke Sha kullum iri iri na kaddara.
Kafin Suna Mama tace a sa Mata Khadija kawai ko Allah zaisa tayi Hali na gari irin na Nana Khadija Matar Manzon Allah,hakika Ahleef ne ya yanka Mata rago manya har biyu taci gaba da raino Yarta ba tare da kyama ba,Haka dangi ma kaf tunda Momee ta sasanta tsakaninta da danginta,Haka ma da Dangin Abba.
Yau Niima tayi arbain yaune Kuma suna zaune suna kallon News suka ji labarin an kama wasu masu safarar kwayoyi zuwa kasar waje sai ga Mubaraq hannunsa daure da Ankwa ta ko Ina an kamasu a airport sannan an dawo dasu Nigeria za a Yankee musu hukunci.
AsmaBaffa.
Taku har kullum afwa bana typing da wuri Uzuri dai nake so ayi min fans Kar kuji haushi next Novel inshallah da time baza ayi Haka ba idan aka fara sai an gama.
Godiya dubu masu Sharhi 😍😍😍😍.
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SANO
END
91-100
Official
By
AsmaBaffa
ASMABAFFA FANS CLUB
JIN DADI SABO
HOUSE OF HAUSA NOVELS.
Ina Godiya sosai da kaunar da kuke nuna min,ga Sharhi akan lokaci Allah ya biya.
Yaune Friday yaune Kuma za a daurawa Niima da Latifa aure,ba wani biki za ayi ba sabo da Yan gulma da tsegumi,Latifa da Yousuf dinta sun so ayi party etc Amma Sabo da Niima za ayi ta surutu yasa Momee ta Hana tace Ana daurawa za a Kai amare ba wani gulma.
Shukura sabo da Murnar Niima zatayi aure ta bar Mata mijinta tun Ana gobe ta addabi Ahleef ita sai tazo ta kwana,yace baza ta kwana ba,Amma ta dinga naci Dole ya kyaleta driver ya kaita,Ana idar da Sallar jumaa aka daura auren Niima da Mubaraq, Latifa da Yousuf, Bayan sallar laasar aka wuce da amare gidajen mazajensu a cikin garin Abuja,cikin Yan Kai Amarya harda Shukura tana motar Sultan,maimakon ta dawo gida sai ta koma gidan Momee, Umma tana gidan itama Driver Yana zuwa daukan Umma sai ta tasa Shukura gaba suka tafi gida, lokacin Ahleef Yana tare da Baba suna Hira yaga Shukura da Umma farin ciki ya Kamashi yasan Umma ce tayi Mata Dole suka dawo tare.
Baba ta gaisar sannan suka hada Ido da Ahleef ya kashe Mata Ido daya,Murmushi tayi kadan Wanda shi kadai yaga hakan, ba kunya ya mike tare da yiwa Baba sallama Yana me yiwa Umma sannu da zuwa yabi Shukura harda daukar Mata handbag ya rike suka jera part dinsu sai zumudi yakeyi sabo da kwana daya kamar shekara yake gani,suna Shiga ya fara warwarewa Shukura hadda da salon love dinsa, dama Shukura kadan ake jira ta Shiga maida Masa da martani yanda taga dama take sarrafa shi shima haka, albarkatun kirjinta ya fara sarrafawa Wanda yasan Yana taba su Shukura zata rude,a nutse suke sarrafa juna sai da suka zauce, Ahleef Wanda dama kwararre ne a wannan fagen rada Mata yayi a kunne da akwai Dadi? Shukura cike da Shauki tace sosai ma itama cikin siga ta rada,
Tambayoyi yake Mata iri iri ba kunya take bashi amsa sai su Kara rudewa, yaudai ansha love,tunda yaje Office washe gari ba abinda yake tsinanawa sai tunanin Shukura da Daren jiya yanda ta jiyar dashi dadi,ba shiri ya tattara ya gudo gida ya Kara kwasar harkoki ya samu nutsuwa ya sake fesa wanka Yana nishadi ya koma Office.
Niima Amarya Suma sun kwashi love dama sun Saba da juna,Haka Mubaraq yaji dadin harkar sabo da Tasha gyara, yarsu Khadija tana wajen Momee anyi Mata yayen dole sai sun Gama cin Amarci za a kawo musu yarsu suci gaba da rainonta,Mubaraq da Niima sunce sun barwa Momee ta rike ta, Momee ta karba hannu biyu kuwa tunda yarinya ba ruwanta Kuma yanzu Babu kowa a gabanta sai Yan aiki.
Latifa da angonta Yousuf suna can Suma Ana kwasar Amarci, abinda Latifa tayi shi mijinta yayi shima ya tuba Dan Haka ba Wanda zai wa wani Gori,Sunyi shaye shaye sun tuba,Niima kuwa dama tare suka sheke ayarsu Kuma suka yi aure Bayan Sunyi Nadama.
Maman Hafcy da Alhj Adamu sun kwantar da hankalinsu suna Shan magani sai ka rantse sunfi kowa lafiya ma,Babu Wanda zaice suna dauke da HIV, haka ake so mutum ya kasancewa me yadda da kaddara,ba Wai dan cuta ta samu mutum ba ya zauna yayi ta tunani duk ya rame bakin ciki ya kasheshi a banza,ayi Addua Ana fadawa Allah ko maganin ne sai Allah ya kawo ma,idan ma Bata da magani sai kuga Allah ya Hana cutar tashi har ta cutar da mutum.
Hafcy da Zahra sun samo miji amma duk ba Wanda ransu ke so ba Haka suka hakura domin dattijawa ne,Alhaji Danliti shine na Zahra Yana da Mata da Yara Bakwai duk manya ne yaran, Alhaji Zubairu kuwa tsohon tuzuru ne Wanda yafi shekaru ashirin ba tare da yayi aure ba Tunda Matarsa ta rasu ta bar Masa Yara uku Yan Mata dasu, Baban su Hafcy da kansa ya Kai Masa tallan Hafcy ya aureta.
Kasancewar mazajen masu kudi Ne a shirye suke aka sa biki wata daya tal.
Hafcy da Zahra tare da Mama har gida suka je suka bawa Momee hakuri tare da Ahleef har Shukura suka yafi juna sannan suka ci gaba da mutuncinsu sama sama da Momee.
Duk da Haka Basu da kwanciyar hankali da zarar sun tuna fa Mama da Dad dinsu suna tare da cutar HIV ko yaushe zasu iya fecewa lahira.
Shukura cikinta ya cika 7mnths ya fito kato dashi ga makaranta kullum tana zuwa,tana kula da mijinta sosai ga Tsafta ga iya kwalliya,girki gashi tayi wani irin wayewa ta daban,fagen soyayya kuwa Shukura ba a cewa komai,Umma wannan shekarar Ahleef ya Kuma biya musu Hajji da Umra,sannan idan sun dawo zasu tattara gaba daya suje Niger wurin dangi,Shukura ma rigima ta ajiye Wai idan Sunyi hutu sai ya biya Mata ta Kara aikin Hajji da Umra,Ahleef Kuma yace sai ta haihu zai biya musu suje tare da zaga kasashe.
Zaune Ahleef yake saman luntsumemiyar kujera dake palonsu na kasa,Karar door bell yaji,bude kofar yayi ya iske Farhan da Amaryarsa Fatima sun Sha kyau, uhm manyan gari Ashe kune Amma ko ku sanar damu zuwanku sai dai mu ganku, Bayan sun zauna suka gaisa Ahleef ya mikawa Farhan hannu suna gaisawa,Shukura ta fito taci wanka cikin doguwar Riga ta wani lace tsadajje,tayi mugun kyau,da Dan cikinta a gaba ya Mata kyau,Gefen Ahleef ta zaune tare da kwantar da kanta a saman kafadarsa tare da narke masa.
Fatima ta kalleta tana dariya,Ahleef yace bashi kike ci Fatima akwai time zamu Rama muma,Farhan Wanda ke dariyar shima yace sai dai ku rame, sun Sha Hira kafin daga bisani su Shukura suka shirya suka fita tare su hudun,Gidan su Sultan suka je,sannan suka wuce gidan Niima da Latifa,karshe har gidan Momee sukaje sannan suka biya yawon shakatawa suna ciyen ciye gwanin birgewa sai soyayya ko wannensu ke zubawa Dan uwansa, Shukura duk ta fitsare kafafunta Bata kunyar mutane zaman Abuja cudanya da arna duk sun jawo ta rasa kunya mijinta ko a gaban waye ba ruwanta, Fatima ce take Dan jin kunyar Ahleef ma Amma shi ko a jikinsa Hankalinsa Yana ga Shukuransa.
Wani kallon so Shukura ta zubawa Ahleef shi kanshi dariya abin ya bashi Bai San sanda ya Shiga murmusawa tare da cewa Allah ya shiryeki Honey,dariya itama tayi taci gaba da bashi Ice cream din da suke Sha, kowa ya wuce sai ya kalli wannan masoya,Fatima Kuma Farhan ke Bata da kansa suna hirarsu, sun Gama suna niyyar tafiya sai ga Niima da Mubaraq dinta Suma sunzo,Har ga Allah Niima a rashin Ahleef ta auri Mubaraq tafi son Ahleef Amma ya ta iya yafi karfinta,Dole ta rungumi minjinta Haka,Ahleef yace Ashe Nan zaku zo Kuma,Mubaraq yace bamu yi niyya ba kaga sarkin yawon da ta matsa sai mun fito,dariya sukayi gaba daya sannan suka wuce,Farhan motarsa tana gidan Ahleef suna komawa suka koma motarsu suka wuce gida.
a kwana a tashi Ana zaune lfy da juna,Shukura cikinta ya Shiga wata tara, Ahleef tafiya ta taso Masa zuwa Canada Amma yace ba zai je ba sai Matarsa ta haihu zasu tafi tare, yau Monday Ahleef Yana Office Shukura ta fara Nakuda,Umma ta shigo dubata ta isketa tana murkususu Bata bi ta kan Ahleef ba tasan halinsa a kan Shukura sai yaje yayi hatsari a banza, Driver tasa ya wuce dasu asibitin kudi,kamar jira sukeyi Ana zuwa Shukura ta haifo danta Namiji katon gaske kyakyawa jajir dashi, Shukura tayi juriya sosai Babu wani kuka ko wani surutai ta birge Umma kwarai,Bayan an gyarata tare da jariri yasha adduoi, Umma tasa aka gogeshi tas da Man zaitun Dana habba,dake Private ne dakin kowa shi daya,kamar wani Hotel, anan Shukura tayi wanka ta da ruwan zafi tare da gasa kanta sosai sabo da Umma ta Gama nuna Mata darajar gasa jiki, Bayan sun Gama komai an rubuta Magunguna na Karin jini da wasu masu warkar da rauni aka sallamesu, suka dawo gida part din Umma.
Nan Umma ta Kara dafa Mata ruwa akayiwa jariri wanka fes itama ta sakeyi ta shirya cikin wata atamfa hadaddiya riga skert sun kamata daf kamar ba itace ta haihu ba tayi Masifar kyau ita da jariri,dama Ahleef tunda ta kusa haihuwa yake ta siyan kayan jariri, kamshi suke zubawa kawai,Umma ta kawo Mata farfesu da abinci lafiyayye suka ci suka koshi,Baba yazo ya dauki jariri tuni Yana sheka Masa Addua,yace Banga Ahleef ba,Shukura kamar zatayi kuka cike da Shagwaba tace Umma ta Hana a fada Masa Wai har sai ya dawo ya gani,Wai zaizo ya dameta da sintiri, wannan Shirme ne ai cewar Baba Bari na kirashi Yana latsa wayarsa ya Kira Ahleef Yana dagawa yace Allah ya sauki Shukura lfy kazo gida,Ahleef Bai San sanda ya buga ihun dadi ba Nan ya fara Godiya ga Allah sannan ko escort Bai wani jira ba ya figi mota ya figota a tamanin, sai gida direct part dinsu ya nufa,sai ya iske a kulle,Part din Umma yayi Yana fyalla uban sauri kamar zai tsinke kafafunsa fit ya shige Palon Umma ya manta da wata sallama,Umma tana rike da jariri a palonta Shukura tana gefenta tana cin Apple.
Tsayawa yayi a tsakiyar Palon tare da tsurawa jaririn Ido Yana kallonsa Yana wani Murmushi me kayatarwa, sumarsa me yawa da santsi ya shafa,Baki bude Umma ke kallonsa,Shukura Kuma Ahleef take kallo itama tana wani Murmushin Jin dadi sun haifo dansu, Sai da ya dauki lokaci sannan ya Karasa wajen Umma ya Kai hannu cike da zumudi zai dauki jariri,Umma ta Hana shi, sai ka koma kayiwa mutane sallama,da sauri ya koma yayi sallama suka Amsa sannan ya shigo zai karba Umma ta sake hanashi,kamar zaiyi kuka yace Ohhhhh Umma pls mene Haka,dariya Shukura tayi tace Umma ki bashi kina sa Masa Rai,Mika Masa Umma tayi tana Masa dariya ta Shiga kitchen, adduoi ya Dinka zubawa dansa sai da ya Gama sannan ya zauna kusa da Shukura kafadarsu na gugan juna.
Yaro ya kalla ya kalli Shukura sannan ya Kara kallon kansa yace Dani yayi Kama yarinya,Amma dai kasan na Dan fika haske kadan sabo da Haka skin Dina ya gado, Musu suka dingayi har Umma ta iske su kowa Yana cewa shi jariri ya gado, banza Umma tayi musu ta wuce Bedroom taga ba kunya garesu ba.
Momee da sauran dangi,kawaye da abokan arzuka duk an sanar musu,Gida Kullum cika yake da Baki taf,fnds din Ahleef ma suna ta zuwa kullum Yana sintirin daukan jariri Ana nunawa abokai,Dan ma Umma tana hanashi,Haka kullum sai yazo da safe a gabansa za a bawa jariri Nono da dare ma Haka,wataran ma dakin da Shukura take a part din Umma a Nan Ahleef yake nacewa ya kwana.
Shukura ma an sanarwa da danginta kaf,Ana gobe suna kuwa Yan uwan Shukura maza da Mata sun zo mota guda Bus,Washe gari yaro yaci Sunan Abba Baban su Niima Abubakar,Ahleef yace ana kiransa da Farhan,sabo da yanda suke Aminan juna, an jefi tsuntsu biyu da Danko daya,Real name na Dad Nick name Farhan.
Wuri Ahleef ya kama me tsada anan akayi suna, Farhan sai Murna,Haka su Momee ma,anci an Sha anyi pics,ga kida ansha, frnds na Shukura Yan schl dinsu sunzo,bayan suna duk Baki sun tafi na kusa Dana nesa.Shukura Tasha kyauta iri iri,Farhan kuwa kayan da yayiwa jariri harda na hauka ma.
Bayan Shukura tayi sati biyu da haihuwa Ahleef ya nemi Umma ta bashi Shukura su koma part dinsu,Fafur Umma taki yarda, yau ma Ahleef na zaune kusa da Umma yace Dan Allah Umma da Nan da can ai duk daya ne,Ban yarda da Kai ba Ahleef,Ana yi ma abinci,part dinku kullum a gyare yake to me kake nema?.
Shuru yayi ya gaji da magiyar a bashi Matarsa,Shukura Kam ita tausayin mijinta take ji tasan Halinsa da Sha'awa baya jira,gwara tana kusa dashi Kar ya Shiga wani Hali,Shukura ya samu a Bedroom tana lallaba Little Farhan yayi bacci Ahleef ya zauna gefen bed Yana hadiyar yawu yanda Shukura ke kashe wanka yafi gaban ya iya hakura har sai tai 40days.
Itama Zama tayi kusa dashi tare da cewa ya akayi ne My Hero,sai da ya Dade kafin yayi magana cike da takaici ga Shagwaba da wani narke Mata da yakeyi kansa ya kwantar a kafadarta ita Kuma tana shafa Masa gemunsa na matasa, yace Umma tace baza ki koma part dinmu ba sai kinyi arbain,wannan wacce alada ce Haka? Ni bazan iya jira ba,ai ma kin warke Kuma kina sallah kawai ki sato jiki anjima kizo pls Honey.
Tausayi da so yasa Shukura tace karka damu zanzo da dare,murna sosai ta bayya a fuskarsa,kiss ya manna Mata sannan ya mike yace ina jiranki, Shukura tace to.
9pm Shukura tasan yanzu Umma tuni Sunyi bacci ma sabo da dama da wuri suke bacci,wanka tayi ta Sha turaruka tasa wasu shegun kayan bacci sannan tasa Hijab har kasa tana kamshi ta fito cikin sanda Sadaf Sadaf,idan ba kuruciya ba Taya zata bar jariri shi daya a daki,Amma haka ta bude kofar a hankali kawai taji Muryar Umma Ina Zaki je? Ba tare da ta juyo ba ta rumtse Ido sannan ta juyo cike da kunya ta fara kame kame ah...ahm....uhmm...can..can part din zanje dauko wasu Kaya,to koma ki kwanta ba inda zakije ai duk na San plan dinku,Ni zakuyiwa wayo,Sum sum Shukura ta koma Bedroom sannan ta Kira Ahleef a waya ta sanar Masa Umma ta kamata,Ahleef yace to zanzo Ni anjima,karfa a kamamu cewar Shukura,wayar ya datse,ita Kuma Umma tuni ta garkame kofar Palon da key Kuma ta bar key din ajiki yanda baza a iya budewa ba,Ahleef yazo yayi yayi kofa taki buduwa,yasa spare key shima yaji akwai wani a jiki.
Dole ya hakura ya koma part dinsu,Ya sanarwa da Shukura ta waya, Dole suka hakura yau.
Duk yanda Ahleef yaso suyiwa Umma wayo abin yaci tura,gashi har Shukura ta kusa arbain,Yana Murna Umma tace to Kauyensu zamuje sannan mu wuce Niger idan mun dawo daga ziyarar ganin dangi sai ta koma part dinku,takaici ya Hana Ahleef magana, Shukura Kuma sai dariya take Masa a boye.
Barin gidan yayi sai Gidan Momee,Momee ta ganshi hankali tashe, da sauri tace lfy son? Momee pls kije kiwa Umma fada mutum da Matarsa ace baza ta zauna a gidanta ba,dakin mijinta yafi karfinta sai can wurin Umma,Dan Allah kiyi magana Ko na bar kasar nan,Dariya Momee tayi sannan tace nasan Halinka Ahleef kayi hakuri Haka akewa masu jego,Akan Mace har yaji zakayi Haka me yayi zafi za a dawo ma da matarka,Takurawa Momee yayi sai da ta shirya ya kaita wajen Umma,Umma tace au karata ka Kai wajen Momeen taka,Umma da Momee sukayi magana Lallai baza a bashi Shukura ba sai tayi arbain,Ahleef tunaninsa Momee ta gyara komai,Amma sai yaga ba abinda ya faru.
Yau tunda ya shigo da dare Bayan Isha yaki tafiya jariri Yana hannunsa,duk inda Shukura tayi sai ya bita yuuuu da kallo,Umma ta koreshi yaki tashi,Kazo ka tafi bacci muke ji mu zamu rufe kofofi,Ahleef yace to Yana Jin haushi yayi fushi ya fice a fusace.
Haka yayi ta fushinsa ya daina zuwa part din Umma Baki daya,Shukura duk ta damu Ahleef Yana fushi da ita,tana yin arbain Shukura da Umma har Baba suka tafi garin su Shukura, Ahleef Yana ta fushi yace ba zai je ba,Suna dawowa suka wuce Niger abinsu,sati daya sukayi sannan suka dawo,Amma Umma tace Shukura sai ta je ziyara gidajen frnds da Yan Uwa,gidan su Momee,Niima,Latifa,suhail,Farhan etc Ahleef duk ya canjawa gidan tsari ya Kara haduwa an canja komai, Bayan ta Gama yawonta yau Sunday yaune Umma tasa masu aiki suka Kara gyara part din Shukura sannan aka Kai kayanta tare da Dattijuwa me taya rainon little Farhan.
Shukura wani wanka data dauka ka rantse ganin sarauniyar England zata je,Kamar sabuwar Amarya ga Umma dama ta Kara tsumata sosai.
Abin mamaki tunaninta Ahleef zaiyi fushi da ita sai taga ba abinda yayi jaririnsa ya dauka Yana Masa Wasa suka koma Bedroom,Shukura tace My Hero nayi tunanin baza ka kulani ba,Akan me? Ai ba Ke kika min laifi ba kuma idan banyi hakuri ba me zanyi,Rungumeshi Shukura tayi tare da cewa I love my Heart, love u more, dare Yana yi Farhan Yana wajen nanny dinsa, Ahleef sai zumudi yakeyi kamar Bai San Shukura ba,ji yake kamar yau aka kawo Masa ita Amarya.
Shukura kuwa har wani tsoro ma take ji yanda taga yanayinsa,Wanka yayi sannan ya karaci kakalen sa jikin mirror,Shukura ma tana wanka ta fito ta shirya tare da shafa turarukanta zata sa kayan bacci kenan Ahleef yayi sama da ita sai bisa bed ya zare Dan towel din ya jefar dashi, sannan ya Shiga Sarrafa ta yanda yaga dama tun tana nokewa har itama ta fara maida martani,maitarta ta tashi, suna tsaka da Holewa suka jiyo kukan Farhan Yana tsaga uban ihu,Ita kanta Nanny ta kasa lallashinsa, Shukura tace kaji kukan Farhan fa yaki yin Shuru mu Bari na lallashe shi idan yayi bacci sai muyi abinmu, Ahleef ko kulata baiyi ba,yaci gaba da aikinsa,Shukura tace Farhan fa Yana ta ihu kana jinsa,Ahleef da kyar ya saita muryarsa yace idan ya gaji ya daina,yaro bazai tashi kuka ba sai dare zai na Hana mutane sakewa.
Shukura Kuma uwa sarkin son danta ta ni dai bazan iya ba hankali na Yana kansa ka tsaya naje na dawo,Wlh kinji na rantse yaron Nan ko mutuwa zaiyi tsabar kuka baza a dakko shi ba, yaro sai kukan dare idan ya gaji ya daina.Tunda Shukura taji ya rantse kawai ta hakura suka ci gaba da soyewa,Yaro Kuma Yana ta tsaga uban ihu can kasa wurin nanny har ya gaji yayi bacci, ranar Sai da gari ya kusa wayewa Basu rabu da juna ba suna soyewa.
Haka rayuwa taci gaba cikin kwanciyar hankali da nishadi,Shukura tana kula da mijinta yanda ya kamata,shima Ahleef Haka,Momee da Umma Kuma sosai suke muamula,yayin da Matan su Sultan suka samu ciki, Fatima matar Farhan ma ta kusa haihuwa,Niima da Latifa ma suna dauke da juna biyu, Zahra da su Hafcy sunyi aurensu Suma suna Shan Amarcinsu.
Bayan Shekara uku Shukura ta Gama schl dinta,danta Farhan dagwas dashi Yana yawo ko Ina,Kuma Bata Sami ciki ba har yanzu,Sunyi wani kyau ga zuwa kasashen turawa suna Hutawa,duk Shekara Kuma Ahleef kaf yake biya musu makka Umrah harsu Niima.
Lokacin Matan sultan sun haihu,su Niima ma Sun haihu,Haka Hafcy da yarta mace,Zahra da Habiba Kuma ciki tsoho garesu.
Ahleef ya dauki Shukuransa zuwa England wannan lokacin Farhan a gida aka barshi wurin Umma,idan ya gaji Kuma a kaishi wajen Momee ko gidan Farhan yayi hutu can.
Sai da suka shafe wata biyar sannan suka dawo Nigeria Shukura dauke da cikinta Dan wata Uku,Sai Murna sukeyi zasu Kara haihuwa.
Bayan wata 6 Shukura ta haifi yarta mace,aka sa Mata suna Noor,kyakyawar gaske ce ta karshe,Farhan karami duk ya dameta da tsokana.
Bayan wata 7 Shukura abar kallo ce yanda take tashen kyau da iya daukan wankan Sugar,ga wayewa ta Zama gogagiyar gaske ta gaban kwatance,Ahleef wani ji yake da ita,yaransu masu tarbiya gwanin Sha'awa,Farhan Fatimansa tana Nan da tsohon ciki,Momee kuwa sosai take ji da yaran Ahleef,Haka su Niima dasu Hafcy duk sun zama kawayen Shukura suna ziyartar juna, Haka mazajen ma suna zumunci.
Umma da Baba suna zamansu lfy,Shukura tana zuwa wurin danginta ayi musu Sha Tara ta arziki,suna Alfahari da ita.
Yau ma Shukura da Ahleef sun fito Noor tana kafadar Ahleef tasha kyau cikin kana Nan kaya farare,gashinta yasha gyara na Yan gayu,Little Farhan ma Yana cikin kana nan Kaya Dan gayu dashi sabo da ko aski ba a fiye yi Masa ba style ake Masa da gashin kamar Dan turawa, Shukura Tasha Riga Arabian gown wacce Tasha aiki ga tsada black and blue,Ahleef yasa light blue shadda dinkin zamani,kowa ya gansu sai sun birgeka,da gudu guards suka bude mota suka Shiga ta alfarma sannan ga driver yaja yau ba escort zasu fita,sai Wani hadadden park na wasan Yara yaran masu hannu da shuni ke zuwa.
Basu dawo ba sai dare,Nanny ta karbi yaran tayi musu wanka tare da shiryasu cikin kayan bacci suka kwanta sai bacci sabo da Farhan ya fara zuwa schl kasancewar Yana da wayo ga Saurin girma.
Ahleef bayan Sunyi Shirin bacci ya manne Matarsa a jikinsa,a hankali Shukura ta juyo suna Facing juna ga wata Shagwaba da takeyi Masa me kashe Masa jiki,a hankali ta tallafi kumatunsa ta Shiga kissing dinsa sosai kamar zasu cinye bakunansu,ga wani kamshi dake tashi a jikinsu,Albarkatun Kirjinta Ahleef ya fara wasa dasu tana wani shidewa,ya furta Allah ya Miki Kira Honey ki godewa Allah Ni nayi Dace wannan basa zubewa kamar Yar 16 to 17 Haka suke naji dadina,ya Shiga tsotsarsu,Shukura tace karfa ka shanyewa Noor milk dinta tunda Kai har milk din shanyewa kakeyi dariya yayi kadan yace zan rage Mata ke Ina ruwanku mu da abinmu namune Ni da yarana.
Sun farantawa juna Rai sosai kamar yau suka San juna,Haka suka dinga kalamai masu dadi kowa Yana yabon Dan uwansa,suna zubar da kalaman soyayya wa juna,Ahleef sai albarka yake sawa Shukura da yaransa, tace I love my Hero, love u too Honey wani shaukin kauna na shigarsu. Basu da matsala sai wacce ba a rasa ba,ga addini ba Sanya...Allah ka bamu itasu muma da me typing da readers nace Allah biya Mana bukatunmu Na alkhairi.
Nan na bar su Ahleef suci gaba da rayuwarsu ta Jin dadi Dan na fara kishi da Shukura Nima.
ALHMDLLH
Na kawo karshen littafi lafiya,Masu karatu da Masu Sharhi,masoyana na ko Ina Ina matukar sonku,Ina kuma Godiya tare da sambada muka albarka,Allah ya biya Mana bukatunmu,ya yafe Mana kurakurenmu.
Allah yasa muyi amfani da darasin da muka koya na wannan Novel,abinda bashi da Amfani Allah ya bamu ikon watsi da shi Ameen.
Wannan Novel nayi delay wajen typing fans ayi min afwa,Inshallah Allah next Wk zamu fara sabo Wanda idan aka fara inshallah sai an Gama Babu Bata lokaci.
Kuyi min afwa time ne bana samu.
Masoyana Ina Miko gaisuwa da ban gajiya Allah bar zumunci.
Sabon Novel dina Next wk Inshallah
🏕HADIN KAI🏕
Wannan Novel akwai Comedy,love da Kuma fadakarwa,labarin me Dan tsawo ne.masu karatu aje a huta a dawo a sake bude sabon shafi.sannan Fans zaku Sha kyautar page ga masu Sharhi.
Allah ya nuna Mana da Rai da lfy.
😍😍😍😍😍😍😍😍😍😍😍💋
AsmaBaffa.
[7/22, 1:14 PM] Sis Asma: 🍱🍱🍱
JIN DADI SABO
81-90
Official
By
AsmaBaffa
AUTA tawa,DIYAR KATIBI, SAMEERAN GAYA,MARCYCOOL,ASYCOOL,HUMAIRA,JANNAT and JIDDA ZARIA
Yanzu kun girmi a baku page sai gaisuwa da jinjinar ban girma.
MASU SHARHI DA GODIYA wannan page naku ne fans.
Niima wacce ke zaune tana shayar da yarta,Hawaye suka zubo Mata tare da tausayin Khadija yarta gata Bata hanyar halak aka same ta ba ga Kuma ubanta mutumin banza,Momee tace Dana sani yanzu kin fara gani Niima tunda har kika zubar da mutunci a gari,Allah ya taimakemu ma da Ahleef da tuni talauci ya baibayemu,gashi yanzu Ahleef shine gatan mu a duniya rayuwa Kenan baka San me taimakonka a rayuwa ba.
Wanka Ahleef ya dauka sosai kamar zai je Dinner, sanye yake cikin wata shadda Yar gaske ta gani ta fada fara tas,yasha takalmi da hula,sai ka lakace wajen kallonsa ka kasa dauke Ido a kansa sabo da haduwarsa,Fitowar Shukura a kitchen kenan sanye take cikin English wear pencil tight blue trouser da rigarta pink color, gashinta yasha gyara da ribbom ba dankwali a kanta tana Kamshinta me dadin gaske ta Kara wani haske da Yar kiba tana sheki da walwalin kyau, tana sauri zata je wajen me gidanta,taganshi Yana sakkowa daga sama kamar wani basara ke Yana latsa makekiyar wayarsa da key din mota a hannunsa,gaban Shukura ne yace wani dummm ina zaije Kuma Haka ga yamma tayi Haka,Ido suka hada ya Mata wani shuumin kallon dake sumar da Shukura.
Ido ta lumshe Masa itama Bata fasa Hawa saman ba shima Bai fasa sakkowa ba so yake ya tsokaneta kawai sai yaki kulata ya raba ta gefenta ya wuce ya sauka kasa, har tayi niyyar kyaleshi taga baza ta iya jurewa ba sai ko ta sakko da sauri tace Ina zaka je ko magana Babu kamar muna gaba da juna? Murmushi ya saki yace sorry Honey sauri nake zanje gidan Farhan tunda yayi aure ban koma ba sai masifa yake min,zan biya gidan Momee na gansu.
Tunda Shukura taji ya ambaci gidan Momee sai ta hade Rai tare da Shagwabe fuska zatayi kuka tunaninta kawai Niima da Ahleef zasu hadu, Yaya dai Honey ko Zaki je muje tare da sauri tace ae zanje a tafi Dani,a ransa yake ta dariya yasan kishi ne kawai yake damun Shukura,da sauri ta haura sama kamar walkiya tayi wanka sharp sharp,Mai ma hannu da kafafu kawai ta shafa sannan ta dankara wani material me arnen tsada da kyau black and white,takalmi da Jakarta harda mayafi ma same color,powder ta shafa da Dan jambaki ta zizira kwalli a idonta abinka da me kyau sai gata ta fito wani das tana kamshi.
Mamaki Ahleef yayi abinda Shukura sai ta Dade Bata Gama shiri ba Amma yanzu gata 30mnt ta shirya ta fito,hannunta ya rike Yana Wasa dasu tayi Masa kyau matuka, Yar Jakarta ya karba ya rike Mata hannu suka fita,yau ba ruwansu da Driver ko escort shi zaiyi Driving da kansa.
Sai da ya bude mota da kansa ta Shiga sannan shima ya Shiga yaja suka bar gidan,Basu tsaya ba sai Gidan Farhan,Fatima na bude kofa taga Kawarta Shukura da matukar murna ta rungumeta kamar zasu Fadi,Ahleef yace yi min a hankali da ita pls karta Fadi ki jawo min,Dariya Fatima tayi kadan tace ayi Hakuri sannan suka zauna, gaba daya Shukura da Fatima suna zaune a 2seater.
Farhan ne ya fito daga kitchen dauke da plate da cup a hannunsa,Bai San ma Sunyi Baki ba,Yana fitowa yasha mamakin ganin Ahleef da Shukura, Ahleef yace to rufe bakin Yar talatuwa Kai Mata abincinta sai ki dawo,Dariya Farhan ya Shiga yi wlh baka da mutunci nice ma talatuwa din? to ba nata bane nawa ne bare kace, Shukura tace an dai kamaka zaka waske,Fatima tayi Murmushi tana Jin kunya tace to idan ma nawa ne Ina ruwanku Wai,Kuma ma mene a ciki,
Farhan dai da Yar jallabiyarsa tsangalalliya irin ta sabon Ango Yana hutawa ya zauna kusa da Ahleef suka tafa sannan suka tsunduma hirar duniya,Shukura Suma suna tasu Bayan Fatima ta kawo musu kayan ci da Sha,Gaskiya gidan Farhan ma ya Hadu karshe, Shukura ta zunguri Fatima suka tashi tsam sukayi Bedroom din Fatima tare da zubewa bakin Bed,Fatima ta kalli Shukura tace Shukura wlh ki yarda da maganata ciki ne dake kamar,Shukura tace ke bani da komai fa mutane ke ganin Haka,Gashi dun kin Kara fari da kiba komai naki ya karu,tabe Baki Shukura tayi tace Jin dadine kawai ki yarda Allah,kin San Hero na Yana ji dani.
Yanzu to tsuminki Zaki bani ko ki koya min mazan Nan naci garesu Farhan baya Bari ina Hutawa ko yaushe cikin yi yake,Murmushi Shukura tayi irin tsohon hannun Nan tace Zaki Saba ne yarinya Ni banga qbin naci da damuwa ba wannan abin dadi Haka to Ni wlh watarana Nike jajibo kayana yanzu idan ba ayi ba kullum bana Jin dadin duniya, Fatima ta bude Baki tace ke ko Harija ce to wannan jaraba haka, Ni bana so wlh,Shukura tace tab zauna Ni yanzu tafiyar kwana daya bazan iya ba gwara Ina kusa dashi,Ni Umma ke hada min Amma tana koya min wasu ma Ina yi da kaina,Bari zan koya Miki on WhatsApp sai Kuma zansa Umma ta Miki naki kema sai ki Aiko a karbar Miki Amma karki Bari ya gane kina yi, Fatima tace ai bazai sani ba dama hauka nake, Shukura tace harfa na maza Ana hada musu idan kina so kiji mijinki zam zam shima kina bashi kalar nasu na maza da Kuma na yayan itatuwa ingantattu,ba kawai kiyi ta gyara kanki ba shi kuma mijinki ba cikakkiyar lfy sai ku cutu,idan baya gamsar dake ma Zaki iya dinga hada Masa wasu fruits juice da abun sai ya shanye Bai sani ba ai idan sau goma kike a Rana shi zai iya dake, dariya Fatima tayi ke Dan ubanki Ina kika San salo haka? Umma ce wlh take nuna min hanya Amma ta dabara Ni Kuma sai na dau haske,gaskiya kinyi dacen suruka,Shukura tace aifa Kam Alhmdllh.
TV ce a room din Ana wani American film suka fara xxx a film din dama su ba kunya,Shukura tace ke kashe wannan abin karki sa yanzu na dauki Mijina mu koma gida,Fatima ta sheke da dariya tare da furta Amma maitar taki tayi yawa da gaske kikeyi,Shukura tace to mu fulani masu lfy ne,lafiyayyu ne mu,uhm naga Alama cewar Fatima.
Tare sukayi sallar Magrib su Kuma mazan suka je masallaci,Yana dawowa Ahleef yace Shukura ta fito su tafi,Fatima tace to Ni me zan Baki Shukura me kika gani kina so a gidana na Baki? Shukura tayi dariya sannan tace babu Hajiya Amarya mun wuce mu,har Mota suka raka su sannan suka dawo gida,su Kuma suka wuce gidan Momee.
Sallama sukayi a Palon Niima ce da Latifa zaune suna yiwa jaririya Wasa,tunda Niima taga Ahleef hankalinta ya tashi ta rasa ma Ina zata sa kanta sabo da murnar ganinsa,matukar so take yi Masa marar misali,Shukura ta koma jikin Ahleef kusa dashi ta makale kafin Nan suka gaisa dasu Niima faran faran,Latifa tace Bari na Kira Momee,Niima tace Shukura ya gida har yau Baki fara University ba? Cike da Shagwaba Shukura ta furta har yau nace ya kaini yaki sai sanda yaga dama,Ahleef kamar baiji su ba Yana Danna waya abinsa har Momee ta fito tana Shukura yau ma dake aka zo Ashe? Ae Momee Ina yini suka gaisa sosai har da Hira, Ahleef ma Haka,Sultan da Suhail suka shugo Ana ta hirar bikinsu ya kusa.
Niima in Banda kallon Ahleef ba abinda takeyi kamar zata Hadiye shi,Shukura tana kallonta duk abinda takeyi,hankalin Shukura duk ya tashi ta gama tsorata da Niima kamar Mayya.
Sultan yace Shukura yau lfy kike kuwa naganki so silent? Murmushin yake tayi tare da cewa lfy nake na gaji ne kawai, Murmushi Momee tayi tace tashi ku tafi gida Ahleef tunda ta gaji, kyaleta Momee sai munyi sallar Isha sai mu wuce, Shukura tana ji tayi Shuru da ita, Sultan sunje Masallaci sun dawo Suma su Shukura gaba daya Sunyi sallah ta dauki Yar Niima tana Mata Wasa Momee tace kowa yazo a ci abinci, a gidan suka ci suka Sha sannan yace tazo su tafi,kamar jira takeyi zumbur ta mike suka musu sallama suka tafi gida.
Ahleef kullum Kara kaunar Shukuransa yake yi suna zuba soyayya kamar zasu cinye juna har Allah ya kawo bikin su Suhail,an fara biki an Kare lfy ansha shagali ko wanne an Kai Masa Amaryarsa radeden gidansa da suke makwafta da juna,Ahleef da Shukura Sunyi rawar gani a bikin kusan komai Ahleef ne ya dauki nauyinsa.
Latifa Allah ya taimaketa a bikin ta samu wani Matashi cikin abokan angwaye Yousuf nutsatse shima da yayi shaye shaye Allah ya shiryeshi ya tuba Babban likita ne soyayya ta kullu tsakaninsu me karfi.
Hafcy tare da kannenta su Zahra aure suke so suyi yanzu koma waye sunce aura zasu yi,Amma Babu namijin dake neman su bare suyi auren duk sai na banza,Mama da Alhj Adamu suna ta Shiga cikin manya Akan a fitar da Mubaraq,Allah ya taimakesu Kuma wani abokin Alhj Adamu Asp ne ya Shiga case din Nan da kyar aka San yanda za ayi tunda kasar tamu cin hanci yayi yawa sai talaka ake kamawa a kulle Amma yaran masu kudi ko kisa sukayi ruwa Tasha.
Mama da Mijinta tare da su Hafcy murna sukeyi Mubaraq ya fito,gaba daya ya rame ya lalace ga uban duka da yaci sai Asibiti aka wuce dashi,Bayan komai ya lafa Mama tace Lallai ya shirya yaje yaga yarsa Khadija,mamaki,da tarin kunya suka rufe Mubaraq,Dana sani ya fara yi Yana zub da Hawaye, Mama ta mike tare da Shiga dakin Alhj Adamu daga kofar taji Muryar Mijin nata Yana waya da likitansa yace Doctor bazan iya fada Mata Ina da HIV ba,Idan taji da matsala,Doctor yace ya kamata a gwada ta idan tana dauke da ita a daura ta a magani,Wlh nayi mamakin ace Ni Alhj Adamu da Hiv,Sai da Momee ta Gama Jin komai Sannan ta banka cikin room tana kuka.
Rasa ma me zata ce tayi sabo da bacin Rai kawai ta zurma Hijab ta figi Mota sai asibitin kudi hankalinta a tashe,test din HIV akayi Mata sai ko gata dauke da cutar itama a jikinta,sai da aka gwada ta different Hospitals Kuma duk possitive ya nuna tana da cutar, Mama ta barke da kuka a asibiti cikin bainar jama'a tana kuka Ana Bata Baki da kyar wani Dattijo Babban malami ya sata a gaba da nasihohi masu ratsa jiki sannan taji sanyi a ranta har ta mike ta samu kwarin gwiwar zuwa a daurata a magani ta tafi gida. Ko data Isa gida yaranta ta Tara kaf har Mubaraq Wanda ya rame sabo da talaucin da yake ciki ya Saba rike kudi sabo da duk dukiyar dasu Momee suka bashi ya karar da ita ta hanyar safarar kwayoyi etc.
Mama tace tofa yarana duniya Dole mu dawo mu bita a sannu,mun shuka Abubuwa Marasa kyau gashi yanzu muna karbar sakamakonmu tun daga Nan duniya ku daure ku Mata kuyi aure tun muna Raye kafin lokacinmu yayi domin mu tamu ta Kare, Mubaraq Kaine Babba ka samu ka koma wajen wacce ka yaudara tare da dirka Mata ciki ka aure ta Haka tunda ta haihu ku hada kanku ku raini yarku Ni Nan da kuke gani na da gawa kuke magana tawa ta kare.
Hafcy ta fara zub da Hawaye tace Mama bamu gane gawa ba,me yake faruwa ne,Hawaye ya tsiyayowa Mama sannan tace Dole na fada muku cewar muna dauke da cutar HIV daga Ni har Babanku,ya dauko Mana cuta ya jona min, Palon ne ya rude da kuka,ba abinda kake ji sai kukan Yan Mata sun hada Kai suna rairawa,Ana Haka sai ga Alhj Adamu ya shigo ya samesu Haka,wuri ya nema shima ya zauna Yana tambaya lfy,Mama ta zuba Masa Harara sannan tace Allah ya Isa tsakanina da Kai,ka cuceni ka shafa min cuta fasiki ba abanza ba Ashe Mubaraq yayiwa wata ciki Ashe Kai ya gado algungumi,Mubaraq Wanda tsabar bacin Rai sai yanzu ya iya magana da Mama ya Isa Haka koma mene ya rigada ya faru sai yafiyar Allah data mutanen da muka zalunta kawai zamu nema.
Washe gari Niima tana zaune a Palo Me gadi ya shugo yace tazo tayi bako,Mamaki ya kamata waye Kuma Haka ta daure ta gyara kanta ta fita dauke da yarta Khadija wacce tayi wayo bulbul da ita,Mubaraq ta gani jingine jikin mota har zata juya sai ta fasa ta Karasa kawai tare da sallama,Sai kallon Khadija yakeyi da gani yarsa ce wani son yarinyar da kaunarta ya kama shi,hannu ya Mika Aiko Niima ta Mika Masa yarsa,ya dauketa Yana ta wani murna,sai da ya Gama Mata Wasa sannan ya durkusa har kasa Yana me bawa Niima hakuri akan laifin daya aikata Mata,tana Jin Sa har ya Gama, ba wani jayayya tunda itama tasan tayiwa wasu laifi Kuma sun yafe Mata kawai tace na yafe maka, wajen Momee ta rakashi.
Momee Bayan sun gaisa ya fara neman afwa, Momee ma tasan itama tayiwa wasu laifi an yafe Mata Babu ja tace na yafe maka kuma kudi ba rokar mu kayi ba Ni na kasa tunani me kyau na baka, duk hakkin Ahleef ne ya kama mu.
Mubaraq yaji dadi sosai anan yace zai auri Niima,Har Niima tace A'a Momee tace ba damuwa idan ya shirya ya tura Manyansa.
Haka kuwa akayi Bayan wasu lokuta Mubaraq ya turo Manyansa aka sa biki Nan da 3months.
Alhj Adamu ya damkawa yaransa kaf Dukiyarsa su suke juyawa su Kuma suna kula da Shan maganinsu,gaba daya gidan sun nutsu sosai Sunyi hankali,Mubaraq kuwa suna soyayyarsu da Niima yayi wani kyau da kiba abinsa, tunda Shukura taji labarin auren Niima hankalinta ya kwanta tafi kowa Murna.
Shukura ce zaune ta rike Mara tana Mata ciwo,ga Ahleef Yana Office,wayarta ta jawo a hankali tare da dannawa Ahleef Kira,Yana dagawa yaji Muryarta wata iri,da sauri yace lfy? Kuka ta fashe Masa dashi,zumbur ya mike ba tare da Bata lokaciba ya bar Office ya figi mota sai gida,Yana zuwa tun daga waje yake faman kwala Mata Kira har ciki ya isketa tana murkususu.
Shi bai taba ganinta cikin wani Hali Haka ba,daukanta yayi Yana me ya faru da ke? Me kika ci, da kyar ta furta ka kaini asibiti zan mutu,Bai jira ta Karasa ba yayi waje da ita a mota ya sata ya Shiga suka tafi da gudun tsiya, Allah ne kadai yasa Bai tafka hatsari ba don Yana tuki Yana kallon Shukura hankalinsa tashe shi yasan Bata da ciki bare yace ko shine zai zube, kukan da take Yana Kara tayar Masa da hankali,gani yake kamarfa mutuwa ma zatayi,Nan ya fara Hawaye shima har suka Isa asibiti na kudi me tsada,da kansa ya Saba Abarsa a kafada yayi ciki da ita yana Kiran Doctor, kafin kace me har an bashi daki dake na kudine ba Bata lokaci aka fara dubata cikin gaggawa, suna gwaje gwajensu aka gano Shukura na dauke da ciki har na 2mnths, doctor ya tambayeta me kika Sha? Ko kinci wani Abu? Shukura tace zobo kawai Tasha marar sugar dake dama tana yawan Sha,Doctor yace ae to shine ya Baki matsala karki Kuma Sha sai cikin yayi kwari ya Kai 7mnths sabo da Zobo marar sugar Yana wanke dirty na mahaifa idan mace ta tafasa da kaurinsa ba sugar Tasha suna Gama jimai da mijinta to zai wahala ta samu ciki sabo da zai wanko ko mene da yake Zama a mahaifa,Haka masu ciwon Mara na period ko shaaawa idan tayi karfi tana sa ciwon Mara to suna Shan Zobo ba sugar su tafasa yayi kauri Kar a tsuga Masa ruwa,Yana magun guna da yawa ga Karin jini etc.
Nan aka yiwa Shukura abinda ya Dace ta dawo normal kamar ba ita ba,ba abinda ya sata farin ciki irin yanda aka ce tana da ciki,Ahleef Yana waje Yana jira yaji result duk hankalinsa a tashe,Magunguna doctor ya rubuta musu sannan yace Shukura ta fito su tafi an sallamesu Amma Nan gaba zata Fara zuwa awo, da murna ta fito,Ahleef tunaninsa Doctor ne sai ya fara ganin Shukura ta fito Doctor Yana bayanta.
Farin ciki ya lullubeshi Likita ya Masa bayanin komai Ahleef sai da yayi sujjadar Godiya ga Allah,Yana ta murna Shukura ta samu ciki,itama Murna takeyi suka tafi sai da ya tsaya ya siyo magun gunan sannan suka wuce gida,part din su Umma yaja ta suka Shiga,Umma tana kitchen taji Shugowarsu ta fito tana cewa ku Kuma daga Ina ko anguwa zakuje? Ahleef Yana Murmushi tare da Sosa Kai yace daga asibiti muke mararta ya fara ciwo so muna zuwa Ashe ma Wai ciki ne da ita har wata biyu, Murmushin Jin dadi Umma tayi tace Alhmdllh Allah ya raba lfy,Shukura kunya ta kamata duk ta kasa sakewa. Baba ne ya fito da niyyar fita sai yaga su Ahleef a zaune suna kallo a Palon Umma, gaisawa sukayi ya zauna sukayi Yar Hira sannan ya fita, Umma bin Bayan Baba tayi a compound ta sanar Masa Shukura nada ciki,Murna ta kama Baba shima Addua ya kwarara sannan ya fita cike da farin ciki.
Shukura tana zaune ta zame tare da kwanciya saman cinyar Ahleef suna kallonsu Yana shafa gashin kanta Umma kuwa tana kitchen abinta.
Ahleef a hankali yace na kusa Zama Dad,Yana shafa cikinta,Shukura ta dago kanta suka hada Ido tayi Masa wani fari da Ido tare da kashe Masa Ido daya a hankali tace karfa Umma ta fito zamuji kunya,tashi to mu tafi part dinmu baza a takura min ba,Kafada ta make tare da cewa nakiya kamshin girkin Nan nake son Shaka Kuma so nake ta Gama naci sabo da tun yanzu shaawarsa nakeyi, Murmushi yayi to Bari na koma Office dama ban Gama abinda nakeyi ba,dariya tayi tace ai ka dawo kenan yau sai Kuma gobe idan Allah ya kaimu, cike da Murmushi yace kin Gama maidani Mijin tace ko Honey? Yatsunsa take Wasa dasu ta danyi dariya kadan, har Umma ta shirya Dining ba tace su suci ba suka koma Dining suka zuba abinsu suna Santi suna ci sai da suka ji su dam dam sannan suka tattara suka koma part dinsu tare da bude sabon shafin soyayya suna ta jiyar da juna dadi.
Bayan wata biyu bikinsu Niima da Latifa Yana karatowa,lokacin kuma Ahleef ya Kai Shukura Private University dake garin Abuja tana zuwa hankali kwance,yayin da cikinta ke Kara girma. Shukura ce ta dauki nauyin gyaran jikin Niima da Latifa,Ahleef Kuma shi ya musu kayan daki na gani na fada,Mubaraq matukar Dana sani yakeyi da yarsu an haifeta Bata hanya me kyau ba,Niima ma Haka kamar auren Igbo ko Yoruba sai an haihu sannan ayi biki aje da Dan dakan daddawar Miya.
Haka suka hakura da juna za ayi aure da dadi ba dadi a rufawa juna asiri.
AsmaBaffa
COPY BY ZAINAB BUTALAWA
No comments