Recent Updates

Intisaar Book 1 Complete

 


INTISAAR BOOK ONE

.

Khaleesat haidar.

A gajiye ta shigo gidan hade da kullo gate, ta

nufi sashin su ba tare da ta kula da mutanen

dake tsakar gidan ba, bare ta gaishesu,

"lallai

yarinya nan kin rika... Ta juyo da sauri tare

dadawowa da baya tace "kuyi hakuri ban kulabane

wallahi, ina yinin ku?" wata farar mata mai

matsakaicin jiki tana linke kayan shanya tayi

tsaki hade dace "ai bamu ba, wataran mahakaxaki mance da uwarki, munafukar Allahkawai,

bace mana da gani, ta tsunkuyar da kai takasa

wucewa, don ita har ga Allah hankalinta nebayawajen amma tasan baxata iya fidda kantaba.

Dan haka kawai sai ta kara maimaita "kuyihakuri"

kawai. Tabe baki ta xaunen tayi tare da mikewa tace "banxa Agola kawai, tayi sashinta tashigetare da banko kofa, itama farar hakan tayimata

hade da cemata shegiya tayi nata sashin.

Jikintaa mace ta karasa palon nasu, momynta dake

kwance tana karatun Adduo'i, ta dubeta bata ce

komai ba ta kau da kanta, ta nemi guri taxauna

tare dacewa " ina yini momy, momy ta mikexaune tana dubanta tace me ya faru

Intisaar? Ta

kirkiro murmushi tace bakomai momy, batasakecemata komai ba, sai ca tayi "ya mai jikin?"

tacejiki da sauki sosai, hajiyarsu tace kila gobema asallamesu daga Asibitin, momy tace "to Allah

yasauwake, kiyi sallah ga abincin ki can arufe,"

tace to sannan tashiga bathroom tayi alwala

tafito, tana idar da sallan ta jawo abincintata fara ci, "momy ina ihsaan,? Momy tace taje

kitso

tare da mikewa tashiga bedroom dinta,

Intisaar

na gama cin abincin ta fita da kwanukan ta

dawo, ta watsa ruwa, sannan tace wa

momy ta

tafi wajen Innah. A hanya suka hadu daZainab,

Zainab ta dubeta tace "har kin dawo dagadubiyan?" eh na dawo daxun nan, ban madade dashigo wa gidan ba, tana magana ne tana

tafiya,

Xainab ta dan kwala mata kira hade dacewa

"wajen innah xaki ne?" eh can xani me yafaru?

Ok kice ta bani dambu na, dan daxu kursumtace

min ta siyo mata dayawa, intisaar tace tokixomuje mana, "aa Hajiya ta aikeni ne " toshikenan

idan ban manta ba xan karbo maki, xainab taharareta da wasa tace "xaki gane kuranki nekuwa

idan kika manta" intisaar bata ce komai ba, ta

wuce tana dariya. Cikin gidan innar tasutake,

dan babban gida ne na gaske. Tana isasashin

innar ta ganta xaune a bakin kofar falonta, tanakulla magunguna, intisaar ta hade rai tace"wai

innah bakya gajiya da daure daurenmagungunada kunce kuncensu ne, innah ta hade raiitama

tace "to dan gidanku ba duk dan saboda kunakeyiba" intisaar ta gyara xamanta tace "to ina

dambuna da xainab innah? Da sauri ta juyotanaduban intisaar din tace "oh ni Rahmatu

nashigauku, to yanxu uban wa yace maku na siyadambu,?" intisaar ta tabe baki tace "cinye

kayanki innah, sannan ta mike ta shigepalon tayikwanciyarta." daga waje taji innah na cewa

"inatakwarata?" ta yi shiru kamar baxata amsa ba,

Saikuma tace "tana wajen kitso," to meyasabakikawota nayi mata ba.? "Ke har wani kitsokika

iya innah.?" innah bata sake cewa komai bahartagama abinda takeyi ta shigo parlon. Sunjimasuna hira da inna, har aka kira maghrib ta yi

salla,

sannan ta diba abincin da fadila ta kawowainnahtaci. Ba ita ta bar sashin innah ba sai wajen

karfe goma saura, bayan ta dibar wa xainabdambunta itama ta debi nata, tayi mata saidasafe ta kama hanyar sashinsu, duk da tsakargidan da haske sosai dan ko ina kwan fitila

ne.

amma gabanta faduwa yake yi sosai,da sauri ta karaso gida ta bude kofa ta shige tare dakullewa, momy ta dubeta tace " ke da waye

haka,?

Tayi dariya tace bakowa, momy tace to yayi.

Washegari bayan sun karya ita da kanwarta

Ihsaan suka je goudan Abba, yana xaune aparlonsa yana sauraren labarai suka shiga,

kursum na xaune a kasa ta hade rai, daalamarabu take jira. Ya amsa masu yana murmushi, ya

dauki ihsaan yace "mamata yau kin tashi da wurikenan, sannan ya dubi intisaar yace ke kikayimata

kitso ko inna? Tayi dariya tace a’a saloonakayimata," to yayi kyau, ya dubi kursum yace"yauwa

ina jinki, Tace dama Abba gyaran gashi xanje asaloon, yace nawa ne? Dubu biyu ne Abba,

yaxaro ya bata, sannan ya dubi intisaar yaxaro

dubu biyun ya mika mata yace "ke ma kigyaragashin naki, sai kuje tare," tayi murmushihade

da godiya, kursum ta dubeta cikin tashin hnklidatakaici, sannan ta mike tace ngd Abba, ta

fice.

Intissar ta da da yi masa gdya sannan takamahannun kanwarta suka bar parlon. A hanyasukahadu da Hajiya tsaye suna jiranta, gabnta yyi

mugun faduwa, ta daure ta karaso bakintanarawa tace "ina kwana hajiya.... Ido ta xaromata

tace "ban kwana ba dan ubanki, da sauriIntissarta mika mata dubu biyun dake hannunta, takarbe

kuwa, sannan tace "bnxa kawai, sukayigaba daita dasu kursum, kursum tayi mata gwalotare da

fashewa da dariya, ita dai bata ce komai bata

kama hannun kanwanta suka yi sashinsu.

Ihsaantace, "amma anty ai ke Abba ya ba wa kudinkika

basu?" intisaar tayi mata murmushi tace ai nasu ne dama, sannan ta ja ta suka shigepalor.

Momy na shara ta karbe ta karasa sannan

ta gyara gidan, ta kwaso kayanta tana guga.

Ihsaan na jikin momy suna kallo, tace

"momy,daddy yace kitso na yyi kyau wai, momy tayimurmushi tace "sosai ma kuwa" intisaartace

"nima ae irin shi xanyi," to ba kin ba sumomynanty Xainab kudin ba, momy ta dube intisartace

"wani kudin?" nima bn san mata ba. Ihsaan tace Abba ne ya bata two thousand yace tayikitso

shine momynsu khadija ta karbe, momy tamikeba tare da tace komai ba ta dauki hijab tace"idan kin gama gugan ki dauki kudi ki siyogolden

morn tun daxu ihsaan take so kuma bbu, ni

xanje

na gaida innah, ihsaan ta mike tace momynimaxan biki, eh dama tare xamu ae daukohijabin ki,

suka fice tare. Intisaar ta cigaba da guganta. xainab ta shigo, ta dubeta tace inadambuna, saida ta ja mata rai sannan ta dauko ta bata

tanadariya, xainab tace amma ke kka dibar minko?

Eh nima ga nawa can, xainab tace shiyasanaganshi dan kadan, intisaar dai bata ce matakomai ba ta karasa guganta ta kashe dutsengugan ta kai kayan daki, ta dawo ta dubixainab

tace yau baxa kiyi kwalliyan friday bne? 

Tace "uhum bari ma ki ga, aikena pa hajiya tayi.

Tayi hanyar fita, intisaar tace ina xaki,?

Supermarket!

Tace ba tare da ta kalleta ba, tace jirani nimaxan siyo golden morn yanxu, ta daukokudin da

hijab suka fita ta rufe kofa, xainab tacemomytana wajen innah ne, yea tana can, sukakamahanyar supermarket. Da kafa suka taka dan

bawani nisa sosai, sai da intisaar ta rakatagidansukawarta dake Area din ta karbo litattafaisannan

suka kama hanyar gida. Umma suka gani atsakar gidan ita da 'yar ta Rahmatu tanamatatsifa, intisaar ta gaida ta, bata ko kalla indatake

ba bare ta amsa, ta dubi xainab tace ke danubanki ba aikenki hajiya tayi ba kika biwannangantalalliyar ku ka je gantali koh? Xainab tayatsine fuska ta danyi tsaki ba tare da tace matakomai ba ta nufa sashinsu, intisaar taisashinsuita ma da saurinta.

... Tana shiga parlonsu ta tar da ummanta

tana shiri xata fita, tace "momy ina xaki?"

momyba tare da ta kalleta ba tace "inda kikaaikeni"

sai da ta gama shirinta tsaf sannan tacexasu je

dubiya da innah... Wayan intisaar yyi kara tadauka tana cewa "kar dai har kun dawosamira?"

daga can bangaren samira tace nace makiaetare xamu, ni ga ma ni a gate dinku kiyimaxa kishirya, tace mata "Allah karki ba kankiwahala ni

bbu inda xani, ta kashe wayan. Momy tadubeta

tace ina xaku, "wai dole tare xamu gidanMaryam

kuma nace masu baxa ni ba, momy tace"waimaryam da akayi bikinta?" eh ita... Aa bakikyauta ba intisaar ayi bikinta ki ki xuwakumayanxun ma kuje gidanta kice ba xaki ba, ki

dauredai ki shirya kuje, amman karki dde, ni natafi. innah tana jirana, ki tabbatar kin kulle minkofa,

tace"to momy Allah ya kiyaye, a bakin kofatahadu dasu samiran suka gaisa sannan tawuce.

Ba dan ranta ya so ba ta shirya suka bargidan,

suna ta mata tsiyan bbu wanda xai xo

bukinta,

ita dai murmushi kawai take yi dan bata dalkcnsu, karfe sha biyu suka iso gidanmaryam,

tayi murnar ganinsu sosai, amma sai tahade waintisaar rai, da kyar intisaar ta shawo kanta, tana

dariya, dan tasan bata kyauta mata ba tundabata je bikinta ba. Ta cikasu da kayen ciyeciyeda soft drinks, lkcn sllh nayi suka yi gaba

dayansu, sannan ta kawo masu abinci sunacisuna hira. Daga bisanni intisaar ta basuuxurintana cewar xata wuce gida dan momy batanan,

maryam ta fahimce ta dan hka tayi matagdyanxuwan da tayi, intisaar ta hada ta da dubu biyu

ta amsa da kyar sannan ta bar su samira agidanta wuce. A dai-dai gun da xata hau motaummi

ta kirata, ta dauka tana cewa ummi ansallameku

ne, ummi tace "eh yanxu ma xamu wucegida, cama nake xaki xo intisaar, intisaar tayimurmushi

tace "to bari na taho ina hanya dan munjegidan

maryam." tana isa hsptl ta gaida nurses dindakereception ta haye sama taje ward din daummin

take, cak ta tsaya a stairs din gabanta na

faduwa, kamr warce aka hankado ta juya dasauri ta fara sauka, da sauri ya bita har sukasauka kasa ya maxa ya shige gabanta yace"meye kika gudu 'yan mata, nayi laifi ne,

fuskartaa daure tace a'a ta juya ta haye sama, jin ya

biyota ne ya sa ta tsaya, ya karaso yace "yakika tsaya kuma, bata ce komai ba tayi hanyarward

din kawarta yana biye da ita. Xaune tagaummi

tana duba Novel, ta karaso, shima ya shigodakin,

gefen ummi ta xauna tana ce mata ya jikin,

taceda sauki ya su mummy? Ta daga kanta dasauri tace doctor dama ka shigo, yyi murmushi

yace

"yea, kin warware sosai yanxu ko? Tace "eh

nagode Dr. Yace no probs wannan kawarkice, tadubi intisaar tace eh, yace hmm.., what's her

name? Ta dubi intisaar da tayi kmr ma batasansuna yi ba tace "Intisaar sunanta" waww..

To menayi maki intisaar tun jiya kke guduna, itadaibata ce komai ba sai wayanta da take

dannawa,

yyi murmushin karfin hali yace o.k , am srrytoidan ina damunki, tace "o.k" sannan ta dubi

ummi tace momy pa, ummi tace "sunje kirantaxi

ita da su falmata yanxu xamu wuce dama." Shikam juyawa yyi ya bar dakin, intisaar ta danja

tsaki, ita dai ummi bata ce komai ba. Karfeukusuka bar hsptl din, bayan ummi taje tayi maDrfaruuq godiya dan yana da kirki sosai, takuma

maida masa Novels dinsa da ya bata takekarantawa, sannan ya nemi alfarman tabashinmbr intisaar bbu musu ta bashi yyi mata

gdya.

Har bakin taxin ya rako su, momy ta sakemasagdya sannan ta shiga motar, suka kamahanyargida.

Yau wajen sati uku kenan, kullum sai Dr,faruuq ya kirata, wani lkcn ta dauka, wanilkcn taki dauka dan ko ta dauka bashi da watamgnar

da ya wuce ta amince masa, ita kuma yanxukam ba abinda ke gabanta ba kenan.

Ummi ba mata adalci ba da a bashi nmbrta, kuma taje har

gidan nasu ta nuna mata bata ji ddin hknba.

Suna xaune da momy suna kallo da daddareyakirata, ta mike ta shige daki da sauri danbatasan ta jawo hnkln momyn tata, ta daga, taji

Yace"intisaar, tace ina jinka, murya can kasa yacemata " bni da lfya yau, sosai ki mani addu'akinji,

tace "xan mka Allah ya sauwake, yacenagode.

sai da safe, tace tam. Tana fita hanyar ktchen tayi taje ta wanke kwanukan da aka ci abinciagidan dan momynta ce tayi girki, ko da takomapalonsu ihsaan tayi bacci. momy kuwa,Abba yakirasu da su hajiya yana masumagana, tana

kwantar da kanwarta tayi wanka ta kwantaitama. 

Washegari bayan sun dawo daga

makaranta, taje tayo wa momynta cefanesukashigo gidan tare da xainab, ita ma an aiketa,kayanta da ta shanya taga fadila tanakwashewa

tana xuba su a kasa, xainab tace "meye hkafadila, fadilar tace mele. Intisaar tace"meyasa

baxaki kira ihsaan ta kai mun ciki ba fadila,"fadilar tace "sbda baki isa ba," intisaar tace"shikenan nagode," kursum ta fito da sauri

tace"kar ma ki gode mana mahaukaciya kawai,

intisaar tace "nagode" sannan ta kwashekayannata xata wuce ciki, fadila ta banke ta,cukumota

xainab tayi tana cewa ke wacce irin dabbacefadila, wllh sai kin gya min me intisaar tatsaremaku a gidan na, kokuwa suka farayi, sai gauwarsu ta fito da gudunta, me ye hka?? Meya

faru, kursum da sauri tace "wancan dabbarce tahada su fada, bata bi ta kansu ba ta cafkointisaar ta dinga xuba mata duka, tana kukatace"

wllh momy ni banyi mata komae ba, ummabata

saurareta ba ta dinga jibgar ta kamranaikota

tana cewa "kaji min matsiyaciya, dan

uwarki, nandin gidan ubanki ne da xaki hada manayara fada

munafuka, tuni xainab ta cika fadila tana"waiumma me tayi maki ne, dan me baxa kitambayi

munafukar yarki abinda tayi ba to.... Tanamagana ne tana kuka, sai ga hajiya ta fitodasauri ta cafke xainab tana cewa , danubankiintisaar kanwar uwarki ce ko ubanki, kukaxainabtake yi kawai, uwar ta watsa mata mari tajefarda ita sannan ta koma kan intisaar, daga itaharumma sukayi mata tatas, da kyar ta samusukabarta ta shige palonsu tana kuka sosai,momynta

na xaune tana yanka alaiyahu. Xubewa kasatayitana kuka sosai, ihsaan ta xauna kusa da itatana

share mata hawaye, momy bata ce komai ba, ta

karbi cefanen ta wuce kitchen, tayi kukasosaihar barci ya dauketa. Da magrib momy tatasheta tayi sllh, ta bata abincin kowa ta kai

masa sashinsa, hajiya ta fara kaiwa, xainabnabakin famfo tana alwala ta karaso da sauritakarba tana cewa kiyi hkuri intisaar Allah xaisakamaki, tayi murmushi bata ce komai ba tawuce. Ta dauki na umma ta kai mata, yusuf ta ganibakin kofa ta mika masa ya amsa sannan tadauki na inna ta kai mata. Tana xaune kandarduma, ta gaisheta, ta dubeta da kyautace

"wa ya saki kuka intisaar,?" ta sunkuyar dakanta

tace "ciki na ne ke mani ciwo, da sauri innatamike ta shige ciki ta dauko magani ta jika tabata tasha, batayi musu ba ta karba ta sha,

innata xauna tana ta mita wai cikinta na ciwobaxa

ta xo ta karba magani ba tana san ta kashekanta, da kyar ta samu ta barta ta wucesashinsu. Tasan dan inna bata nan neshiyasa

sukayi mata hkn, dan da tana nan bbuwanda xaimata hka. Ko da tashiga parlonsu, momy takaiwa Abba abinci a sashinsa, ta dan ci abincitayiwanka sannan ta kwanta. Tana xaune tana

sama ihsaan rani, momy kuwa na daki tajianyisallama, da sauri ta jawo hijab dinta ta sadanyar shimi kadaine jikinta da xani, sannan taamsasllmn tana mikewa, daga wajen yashigoyana

murmushi yace ihsaan lalli ake yi, tace eh"unclesannu da xuwa," ya dubi intisaar yaceyauwa

kanwas ya momy pa, sai ga ta ta fito taceHaisam yaushe a garin, yyi murmushi yadurkusaya gaisheta, yace "da safe naxo momy,amma bn

dde da shigowa gida ba." ayya to ya hanya,? YaceAlhmdllh, ita kuwa intisaar ta mike ta kawomasaruwa ya amsa ya sha yana gdya, suna hiradamomy sai ga kursum, ta shigo ba ko sallama babu.

Tace

"yaya umma na kiranka, yace baki iya

Gaisuwabne, ta yi tsaki tace ina yini ta fice, ya bita dakallo ya kasa cewa komai, ya mike yyi yakeyace"momy da daddare xan xo muyi hira, tace toHaisam Allah ya kaimu, ya dubi intisaar yace"kanwata naga sai kyau kika karawa meyesirrin,

Tayi dariya tace "kai yaya bnda sharri, yyidariya

yace, "da daddare kije wajen inna mushahira,tace "to yaya Allah ya kaimu, sannan ya fice

dasauri dan ya riske Kursum amma har tashigegida. Yana shiga uwar tashi ta farabalbalesa damasifa, ita bata san shige shige da gantali, dagaxuwansa ko hutawa bai yi ba har yaje yawo,yyidariya yace "yau naga ikon Allah, bnda ikonxuwawajen matar ubana, A'a uwar ubanka, bamatarubanka ba, wllh ka fita harkana haisam.

Mikewa yyi yace "to Allah ya kyauta sannanyyi sashinsa yana waige-waigen inda xai gaRahma amma bai ganta ba. Da daddaresukahadu da yaya Haisam a sashin inna, sunyi Hirasosai tun suna yi da inna har ta bingire awajentana barci, Intissar ta dinga dariya, yace "tokarki

tasheta mana kanwa," tace to na daina yaya. Yace to yanxu samarinki nawa,? 

Tayi dariyasosai sannan tace "ko daya yaya," yace "kinmaidani wawa ko?" tace "lah, hava yayanawllh

a'a," yace to gya min gskya, tace "Allah yayabana kulasu, yace "to ki daina hka, wataranAbbaxai ce ki fito da miji, idan kuma baki da, xai

iyahadaki da wanda ransa yaso, dan hka, kidai-daita da mutum daya, kuma bance wai ki tarasamari ba, tayi dariya tace "to yayana," a hkaya

rakota har sashinsu yyi mata sai da safe.

Ta fitodaga wanka kenan wayanta yyi kara, sai dayakatse aka sake bugowa sannan ta dauka,

"intisaar," taji ya kirata, ta amsa ba tare datakula ba, yace "ya gida"? Tace lau, yyimurmushi

yace to yyi kyau, dama na kira ne na gaidaki,bye.. 

Ba shiri ta samu kanta da ce masa yajiki?Yyi jim, sannan yace "to da sauki, ammadaxunnan aka cire min drip, tace "to Allah yasauwake,

yace ameen ngd, sannan yyi mata sallama yakatse wayan. Washegari da ta dawo dagamkrntasai ga mis cals dinsa, ta dauka tana kallonwayan, samun kanta tayi da send din nmbr,ba

tare da ta shirya ba, ya dauka, suka gaisa,sannan da sauri ta fara kame-kame, "emmdama

mis cals dinka na gani," yace hmm, yea nakiraki

daxun, "ok naje mkranta ne," sai tayi da tasanin

kiransa ma, ta dai dake dai tace "ya jikin,"yaceAlhmdllh, daxun ma naje karban treatment,tayishiru, can dai tace "to mene ya sameka?"yace

hmm... Owwh bari na kiraki, na manta wllh,

........

Yana katse kiran nata ya kirata, "yi hkuriIntissaar, i 4got, tace o.k, sannan yace"idona keciwo," 4 d past 4 dayz yanxu,spec dina ya

Bugeni a idon, Ayya, Allah ya sauwake.. Ameen

ngd.

A hankali taji ya kira sunan ta, ta amsa tana

saurarensa, "ki bani ixini naxo gidankumana, dasauri tace "a'a karka damu, kaga bye.. Yanxu

inaaiki ne, sai anjima, ta kashe wayan. Taxaunatayi jim tana tunanin abinda ya Haisam ya

gyamata jiya, ihsaan ce ta shigo tace "Anty, innatace na kiraki, tace "to, tare da mikewa tadaukihijab, sai kuma ta tuna bata cire uniform ba,

tacire, sannan taje kiran da innah ke mata.Rahma da khadija suna wankin uniform dinsu abakinfamfo, suna ganinta sai suka tare hanyarwucewa, ta dan yi jim a wajen, sannan tace

"kugafara xan wuce, Rahmatu tace "idan anki

pa?"khadija ta kara dacewa "ko gidan ku ne

nan?" itadai bata ce komai ba sai kallonsu da ta tsaya

yi,kumfar wankin Rahmatu ta debo da yawa

ta

yarfa mata a fuska, ihsaan ce ta xo da gudutana

cewa me "me tayi maku?" khadija ta tura taharsai da ta fadi, intisaar ta kalleta cike datakaicitace "ita kuma me tayi maki khadija"?

Ihsaan

kuwa tuni ta mike tana kuka ta cire talkaminkafarta tana dukanta dashi, daukartakhadija tayia fusace ta tsoma ta cikin guttern dakewajen,

intisaar bata san lkcn da ta fixgo khadija batadinga dukanta har ta jefata cikin kwatan

itama,da gudu rahmatu na kuka da ihu taje ta kirahajiya da umma, dan suna kusa da gate axaune. Da gudu kuwa suka karaso wajen, hajiya tafara ciro 'yar tata daga ciki kwata tana salatitare da cewa "mai xan gani hka?" ummahkuwata cafko intisaar din da ta juya da gudu xatabarwajen, dukan fitar hnkli ta dinga yi mata dadukakarfinta, hajiya ma ta xo ta sa hannu, kukaihsaan ta dinga yi tana kwalawamommynsu kira,sai ko gata ta fito, ta kallesu bata ce komaiba,ta juya ta wuce abinta, su fadila da kursumduksun fito, hka aka dinga hayaniya, dukansunaxagin intisaar, "wllh sai naga bayan ku da

uwarkua wannan gidan, shegu munafukai kawai,tunda Kuka shigo gidan nan muke.... Muryar inna

dasuka ji na ya katse su, sai ummah dake tataunan cingam, "me xan gani hka Aisha?"

cewarinna knan tana duban Hajiya baki bude,ummahtace cin halin ko in kula, gata nan kitambayetamana, hajiya ta maxa tace "kashe min 'ya

xatayida har xata danneta tana duka?" innah tadubiintisaar dake ta faman rusa kuka ita daihsaan,

tace "nashiga uku ni Rahmatu, yanxu me'yar nantayi maku da har xa kuyi mata taron dangi?

Harda gore gore ina ji?" nan fa inna ta dingarusamasu kuka har da durkushewa a wajen,dagahajiyan har umma suka tabe baki, hajiya

tace "toinna da yafi da ne?" sunan momyn intisaarinnata shiga kwalawa tana cewa "zainabu,

zainabu,da sauri ta fito tana cewa "na'am inna?"inna tasharbe majina tace "ke wai wace irin sha-sha sha

ce, ynxu kina ciki ana neman kashe makiya'ya kin ki fitowa? To Allah ya isa ban yafe ba, wllhtllhsai naci uban mutum yau, ta fadi tana kallonhajiya da 'ya yansu gaba daya, Zainab ce takaraso da sauri dan dama bata gidan, tanacewa

"inna me ya faru,?" inna ta ciro wayarta dasauri

ta mikawa xainab tace "maxa ki lallubo min number Abubakar, jikinta na rawa ta saka nmbrAbbansu

ta mikawa inna, inna ta karbe da sauri tace"Abubakar maxa ka dawo gida yanxunnan,.. A'a

idan kaxo ka gani, ta mikawa xainab wayantace"kashe min kayana, sannan ta kamo hannunintisaar din ta wuce sashinta da ita, ihsaan

nabiye dasu. Tab! Hka hajiya tace cikin tashinhnkli, yanxu hadasu tayi da Alhaji sbdawannanAgolan, lallai akwai sake, nan xainab tabarsu atsaye ta wuce, momy kuwa tuni dama takomasashinta, ummah ta dinga gyada kai tanacewa

"yau munga ikon Allah agola ta fi masu gida,nansuka dinga tsakar wa momy habaici damaganganu marasu dadi, ita dai bata tanka ba

tana daki abinta, Haisam ya shigo yanadubansu,

mamaki ya bayyana a fuskarsa yace "momymeyafaru, hajiya tace "agola ce tafi ya'yanmasu

gida, yau munga ikon Allah, tsaki yyi ya barwajen kawai, ya samu xainab tana kwashekayanta, ta gya masa abinda ya faru, saikawaiyyi sashin inna, tana xaune sai rusa kukatake

tana Allah wadai da matan Abubakar, danko itabasu ganin girmanta, kuma yau tasu ta kare

agidan nan, intisaar na xaune ta xubawa TVido,

dan ita bata ga abin kuka a nan ba da innaxatadinga yi, ihsaan kuwa na lullubeda towelalamar

wanka tayi, haisam yyi sallama ya shigo,batajiraya xauna ba ta dinga jero masa abinda ya

faru,sai ka rantse kace tana wajen, hkuri ya

dingabata, amma kmr yana xugata, dan hka sai yajuya ya dubi intisaar yace "ki yi hkuri

intisaaridan Abba ya dawo xasuyi bayani, da sauri

innatace sake kira min Bukar din, ko abinda yke

yiyafi kiran nawa ne, a lkcn Abba ya shigo

gidandamotarsa, haisam yace to gashi can ma yadawo,

tashi tayi da sauri taje ta samesa, haisam yagirgixa kai ya mike ya dauki ihsaan yace"srrykinji ko bby, yau nasan ai Abba sai yyi masubulala tunda suka tabo mamarsa, dariya

kawaiihsaan tayi, sai ga Abba da inna sun shigo,

haisam ya mike ya bar parlon bayan yagaidaabban nasa, intisaar a xata tashi inna tace"dawoki xauna, sannan inna ta fara jawabinta

tanamatsar kwalla, ya ma rasa mai xai ce, kawaisaiya mike, yace "ina xuwa baba, ya fice, sashin

hajiya ya nufa direct, ya dinga kwada matakira,

Aisha, Aisha, tace na'am Alhaji sannan ta fitodasauri tana cewa lfya kke kwada min kirahka,

yace "maxa ki bar gidan nan ki tafi gidanku,danban aure macen da xata sa mahaifiyatakuka ba,bai jira cewarta ba, yyi sashin Shafa, watoumma,ita ma ya gya mata hkn sannan yace dukwandaya dawo ya samu bai tafi ba to a bakinaurensa,ya juya ya koma wajen inna, hka ya dingabatahkuri sannan ya tabbatar mata da duk suntafigida, nan inna ta samu natsuwa dan itakadaitasan irin wlkcn da matan nasa suke mata,dakuma yanda suka sa xainabu da yaranta agaba,

sai da ya tabbatar ta hkura sannan ya daukiihsaan yyi hanyar sashin su intisaar din,intisaar

ta mike taje tayi wanka a bayin inna, ko datafitosina xaune da haisam tana tayi masa mita,intisaar tace inna wllh kin cika mita, inna

tace"nayi din, sannan taci gaba daga inda tatsaya,"

da kyar haisam ya samu ya lallabata ya barmatadakin, Abba kuwa ya kira su kursum dakhadijagaba dayansu yyi masu ta tas, sannan yasasukneel down a tsakar gidan, ya tabbatarmahaifiyarsa ta sakko sannan ya komaoffice,

Su Aisha da Shafa kuwa tuni suka bar gidandansunsan Alhaji baya magana biyu.

Washegarin ranar suna xaune ita da xainab

Dr faruuq ya kirata, taki daga wa har sabiyu xainab tayi mata mgna sannan ta daga,

Sukagaisa, tayi masa ya jiki, yace "jiki da saukiintisaar, ya su momy?" tace "lau suke" ohk..Inakofar gidanku... A dan firgice tace "me?"yace

"eh".. Kaga bna san hka malam ka rabu danidanAllah, ta katse wayan da sauri. Xainab taceb"waye?" intisaar tayi tsaki tace "oho nimaina nasani, wai wani gashi a kofar gidanmu saikace nagayyato sa, wllh xan bata ma ummi rai ne, ni

Tadaina min shisshigi," xainab ta mike hadeda tabebaki ta dauki hijab, intisaar tace "ina xaki?"ba

tace komai ba har sai da ta isa bakin kofasannan tace "am cummin" sannan ta fice. KofarKofargida ta nufa, bakin gate ta tsaya tana waige-waigen inda xata hango bakon intisaar din,hardai ta hangosa jikin wani flower yana tsayeyanadanna wayarsa, ya daga kai yana kallonta....Nan

ta gane shine bakon, dan da alama waniyakejira, tace "kai ne faruuq wai?" ya dubeta dakyauyace eh nine, tace "bisimillah wai ka shigo,"yace"to ngd sosai," tare da binta har cikin gidannasu,

tayi masa iso har sashin inna. Tana xaunetasaTV a gaba wai tana kallo, xainab tayisallamahtashiga tana cewa "inna kinyi bako," innatace"waye?" xainab ta xauna gefenta tana yardariyatace "saurayin intisaar ne, wai kunyar kawomaki

shi take yi," da fara'a sosai inna ta tarbesa,tabude fridge ta kawo masa ruwa da lemotana samasa albarka, hkn yyi ma faruuq ddi sosai

yadinga gdya, nan dai inna ta dinga jan sa dahiratana basa lbrin Intisaar, xainab kam saidariyatake yi, ta mike da sauri ta barsu tayisashinsuintisaar, intisaar tana xaune tayi shiru,alamar

tana cikin damuwa, xainab tace mata "meyafaru?" tace "wllh xainab ni bna sanwalakantawannan mutumin amma yasani gaba...

Xainabtace "to kuma meye abin damuwa bayan kinkoresa?" intisaar ta tabe baki tace bbu!

Xainabtace gskya kam, inna dai tace na kiraki tanajiranki, xainab na kai wa nan ta fice ta barmata

parlon. Jikinta a sanyayye ta dauki hijab tayisashin inna, tayi sallamah, inna ta amsa dakarfinta har abin ya ba intisaar dariya, koyaufarin cikin me inna take yi hka? Duk da

takalminda ta gani bakin kofar inna bata kawokomai a kaba, dan a tunaninta ya Haisam na ciki ne,

tanashiga palon tace "ya Haisam ka min promise

ndfail ko? Cak ta tsaya ganin faruuq xaune aparlon, kanta ya dinga mata wani irin juyi takasafahimtar komai, ya dago kai yana dubantakawaiba tare da yyi mgna ba, dakin inna ta shigedasauri, inna tace "yo kunyar me xaki ji kuma?Saikawai ta fashe da dariya" intisaar taji wani

irintakaici ya lullubeta, yanxu xainab ta kyautamataknan?

Sa ta tayi taje wajensa bare har tashigodashi gidansu kuma ma wajen innarta,

Sallamanya haisam da taji ne ya sanya ta kararudewa,inna kuwa sai xuba take ta wa faruuq,

shima yabiyeta suna ta yi, inna ta amsa wa haisamsllmaya shigo, tana wangale baki tace "haisamwannan saurayin intisaar ne yaxo gaisheni,haisam ya kallesa da mamaki suka gaisa dafara'arsa, sannan yace "to ina intisaar dininna?"

inna tayi dariya tace "wai ita kunya tun daxuta shige daki," haisam ya kirata ta fito gabantana

faduwa ta nemi gefen inna ta durkusa tanagaishesa, ya amsa yana daria yace "wayewannan?" ta kalli faruuq tace "nima ban san

shiba " dariya haisam yyi yana kallon inna, shi

kuwafaruuq yyi murmushi ya dukar da kansakawai,

hka Haisam ya ci gabada xolayarta amma itahnkalinta na waje daban, tunani kala kala yakasu a ranta, da daga kai ta dan saci kallonfaruuq din suka hada ido ta kauda kanta da

sauri,hka suka ci gaba da hira gaba dayansu

ammabnda ita da ta kurawa plasma ido. Wayan

haisamda yyi ringin ne yasa inna ta dakatar dasurutunta tana tambayansa waye, salanta

knan,da taji wayarka yyi ring xata tambayekawaye dasaurinta, yace mata mijinki ne, sannan yadaga,bai jima yana mgna ba sukayi sallamah yakashewayan. Inna tace Aliyu ne ko wa? Yace "eh

shine" inna ta girgixa kai tace "oh yaronnan baida kirki, halinku ba daya ba da nashi, bai dakirkiko kadan, bai yo halin Bukar ba, halinsa saknauwarsa... Haisam ya maxa ya katse ta yace

"toxabiya, ni xanje GRA ne ynxu sai na dawo"tace

to... Amma me Aliyun yace mka yanxu,?

Yausheyace xai dawo,? yana ina ne yace mka? Kode

yana hanya ne? Cike da kufula Haisam yacekaini inna ban sani ba, ca yyi na gaida innaRahmatu kawai, sannan ya mike sukayixchange

din nmbr da faruuq, yyi masu sallama yafice,

intisaar ta mike da sauri tace "inna bari narakasa gate ina xuwa"inna tace to kiyi maxamaxa ki dawo, tace to. Sannan tabi bayanhaisam da sauri.

Haisam ya dubeta yace "saurayin naki yahadu intisaar, ta ce "bna so yayana, ni ba ninakawosa gidan nan ba, yyi dariya yace "bndakarya dai kanwata" nan ta marairaice masa

Tayimasa bayanin yanda suka hadu da faruuq Harxuwa yau da ya xo, yyi dariya sosai sannanyace

"to amma kanwata naga ai bai da aibukumayanada hankali, ki dan basa dama mana."ita daibata ce komai ba har suka iso gate sannan

Yadubeta da kyau yace "kar fa ki ki komawakanwata, kinsan dai walakanci bai da kyau,kibasa dama ku saba, tace "to yaya baxangudu baxan koma" yauwa kanwata gud of you.

Nan sukayi sallama ya wuce ita kuma ta koma

Sashininna. Suna hira har ynxu, ta nemi gefe taxauna,tana jinsu kawai sai dai tayi murmushi. Sai

Wajenkarfe shidda yyi sallama da inna, ya batakudimai yawa, ta karba tana godya, hkn yyimugunbata wa intisaar rai, kamr warce ke jiramaimakon tace ya barshi, har bakin kofainna tarakosu sannan ta koma ciki tana masa Allahyakiyaye hanya. Suna tafe ne bbu wanda yacekomai, can dai ya dubeta yace "ngdintisaar,"bani ce da gdya ba, ta fadi ba tare da takallesaba. Yace to waye? Bata kallesa ba tace

xainab,yyi murmushi yace gskya ne, bbu wanda yasake

mgna a cikinsu har suka isa gate sannan yadubeta ita ma ta kallesa, sai ya sakar matamurmushi , ta sunkuyar da kai da sauri,bata

sanlkcn da itama tayi murmushin ba. Yyi ajiyar

xuciya yace "to kira min xainab din muyisallama," aa dare yyi ka bari sai wani lkcin,

yaceba nan gidan take bane?" eh nan takeamma

ynxu ta shiga gidansu. Yace gskya ne. Tointisaar i am vry grateful, ngd sosai, tagyadamasa kai kawai sannan ya juya ya fice, ta bisa

da kallo, ya juya suka hada ido kunya yakamatatayi saurin rufe gate din sannan tayisashinsu.

Gabanta yyi mugun faduwa ganin su

Kursum labe ta windo suna kallonsu, da sauri tayisashinsu tabude kofa ta shige. Ko da tashiga ta tarar

Momybata ciki, tayi hanyar kitchen, ta ganta daxainab Suna raba abinci, taimaka masu tayi sukagama

A tare, ita ta kai ma inna nata, xainab kuwa takaima su kursum nasu, intisaar bata ce daxainab

komai ba, itama xainab din haka.su hajiya kamyau kwanansu uku basa gidan, xainab batadamuba, hka ma haisam ko a jikinsa, su kursum

dai nehankalinsu a tashe, momyn intisaar tayikkrinshawo kan Alhajin amma hkn bai yiwu ba,innakam ko a gyalenta, dan gidan ma sai yyi

mataddi. A kwana a tashi intisaar suka shaku dafaruuq sosai, fiye da tunaninta, faruuqmutum ne

mai kirki da fara'a, duk gidansu an sanshidanduk jumm'ah sai yaxo gaida inna sannan yashigaya gaida momy. Su fadila da su kursum kambakin ciki kmr xai kashesu, gashi yau wajensatiuku knan Alhaji yaki barin iyayensu su Dawo.

Intisaar ta samu kwanciyar hnkli sosai agidandan bbu mai takura mata ynxu, yawanciIdanfaruuq yaxo gidan tare suke xaunawa har

Daxainab suyi ta hira, a wajen ummanta kuwabatada hiran da ya wuce na faruuq, hka ma awajen

inna. Abba kadai ne bai san dashi ba a gida,amma har su Hajiya da umma da basa gidan

'yayansu su kirasu sun fesa masu. Yau ma kmr kullum faruuq yaxo gidansu da yake Friday ce,

wajen karfe shidda ta rakosa xai wuce sukaiskefadila da khadija a kusa da gate a tsaye, dukdasun gansu amma basu yi kkrin matsawa

dagagate din ba, faruuq dai bai ce komai ba dantundayake shigowa gidan basu taba bude baki

sungaishesa ba, shima bai taba masu maganabadukda ba ma ganesu yke yi ba, bayan ga xainab.

Dakyar intisaar ta iya cewa ku gafara dan Allah,ganin sun kusa minti uku a tsaye kuma sun Kibarin hanyar, ke din a su wa? 

Khadija ta jefomata tambayr, tayi shiru bata ce komai ba,khadija ta kara da cewa "nan gidan ubanmu

Nedan hka ba ki isa kixo ki mana iko dashi ba"saiki bari idan kin samo ubanki sai kiyi iko dagidansa idan ma yana da" fadila ta fadi awalakance tana girgixa kafa, kuka ta sakar

Masua wajen, faruuq kam kansa ya daure, ya ma

Rasame xai ce, khadija ta dubesa "bawan Allahkanabani tausayi wllh, ga ka kyakkyawa maiasali,

amma ka rasa warce xaka bige da nema saiwarce har yau ba a san ko yar gidan uban

wayebace, sai yar tsintuwar innarmu, da sauriintisaarta juya da gudu ta bar wajen, ya bita dakallo,

bakinsa yyi masa nauyin kiran sunan natama,

fadila taci gaba tana kallonsa, "ita ba yarkowabace, sannan ta samu wajen fakewa agidanmuita da uwarta sai su dinga mana isa, yauwatadaya da sati biyu knan da suka sa Alhaji yakoreiyayenmu a gidan nan sbda ita da uwarta,kadijatayi tsaki tace "ai basu ga komai ba matukunna,sai suma sun bar gidan nan kmr yanda sukasaaka kore uwata." fadila tace "nima hka,"

sannan

suka bar wajen gate din suka shige cikingidaxuciyarsu pal da murna. Sai da faruuq yyikusanminti biyar a wajen a tsaye, sannan ya bargidanjikinsa a sanyayye..

Momy ta dube Intisaar dake ta famankuka tun da tashigo a karo na farko tayimatamgna "me ya faru?" ta girgixa kai tana gogehawaye, cikin kuka tace "momy wai ni kigya minranda xan ga abbana, na gaji da gorin daakemani," hawaye ya ciko idon mahaifiyar tata. Tayi kokarin gogewa da sauri tace "me kuma yafaru?"

cikin kuka me tsuma xuciya intisaar ta koromataduk abinda ya faru, momy ta goge hawayenidonta tace "kiyi hkuri intisaar, watarana sai

lbri,

na sha gya maki" sannan ta mike tana cewa"saikiyi ma faruuq din bayanin komai, sannan tashiga dakinta." bayan faruwan hkn da

wajenkwana uku faruuq bai ce mata komai ba,iyakadai ya kirata suyi hira sosai. Ranar watalarabayake ce mata yana so su hadu gobe da

daddarea kofar gidansu, bata yi masa musu ba taceAllahya kai mu, amma gabanta na faduwa dan

tasanbaya xuwa gidansu sai ranar juma'ah.

Washegarin ranar alhamis ta gyawa

Ummantayanda suka yi dashi, tace "shikenan, ammakarkiboye masa komai intisaar," tace "to momy."

sannan ta wuce sashin inna ta taya ta hira.

Koda wasa bata gayawa inna abinda su fadilasukayi mata ba, ta barshi a xuciyarta kawai.

Da yammacin ranar wajen karfe bakwai damintigoma faruuq ya iso gidan nasu, ta nemiixini gunmomynta ta fita da cewar ba ddewa xatayiba. KarKar Abba ya sameta a waje. 

Yana xauna kanwani dakali, ta karaso wajensa, ya tare ta damurmushi, tun kan ta karaso wajen

Kamshinturarensa mai ddi ya doki hancinta, takallesahade da sunkuyar da kai, ya mike yana matasannu da xuwa. A hankali ta gaishesa, ya

Amsayana cewa "ya momy da inna?" tace sunalfya.

Sannan ya xauna ya nuna mata gefensa, ta Dan yi jim, kmr mai naxari sannan ta xauna. ShiruShirubbu

wanda yace komai, can dai ya katse shirunyace

"i luv yhu my Intisaar," ta rufe fuskartakawaibata ce komai ba, ya kalli fingers dinta yace

"ringdin waye wannan?" tace na xainab ne, yace

Ok, ita ta baki? Uhm ko kana so ne? "yace aa da Dainaki ne" tayi murmushi kawai. 'intisaar' taji

Yakirata a hankli, tace "na'am" a sanyaye. Lbrinrayuwarki nke so ki bni yau, kinga am vrybusybut na ajiye komai aside, dan naji tarihinintisaardita. Ta kirkiro murmushi kawai bata ce komai ba. Bismillah if u re ready, tace "uhm to ta

Inaxan fara?" yace "ko ta ina ma Intisaar," nan da nan taji hawaye ya ciko idonta sannan tafara batare da bata lokaciba.

Ni sunana Fateemah Umar faruuq,

Ya xuba mata ido yana kallonta, can dai yasakarmata murmushi ya gyada mata kai alamartacigaba, ta cigaba ba tare da ta kallesa ba, ninataso ne a Zoo road nan kano da mahaifiyata,tana yi ma wata aiki lkcn ina da shekarahudu,

momy tace min a nan gidan ta haifeni in datakeyin aiki, dan ta fara aiki da sati biyu ne tahaifeni. Inna ita ce warce ummata ke yi maaiki,da farko dai ni na taso a tunanin inna ce tahaifeni, amma ita da bakinta ta kan ceminnadaina damunta ga mamata can, a hankli dainagano wacece mahaifiyar tawa, inna mutumcemai kirki sosai, ko sau daya bata tabawalakantamu ba, ta dauki ummata kmr ita ta haifeta,nikuma ta daukeni jikarta. A kwana a tashi

inna tasani a sch, lkcn har na isa primary 5,watarana asch aka ce mana kowa yaxo da babansaxa'ayimeetin, ni ban kawo komai a ka ba dannasanummata xata xo min, amma muna shiga ajisaiwata classmate dita maimuna tace min"intisaarke kina da Abba ma kuwa? Bamu sanbabanki ba,mu babanmu xai xo gobe. Tun da nake bantabakawo mahaifi a rai ba sai rannan, sai naji ba ddi ganin yanda kowa ke dokin babansa xai xo,nakagu mu tashi naje gida a gya min inda

babanayake, dan ba'a taba min mgnarsa ba, ina isagida Kuwa da tambayar da na tari mamata knantanawanke wanke, naga tashin hnkli ya bayyana a fuskarta sosai, inna ta fito da sauri tanacewa,waye ya aiko ki? Nace gobe akace mu kawobabanmu a makaranta, inna ta ja ni tashigardanidakinta tace "ki kwantar da hankalinki yarlele ta,gobe uwarki xata je, nan na fashe mata dakukanace ni dai babana ne xai je ba mamata ba.

Innata hassala tace "to dan ubanki xauna ki ji,babanki bamu san inda yake ba,mahaifiyarki natsince ta a titi ne ranar na dawo daga gidanaminiyata, tana da cikinki lkcn, a sume mukakaita asibiti mu da bayin Allahn dake wajen,

bayan kwana biyu ta farfado, cikin bayinAllahnda muka kawota asibiti ni da wata baiwarAllahkadai muka rage, dan sauran duk sun tsere

dawashegarin ranar. Ana sallamota na kawotagidana. Ita kuwa talatu, sunan matar knandamuke ta sintiri da ita a asibiti, a haife dai nahaifeta, na nuna mata xan kula da

mahaifiyarkixainab, dan itama ta damu kwarai da gaske,

tokinji dalilin ganin ki nan gidan da kikayi, inna

tacigaba tana kallona, bayan satinta daya nagatawarware sosai, nake tambayrta ita wacece.

Nanmomy tabawa inna tarihinta, tace daga

Misrataxo nan Nigeria, mijinta ne ya barta wajenwatatara knan bata san in da yake ba, sbda Bakincikin hkn ne ya sanya ta kasa gano yandaakayita baro Egypt, kawai ta ganta a nan Nigeria,

sannan tace ma inna tana da kishiya kuma ataresuke, to bayan sati daya inna tace ummatatahaifeni a nan gidan nata, danta tasa yayankamin rago aka sa min fateemah, Sauran

bayanandai ne duk na manta. Da yake lkcn ba wani

wayogareni sosai sosai ba ban wani nunadamuwanada yawa ba, washegarin ranar inna ta kiradantamuka je meetn din mkrantar tare. Inna tamanaabinda ko na jininmu baxai mana ba, innatatausayawa mahaifiyata sosai, duk da dailkcn dukwannan abun da take ba da san ran dannatabne, dan baya san yanda inna ta makalemanadaga ganinmu ba wai saninmu tayi bakuma tayrda damu, amma ta nuna masa bai isa yahanata abinda tayi niya ba. Lkcn ina da 3 yrs

inna ta tilasta ma danta yyi mana visa mukajeegypt nemo mahaifina, har da ita. Da kyarummata ta iya gane gidan abban nawa,amma koda suka je, sai suka ga wai stepmum dita tasaida gidan, hka muka sake dawowaNigeria.

hankalin momyna a tashe, inna ta dingakwantar mata da hankali tana cewa wataranaabbana xaixo gareta, wannan ba komai bne illa aikinasiri damuguwar abokiyar xaman tata tayi kawai.

Tundaga lkcn inna ta dauki ummata kmr yar ta,

Ta nemo wata yar aikin daban dan yanxu waimunxama yan gida.sai abinda baxa a rasa bakaidaimomy ke mata, inna da ta tashi sani amkrnatsai ta sani a mkrntar kudi, Abba na biya,ummata

gani tayi kmr inna ta daurawa dan natanauyinmune, dan shima yana da nasa iyalin, dan lkcnmatansa biyu da ya'ya shidda, dan hkamomytace wa inna ta barta dan Allah ta nemiwanidan aikin da xata dinga yi, inna ta nunabacinranta sosai, tace momy kar ta sake matahka,

bbu ruwanta da lamarinta da na danta dantsakaninsu ne, sau dayawa duk bayan satibiyusai jikokin inna sun xo gidanta, ba karamintsanata sukayi ba baya ga xainab dake sonasosai, kuma dama sa'a ta ce, na sha hantarawajensu da na iyayensu, basa sona damomyna,sun tsanemu, bn san ko dan muna cin arxikinsu bne, Abban nasu kuwa tun yana dauremana da,har ya sake mana sbda yanda yagamahaifiyarsake sanmu sosai. Ya maida ni kmr yarsa,

komaiyyi ma yayansa sai yyi min nima. Tun asalidama yaya haisam yana ji dani sosai, ya daukeni kmrkanwarsa kuma yana girmama mahaifiyata.

Inada shekara 12 lkcn ina jss2 inna ta hadaaurenmahaifiyata da danta, wato AbbansuHaisam.

Ba karamin tashin hnkli momyna tashigaba dan babana bai sake ta ba ai, inna tadingamata jaraban wai ynxu kusan shekara 13 knan tana jiran wanda kila yanxu ya mace, kumama aia musulince ta halatta tayi aure tunda yadderabon da ta gansa ko sanin inda yake. Hkananinna tasa Alhaji Abubakar ya aure ummata,

Shibai nuna abin ya damesa ba, dan dukabindamahaifiyarsa take so shi yke yi. A hka ni damomyna muka koma gidansu dake shagariqtres,

wato wannan gidan na yanxu... Uhum tadanyishiru sannan taci gaba ganin yanda faruuqkekallonta a raunane, tun daga ranar har yauni daummata bamu samu farinciki ba gidan nan,saiwajen Abba da inna, sai kuma xainab dastepbrother dinta Haisam, sun tsane mu,basason mu, sun takura mana, kumahar yau

basutaba shiri da ummata ba, ita kuma tundatakebasu taba mata abu ta tanka masu ba,shiyasahar gobe Abba ke alfahari da ita kuma yanaji daita, momyna tana da hkuri sosai, da kau dakaiakan abu. Ihsaan kadai momyna ta haifa anangidan, bayan nan bata sake haihuwa ba,

Yanxu ihsaan shekaranta kusan 6 knan. Sbda irinyandasuka samu gaba ne ya sanya inna ta sa abba

Yagyara mata sashinta na nan gidan ta dawo,dandama can yayi-yayi da ita ta dawo nan daxamadan ya kula da ita da kyau amma taki dan bagirmamata matan nasa ke yi ba. Hkn yakarawamomyna tsana a wajensu hajiya, dan innatafififfitata a kansu, kuma tafi son ni da ihsaanakanya'yansu, a makaranta daya muka gama secsch

da xainab, fadila da kursum, khadija darahmakuwa suna ss2 ne ynxu hka.

Hajiya Aisha itace

matar Alhaji ta farko, ya'yanta uku, yayaAliyu,xainab da khadija, ita kuma umma shafaya'yanta

hudu, yaya haisam, fadila,kursum da rahma,saijikanta yusuf dan fadila ta taba aure ammasunrabu da mijin. Faruuq yyi ajiyar xuciya yace

"toshi yaya Aliyun yana ina?" ta dan xaro ido tace

"nima ban sani ba wllh," amma baya gidanynxuhka, ok xainab ce kanwartasa knan, eh...tacekanta a sunkuye, to meye na kuka intisaar,

Wllhnaji na kara sonki ne ma, ya ciro

handkercief yagoge mata fuskarta. "i luv you my intisaar,"

tagyada kai kawai ta kasa cewa komai, ki baniixinina turo gidanku plss, ta danyi jim, sannantace tosai nayi shawara da innata, yace o.k gobemaxan xo ai wajen innar, da kyar ya bartatashigaciki dan duk ya birkice mata ta amince masakarta ya dashi, shi din mai sonta ne da gskya,harbakin gate ya rakota ta shiga sannan yawuce,

Taji ranta yyi fari sosai, taji ta kara sonfaruuq…….

Washegarin ranar da magrib faruuq ya bargidansu, sun dde suna hira da inna dagabisannitace idan tayi shawara da danta xatagayamasalkcn da xai turo, har gate ta rakosa, yaya haisamya shigo suka gaisa da faruuq, ya danxolayeta Sannan ya wuce, faruuq ya dubeta yace

"yanaaiki ne haisam,?" tayi dariya tace kaibarrister nehka pa da ka gansa, a Abuja yake aiki kila

hu2yaxo nake ga, yace " to shi da Aliyun wayebabba?" ta danyi jim sannan tace "ya Aliyunemana" o.k shi kuma Aliyun wani aikin yakeyi?

Ko bai fara ba? Tace "wllh nima bn sani ba,"ya

dubeta da tuhuma yace "baku interact dashine?"

tayi murmushi tace aa ni bamu san junasosaiba,

o.k... Duk xamanki gidan nan baya nan ne?

Tadan xaro ido tace "a'a yana nan mana,"

Faruuqyyi murmushi yace "ko bae sake maki bne?"

Tadanyi shiru sannan tace uhm, dan ita batamasan ana tuna mata ya Aliyu ko kadan, duk takagu ya rabu da ita da xancen Aliyu, shi kammurmushi yyi yace "to shknan intisaar, nixan tafi,ya ciro kudi mai yawa ya bata," tace hava na

Mene yaya, yace yau juma'ah shi yasa, tace a'a nagode,ka barshi kawai, ya bata rai yace "tundamukedake na taba baki abu intisaar? Wllh nasanabinda nakeyi, ki karba nace, da kyar takarbatayi masa gdya sosai, sannan tayi sashinsudasaurinta. Xaune take a kasan parlon Abbayanaduba jarida, can dai ya dubeta yace "me ya

Faruintisaar ya akayi ne?" a hankli ta faramaganamuryarta na rawa, Abba dan Allah danannabikayi hkuri ka bar su Hajiya da umma sudawo,Abba ya katse ta da sauri yace "to ai ni bnida tacewa a nan, sai abinda kakarku tace, dan itakeda iko dani, kinga kuwa bni da laifi a nan."

Tayishiru, sannan ta mike tace "to Abba shknan"ta Fice ta bar palon. Yyi murmushi dan yasanuwarta ce ta turo ta, dan ya nuna mata kartasake masa mgnarsu Aisha kwanaki uku da

Sukawuce tana basa hkuri. Intisaar na fita sashininnata nufa, ko da tayi mata mgna ma bata rai

Tayisosai, tace "maxa fice ki bni waje ka finraina yabaci, idan ma uwarki ce ta turo ki kije kicematanace tashiga hankalinta, idan ba naci ba mamutanen da ba sonta suke ba ta wani damukanta a kansu" intisaar ta fice mata dagapalonnata a fusace dan ita bata san me inna take

Nufiba, to don me baxa su ci darajar ya'yansuba maa barsu su dawo gidan. Ita kam tausayinxainabdasu kursum take yi sosai, shi kam haisam

ko ajikinsa dan ko xancen ma baya so. Tana tafetana waya da faruuq, ynxu kam shakuwarsuyawuce misali, dan inna kadai yake jira tayi maabba magana dan shi a shirye yake, kuma yace xai dauke mata nauyin kara2n ta gaba daya,dariya tayi sosai tace "kai ya faruuq wajeninnapa xani ba wani gun ba, yace "ohk ai nayi xaton fita xakiyi ne shiyasa nace hkan," a hka takarasosashin inna tana ce masa "yayana ko sllh mapabn yi ba" yace "hva de kanwata gashi harwajenkarfe takwas, to kiyi alwala a bakin tap, nanwajen kafin ki shiga mana," tace "dama hknxanyi yayana, bn gama abinda nkeyi bnedaxunshiyasa lkcn sllhn ya wuceni" ko da ta isabakintap din ma sai ta tarar ana alwala, tace "kgayaya haisam ma na alwala a wajen," yahaisam,yayana yana gaisheka wai, hka nan suka ci

gabada hira da faruuq tana jiran haisam itamatayialwalan sai ta shiga ciki, "hmm to shknankanwata yi alwalarki anjima mayi magana,"faruuq ya fadi yana kkrin kashe wayan, tacea’a

ai ya haisam bai gama ba, dariya faruuq yyiyace

"baki gajiya da jin muryata ko bbynah?"

kunya yakamata tace "lalle ma yayana to bye" oh srry

myintisaar wasa nke maki, a dai-dai lkcn maialwalan ya dago, sukayi ido hudu da yaAliyu,wani irin muguwar faduwar gaba yaxomata,bakinta ya fara karkarwa ta ma rasa nemomgnar da xatayi masa, kallo daya yyi matayadauke kai ya shige parlon inna. 

Faruuq kamyakira sunanta yafi sau biyar, duk da wayanna karea kunnanta amma ta kasa cewa komai, haryagaji dan kansa ya kashe. Kasa koda motsitayidaga gun da take, ta dai dake a hnkli ta juyaxata koma sashinsu taji inna ta kwado mata

kira,

da sauri ta dawo amma ta kasa amsawa, tajiinna nacewa "Aliyu ba muryar intisaar nake

jidaxu a waje ba?" shi dai baice mata komaiba illadardumar da ya dauko ya shimfida, a'a

baxakamasallaci bne, yace eh... Ya tada sallansakawai.

Sai da inna ta leko tayi ma intisaar mgnasannantayi alwala tashigo palon, gabanta namugun

Faduwa.

Sai yanxu kika ga daman xuwan knan,

intisaar ta dube innar tace "aiki nke yi ne" tokeda faruqu kke waya ko wa? Tayi shiru batace Komai ba sai hararan innar da takeyi, innatatabe baki taci gaba da dama furar da takeyi,

Aliyu ya idar ya mike, inna ta dubi intisaartace "ba ki ga yayan naki bne ba ke," ta dubesa dasauri tace "ina yini yaya," lfya kadai yace ba

Tareda ya kula ba ya nemi guri ya xauna, inna ta Nunamata dardumar da ya mike daga kai tace

"kijekiyi sllh ga shimfida can, ta mike take ta tadasallah tana dan satan kallon Aliyun. Har taidar.

inna bata daina mitan da takewa Aliyu ba narashin son xuwa gida ba, don ynxu ma badanubanshi ya kirasa ba, ba xuwa xai yi ba, shi

kamhankalinsa na wajen news din da yke kallogabadaya, hka tayi ta surutu intisaar na kallonsukmrtayi dariya, inna tace "iyye!! Gamahaukaciya namagana ko? Shi kam bai ma san tana yi ba,

innatace "ba mgna nke mka ba Aliyu," ganin baisantana yi ba yasa ta daka masa tsawa ya dawodaga kallon a dan firgice, "wai meye ne hkainnarahma?" ya tambayeta a fusace, ta mike takashe TVn, kan ta juyo shima har ya mikexai fita, ta juya tana dubansa tace "ynxu Aliyu ni ka maida mahaukaciya," to hva inna news pankekallo kke takurani hka, ta tura kofarta ta

rufe,tana cewa "sai ka tambayi haisam yandaakayi anews din" yyi murmushi ya xauna yace toinajinki tsohuwa, ta koma ta xauna ta dinga

masabnasiha ya daina abubuwan da yake yi, yagirgixa

kai yace "to menake yi inna?" kusan kullumsaiBukar ya kawo min kwamplan a kanka,dariya yyisosai yace "to ayi hkuri Hajiya" ta hade raitaceka tsaya ka saurareni ni dai," nan tacigabadabatunta, shi kam wayarsa ya fito da ya na tadanne danne. Ganin wannan nasihar ba maikarewa bane yasa intisaar ta mike tace"inna niguga xanyi, xan tafi," ehh dama tsifa xakiyi

minkuma xainab da kursum sun min daxu,gobe dasafe dai ki xo, tace "to inna, amma baki bnifurarba," inna ta dubi furar dake gaban Aliyun

tace"ga na Aliyu bai sha ba ki dauka kije dashi"intisaar ta dago kai ta dubi Aliyun ta gakallonta yake yi, suna hada ido yyi murmushin da takasa gne ko na mene, amma dai tasan bna arxikibne ,

ya kalli inna a fusace yace "to sai nace makibaxan sha bane" inna ta tabe baki tace "je ki

kidauko kofi ki diba," kai dai ban san waniirinmutum bne, har yau baxaka canxa halinkaba ko,

wae ma dan meyasa baxakayi koyi daHaisam bane, nan kuma ta fara sabon fadan, intisaardai tadeba wanda xata deba tace "to inna sai da

safeni na wuce" Allah ya kaimu. Inna ta fadi batareda ta kalleta ba. Ta dan saci kallon Aliyun dayamike tsaye yana duban inna kawae kmr yamareta, intisaar ta bude kofar ta fice, ya juyashima ya fice, inna tana baxaka sha furarbnekuma, bai ce komai ba ya fice abinsa.

Intisaar natafe tana waige-waige, can ta hangosa daganisashima ya fito ta xuba a guje, taji taci karo damutum, ta daga kai a tsorace sukayi idohudu daHaisam, yana kallonta yace lfya? Tana mai danumfashi tace tsoro nke ji ne, Aliyu yakaraso,

haisam ya dubesa ya dubeta, yace "ina yinibro,"ya amsa hanklinsa baya wajen, sannan ya

dubiintisaar yace "wllh wllh ki ka sake ganinakkakwasa a guje kmr kinga uwarki to sai naciubanki,na maki dukan fitar hankali, kanta a kasa

tace "nisauri nke yi ne shiyasa nke gudu," bai bi takantaba yyi gaba abinsa yana cewa "ko ma uban

mekke yi ni dai na gya maki" haisam ya dubetayace

"ki daina gudu idan kin gansa, shima aiyasan koyyi hauka ne baxai taba ki ba," bata cekomai batayi ma Haisam sai da safe sannan tayihanyar

sashinsu. Tana isa ta tarda rahmatu daxainab aparlonsu, ba abin mamaki bne don tagarahmatua sashinsu don duk fitsararta ita da kursumsunashigowa khadija da fadila dai ne basashigowa,

wajen karfe tara da rabi ta rakasu sashinsu,

xainab na mata dariya tace " kinga babankidaxua wajen inna," tayi murmushi kawai dansbdayanda take mugun tsoran Aliyu suke cemasababanta, don ko momy da Abba batabtsoransubhka, ita kam duk duniya bbu wanda taketsorokmr Aliyu, baxata taba iya mantawa da Aliyuba arayuwarta..

Inteesar Tana xaune a balcony tana ferewa momydankali, momy na wanke-wanke a bakintap, tadubi momyn tata tace "momy yaushe yaAliyu yadawo?" momy ta juya ta watsa mata harara

Tace

"ya xa'ayi na sani ni kuwa, kinga yaxo

Gaishenihar ynxu, bare nasan ya dawo ko kumayausheya dawo?" intisaar bata sake cewa komai ba

Tacigaba da abinda take yi. Xainab ce ta karasodasauri, tayi ma momy sannu da aiki sannan tadubi intisaar tace "inna tace na kiraki" takammala abinda take yi da sauri, sannan tanemiixini wajen momynta, tace "to amma kiyimaxa kidawo xaki min abu ne" to! kadai tace sukawuce.

A hanya take tambayar xainab me xata yiwainnar, xainab tace "aikenmu xatayi wai" abakinkofar inna suka tarda ya Aliyu tsaye, yana taxuba, xainab tace "kai yaya har ynxu bakaragewannan surutun naka ba sai ma....." da sauriyajuya yana kokarin cafkota yaga tare suke daintisaar, nan da nan ya hade rai, ya lekaparloninna yace "inna ni na tafi," tace aa har mungama hirar mai gidana,? Bai ce komai ba yabarwajen, xainab tace kai! Yaya kaga yandakayiwani irin fresh kayi kyau? Tab! Inna ce tafito dasaurinta tana cewa "Aliyu xo dan Allah." har

Yyinisa ya juyo tare da cewa ya akayi? Xo danAllahnace. Yace "aa ni baxan iya dawo wa ba."sannan yyi gaba abinsa, inna tayi tsaki tacegantalalle kawae, dama hanya nke son yaragemaku wllh, intisaar tace "aa bama so inna,

Da mayaya Haisam ne." dole ta basu kudin motardaaiken da xasu kai wa kawarta hajiya maimuna. Sun isa gidan suka bata sakon, tayi ta samasualbarka sannan ta basu dari biyar su haumota,

Jikarta murja ta rakosu har inda xasu haumota,sannan ta koma. Xainab ta dubi intisaar tace

"kk muyi save din kudin mu, mu taka kawaitunda bawani nisa, da kyar ta lallaba intisaar sukafaratrekkin don da kin yrda tayi. A dai-dai wanikatonpharmacy faruuq ya fito rike da leda ahannunsa,xainab ce ta fara hangosa, tace "lah..Intisaarkinga faruuq," da sauri intisaar ta juya suka

Hadaido, ya sakar mata murmushi ya karaso dasauriyace "daga ina hka?" suka gaya masa dagaindasuke, bayan sun gaisa ya bukaci da ya rage Masuhanya, bbu musu suka shiga, yyi drop dinsuakofar gidansu, suka fito suka yi masa gdya

sannan ya kashe wa intisaar ido, ya ja motaryawuce hade da cewa sai munyi waya, kugaidamin da inna." Aliyu suka ci karo da a gateyanatsaya, cak suka tsaya ganinsa a wajen,xainabtayi karfin halin cewa "yaya me kke yi anan?" yaxura wayarsa cikin aljihu sannan ya ddubet dakyau yace "motar uban waye kika shiga?" tahade rai tace "saurayin intisaar," ya bude

bakiyana kallonta, ganin yanda tayi mgnar kotsorobbu,kika ce me? Ya sake tambayarta, tamaimaita ranta a hade, mari ya watsa matamairai da lfya, tuni intisaar ta fara karkarwa,xainabkuwa ta fashe da kuka, ya fixgota , ta turasadakarfinta, ta xuba a guje sai bangaren suintisaar,bin ta yyi da saurinsa, intisaar kuwa naganin hkatayi wajen inna da gudu gabanta nafaduwa.

Parlonsu intisaar xainab ta afka, ya bita harcikiyana cewa "dan ubanki yaushe na farawasadake xainab," tayi bayan momy da gudu

Tanahakitare da goge hawayen fuskrta tana kumahararansa, momy ta dubeta tace "me ya faruxainab," ta fashe da kuka tana cewa " marina yyimomy banyi masa komai ba, kuma Allah yaisaban yafe masa ba," dan uwarki xo ki fita, yadakamata tsawa a fusace, xainab ta wasa mashiharara tace "anki din, kuma ka sake mamutanekofar su ka bar wajen, tunda a gidanku ba akoyamka kayi respect ba, bare har kayi gaisuwa."

Tuniidonsa yyi jajir yana kallonta kamr wanixaki.

Momy ta dubi xainab tace "shiga daki

xainab," tashige da sauri, ita kuma taci gaba da abindatakeyi," da kyar ya iya sake kofar parlon yaja dabaya kmr ya hadiyi xuciya, tsaye yaga sukhadija,kursum, da rahmatu suna kallon abinda yafaru,

wani irin wawan kallo yyi masu da yasasukakwasa a guje suna dariya. Kmr ance ya juya

tagefensa ya ga intisaar a tsaye, duk a birkicetake,

yana juyowa sukayi ido hudu, ta budo kofaratsorace xata shige parlonsu ya cafkota, kuka

tasaka tana cewa "nashiga uku yaya, wllh kayihkuri bni bace ba..... Bai ko kulata ba ya cire

takalmin dake kafarsa ya dinga xuba matadakarfinsa kmr an aikosa, kuka takeyi tana

kiranmomynta, yace "don uwarki an gya maki inada lkcnki ne bare na lamarinki,to ba a mota ba,ko ajirgi ne akayi park dinki a kofar gidan nanbburuwana, na dai ce maki ni ba dodonki bne,idankka sake ganina kika gudu sai na babbalaki

jakarbnxa kawai mahaukaciya, ya turata cike datsanayana huci, haisam ne ya iso wajen da sauri

yanacewa "hava Aliyu, me tayi mka hka xakabiyotahar kofar daki kana dukanta, Aliyun yahararesayace to sai ka rama mata

..

Haisam ya tambayesu me kuka yi masa,xainab ta fito tana goge hawayenta tace"inna ceta aikemu, shine don yaga Faruuq ya ajiyemusai yake xagina har da duka," ta dubi

Intisaartace "kema meyasa bakiyi wajen inna bakika xonan," ta goge hawayen idonta tace bata nanne, adai-dai lkcn inna ta bullo, ta karaso dasaurintatana dubansu tace "me ya faru, hatsarikukayi,ne? Nan da nan ta rude masu, haisam yyidariya,xainab kuwa ta kwashe duk abinda ya faru

Tasanar da inna, nan inna ta dinga bala'i tanamasifa tayi dakin Aliyun tana cewa Allah ya isar masu. Haisam ya dubi don intisaar ta rigatashiga ciki yace "momy bata nan ne?"

Xainabtace tana ciki, ya girgixa kai yace ammaAliyubashi da kunya ko kadan. Ya shiga sukagaisa da

momy, sannan ya basu hkuriya bar sashinnasu.

Suna xaune su uku suna hadawa yaya

Haisamkayansa don anjima xai komai Abuja, xainabtalinke wa, intisaar na gyarasu cikin jaka,rahma dakursum na kwance da yake a dakinsa suke,sunakallo

Xainab ta dubi intisaar tace "jiya faruuqsaewajen karfe goma ya bar wajen inna,"

intisaar

tace "hva" ba tare da ta kula ba,xainab taceehmana, ai can na kwana, kursum ta dubixainabdin tace kai xainab tara da rabi fa naga yabargidan nan. Xainab ta dubeta a fusace tace"jakabki ji abinda nace bne?" ca nayi har wajenkarfegoma, bnce karfe goma ba, ita dai intisaarhankalinta na wajen abinda takeyi bata cemasukomai ba. Ya haisam ya shigo yace idan sungama su rufe masa dakin, xai je wajenummarsayyi mata sallama, kursum tace "ayya yayaxanbika don Allah, abba baya bari muje wllh" yadubeta yace to xo muje, nan rahma ma tacexatabisa, yace duk su xo su tafi, ya tambayi

xainabko tana da sako dan xai je wajen hajiyarsuma,tace aa kawai dae ya gaisheta. Nan yakwashekanninnasa sukayi gidanmahaifiyarsu donyasansunyi kewarta sosai barin Rahma autar ta.

Bayansun tafi ne intisaar take tambayr xainab inakhadija, tace mata sun fita tare da ya Aliyu,batasake cewa komai ba don tasan yana ji dakanwarnan tasa khadija duk cikin kanninsa saekumarahma da kursum. Jiya maganar aurenkufaruuqyyi da inna pa.. Intisaar dai bata ce matakomaiba ita kuma taci gaba da maganarta " tace

Yabata sati biyu don akwae wani shawara dasukeyida Abba ne," intisaar tace "uhmm" ta cigaba dabinda takeyi kawae. Basu bar dakin ba saiwajen karfe biyar na yamma, sannan sukakullomasa kofar sukayi sashin inna, hirar daxainabtayi mata, shi innar ma tayi mata, ta kara dacewa "ynxu dai nace masa ya dawo bayansatibiyu kafin lkcn mun gama shawarar dababanku"

ita kam intisaar binta tayi da uhm kawai. Suna cin abinci da daddare khadija ta shigo, innatacesae ynxu? Tace eh, ta nemi kujera takwanta,

inna tace " to ina Aliyun?" tace oho! Kamr yaknan oho? To ni da kafa na dawo don ban Sakeganinsa ba, xainab ta fashe da dariya tace

"Allahya kara," intisaar dai jinsu kawae take yi, tamiketace inna ni sae da safe don barci nke ji.

Tana tafe a hnkli cikin sassarfa kmr mara gskyatajikamshin turaren Aliyu, gabanta yyi mugunfaduwa, tasan duk yanda akayi yana nan

wajajen,nan da nan ta fara neman wajen da xatabuya,har wani rawa jikinta yke yi sbda tsoro, jikinwataflower dake wajajen ta labe xuciyarta nabugawa,

yana ko karaso wa dae-dae wajen sai yatsaya

kmr mai tunani, ganin hka ya sa ta fasa ihudona tunaninta ya ganta ne, ba karamin firgitayyi bada karar da tayi, ya koma baya da sauri yanasallati, da sauri ta fito daga flowern ta nakokaringudu, yyi hanxarin cafkota, ta kara fasa

masawani ihun, muryar Abba sukaji, yana cewa"fateemah me yafaru?" ba shiri ya cikata

tare dadurkushewa yana kallon kafarta yace

"subhanallaimae kika taka?" Abba yakaraso da sauri

wajen,me kka taka fateema, me ya faru, ta ma rasa

mexata ce, amma har ynxu jikinta bari yake,Aliyun

yyi maxa yace "ina jin abu ta taka naxowucewane naji tana ihu," tambayar Abba ya sake

jefomata muryarta na karkarwa tace "Abbanima bnsan meye ba" Abba ya ciro da torch yana

haskakafar, Aliyu ya karba yana duba mata kafaryace"sannu, amma ai ba komai a kafar, yana

makiciwo ne," tace aa da sauri, Abba yace "toAllahya kiyaye dai, me ya hanaki kwana wajeninna,?

Tace bakomai, yace "to Aliyu dan rakatacikingida," yace to Abba, tashiga gaba yana biyedaita a baya, Abba kuma yyi nasa parlon.

Tana gaba yana biye da ita a baya, yanadan waige-waige yana duban kofan palonabbannasa, har dai yaga ya kashe wutan parlonalamarxai shiga bedroom dinsa knan, ya ji ddinhknsosai, ya juya da hanxari xai shige gabantaamma yaga wajen wayam bbu kowa, itakam

abba na shigewa palonsa tayi ta kanta dantasan sauran bayanin, cikin rashin sa'a ta tarda momy ta kulle kofa, a rude ta shiga jijjiga

kofartana kwalawa momyn nata kira, momyn tatamaa tsorace ta iso xata bude kofar tana cewa"lfya,

menene,?" amma tuni ya karaso wajen, taxabgaihu tana "wayyo momy ki....." bugun da yakaiwabakinta ne ya hanata karasawa, a dai-dainan Momy ta bude kofar, hkn kuma bai hanasariketakmr wata 'yar shi yana duka ba, momy tajuya takoma ciki ba tare da tace komai ba, "donAllahyaya kayi hkuri wani abu ne ke bina shi yasanayi ihu," dukanta ya dinga yi ba sassaucihar daidaga karshe yyi wani irin juyi da ita yawurgar,sannan ya bar wajen yana huci kmr xaki,kuka tadinga yi tana kiran ummanta, can dae ganinmomy ba fitowa xatayi ba yasa ta mike da

kyarta shiga palon nasu. Ita dai har tayi barcimomybata ce mata komai ba, sai ma ca mata datayixata kara mata idan bata rufe mata baki ba,

doletasa ta hadiye kukan nata har bacci yyi gabadaita. Da safe ita da kanwarta suka gamabreakfst,ta kwashi kwanukan xata je ta wankemomy tagatana dingishi, "xo nan intisaar", ta dawotanakallon momyn tace na'am, me ya samikafarki,

"yaya Aliyu ne ya buge min kafar" to yyikyau, Jeki. Haushi ya cikata sosai amma bata cekomaiba ta gama wanke-wanken ta ja kanwarta

Sukayisashin Abba su gaidashi. Inna na palon nasa A xaune rahma na kusa da ita a xaune, a taresukashiga parlon da xainab da ita ma taxo gaida

Abba, abba ya dubi intisaar da ta nemi guritaxauna yace "ya naga kina dingishi,?" innatace"me ya samu kafar," tace "bugewa nayi"garinyaya? Inna ta tambaya tana kallonta, abbayace"ko dae jiya kin ji ciwo ne?" eh kadai tacesannanta fara gaida abba, ya amsa, xainab ma tagaidashi, ya dubi intisaar yace "to bari Aliyu

Yaxo ya duba maki kafan ko?" bata ce komaiba,

sai TV da ta kurawa ido. Anjima xaku jegidannafisa ku taya ta gyare-gyare ta dawo jiyadadaddare, Nafisa kanwarsa ce, kuma autawajeninna, shekaransu goma knan aiki ya kai

mijintagermany, xainab taji ddisosai, intisaarkuwa batawani santa sosai ba, xainab tace "to abba

wa xaikai mu ne, bamu san gidan ba ai, abba yace

"ehAliyu xai kai ku dama ai," a dai-dai lkcn Aliyuyashigo palon da sallamarsa , yana sanye da

Fararshirt da bakar wando, kamshin turarensa yagauraye ko ina, ya nemi gefe ya tsugunna yagaida inna, ta amsa tana cewa sai ina? Baikulata ba ya gaida abbansa ya amsa yana

Cewaka tashi lfya? Bai ce komai ba ya maidawayarsaaljihu ya xauna. Xainab ta dubesa tace "inakwana yaya?" yace "lfya lau" intisaar ma tagaishesa ya amsa da lfya! Abba yace "yauwaxaka kaisu jan bulo gidan Nafisa ina fatan

Kasanta dawo, ya hade rai bai ce komai ba, xainabtace"ki tashi muje mu shirya intisaar," abba yace

"kugyawa fadila ma, har da ita xaku." suka ce to, sannan suka mike xasu bar palon. YauwaAliyuka dubawa fatimah kafarta dingishi take yiwaijiya bugewa tayi, ya dago da sauri yana

Kallonkafartata, ita kam da sauri tace "lah Abba

wllh bawani ciwo yke min ba ya ma daina." inna

tacemunafuka a hkn ya daina maki ciwon? Batatanka mata ba ta fice da sauri xainab ta bibayanta. Fadila xainab taje ta sanarwaabindaAbba yace, ta kama hanya abinta ta wuce.

Dakyar xainab ta lallaba intisaar ta shirya donkukata dinga mata wai bbu inda xata Aliyu kashe Taxai yi a hanya, tun xainab na dariya har ta

daina,tace "wllh bai isa yyi maki komai ba..

Ba don ta yarda da maganar Xainab ba tagama shirinta, don tasan kila ma ya damketaxainab din ba tsayawa xatayi ba. Su ka yiwamomy sallama, ta hada su da ihsaan suje, a

Canbangaren inna suka sami Aliyun, inna tace"maxaka kai su Aliyu, bai ce komai ba ya mike yaficesuna biye dashi a baya, intisaar duk a

Tsoracetake, kofar gida suka yi gaba daya, xainab

dai saikallon ikon Allah takeyi, suna fita ya cirodububiyu ya mikawa xainab yace "gashi ku haubike,ni ina da waje mai important da xa ni," bani

wayarki na sa maki nmbr Nafisan idan kinjecanki kirata..... Ta mika masa yasa mata nmbrsannan ya mika mata wayanta, yyi wajen motarsa dake parke a gurin, ya bude knan ihsaan tace "uncle amma kai dady yace ka kai mu,"yajuya yana kallonta sannan yace "xo nan,"

intisaarta ruko ta da sauri dan xuwa xatayi, waniirinkallo yyi mata ba shiri ta sake kanwartata, tatafi

kuwa da saurinta, "me kika ce?" ta sakemaimaitawa tana kallonsa, rankwashi ya kaimata a ka har sau uku, ta fashe da kuka,

yace"na taba wasa dake ne?" nan da nanhawaye yaciko idon intisaar, xainab ma ta hade raiammabata ce komai ba.... Daga ta yyi sama ya sako

gaban motar sannan ya kulle motar ya ja tasukayi gaba, intisaar ta xaro ido tace "ya tafi daitaxainab," xainab tace "mu tafi kawae ae xai

dawoda ita," ba don ran intisaar ya so ba xainabta jata suka yi busstop, don duk hankalinta na

wajenkanwarta, kuma taso taje ta sanar da momyamma xainab ta hanata, wae ai ba gudu xai

yi daita ba. Anty nafisa tayi farin cikin ganinsusosai barin yanda taga sun xa ma yan mata gabadaya. 'ya'yanta biyar suma duk sun girma,

Antynafisa tana da kirki sosai, aiki suka je taya taamma bata bari sunyi komai ba sai hirar dasukadinga yi, basu bar gidan ba sai wajen karfetakwas mijinta ya mai dasu gida, ta cika sudatsaraba sosai, sannan tace ita ma xata xogobe.

Amma abinda ya daure masu kai bai wucerashinganin fadila a gidan ba amma basu cekomai basuka ja bakinsu sukayi shiru. Ko da suka

Koma gida Aliyu bai dawo ba, hnklinta ya tashisosai, ta

gyawa momynta da ihsaan ya fita tun dasafe,momy bata ce komai ba tana ta harkargabanta,

ganin hka ne yasa tayi sashin inna ta gyamataita da xainab, inna tace "duk inda suka jexasudawo, meye abun damuwa, ba kanwarsa

bace,"

ita dae hnklinta bai kwanta ba. Xainab tabajewainna tsarabar da nafisa ta basu, tana ta saalbarka. Karfe tara da minti hudu Aliyu ya

shigopalon, yana rungume da ita tayi bacci...

 Inakukaje hka Aliyu, yace "in da kka aikeni," batasakecewa komai ba, ya kwantar da ita sannanyace"sae da safe" ya fice. Da sauri intisaar ta

Miketaje kusa da ita da durkusa tana tada ta,

Innatace "ya haka tana barci xaki tashe ta, je kishinfide ta a daki" ta dauketa tashiga daki

Takwantar, sannan ta fara duddubata don ita

Batayarda da Aliyu ba kilama cutar ta yaje yayi, sai Da inna ta kirata sannan ta dawo parlon, inna

Tace"Aliyun ya shiga ya gaida nafisa,?" duka suka yiwuri-wuri suna kallon inna, intisaar ta maxa

taceeh," to meyasa fadila baku dawo tare ba?

Tun takwas ta dawo ita, xainab tace "ohonmata," nandae inna ta dinga yi masu surutu, harintisaar ta

mike tace "inna ni dae sai da safe bacci na keji,"

kamar warce ta tuna abu kuma tayi saurincewa

"au na manta a nan xan kwana, sannan tashigedakin inna," sae da tayi wanka tayi shirin

Baccifaruuq ya kirata, sun jima sosai suna waya daga bisani sukayi sallama ta kwanta.

.

.... Yau wajen watan su Hajiya uku basagidan, bbu yanda momyn intisaar bata yi daAlhaji ba amma yaki hucewa, inna kuwaidan kana son ganin bacin ranta kayi matamaganansu, ko kayi nuni da cewar tayihkuri tabar Abba ya dawo dasu, nan da nan xaku Batada ita. Yau Aliyu ya cika sati hudu da dawo

wa,har ya gaji da yi ma Abbansu magiyan yabaruwarsa ta dawo gidan, Anty nafisa ma taxo

tayima inna magana da ta fuskanci abinda akeciki,amma tace lallai sai sunyi shekara daya agidaniyayensu, abun yana damun Aliyu sosai,xainab ma harta fara damuwa, ita kuwa fadila daman satan hanya take yi taje wajen mahaifiyar ta suyi ta sake sake da kwance kwance. 

Yaukam abin ya ishe Aliyu yaje suyi tata kare da inna,tana xaune gaban akwatin talabijin waetanakallo, intisaar tana daki lkcn tana kwance,

Aliyuya nemi gefe ya xauna yace "inna wajen kinaxo,"

tace "to sannu da xuwa" ya danyi tsaki yace “nifa inna na gaji da rashin uwata a wannangidan, ke waye ya raba ki da danki da harxakirabamu da uwarmu sbda wani dalilinbanxa, toni de na gaji wllh, idan xaki kira danki kiyimasamagana ya maido min da hajiya ta gidannan to,idan kuma ba hka ba wllh na bar gidan nansaekun sake ganina, ta juya tana kallonsa tace"kwantar da hankalinka, uwartaka tacidarajarintisaar xan sa a maido ta, amma ba donhka bawllh sai na nuna masu ni na haife Abubakar,

yace

"darajar wa?" inna tace "intisaar," dondaxun nantaxo ta sani gaba tana kuka, kuma don hkaxansa a maido Aisha da shafa, wani irin bakin

Cikida takaici ya mamayesa, ita intisaar dinwaceceda har xa aci darajar ta, lalle inna, ya dubetayace " intisaar din banxa, ai sae daimahaifiyatataci darajarmu ba ta wata intisaar ba,wayanintisaar dake palon ya fara kara, inna takwalomata kira taxo ta dauki wayarta kuma wayeyakirata," ba karamin tashin hnkli Aliyu yashiga bada ya gano intisaar na dakin, a sanyaye tafito tadauki wayartata ta koma ciki, ya mike a fusace yana duban inna, "wllh idan kika sake

Takuramauwata a gidan nan hajiya Rahmatu sai na......

Kamin duka ko? Inna ta karasa masa, danbnxanyaro fitsararre, mai halin bnxa kawae, yajuyayana dubanta yace ni? Tace a'a uwarkaAisha, yyihuci yace shknan mu xuba dake, ya juya yaficea fusace, a gaban wannan jakar inna kexaginsa,tab lallae, inna ta fashe da dariya tana "donubanka ya ka wuce, ka tsaya mana muga ni Dakai waye tatattce, bai tanka mata ba yyigaba,

Yaron bnxa kawae, kai Allah dae ya shimaHaisam Albarka yaro mai kirki, mai hankalidabiyayya, intisaar ta fito tace "hva inna donAllah

ki dena biye yaya Aliyu, inna tace "mantadashi dai dai nke dashi dan uwarsa, kuma bariuban

nasa ya dawo, kece shaidata kinga daiyanda yaxaxxageni, intisaar ta xaro ido a tsoracetace "A'a wallahi ni ba shai'dar ki...

Tana kwance a palon momyn ta suna kallon tashar Kidscov ita da ihsaan, momy kuma tana bedroom kursum tashigo, "intisaar ana kiranki," ta dubeta da sauri tace "wa?"

Kursum tace "inna" ta mike da sauri kmr dama jira take tace "momy inna tana kirana," momy tace "sai kin

dawo" kursum tace "ina kwana," lfya lau, momy ta amsa daga ciki sannan suka fice, a hanya

intisaar ke tambayarta ko aiki inna xata sa ta, kursum tace "oho tana dai palon abba," su

ka shiga da sallamarsu palon, inna na xaune kan carpet xainab na kusa da ita, Abba na xaune

yana kallon Aliyu dake durkushe a gefensa kamar me neman gafara, fuskar nan tasa a hade, nan

da nan taji gabanta ya fadi, ta daure ta nemi gefen xainab ta xauna, ta gaidasu.... "ehe , ki

gayawa babanku abinda Aliyu yyi min jiya, don ya karyatani ynxu," inna ta fadi tana kallon

intisaar ranta a hade. Abba yace "intisaar ki gaya min me ya faru jiya, me Aliyu yyi ma Inna?

Intisaar tuni ta firfito da idanuwa a tsorace tace "ni?" inna tace "kwarai kuwa ke kadai ce

shai'data a nan don ya karyatani," Ni Hajiya ki daina cewa na karya taki don.... Abba ne ya katse shi da

tsawa "wllh ka sake bude bakin ka a nan Ali xan watsa maka mari," Abba ya dubi intisaar yace "ina

jin ki fateema," ita kam tuni ta fara rawan dari, ta juya ta sace kallon Aliyun, ta ga kallonta

yake yi, idon nan nasa yyi jajur. Ta girgixa kai muryarta na rawa tace "wllh Abba ni ban

san komai......" inna ta daka mata tsawa tace "to ke din ma karyatani xaki yi, bayan nace kina

wajen kuma kece shai'data,?" aa inna, ta fadi tana kokarin maida kwallar da ta taru a idonta, xan fadi

gaskiya. Ta juya ta kara sacen kallon Aliyu, har yanxu kallonta yake yi, ta ma rasa wani irin

kallo yake mata, can dai tace "Abba dama yaxo ya same inna ne akan maganar dawowarsu

Hajiya,

shine sae inna ta fara masa masifa......" fashewar dariyar xainab ne ya katse ta,

Abba yace "meye haka,? get out" da sauri xainab ta mike ta fice tana dariya. Inna kam tuni ta

Bude baki tana kallon intisaar, Abba yace "ina jin ki fateema" ta dan gyara xama tana kallon

Aliyun sannan taci gaba " shine sai bai ce mata komai ba, tana ta fada har......" murmushin da taga

Abba yayi ne yasa tayi shiru. Sai a lokacin inna Ta saka salati tana tape hannu baki a bude,

Abba ya dube intisaar yace "je ki fateema" ta mike da sauri ta bar falon ba tare da ta kalle kowa ba.

Da sauri ta shige palonsu, momy dake xaune ta dubeta tace "lafiya?" ta kirkiro murmushi tace

Ba komai. To ranar dai Intisaar ko nan da kofa bata fita ba, tana palo a xaune har da yamma,

Xainab ta shigo tana ta tuntsirar dariya, ita dai bata Ko kalleta ba ma, ta dae gama dariyar ta ta fita.

Wajen karfe biyar taji muryar inna da alamar sashinsu xata yo, da sauri ta figi hijabinta ta

fice, momy tana ina xaki amma tuni ta fice, ta canxa hanya don ma kar su hade da innar,

Ta sashinsu xainab ta bullo, xainab tace "daga ina haka? Ina xaki" ko kallonta ma bata yi ba tayi

gaba abinta, dariya xainab tayi tace "yau yarinya ta watsa ma innar ta kasa a ido," hanyar gate

intisaar tayi har wani xaxxabi ma take ji, xaune taga Aliyun a kusa da gate yana waya......

.. Yana ganin ta kuwa ya mike, ta tsorata sosai ta juya xata gudu, yayi hanxarin fixgo ta,

Ta saki kuka tace "na shiga uku me nayi....." tura ta da yayi ne ya sanya ta hadiye sauran

Maganar tata, "Allah ya taimake ki yau da sai nayi gunduwa gunduwa da ke" ita kam babu baki

Sai gyada masa kai kawai takeyi, tashi a gaba kar nayi ball dake, da sauri ta fice daga gate din

Ba tare da tasan inda xata ba. Gidan wata kawar xainab dake nan layin ta shiga, farida tayi

mamakin ganinta don tasan baxuwa gidansu intisaar take ba, nan dai ta tsaya har tayi

maghrib sannan ta kama hanyar gida, yanxu tsoranta daya gamuwar ta da momynta don

tasan inna ta gya mata. Tana isa gate tayi jigum a bakin gate din ta kasa shiga, can dae sai

ta fara leke-leken cikin gidan, taji an kirata, da sauri ta juya a dan firgice suka yi ido hudu da

faruuq,

"lah.. Ya faruuq yaushe kaxo?" yace "hmm” leken

me kike yi a cikin?" 

no xainab nake jirane, mu shiga ciki," tayi saurin shigewa gidan, ya bita a

baya yana murmushi, yasan ba gaskiya ta fadi ba.

Ta juya ta dubesa tace kaje can wajen inna gani nan xuwa dama momy ce ta aikeni," to bari

Na fara gaida momyn mana," da sauri tace "a’a kadai je gun inna idan xaka tafi sae ku gaisa,"

yace ok

sannan yayi sashin inna.

Tana isa kofan parlonsu sae da tayi kusan minti biyar sannan ta shiga,

momy da ihsaan na cin abinci, ta nemi gefe ta rakube, momy ta  harareta bata ce komai ba.

A haka suka gama cin abinsu. momy taje tama ihsaan wanka, ita dae tana nan a bakin kofa

A xaune. Xainab ta shigo da sallama tace "ke yar walakanci ce pa yarinyar nan, shine xaki bar

bawan Allah tun daxu yana jiranki," ta mike da sauri tace "bari nayi wanka na manta ne,"

sannan ta shige bathroom tana satan kallon momy dake shafawa kanwar tata powder. Ta saka

kayan barcinta sannan ta dora dogon hijab har kasa ta fito, ta dubi momy tace "ina xuwa momy,"

ko kallonta ma bata yi ba ta fice a sanyaye, ko me inna ta tsara mata oho. Tana isa sashin inna

ta  nemi gefe ta tsaya sannan ta fara kiransa, bugu daya ya dauka tace "ka fito ya faruuq ina

nan waje," yace "baxaki shigo....." da sauri ta katse sa ta hanyar cewa "aa ka dai fito ina jiranka

sannan ta kashe wayan" ya dubi inna yace "inna ni xan tafi sai wni lkcn," aa to ina intisaar

dinm baxa ta xo bane, yace "aa tana nan waje tana jirana. 

Yana fitowa ya kalleta yayi murmushi yace "sae yanxu?" bata ce komai ba sae gyada

Masa kai da tayi, sae da ya fara shiga suka gaisa da momy sannan ta rakosa gate, ya dubeta yayi

Yar dariya yace "me ya hadaki da innar taki baki San shiga wajenta?" tayi yake tace "aiki xata

sani ne shi yasa" yyi dariya yana kallonta yace "ke dae fadi gaskiya kanwata," ta kauda kai bata ce

komai ba sae hmm. To bara na wuce kar Abbanki yaxo ya same mu a nan ko?" da sauri tace

"wa?"

ya kashe mata ido yace "Aliyu mana" tace

"uhum kaga sai da safe ya faruuq yau ba hira kake san min ba" yayi dariya yace "dama ae wuce wa

Xanyi bayan kinsan kin wa inna laifi xaki turani can" bata ce komai ba sai murmushin da tayi, ya

Ciro kudi mai yawa yace taba ihsaan, don yasan ita ba karba xata yi ba, shima din da kyar ta

Karba, suka yi sallamah ya wuce, sannan tayi

sashinsu.

Tun faruwar abin suke wasar 'yar buya da inna, yau dae kam har dakinsu inna taxo ta

sameta, tayi mata tatas, ita dariya ma abun ya bata, can dae ganin ba kyaleta inna xatayi ba tace "to

naga dae inna ba sharri nayi......" dundun da inna ta kai mata ne yasa ta fashe da dariya, tace

"kai ni inna ki kyaleni, haka kawae ban ji ba ban gani ba ya Aliyu ya min duka," da kyar inna ta kalleta

Ta bar sashin nasu, momy dae bata ce masu komai ba, sai gashi da daddare wae xata wajen

inna, momy tace "amma baki da kunya wallahi" tayi dariya tace "to momy ae dae inna ta ce."

A hanya suka hadu da xainab, ta bude baki tace yau kuma wajen inna xa a? Har an manta... Duka ta kai

mata ta bar wajen da sauri, xainab ta bita ita ma tana cewa "tab ae wllh sae na rama" da

sauri ta bude kofar palon ta afka ciki tana dariya,

Inna tace "lafiya ke da wa?" ta juya da sauri xatayi magana sae kuma tayi shiru ganin Aliyu

xaune a parlon yana cin abinci... Xainab ta shigo ta da'da mata duka ita ma sannan tace "na rama"

intisaar dae bata ko kalleta ba sae kame-kamen da ta fara yi, inna tace "ku dae ban san randa

xaku girma ba," Aliyu ya mike yayi tsaki ya dube

xainab yace "get out kar na fasa maki kai," ta harare sa

tace "saboda kan nawa......" da gudu ta fice ganin ya yo kanta, ae intisaar na ganin haka ita ma

ta fice a guje, inna tace "kai wallahi mugu ne yaro nan" kofar ya rufe ya dawo yaci gaba da cin

abincinsa yana kallo. Suna xaune a palon inna,

xainab na daddanna mata kafa, intisaar kuwa kallo takeyi sae kursum dake kwance ita ma

tana kallon, inna tace "wannan yaron yace xae xo da bakuwa yau ko me xamu girka mata?"

xainab ta yatsine fuska tace wai Aliyu? Inna tace "eh," ta tabe baki tace abinda muka dafa a gidan

xamu bata mana. Khadija dake dakin inna tace "kamar ya abinda muka dafa xamu bata? Ita bakuwar

xa a ba wa dafa duka?" xainab tace "shi kuma dafa dukan ba abinci bane ba koh?" khadija tayi

tsaki tace oho. Kar ki min rashin kunya wallahi don xan fasa maki baki, xainab ta fadi tana kokarin

mikewa, inna ta fixgota tace rabu da ita.

kursum je ki ki kira min Zainabu, da gunguninta ta fice wae ita ta gaji. Ba a jima ba momy ta

iso, inna tace "zainabu shinkafa da miya xaki girka min, wae Aliyu xai xo da bakuwa, wannan

gantalallun 'ya yan sai yawo suke da hankalina.

Ta ce "to inna sannan ta fita." xainab tace "inna budurwarshi ce?" inna tace kya barni

budurwa,"

kursum tace yau akwae buduri kenan. Nan inna aka tashi aka fara gyare gyare su xainab na

tayi mata dariya kuma suka ki taya ta, intisaar kadai ce ta kama mata aikin don wae bayan

la'asar xasu iso. Momy ta gama girki ta kira xainab taxo ta dauka ta kawo sashin inna. Karfe hudu

da rabi ya shigo parlon da sallama, yana sanye da kananan kaya yayi kyau sosai, inna ta amsa

da fara'arta tana cewa "ina yarinya," yace tare muke, sannan ya dubi su xainab yace "ku kuma

uban me kuke yi a nan, da sauri intisaar ta shige dakin inna, xainab ma ta bita kursum kadae ce

taki tashi, har yarinyar tayi sallama da siriyar murya, inna ta amsa da karfinta tana wangale baki,

yarinyar ta shigo palon.

... Tana shigowa palon ya nuna mata kujera ta xauna, kursum dake kwance dama tuni ta

mike tana karewa yarinyar kallo, doguwa ce kyakkyawa fara amma da ganinta kasan ta

hada da mai, tana sanye da atamfar Holland an mata shegen riga da skirt dinkin ya dameta sosae,

sannan ta sakale wani dan guntun mayafi kalar atamfar tata yellow a wuya, make up kuwa

har da na hauka don har da su blusher, sae

wani yatsine fuska take, inna dama tuni bakinta a bude yake... Kursum ta dan sa kafa ta bugi

inna alamar ta rufe bakin, ba shiri kuwa ta rufe hade da cewa "ikon Allah! Ina yini? Yarinyar ta

kalle innar tace "sannu baba" tana taunar cingam hade

da karewa parlon kallo, inna tace "yauwa pa" Aliyun kuwa tuni yayi hanyar fridge xae

dauko mata lemo da ruwa. Inna dae ta dage sae kallonta take daga sama xuwa kasa, can sae

ta fashe da dariya, kursum ta rufe fuskarta cikin kujera dan ita ma kar tayi, don shi ke cinta,

daga yarinyar har Aliyu juyawa sukayi suna kallon inna, inna dae ta kasa daena dariya, Aliyu yace "wae

meye haka ne Hajiya?" tayi kokarin shanye dariyar tace "wallahi wani abu na tuna ne" sae kuma

ta kwalo wa xainab kira, "xainab ku xo gu gaisa da Antyn taku mana" xainab dama kamar jira

take tafito da sauri don tuntuni take son lekowa amma tana tsoran kar Aliyu ya ganta, intisaar ma ta

fito don tana san ganin budurwar tashi, gefe suka nema suka xauna, xainab ta kalle yarinyar

sannan ta kalle intisaar da ta sunkuyar da kai

saboda dariyar dake cinta, ita kanta xainab daurewa take amma da tuni ta fashe da ita.

Inna ta sake kwashewa da dariya tana kallonsu xainab din, tace "ku kawo ma antyn taku abinci

“No”a barshi kawae naci a gidanmu kafin na fito," Aliyu sae kallon inna yake cike da takaici.

Inna ta kara dacewa "to ai bamu ma san sunanki ba" sunanta safeeyna, Aliyu ya taya ta fadi. "ayya

amma wannan telan naki bai maki adalci ba, atamfa har atamfa amma ya tashi yayi maki

dinki kamar 'yar babyn roba, ae wannan riga taki ko ihsaan jikin ta baxae shigeta ba, amma

wannan anyi dan banxan tela," inna ta fadi tsakaninta da

Allah babu ko dar. Xainab bata san sanda dariyar da take ta hadiyewa ya kubce mata ba, ta

Xube jikin intisaar tana dariya kyal kyal kyal,

intisaar ta daure iya daurewa amma ta kasa rike nata dariyan, nan ita ma ta fashe ta har da

xubewa kasa, kursum ma yi take har da bingirowa daga kan kujera, inna ta bude baki tana kallonsu

da mamaki can ita ma dae ta fashe da dariyar suka taru suka dinga yi, "ni wallahi ca nake xabiya

ce ma ta shigo don hasken yayi yawa, tsoro ma ne ya kamani...." inna ta sake jefo masu. Xainab

har da hawayenta don dariya, intisaar cikin hijab din xainab tashige ta dinga yi kamar wasu

sababbin kamu. Aliyu kam kasa cewa komae yayi sae kallonsu da yake yi daya bayan daya.

Safeenah kam iya kan kulewa tayi shi, ta mike tsam tana kallon Aliyun a nutse tace "Haidar help me

out of dis forsaken house plss" inna tace "lah har xata wuce?, ko me take cewa?" tuni safennar ta

fice daga palon innar da takalminta me kamar tsani,

inna ta tafe hannu tace "ohh yanxu idan ta fadi da tsautsayi ba karyewa xatayi ba da wannan

tsanin dake kafarta" ya mike da sauri duk a rikice yake ya fice ya bita yana kiran sunanta, inna ta bude

baki tace "ikon Allah ko sallamah babu ni Rahmatu" sae kuma ta mike da sauri tayi

bakin kofa tana cewa "Aliyu kakai ta, ta gaida xainabu tana ciki" amma tuni har sun ma isa gate. Ta

dawo tana cewa "inda ranka xaka sha kallo" ta kallesu xainab da har yanxu dariya suke kamar

mahaukata, ta hade rai tace "kai ni fa bana son iskanci dariyar meye haka?" kursum ta mike

tace "na tafi wajen momy ni kam kun ga tafiyata, don yau idan ya Aliyu......" shigowar khadija ce ta sa

tayin shiru, don dama taje wanke gashi, ta dubesu idonnan na ta a xare, tace "kai!! me

kuka yi wa yaya Aliyu? Naji yace wallahi sai ya sumar da mutum daya a gidan nan " tana fadin haka,

kursum ta bar falon a guje xa ta sashinsu intisaar, nan da nan hawaye ya fara sintiri a idon

intisaar, cikin kuka tace"xainab wallahi ke ce kika....." wani axababben ihu can ciki ciki

suka ji kursum ta saki... Sallati inna ta saki ta fice a

guje tana cewa shikenan ya kashe ta!!

Intisaar ta daura hannu biyu aka tace wayyoo nashiga uku na lalace, xainab tuni ta firfito da ido cike da

tsoro tace "mun shiga uku!!!"

 Aliyu ya kauda kanshi ba tare da yace

mata komai ba, sai da Abba ya bari tayi mai

isarta tayi shiru sannan ya nisa yana duban

Aliyun da kyau yace "ka gya min meye

Matsalar ka a gidan nan, me ke damunka?" kansa kawae

ya sunkuyar ba tare da yace komai ba, "why is it alwayz you  in this house? Don me ba a kawo

min karar haisam sae taka? Look.. Wallahi ka sake taba min wani a gidan nan sae nayi mugun saba

maka,

mutumin banxa kawae, tunda ka dawo gidan nan hankalina bae kwanta ba" ya dago kai da

kyar

yana duban Abban nasa yace "to Abba ka

gyawa inna ta fita harkata ta daina min...." shut up!

Abba ya katse sa a fusace, " dama duk cikin 'ya yana kai ne baka da manner, amma xanyi maganinka" Abba ya mike ya shige

Bedroom sakamakon kiransa da akayi a waya, sae a sannan Aliyun ya dago ya fara kallonsu daya

bayan daya a palon, ya mike yana duban innar dake kallonsa yace "ba wata tsiya bace idan

na bar maku gidan, amma sae kun sake gani na "

sannan ya juya xae fice, inna ta mike da sauri tana cewa "to Bukar sae kafito gashi nan ya

hada kaya xae bar gidan wae" ido Aliyu ya xaro yana kallonta, ya koma inda yake da sauri, Abba

ya fito yana kallonsa yace "to tashi ka wuce" bae ce komai ba sae tiles din palon da ya xubawa

ido,

Nan Abba ya dinga masa fada kamar xae ari baki, inna na ta xuga sa, har dae daga karshe

Abba yace ya fice masa a palo, ya mike ransa a bace kamar ya hadiyi xuciya ya bar palon.

Da Yammar ranan intisaar da xainab suna tsakar gida tare da inna dake yi ma ihsaan tsifa take tambayar su

Ko sun ga Aliyu tun daxu don tun bayar barinsa palon abba basu sake ganinsa ba khadija

ma ta kai masa abinci daxu da rana ta gama bubbuga kofarta ta dawo bae bude ba, xaenab tace

"kila tafiyar yayi," inna ta dan marairaice fuska tace "Allah dae yasa ba tafiya yayi ba...."

Budewar gate din da akayi ne ya sanya su duka suka maida hankalinsu wajen, Aliyun ne ya shigo, yayi

Sashinsa ba tare da ya kalle su ba, sae ga Hajiya ma tashigo rike da jaka, umma na biye da ita a

baya,

sannan khadija ma tashigo da wani jakar a hannunta, da gudu xainab taje ta rungume

uwartata, kursum ma dake kusa da wani flower a xaune taje da gudu ta rungume ummarta

harda kuka, nan da nan inna ta hade rai kamar bata taba dariya ba, intisaar ma ta mike da sauri ta

karbi kayan dake hannun hajiyar tana masu sannu da xuwa, har kasa suka durkusa suka gaida

inna, ta amsa masu can ciki-ciki ba tare da ta kallesu ba, momyn intisaar ma ta fito tayi masu sannu

da xuwa da fara'arta, sannan duka sukayi sashinsu, tsakar gidan ya rage daga inna sae intisaar

da ihsaan, inna ta tabe baki tace "shegu munafukai,

wallahi ni banyi farin ciki da xuwansu ba tsinannuna mutane." intisaar cike da jin haushi tace "ni

bana son wannan abinda kike yi inna wallahi,"

sannan ta bar mata wajen ta koma sashinsu.

.. Tun ranar da Hajiya da umma suka dawo gidan suka shiga taitayinsu, don ba karamin

tashin hankali suka shiga ba kwanakin baya don a nasu tunanin Alhaji ya sake su ne basu sani

ba.

Kullum da sassafe suke xuwa gaida inna. Abinda basa yi da, har wani shiri suka tsiri yi da

Momy duk da na munafurci ne. Yau kam intisaar na xaune gaban inna tana mata hira, inna tace

"yauwa wannan yaron faruuq yaxo ya sameni jiya da daddare wae yana so ke da xainab kuje

Gaida mahaifiyarsa," intisaar ta firfito da ido tace

"kai; inna sae kika ce masa me?" eh nace ranar juma'a ya xo ya kai ku, gobe kenan." intisaar ta hade

Rai tace a’a ni babu inda xanje inna, ke kinga hakan ya dace? Saboda gantali kawae sae na kwashi jiki

Naje gidansu" nan da nan inna ta hade rai tace "to idan yaxo goben karki bisa" intisaar ta mike

Ta fice daga palon tana cewa "ni kam babu inda xanje." tana komawa sashinsu ta fadi ma

momynta, momy tace "A'a ko da ma xaki je gidan nasu ba yanxu ba sae lokacin da ya dace," da

yamman ranar faruuq din ya kirata, da kamar baxata dauka ba sae kuma ta dauka don taji

haushinsa sosae, anata tunanin it’s not decent yace xae kai ta gidansu bayan ba ayi

maganar komai ba tukun.

Bayan sun gaisa yake ce mata

inna tayi mata magana, tace "eh amma babu

inda xani" yayi murmushi yace "to shikenan kanwata." nan dae ya dinga mata hira har yace mata

xae je masallaci don lokacin sallah ya kusa.

Da daddare xainab ta shigo palonso intisaar din tace "ke wae inna tace gobe faruuq xai kai mu wajen

momynsa" intisaar tace "eh amma babu inda xani"

xainab tace saboda me? Ke kinga hakan ya dace?

Intisaar ta tambayeta tana jiran amsa"

Xainab tace "to meye a ciki don munje gaida mamarsa?

Ni dae banga rashin dacewar hakan ba wallahi" intisaar ta mike tace "ke kya iya xuwa, amma ni

baxan je ba." sannan ta shige daki, xainab ta tabe baki ta yi gaba abinta. Washegarin ranar juma'a

inna ta xo sashinsu wajen karfe sha daya, tana kwance tana kallo, momy kuwa na bedroom, inna

tashigo palon tana cewa "ke wai wace irin yarinya ce xaki bar bawan Allah tun daxu yana jiranki,

wannan wani irin wulkanci ne, na aiko a kiraki yafi sau hamsin sae kice min kina xuwa?" intisaar

tabe baki tace "ko ma de sauna nawa ne ni dae

ki rabu dani inna babu inda xani pa" au uwar taki ta hura maki kunne kice min baxaki ba kenan?"

da sauri momy ta fito tace "maxa ki shirya kuje, ni ban hanata ba inna" dolenta ta shirya cikin

atamfa java red colour an mata dinki riga da skirt dama gata fara sosae sae ya amsheta, ta danyi

kwalliya tayi kyau sosai sannan ta dauki hijab dinta har kasa, ta fito palo tace "momy na

tafi" momy tace "ki kama kanki, kuma ku tafi da ihsaan, sannan ki turo min xainab" ae da ita

xamu momy, momy tace "eh nasani," tana fita tayi sashin su xainab, ta hadu da khadija a

bakin kofa tana dauraye cup, tayi mata wani irin kallon

banxa sannan tace "amma de kinyi batan hanya ne ko?" tayi jim sannan tace momyna ke kiran

xainab. Aliyu ne ya fito yana dubanta yace

"get out" cikin tsawa, xainab ta fito da sauri ita ma ta

shirya cikin wani material ja, tace gani nan xuwa intisaar. Gidan uban wa xaki? Aliyu ya

tambaya yana kallon xainab din, "inna ce xata aike mu gidan kawarta wae," bae sake cewa komai

ba ya shige ciki kawae, hajiyarsu kuwa tana sashin umma suna tseguminsu da suka saba. A

tare suka je sashin inna da xainab din bayan taje kiran da momy ke mata, ita dinma ta ja mata

kunne ne akan su kula da kansu, ashe faruuq din

ma bae xo ba inna duk tabi ta axalxalesu.

Sha daya da rabi ya shigo gidan, suka gaisa sannan,

inna tace, "amma dei da wuri xaka maido su ko?" yace in'sha Allah inna. Ita dae intisaaar

hade rai ko kallonsa ma bata yi ba. Har bakin kofa ta rakosu sannan ta koma. Sae da suka

hau kan kwalta sannan ya fara hira da xainab, ita dae jinsu kawae takeyi sae wayanta da take ta

daddannawa.

Tafiyar kusan minti talatin sukayi sannan suka iso gidan nasu, yayi horn aka

Bude gate ya shiga yayi park, sannan ya bude masu kofa suka fito, da ganin gidan kasan lallai

mahaifinsa mai kudi ne sosai. Kanwarsa ya kira ta fito,da ganinta baxata wuce su ba, tayi

masu sannu da xuwa tashiga dasu ciki da fara'arta Har palon mahaifiyarsu tayi masu iso,

sannan ta nuna masu kujera su xauna ta cika su da drinks da kayan ciye ciye, ba a dau lokaci ba

mahaifiyar tasu ta shigo palon, suka sauka har kasa suka gaisheta ta amsa da fara'arta

tanai masu sannu da xuwa sannan tace suyi xamansu a kan kujerar, xainab tace nan ma yayi momy,

"a’a don Allah kuyi xamanku nan ba bakon waje bane," da kyar dai xainab ta xauna kan

Kujerar amma intisaar taki xama, hakan yasa momyn

Ta gano ita ce fateemar. Nan dae ta tambayesu ya mutanan gidan suka amsa mata da duk

Suna lafiya. Ba a jima ba faruuq ya shigo yace xae wuce masallaci tayi masa Allah ya kiyaye hanya

sannan ya wuce yana kallon intisaar amma bata bari sun hada ido ba, sae da suka fara yin

sallah, sannan aka cika su da abinci kusan kala hudu,

Ita dae intisaar ta kasa sakin jikinta ga kunyar momyn da take ji, ganin hakan yasa momyn ta

basu waje tashiga ciki, a tare da kanwarsa ummi suka ci abinci, yarinyar na da kirki sosai,

suka dinga hira kamar da can sun san juna. Karfe biyu faruuq ya shigo gidan ummi ta kai masa

abincinsa dakinsa sannan ta dawo suka ci gaba da hirarsu akan makaranta da sukeyi, sae da

faruuq ya dawo parlon sannan momy ma ta fito, nan dae aka dinga hira amma ban da intisaar da

sae dae tayi murmushi, karfe uku da rabi yace xae maidasu gida saboda traffic, momy tashiga ciki ta

hado masu tsaraba mai yawa tun daga kan atamfa har xuwa sabulai da omo da

jeweries na fashion masu kyau, da after dresses, ummi ma tashiga ta hado masu nata tsarabar na

kayan make-up da turarruka kala-kala, intisaar tace "mun shiga uku xainab, don Allah kice ma

faruuq yace su rage sunyi yawa wllh. Xainab tayi banxa da ita ta dinga godiya kawae, har kusa da

motar suka rakosu sannan ya ja motar suka bar gidan.

Ganin yayi park a wani supermarket ne ya sanya intisaar tace masa "me xamuyi a nan, yace

wannan ba matsalarki bace. Sannan ya shiga ciki, wani tsarabar ya kara hado masu, sannan

ya siya ma inna malt carton daya, da peak milks holland, aka xo aka xuba kayan cikin booth

sannan suka bar wajen. Ana gama sallar la'asar suka iso gida, ya fiffito masu da tsarabar

tasu xainab ta bude baki tana kallonsa tace "me yasa xaka daurawa kanka nauyi haka ya faruuq,"

yace ni dae ku shiga dasu ciki xanje masallaci nayi sallah yanxu, sae na dawo. Kursum ce ta taya su

suka dinga jidar kayan suna sashin inna dasu, shima dan gulma tayi hakan amma ba don

saboda da Allah ba, Aliyu suka tarar xaune a palon, inna ta mike cike da doki tace "kar dae har kun

dawo?" intisaar tayi mata alamar tayi shiru saboda Aliyu dake xaune, haka ma xainab da ta daura

hannunta a baki alamar inna tayi shiru, inna tace "ayyo

haka ne pa." Aliyu yace "ina suka je da?" da sauri inna tace "gidan hajiya Maimuna na aikesu." to

wannan kayan meye haka? Cikin in ina inna

tace

"eh eh.. au ita ce ta bada a kawo min mana" nan ya shiga bubbuda ledojin yana kallon kayan baki

bude inna tayi maxa tace "maxa kuje can guriin xainabu gani nan xuwa" da sauri kuwa

suka juya suka bar wajen, sannan inna ta dinga kwasar kayan tana shiga dasu dakinta Aliyu na

binta da kallo "Allahu akbar.. Yanxu har da maltina aka kawo min?? Lah har da madara ni rahma,

amma mutanan nan anyi mutanan kirki."Aliyu ya bude baki yana kallonta sae kace warce bata taba

shan madara ba ko malt, ita da duk wata abba ke jido mata su dayawa, amma ko sati biyu

ba sayi take shanyewa da yara. "kai Allah ya shima wannan yaron Albarka" Aliyu ya dubeta yace

"wani yaro?" au na manta ne Allah ya shima maimuna Albarka xance, ko da yake ma duk

Daya ne, don dan ta da ya dawo daga waje ne yayo min tsarabar. Aliyu ya tabe baki ya jawo

Abincin gabansa xai fara ci akayi sallama faruuq ya shigo palon bayan inna ta amsa da karfinta,

Mikewa tayi ta rasa inda xata sa shi sae ca take "sannu da xuwa dan Albarka," ya nemi guri ya

xauna ya gaidata ta masa cike da jin dadi, sannan ya ba

Aliyu hannu sukayi musabaha, da dan fara'arsa Aliyun ya karba don bai san sa ba. Inna ta

Mike ta bude fridge ta jido masa lemo kusan kala hudu da ruwa roba uku, ta dire masa a gabansa

Tana tambayensa ya hanya, sannan ta shige ciki ta fito da cin-cin da alkaki bakin nan nata yaki

rufuwa. Godiya ya dinga yi mata, don yana jin dadin yanda inna ke nan nan dashi, ko xaka ci

abinci ne, bari na kawo maka cokali kuci tare da Aliyu, wannan shine Aliyu jikana da nake baka labari,

dariya ma abin ya ba Aliyun, ta dauko cokalin ta saka masa tace suci tare. Aliyun bai yi musu

ba ya sauko yana cewa ki dae yi a hankali karki fadi da wannan barin jikin da kike yi. Bata ko

tanka masa ba tace "wannan shine faruuq saurayin intisaar ae nasan baka san shi ba, Haisam ne

ya san sa," dago kai Aliyu yayi yana kallonsa, nan da nan dan fara'ar dake fuskarsa ya bace, inna

tace to kuci abincin mana kar ya huce, ajiye cokalin hannunsa yayi fuskar nan tasa a yatsine yace "ya

dae ci, amma ni wannan ba isar mu xai yi ba," faruuq ya dago yana kallonsa, ya gane

nufinsa,don hka sae yayi murmushi yace to ni bari naci tunda bako ne ni, da sauri inna tace eh

hakan ma yayi sae ya hakura ayi na dare. Hade rai Aliyu yayi yana kallon inna yace

"kamar ya na jira na dare? Ban gane nufinki ba?"

Inna ta mike ta tabe baki hade dacewa "maida wukar dan nan" sannan ta shige daki sae ga ta ta

Fito da garin rogo da suga ta xube masa a gabansa tace "ka debo ruwa a pampo ka jika kasha don

ruwan kenan na kwaso wa faruuq.

Takaici ya hana Aliyu cewa komai sae bin inna da yake yi da kallo har ta koma ta xauna tana ci gaba da

hirarta da faruuq, shi kanshi faruuq din abin ya basa dariya sosae don har sae da ya dan

dara,

can sae Aliyu ya turawa faruuq din garin yace "shi da ya kwaso yunwa har haka ya shigo sae ya hada ya sha, ni kam am okay" ya fadi a walakance yana duban faruuq din da har

yanxu murmushi na fuskarsa, sallamar Haisam ne ya sanya inna bata tanka masa ba, inna ta

amsa da murnarta tana cewa "yawwa yaron kirki sannu da xuwa shigo ka taya ni godewa faruuq abin

arxikin da yayi min" haisam ya shigo suka gaisa da faruuq da fara'a sannan ya gaida inna da

bakinta yaki rufuwa, yace kinga inna bari naci abinci tukun yunwa nake ji, idan yaso in nagama

sae na taya ki murnar, faruuq ya dubi haisam yace "bismillah kaxo muci wannan don ni ba

wani yunwa nake ji ba," nan da Haisam ya xauna suka fara cin abinci da faruuq din suna hira inna

na tsoma masu baki, haisam ya dubi Aliyu da ya kura wa TV ido yace "ya dae bross lafiyanka?,

kardai yau ma baka je clinic din ba" Aliyu ya watsa masa harara yace a fusace "spare me malam bana

son sa ido plss" daga haisam din har faruuq suka kwashe da dariya inna na tayasu har da

kwanciyarta, Aliyun ya kulu matuka amma bai sake cewa komai ba illa gnash din hakora

da yayi fuskar nan tasa a tamke. Har dae suka gama cin abinsu sannan inna tace idan basu koshi ba

ga gari su jika, faruuq yace a’a ya koshi haka ma, Haisam Nan inna ta fara jawabinta tana

washale hakora " kaga haisam daxu su intisaar suka je gaida mamar faruuq suka yi masu sha tara

ta arxiki, bari na kwaso maka ka gani, gaskiya gidan mutunci ne wannan gida" nan inna ta dinga

jido ma haisam kaya yana ta yabawa da kara taya innar tasa godiya. Ido Aliyu ya xuba mata yana

kallonta cike da mamaki, daxunan tace masa kawarta ta bada a kawo mata yanxu kuma

tace daga gidansu faruuq, dama gidansu faruuq din sukaje? "kaga har kwalin maltina fa haisam,

kai ni dae banda bakin gode maka faruuq, Allah dae yayi maka albarka ya dada budi," ta fadi tana

kallon Aliyu baki har kunne, taga yana mata wani kallon rainin wayo yana girgixa kafa, ta juyo

tana kallonsa da kyau tace "meye kake kallona haka,?

Ka taba kawo koda gwangwanin madara daya ka kawo min gidan nan ne bare maltina? Kuma

Don yanxu na samu me min sae ka dinga min bakin ciki? To ahir dinka, Allah ya fika, har gwanda

haisam duk sati yana yo min tsaraba amma ban da kai don bakin rowa irin taka," ta juyo

tana murmushi taci gaba da shi ma Faruuq da haisam albarka. Ya mike tsam yana kallonta bacin

rai karara a fuskarsa yace "ai ke ba uwata bace da xan dauka gwangwanin madara na kawo

maki,

Idan ma kyautar nake son yi ae uwata na nan da ranta, don haka baki isa nayi maki kyauta ba

Hajiya, wa inda suka ga xasu iya sae su maki.

Aikin banxa kawae aikin hofi, mutum ya tsufa bae san ya tsufa ba" yana kaiwa nan ya fice

Ba tare da ya jira cewarta ba, sashin hajiyarsu ya

nufa, yana shiga ciki rae bace ya fara

Magana "mumy kina gidan nan xaki bar 'yar ki ta fita

raka wata banxa can gidan saurayi? Hajiya ta mike da sauri tana cewa wa kenan? Kursum

daka palon tace "xainab mana daxu ta raka intisaar gidan saurayinta suka dawo da kaya niki-

niki wallahi," hajiya ta xabga salati tana tafe hannu tace "wallahi ca tayi min inna rahmatu ce xata

aiketa gidan kawarta...." bae kara sauraran mahaifiyar tasa ba ya dubi kursum cikin tsawa yace

"ina xainab din?" a dan tsorace tace "tana can Palonsu intissaar can inna tace suje ae" maxa jeki ki

kiramin ita, ta dan marairaice fuska don ita mugun tsoransa takeyi tace "yaya ko naje

ba xuwa xatayi ba da dae kaje da kanka" bae kara bin ta kanta ba yayi sashinsu intisaar din rai

bace yana kwadawa kanwartasa kira, yana isowa wajen sae ya daina kiran nata don yasan

xata iya gudu idan taji muryarsa, daga dan nisa ya hango ihsaan bakin tap tana dauraye cup

din da tasha corn-flakes, tana ganin sa ko ta ruga ciki a guje tace "momy kinga ga uncle nan xuwa,"

intisaar ta xaro ido tace ya Aliyu? Ihsaan ta gyada kanta, nan suka shige bedroom din

momy a guje don tsiyace kadae ke kawo Aliyu

sashinsu, yana isa bakin kofar ya bude yana karewa palon kallo, momy na xaune dama ita ma a palon,

ya kalle ihsaan yace "xo nan," ta isa gareshi tana kallonsa, yace "me kika gudo kika cewa,

kuma idan baki gaya min gaskiya ba xan xaneki yanxu a nan" nan ta marairaice fuska xatayi kuka

tace "nace ma Anty xainab da Antyna kana xuwa"

shine sae sukayi me? Ya tambayeta yana kallonta, "shine sae suka gudu suka shiga

daki," rankwashi ya kai mata har sau uku yace "ki

ka sake gani na kika je announcement sae na cire maki wannan katon idon naki, wawiya

kawai fice min a gaba. Ta ruga da gudu ta fada jikin momynta da ta tsurawa TV ido tun daxu,

tana kuku Ya juya xae bar wajen kenan don yasan ba fitowa xasu yi ba ya ci karo da hajiyarsu

itama ta karaso wajen a fusace, Aliyun yace "me kuma kika xo yi nan Hajiya?" bata bi ta kansa ba ta

dinga kwada ma xainab kira tana cewa

"wallahi ki fito daga gidan nan kar na ci ubanki

Munafukar yarinya," ganin momyn intisaar din a xaune

A palo ne yasa ta ja ta tsaya, Aliyu yayi dan tsaki yayi gaba abinsa, don baya son uwarsa tana

masifa ko neman magana a gidan, ita kuma aikinta kenan. "Zainabu! Ki gya min dalilin sa 'yata

bin watsatsiyar yarki gidan saurayi don a bata ta?"

hajiya ta fadi fuskarta a tamke, ko kallo bata ishe momy ba da ke ta aikin kallonta tana

rungume da 'yar ta, hakan ya kara hassala hajiya don tana matukar bakin cikin sharesu da

momyn ke yi a gidan, kenan ma mahaukata kawae ta maidasu don ba dai amata abu ta tanka a

gidan ba, cikin daga murya hajiya tace "wae ba da ke nake ba ko kurama ce ke?" nan ma de

momy ko kallonta bata yi ba, hava nan hajiya ta dinga

gaya mata maganganu marasa dadi masu kuntata xuciya duk don momy ta kulata amma bata

ci nassara ba don momy murmushi ma kawae take yi. Hayaniyar hajiyar ne ya fargar da umma

ta karaso sashin da saurinta tana cewa "lafiya hajiya me ya faru, rashin kunya ta maki ko me?"

ina fa,, yawon iskancin da da ta sa 'yar ta take yi, shi xasu koyawa xainab dita, tunda gashi yau

har shiryata tayi suje gidan saurayin 'yar tata. Umma

ta xabga salati tana jujjuya kai tace "wallahi kursum taxo ta sameni wae xainab ta bi intisaar

gidan saurayi ya cika su da kaya duk na tsamman shirmanta ne shiyasa ban tanka mata ba"

hajiya tace "Allah ya isa tsakanina dasu," umma tace "to yanxu ina shegiyar xainab din take" bata jira

amsa ba ta afka palonsu intisaar din ta tsaya

gaban momy tana cewa "ki fito mana da 'yar mu kar mu aki abinda baki xata ba gidan nan yau,"

tana magana ne tana nuna momy da dan yatsa, momy tayi murmushi mai sauti, ta kama hannun ihsaan

suka shige bedroom ta kulla kofar. Galala umma ta bita da kallo, hajiya ma ta shigo palon

tace "idan ba tsoro ba dan uban mutum meyasa bae tsaya ba" nan suka dinga xaxxaga mata

rashin mutumci kwando-kwando suna xage-xage, gori kam ta sha shi kala-kala, abinda ya fi bata

masu rai bae wuce yanda ta barsu su kadae suna ta haukansu ba, don a da can idan suna mata

tayi shiru har dadi sukeji a nasu tunanin tana tsoransu ne,.

Ido Aliyu ya xuba masu yana kallonsu, yayi murmushin da xa a iya kiransa da na mugunta

sannan ya hade rai yana kallon xainab din yace "ina kuka je jiya?" ta yarfe hannu hawaye na

sintiri a fuskarta tace "don Allah kuyi hakuri..."

wani irin tsawa ya daka mata yace "it seems kina wasa dani ko?" cikin kuka tace "aa yaya"

gud! Gaya min inda kuka je jiya. Ta juya tana kallon intisaar dake kuka wiwi sannan ta kalle

abban nasu da ya Aliyun tace "gidansu faruuq muka je

gaida mahaifiyarsa" abba yace "waye faruuq din?" saurayin intisaar ne," ta fadi, kanta a

sunkuye.

Cike da mamaki abba ya tsaya kallonsu,

Aliyun yace "amma ina kika ce mun xaku jiya?" "aa

Inna ta...." wani irin tsawa ya daka mata yace "rufe min baki kar na taka ki" yayi hakan ne don baya

Son Abba yasan da ixinin inna suka je, kawae so yake

ya lallasa su barin intisaar. Xainab na ganin hakan tasan yau kam sun banu, nan Aliyu ya dinga

tsarawa abba yanda suka yi jiyan da irin karyar da sukayi mashi, xainab ta san inna ce kadai

gatansu yanxu don abba yayi fushi matuka, da dubara tashiga yi ma kursum tex da wayan

dake hannunta kan cewa ta kira masu inna suna palon abba xa ayi masu duka, duk a rude take,

ganin yanda Aliyu ke tayi wa abba tsari yana dada bata masa rai. Ba a jima ba, kursum ta maido

mata reply, ta bude da sauri hannunta na karkarwa taga me tace, "NO" abinda ta gani knan

boldly

wato baxata turo innar ba. Ta kara sautin kukanta tana kallon intisaar da ta kife kanta

ita ma tana yi, tun ba yau ba tasan kursum muguwa

ce. To wa xata kara yi ma tex yanxu? Don kursum ce kadae hope dinsu, ita ma tace no. Yaya

haisam ta tuna, don haka da hanxari ta shiga yi masa tex duk da baya gidan, ya taimaka ya

kira masu inna taxo. Kafin tayi sendin Aliyu ya

ganta

ya fixge wayar da sauri yana cewa "you re

vry

stupid, wat do yhu fink yhu re doin?" abba

ya

karba wayan ya ajiye gefensu yana kallonsu.

Haisam yyi dariya sosai da yaga tex din, don

sbda tsabagen masifa Aliyun yyi sendin bai

sani

ba. Ai kam yana kiran innar ya gya mata ta

taho

da gudunta tana salati. Tun daga bakin kofa

ta

dinga kwada wa abba kira, hkn ba karamin

bta

wa Aliyu rai yyi ba, don yyi niyar yyi masu

laga-

laga ne, sai yaji kmr ya hankadata ta koma,

nan

ta sake masu kuka tana cewa "ynxu Bukar

don

na tura yaran nan su gaida uwar yaron nan

me

kirki shine nayi laifi?" Abba ya girgixa kai

yace

"dama ke kika ce su je?" ta goge hawayen

dake

idonta tace "eh mana," basu gaya min ke

kka ce

suje ba ne." ya kallesu yace "ku tashi ku tafi."

yyi

hkn ne don baya son uwartashi ta daga

masa

hnkli. Aliyu ya dan bugi kafarsa a kasa yace

"shit" inna ta dubi hajiya da umma dake

xaune a

palon kmr su hadiye xuciya don takaici tace

"to

munafukai ae sae a tashi a bashi waje kuma

ko,"

tayi tsaki ta wuce tana surutanta, don ana ta

tunanin su suka gya masa, duk da su din

suka

gya masa.

.

Suna fita Abba ya girgixa kai cikin damuwa

yace "ni bn san me ke damun inna ba, tana

tsufa

ne hnklinta na komawa na yaro," hajiya ta

mike

ta tabe baki hade dace wa "kawae de ta

kare

matarka ne, amma ka dae yi bincike da

kyau."

tana kai wa nan ta fice, umma ma ta bita a

baya

tana cewa "mu dae Allah ya rufama 'ya yan

mu

asiri kar a sa su a hnyar da bae dace ba, don

wannan lamarin akwae abun dubawa a

ciki"

momy de bata ce komai ba, amma tasan da

ita

suke, ta mike itama xata bar palon Abba ya

kirata ta dawo, Aliyu ma ya tashi ya bar

masu

palon cike da jin haushin inna, ko waye yaje

ya

gya mata ma oho. Suna tsakar gida a tsaye

ita

da xainab suna ta dariyan abinda ya faru

jiya da

safe, hajiya da umma sun je barka, inna tana

can

sashinta, su biyun kadae ne a tsakar gida,

shirun

da intisaar tayi ne fuskarta ya bayyana

alaman

tsoro ya sa xainab ta dakata daga surutun

da

take yi tace "me ya faru," tana waige-waige,

da

sauri intisaar ta fixgota da gudu suka je

bayan

wani flower suka buya, xainab na maida

numfashi a tsorace tace "wae menene?" ita

din

ma numfashin take mayar wa tace "ya

Aliyu."

xainab tace "a ina kika..." tsit tayi ganin

Aliyun ya

doso ta inda suke, cikin kasaita yake tafiyar

tasa,

yana sanye da t'shirt fara kal, da 3quatre

shima

fari tas, intisaar ta bi shi da kallo da

idanuwanta

kmr xasuyi magana, farar kujerar roba ya

dauka

ya ajiye ta opposite inda suke ya xauna.

Basu da

wata fargaba don sun tabbatar idan ba

kusa da

flowern ya xo ya tsaya ba baxae gansu ba,

ya

ciro wayrsa daga Aljihu yana dubawa, suka

ga yyi

murmushi mai kyau har sae da dimple dinsa

ya

nuna, ya lumshe manyan idanunsa ya sake

budesu, ko me ya gani oho. Ashe dae ya

Aliyu na

murmushi, tambayr da intisaar tayi ma knta

knan

a xuciyarta, nan dae ta tsaya ta kare masa

kallo

sosai, don ita kullum kallon tsoro take masa

a

gidan. A xuciyarta tace "ashe dae yana da

kyau

har hka," ta tsura ma sajensa da ya kwanta

luf-

luf a fuskarsa ido, daga sama xuwa kasa ta

dinga kallonsa ko kifta ido bata yi, ashe dae

shi

din kyakkyawa ne sosai, amma duk da hka

faruuq dinta ya fisa kyau tasani, xainab ta

xungureta tace "ke wannan kallon fa?" a

tsorace

intisaar din tace "da'alla dubi yanda kika

bani

tsoro."xainab tace "to naga kina neman

cinye min

yaya da ido, intisaar ta tabe baki tace "ni

kallon

mamaki nkeyi masa" to wae taya ma akayi

kika

san yana xuwa? Xainab ta tambaya tana

kallonta, kamshin turarensa, intisaar ta bata

amsa ba tare da ta kalleta ba. takun da suka

ji

yasa suka kara labewa sosai, momy ce taxo

ta

wuce, bai ce mata ba, bata cemasa ba har ta

wuce sa, da alama sashin inna xata, sae da

ta

wuce shi sannan ya bita da kallo har ta kure

masa, yyi murmushin da intisaar ta gaxa

gane ko

na menene, sannan ya cigaba da danna

wayarsa,

xainab tace "yau mun shiga uku hka xamu

ta

tsayawa ni kam na gaji wllh" intisaar bata

tanka

mata ba ta dan kara satan kallon Aliyun,

taga

kara hakikincewa yyi ma kan kujerar. Ihsaan

ce

taxo wuce wa tana kuka, kila ta tashi bata

ga

momynta ba da yayarta, don bacci take yi,

xata

wucesa ya fixgo ta yace "cum hia, wa ya

dokeki?"

bata ce komai ba sae kallonsa da takeyi, ya

daura ta kan kafarsa yana cewa "idan kika

sake

kuka xan maki allura" ba shiri tayi shiru ya

dago

wayrsa yana ta nunamata ko pix ne ko

meye ma

oho dae, su dae hka suka dinga lekosu har

daga

karshe suka ga ya sauke ta ya mata mgna a

hnkli ta ruga sashinsa da guda, ba ajima ba

ta

dawo rike da chocolate, suka ji yace mata

"run..

Momy tana wajen inna je ki sameta," da

gudu

kuwa tayi sashin innar. Idan ba don intisaar

da

ta dinga rike xainab ba da tuni ta mike ta

bar

wajen, ita kam tsoran abinda xai yi masu ne

yasa ta dinga rike xainab kar ta tona masu

asiri.

don sun gaji sosai gashi aliyu yaki barin

wajen

har sunyi kusan awa biyu a durkushe,

momy da

ihsaan ma tuni suka xo suka wuce. Ba su

suka

bar bayan flowern ba sae da aka kira la'asar

Aliyu ya wuce massallaci. Tana xaune gefen

inna

da ta dage tana ta kirgan kudi 'yan dubu

daddai,

da ta kirga sai ta mikowa intisaar ta duba

ko dai

dai ne, intisaar kam ta xuba mata ido don

bata

san inda ta samu kudin ba, har dae daga

karshe

suka gama kirgan kudaden inna ta dubi

intisaar

din bakinta a wangale tace "nawa knan

gaba

daya?" intisaar tace "dubu dari biyu da

hamsin,

ina kika samo su inna?" ba tare da inna ta

kalleta

ba tana kkrin hada kudaden waje daya tace

"fili

na na saida." intisaar ta xaro ido hade da

bude

baki tana kallon inna. Sallamar haisam ya

sanyata rufe bakinta, inna ta amsa mashi ba

tare

da ta lura da halin da intisaar ta shiga ba ya

shigo, suka gaisa yace "kina sha'aninki inna,

ina

kika samo kudi hka?" ya tambayeta yana

karewa

palon kallo, a xuciyarshi yana cewa kar dae

wani

abun inna ta kuma saidawa, don saranta

knan, in

dae bata da kudi to bata ki koh plaxman

palonta

ta saida ba, hkn kuma na bata wa abba rai

sosai

ba kadan ba, don duk abinda yke mata bata

gani

sae ta saida wani abun palonta ko daki,

"wllh fili

na na saida haisam" haisam yace "mene?"


Ba tare da inna ta kallesa ba tace "nace

mka fili na na saida. Ko bka ji ne" ya nemi

kujera

ya xauna yana kallonta cike da mamaki yace

"wani filin inna?" don dai shi yasan a ynxu

hka

inna bata da fili, idan ba dae wanda ake

mata

gini taje ta saida ba, "wannan din da

babanku ya

siya min" ta fadi tana mikawa intisaar

kudaden

ta kai mata daki. Haisam ya yo waje da ido

"yace wani filin abba ya baki?" inna ta hade

rai

tace "na jan bulo mana" haisam ya saki

salati

yana kallon innar, inna tace "kai ni don Allah

ku

rabu dani, ina da bukatar kudi kuma baxan

saida

kaddarana ba?" haisam yace "ya salam!

Ynxu

inna abba ca yyi maki filin naki ne? Daga ya

baki

takardu ki ajiye masa sae ki je ki saida fili?

Wai

ma nawa kika saida filin?" "ni dubu dari

biyu da

hamsin aka siya," inna ta fadi a marairaice.

Haisam ya mike da sauri yana kallonta ya ma

kasa cewa komai," filin abban kika saida

masa

dubu dari biyu da hamsin? Kin san nawa ya

sayi

filin inna, haisam ya girgixa kai yana kallon

innar

cike da takaici, ita kam sai wuri-wuri take

da ido.

Aliyu yyi sallama ya shigo yana cewa "har

kin

dawo daga yawon inna?" ya kalli haisam da

yanayinsa ya sauya xuwa bacin rai yace "me

ya

faru guy?" Aliyu filin abba taje ta saida dubu

dari

biyu da hamsin wae" haisam ya fadi cike da

jin

haushi, Aliyu ya xaro ido yace "wat?" filin da

yke

cewa xai fara gini cikinsa nxt yr?" dariya

Aliyu ya

dinga yi har da dafa bango, intisaar kam ido

ta

xuba masu tana kallonsu ita ma tasan inna

bata

kyauta ba, tuni inna aka fara hawaye, irin

dariyar

da Aliyu yake yi ne ya kara kullar da haisam,

to

meye abun dariya a nan, ta rangada wa

abbansu

asara, don ko shi bai sayi filin hka ba, cikin

karkarwar murya inna tace "to ni ina nasan

filinsa

ne, da naga bai sake min mgna ba ai nayi

xaton

ya bani ne, kuma Aliyu ba kai ka bani

shawarar

ba to?" Aliyu ya xaro ido yace "wa? Aa karki

sake

saka ni cikin wannan case din Hajiya" inna

tace

wllh kai ka sani, kana ji ko haisam, jiya ya

shigo

da daddare nake ce mashi bnda kudi kuma

ga

bikin jikar aminiyata ya taso bari bukar ya

dawo

na tambayeshi kudi, sae Aliyu yace min ae

Bukar

bai da kudi ynxu hka sae dae idan xan saida

kujeruna ne na biya bukatata, to naga dae

taya

xa ayi na saida kujerun palona, palo ya

xamo

wayam, kuma kwanakin baya ma da na

saida

fridge dina ma ae sae da bukar yyi min

masifa,

to yana fita a jiyan sae na tuna ai akwae

takardun filin da bukar ya bani......" Aliyu ya

daka

mata tsawa yana cewa "ke inna rahmatu

wllh kar

ki saka ni cikin wannan case din na gya

maki,

idan dae mutum ba hauka ya fara ba ta ya

xai

kin kima kujerunsa ya saida don an bashi

shawarar, ni dama wasa nke maki, kuma

magana

ce na gya maki." tuni inna aka fara kuka

wiwi,

Aliyu ya fice yana dariya, Haisam kam kasa

cewa

komai yyi, tun ba yau ba yasan Aliyu mugu

ne,

idan ba hka ba taya xa a saida kaddarar

mahaifinsa mai muhimmanci yayi ta dariya.

Ya

juya ya fice kawae ba tare da yace da inna

komai

ba, to waye ma yyi mata jagora taje tayi

wannan

aika aikan, Aliyu na fita yaje ya sami

hajiyarsa

yana ta dariya ya bata lbrin abinda inna tayi,

ta

hade rai tace "to meye abun dariya a nan

Aliyu,

gadonku fa ta walakanta kke dariya hka?"

ya

mike yana kallon umman tashi yace "ni

banyi

depend a gado ba mum, Allah ya hore min

don

hka, 4 ol i care," ya fice yana ci gaba da

dariyarsa don yasan drama xa ayi a gidan

yau

idan abba ya dawo. Abba ne tsaye kan inna

yana

faman bambamin fada kmr xae maketa,

inna ba

baki sae idanuwa, "kinsan nawa na sayi filin

ne

xakiyi min hka inna, daga baki ajiya sae ya

xama

naki, ina aka taba yin hka? Bbu shawara

bbu

komai xaki je ki walakanta min abun da

akalla

xan iya saida shi miliyan daya da rabi."

hajiya da

umma dake palon ji sukayi kmr su shide

don

murna, Aliyu ya kasa hadiye dariyar dake

cinsa

ya fasheta, abba ya juyo kansa ya dinga

masifa

kmr xai maresa, ba shiri ya kame kansa, don

ran

abba yyi mugun baci ranar. Ganin ba sarki

sae

Allah yasa inna ta fashe masu da kuka tana

cewa "tunda yusufa ya rasu dama nake

shan

wahala a duniyar nan, daga kai har 'ya

yanka

bakwa tsinanani da komai, ni ke yi ma kaina

duk

bukata, Abba ya bude baki yana kallonta ya

ma

kasa cewa komai, shi din ne baya mata

komai?

Gnin ta dage sae rera msu kuka take ne

yasa ya

shiga bata hkri, tce "hka kawae baxan

kyautatawa

aminiyata ba jikarta xatayi aure, kuma

nasan idan

na tambayeka ba bani xakayi ba," Abba ya

girgixa kai yana mamakin uwartashi, duk

juma'ah

sae ya bata dubu goma bayan abubuwan

da yake

siyo mata duk karshen wata sannan ya

damka

mata dubu ashirin ko tana da bukatar kudi,

amma yanxu kiri-kiri tace bbu mai taimaka

mata

a duniyar nan sae Allahnta, komai ita take

ma

kanta. Abba yace "to shknan inna, Allah yasa

hkn

shine mafi alkhairi, kudaden sun isheki de

ko? Ta

dan fara kame kame tana goge kwalla tace

"ni

idan san samune akara min dubu hamsin,

ko

kuma dari ma." takaici yasa abba gyada kae

kawae, ya dubi Aliyu yace anjima ka ciro

mata

dubu hamsin Ali, xan bka, "tab! Ai ni abba

accnt

dina ko dubu goma bai kai ba ina ga ma."

... Inna ta galla masa harara tace "Allah ya

dauwamar dasu a hka," Haisam yace

"anjima xan

ciro na kawa maki inna." nan ta dinga sa

masa

albarka, abba yyi mata sallama ya fice daga

palon nata cike da jin haushin hali irin nata,

Aliyu

ya bi bayansa yana cewa "wannan ai sata

kiri-kiri

ne kawae, daga an baki ajiye sae ki

maidashi

naki" bai jira me xata ce ba ya fice da sauri

yana

dariya. Haisam na fitowa daga palon innar

umma

ta aika a kira mata shi yaje, nan kuwa ta

balbalesa da masifa tana cewa" kai dinnan

soko

ne wllh, Aliyu ya fika wayo nesa ba kusa ba,

kana tunanin idan ka dauki kudin naka har

dubu

hamsin ka bata Alhaji bka xai yi ne? Kai dae

bn

san wani irin yaro bne Allah ya bani, don

meyasa

baxakayi koyi da Aliyu ba, duk ka bi ka tare

gurinta sae kce ta asirce, wllh idan baka yi

gaggawan sauya wannan mugun halin

naka ba

sae na saba mka" haisam ya girgixa kai cike

da

takaicin hali irin na uwartasa yace "Allah ya

kyauta! Sannan yafice a fusace. Shi kam

Aliyu

hajiya yaba masa ta dinga yi tana sa masa

albrka, shi dae bai tanka mata ba. Da

yammacin

ranar Haisam ya kaita gidan aminiyartata

bayan

ta shiga kasuwa tayi kaca-kaca da kudin, a

dole

ita wae sae ta kyautatawa kawartata tunda

bikin

jikarta ce. Su hajiya kam sun ji ddin xuwan

inna

gidan bikin don kwana biyar tace xata yi, ko

ba

komai xasu dan samu sarari a gidan su

sheka

tsiyarsu yanda suke so. Intisaar na daki

wajajen

karfe goma na safe tana duba wani Novel

na

turawa taji hayaniyarsu hajiya a tsakar

gidan, ba

shiri ta fito ta tarda su hajiya sun saka

momynta

a gaba sae maganganu suke gya mata fadila

na

taya su, "idan banda rainin wayo tun asubar

fari

take ta facakala da ruwa sae kace ita daya

ce a

gidan, ynxu idan ruwan ya dauke mu da

wanne

xamuyi ayyukan mu, mun xo muna mata

mgna

kuma ta maida mu mahaukata, to dae mai

daure

maki kugu a gidan bata nan, idan kikayi

wasa...."

xainab ce ta karaso wajen da sauri ita ma

tana

cewa hva hajiya meye yyi xafi hka da

sassafe xa

ku sa momy a gaba kuna..." kyakkyawan

mari

hajiya ta watsa ma xainab din tana cewa

"wuce

ki bni waje munafuka kawai, dama tun ba

yau ba

kike nuna ni ba komai bace a wajenki, idan

bnda

hka taya xa a maida ni mahaukaciya baki xo

kin

tsaya min ba xaki gya min mgnar bnxa, baki

ga

yanda fadila take yi bne don ubanki,"

intisaar ta

kalle momynta da ta tsaya tana kallonsu

kawae

bata ce komai ba, umma ta hankade xainab

tana

cewa bace mana da gani mara xuciya

kawae

warce bata san ciwan kanta ba. Girgixa kai

momy tayi kawae taci gaba da wankin da

take yi

a bakin famfon, hajiya ta fixge bokitin a

fusace ta

xubar da ruwa da kayan dake ciki sannan

tasa

kafa tayi ball da sauran bokitan tana cewa

"don

babanki baxa kiyi wankin nan ba yau wllh,

mu ma

muna da bukatar ruwa" umma ta kashe

famfon

tana kwadawa rahma kira ta kawo mata

kwado

su kulle. Intisaar ta goge hawayen idonta ta

dubi

momynta da ta tsaya kallonsu kawae ba tare

da

tace uffan ba, tace "momy ki bari anjima xan

je

waje na debo makii ruwan wankin, xo mu

tafi" ta

fara jan hannun momyntata su bar wajen,

momy

kam kasa barin wajen tayi, ta xubawa fadila

dake ta faman xaxxaga mata xagi tana

cewa

"mutum ya xame mana annoba a gida,

kuma idan

ana magna ya dinga yi kmr kurma don

tsoro,

wllh hajiya ni kawae da kun bari watarana

na

lallasa ta na nuna mata....." ji kke tass! Momy

ta

xuba mata tagwayen mari masu rai da lfya,

hava

wa! Nan fadila ta gigice ta fasa ihu don

batayi

xaton marin ba, cike da mamaki hajiya da

umma

suka dinga salati suna cewa ita fadilar kika

mara? Hajiya ta fixgo fadilar tace "xage ki

rama

fadila, wllh sae kin rama," umma kam tuni

aka

shige gida da gudu anje shirin dambe, don

tace

wllh sae ta rama ma 'yar ta. Fadila ta dage

xata

mari momyn, intisaar ta fixgota da karfi

tana

cewa "ke yar karamar 'yar iska, ni xakiyi

facing

ba momyna ba," nan intisaar ta dage ta

dinga

xuba mata mari tana tana cakume da

kwalar

rigarta. Nan fa gida ya hautsine, umma ta

fito da

gudunta bayan ta canxa kaya, tayo kan

momy da

gudu tana cewa "ae yau sae dae ni ko ke?"

tam

nan fa momy ta xage ta kai umma kasa suka

dinga cin dambe. Su rahma da kursum suka

hadu suka dinga dukan intisaar din da taki

sakin

fadila har ynxu bayan ta kaita kasa ta haye

kan

ruwan cikinta tana jibgarta iya karfinta.

Hajiya na

ganin an kai umma kasa ana ta nakada, ta

fice

waje da gudu tana kiran jama'ah su xo su

ga

xainabu xata kashe Shafa. Xainab na shiga

daki

da kukanta dama abba ta kira amma yaki

xuwa,

ya Haisam ya tafi kaduna tun jiya, don hka

kawae sae ta kira Aliyu tana kuka ta gya

masa,

sannan ta fito taga irin damben da ake ci,

kuka

ta dinga yi sosae ta ma rasa abinda xata yi

ga

muryar Hajiyrsu can a wje tana aibanta

momy,

mata suka dinga tururuwa cikin gidan duk

da wsu

gulma ya shigo dasu, ihsan ma kuka ta

dinga yi

a kusa da xainb tana cewa "Anty kice

momyna ta

bari." da kyar matan suka kwace umma a

hannunm

momy, sannan aka raba su intisaar shi ma

da

kyar don intisaar komawa tayi kmr

mahaukaciya

duk tayi ma fadila kaca-kaca hka ma kursum

dake..


Xainab ta karasa kusa da intisaar da

hanxarinta

bayan an rabasu, ta fara janta ixuwa

palonsu,

fadila kam ihu ta dinga yi tana fixge fixge

daga

rikon da akayi mata wae a barta sae ta

kashe

intisaar yau, momy ta ja bokitin ta ta tara a

famfon tana cewa "kuma wanki yanxu na

fara,

bnga uban da ya isa ya hanani ba, kuna

tunanin

shirun da nake maku tsoro ne, wllh duk

wanda

yace baxae kame girmansa ba a cikin ku xai

ko

sha mamaki." rirrike hajiya aka shiga yi wae

sae

tayi ma momy duka, hka ma umma ko

kunya

bbu. Wata yar dattijuwa da tashigo gidan ta

dube

momy tace "to ke 'yar nan tunda gaba suke

dake

ki bari anjima kiyi wankin mana, ina ce

sunce aiki

suke son suyi da ruwan su ma" momy tace

"ki

bari kawae baaba wllh munafukan mutane

ne,

idan bnda hka famfofin gidan nan sun kai

biyar

pa, kuma ko wanne na da nasa pampon a

bangarensa, nan bangarena ne amma sbda

neman mgna suka kwaso jiki suka xo wae

baxanyi wanki ba, kuma wllh baaba tank

din

gidan nan babba ne, ko xan kai washegari

ina

wanki bbu abinda xae ragu a ruwan amma

dayake jirana sukeyi shi yasa nayi laifi, toh

bari

kuji, wllh tllh daga yau duk shegen da yace

xae

sake takani a gidan nan sae ya sha

mamaki."

hajiya tace "mu kke gyawa magana hka

xainabu,

dama ashe kina mgna hka amma don

munafurci

idan kinga Alhaji sae ki dinga yi kmr na

kirki?

Don Allah ku sakeni na gwada mata hnkli."

momy

tace "ku kyaleta don Allah" umma ta dinga

dura

mata ashar ta uwa ta uba tana daga inda

take,

don bata sake gigin matsowa kusa da ita

ba, a

dai-dai lkcn Aliyu ya shigo gidan, ya girgixa

kai

cike da takaici ya jingina gefen gate din

rungume

da hannuwansa yana kallonsu, muryar

momy yaji

tana cewa "don Allah don Annabi ku kyaleta

ta

dokeni, wllh tllh Aisha sae kinyi da kin sanin

sani

na, don laga-laga xan maki kuma ba lallai ne

mijin ki ma ya gne ki ba. A fusace Aliyun ya

karaso cikin tsakar gidan yana kallonsu

daya

bayan daya, basu ma san yashigo ba, ya

dubi

fadila da bata da maraba da hauka gashin

nan

yyibuya-buya, daga ita sae leggings, intisaar

ta

dube fadilar dake xaginta ta uwa ta uba

tana

kiranta da 'yar tsintuwar innarsu, tace " duk

da

hkn dae ban xage ina karuwanci ba, na fita

tun

asuba na dawo karfe takwas din dare."

fadila ta

kara rudewa ta shiga galla wa masu rikonta

cixo

wae sae sun saketa ta mata duka, sae kace

ba

ita aka kwata da kyar daga hannun intisaar

din

ba ynxu, Aliyu ya karaso wajen ya sa kafa ya

kwashe fadilar ta xube kasa sannan yashiga

ball

da ita yana cewa "yau xaku ci ubanku gaba

daya,

go down on ur kneels, i said go down on ur

kneels." ya fadi cikin tsawa sannan yyi kan

intisaar din da tuni ta juya a guje xata bar

wajen

ita ma ya cafkota ya watsa mata mari

lafiyayye,

momy ta karaso inda yke da sauri tana

cewa

"kai! Kai! Wllh kar ka kuskura ka taba min

'ya,

cika ta, ta fixge hannunsa daga rikon da yyi

wa

intisaar din, cikin tsawa tace mata shiga ciki,

ta

ja ihsaan ma suka bar wajen" binta yyi da

kallon

mamaki, ya juya kan su hajiya dake ta cacan

baki amma an rasa wanda xae tunkareta

yace

"wllh hajiya kina bni mamaki, ynxu meye

amfanin

irin wannan abun, don me baxa ku kama

girmanku ba, dube yanda yar cikin ku tasa

ku

gaba tana gaggaya maku maganganu, sae

faman

kumfar baki kuke," kai Aliyu kasan me ya

faru

ne? Kasan irin abinda tayi ma umma?"hajiya

ta

fadi tana xaxxaro ido, yyi tsaki yace koma

me

tayi maku kuka siyar wa kanku. Ya dube su

kursum da har ynxu suka ki yin shiru ya

daka

masu tsawa yana cewa "bna son naga ko

wani

dabba a tsakar gidan nan ryt now, get out"

da

sauri duka suka watse suka yi sashinsu,

shima

yyi nasa bangaren ya bar umma da hajiya a

wajen..

Gaba daya mutan gidan sun hallara a

falon Abba washegari da safe, Momy na

xaune

kan 1seater fuskar ta a daure ta xuba ma

plasman ake manne jikin bango ido, intisaar

na

gefenta a kasa a xaune, hajiya da umma na

xaune a 2seater suma rai a hade, sauran

'yan

matan ma gaba daya sun nemi gu sun

xauna a

palon, ihsaan kadae ce ke gefen abbanta a

xaune, Aliyu ya shigo da sallamarsa a dalilin

kiran da abba ya aika ayi masa, ya nemi gefe

shima ya xauna. Abba yyi ajiyar xuciya ya

dubi

intisaar yace "fateemah ki gya min abinda

ya faru

a gidan nan jiya bayan na fita" nan intisaar

ta

koro masa duka abinda ya faru a jiyan, ya

jinjina

kai yace "ikon Allah" hajiya ta yi saurin cewa

"kaji

munafuka amma ai baki gya masa irin

fitsarar da

uwartaki ta dinga mana ba" abba ya daka

mata

tsawa ransa a bace yace "ki shiga

hankalinki." ta

ja bakinta tayi shiru tana hararar sa. Abba

yyi

shiru sannan ya nisa ransa a bace yace

"xainab

ban san ki da irin wannan halin ba, amma

gskya

jiya kin ban mamaki, a tunanina ko da ace

abinda yafi xagi shafa ta maki bata cacanci

ki

rama ba bare har ki hau ta da dambe ba,

kinga

kina da laifi a nan tunda dae shafa ba

sa'arki

bace, don me baxaki jirani na dawo ba ko ki

kirani a waya? Har xagi dubi tsabagen idon

Aisha

baki ji kunyar 'ya yanta ba kice mata

karuwa.?"

tsam momy ta mike tayi masa wani irin kallo

tayi hanyar fita daga palon ba tare da ta ce

komai ba, kiranta abba ya shiga yi amma ko

waiwayowa bata yi ba har ta fice daga

palon.

Hajiya tayi murmushin takaici tace "ka gani

wa

idon ka ko? Wllh jiya na dde ina naxarin

anya

kuwa xainabu ce wannan, rirrike ta fa aka

dinga

yi xata min duka bayan an rabata da umma.

Umma ta tabe baki tace "uhum ae ni naga

abun

mamaki jiya, yarinyar da mutum sae ya

rantse ya

dada rantse wa yace ko kuda baxata iya

kashewa ba, amma ashe duk wannan shiru

shirun

da take yi don taga inna na nan ne, jiya ta

nuna

mana ko ita wacece." Aliyu kam tunda ya

shigo

falon yake ta daddanna wayrsa bae ko daga

kai

ba. Abba ya dube su intisaar din gaba daya

yace

"daga yau na sake jin abu makamancin hka

ya

faru a gidan nan wllh tllh sae na karya

mutum,

kuma bna son naji wata magana ya fita

daga nan

har yaje kunnan inna, idan na kama mutum

da

karya wannan dokan sai na saba mashi

kwarai

da gaske, ku tashi ku ban waje shashashan

bnxa

kawai" duka suka mike suka bar palon,

intisaar

kam jikinta yyi sanyi sosae. Hajiya tace tana

nuna intisaar "har da 'yar mitsitsiyar 'yar

nan, ta

dubi tsabagen ido na tace min mayya" sae

kuma

ta fashe da kuka tana girgixa kai tace amma

bbu

komai ai tun farko idan muka ce mka ga

abinda

xainabu tayi bka yarda ynxu kam ai ka gani

da

idonka, Aliyu ya mike yana kallon abban

nasa

yace "kayi hkuri abba," sannan ya fice. Nan

hajiya da umma suka dinga aibanta momy,

hajiya

sae matse kwalla take, abba kam tv ya xuba

ma

ido bai tanka masu ba, umma tace "har ca

tayi

wae fadila ba 'yar ka bace karuwan....."

tsawa

abbaya daka masu ya mike yana cewa "ku

fitar

min a palo don Allah, sannan ya shige

bedroom."

hajiya ta bude baki hka ma umma, hajiya

tace

"da yake ran matan so, kuma yar gwal ya

bace

dole duk ka fice hayyacinka ae. " nan da

suka

gaba babatunsu su mike suka fice daga

palon

kowa da takaicinsa.

Intisaar na xaune kan darduma bayan ta

idar da sllhr isha'i, Abba yyi sallama ya shigo

palonnasu, ta ce "sannu da xuwa abba, ina

yini"

yace "lfya lau fatima ina momyn taku?" tace

"tana cikin daki" bai ce komai ba ya shiga

dakin

da sllma, ba kasafai Abba ke shigowa

bangaren

matan nasa ba sai da babban dalili, ta mike

ta

kwashe kwanukan da suka ci abinci ta fita

dasu

ta wanke don momynta ce tayi girki, sae da

tashiga kicin ta kwaso sauran kwanukan

wanke-

wanken mutan gidan sannan taje bakin

famfo

tana wankesu don tana tsoran wankesu a

kicin

kar 'yan gidan su rutsa ta, tun da safe dama

momy bata barta ta fito ba, ita tayi duka

ayyukanta sae xainab da ta fake idon

hajiyarsu

ta dan kama mata. Tana gama wanke

kwanukan

ta kwashesu tayi kicin din don ta ajiye ko

wanne

a maxauninsa, Aliyu ta gani tsaye yana hada

coffee, ta juya da sauri xata bar wajen taji

yace

"one more step, yhu are in trouble."

mutuwar

tsaye tayi a wajen xuciyarta na dukan uku-

uku,

yau ta shiga uka dukanta xai yi tasani " ya

karaso inda take ya xagayo ya tsaya

gabanta

yana mata wani irin kallon, tuni kwalla ya

taru a

idonta, yyi murmushin mugunta yace

"yaushe

kuka fara samun liver a gidan nan daga ke

har

uwarki," amsar ki kadae xata ceceki yau a

nan,

idan ba hka ba wllh tllh sae na fasa kanki a

nan

wajen, save my tym ki bani amsata, am ol

ears.

Ya fadi da tsawa " kuka ta fara yi tace "ni

dae

don Allah don annabi kayi hkuri ka....."

muryar

Abba suka ji yana cewa "wat's goin on in

there?"

ya fadi da xolaya, Aliyun ya kirkiro

murmushi ya

fara kame-kame, No Abba.. Kawae taimaka

mata

nke ne... Sae kuma ya karbi kwanukan dake

hannunta ya fara kkrin ajiye su inda suke,

Abba

yace "uhum ok yyi kyau hkn, idan ka gama

kaxo

ka sameni, we hve an issue 2 discuss"

Aliyun

yace "yes sir" batare da ya kallesa ba sannan

abba ya bar wajen, da gudu intisaar ta juya

ta

bar wajen bayan Abba yyi gaba, wae

juyawar da

xai yi sai ganin wajen yyi wayam ba kowa,

ya

cije lebe cike da takaici sannan ya ajiye

kwanukan hannunsa ya juya ya bar kicin

din

yana tunanin irin abinda xae mata idan ya

kamata. Bayan kwana biyu komai ya dawo

nml a

gidan, da momy ta dauki xafi sosae amma

abba

na xuwa ya bata hkuri sae ta ajiye fushin da

tayi

da tace masa komai ae ya wuce, ya ji ddin

hkn

sosae don idan ba wannan karan ba ma bai

taba

ganin bacin ranta ba kuma ya gano ita ke

da

gskya bayan yyi bincike sosae a kan lamarin,

su

hajiya kuwa ya je yyi masu kashedi mai

girma

akan su fita harkar matarshi, idan xaman

gidan

da suka je sukayi na kusan wata hudu bai

ishesu

ba to xasu koma ne, hkn yasa suka kame

kansu

don sun san shi sarai. Ranar laraba inna ta

dawo

gidan da mota shake da kaya, har gida aka

kawota aka ajiye, su intisaar da xainab suka

dinga shigowa da kaya kowa na murnar

dawowan ta, ita kuwa baki har kunne ta

dinga

fadin irin yanda aka dinga karramata a

gidan

bikin don inna akwae son girma, bakin

kofarta su

hajiya suka tsaya sukayi mata sannu da

xuwa

sama-sama suka yi gaba. Ta ja dogon tsaki

tace

"munafukan bnxa kawae da alamar ma

basu yi

farin ciki da dawowa na ba." intisaar dake

ta

faman bubbude kayan da suka shishshigo

da

bata tanka wa inna ba. Momy ma taxo tayi

mata

sannu daxu suka danyi hira sannan ta

wuce,

falon ya rage daga ita sae jikokinta tana ta

faman kullawa kowa tsarabarsa a leda.

Intisaar

ta kai nasu gida, hka ma xainab da kursum.

Fadila ta shigo gaida inna, inna ta saka

sallati

tana kallon fadilar tace "hatsarin mota kika

yi

fadila?" ta tambaya ganin yanda bakin fadila

ya

kumbura da fuskarta, xainab dake cikin

bedroom

tana gyara ma inna daki, ta toshe bakinta

ganin

dariya na neman subce mata. Fadila ta

harari

innar tace "hatsarin jirgi nayi ba ta mota

ba." ta

juya ta fice fuuuu. Inna ta kwashe da dariya

tana

cewa "ikon Allah," xainab na gamawa ta fito

tana

dariya tace "inna ki min alkawari idan na

gya

maki maganar nan xaki barshi a cikin ki"

inna

tace "hva Abu, sae kace wata yarinya sae

naje

ina cewa ga abinda xainab tace min."

xainab tace

"yauwa inna." nan xainab ta xauna ta

xayyane

wa inna abinda ya faru kwana hudu da

suka

wuce a gidan." bata kai karshe ba inna ta

mike

tana cewa " kut! Ae yau sae sun gya min ko

pampopin gidan nan na ubansu ne, sae sun

gya

min me xainabu ta tsare masu a gidan nan"

xainab ta mike a rude tana cewa "nashiga

uku

inna don Allah ki rufamin asiri abba yace kar

wanda ya gya maki, ballani xai yi wllh" shi

bukar

din yace kar a gya min? to xai dawo ya

sameni

shima," inna ta fadi a fusace ta fice daga

palon."

da gudu xainab tayi sashinsu ta shige

bathroom

ba tare da ta bari hajiya ta ganta ba jikinta

na

bari. Inna ta karaso tsakar gidan cikin daga

murya tane cewa "ina munafukan gidan...

To don

ubanku ku fito ku gya min ko ubanku ne ya

dasa

ma da'na famfofi a gidan, ku fito ku gya min

ko

nairan ku nawa ne a ciki na biya ku. Sbda

me

xaku sa min 'ya a gaba a cikin gidan nan,

uban

me ta tsare maku? Ku fito ku gya min me

xainabu ta tsare maku nace matsiyata "

cikin

daga murya inna ke ta xuba masu rashin

mutumci.

Momy ta dube intisaar fuskarta daure tace

"don ubanki sai da kika je kka gyawa inna

wannan mgnar bayan abinda....." intisaar ta

xaro

ido a tsorace tace "wllh momy ban gya ma

inna

komai ba, tana bani tsarabar mu ae ban

sake

komawa ba ma." abin ya daure wa momy

kai, to

waye ya gya ma inna wannan mgnar? Hajiya

kuwa kasa xaune tayi sae kaiwa take tana

komowa a palonta, ynxu xainabu sae da

taje ta

gya ma tsohuwar nan wannan mgnar. Hka

ma

umma dake ta lekar innar ta taga da 'ya

yanta,

tsinuwa kam sun sha shi ba adadi . Ganin

inna

taki barin tsakar gidan ne tana ta masifa

yasa

momy ta fito ta dinga bata hkuri ta koma

sashinta, amma kememe inna taki ta dinga

xunduma masu ashar tana cewa ae yau sai

tasa

sun bar gidan nan, momy tayi sumsum ta

koma

sashinta ganin ba sauraranta inna xatayi ba.

Tun

a kofar gida haisam da Aliyu suka dinga jin

muryar inna kmr speaker, Aliyu ya tabe baki

ya

koma mota ya ciro apple dinsa da ya manta

a

ciki, haisam kadae ya karaso gate din ya

shiga

gidan ransa a bace, wannan wani irin

masifa ce

hka, kullum sae anji hayaniya a gidansu sae

kace

makaranta, yana shiga gidan ya ga irin

rashin

mutuncin da inna ke xubawa a gidan ya

juya ya

bar gidan kawai. Dariya Aliyu yyi ganin

yanda

Haisam ya fito daga gidan, ko kallonsa

Haisam

bai yi ba ya shige motarsa yyi gaba. Aliyu ya

shiga gidan ya dauki farar kujerar roba ya

xauna

gefen wani flower yana ta kallon inna yana

cin

apple dinsa with much interest. Tana ta

masifa

har da kukanta, "wllh kwado xan sa wa

duka

famfofn gidan, duk shegen da xae yi amfni

da

ruwa yaje waje ," tana kai wa nan ta fice

daga

gidan tana gunjin kuka. Dariya Aliyu ya

dinga yi

har da buga kafa, hajiya ta fito jin muryar

dan

nata, ta rike haba tana cewa "ka ga makirci

ko

Ali, ynxu bayan duk abinda Alhaji yace sae

da

wannan tsinanniyar matar ta gya wa

wannan

mayyar tsohuwar ko?" shi dai bai ce komai

ba

yana ta cin tufarsa. Umma ta fito ita ma tana

cewa " wannan anyi makirar mace....."

shigowar

inna ce ta sa su yin tsit. Kananan

kwadunaye

inna ta shigo da har guda biyar, su ka bita

da

kallon mamaki. " idan akwae shegen da ya

isa ya

matso kusa da famfofin da na ya gani." hka

inna

ta dinga dasa wa famfofin kwado tana mita,

sashinsu intisaar da nata kadae ne bata je

ba,

Aliyu binta yke tayi da kallo har ta gama, ta

dawo tsakar gidan ta dauki kujera ta xauna

tana

girgixa kafa. Sumsum su hajiya da umma

suka

shige gida, Aliyu ya mike yyi hanyar kicin sae

gashi ya fito da tabarya, yyi hanyar daya

daga

cikin taps din, bugu uku yyi ma kwadon ya

balle,

inna ta taso da gudu tana cewa xan ci

ubanka

wllh idan ka sake shiga gonata Aliyu....

Tsawa ya

daka mata yana cewa "to me kke nufi hajiya,

baxan wanke hannuna ba kuma ko meye?"

yyi

tsaki ya bude tap din yana wanke

hannayensa,

ranar dae hka Aliyu ya maida inna

mahaukaciya a

tsakar gidan, tana yi, yana ta kyalkyale

dariya,

hkn yasa ta dinga rusa kuka wae bukar take

jira

a tsakar gidan. Abba yyi jigum yana

sauraran

maganganun uwartasa da bae da ma'ana

kuma

bai da tushe, ya jira har ta kai aya sannan ya

mike yana kallonta rai bace "to wae baaba

meye

na tada maganar da ya wuce kwana da

kwanaki,

meyasa kike yin hka ne fisabilillahi, ynxu ca

akayi

maki xainab din bata hkura bne ko kuma su

hajiya basu amsa lafin nasu bne?" inna ta

marairaice fuska tace "to ni ina nasani, ca

nke ae

maganar tana nan ne har ynxu," Abba yyi

tsaki

yace "wannan wani irin abu ne don Allah,

ko ma

bai wuce ba ina ruwanki cikin maganar,

tsakanina

ne da iyalina," inna dae sae wuri-wuri take

da ido,

su hajiya kmr su yi shewa don murna, ya

dube

gaba daya 'ya yan nasa dake falon fuskarsa

a

tamke yace "cikin ku waye ya gya ma baaba

wannan maganar? Kuma duk wanda yyi

min krya

sae na yi mugun saba masa wllh" yasan

momy

baxata taba gyawa inna wannan mgnr ba

duk da

su hajiya sun ce masa ita ta gya wa innar

amma

bai tanka masu ba, don yasan wacece ita.

nan

xainab ta dinga cunkulin inna alamar ta rufa

mata asiri jikinta na bari, hankadata inna

tayi

tana cewa "ke don ubanki ki rabu dani sae

shisshigeni kike yi sae kace yarinya," xainab

saura kadan ta saki fitsari don ca take inna

tona

mata asiri xatayi. Aliyu ya daka ma

kanninnasa

tsawa yana cewa "ba magana ake maku ba

wawaye kawai," inna ta kalle Aliyun kmr me

naxari, can sai tace "to ni Aliyu ne ya gya

min

wannan mgnar ba kowa ba." Aliyu ya firfito

da

ido yace "ni inna," ta galla masa harara tace

"munafuki kawai, shine ya gya min bukar,

ko

karya nayi mka?" Abba ya juya yana kallon

Aliyun

ransa ya dada baci, Aliyu xai yi magana abba

ya

daka masa tsawa yana cewa "karya knan

tayi

mka," inna tace "Atoh dae, ina xaune yaxo

ya

sameni ya gya min, intisaar ae tana wajen

lkcin,

ko krya nayi intisaar?" ta tambaya tana

kallon

intisaar din.


Intisaar tayi narai-narai da ido cikin

karkarwar murya tace "don Allah don

annabi inna

ki rufa min asiri ni wllh ina gidanmu lkcn, bn

san

kun yi ba" inna tace "au hka ne kuma, daga

ni

sae shi a palon lkcn." haisam ya kalli Aliyun

da

ya ma kasa cewa komae sae kada wa da

idonsa

yyi yana kallon innar ko kifta ido baya yi, sae

dariya ta subce masa, abba ya juya yana

kallonsa a fusace, ya mike yyi saurin barin

palon

yana yar dariya, shi dae yasan inna sharri

tayi

ma Aliyu don Aliyu bai da surutu kawae dae

yasan ramuwar irin abinda Aliyu ke yi mata

a

gidan tayi ne. Ranar kuka ne kawae Aliyu

bai yi

ba, don wanki babban bargo Abba yyi masa

"tashi ka bni waje karka sa na watsa mka

mari,

abinda yaci ace kanninka ne sukayi sai

gashi wae

kai da knka kayi" Abba ya fadi cikin bacin rai

bayan yyi fadan har ya gaji, Aliyu ya mike

kmr

xaki ya fice fuu daga palon, inna ta rakasa

da

cewa "munafuki kawae." hajiya ta mike a

fusace

ita ma ta fice daga palon, sae bayan ya fita

su

kursum suka fashe da dariyar da suke

hadiyewa

tun tuni, inna ma ta taya su dn ta rama

iskancin

da ya dinga mta a tsakar gida jiya, har

xainab

sae da tayi dariyar, intisar kadae ce bata yi

ta ba

ta hade rai. Intisar na tsakar gda tana taya

xainb

tsifan kanta aka bude gate din gidan gaba

daya

suka maida hnklinsu wurin gate din su ga

wanda

xae shigo, Aliyu ne da safeenah su ka shigo

gidan, xainab tace "tab, amma wannan

yarinyar

jaka ce mara xuciya, ynxu sae da ta sake

xuwa

gidan....." da sauri intisaar ta katse ta da

cewa

"kinga ni ba ruwana ki bar xancen nan

xainab"

bangaren hajiya suka wuce bayan intisaar

da

xainab sun gaisheta tayi masu bnxa, shi ko

ya

watsa masu harara. Xainab ta fashe da

dariya a

hankali tana cewa "ina ma Allah ya kawo

inna

nan mu ci dariya wllh," intisaar tace "ki dae

ci

dariya amma bnda ni" xainab tayi dariya

tace

"shegiya matsoraciya, dubi fa kayan da tasa

yau

har gwanda na ranan nan," intisaar ta mike

tace

"kinga idan baki son tsifan nan ne na wuce

don ni

bbu ruwana wllh karki ki jaxa min" xainab

ta

fixgota tana dariya tace "to yi hkuri nayi

shiru xo

ki karasa min." suna wajen har bayan kusan

awa

biyu sannan suka fito, hajiya sae wangale

baki

take yi tana cewa "Allah yyi maki albarka

safeenah, mun gode sosai, ki gaishe min da

hajiya kice sae naxo, umma ma tafito tana

cewa

"Allah dae ya nuna mana wannan abun

arxikin"

leda kato su hajiya da umma suka cika mata

da

tsaraba khadija na rike da ledan kmr xata

shige

jikinsafeenar dake ta murmushi tana gdya,

hajiya ta hade rai ganin xainab da intisaar

tace

"don ubanki kin xo kin gaida antynki ko sae

na

taka ki a nan," ta galla wa intisaar harara

tace

"tashi ki ba mutane waje munafuka kawae."

da

sauri intisaar ta mike ta bar wajen tayi

sashinsu,

safeena tana yatsine fuska tace "wae hajiya

wacece wannan yarinyar?" hajiya ta tabe

baki

tace "agolar gidan ce" safeenah tace

"tabdijam"

umma tace to ya muka iya. Aliyu ya fito da

makullin mota don maida ta gida xai yi yace

"ta

yi maki wani abu ne dear?" ta tabe baki tace

"muje kawae" har gate hajiya da umma

suka

rakota suna sa mata albarka, hajiya tace "ki

fa

ba wa hajiya sakona," tace "xan bata hajiya"

sannan suka wuce ita da Aliyun. Umma tace

"gskya amintakan ku da hajiya mairo yyi,

tunda

har ta dauki tilon 'yar ta xata ba danki,"

hajiya

tayi murmushi tace "ae ni bbu abinda xance

da

mairo, baki ji yanda naji ba ran da ta kirani

take

gaya min irin rashin mutuncin da tsohuwar

nan

tayi ma safeenah da bama gidan, wllh naji

takaici

sosae" umma tace "to ae laifinsa ne, don me

yasan bama gidan xai daukota ya kawo ta

bayan

yasan yan hassada ne a gidan, idan kin

bibiya

ma xainabu ce ta xuga innar tayi ma

safeenar

hkan." hajiya tace "ae ba takanas ya dauko

ta ya

kawo ta gidan ba, hanya ce ta biyo dasu ta

nan

shine yace bari ta gaida kakarsa, ae tasan

bama

gidan." muryar inna da suka ji tana kwada

wa

fadila kira ne yasa suka yi tsit, kursum tace

"bata nan" inna ta rike haba tace "ohh ni

rahmatu

yarinya ta maida kanta gantalalliya kmr

akuya

anki tsawatar mata, amma ba laifin kowa

bne, na

bukar ne, ae da ya aurar da ita da duk hka

bata

faru ba." tayi gaba tana ta mitocinta. Hajiya

da

umma suka tabe baki, umma tace "randa

wannan

tsohuwar xata mutu ae sae na xuba ruwa a

kasa

nasha," hajiya tace "ae ba ke kadai ba

shafa."

Abba yace "gani inna," bayan yaje kiran da

mahaifiyar tasa ke masa. Dama bukar dubu

ashirin xaka bani nayi ma yaran Nafisa

tsaraba

don gobe xanje gidanta, Abba yace "to inna

bari

haisam yaxo ya ciro maki." tace "yanxu fa

nake

so ni dae wllh, don bn yarda da wannan

wayon

naka ba, sau dayawa hka kke min" Abba ya

jin

jina kai yace "ynxu xai kawo maki baaba."

cike da

jin haushi yyi maganar ko sati uku ba ayi ba

da

ta saida masa fili sannan ya kara mata da

dubu

hamsin amma har tana tambayar wani dubi

ashirin din. Haisam tasa ya kaita sukayi

shoppin

din, ta jida kayan kusan dubu talatin, dole

shi ya

cika sannan ya maido ta gida. Washegari ta

samu Abba wae ya samo wanda xai kaita,

haisam baya nan, don hka dole yasa a kira

masa

Aliyusukayi

Aliyu na shigo wa palon Abban nasa ya

nemi gu ya xauna ya gaida shi a ladabce

sannan

yace "gani Abba" Abba ya hade rai yace "ka

gaida

inna ne yau?" inna ta tabe baki tace "ae ni

rabon

da Aliyu ya gaida ni tun ran da na ce shi yyi

min

wannan gulman" Aliyu ya xaro ido yace "kai

inna

ki dinga jin tsoron Allah mana" inna tayi

salati

tana kallon dan nata tace "wllh Bukar tun

ranar

Aliyu ko bangarena baya xuwa, ko ya gan ni

sae

ya kauda kai." Abba ya dube Aliyun yace

"gidan

nafisa xaka kai ta anjima," da sauri inna tace

"xuwa karfe sha daya dae" Aliyu ya mike

yana

kallon Abban nasa fuskarsa a tamke yace

"gskya

Abba ina da urgent meetin da xan wuce

ynxu...."

Abba yace "ni kke gayawa hka?" ya kauda

kansa

bai ce komai ba, inna kuwa ta dage da cewa

"wllh shi xai kaini, dolensa sae ya kaini, Allah

kai

xaka kai ni Aliyu" Aliyu ya juya yana mata

wani

irin kallo kmr ya maketa don haushi. "iyye

yaro

bashi da mutumci ba shi da kunya sae kace

ba

jininka ba Bukar, wllh bae yo halinka ba,

Haisam

kadae da xainab suka yo halinka a gidan

nan"

abba yyi murmushin takaici ya kalli Aliyun

yace

"je ka kawai." Aliyu yyi maxa yace "ohk naji

xan

kai ki ki shirya" inna tace "kaci sa'a wllh"

fice wa

yyi ba tare da ya bari sun hada ido da

abbansa

ba. Tare da intisaar da xainab inna xata,

amma

hajiya na ganin hka sae ta tura xainab gidan

wata kawarta wae ta karbo mata sako, duk

don

kar ta bi innar, don tasa xainab ko ta hanata

xuwa ba ji xata yi ba shi yasa ta bullo da

hkn.

Intisaar bata san Aliyu xai kai su ba da

baxata

fara bin inna ba, wae sae da suka fito

tukunna

inna ta fara kwada wa Aliyu kira a tsakar

gidan

wae ya fito sun shirya. Intisaar ta dafe kirji

tace

inna shi xai kai mu dama, nayi xaton adai-

dai ta

sahu xamu hau ae, inna harareta tace "ka ji

shirme, gidan dan nawa da motoci xan hau

motar

haya, inna ta sake kwada wa Aliyu kira sae

gashi

ya fito fuskarsa daure yana sanye da polo

fari da

baki, da 3quatre fari kal, shi dae kam yana

san

3quatre, intisaar ta fadi a xuciyarta, inna ta

xabga salati tana tafe hannu tace "uban wa

xaka

bi a hka yaron nan?" Aliyu ya hade rai yace

"kmr

ya wa xan bi a hka?" tace "nashiga uku ni

Rahmatu nace uban wa xaka bi da wannan

dangalallen wandon?" yyi tsaki ya ce "idan

xaki ki

wuce na kai ki, don ina da gurin xuwa

hajiya,

meye ruwanki da abinda nasa" inna ta

girgixa kai

kmr xatayi kuka tana cewa "la! Wlh baxan je

da

kai a hka ba kaji min gantalallen yaro." Aliyu

ya

tabe baki yace "to Allah ya raka taki gona,

dama

ni bnyi niyar kai ki ba ae," sae ma a lkcn ya

kula

da intisaar da ta labe a gefen innar, duk

wannan

abinda akeyi su hajiya na labe a taga suna

lekowa, hajiya taji ddin yanda dan nata yyi,

inna

ta lalubo waya tana kallon intisaar tace "kira

min

bukar" da sauri intisaar tace "bn iya ba ni

xainab

ce ta iya."a fusace inna tace "amma kin ji

haushi

kuwa" nan ta dinga kwadawa fadila kira

taki

fitowa, sae tayi waje don neman wanda xae

ciro

mata nmbr dan nata, a dai-dai lkcn Abba ya

kirata, ta dauka da sauri tana cewa "Bukar

ne?"

Abba yace "nine baaba kun tafi ne" tace "ina

fa,

wandon shaidanu yasa wae xae bini dashi,

irin

wandon nan dae da ya saba sa wa a gida"

Abba

ya kashe wayan ya kira a Aliyun, kasa daga

wayan yyi ji yake kmr ya makure inna don

takaici, can dae ya daga bai ce komai ba har

Abba ya gama sannan Abban ya kashe

wayan,

idonsa yyi jajur, ya juya fuu ya shige ciki,

inna

tace "Atoh dae." bai jima ba ya fito da

dogon

wando yyi hanyar motarsa inna ta ja

intisaar

suka bishi, tana cewa "hka kawae ya janyo

mana

kallo a gari, yaro sae kace kafiri." shi dae bai

tanka mata ba har ta ja intisaar suka shige

motar, intisaar dae jikinta bari yake, don

bata

bari sun hada ido dashi ba, "to uban wa

kuka

cewa da wannan yarinyar xan kai ku?" ya

tambayi innar fuskarsa a murtuke, inna tace

"ubanka muka cewa" to bata isa ta xauna

baya

ba na ja ta don bata kae wannan matsayin

ba

tun wuri ta dawo gun da ya dace ta xauna,

gaban intisaar ya fadi ta kalli inna, to ina

xata

xauna, ita fa wannan tafiyar ba dole sae ta

koma

gida, dama don taga tare da inna ne kuma

baxai

iya yi mata komai ba don inna baxata bari

ba

shiyasa ma bata ce ta fasa ba, amma da ace

da

su xainab ne to fasawa xatayi, inna tace "to

bbu

gun da xata xauna da ya wuce nan, bai sake

cewa komai ba don baya son magana, ya ja

motar suka wuce. A hanya hka inna ta dinga

magana a hnkli a kunnen intisaar, intisaar

dae

hadiye dariyarta kawae take don bata ma

san me

inna ke cewa ba ta dage sae mutsu-mutsu

take

mata a kunne, ita a dole xata ba Aliyu

haushi,

kallonsu kawae yake ta madubi, intisaar ta

lura

da hkn sae ta shiga taitayinta, yyi tsaki

kawae ya

kara volume din wakar dake tashi a motar, a

hankli intisar ta matso kusa da inna take

nuna

mata hanyar gidansu faruuq cikin murya

kasa

kasa take magana, inna ta bude murya tana

cewa

"Allah sarki yaron Arxiki" brake Aliyu ya taka

da

karfi, inna ta saka salati a rude tana cewa

"lfya?"

ya fito da sauri ya bude bayan motar, da

gudu

inna ta fito tana cewa "fito intisaar yau mun

shiga uku me ya faru?.

A rude inna ta dinga tambayrsa me ya

sami motar bayan intisaar ta fito, bai ko

kalleta

ba ya shiga kwaso masu ledojin tsarabarsu

da

saurinsa, inna ta dada rudewa tana cewa

"purse

dita na ciki akwae kudade da yawa fito min

dashi

da sauri wllh har da daham dina a ciki, ya

ciro

purse din ya ajiye kan ledojin da yake ta dire

su a

gefen titi, inna ta kin ki me abinta da sauri

tana

lekar motar a tsorace, "to wae me ya samu

motar?" inna ta tambaya tana jan intisaar su

matsa daga kusa da motar, bai ko kalleta ba

har

sae da ya tabbatar ko tsinkesu bai bari a

cikin

motarsa ba sannan ya rufe motar, ya juyo

yana

kallonsu fuska daure yace "ku nemi motar

haya

da xae kai ku inda xaku, don baxan bata lkci

na

na bar abinda ke gabana na dauko ku a

mota ku

dinga min iskanci a cikin motar tawa ba."

Yana

kai wa nan ya shige motarsa ya ja ta ya bar

su

tsaye a wajen, inna ta xabga salata tana

girgixa

kai tace "amma wannan yaro na Bukar anyi

tantirin dan iska, ynxu xubar damu yyi a

dajin

Allahn nan ya wuce?" sae kuma ta fashe da

kuka

tana cewa "wannan masifa da me yyi kama

ni

Rahmatu" intisaar ta dinga tuntsire dariya

tana

karewa inda ya ajiyesu kallo ita dae bata ga

alamar daji ba a wajen amma inna tace daji

ne,

sannan ga motoci na ta wuce wa abinsu,

har da

mutane ma nata harkokin gabansu a wajen.

kukan da inna ta dinga rusawa ne ya fara

jawo

hanklin jama'ah wajen, intisaar tace "kai

inna don

Allah kixo muje mu hau mota mu wuce,

dube

yanda kika janyo ana ta kallonmu," cikin

kuka

wiwi inna tace "wllh baxan hau motar haya

ba

don ubanki, hka kawae dan nawa na da

motoci

sae na buge da hawa ta haya" intisaar ta

kulu

matuka ita kam da ta sani bata bi inna ba,

wannan disgrace din har ina? Taruwa

mutane

suka fara yi a kansu ana tambaya lfya? Nan

inna

ta dinga surutu ratata akan abinda jikanta

yyi

mata, intisaar ji tayi kmr ta nutse a wajen

don

kunya, da sauri tayi gaba ta barta a wajen

cike

da takaici, ita ba kudi ta fito da ba bare ta

hau

mota ta koma gida, ta juya daga nesa tana

kallon inna da mutane suka gama

kewayewa, ko

me take gya masu oho. Da kyar mutane

suka

lallaba inna ta hau adai-daita sahu, tana

gunjin

kuka ta shiga tana cewa "Allah dae ya isa

tsakanina dashi," sae kuma ta fara

kwadawa

intisaar kira tashigo su wuce, kasa xuwa

wajen

intisaar tayi sbda mutanan da suka taru a

gun,

har kusa da ita tricycle din ya tsaya sannan

inna

tace "maxa shigo intisaar, Allah xai saka

mana,"

fuskarta daure tashiga, mutanen wajen

suka bisu

dacewa " Allah ya saukeku lfya Hajiya, Allah

ya

kiyaye, ya ja da ranki" inna ta ding a

washale

baki tana gdya tare da daga masu hannu,

shi

kanshi mai tukin dariya yake yi. Sae da suka

yi

nisa sannan inna ta dube intisaar tace

"kinga

mutanen arxiki koh, har biya mana sukayi,

Allah

yyi masu albarka dae" intisaar bata ko

kalleta ba

bare ta tanka mata. Har bakin gate Napep

din ya

ajiyesu, inna ta dinga gdya ya fiffito masu

da

kayansu, intisaar ta dauki wanda xata iya ta

shiga cikin gidan inna na biye da ita a baya

tana

cewa "to ynxu bayan duk wlkcn da yyi mana

ba

gamu a gidan ba. Nafisa tayi murna da

xuwan

mhaifiyar ta ta sosai,'ya yanta duk suka xo

gaida

kakar tasu dayake ranar asabar ce suna

gida,

sae da inna taci ta sha sannan ta soma

xayyano

wa Nafisa irin abinda Aliyu yyi masu a kan

titi,

Nafisa tace "amma wllh Aliyu bai da

mutumci ko

kadan inna, kinsan kuwa tunda na dawo ko

sau

daya bai taba xuwa gaida ni ba ko yi min

sannu

daxuwa, amma haisam xuwansa biyu

knan," inna

tace "ranar da ya kawosu xainab bai shigo

ba?"

Nafisa tace "xan masa karya ne inna?" nan

inna

ta kwadawa intisaar dake dakinsu maryam

kira,

dayake maryam din sa'arsu ce da xainab,

suka

shigo tare da maryam din, inna tace "ranar

da

Aliyu ya kawoku gidan nan dama bai shigo

ba?"

intisaar tayi jim don dae ba Aliyu bane ya

kawosu

motar haya suka shiga amma da suka koma

gida

basu ce kin kai su yyi ba, da sauri tace "eh

bai

shigo ba" inna ta galla mata harara tace

"munafukan bnxa kawae amma ca kuka yi

min ya

shigo da na tambayeku," intisaar tace "uhm

ae

xainab ce bni bace" nafisa tace jeki kawae

abinki,

kika san ko yy masu gargadi akan kar su ce

bai

shigo ba, bala'i inna ta dinga yi tana cewa

"wllh

yaron nan mugun shaidani ne, amma xai ci

ubansa bari na koma gida dae" intisaar ta

fice.

The end of book one.





No comments