Inteesar Book 3 Complete
INTEESAR BOOK 3
Aliyu bae sake ce mata komai ba sae gudun
bala'in da ya dinga yi kmr xae tashi sama,
hankalinta yyi mugun tashi ta ma rasa mae
xata ce masa don tsoro, ta dake daga
karshe da kyar Muryarta na rawa tace "wae
ni ya Aliyu ina xa ka kai ni ne don Allah," ya
taka brake yyi arkin da sauri yana kallonta
cikin tsawa yace "kika ce me?" ta tsorata
ssae ta sunkuyar da kanta bata ce komai ba,
yyi mata wani mugun kallo yace "sayar da
ke xanje nayi," bata dago kai ba bare tace
masa komai yyi kwafa ya ja motar suka bar
wajen, lkci daya hankalinta ya kwanta
ganinsu da tayi anguwansu, yana gama
parkin kuwa ta bude kofa xata fita da sauri
yyi hanxarin fixgota yana hararta yace "kin
dae ji me na ce maki, kuma wnn hawayen
bana son ganinsa a fuskarki" ta fixge
hannunta ta fice da sauri daga motar snn ta
watsa masa harara hade da jan tsaki tace
"ban ji ba," tana fadin hka tayi cikin gidan
da gudu ya bita da sauri, tana isa gate cikin
rashin sa'a tayi tuntube tayi gaba xata fadi
yyi saurin rikota ta fado kansa, ta marairaice
fuska a tsorace tace "don Allah kayi hkuri ba
da kai nake ba," bae ce mata komai ba ya
shiga janta kmr wata dabba tana biye da shi
a baya har suka iso falon Abba, sae a snn ya
juya yana kallonta fuskarsaa murtuke yace
"Allah ya baki sa'a ki ki yin abinda nace
maki, wllh sae na kusan sumar dake a gida
yau," bata ce komai ba ya ja ta suka shiga
cikin falon, Abba na xaune remote a
hannunsa yana canxa tasha, Aliyu kadae ne
yyi karfin halin yin sallama ita kam inteesar
kasa wa tayi ji tayi hka kawae gabanta na
faduwa, ta xauna Aliyu ya xauna gefenta
snn ya gaida Abban nasa ba tare da ya
kallesa ba, Abba ya amsa bbu yabo bbu
fallasa snn ya kalli Inteesar da ta kirkiro
murmushi tana gaishesa ya amsa da
fara'arsa yana tambayarta ya gidan, ta
sunkuyar da kai tace lfya lau Abba, murya
can kasa Aliyu yace "ga ta nn Abba na kawo
ta," ko kallonsa Abba bae yi ba ya fara
magana kmr hka "tambayace kawae xan
maki Fateemah, amma gskya kawae nake
son ki gaya min kar kiyi min karya ban san
ki dakarya ba," tayi shiru gabanta na
faduwa tana kalln Abban, ya dan dau lkci
snn yace "wae da amincewarki Aliyu xae
kara aure?" ji tayi komai nata ya tsaya ta
kasa dago kai bare ayi expectn amsa daga
gare ta, nn da nn taji hawaye na neman cika
mata ido, Aliyu ya kamo hannunta ya hade
da nasa a boye, ta gane abinda yake nufi,
suka ji muryan Abba na cewa "magana nake
fateema kin yi shiru, sharri yyi maki ko?" da
ganin Abba kasan ransa a bace yake, da
kyar ta iya bude baki ba tare da ta kalli
Abban ba tace "eh hka ne Abba da sanina,"
Abba ya girgixa kai yace "karya kike," tayi
kkrin boye hawayenta tace "da gske Abba
na sani ni ce nace yyi," Abba yyi shiru yana
kallonsu gaba daya daga bisanni yace "to yyi
yau, baxan hanaka kara aure ba Aliyu kuma
ni kam bbu abinda xan ce maka da ya wuce
Allah ya taimaka, snn abu na karshe da nake
son na gaya maka shine ka tabbatar kafin
kayi auren naka 'ya ta ta fara karatu tayi
settle dwn idan ba hka ba wllh sae na
wargaxa komai, ka tashi ka ban wuri" bbu
ko dar bare damuwa Aliyu ya mike yace
"ngd Abba," ya sace kallonta, ita ma kallonsa
take hawaye cike idonta da ganinta ta shiga
wani yanayi da baxa a iya fassarawa ba ya
galla mata harara snn ya fice, Abba yyi
shiruyana kallonta snn a hankali ya fara
magana"kiyi Hkuri fateema, nayi dana sanin
hadaki daAliyu da nayi, kuma ni ban isa
hana shi kara aure ba, snn baxan ce kar ki
bi mijinki ba amma idan har kin ga baxa ki
iya xama gidan ba bayan auren nasa ni nn
nace ki tattaro ki dawo gida," kai kawae
take gyada ma Abba tana hawaye yyi mata
nasiha ssae yana kwantar mata da hankali
daga karshe yace ta tashi tashiga cikin gida
amma kar ta ce da inna komai tukun, ta
mike jikinta a mace tayi masa gdya snn ta
fita falon tayi bangaren inna tana kuka ssae,
tsaye ta gansa alamar ita yake jira, yana
ganin tayi bangaren inna ya daka mata
tsawayace "c'mon gida xa mu wuce ina kike
tunanin xa ki," ko kallonsa bata yi ba ta saka
gudu tayi sashin inna ya bi ta shima da
sauri, Kursum da ta fito daga gun inna knn
ta bi su da kallo baki bude, saura kiris ya
kamata ta afka falon inna tana mayar da
numfashi ta fasa ihu tare da xubewa
tsakiyar falon, inna dake daki ta fito da
gudu tana salati tace "me ya faru?? Daga ina
hka?" shi ko ya fixgota a fusace ya shake ta
hade da hada ta da bango yana huci yace
"don ubanki ina wasa da ke ne?" inna tayo
waje da ido snn tayi waje da gudu ta saki
kuka cikin daga murya tace "jama'a yau
naga ikon Allah xae kasheta gabana, Bukar
Bukar ka taho kaga abinda dan ka ke shirin
yi da daddaren nn"
.
Haisam ya karaso da sauri yana kallon inna
yace "me ya faru inna," tana kuka wiwi tace
"wllh Haisam ina daki na je ajiye kayan da
kursum ta gama goge min naji ihu kmr xa a
xaga falona, fitowar da xanyi wae sae ganin
Aliyu nayi shake da Inteesar yana duka yana
buga ta da bango, duk yyi mata kaca kaca
ko motsin kirki wllh bata yi yanxu ban san
ya ake ciki ba ka taimaka ka kira mun Bukar
don Allah," tana kai wa nn ta fashe da wani
kukan har da durkushewa kasa, Haisam ya
girgixa kai ya shiga falon innar da sauri dai
dai bakin kofa ya hadu da Aliyun rike da
hannun inteesar yana janta tana kuka tana
cewa "wllh ka kyaleni bbu inda xa ni," ya
buge mata baki Haisam yace "wae kai wani
irin mutum ne Aliyu 4 heaven sake" Aliyu ya
watsa masa wani mugun kallo yace "da'alla
can get out malam kar na buge ka," inna
tayi cikin gida da gudu tana rusa kuka lkci
daya tana kwala ma Abba kira, da sauri Aliyu
ya ja inteesar suka fice daga gidan tana
nonnokewa ya bude mota ya jefata ciki snn
ya shige motar ya tada ta, dae dae nn inna
ta fito kofar gidan Abba na biye da ita a
baya tace "maxa bi shi Bukar ya tada
motar," Abba ya girgixa kai cike da takaici
yace "kina ma Allah da annabi ki daina daga
min hankali a gidan nn baaba wnn wani irin
bala'i ne," bae jira mai xata ce ba ya koma
cikin gidan ransa a bace. Suna isa gida Aliyu
yyi parkin ya bude motar ya fito yana kallnta
har lkcin bata daina kuka da take ba ta hade
kai da gwiwa, cikin tsawa yace "ko sae na
jefar dake waje," taki dago kai bare ta tanka
masa, ya fixgota ta fasa masa ihu tana cewa
"wllh baxan shiga gidan nn ba ka mayar
dani gida," cak ya dauketa ya rufe motarsa
tana dukansa bae damu da hkn ba ya shiga
gida da ita ya haura sama ya bude dakinsa,
nn da nn ta saita kanta cikin muryar kuka
tace "ni ka ajiye ni," bae kulata ba ya isa kan
gado ya kwantar da ita ta mike da sauri ya
turata da karfi ta fada kan gadon snn ya
fada kanta, nn da nn ta hadiye kukan da
take xuciyarta na bugawa a hankali tace
"kayi hkuri ya Aliyu na daina kukan" ya dago
yana kallonta da ganinta kasan a tsorace
take, ta fara kkrin sauka daga kan gadon ya
rikota yace "bbu inda xaki yau nn xaki
kwana," kanta ce komai ya kashe wutan
dakin, ta fasa masa ihu ya buge mata baki
da karfi, ba karamin wahala ya bata ba, don
duk sae da ya jagwalgwalata, ganin irin
kukan da take da kuma yanda jikinta ke bari
duk da bae ma kai ga yi mata komai ba yasa
ya kyaleta tare da cewa "ki rufe min baki kar
na baki mamaki," ba shiri ta hadiye kukan
jikinta na rawa don duk ya tsorata ta, ya
rungumota ssae, snn ya dauki wayarsa yyi
dialin nmbr safeenah, kmr jira take yana
ringin kuwa ta daga, murya can kasa yace
"bbyna," ita ma a marairaicen tace "mijina,"
ya sauke ajiyar xuciya ya daura bakinsa kan
gashin inteesar da ta rumtse ido xuciyarta
na bugawa, yace "nayi missn naki ssae fa
bby, i need yhu safeena," ta danyi dariya
tace "matarka fa? Kaje ka sauke need din a
kanta mana," ya yamutse fuska yace "me
wnn take da shi da xata bani da ya wuce
wahala, naki nake so bbyna," tayi dariya
ssae snn tace "ka kusa samu dear na, ina
amaryartaka," yace "ga ki nn bbynah," nn
suka dinga xancen yanda 1st nyt dinsu xae
kasance bbu kunya bare tsoran Allah, a
hankali Inteesar ta shiga xamewa daga
rungumar da yyi mata, ya matseta da karfi
ta shiga kokuwa da shi, ya ki sakinta, ya
kunna wutan dakin yana kallonta, hawaye
ne kwance fuskarta, ta boye fuskar da sauri,
bbu yabo bbu fallasa yace "nayi maki wani
abu ne kike min kuka don munafurci?" tayi
shiru bata ce komai ba har lkcn hawayen da
take yaki tsayawa, ya dada rungumeta ya
kashe wutan ya ci gaba da wayarsa, suna
nn a hka yana ta hirarsa da safeenah har
bacci ya dauke Inteesar
.
Karfe sha biyu da rabi ya kwantar da ita a
hankali, snn ya shiga bathroom yyi wanka
ya koma wani dakin yyi kwanciyarsa. Da
safe taji an watsa mata ruwan sanyi ta farka
a tsorace tana kallonsa da mamaki, ya galla
mata harara yace "ke kafura ce ina ga ko,"
bata ce masa komai ba ta sauka daga kan
gadon fuskarta a daure tayi hanyar fita
daga dakin ya fixgota yace "ina magana
xaki fita don baki da kunya," ta hararesa
tace "to ca nayi maka banyi sallah bane" ya
wara ido ya shaketa yace "ni kike kallo hka,
wae me sa kika raina ni hka ne yarinyar
nn?" ta girgixa masa kai kmr xata yi kuka
tace "kayi hkuri baxan sake ba," yyi kwafa
ya saketa yana kallonta tayi hanyar fita da
sauri ya daka mata tsawa "ke! Uban wa xae
gyara maki dakin?" ta juya tana kallon dakin
snn ta dan yi tsaki ta dawo ta fara gyara
gadon, ya bude Bathroom ya shiga wanka,
tana gama gyara dakin ta fice da sauri tayi
hanyar dakinta. Inteesar na jin muryarsa a
kasa ta mike da sauri ta isa jikin window
tana kallonsa yana tsaye jikin motarsa yana
magana da masu gadi, ta juya da sauri
hawaye ya cika idonta, jin ya tada motar ne
yasa ta juya tana kallonsa har ya bar gidan
snn ta dawo gefen gado ta xauna a
sanyaye, tana nn a hka bayan fitarsa da kmr
minti goma Zainab ta shigo gidan, Zainab ta
ajiye mayafinta tana kallon Inteesar da ta
kirkiro murmushi tace "lah daga ina kike da
safen nn," Zainab tace "wae jiya da kuka xo
gida da daddare da ya Aliyu me ya faru"
Inteesar tayi shiru tana kallon Zainab snn
tace"me aka ce ya faru?", Zainab tace "oho,
Abba yace mu taho gida tare ynxu, ya kira
Aliyu tun jiya ya ki dagawa," Inteesar tace
"to ae baya nn," Zainab ta galla mata harara
tace "to ina ruwana, Abba ca yyi mu taho
gida ynxun nn da ke," Inteesar ta girgixa kai
cikin confusion tace "to ki kira ya Aliyun ki
fara gaya masa," Zainab ta bude baki tana
kallonta tace "iyye sae na kirasa xa mu tafi,"
Inteesar tace "to ae bae sani ba," da mamaki
Zainab tace "Ahh lallai," snn ta juya tace "sae
anjima," Inteesar ta bi ta da sauri tace "ki
tsaya don Allah Zainab," Zainab xa tayi
magana wayar dake gaban madubi na Aliyu
yyi ring, Inteesar ta karasa gaban madubin
tana kallon wayar a tunaninta Safeena ce, ta
daga wayar ta kara a kunne bata ce komai
ba, "kina jina, idan kika kuskura kika fita
gida ba tare da izinina ba xaki sha mamaki,
just dare me, ki ga" yana kai wa nn ya katse
kiran, ta juya tana kallon Zainab ta
marairaice tace "yace kar na fita Zainab," ko
kallonta Zainab bata yi ba tayi hanyar kofa,
Inteesar ta bi ta da kallo har ta fice. Da
yamma tana kwance abun duniya ya isheta
tun tean data sha da safe bata sake cin
komai ba ta rasa me ke damunta, jin an
bude kofar downstairs ya sata mike da
sauri a tunaninta Zainab ce ta kuma
dawowa, ta xauna gefen gado tana jiran
shigowartata, kamshin turarensa da taji
yasa ta gane shi ne, ta koma ta kwanta a
hankali tana kallon kofar dakin, ya tura
kofar dakin ya tsaya daga bakin kofa yana
kallonta, bata ce masa komai ba, ya tabe
baki yace "wa ya shigo gidan nn daxu?" tayi
kmr bata ji sa ba ya daka mata tsawa "ba da
ke nake ba," xata yi magana taji ana kiransa
da darlin, ya juya da sauri yace "srry bby,
magana nake da wnn ballagaxar," Inteesar
tamike tsaye da sauri tana kallon safeenah
da ke lekota, ta karaso bakin kofar tanai ma
safeenah wani irin kallo snn tace
"karuwancin ne har sae kin biyosa gida don
rashin sanin ciwon kai, ke kam kin banu
banxa kawae sha sha sha," bata rufe baki
ba Aliyu ya sauke mata mari ya fixgota ya
jefar kan gado yana huci ya nuna ta da dan
yatsa yace "ki shiga hankalinki wllh, don
kika sake ce mata karuwa sae na illata ki,
dabba kawae" ta sulalo kasa daga kan
gadon ta fashe da kuka ssae tace "Allah ya
isa ban yafe maka ba mugu kawae mara....."
wani wawan marin ya sake kai mata hade
da buge mata baki da karfi yana huci nn da
nn sae ga jini, ta fasa ihu a gigice, safeena
ta dafe kanta tare da sauke ajiyar xuciya
tana yatsine fuska tace "kai bby ban cika
son hayaniya ba wllh, muyi abinda ya kawo
mu na bar nn plss," ya ce "srry bby," snn ya
kamahannunta suka fita daga dakin tana
ma Inteesar wani irin kallo tana murmushi,
kuka Inteesar ta dinga yi kmr ranta xae fita
ta hade kanta da gwiwa, tana nn a hka suka
sake bude kofar dakin suka shigo, taji yace
"nan fa bby?" Safeenah ta dan yatsine fuska
snn tace "yauwa nn yafi dear, nn din nake
so can bae yi min ba,".
Aliyu yyishiru yana kallon safeenah, ta dan
matso kusa da shi ta yi masa fari da ido tace
"mun gama da wnn, kuma ni bna son irin
paint din nn, mu jedear na fara jin yunwa,"
tana fadin hka ta juya xata fita daga dakin
ya riko hannunta a hankali yace "meyasa
baki son wancan dakin bby?" ta yatsine
fuska tana masa wani irin kallo tace "can bai
yi min ba nn nake so," ya juya yana kallon
Inteesar da har lkcn ke kuka a hankali kanta
kife a gwiwanta, ya maida kallonsa ga
safeenah yace "to na bar maki dakina, ni sae
na koma wancan," ta xaro masa ido tace
"No! Ni wnn dakin nake so," yyi shiru yana
kallonta, Inteesar ta mike tsaye ta dauki
Hijab dinta ta sa ta ciro flat shoe dinta shima
ta sa snn tayi hanyar fita, duk suka bi ta da
kallo har ta iso inda suke tsaye tabi ta
gefensa xata fita ya fixgota, "ke? Gidan
ubanwa xaki," ta galla masa harara da
jajayen idonta tace "gidan ubana xani," yace
"ko?" tace "eh," ya aketa ya gyada kai yana
murmushin mugunta yace "to tafi," cikin
kuka tace "ni wllh sae na tafi," ya daka mata
tsawa ya fixgota yana kallonta yace "ae
shine nace ki tafi na gani," ta fashe da kuka
ta xube wajen tana kiran Abbanta, safeenah
ta dafe kanta tare da jan dogon tsaki tace
"gosh! kaga nifa Hydar ban cika son
hayaniya ba wnn abu hka sae kace ina
kindergarten, don Allah ka taho muyi abinda
ya kawo mu ka mayar da ni gida yau fa xan
fara gyaran jiki" Inteesar ta mike tsaye da
sauri tana mata wani mugun kallo tace
"da'alla fice min daga daki rahama ya shigo,
banxa da ke kawae jahila" Safeenah tayi
wani dariya tana taunar cingam din yan iska
tace "ae sae dae ki kira wani gun da dakin
ki amma ba nn ba, don dis is myn, kuma
kika sake ce min jahila wllh sae na kusan
illataki kmr yanda mijinki ya gaya maki daxu,
don wnn karan ba sae ya dukan min ke ba,
ni da kaina xan nakade ki, ki san cewa ni ba
sa'ar uwarki bace bare......" bata rufe baki ba
Inteesar ta sauke mata tagwayen mari masu
rae da lfya nn da nn fuskarta ya koma ja
don axaba, ta dafe kuncinta a gigice tana
kallon Aliyu da ya jingina jikin bango
rungume da hannayensa yana kallon
Inteesar da mamaki tace "wat? She slapped
me Hydar" Inteesar tace "ae kadan ma kika
gani," bata jira me Aliyu xae ce ba tayi kanta,
inteesar na ganin hka ta fasa ihu a tsorace
tayi hanyar bathroom, safeenah ta fixgota ta
buga ta da bango ta shaketa tana huci snn
ta shiga dukanta kmr an aikota Aliyu yyi
kansu da sauri ya fixge safeenar ya watsa
mata mari ya buga ta da bango yana huci
yace "don ubanki kasheta xakiyi ne,"
Safeena tayo waje da ido tana kallonsa da
mamaki, Inteesar ta sulale kasa gabanta na
faduwa tana kallonsu, Safeenah ta girgixa
kai ta fashe da kuka tana kallon Aliyun, ya
saketa ya dafa bango tare da sauke ajiyar
xuciya, can ya dawo gabanta a hankali yace
"meyasa xaki kulata Safeenah baki ga
yarinya bace warce bata san ciwan kanta
ba, bbu abinda ta sani nn da kike ganinta
she's just a kid," Inteesar ta mike tsaye tace
"ku dae ne baku san ciwon kanku ba amma
ni nasan ciwon kai na," Aliyu ya bude baki
da mamaki yana kallonta, tayi hanyar
bathroom da sauri xata shige ya bita ya
fixgota a fusace, ta fasa masa ihu tare da
durkushewa a kasa tace "wayyoo Abbana,"
ya durkushe shima da sauri gabanta yana
kallonta yace "me ya faru?" ta dago tana
kallonsa kmr xata yi kuka tace "to ba kai bne
xa ka doke ni
.
Aliyu yyi kwafa ya mike tsaye, ita ko ta ja da
baya daga xaunen da take tana goge
hawayenta, ya juya yana kallon Safeena
dake hawayen takaici xae yi magana ta juya
da sauri ta bar dakin yaji ta bude kofar
dakinsa ya gane jakarta xata dauka a ciki ta
bar gidan, ya juyo yana kallon Inteesar da ta
bi ta da harara, ya sa kafa ya haureta yace
"xan babbalaki a gidan nn wllh idan kika yi
wasa," ta mike tsaye da sauri tayi tsaki can
ciki ta koma kan gado ta xauna tana ci gaba
da share hawayen fuskarta, danna bell din
gidan da aka yi yasa ya juya ya fita daga
dakin dae dae lkcn da Safeena ma ta fito
daga dakinsa rike da handbag dinta, yace
"haba bby ina kuma xaki?," ko kallonsa bata
yi ba ta fara sauka daga stairs, ya bi ta da
sauri yana kiran sunanta,tsaye suka ga
Hajiya a falon tana kare ma ko ina kallo
fuskarta a tamke, ya juya da sauri ya koma
dakin Inteesar, tana nn yanda ya barta ya
karasa gabanta yana kallonta ya kama
hannunta ta fixge tana hararansa tace
"meye hka," ya buge bakinta ya fixogata ya
bude bathroom ya tura ta ciki snn ya kulle
da makulli ya cire makullin yasa a aljihu,
kofar ta shiga bubbugawa tana kuka, ya fice
daga dakin ya sauka downstairs da sauri,
tsaye yaga safeena kusa da Hajiyan tana
mata magana tana kuka, ko me take ce
mata oho, ya karaso yana kallonsu Hajiyar
dake ta faman huci tayi hanyar stairs kmr
xata tashi sama, ya juya yana kallon
safeenar yace "me kika gaya mata," ta galla
masa harara tace "meye baxan gayamata
ba," yace "haba safeenah kin san fa ina
sonki kuma dae kinga abinda na mata daxu
a kan rashin kunyar da ta maki,yarinyar ce
bata jin magana wllh ban san yanda xanyi
da itaba," tace "dnt tell me dat kai dae kace
ka fara sonta kawae,idan ba hka ba yarinyar
dake mugun tsoranka kmr mutuwalkci daya
xata rainaka hka idan ba wani abun ya
shigatsakaninku bane kana xuwa gurinta
da daddare karban sweet tunda dae kai a
wnn bangaren baka da maraba da maye,"
yace "ya salam, haba safeena wllh bbu
abinda ke shiga tsakaninmu me take dashi
da xata bani, baki yrda dani bne, wllh
Abbana ne yasa ta rainani hka ke ma kinsan
ba wasa da ita nake ba," safeena taki cewa
komai sae tabe baki da tayi, ko minti biyar
ba ayi ba Hajiya ta sauka tana huci tace
"kaban mamaki Aliyu ban xaci hka daga
gareka ba," sae kuma ta fashe da kuka "ni
dama nasan cika bakin naka na kwana biyu
ne sae sun juya min kanka, na shiga uku ni
Aisha," safeenah tace "no Hajiya shi ba
ruwansa ae bae yi supportn din ta ba, har
dukanta ma sae da yyi amma hkn bae sa ta
daddara ba, ina ga kmr a gida ake xugata"
Hajiya kmr xata hadiye xuciya don bakin ciki
tace "to na shiga dakin ban ganta ba kuma
ai," Aliyu yace "nima na shiga ynxu nace ta
tafi gida ban ganta ba," Hajiya tace "xata ko
ci ubanta shegiya tsinanniya, daxu fa a
gabana Alhaji yace xainab taje tace ta dawo
gida taki dawowa, ita ta samu gidan hutu
ko to wlh ba gidan dana ba don ubanta
kuma idan Allah ya yrda baxa ki shigo ki
sameta a gidan nn ba Safeena," safeena tayi
murmushi tace "to Hajiya naji ddin jin hkn,"
Hajiya tace "to ya shirye shirye safeena, kin
xo ganin Aliyun ne, shi me ya hanasa xuwa"
safeena tace "ehh dama yace na xo na xabi
dakin da nake so ne, kuma nace wanda take
ciki ne yyi min," Hajiya tace "to ae shknn sae
yasa ta fiffito da kayan nata, abinda ma ba
samunta xaki yi a gidan ba ae Alhaji ya nuna
kawae ta dawo gida" Aliyu ya juya ya koma
sama ya shiga dakin nata, ya ciro makulli ya
bude kofar bathroom din, ta mike tsaye a
tsorace da ganinta kasan kuka ta ci, ya
karaso yana kallonta ya galla mata harara
yace "uban me aka maki munafuka," ta
girgixa kai a tsorace xata yi magana suka ji
muryarsu alamar suna haurowa sama, ta
shiga yarfe hannu tana hawaye tace "wayyo
tsoro nake ji xata dawo," ya juya yana kallon
kofar dakin, yaji safeenah na cewa "bari mu
je dae ki gani Hajiya" da sauri Aliyu ya rufe
kofar bayin ya sa makulli ya koma baya ashe
tana dab da shi ya bugeta tayi baya xata
fadi yyi hanxarin rikota ya rungumeta,
taboye fuskarta a kirjinsa tana kuka a
hankali har wani rawajikinta yake, su Hajiya
suka bude kofar dakin suka shigo safeena
na cewa "ban ma duba bathroom din ba
wllh," Hajiya tace "ehh duk sae mu duba
ynxu," xamowa Inteesar ta shiga yi daga
jikinsa ya bita ya riketa yana mata wani
mugun kallo, a hankali cikin muryar kuka
tace "tsoro nake ji," ya mike tsaye ya dagota
jin suna bude drawers dinta yasa ta girgixa
masakai taki mikewa tsaye, taka kafarta yyi
yana mata mugun kallo ba shiri ta mike har
tana bugesa makullin hannunsa ya fadi,
yasa kafa da sauri ya take amma duk da hka
sae da yyi kara,ta toshe bakinta a tsorace
tana harharde kafa ta rikesa tace "wayyo ya
Aliyu fitsari xanyi,"
.
Safeenah tace "ina ga kamar fa da mutum a
bayin can," Hajiya tayi shiru tana kallon
bayin snn ta karasakusa da bathroom din ta
murda kofa ta ji shi a rufe, tana kallon
safeena tace "a rufe yake ma," safeenah ta
karaso ita ma ta murda taji shi a rufe, ta sa
kunne ko xata ji motsi, Hajiya tace "to wae
ma ina Aliyu yyi ne ban gansa ba," Aliyu ya
tsura ma kofar ido yana kallo, ita ko Inteesar
sae yarfe hannu take hawaye na bin
kuncinta tanabubbuga kafa a kasa a
hankali, har gobe ita dae tasan baxata daina
tsoron Hajiyar nn ba, suka ji Safeenah tace
"bari naje naga ko kofar iri daya ce da na
dakinsa na dauko tasa makullin," Inteesar ta
dafa sa a tsorace tace "nashiga uku wayyo
Abbana," har wani bari jikinta yake, ya
riketayana kallonta yace "xaki sha mari, idan
baki rufemin baki ba," ta sa hannu ta toshe
bakin jikintana rawa, hajiya kuwa na ta
bude buden drawersdin dakin tana ta xage
xage ita kadae harsafeena ta shigo rike da
makullin, Hajiya tace "kinsamu," safeena tace
"eh iri daya ne, bari mu budemu ga,
munafuka kila tana ciki," Inteesar ta
kamohannunsa hawaye ya gama wanke
mata fuskamuryarta na rawa kmr mae rada
tace "ya Aliyuwllh fitsari xanyi," ya jawota
yana kallonta yashiga xuge mata xip din
skirt dinta, ta rike skirt din da sauri tana
xaro ido, ya galla mata harara murya can
kasa kasa yace "ba fitsari xaki yi ba," ta
girgixa masa kai sae kuma ta gyada kan da
sauri kmr wata wawuya, ya xuge mata gaba
daya Zip din ta rike hannunsa da sauri tana
xaro ido, suka ji Safeena na kkrin saka keyn
cikin kofa, ta rungumesa tana kuka a
hankali tace "ya Aliyu wllh dukana xasuyi
tsoro nake ji," shima ahankalin yace "ae
gwara su doke kin ni da kaina ma xan bude
masu kofar idan sun kasa," ta shiga girgixa
masa kai cikin tashin hankali tace "A'a don
Allah kayi hakuri ka kai ni gidanmu yau
Abba dama yace na dawo," safeena dae na
ta kiciniyar bude kofar Hajiya na taya ta, a
hankali Aliyu ya bi skirt dinta da ya shiga
xamewa daga jikinta da kallo har ya sauka
kasan bayin, ya tsura ma laps dinta da
kafafuwanta ido, don tsabar tsoro bata ma
lura da hkn ba ganin wani irin kallon da ya
shiga mata yasa ita ma ta kalli inda yake
kallo, ta durkusa da sauri tace "na shiga
uku," ya dagota, nn da nn yanayinsa ya
canxa tace "wayyo Abbana......" a hankali kmr
wan mashayi yace mata "ae baxa su iya
budewa ba tunda ba makullin bane dnt...."
bae karasa abinda xae ce ba ya shiga kissin
dinta kmr xae cinyeta, ta shiga turasa da
karfi suka xube kasa, bata san lkcin da ta
fasa wani ihu a tsorace ba jikinta na rawa.
Safeenah ta juya da sauri tana kallon Hajiya
tace "ba nace maki tana ciki ba" Hajiya ta
shiga buga kofar da sauri tana cewa "don
ubanki fito ki bar gidan nn kar na kasheki
shegiya munafuka, gidan da na yafi karfinki
wllh" a tsorace cikin kuka ba tare da ta
shirya ba tace "kiyi hkuri mumy xan....." buge
mata baki Aliyu yyi da karfi ya mike tsaye
yana kallonta ya sa kafa ya haureta, ta toshe
bakinta ta koma baya da sauri hawaye na
cigaba da bin kuncinta, safeenah tace
"Hajiya kawae mu kira kafinta ne ya balla
kofar don ba budewa xata yi ba," a fusace
Hajiya tace "to wae ina Aliyu ne, ya xo ko
xae iya ya bude don wllh wllh yau sae ta bar
gidan nn don ubanta," safeena ta ciro waya
tace "bari na kirasa," yana jin hka ya ciro
wayarsa da sauri ya kashe, safeena tace
"kinji tsiya wae a kashe yake," nn Hajiya da
safeena suka dinga xaginta suna cewa ta
bude kofar ta xo ta wuce gida kar su balla
su kasheta, ita dae bata ce komai sae kukan
da take yi a hankali, shi ko Aliyu na tsaye sae
kallon kofar yake yana girgixa kai, sun kai
kusan minti goma a dakin suna abu daya
daga bisanni suka bar dakin Hajiya nacewa
"ae yau da ta kwana gidan nn gwara gidan
ya babbake, bari muje mu samo kafinta ya
cire kofar kawae, shi kuma Aliyu don tsabar
wlknci ficewa yyi ya bar gidan ga yar iska ta
xo" Safeena tace "ni wllh Hajiya tsoro ma
Aliyun nn yake bani," yana ji sun fita daga
gidan gaba daya ya juya yana kallon
Inteesar da ta xama kmr wata marainiya ya
daga hannu xae xabga mata mari ta fasa
ihu sae kuma ya fasa, ya fixgota yana mata
mugun kallo yace "daga yau kika sake bara
min wnn shegen bakin naki kmr na xaki a
gidan nn sae na cire maki hakora wawiya
kawae," yana kaiwa nn ya bude kofar ya fice
ya bar ta nn durkushe tana kuka, direct gun
mai gadi ya nufa yace "kar ka bude ma
kowa gate ya shigo gidan nn, snn kar ka
bari ta ciki ta fita" mai gadi yace "to yallabae,
snn ya shiga motarsa ya bar gidan shima,
hka Inteesar ta yini tana kuka ranar gashi
mai gadi yaki barin ta fita, tsoranta daya kar
su Hajiya su dawo, cikin ikon Allah kuwa
bata ga sun dawo ba, har ta kwanta ranar
Aliyu bae dawo gidan ba. Yau tana xaune ita
kadae abun duniya ya isheta rabonta da
Aliyu tun ranar da Hajiya ta xo gidan aka yi
wnn draman gashi yau kusan kwana uku,
budewar kofar dakinta yasa ta mike a
raxane don ynxu ba karamin tsoron gidan
take ba, Zainab ce ta karaso tana kallon
Inteesar tace "wae dama ashe aure Aliyu
xae yi Inteesar," jikin Inteesar yyi sanyi kmr
lkcn ta fara jin xancen, tayi shiru bata ce
komai ba, ganin Zainab ma tayi shiru yasa
tace "wa ya gaya maki," Zainab tace "yau
Abba ke gaya ma Inna wae ashe ma saura
sati daya, tun safe inna ke kuka tana tsine
tsine a gidan wae xamanta ya xo karshe a
gidan," Inteesar ta xauna gefen gado bata
sake cewa komai ba, Zainab tace "in ni ce ke
Inteesar wlh baxan xauna gidan nn ba,
infact na gama auren ma gaba daya, duka
duka watanku nawa da auren ko three
month fa bae cika ba," budewar kofar dakin
yasa suka juya da sauri suna kallon waye,
Aliyu ne ya shigo dakin yana ma Zainab
wani irin kallo, nn da nn hanjin cikinta ya
kada.
.
Zainab ta dauki mayafinta gabanta na
faduwa ta kalli Inteesar tace "na tafi
inteesar, inna tace na xo nace maki ki hada
kayanki tana nn xuwa," tana kai wa nn ta
juya ta dake tana kallonsa tace "ina yini
yaya," bae tanka mata ba sae dae har lkcn
kallonta yake, ta bi ta gefensa xata wuce ya
cakumota ya watsa mata mari cikin tsawa
yace "daga yau, na sake ganin shegun
kafafunki cikin gidana wllh sae na ji maki,"
kuka ta fashe da tace "ni me nayi maka xaka
mareni hka wlh sae na gaya ka da Abba,"
wani marin ya kai mata snn ya fixgota ya
shiga janta har suka fita daga gidan, ita dae
Inteesar bata ce komai ba sae kifa kanta da
tayi kan gado tana kukan da bata san
dalilinsa ba, suna isa gate Aliyu yace
mamaigadi "kar ka sake barin yarinyar nn ta
shigo gidan nn," mai gadi yace "to yallabae,"
snn ya jefar da ita waje ya rufe gate din ya
koma cikin gida. Washegarin ranar da
daddare Inteesar na gaban madubi ta fito
daga wanka knn tana shafe shafenta gaban
madubi wayarsa dakegunta yyi ring ta duba
ta gane nmbrsa ce dayan, ta daga yace "ina
jiranki downstairs," da kmraxa ta je ba sae
kuma ta dauki Hijab dinta har kasa ta sa snn
ta sauko downstairs yana xaune remote a
hannunsa, yana daura idonsa kanta ya daka
mata tsawa "ke daga yau kika sake sa irin
wa innan hijaban a gabana sae na ci ubanki
daga ke har hijabin, wawuya kawae get
out," ganin bbu alamar wasa tattare da shi
ya sa ta koma sama ta sa kayan barcinta mai
dan mutunci don dama xani kadae ne
jikinta snn ta sa gashinta cikin net ta sauko
kasa fuskarta a daure, kallo daya yyi mata ya
dauke kansa yace "ga kayanki nn ki kwashe
su gabana," ta tsura ma akwatinan da ya
nuna mata ido snn ta dake tace "na me," ya
galla mata harara yace "na xubar wa, c'mon
kin xo kin kwashe su gabana ko sai na bata
maki rae" ta girgixa kai tana kkrin mayar da
hawayenta tace "na yafe bana so, ka kara
mata a nata," tana fadin hka ta juya da sauri
ta koma sama, ya bi ta da kallo, kan gado ta
fada ta fashe da kukan takaici tana data
sanin kin bin Zainab da tayi ranan, don dae
ko hauka yake baxae je yace xae daukota
ba, Aliyu ya cuceta ya walakantata bakin
cikin ta daya ynxu ya raba ta da budurcinta,
hka ta kwana ranar tana abu daya.
Washegari da safe ya shigo dakin yana
kallonta bbu yabo bbu fallasa yace "ki shirya
anjima xa a raka ki registration na Jamb,"
yana kai wa nn ya juya xae fita ta mike da
sauri tace "bbu inda xa ni wllh," ya juya yana
mata wani mugun kallo yace "to sae me, me
xa a fasa mutuwan ko hisabi, kar Allah yasa
kije din jaka kawae" ta fashe da kuka tace
"ni a jaka bace wllh, ka jira jaka na nn
shigowa nnba da ddewa ba," ya karaso
cikin dakin ya kwashe ta da mari ta fasa ihu
tana kiran Abbatace "Allah ya isana ban yafe
maka ba wlh mugu kawae," juyawa yyi ya
fice daga dakin da sauri ta mike jikinta na
rawa ta shige bathroom ta rufe da key.
Karfe sha biyu saura taji ana ring din Bell, ta
sauko gabanta na faduwa don tasan Aliyu
baya danna bell, ta karaso kusa da kofar
tana lekan ko waye, wani mutumi ta gani
tsaye, ta ki bude kofar tace "waye," yace "ina
yini madam, Yusuf ne, oga Hydar ne ya
aikoni waexamu je registration da ke yau,
shi yana buzy," tace "kaje kace masa ban
xuwa," bata jira me xae ce ba ta koma sama
abunta, da daddare Aliyu ya dawo gidan
direct dakinta ya nufa ta hada tea knn xata
sha, duk da ba karamin tsorata tayi ba
amma ta dake bata nuna ba, kuma taki
dago kanta, ya karaso inda take ya fixgota
cikin tsawa yace "wani sako kika bada a
kawo min daxu," ta shiga kikkifta ido a
tsorace tace "ni ka kyaleni wllh," ya jefar da
ita ya fice daga dakin ta bi sa da harara, ko
minti biyar ba ayi ba ya dawo rike da belt, ta
fasa ihu a tsorace ta mike tsaye tace "na
shiga uku, wayyo Abbana," ya fixgota ya
shaketa yana huci yace "na rantse da Allah
idan baki kama kanki a gidan nn kinsan da
wanda kike xaune ba sae na sumar dake
watarana" yana kai wa nn ya buga ta da
bango ya fice daga dakin, hka ta kwana
kuka da ciwon kai ranan, Da safe yana fita
ita ma ta shirya xata bar gidan amma mai
gadi yaki bude mata gate ta dinga rusa
masa kuka tana rokansa ya bude mata gate
amma yace "to ko yau sae da yallabae ya
kara jaddada min cewar kar na bari ki fita,"
ta fashe da kuka abun tausayi ta kasa cewa
komai, kmr daga sama taji Muryar inna da
karfi tana cewa "salama alekum, kin tabbata
nn ne gidan kursum"
.
Inteesar na jin muryar inna ta fasa kuka
tana kallon gate din, inna ta shiga bubbuga
gate din tana cewa "lah nn ne kursum ga
muryarta nn naji, a bude mana" Mai gadin
yace "waye wnn," inna ta bude baki tace
"nashiga uku amar ya waye? Waye ke min
wnn tambayar," Inteesar tace "malam ka
bude mata kakata ce fa," mai gadi yace "ko
ma wacece yallabae yace kar na bude ma
kowa gate," cikin daga murya inna tace "yau
naga jaraba waye wnn kuma" kursum tace
"mai gadi ne," inna tace "mai gadi? To ya ci
ubansa ba a gaya masa ko ni wacece bane
ni da gidan jikokina xae hana ni shiga,"
kursum ta fashe da dariya inna tace "ke ban
san shashanci fa," sae kuma ta shiga kiran
Inteesar," cikin kuka inteesar tace "Na'am
inna yaki bude gate din," a fusace inna tace
"yau ni naga jarababben dan iska gate din
ta ubanka ce ko ko, kaji min mutum," dariya
ma abun yaba mai gadin inna tace "shi
Aliyun yana ina," Inteesar tace "oho nima
ban sani ba," inna ta shiga buga gatedin da
karfi tana duddura ma mai gadi xagi,shi dae
yana xaune sae shan rakensa yake inteesar
tace "wae kai wani irin mutum ne baka jin
ka bude mata gate ne ka maida mutane
mahaukata," inna tace "ki rabu da shege,
kursum maxa kira min Bukar," kursum ta
karbi wayar ta kira Abba ta mika mata tace
"Bukar Bukar gani gidan Aliyu wani kato
yahanani shiga, na kai awa biyu tsaye cikin
rana Bukar," Abba yyi murmushi yace "to ae
umarnin da aka basa knn baaba ku koma
gida kawae," cikin kuka inna tace "kambu,
Al'quran bbu inda xani sae ya bude min
gate don uwarsa," nn ta shiga jijjiga gate
din kmr xata cire tana tsine ma mai gadi,
maigadi yyi tsaki ya ciro dan wayansa ya
kira Aliyu "oga ga wata tsohuwa nn ta xo ta
cika anguwa wae sae an bude mata gate,"
Aliyu yyi dariya yace "karka kuskura," snn ya
katse kiran mai gadi ya mike yana fito ya
shige dakinsa. Inteesar taji kmr ta shakesa
ta karasa kusa da gate din tace "inna Aliyun
ne fa yace kar ya bude maku wlh, ku tafi
gida kawae ba budewa ae yi ba," inna ta yo
waje da ido tace "me? To wllh bbu inda xani
ina nn har sae an bude min gate din," cikin
kuka take maganar, kursum kuwa sae
dariya take har da faduwa,inna ta nemi
dakali ta xauna tana sharbe majina, tace "ae
yau bbu abinda xae hanani shiga gidan nn
wllh sae na shiga" Inteesar ta gaji da
tsayuwa ta shiga, ciki lkci lkci ta kan fito ta
tarar suna nn, sae tausayin innan ya cika ta
taji kmr ta dinga ihu don takaici lallai Aliyu
ya cika mara mutunci, duk irin yanda ta
lallaba inna ta tafi kin wucewa inna tayi, har
aka kira azahar inna na nn xaune kursum ta
gaji ta kama hanyar gida inna ta rakata da
xagi, shegiya kawae ni ba mutum bace
kuma ban san ciwon jikina ba sae ke ko,
ganin har kusan karfe hudu inna na nn a
xaune yasa inteesar ta fito da ruwa tana
kallon mai gadi tace "don Allah don annabi
malam ka dan bude gate din sae ka mika
mata ruwan nn wllh tsohuwace," da kamr
baxae tashi ba sae kuma ya mike ya karbi
ruwan da take mika masa ya dan bude gate
din yana lekota yace "ga ruwa kaka," ta
mike tsaye tana kallonsa da shirin masifa ko
me ta tuna sae kuma tafasa, ta karaso kusa
da gate din kmr xata karbi ruwan ta
bangajesa da karfi ta shige gidan da gudu.
Me inteesar xata yi idan ba dariya ba, ta
durkushe kasa ta dinga dariya kmr cikinta
xae kulle, mai gadin ya bude baki yana
kallon inna dake huci tace "don buhun
ubanka ni xaka hana shiga gidan jikokina,
mugu katon bnxa kawae, wllh baka sameni
lkcn ina Rahmatu ba da yau bbu ubanda xae
hanani faffala maka mari dan iska,"
Inna na kai wa Aya ta yi hanyar garden kmr
xata tashi sama tana huci Inteesar ta bi ta
da sauri tana ci gaba da dariya tace "ba nn
bane hanyar shiga inna," Mai gadin ya sauke
ajiyar xuciya yana bin inna da kallo, bae taba
ganin tsohuwa da karfi hka ba, har suka
shiga falo Inteesar bata daina dariyar da
take ba inna ta hade rae tace "ke ni fa ban
san tsiya meye abun dariya a nn, wlkncin da
katon can yyi min ko me" kan Inteesar tace
komai inna ta rike haba baki bude
tace"A'aah bene kuma cikin gida ni
Rahmatu naga abinda ya ishe ni," Inteesar
tace "kuma shi xaki hau muje daki ba," inna
tace "ni ina xan iya," inteesar na dariya ta ja
ta suka haura sama tana mitan kafafunta na
ciwo, sae da inna ta fara sllh snn Inteesar ta
kawo mata abincin da ta dafa kmr dae
tasan inna xata shigo gidan daga karshe,
inna aka xauna aka bubbude kafa tana ci
tana xagin mai gadi da Aliyu, sae da inna ta
gama cika cikinta snn Inteesar ta xaga da
ita ko ina na gidan har dakin Aliyu sae da
suka shiga, inna sae washe hakora take
tace "ashe dae xan ga wnn rana da xan
taho gidan jikokina ni rahmatu, ae Bukar
bae yi ba, ni ban san meyasa yake min hka
ba gidan jikokina ma ya hanani xuwa sae
da ixininsa sae kace ubana, daba dan hka
ba ae sae na dawo nn ma gaba daya gani
ga ku, ni dae ynxu 'ya yana nake son gani
duk da bamu san gawan fari ba, xan so
naga yayanku da Aliyu," Inteesar dae bata ce
komai ba a xuciyarta tace Allah shi kyauta
na Haihu da Aliyu, inna ta juya tana kare
mata kallo tace "wae ni ya naji shiru ne har
ynxu Inteesar ga fadila can da ciki, anya
kuwa bakwa shan abu yaran nn, barin ke,
nafi tausaya maki don shegen yaron nn kai
ki xae yi ya baro ki" Inteesar ta hade rae tayi
gaba ta barta nn tsaye, inna ta bita a baya
tana cewa "to ni dae banga abun bata rae
ba a nn daga fadan gskya" suna komawa
daki inna ta xauna ta hade rae tana kallon
Inteesar tace "ki maxa ki hada kayanki tafiya
na xo yi dake dama, wae ashe gantalallen
yaron nn aure xae yi ban sani ba," sae kuma
ta fashe da kuka tace "sakayyar da xae
mana kenn, wllh sae ya baki takardar ki ba
rasa masoya kika yi ba," Inteesar tayi shiru
da mamaki tana kallon inna kmr ba ita ba
kuma mai son ganin ya'yansu, inna ta gama
ta mike ta koma kan gado tace "bari na dan
runtsa kafin nn kin gama hada kayanki,"
Inteesar dae bata ce mata komai ba har ta
fara bacci, ta kalli agogo ta ga biyar ya gota
ta mike a sanyaye ta shiga kitchen tana
tunanin abinda inna ta gama gaya mata
ynxu, to ynxu knn hada kayan nata xatayi
gaba daya su koma gida, jikinta ba kwari ta
shiga girka mata tuwan shinkafa da miyar
vegetable don tana da kayan girkin gaba
daya a deep Freexer, sae kusan Maghrib ta
gama komai snn ta koma daki tayi wanka
tayi alwala ta fito ta tada inna tayi sllh, karfe
bakwae da rabi ta shigo ma da inna abinci
inna tace "uban wa yace kiyi girki mu da
xamu bar gidan ynxu, kin gama hada kayan
naki" ta hade rae tace "to inna ki ci abinci
dae tukunna mana," inna ta sauko tace
"Atoh don xaman ki ya xo karshe a gidan nn
yyi ta xama da amaryar tasa, wae in
tambayeki wnn me sa kayan 'yar bbyn mai
kaman xabiyar nn ce xae auro," Inteesar ta
gyada mata kai kawae, inna tayi kwafa tace
"xasu ci ubansu," snn ta fara kai loman
tuwo, a tare suka gama cin abincin da inna
ta kwashi kwanukan ta kai kitchen ta shiga
wanke wanke ta gama ta fito knn Aliyu ya
shigo gidan, suna hada ido ta dauke kanta
da sauri tayi hanyar stairs yana yatsina
fuska yace "wa yace kiyi girki da kifi a gidan
nn, kinga ina son jin warin kifi?" tayi masa
wani mugun kallo ta haura sama ta bar sa
nn tsaye, ko da ta koma ta tarar inna na
shafa'i da wutr, ta shiga bayi ta wanke baki
snn ta fito ta xauna gaban madubi tayi
shafe shafenta ta saka kayan barcinta ta
kwanta don tayi isha, inna na idarwa tace
"to ynxu dae tunda dare yyi, sae mu bari
gobe da sassafe mu bar gidan nn, shi kuma
wnn yaro dama baya dawowa gida ne naji
shiru har ynxu, ko dama ke daya ke rayuwa
cikin gidan," Inteesar bata tanka ta ba tana
ta game da wayar Aliyu, inna ta tabe baki
tace "to Allah shi kyauta, ynxu dae kije ki
hado min tea don idan ban sha ba bana jin
ddi" Inteesar tace "kai inna duk tuwon da
kika ci," inna tace "naga dae ba ke ke
siyowa ba jikana ke siyowa," inteesar ta
harareta ta mike tayi hanyar fita xata je
hado mata tean, tana bude kofar ta kusan
cin karo da Aliyu dake labe jikin kofar, shi
ma xuwansa knn, suka xaro ido a tare xata
fasa ihu don ba karamin tsorata tayi ba
kuma bata yi xaton ganinsa gurin ba yyi
saurin fixgota ya rufe kofar
.
.
Inteesar ta turasa xata koma cikin dakin ya
rikota da sauri ya toshe bakinta ya ja ta
suka shiga bedroom dinsa ya tura kofan ya
jingina jikin kofar yana mata wani irin kallo,
tace "meye hka ni ka bude min kofa na fita,"
yace "hakkina nake so ki bani yau," ta xaro
ido gabanta na faduwa tace "meye
hakkinka kuma," yace "bari na nuna maki,
yyi kanta ta koma baya da sauri tana cewa
"wllh xan maka ihu idan baka bude min
kofa ba," a tsorace tayi maganar ya galla
mata harara yace "kiyi mana," ta girgixa
masa kai kamr xata yi kuka tace "don Allah
kayi hkuri tea fa xanje na hada ma inna,"yyi
murmushi yana kare mata kallo, rigar bacci
ne sky blue mara nauyi iya gwiwa a jikinta
mai hannun singlet, ta saka gashinta cikin
net, ya lumshe ido yace "bani hakkina tukun
sae kije ki hada mata kitchen din gaba daya
ma," xata yi magana ya daga ta sama kamr
wata yar bby sae kan gado, ba karamin
tsorata tayi ba cikin muryar kuka tace "ya
Aliyu don Allah ka bari ni ban san me kke
nufi ba," ya cire jallabiyar jikinsa yana
kallonta ya ajiye yace "xan gwada maki
abinda nake nufi," xata sauko daga kan
gadon ya danneta tace "wayyo na shiga
uku," kissin dinta ya shiga yi yana rungume
da ita, duk ta gigice ta shiga turasa amma
yaki sakinta ya shiga romance dinta, kuka
ssae ta shiga yi ganin abun nasa ba na
wasa bne, suka ji inna ta bude kofar dakin
Inteesar din ta fito tana cewa "yau naga
rayuwa daga xuwa a hado min tea shiru
har ynxu," inna ta rike haba tace "lau ko dae
shafe shafen nn da naga tana yi daxu gun
mijinta xata" sae kuma ta fita ta samu mai
gadi tana kallonsa tace "kai mara mutunci
mai gidan ya dawo ne," da kmr baxae kulata
ba sae kuma yace "ehh" tace "amma
yarinyar nn anyi yar bnxa gun mijinta ta tafi
ta barni," ta koma ciki ta hada tean da kanta
ta koma daki tace "ikon Allah, amma wnn
anyi munafuka" Inteesar na jindawowanta
cikin kuka tace "kayi ma Allah ka kyaleni na
kai mata abinda ta aikeni," Aliyu bae ma san
tana yi ba lkci daya yanayinsa ya canxa ya
xaman mata kmr wani xautattce, duk ita ma
ya bi ya kashe mata jiki ganin ya soma
rabata da kayanta yasa ta kankamesa jikinta
na rawa tace "don Allah ka bari ya Aliyu ka
tausaya min wllh tsoro nake ji," ya girgixa
kai da kyar yace "plss fateema ni ma ki
tausaya min," cikin kuka tace "wllh baxan
iya ba," murya can kasa yace "don Allah fa
nace maki," ta shiga turasa jikinta na rawa
tana kuka tace "wayyoo tsoro nake ji don
Allah kajitausayina wllh bna so," ya fada
gefentayana mayar da numfashi, ganin tana
nemansauka daga kan gadon yasa ya
fixgota ya rungumeta, cikin shessheka tace
"don Allah kaji tausayina ka bari," da kyar
yace "bbuabinda xan maki," duk da hkn
bata kwantar da hankalinta ba sae kuka
take, shi dae yana rungume da ita idonsa a
lumshe, hkn yasa tayi shiru sae ajiyar
xuciyar da take,suna nn a hka har bacci ya
dauketa, ya kwantar da ita ya lulluba mata
bargo ya koma dayan side din jikinsa a
mace ya kwanta, hka ya kwanta ranan a
wahale da ciwon ciki, ita ko tana ta bacci
abunta, cancikin dare ganin bacci ya
gagaresa yasa ya mike ya koma falo ya sami
lime ya sha ya kwanta, da asuba ruwan
sanyi gora guda ya tashe sa
.
Aliyu ya mike xaune
da sauri yana kallon inna a fusace yace
"meye hka," tace "so nake kasan naxo
gidanka," yyi tsaki ya mike tsaye yyi hanyar
stairs ya bar ta nn tsaye tana dariya, yana
shiga dakinsa ya tarda Inteesar ta fito daga
wanka knn, ya kalli agogo yaga biyar saura
minti goma, ta kasa karasowa cikin dakin
dan towel dinsa ne jikinta, bata so ya shigo
ya tarda ita a dakin ba kuma wae nn ita
dubara xata ma inna kawae sae dae ta farka
ta ganta kwance dakin, bae sake kallonta ba
ya shige bathroom, ko me ya tuna sae kuma
ya fito da sauri ita ko har ta isa kan gado ta
sa hannu xata dauki rigar baccinta ta
sakasae ta koma dakinta, ya karasa kusa da
gadon shima ya daura hannu kan rigar
baccin yana kallonta, ta cire hannunta ta
mike tsaye ya dauki rigar da net dinta yyi
hanyar bathroom da shi ya bude washin
machine ya jefasu ciki snn ya rufe kofar
bayin, duk tana kallon abinda yake yi taji
kmr ta fasa ihu, tasan iskanci kawae yake
son mata, ta kalli towel din jikinta ynxu haka
xata fita, ita gashinta dake jike ma yafi
damunta, Allah dae yasa inna bata tashi ba,
ganin kmr tana bata lkcn ta kar inna ta tashi
yasa ta fita da sauri ta bude kofar dakinta a
hankali ta shiga, xaune ta tarda inna kan
darduma da casbi a hannu ta saka Tv a
gaba ko ya aka yi ta kunna oho, inteesar taji
kmr ta nutse don kunya inna ta kalleta ta
tabe baki tace "ban san baki da kunya ba
Inteesar sae yau, idan ba rashin kunya ba
kina ganina a gida ki tafi turakar mijinki ki
kwana daga cewa ki kawo min tea, da kika
tashi dawowa kuma sae ki dawo mun
daure da tawul," Inteesar ta galla mata
harara tace "ku ji min tsohuwar nn me xan
maki idan ban tafi gurin mijina ba to," inna
ta bude baki, Inteesar tayi dariya ta dauki
xani ta cire towel din jikinta ta daura, inna
tace "ae ba dan jiya dare yyi ba da baxa ku
tashi ku tarar dani gidan nn ba, inteesar
bata tanka ta ba ta dauki Hijab ta sa ta tada
slh, ko da ta idar ta gaida inna maimakon ta
amsa sae ca tayi "ni tashi ki hada min kayan
karyawa nayi na bar gidan nn tun kan na
fara ganin abinda yafi karfina," inteesar xata
yi magana Aliyu ya bude kofa ya shigo dakin
yana kallon inna, daga tsayen yace "an tashi
lfya," inna ta galla masa harara tace "ban
tashi ba, hka kke gaida uwarka," Aliyu yace
"har gida xan xo na rama abinda kika min
daxu wllh," Inteesar ta mike ta fita daga
dakin ya bi ta da kallo ya tabe baki yana
kallon inna yace "yar nn bakuyi mata trainin
me kyau ba a gida, bata san ta tashi ta gaida
mutum ba da safe," inna tace "ae gun
uwarka ta gaji hka, wae ni Aliyu ya naji
shiru har ynxu ban ganta da ciki ba," Aliyu
yace "ita ce tace bata son Haihuwa,shine ma
yasa xan auro warce ke son Haihuwan"
inna tayo waje da ido tace "kmr yaya," xae yi
magana wayar inna ta cika daki da ruri ta
daga da sauri tare da cewa "salama
alekum," ya mike ya fice daga dakin, kitchen
ya sameta tana hada ma inna break, ya
karaso kusa da ita yana kallonta yace "ke
gidanku ba a koya maki idan kin tashi da
safe kiyi gaisuwa ba ko," ta tabe baki bata
ko kallesa ba bare ta basa amsa, kmr xae yi
magana sae kuma ya fasa ya matsa dab da
ita yace "gobe xa a xo ayi ma amaryata
danki, kuma tace dakin da kike ciki take so
don hka nake so kije ki fara fiffito da
kayayyakin dakin ki xaba wani dakin ki
xuba su ciki," tayi yar dariya bata ce komai
ba, yace "hope dats clear," tayi masa wani
mugun kallo ta juya xata fita daga kitchen
din ya kamo hannunta.
Inna na xaune a daki tana kallo bayan ta ci
tayi kat, inteesar kuwa na wanke Bathroom
Aliyu ya shigo yana kallon inna yace "inna xo
mu je indan xaga dake gari mana tunda ina
gida yau," inna na kallonsa da mamaki don
daxun nn suka gama fada tace "kai da
gske? Amma fa ba tukin nan taka ta
ganganci xaka yi dani ba fa," yace "wllh a
nutse xan tuka ki," ta mike da sauri tana
gyara daurin dankwalinta tace "to ita
Inteesar ita kadae xa mu bari gida, wae ma
to wa xae je ya kwaso min kayana ne," yace
"ehh xan kira Zainab ta kwaso maki, inna
tace "Inteesar ke baxa ki je bane, Aliyu yace
"ki dae gaya mata me xata girka maki kafin
mu dawo," inna tace "to kiyi min tuwan
semo da miyar kubewa," inteesar ta fito
tana kallonsu, ko kallonta inna bata yi ba
tace "sae mun dawo," ta fice Aliyu ya juya ya
galla mata harara snn ya fice shima, mai
gadi na bude masu gate tace "yauwa Aliyu
wnn ba mutumin arxiki bne jiya kokuwa ya
dinga yi dani ka koresa," yace "to inna,"
suna ta tafiya suna hira inna sae kyalkyale
dariya take duk da Aliyu bae ga abun dariya
ba don hiran ma ba ganewa yake ba, tafiyar
kusan minti talatin suka yi snn yyi parkin
yana kallon inna yace "to fito in siya maki
nama," inna ta fito da sauri tace "yauwa dan
albarka" tana kare ma inda suke kallo
bakinta a wangale, can sae fara'ar dake
fuskarta ya bace tace "nn ae anguwansu
farida ne Aliyu," yace "yauwa ashe kin gane,
kuma nasan xaki iya gane gida daga nn
kina shan kwana xa ki ga gate, in kin koma
sae kice da Haisam ya siya maki naman don
ban fito da kudi ba" yana kai wa nn ya shige
motarsa yyi gaba inna ta fasa ihu tana salati,
mutanen dake gun suka taho da sauri suna
tambayar lfya. Inteesar na kwance da
daddare ya shigo gidan ita dae tasan bbu
maganar dawowan inna gidan, tana ji ya
bude dakinsa ya shiga, ta mike xaune ta
rafka tagumi tana naxarin abinda yace mata
daxu da safe ita har lkcn ta kasa gaskata
wae Aliyu aure xae yi nn da kwana hudu,
tunanin hkn yasa hawaye ya cika idonta,
tana nn xaune har kusan karfe daya ganin
bacci ya kaurace mata yasa ta mike a
sanyaye ta shiga bathroom ta dauro alwala
ta fito ta fara sllhn dare. Da safe tana gaban
madubi tana gyara fuskarta ya shigo dakin,
1st tym in history Aliyu ya shigo mata daki
da sallama ta amsa ba tare da ta kallesa ba
yana kallonta bbu yabo bbu fallasa yace
"kina jina, ki kama kanki safeenah xa su xo
gidan nn anjima don nasan baki da kunya,
infact bance ki fita ba ma," tace "akan me
baxan fita ba? Wllh bbu abinda xae hanani
fita," yace "shknn, ni kuma xan ce mata duk
abinda kika yi mata tayi min maganinki" ya
juya ya fice daga dakin bayan kmr minti
goma ya dawo yana kallonta yace "kinga
dakina yyi kama da dakin kaya, c'mon kin
wuce kin dauke min kayanki da kika ajiye
min a ciki ko sae na bata maki rae," xata ce
wani kaya sae ta tuna kayan baccinta dake
dakinsa ta mike fuskarta daure ta fita tayi
hanyar dakin ya bita a baya tana shiga
dakinsa ya jawo kofan yasa key, ta juya da
sauri tana kallon kofar ta shiga bugawa
tana cewa "meye hka," yace "hka xaki tsaya
har sae na dawo," ya rufe nata dakin ma da
key snn ya fice ya bar gidan, kuka ta fashe
da ta durkushe tana kare ma dakin kallo,
sae a snn ta lura da kayan tea da cakes din
da ya ajiye mata kan fridge sae plantain
chips, karfe sha biyu taji ana shigowa gidan
da motoci ta mike da sauri don bayan ta
gama cin kukanta ta gaji kwanciya tayi, ta
karasa jikin window taga manyan motoci
shake da kaya har kusan guda uku, wasu
lafiyayyun motoci suka shigo gidan, manyan
mata kusan su goma suka fito suna
daddaga hanci, sae ga wata motar ma ta
shigo safeena da kawayenta suka fito daga
cikin motar tana gwada masu ta inda xa su
bi su shiga gidan, tuni aka fara sassauke
lafiyayyun funitures din da aka shigo da,
Inteesar ta sake labulan a sanyaye ta koma
kan gado tayi kwanciyarta tare da lumshe
idonta da taji na neman kawo kwalla, duk
suka cika gidan da hayaniya wasu na sakin
magana, ana ta shigo da kaya. Ko minti sha
biyar ba ayi da shigowarsu ba Anty Nafeesa
da Zainab suka shigo gidan, suna shiga falo
duk aka juya ana kallonsu, batare da Anty
Nafeesa ta kallesu ba tace Sannunku fa,
Zainab kuwa dama ko kallonsu bata yi ba,
Safeena dake kwance kan kujera da
kawayenta suna ta hira da shewa ta bi su
da wani irin kallon raini hka ma iyayen nata,
cikin daga murya Anty Nafeesa tace "to ina
uwar gida sarautan mata kuma ran gida
take ne," Zainab tace "ina xata iya da wnn
hayaniyar Anty, kila tana can cikin daki,"
.
Safeenah da 'yan uwanta suka bi su da kallo
har suka haura sama Anty Nafeesah na
cewa "gskya kam ina xata iya da wnn
hayaniyar," wayar Zainab yyi ring ta duba ta
ga ya Aliyu, tace "ashe dae ya Aliyu na da
nmbrna," ta daga yace "ki fito waje ki
karbar maku makulli," tace "na me," yace
"ban sani ba snn ya katse kiran" ta kalli Anty
Nafeesa dake buga kofar inteesar tana
kiranta tace "wae yaya naje na karba makulli
a waje," Anty Nafeesa tace "na me, ko tare
suka fita da Inteesar din ne," Zainab tace
"kila, ina xuwa na karbo keyn," ta fice da
sauri, yana cikin mota yana jiranta ta karasa
ya mika mata keyn dakinsa da na Inteesar,
tace "to ina inteesar din," yace "in kun bude
xa ku gani," ya ja motarsa yyi gaba, ta tabe
baki ta koma cikin gidan, dakin Inteesar
suka fara budewa bbu kowa ciki, snn suka
bude nasa, tana xaune ta hade kai da
gwiwa, suka karaso cikin dakin Anty
Nafeesah tace "amma Aliyu dan rainin wayo
ne kulle ki yyi a daki don ya isa," Zainab ta
dago kanta tana kallonta, kuka take, Anty
Nafeesa ta galla mata harara tace "ban san
shashanci kukan lfya" ita dae bata ce komai
ba ta gaida Anty Nafeesa, Zainab tace "meye
na kuka Inteesar" Anty Nafeesah tace maxa
tashi kije ki gyara fuskarki kiyi kwalliya kar
na bata maki rae ke dae baki gajiya da wnn
shegen kukan naki komai kuka komai kuka,
ita dai bata ce komai ba suka bar dakin
Aliyu Zainab ta kulle suka koma nata dakin,
sae da ta sake wanka snn Anty Nafeesa ta
sa ta gaba ta tsantsara kwalliyanta snn ta
fito mata da wata shaddarta dogon riga
maroon colour ta saka Nafeesa tayi mata
dauri mai kyau, Zainab tace"waw yan matan
yayanmu kin ga yanda kika xama kmr wata
balarabiya," inteesar ta galla mata hara, ba
karamin kyau tayi ba duk da ta rame ssae,
Anty Nafeesa tace "to akwae abinci ne a
gidan? Don ni yunwa nake ji," Inteesar tace
"sae da na girka maku," Anty Nafeesah tace
"to da dae yafi," ta ce "toAnty suna falo
kuma," Anty nafeesa tace "to ina ruwanki da
su ae don su ganki da kyau nake son kije
kiyi mana girkin," ta mike ta dauko mata
takalmikalan shaddar ta ajiye mata snn ta
feshe ta da turare tace "maxa sa ki tafi
indomie kawae xaki girka mana," Zainab
tayi dariya tana kallon Anty Nafeesa,
Inteesar kam murmushi tayi ta sa takalmin
gabanta na faduwa ta fita xuwa kitchen,
duk suna xaune falon har da safeena kusan
su goma banda wa inda ke ta jere a daki,
Inteesar bata ko kalle inda suke ba a nutse
cikin takunta mai jan hankali ta nufi kitchen
ta bude kofar kitchen din tana yatsine fuska
don duk sun dauki cups sun sha lemo da
shi, ta dan tabe baki ta shiga kitchen din,
duk kawayen safeena suka juya suna kallon
safeena da yanayinta ya sauya lkci daya
xuwa bacin rai tana kallon kofar kitchen din,
inteesar ta kunna gas ta daura ruwa snn ta
fito falon ta shiga kwala ma Zainab kira
cikin wani irin tsiga, da sauri Zainab ta
sauko tana cewa "na'am yan matan
yayanmu wnn kira hka," inteesar ta galla
mata harara da wasa tace "ban fa son
iskanci indomie nawa kike ga xae isheku,"
Zainab tace " wani irin tonan asiri ne wnn,
ko ma dae duka nace ae gidan yayana ne nn
bbu uban da ya isa ya hana," Inteesar tayi
dariya ssae tace "ikon Allah to shigo ki girka
maku kinsan dae ni ba daga nn ba ban gaji
rowa ba kuma duk yanda nace hka xa ayi a
gidan nn bare kice kina tsoran wataran ki
xo...," a fusace safeena ta mike tana nuna
Inteesar da yatsa tace "ke ki kama kanki kar
ki kaini bango don dukan tsiya xan maki
wllh wllh kuma sae dae mijikinki ya gode
min idan ya dawo," Zainab ta yo waje da ido
tace "wa xa a duka ni Zainb" Inteesar tayi
dariya tace"tambayan min ita don ni kaina
ban gane inda ta dosa ba," Safeena ta ciro
wayarta da sauri ta shiga kiran Aliyu, "Aliyu
Aliyu ka ja ma ballagaxar da ka ajiye a gida
kunni wllh ta fita harkata idan ba hka
bakafin na bar gidan nn yau sae na yi mata
kaca kaca, kuma wnn shegiyar kanwartaka
ita ma kaja mata kunne," Zainab tace "wllh
ni ba shegiya bace sae dae kece shegiya,"
Inteesar ta ja ta suka shiga kitchen suna
dariya, safeena tayi shiru tana sauraran
abinda Aliyu ke ce mata tana bubbuga kafa,
sun gama dafa indomien knn xasu wuce
samaAliyu ya shigo gidan, ba karamin
tsorata inteesar tayi ba tayi hanyar stairs ba
tare da ta kallesa ba, Zainab tace "ke kar ki
bada kanki mana ki tsaya ae Anty nafeesa
na nn," Aliyu na kallonta yace "ke xo nn," ta
galla masa harara tace "nayi maka me,"
karasowa kusa da ita yyi ta dake xuciyarta
na bugawa, duk yan falon suka xuba masu
na mujiya, ita kanta Zainab karfin hali tayi ta
tsaya, Safeena kosae taunar cingam take
tana jujjuya ido xuciyarta fal murna ita nn
kawayenta suka yanda ta isa da Aliyu, yana
isa kusa da inteesar ya kama hannunta ta
fixge tace "da'alla malam kyaleni," ya tsaya
kallonta da mamaki bae ce komai ba,ya juya
yana kallon Zainab yace "je dauko mata
mayafinta ko ki bata naki," Zanab ta cire
mayafinta ta mika ma Inteesar taki karba,
shi ya karba snn ya sureta kmr wata bby
suka fita daga gida
.
Inteesar ta tsorata ssae murya can kasa tace
"don Allah kayi hakuri ka saukeni wllh ita ce
ta fara,"Safeena kam binsu tayi da kallo da
mugun mamaki don tsabar mamaki kasa
rufe bakinta dake bude tayi, ita nn jira take
taga ya rufe ta da duka, Zainab kuwa dariya
tayi tace "kai irin wnn soyayya hka, ko me
Inteesar ke ma yayana hka oho," ta haura
sama tana ci gaba da dariya, bayan mota ya
jefata snn ya xaga ya shiga motar ya ja ta,
ita ko kallonsa kawae take gabanta na
faduwa ko ina xae kai ta, sun yitafiya ssae
snn taga yyi horn aka bude gate ya shiga yyi
parkin, ya bude mata kofa yace "fito kar na
mareki," ta fito tana kare ma wajen kalloduk
da tasan inda ya kawota don ta taba xuwa,
lallai ma Aliyu asibiti ya kawota, yyi gaba
tana biye da shi a baya kmr xata yi kuka,
nurses duksuka kama kansu ganinsa, suka
bi inteesar da kallo suna masu sannu da
xuwa, bae ko kallesuba sae ita ce ta
gaishesu ganin yanda suke kallonta, can last
flour office dinsa yake kusa dana aminin
dad dinsa don shine mai asibitin wato
dad din Sadeeq, ya bude office dinsa ya
shiga, ganin taki shigowa yasa ya fixgota, ta
shiga karema office din nasa kallo, ba
karamin haduwa yyi ba kmr ba office ba ita
fa bata taba gskata Aliyuna aiki ba duk da
tasan da sassafe yake barin gida ya dawo
late, ya shiga dakin da ke cikin office din ita
dae tana nn tsaye har ya fito bayan kmr
minti goma sanye da kayan surgery, green
colour yana kkrin sa hand gloves alamar
theatre xae shiga, ya galla mata harara yace
"kada Allah yasa ki xauna kuma idan lkcn
sllh yyi kar kiyi," snn ya fice, tayi tsaki kmr
xata yi kuka ta xauna kan kujera tana kare
ma office din kallo, ko minti goma ba ayi ba
da fitarsa wata nurse ta shigo rike da abinci
a rufe da lemo ta ajiye mata tace "sannu
madam," snn ta fita. Hka inteesar ta yi ta
xama kamar gantalalliya a office kmr tayi
kuka, abincin da aka kawo mata ma kin ci
tayi, ta gaji da xama ta kwanta kan gadon
da ake duba pregnant women tayi
kwanciyarta sae bacci, ko da ta farka taga
biyar ya kusa ita da ta kwanta tun kusan
daya da rabi, bata damu ba don dama bata
sllh, ta bude abinci daxu ta yatsine fuska ta
rufe, aka bude kofa wasu nurse biyu suka
shigo da jarirae har biyu suka yi ma inteesar
sannu, snn suka daura su kan gadon yara
dake office din daya ta kunna wani wuta
mai haske dae dae fuskarsu snn suka fita,
inteesar ta wara ido tana kallon yaran
kyawawa dasu, ta karasa kusa dasu da
mamaki tana kallonsu tace "yan biyu," a
hankali dayan ya shiga kuka yana tsotsan
hannunsa dayan ma ya karbe taji kmr ta
daukesu don tana bala'in son yara, ta rasa
yanda xata yi dukta rude ganinsu tayi can
tayi nn, aka bude kofar dakin Aliyu ya shigo
ta juya da sauri tace "ya Aliyu yan biyu ne?"
ya cire abun bakinsa yace "ehh" ba tare da
tasani ba tace "waw a ina kukasamo su" ya
karaso kusa da gadon yana kallonsu yace
"daxun aka cirosu daga cikin mamansu,
bata farfado ba har ynxu ma" inteesar ta
juya da sauri tana kallonsa kmr xata yi kuka
tace "theatre aka mata," xae yi magana daya
yaron ya tsala ihu tace "wayyo ya Aliyu in
daukeshi," ya harareta yace "basu da
lafiyasuma," tayi shiru tana kallonsu kmr
xata yi kuka.Ya dauki dayan a hankali ya
mika mata yana kallonta.
.
A hankali Inteesar ta sa hannu ta karbi bbyn
da yake mika mata tana murmushi, tace "ya
Aliyu ni ina son twins ssae" yana kallonta
yace "kina sonki haifi twins knn," da sauri
tana kallonsa tace "eh mana ina so," ganin
irin kallon da yake mata yana murmushi
yasa taji kunya ta kauda kanta da sauri, wae
Aliyu take ma wnn maganar? Ita bata ma
sani ba, ya matso dab da ita ya tsaya har
tana iya jiyo numfashinsa a bayanta ya rike
kugunta yace "wnn waist din naki xae iya
daukar twins?," ta bar wajen da sauri nn da
nn ta tsorata xae yi magana ta riga sa da
sauri tace "Yaya yunwa fa suke ji ko," bae ce
komai ba sae kallonta da yake, ta daga bbyn
xata yi kiss dinsa ya dakatar da ita da sauri,
snn ya karbe shi ya kwantar gefen dan
uwansa, tace "yaya baxa a basu abinci ba,"
yace "sae xuwa karfe sha biyu na dare," ta
wara ido tace "sbda me yunwa fa suke ji,"
yace "eh xa ayi ta basu ruwa" kmr xata yi
kuka tace "to waye xae dinga basu kace
mamarsu bata farfado ba," ya daka mata
tsawa "ke da'alla kar ki dame ni" yyi tsaki ya
shiga daki, ta bisa da kallo snn ta tabe baki
ta koma kujera ta xauna, wata nurse ta
shigo rike da mug a rufe tana kallon
Inteesar tace "doctor fa? Ya shigo?" a dari
dari take tambayar, Inteesar ta gyada mata
kai, nurse din ta ci gaba da tsayuwa har ya
fito sanye da kananan kaya, yana kallonta
yace "wathappen" tace "coffee sir," ya daka
mata tsawa "to kaina xaki daura ko me," ta
karasa kusa da table ta ajiye ta fita sum
sum. Ya bude abincin da aka kawo ma
inteesar yana kallonta yace "meyasa baki ci
ba," tayi kamr bata ji sa ba, ya rufe ya koma
kan table dinsa ya xauna kan kujera ya bude
coffeen ya shiga sha, hka yaran suka dinga
kuka Inteesar taji kmr ita ma tayi kukan, ta
kasa jure kukan nasu tace "yaya kuka fa
suke," ya kalleta yace "cnt yhu see they re
under medication," bata sake cewa komai
ba bayan kmr minti sha biyar ya kira nurses
su kashe wutan su fita da su, inteesar ta bi
su da kallo kmr xata bi su suna fita ta bata
rae ta juya tana kallon Aliyu taga kallonta
yake yana murmushi, ta dauke kanta da
sauri, karfe takwas da rabi suka bar asibitin
bayan ya kaita ta kara ganin yan biyun da
mamarsu, ya biya ta eatry ya siya masu
abinci snn suka kama hanyar gida, gidan ba
kowa duk sun watse sae kamshin turaren
wuta ke tashi, ta haura sama ta bar sa nn
falo shima ya bi ta a baya, spare key Aliyu ya
dauko ya bata na dakinta don su Anty
Nafeesa sun tafi da shi, dakin safeena ma a
kulle yake ta tabe baki, ta bude kofar
dakinta, ba shiri ta koma baya da sauri tana
kallon dakin da mamaki kadda cikin dakinta
aka yi ma safeena jere, ta juya tana kallon
Aliyu da ya fito daga dakinsa yana kallota
yace "Abba ne ya ba kansa wahala ya bata
kudinsa shi me 'ya," ya sauka kasa ya barta
nn, sababbin funitures masu rae da lfya
wanda suka fi na da ne a dakin nata, ashe
su Anty Nafisa abinda suka xo yi knn, ta
karasa cikin dakin a sanyaye, bbu abinda ba
a canxa ba a dakin. Tanaxaune gefen
gadonta bayan ta fito daga wanka ta sa
kayan bacci tayi jigum ta ma rasa abinda ke
damunta ya shigo dakin ya ajiye mata ledan
abinci ya fice. Ranar friday da yyi dai dai da
Ana gobe daurin auren Aliyu da safeena
ranar da kuma xa suyi dinner, Inteesar na
kwance a daki da rana duk ta rasa kanta
kmr wata mara lfya, rabonta da Aliyu tun
ranar da ya ajiye mata abinci ya fice sae dae
taji shigowarsa da fitarsa, Zainab da kursum
kadae ke xuwa debe mata kewa, taji an
bude kofar dakinta a xatonta su ne, Aliyu ya
shigo dakin ya xauna gefen gado yana
kallonta yace "mantawa nayi jiya bamu je
party da ke ba" bata ko kallesa ba bare ta
basa amsa, ya tabe baki ya ajiye mata dan
box karami irin na jewelries yace "tunda
kince ba kya son kaya ga wnn, don banso in
shiga hakkinki," ta juya tana kallon box din
ya bude mata, Zinari ne dan kunne da sarka
har da xobunaye biyu, tayi tsaki tace aikin
bnxa me xanyi da wnn gantalin kadae je ka
kara mata don wanda ubana ya sa min a
kayana ma ba damuwa nayi dasu ba bare
wnn, ku wnn ya dama" ya mike tsaye
fuskarsa daure yace "ni kike gaya ma
magana," ta fashe da kuka tace "an gaya
maka din wlh ka fitar min a daki," yyi
murmushi ya dauki box din ya fita daga
dakin, tasulale kasa tana kuka ssae da bata
san dalilinsa
.
ba, karfe bakwae suka shigo gidan da
abokanansa suka shirya suka wuce dinner.
Har
Aliyu ya shigo gidan karfe daya idon
Inteesar biyu,
ta kasa bacci, hka kawae ta samu kanta da
fashewa da kuka har da shessheka, har
kusan
karfe biyu tana xaune bbu alamar bacci a
tare da
ita, taji an tura kofan dakinta a hankali ta
juya da
sauri suka yi ido hudu da shi ta kauda kanta
da
sauri ta mike xata shiga bathroom yyi
hanxarin
rikota ta fashe masa da kuka ya rungumeta
.
Inteesar ta shiga turasa yaki sakinta, har
suka isa kan gado ya xaunar da ita shima ya
xauna yana kallonta ya dago kanta a hankali
yace "me ya hanaki bacci har ynxu," ta
dauke kanta har lkcn tana hawaye ta mike
xata bar wajen ya rikota, a hankali ta shiga
rera masa kuka ya rungumeta yace "ina son
jin kukan ki har wani ddi nake ji idan naga
kina kuka," ta turasa da karfi xata mike ya
rike ta gam yace "not until yhu tel me y yhu
re cryn," ta fashe masa da wani kukan abun
tausayi ya daga ta ya kwantar da ita kan
gadon ya kwanta gefenta ya rungumota
snn ya kashe wutan dakin, ajiyar xuciya
kawae take, a hankali yace "don xanyi aure
shine kike kuka," xata yi magana ya rufe
bakinta da sauri, yace "warce xata haifa
mana 'yan biyu xan auro, kinga sae kiyi ta
raino tunda kina son su," bata ce komai ba
ya daura bakinsa kan gashinta yana kissin
dinshi, a hankali ya kai hannunsa kan
cikinta yana shafawa kmr mae mata rada
yace "xaki iya na baki yan biyun ynxu?" a
tsorace ta rike hannunsa da sauri tace "A"a
wllh baxan iya ba," a hankali yace "plss,"
muryarta na rawa tace "No plsss" ita kam
1st nyt dinsu kawae take tunawa da irin
wahalar da tasha har da suma har abada
bata fatan ya sake kusantarta, ya kankameta
murya can kasa yace "to yi baccin ki," suna
nn a hka har bacci ya dauke ta, ranar dae a
hka suka kwana tana jikinsa kuma ranar ce
rana ta farko da ya kwana a dakinta,
washegari da yyi dae dae da ranar daurin
aurensu da safeena, da asuba ya kwantar
da ita a hankali ya shiga bathroom dinta yyi
alwala, ko da ya fito ya tarda ta xaune kan
gadon tayi tagumi, ta mike ba tare da ta
kalleshi ba ta shiga bayin ita ma tayi alwala
ta fito ta tar da shi yana jiranta, a tare suka
yi sllhn, rana ta farko knn da ta bude baki da
safe ta gaishesa ba tare da ta kallesa ba
yana murmushi ya gyada mata kai kawae, ta
mike xata bar dakin ya kamo hannunta yace
"ina xa ki," ta sunkuyar da kanta bata ce
masa komai ba, ya saketa ta fita, falo ta
sauka ta shiga mrnin duties dinta, ba ita ta
koma sama ba sae kusan karfe tara,ta tarda
shi kwance yana bacci, wanka ta shiga ta
fito ta gama shirinta ta fita daga dakin ta
koma downstairs, bata ba kanta wahalan
hada breakfst ba don bae taba cin girkinta
ba, tayi kwanciyarta a falon don neman
yunwa tayi ta rasa, karfe sha daya taji mai
gadi ya bude gate ta mike ta isa jikin kofa
taga ko waye ya shigo, motoci biyu ne suka
shigo gidan abokanansa kusan su biyar
suka fito, da yake kofar a bude yake
komawa kawae tayi ta kwanta, suka shigo
gidan da sallamarsu duk suna sanye da
fararen shaddodi, ta kara volume din Tv ta
mayar da hankalinta kan TV, tsokanarta
suka shiga yi suna dariya "uwar gida ke
kika rike ango har ynxu yaki fitowa kuma
kika sa ya kashe wayoyo ko to ayi hakuri a
sakar mana shi muje gun daurin aure," bbu
yabo bare fallasa tace "ku dae tambayesa
wanda ya rikesa," ta mike fuskarta a daure
ta haura sama ta bar su nn falo, a step duka
hadu da Aliyu ya galla mata harara, don me
baki tashe ni ba, ita ma ta galla masa
hararan tace "sbda baka isa ba," tayi gaba ta
bar sa nn tsaye, ya sauko suna ta
tsokanarsa wae tsoron uwargida yasa ya
makara, dole suka jirasa yyi wanka snn ya
fito shima sanye da farar shaddar, ba
karamin kyau yyi ba don ko hmm bari dae,
ya shiga dakin Inteesar tana xaune gaban
madubi, kallo daya tayi masa ta madubin ta
dauke kanta yace "kinyi break," tayi bnxa da
shi, ya daga kafada yace "sae na dawo kiyi
mani adduar Allah yasa ayi a sa'a," ya juya
xae bar dakin ta fashe da kuka ba tare da ta
shirya ba, ya juyo yana kallonta, ya karaso
cikin dakin yace "an maki wani abu ne ko
kawae jin ddin kukan ne ke damunki," bata
tanka sa ba, ya tabe baki ya juya ya fita, suka
fita gaba daya da abokan nasa suna masa
mitan ya bata lkci dayawa ko mantawa yyi
yau ce ranar daurin aurensa da sahibarsa
shi dae bae ce masu komai ba har suka
shiga mota suka bar gidan, suna fita daga
gate yace "kun san wani abu ku je kawae
gani nn xuwa, ina son na kai fateema can
gida daga can sae na wuce," namesake
dinsa yace "wae meye hka kke yi ita bata
san hanyar gidan ba sae an kaita baka
ganin saura yan mintoci," Aliyu yace "ni dae
kuje kawae ina nn xuwa, ya bude motar ya
koma cikin gidan," suka yi tsaki kusan gaba
dayansu suka yi gaba, yanda ya barta hka ya
dawo ya tarar da ita, ya dauki hijab dinta ya
mika mata yace "tashi to na kai ki gida,"
bata yi musu ba ta mike ta karbi hijab din
tasa takalminta suka fita, motarsa ya fito da
ta bude sit din baya ta shiga, bai ce mata
komai ba ya ja motar suka bar gidan, suna
isa gida bata jira ya gama parkin ba ta bude
mota ta fice, ya dakatar da ita da sauri ko
kallonsa bata yi ba ta shige gidan da gudu
sae sashin inna, hkn yyi mugun bata masa
rae kuma yasan da mutane cikin gidan shi
yasa bae bi ta ba, ya ja motar kawae yyi gun
daurin aure, mutanen dake tsakar gidan har
da su Hajiya suka bi ta da kallo murna fal
cikinsu, umma ko ta dinga tuntsira dariya
tana guda kawayen Hajiya na taya ta.
ta xube jikin inna ta fashe mata da kuka, a
rude
inna ta shiga tambayarta "meye faru, ke da
waye," ta kasa cewa komai, inna ma ta bare
baki
ta fashe da kukan, Anty Nafeesa ta fito daga
daki
da sauri tana kallon Inteesar tace "wa ya
kawoki,"
inteesar tayi kkrin tsayar da kukanta tace
"shi ya
kawo ni," Nafeesa tace "ynxu kuwa muke
shirin
tafiya can gidan, kukan meye hka kike yi, ke
dae
baki ji ddi ba wllh," a fusace cikin kuka inna
tace
"ban son iskanci ke uwar wa yyi maki
kishiya,"
inna ta mike ta daga inteesar tana share
hawayenta suka shiga daki tana cewa "ki
rabu da
shi, bbu abinda xaki koma gidan nn kiyi,
kuma
bbu uban da ya isa yace ki koma tunda nace
baxa ki ba, ina nn ina jiransa daga shi har
ubansa," Anty Nafeesa tayi murumushi ta bi
su
cikin dakin. Gida ya cika fal da yan uwan su
Hajiya da umma da abokanan arxiki ana ta
shagalin biki har da su Dj a gidan, inna na
daki
xaune gefen Inteesar da ta kwanta tana
bacci
tana mata fiffita ita ma tana gyan gyadi, jin
kide
kide yasa inna ta farka ta fito da gudu har
Anty
Nafeesa da wa inda ke falonta suka tsorata
suka
dinga tambayar lfya, ko kallonsu bata yi ba
ta fita
xuwa tsakar gida da gudu, Anty Nafeesa ta
ma
xaci abu ne ya sami Inteesar suka shiga
dakin da
sauri suka tarar baccinta take, wasu kuma
suka
bi inna da sauri a baya suna tambayar wae
Hajiya
mai ya faru, inna na isa tsakar gidan cikin
daga
murya tace "nashiga uku uban wa ya
gayyato wa
innan shaidanun gidan nn" ta fadi hkn a
fusace
tana nuna masu Dj da kayan kide kiden
nasu, aka
kashe wakar dake tashi, Umma tace "to
naga dae
yau ranar farin ciki ne inna kuma dae daga
yau ba
sake ganinsu xa ayi ba," inna tace "kin ci
ubanki
mai dattin hula, kaji min rubabbiyar
yarinya," ta
karasa kusa da masu dj tana huci ta shiga
bubbuga speakers din tana cewa "ku fitar
min
dasu kar na babbake su, gidan da na ba
gidan
yan iska da shaidanu bane" ba shiri Hajiya
tasa
aka shiga kwashe su a barrow ana fita
dasu, hka
ma canopies din duk sae da tasa suka fita
dasu
tana jaraba an cika gidan dan'ta da tarkace,
hka
mutane suka dinga kallon inna wasu na
dariya
can ciki ciki, "kuma duk shegen da ya xauna
kusa
da flawowin da na ban yafe masa ba duniya
da
lahira tunda dae ba shi ya dasa masa ba, ko
tsinke kuma kar a wurgar a tsakar gidan
nn," ta
fadi tana huci kmr kirjinta xae fashe, Hajiya
dae
shigewa daki tayi kunya kmr ta nutse, wae
juyawar da inna xata yi sae ganin momy tayi
xaune suna hada salad, ta saka salati kmr
xata yi
kuka tace "Allah ya wadaranki Zainabu, ynxu
uban me ya kawo ki cikinsu idan ba
shisshigi da
neman suna ba, ca suka yi maki yi suke
dake
mara xuciya kawae wahalalliya, ni dama
nasan
tun ba yau ba kika tsani yarinyar nn kike
son
ganin karshenta, idan ba hka ba taya xaki
kwaso
kafafuwa ki taho nn cikinsu, wllh daga yau
kar ki
sake nuna kin san Inteesar, ita ma bata
sanki ba
wllh, shi yasa ma da ta xo daxu bata nufi
inda
kike ba dan tasan ba sonta kike ba" ta
karashe
maganar da kuka ssae har da tari, ta bar
wajen
tana cewa "kuma yau bbu ubanda ya isa ya
bar
min tsakar gidan da' na hka, duk sae an
wanke
shi an goge wllh," dariya wasu har da
xubewa
kasa, ranar dae a dari dari su Hajiya suka yi
shagalin bikinsu, jefi jefi inna kan fito taga
ko an
xauna kusa da flowern da tace kar a xauna,
bbu
wanda yyi gigin xama kuwa. Da Magrib
bayan
kowa ya watse inna ta tasa su Hajiya gaba
sae
da suka wanke tsakar gidan su Zainab da
kursum
da Maryam din Anty Nafeesa dariya kmr
cikinsu
xae fashe, dama momy tun daxu ta shiga
ciki
amma sae da inna taje ta fito da ita wae har
da
ita yar bakin ciki maxa su gyara ma dan ta
tsakar
gidansa, sae da taga sun kusa gamawa snn
ta
koma sashinta tana cewa "wahalallun bnxa
kawae" karfe takwas abba yyi kiran Inteesar
falonsa, ta karasa falon a sanyaye tayi
sallama ta
shiga, Zaune ta tarda Aliyu a falon yana
sanye da
shadda brown colour, ta nemi gefe ta xauna
tana
kallon Abba tace "ina yini Abba," Abba ya
amsa
yana kallonta yace "ya gidan," ta sunkuyar
da kai
tace "lfya Abba," Abba ya nisa yace "ranar da
nace ku taho da Zainab don me kika ki bin
ta," ta
daga kai tana kallon Aliyu dake kallonta,
Abba ya
gyada kai yace "to yyi kyau, kuma har ynxu
baki
fara karatun ba ko?" a hankali tace "Abba na
kusan farawa," Abba yyi shiru yana kallonta
snn
yace "to Allah yasa, ki tashi ki bi mijinki, a
cigaba
da hakuri, Allah yyi maku albarka" Aliyu ya
mike
yana kallon Abba yace "nagode Abba," ko
kallonsa Abba bae yi ba, Inteesar ta yi shiru
kmr
xata yi kuka tace "Abba inna tace ba
ynxu......."
Abba ya hade rae yace "inna tace me, tashi
maxa
ki koma dakin ki, kuma bance ki shiga cikin
gida
ba," bata san tayi mugun ba Abba haushi
ranar
da ya aika Zainab kiranta taki xuwa ba, a
sanyaye Hawaye na kkrin sauko mata ta
mike
tace "Abba sae da safe," yace "Allah ya tashe
mu
lfya," Aliyu ma yyi masa sai da safe ya bi
bayanta
suka bar falon
.
.. Suna fita Aliyu ya kamo hannun Inteesar
da sauri ganin bata son jerawa da shi, ta
juya tana kallonsa yace "mu fara shiga na
gaida momynki," tayi masa mugun kallo tace
"ae ko baka fada ba dama momyta ce bance
taka ba," bai ce mata komai ba yana rike da
hannunta suka isa sashinsu, shi yyi sallama
ganin tsaya kawae tayi ta rike kugu, duk da
ita yaso tayi sallamar, Ihsaan ce ta amsa ya
shiga falon tana biye da shi a baya, suna
hada ido da momy ya kauda kai da sauri ya
nemi kujera ya xauna, ita ma ta xauna kusa
da ihsaan da ta kankameta, momy dae na
rike da assignment books din ihsaan, ba
tare da ya kalleta ba yace "ina yini," ita ma
tana neman page din da aka ba ihsaan bbu
yabo bbu fallasa tace "kalau," Inteesar ta
mike ta koma kusa da momynta tace
"assignment ku ke yi momy," momy ta
gyada mata kai, tace "bari nayi assistn dinta
momy," momy ta bar mata buk din, ihsaan
tace "Anty ae na iya," Inteesar tace "to xo
kiyi," ta mika mata buk din ta karba ta shiga
yi, momy ta mike ta shiga daki, inteesar ta
juya tana kallon Aliyu da ya bita da kallo, ko
kadan ba ta jin ddin yanda momy ke masu,
ta mike a sanyaye ta bi ta daki, shi kuma ya
dawo kusa da kanwartasa yana kallon
abinda take yi, tana ganinsa ta daina
rubutun, yana kallonta yace "y did yhu stop,"
tayi shiru taki cewa komai ya mike xae
koma inda yake taji tsoro ssae don ta xaton
dukanta xae yi, yyi murmushi yyi xamansa
yace "to na bar maki wajen," ta ci gaba da
abinda take, da Haisam ne jikinta na rawa
xata fada kansa, amma da yake shi ya koya
mata tsoransa shi yasa bae damu ba, to a
gidan nn ma waye baya tsoransa, yyi
murmushi tuno hka da yyi, yana nn xaune
har kusan karfe tara da rabi snn inteesar ta
fito bayan sun dan yi hira da momy, ta
xauna gefen kanwarta tana kallon abinda
take, murya can kasa yace "ki ce ma momy
xa mu tafi," ta mike ba tare da ta kallesa ba
ta shiga dakin, sae ga ta ta fito a sanyaye
tace "tace to," hkn ya sa ya gane baxata fito
ba knn, ya mike yana kallon ihsaan yace
"bby gud Nyt," ta kauda kanta bata ce komai
ba tana kallon inteesar kmr xata yi kuka tace
"Anty ni xan bi ki," Aliyu yace "je ki tambayi
momy to," ta shiga daki da gudu, sae ga ta
ta fito kmr xata yi kuka tace "tace a'a," yace
"je ki ce mata plss," ta koma da gudu sae ga
ta ta dawo da hawaye tace "tace xan je sch,"
yyi shiru yana kallonta snn yace "i promise
xan xo na dauke ki nxt wk kin ji, sae ki
dinga tafiya sch daga can," ta gyada masa
kai kawae ya ciro dubu biyar ya mika mata
tayi masa gdya snn ta daga masu hannu
suka fita daga falon Inteesar na murmushi,
da kansa ya bude mata gaban motar ta
shiga snn ya xaga ya bude driver sit ya ja
motar suka bar anguwar, bae ce mata ba
bata ce masa ba, suka yi nisa ssae snn taga
yyi parkin ya fita ta bi sa da kallo, tasan me
xae siyo ganin inda suka tsaya, ba a wani
dau lkci ba ya dawo rike da ledoji har biyu
ya bude motar ya shigo snn ya ja ta suka
bar gun suka kama hanyar gida, suna isa yyi
horn mai gadi ya bude ya shiga yyi parkin
snn ta bude motar ta fita shima ya fito ya
kulle motar ya bi bayanta suka shiga gidan,
kamshi ne mai ddi ke tashi a gidan, ta kalli
agogo taga karfe goma da kusan rabi ta
haura sama ta bude dakinta ta shige, ya dde
xaune falo snn ya mike shima ya haura
sama da ledojin a hannunsa yana kallon
kofar dakin safeena ya bude nasa dakin ya
shiga, ba a dau lkci ba ya fito sanye da
jallabiya ya bude kofar dakin safeenar ya
shiga, tana xauna sae taunar cingam take
tana kallo ta wurgar da mayafinta gefenta,
ya karaso yana kallonta yyi murmushi ya
ajiye ledar hannunsa yace "amarya bakya
laifi," ta galla masa mugun harara tace
"daga ina kke Aliyu xaka shanya ni nn, har
kawayena sun gaji da jira sun wuce," ya
xaune gefenta ya rungumota yana shafa
bayanta yace "Abbana ne ya bata min lkci
bbyna kiyi hkuri," ta dan marairaice kmr
xata yi kuka tana shafar fuskarsa tace "har
naji haushi wllh angona," yyi kissin din
goshinta yace "nasan kina jin yunwa bari na
kawo plate da cup na xuba maki chicken da
yogurt din da na siyo maki, tayi kissin din
lips dinsa tace "to mijina," snn ya mike ya
fita, dakin inteesar ya bude a hankali, tana
kwance kan gado ta tsura ma Ac ido, yana
kallonta yace "kinci abinci can gida ne," tayi
bnxa da shi ya karaso kusa da ita ya hade
rae "ba magana nake maki ba," nn ma taki
ce masa komai sae dae me, ya lura kuka
xata fara ta yanda tayi da fuska ya xauna
gefenta da sauri yace "wae ke wace irin
mutum ne da shegen kuka sae kace
marainiya," yyi tsaki ya ce "saura idan na
kawo maki abincin kar ki ci," snn ya fice, sae
da ya fara shiga kitchen ya dauko plate da
cups snn ya koma dakin safeenar, ita ma ta
fito daga bayi knn sanye da dogon hijab ta
xauna gefen gado, kaji uku ne taga ya ajiye
daya gefe da yogurt biyu, ta sauko tana
kallonsa tace "wnn fa dear," yana xuba mata
kajinta a plate yace "na warcan ce" ta
jingina jikinsa ta marairaice tace "xafi nake
ji bby," yace "to cire hijabin mana, a hankali
ta shiga cire hijabin tana masa wani
shu'umin kallo
.
Aliyu ya dauke kansa da sauri ganin wasu
shegun kayan baccin dake jikinta ya ci gaba
da abinda yake, har ya gama ya ajiye mata
nata snn ya dauki na Inteesar ya mike xae
fita ya kai mata, safeena da ta koma kan
gado ta xauna ta daura cinya daya kan daya
tayi yar kara ya juya da sauri yana kallonta
yace "me ya faru bbyna," kamr xata yi kuka
ta shiga nuna masa bayanta ya karasa kusa
da ita yana kallonta yace "me ya samu bayan
dear," cikin tsigar shagwaba tace "nima ban
sani ba," ya dafa ta ya dan duka yana duba
bayan da take nuna masa ta turasa da sauri
ya fada kan gado ya wara ido kan yace
komai ta fada kansa ta shiga yi masa wani
mahaukacin kiss tana shafa kirjinsa, turata
ya shiga yi yana cewa "wait wait bbyna bari
na kai mata abincinta stop it," ko kulasa
bata yi ba ta karbe ledan hannunsa ta ajiye
snn ta kashe wutan dakin ta shiga masa
wasu abubuwa masu rikitarwa da kashe jiki
nn da nn ya fara dauke wuta, shima ya
shiga biye mata, haukatasa ne kadae
safeena bata yi ba daren ranar don
sumbatu kawae ya dinga mata, kamar
yanda ta basa wahala hka shima ya wahalar
da ita, ta shiga rera masa kukan kissa, bae
sarara mata ba har sae da komai ya wakana
ta dde jikinsa tayi lamo har sae da ya dawo
nml snn ya turata gefe ya mike tsaye ya
kunna wutan dakin yana mata wani mugun
kallo yana huci, tana kwance kamar wata
macijiya a kan gadon, ya girgixa kansa ya
juya da sauri ya fice daga dakin ya shiga
nasa dakin yyi wanka snn ya sauko falo ya
kunna Ac duk da da sanyi garin yyi
kwanciyarsa kan doguwar sofa ya lumshe
idonsa xuciyarsa na harbawa da sauri ga
wani mugun takaici da ke masa yawo a kai,"
hkn yasa ya dafe kansa yana kiran Allah a
xuciyarsa, ya mike xaune ganin kwanciyar
baxae masa ba, ya harde hannuwansa yace
"Godforbid," ya kai minti talatin a hka a
xaune snn ya mike yana kallon agogo karfe
biyu da qtre yyi hanyar kitchen ya hado
coffee ya dawo ya xauna ya shanye snn yyi
kwanciyarsa, sae a snn bacci ya daukesa a
falon.
Da Asuba a bayin dake falo Aliyu yyi alwala
ya tafi
masallaci ya dawo yyi kwanciyarsa a falo,
ganin
bae jin komawa bacci yasa ya dauki remote
ya
kunna TV ya rage volume din yana kallon
tashar
Animaux, karfe bakwae yaji an bude kofa
can sama,
ya juya yana kallon stairs din daga
kafafuwanta da
yanda take tafiya ya gane ko wacece, ta
sauko kasa
tana sanye da rigar bacci iya gwiwa, tana
tafiyar nn
nata mai jan hankali, ita bata ma lura da shi
ba sae
da ta shigo falon, kallo daya tayi masa ta
dauke
kanta da sauri tayi hanyar kitchen ya bi ta
da kallo
har ta shige kitchen din snn ya sauke ajiyar
xuciya
ya ci gaba da kallonsa, aka bude kofa kuma
ya bi
stairs din da harara sanin ko waye, sae ko
ga
Safeena ta sauko tana mika da hamma
sanye da
kayan bacci iya cinya, nonuwanta rabi duk a
waje,
murya can kasa kmr mara lfya tace "shine
sbda ba
ka da imani Aliyu xaka tafi dakinka jiya ka
kwanta
bayan ka gama biyan bukatanka ka bar ni
da
wahala, wllh ban samu bacci ba jiya, bayan
hka
kuma gari na wayewa naji ka bude kofa ka
sauko
kasa ashe kwanciyarka ka xo kayi sbda
baka damu
da halin da ka sani ba ko," a tunaninta
budewar
kofar da taji na dakinsa ne bata san
Inteesar bace,
Aliyu ya mike a fusace yyi kanta ya shaketa
yana
huci yace "kika ce me?" ta xaro ido a tsorace
tace
"meye hka kke yi Aliyu," yana mata mugun
kallo ya
jinginar da ita jikin bango a nutse yace "ina
kika kai
Virginity dinki safeenah," ta hade rae tana
kallonsa
tace "kamr ya? Ban gane wnn tambayar
taka ba
Hydar, kana nufin ka kusance ni ne jiya don
kaci
xarafina, ko kai makaho ne baka gane ma
idonka
ba, ko so kke budurcin nawa ya fito yyi
maka
magana," daga ita har shi cikin natsuwa
suke
maganar don hka ba lallai bne wanda ke
sama yaji
me suka cewa sae dae mutum na
downstairs ne,
ya saketa yana mata wani irin kallo yace
"prove it
ynxun nn cewar ke Virgin ce," ta hararesa
tace "ok,"
snn ta haura sama, yyi murmushin takaici
sanin
abinda xata je ta dauko masa ya bi ta da
kallo
xuciyarsa na tafarfasa, sae ko ga ta ta fito
rike da
xanin gadon jiya da ya bace da jini ta jefa
masa
gabansa tana masa mugun kallo, ya daga
xanin
gadon yana kallo, snn ya jefa mata a fuska
yace
"kin yaudari ubanki," ta wara ido ta dafe
kirji tace
"ubana fa kace Aliyu," yace "shi fa, ni xaki
yaudara
da fake Hymen, me kika maidani safeena kin
manta
ko wanene ni? Kin ci darajar ina sonki da
bbu
abinda xae hanani baki takardarki yau, ni ba
maxinaci bane don hka Allah ne kawae ya
kaddaro
min aurenki," tayi shiru gabanta na faduwa
kmr
kirjinta xae fito tana kallonsa, dae dae nn
Inteesar
ta fito daga kitchen rike da cup din tea,
safeena ta
juya da mugun mamaki tana kallonta, tana
wani irin
taku mai jan hankali ta xo ta wuce su tana
ma
Safeenar wani mugun kallon wlknci tana
murmushi,
Safeena taji kmr kasa ya bude ta shige, lallai
Aliyu
ya tona mata asiri idan har dae yarinyar nn
taji
abinda suke cewa, sbda tsabar iskancin
dake cin
Inteesar bata ma san ta isa bakin stairs ba
ta kusan
faduwa ta rike karfen da sauri kofin
hannunta ya
fadi ya fashe ruwan tean ya malale kan tiles
din
falon ta fasa ihu tana cewa "wayyoo xafiii,",
da sauri
Aliyu ya karaso wajen ya dauke ta ya koma
baya
yana kallonta yace "ke makauniyace," ta
marairaice
kmr xata yi kuka tace "to ban sani ba, ido ne
yyi
min yawa," ya ajiye ta kasa ta ce "wayyo xafi
kafar
ke min," ya daga ta yana kallon kafar sae
yarfe
hannu take, yyi tsaki ya dauketa ya haura
stairs din
suka bar Safeena nn a tsaye, kallon safeenar
take
yana rike da ita tana murmushi, suna kaiwa
karshen
stairs tayi mata wani kallon bnxa tana kallon
xanin
gadon dake gabanta a yashe, Safeena taji
kmr taji a
mafarki ne hkn ke faruwa, hawaye ya cika
idonta
tana huci ta shiga kiran layin uwarta, bugu
biyu ta
daga cikin muryar kuka tace "momy mun
bata kudin
mu ne kawae a bnxa ya gane ni ba
budurwa bace,
ya ci xarafina momy ya walakanta na gaban
yar
iskar yarinyar nn duk taji cin mutuncin da
yake
min," a rude uwar tace "kashe kashe kar su
jiki,
xan kira ki anjima" ta katse wayan tana
kukan
takaici, kai amma Aliyu bashi da mutunci ko
kadan,
Aliyu na shiga dakinsa rike da Inteesar ya
kwantar
da ita kan gado yana duba kafar nata ko
kwalba ne
ya shiga, ganin yana ta ba kansa wahala
yasa a
hankali tace "ni ba komai a kafata," ya daga
kai
fuskarsa daure yana kallonta ya mike tsaye
yace
"fita ki ban waje," ta hararesa ta mike ta bi
ta
gabansa ya bi ta da kallo har ta fice daga
dakin, a
corrido taga safeena na kkrin shiga dakinta
ta fashe
da dariya ba tare da ta shirya ba har da
faduwa
.
... Safeena tayi kanta a fusace tana huci, da
gudu ta sake komawa hanyar dakin Aliyu ta
kwala ihu, ya fito da sauri yana kallonta yace
"me ya faru," kmr xata yi kuka tana nuna
safeena tace "ba ita bace ba," ya juya yana
kallon safeenar fuskarsa a daure yace "tayi
maki me?" Inteesar tana kallonsa tace "wae
ta wani yo kaina kmr wata lioness xata
dokeni sae kace uwata," ta karasa maganar
tana hararan safeena, yana kallonsa
safeenar yace "to ki doketa tunda yar ki ce,"
Inteesar tayi tsaki ta wuce su ta bude
dakinta ta shige tana xaro mata ido, safeena
taji kmr a mafarki hkn ke faruwa ta kasa
cewa komai sae kallon Aliyu da take, shima
yyi tsaki ya koma dakinsa ya bar ta nn tsaye.
Inteesar na daki bayan tayi wanka ta shirya
cikin wani less mara nauyi mai shegen kyau
an mata riga da skirt lafiyayye, kwance take
tana game da wayar Aliyu, taji ya buga kofar
dakinta ta dago kai tana kallonsa yace
"uwar wa xae gyara maki falon da kika yi
litter da tea da kwalabe," ta xumburo baki ta
ci gaba da game dinta, yace "ba magana
nake maki ba," ta mike tsaye fuskarta daure
ta bi ta gefensa ta fice ya bita da kallo, ya
sauke ajiyar xuciya, tana sauka ta shiga
kitchen ta fito da mop da bokiti da tsintsiya
da parker ta rasa ta inda xata fara gyaran
ga shegen tean shima ya malale har cikin
falon, ya sauko yana kallonta yace "ohh
tsayuwa kika ma yi knn," kmr xata yi kuka
tace "to ni ban san yanda xanyi ba" ya tsaya
kallonta, ta karyar da kai ita ma tana
kallonsa, sae abun ya kusan basa dariya, yyi
kwafa ya karbe broom din daga hannunta
ya duka ya fara tattara broken mugs din,
tana tsaye tana kallonsa, ya dago yana
kallonta yace miko min abun kwashe sharan
kmr xata yi kuka tace "baka ga kwalba a
wajen ba xan taka," ya tsaya kallonta ya
kasa cewa komai, dae dae nn Safeena ta
sauko da dogon hijabinta xa ta kitchen
hado tea ganin yunwa na neman hallaka ta,
yace "miko min abun kwashe dirt din can
Safeena," bata yi masu ba ta dauka ta mika
masa jikinta na rawa, a tare ta taimaka
masa suka gyara falon Inteesar na tsaye
tana kallonsu, safeena na goge falon ya
daka ma Inteesar tsawa yace "get out kar
na mareki, meye amfanin ki a nn" ta ja
dogon tsaki ta haura sama daga shi har
safeenar suka bi ta da kallo, yyi kwafa
kawae, da daddare ya hadasu a falo xae yi
masu magana, Inteesar dae nata kallonta
abunta, yana kallon safeena yace "kina ji na
Safeena," safeena da ta xama kmr marainiya
ko kuma nace ta kirki tun daga jiya, kanta a
duke tace "ina jinka," ya kalli Inteesar da ta
bar kallonta tana hararanta, yace "kema kina
jina," ta yi bnxa da shi ta ci gaba da kallonta,
ba karamin daure ma safeena kae abinda
Inteesar ke yi yyi ba, lallai xata yi maganin
shegiyar nn nn ba da ddewa ba, Aliyu bae
damu da bnxan da inteesar tayi masa ba
yace "ke kika xo kika sameta a gidan nn
safeena don hka ki sani gaba take da ke a
gidan nn, bana son wani tashin hankali a
gidana ku kame kanku, kar wanda yyi kishi
kaina ban aikesa ba, kowa tasa ta
fishshesa," ya juya kan Inteesar "ke kuma
fitsararriya ki rike fitsararki, ki sani safeena
ta girmeki nesa ba kusa ba, ke din yaushe
kika balaga ma kika san me duniya ke ciki,
yarinya dake sae shegen rashin kunya ki
tambayeta shekararta nawa ta fada maki
kiji, u had beta respect ur self coz she's nt
ur mate, snn girki as frm nxt wk duk every
2dayz xaku ke yi, bana son tashin hankali a
gidana i repeat my self kuyi respectn kanku"
Inteesar ta mike tsaye tana gyara daurin
dankwalinta ta ja dogon tsaki tace "sannu
balagaggu, kuma ba girmata ba har haifata
Safeena tayi," tayi masu kallon bnxa xata
haura sama ya bita da sauri ta saka gudu
amma duk da hka sae da ya kamota ya
shaketa yace "uban waye sa'anki a nn," ta
fashe da kuka tana kiran Abbanta ya jefar
da ita kan kujera yana kallon safeena yace
"in ta maki ki gyara mata xama ni na sa ki,"
xata mike daga kan kujerar yace "in kika
tashi sae na watsa maki mari," ganin bbu
wasa a tattare da shi yasa ta koma tana
kuka, yana kallon Safeena yace "kije ki shirya
mu siyo abinda kika ce," murna fal cikinta
ganin abinda aka ma Inteesar tace "ni a
shirye nake," ya ciro makullin motarsa, ta
mike ta bi bayansa suka fice daga gidan
tana ma Inteesar wani irin kallo tana jujjuya
ido. Basu dawo gidan ba sae kusan karfe
sha biyu, inteesar na kwance bayan ta gama
cin kukanta har lkcn bata yi bacci ba, muryar
safeena taji tana cewa "bby ka bari mu
shiga ciki mana don Allah ka bari," cikin
kissa take maganar, Inteesar ta mike ba tare
da ta shirya ba kuma bata san dalili ba ta
shige bathroom ta kulle
.
Yau safeenah ta cika sati uku gidan Aliyu ko
sau daya kallon kirki bae taba hadata da
Inteesar da ta xame mata jaraba a gidan ba,
gashi ba dama tayi mata ko da kwakkwaran
kallon bnxa Aliyu ya hau ta da bala'i don
yace mata baya so, ta kyaleta kawae
yarinyace kuma yarinta ke damunta, bbu
yanda Safeena ta iya don tana mugun son
Aliyu kmr rayuwarta duk abinda Inteesar
tayi mata sae dae ta gaya masa, wani lkcn ya
shareta wani lkcn kuma ya samu Inteesar
din ya tsoratata ko kuma ya sa ta kuka,
shima ta lura ba a son ransa yake yin hkn
ba, ko sau daya Inteesar bata taba shiga
kitchen tayi masu girki a gidan ba ko da
kuwa ranar girkinta ne sae dae Safeena tayi
a bisa umarnin da Aliyu ya bata, don ca yyi
ta rabu da ita kawae ta dinga girki kullum,
littafin girki kadae ne ke taimakonta don
bbu abinda ta iya da ya wuce tafasa ruwan
xafi, cikin ikon Allah kuwa idan tayi sae ya
dan yi ddi da taimakon littafin, ta adana
littafinta ssae, iyaka idan ta fito inteesar ta
shiga ta dafa indominta ko taliya, ganin
rashin amfaninta a gidan yasa Aliyu ya kai ta
da kansa tayi registratn din jamb ana saura
sati daya a rufe, kila idan ta fara xuwa
makaranta xae samu kwanciyar hankali don
bata tsinanasu da komai sae tashin hnkli a
gidan, wani lkcn yakan yi mamakin ashe
yarinyar nn na da baki hka, kuma
fitsarewarta lkci daya da rashin tsoran
kirkin da take masa yana mugun basa
mamaki shi dae ba wasa da ita yake bare
yace kuma tunda ya auri safeena bae
nemeta ba, gaba daya ta daina tsoransa sae
taga yyi kanta xae doketa ta marairaice
masa tana kuka, gashi abu kadan sae ta
bara masa baki ta fasa masa ihu a gida ba
gaira ba dalili, shi kuma yana kyaleta ne
kawae sbda Abbansa don ko kadan
Inteesar bata gabansa don bbu abinda
Safeena ta rage shi da barin a wajen
kwanciya shi yasa yake ji da ita, duk da
yakan yi murmushi idan ya tuna 1st nyt
dinsu da Inteesar, da yanayin da ya shiga da
har yau bae ji hkn gun Safeena ba, darajar
da Inteesar ke ci kadae a gunsa knn banda
hka da bata isa ta taka masa matarsa da
yake ji da ba, Safeena kanta na mamakin
yanda Aliyu ke share Inteesar duk da
iskancin da take xuba masa, ita bbu abinda
yafi daga mata hankali ma irin mugun
rainata da Inteesar tayi, amma tasan duk
Aliyu ne ya ja mata tunda ga irin tonan
asirin da yyi mata washegarin ranar da aka
kawo ta gidan, wani lkcn takan yi murmshin
takaici tace nasan tanadin da nayi maki
yarinya kiyi yanda kike so lkcn ki ne ynxu.
Ranar da ya kaita tayi registratn din jamb
can ya barota ya bata kudin mota ya wuce
office, bata bari adai daita sahun ya shigo
da ita layinsu ba ta sauka ta basa kudin don
yau tana son ta kare ma anguwar kallo
tunda dae ba fita take ba, tana isa bakin
gate dinsu taga wata yarinya da baxata
wuce ta ba rike da wani kyakkyawan yaro a
hannunta tana waya, Inteesar ta dauke
kanta ganin sun hada ido, yarinyar tace
"sannu fa," inteesar tace "yauwa, ngdd," ta
danna bell mai gadi ya bude mata ta shiga,
taji yarinyar ta burgeta yar kyakkyawa da
ita, safeena na kwance a falo da kawayenta
ta wucesu tana yatsine fuska ta haura sama,
bayan kwana biyu Aliyu ya hadata da driver
taje ganin centre dinta, tana dawowa ta
sake haduwa da yarinyar a bakin titi ita ma
xata karasa layin da kafa tana rike da danta,
bayan sun gaisa Yarinyar tace "amma aure
kike a gdan nn ko," Inteesar tayi murmushi
tace "eh," yarinayr tace "to ya sunanki,"
inteesar ta gaya mata yarinyar tace "ni kuma
sunana Aneesah," Inteesar tayi murmushi
tace "to yaron ki fa," yarinyar tace "sunansa
Abdush-shakur," Inteesar ta karbi yaron
tana murmushi tace "fyn shakur," har suka
isa dai dae gidajensu, yarinyar tace "kina da
kyau ssae, ina son mu xama kawaye,"
inteesar tayi dariya tace "to ai kema kina da
kyau," Aneesah ta bata wayanta tace "sa
min nmbrki to inteesar," Inteesar tace "wllh
wayan mijina ne a hannu na ki bari idan na
samu waya," Aneesah tace "to mu shiga
kiga gidana mana" inteesar ta xaro ido tace
"mai gidanki baya nn," Aneesah tace "A'a a
Abuja yake aiki sae wkend yake dawo wa,"
inteesar ta bi ta suka shiga gidanta, gidane
babba kmr nasu bbu abinda ya xama
bakonta a gidan don duk suna da shi a
nasu gidan, har bedroom ta shiga da
Inteesar, inteesar ta shantake suka dinga
hira kmr da can sun san juna, ta girka masu
abinci ta kawo masu dakin suka ci suna ta
hira tana ba Inteesar labarae kala kala,
Inteesar taji kmr kar ta bar gidan, karfe
shidda saura ta rako Inteesar har bakin
gate kmr kar su rabu, har shakur ya saba da
Inteesar don har da kukansa, wae sae da ta
isa jikin gate tukunna gabanta ya shiga
faduwa a xuciyarta tace "Allah yasa ya Aliyu
bae dawo ba," mai gadi ya bude mata gate
ta shiga taga motarsa a parke a garage
xuciyarta yyi mugun bugawa da kyar tana
jan kafa ta shiga gidan.
Bata tarda kowa cikin falon ba tayi sum sum ta
haye
sama ta bude kofar dakinta a hankali ta
shige,
xama tayi kan gado ta sauke ajiyar xuciya,
jin an
fara kiraye kirayen sllh Mahgrib yasa ta mike
ta
tashiga cire kayan jikinta xata dauki xani ta
daura ta shiga wanka don bata sllh taji an
bude
kofar dakinta, ta tsorata ssae tace "wayyoo
Abbana," ta durkushe da sauri tana kare
kirjinta
da hannunta don undies kadae ne jikinta, ya
karaso cikin dakin yana kallonta yace "daga
ina
kike," taki cewa komai kuma taki dago
kanta
tana durkushe inda take, ya karasa gabanta
ya
dago ta ta shiga nonnokewa a tsorace tace
"wayyo ya Aliyu ban sa kaya ba," ko kulata
bae
yi ba ya jinginar da ita jikin bango yana
mata
wani irin kallo nn da nn yanayinsa ya canxa,
duk
ta tsure tana son durkusawa yaki barinta ta
fashe masa da kuka, ya sauke ajiyar xuciya
ya
sake ta ya fice daga dakin ta tajawo xaninta
da
sauri ta shiga wanka, tana fitowa ta gama
shafe
shafenta ta saka kayan baccinta, ta saka
gashinta cikin net ta fita dafa indominta,
xaune
ta tarda Aliyu a falo safeena na jingine
jikinsa
suna kallo, ya bi ta da kallo har ta wuce su
tana
tabe baki ta isa kusa da fridge ta dauki five
alive ta bude ta sha ta rufe ta mayar da
sauran
don bbu mai shan five alive a gidan sae ita,
ta
juya ta watsa masu harara ta shige kitchen
yin
abinda ya sauko da ita ya mike da sauri
safeena
na tambayarsa inda xa sa bae kulata ba ya
haura sama ya shiga dakinsa bae dau lkci
ba ya
fito rike da kwayoyi har uku a hannunsa,
bae
bari safeena ta lura da komai ba ya shiga
kitchen Inteesar na duke cikinta ya hanata
sakat, ta mike da sauri ta koma baya a
tsorace,
bae ko kalleta ba ya dauki cup ya fice, ta dan
yi
tsaki ta bude tukunyar indomienta tana
dubawa, yana fita falo yyi hanyar fridge
safeena
sae binsa take da kallo, ya juya mata baya ya
ciro drink din five alive din da inteesar ta
bude
ta sha ya xuba kwayoyin a ciki ya rufe ya
mayar
ya ajiye snn ya fito da hollandia yogurt ya
xuba
a cup din da ya dauko a kitchen ya rufe ya
mayar da sauran a fridge snn ya dawo falo
ya
xauna gefen safeena yana shan hollandia
yoghurt dinsa, Safeena tace "ae da kayi
magana
na kawo maka shine ka ba kanka wahala,"
yace
"bana son ki ba kanki wahala ne," bata sake
cewa komai ba ta kwanta jikinsa tana shafa
shi,
shi dae idonsa na kan Tv ganin irin abinda
take
masa yasa ya hade rae yace "stop it am nt in
d
mood," tayi shiru bata ce komai ba amma
bata
ji ddin hkn ba don tana jin ddin Aliyu ya iya
sa
mace ta manta hanyar gidansu gashi yau a
matse take, Inteesar ta fito daga kitchen
rike da
plate din indomienta ya juya yana kallonta
har
ta isa kusa da fridge ta bude ta ciro Five
alive
dinta a xuciyarta tana cewa ni da cikina ma
ke
ciwo, ta dan tabe baki ta rufe fridge din,
juyawar da xata yi suka hada ido da Aliyu ya
kauda kansa da sauri ta tabe baki ta haura
sama, ya sauke ajiyar xuciya har safeena na
tambayarsa lfya, bae tanka mata ba yana ta
kallonsa har kusan karfe sha daya snn ya
mike
yana kallonta yace "xanje in kwanta sae da
safe," ya haura sama ya bar ta nn xaune,
tasan
tunda bae nemeta ba yau idan ta kai kanta
walakanta ta xae yi, don hka sum sum ta
mike
ranta bae so hkn ba don tana bukatansa
yau ta
shige dakinta ranta a bace. Shi kam yana
haurawa sama dakinsa ya shiga ya hada
coffee
yasha don shi mayen coffee ne, snn yyi
wanka
ya canxa xuwa nyt wears dinsa ya bude
kofar
dakinsa yyi hanyar dakin Inteesar, xaune ya
tarda ta a dakin ta jinginar da kanta jikin
gado
idonta a lumshe, ya karasa gabanta ya
durkusa
yana kallonta, ta bude idonta da ya kada yyi
jajur a hankali tana kallonsa.
.
Aliyu yyi murmushi yana kallon cikin idonta
ya daura goshinsa kan nata har tana iya jiyo
numfashinsa a fuskarta ta lumshe idonta ya
dagota ya xaunar da ita kan gado ya dago
kanta yana kallonta, a hankali kmr mai rada
yace "kina bukatan wani abu ne," kin cewa
komai tayi ta koma can tsakiyar gado xata
kwanta, bae hanata ba ya barta tayi
kwanciyarta snn ya dawo gefenta yana
shafa fuskarta yace "to yau baki tsorona"
idonta lumshe bata ce komai ba ya dagota
ya rungumeta ya shiga kissn din wuyanta
yana shafata, da kyar ta turasa muryar ta
can kasa tace "ka bari," shima murya can
kasa yace "shkkn tunda ba kya so," ya sake
ta ya mike ta rikosa da sauri ta fashe masa
da kuka, ya rungumeta cikin rada yace "to
duk me nayi maki kiyi mani ke ma," xata yi
magana ya daura bakinsa kan nata a
hankali yace "kiss me," ta lumshe idonta ta
shiga kissn dinsa, he could'nt belive it, ya
kankameta, ta dauke bakinta daga nasa
tana mayar da numfashi kmr xata yi kuka, a
hankali ya shiga cire mata kayan baccin
jikinta yana kissn dinta, ya shiga romancin
dinta kmr xae hadiyeta ita ma lkci lkci takan
mayar masa da martani ganin yana neman
xautar da ita gaba daya yasa ta kankamesa
tana mayar da numfashi tace "plsss" bae
tanka ta ba har sae da yaga ta fara kuka snn
ya shiga rabata da sauran kayan jikinta,
turata yyi ba tare da ya shirya ba, ya fada
gefen gado yyi rub da ciki yana mayar da
numfashi ta fada kansa tace "no, plss ya
Aliyu," duk ta xama kmr wata mara hankali,
da kyar ya dago ya rungumota murya can
kasa yace "u re nt clean," ta rikesa tana
girgixa masa kai tana hawaye ta kasa cewa
komai sae mayar da numfashi da take, ya
mike da kyar ya fice daga dakin, ta fada kan
gado tana kuka a hankali tunda take bata
taba shiga irin yanayin da ta shiga ranan ba,
ta ma rasa meke damunta kawae, wnn
abun dae da take mugun tsoro yau taji take
mugun bukata kmr xata yi hauka, ta rasa
inda xata sa ranta, ta dukunkune waje daya
kmr mai jin sanyi, Aliyu ya bude dakin ya
shigo ya karasa kusa da gadon rike da kofi
a hannunsa ya dago ta, ta fada kansa tana
kuka tace "don Allah ya Aliyu," ya kai mata
kofin baki ta dauke kanta da sauri yace
"magani ne" ta maida kanta jikinta na rawa
ta shiga shan abinda ke kofi, ruwan lime ne,
sae da ya tabbatar ta shanye snn ya
kwantar da ita ya lulluba mata bargo ta
xama kmr wata mara lfya, yaji tausayinta
ssae gashi har uku ya xuba mata, da kyar ta
samu bacci ya dauketa, snn ya mike ya
dauki juice din ya shiga bathroom ya xubar
ya fice daga dakin, dakin Safeena ya shiga
ya biya bukatansa. Da safe tana wanka ya
shigo dakin, ta kasa fitowa daga bathroom
din duk da ta gama wani mugun kunyarsa
take ji, to wae jiya wani jaraban ne ya
sameta ita kam, tunda take bata taba
experiance din abinda taji jiya ba, ya gaji da
xamansa a dakin ya fice duk da yasan ta
gama wankan fitowa ne kadae baxata yi ba
gashi ta sa key, yana fita ta fito da sauri ta
kulle dakinta da key, tana shiryawa gaban
madubi taji muryarsa da safeena can kasa,
ta mike da sauri ta bude curtain din
window tana kallonsu, tana sanye da wasu
shegun matsatsun kaya, ya bude mata mota
ta shiga ya xaga shima ya shiga snn ya ja
motar suka bar gidan, ta sake labulen ta
koma gaban madubinta amma ta samu
kanta da kasa yin komai kuma, ta mike ta
koma kan gado tayi kwanciyarta tare da
lumshe ido, har rana basu dawo ba, hkn
yasa ta mike ta dauki Hijab dinta tasa snn ta
sa takalminta ta fice daga gidan, mai gadi
yace "ina xa ki," tace "bae gaya maka inda
da exams yau ba," ya bude mata gate din ta
fice tayi gidan Aneesah.
.
Aneesah tayi farin cikin ganinta ssae ta kai
ta har bedroom ranar ma , snn ta kawo
mata lemo, Aneesah tace "to ni yaushe kike
son na shigo gidan ki kawas," Inteesar ta
tabe baki tace "ae ni ba ni kadae bace, ni da
kishiyata ce," Aneesah ta yo waje da ido
tace "da gske, ke ce ta farko ko ta biyu,"
Inteesar tace "ta farko," Aneesah ta bude
baki tace "shekaranku nawa da auren? Ko
don baki haihu bne har ynxu," Inteesar tayi
murmushi tace "watanmu biyar knn da
aure," Aneesah ta dafata da mamaki tace
"kai Inteesar, to dama ba auren soyayya
kuka yi bne ko kuwa kinsan ba ke kadai
bace," Inteesar tace "kusan auren xumunci
aka mana, baya sona bana sonsa," Aneesah
tayi shiru tana kallonta snn ta sauke ajiyar
xuciya tace "ke xaki koya masa sonki
Inteesar namiji fa wawa ne cikin lkci kalilan
xaki ga kin mallake abunki sae kace ba
mace ba Inteesar," Inteesar ta tabe baki tace
"tabdi me xanyi da shi, hanyar jirgi daban ta
mota daban, baya shiga harkata bana shiga
tasa," Aneesah tace "to amma kuna plannin
ne ko," Inteesar tace "kinga ni ki rabu dani
da hirar nn, ina shakur?" ba don ran
Aneesah ya so ba suka bar xancen suka
kama wani hirar, ranar ma a gidan ta ci
abincin rana, bata bar gidan ba sae kusan
karfe shidda ta shiga ta tarar sun dawo,
safeena na kitchen da dan littafinta da take
boyewa tana hada masu girki shi kuma
yana xaune falo yana kallo, ta hade rae xata
wuce sama ya daka mata wani mugun
tsawa da ya raxanata ta tsaya daga inda
take tana masa mugun kallo ya mike ya
karasa kusa da ita fuskarsa daure yace
"daga gidan ubanwa kike," ta tabe baki tace
"aikena kayi to," bata rufe baki ba ya watsa
mata mari ta fasa ihu ta durkushe wajen
tana kiran Abba, safeena ta leko tace "haba
cweety nace ka rabu da ita yarinya ce bata
san ciwon kanta ba tukun yarinta na
damunta, meye kuma na dukanta, nasiha ya
kamata kayi mata dear," Inteesar ta mike
tana kuka tace "don uwarki sae ki xo kiyi
min nasihar munafuka kawae jaka" yyi
kanta ta fasa wani ihun ta saka gudu ta bar
wajen ta haura sama tana ci gaba da rusa
kuka kmr xata tsaga gidan, ranar hka taci
kukanta ta koshi bbu mai lallashi ta gaji ta
kwanta tayi bacci ba tare da ta ci abincin
dare ba, karfe goma ya shiga dakin nata, ko
wanka bata yi ba bare ta canxa kayanta
karewarta ma kasa tayi kwanciyarta, ya
daga ta ya cire hijabin jikinta snn ya mayar
da ita kan gado yana kallon fuskarta, ya
lulluba mata bargo ya kashe mata wutan
dakin ya fita. Washegari kin fitowa tayi daga
dakinta tana ta xaune har axahar bata karya
ba, ya shigo dakin ya tarar da ita xaune kan
darduma ta idar da sllh, ta mike ta shige
bathroom ta bar sa nn tsaye, yyi tsaki ya fice
daga dakin, ranar ma hka suka fita suka
barta ita kadae a gidan, taci kukanta ta fito
ganin yunwa na neman hallakata ta nemi
abinda xata ci, har da na dare ta tanada don
ba fitowa xata sake yi ba, Ana gobe xata je
ta xana jamb dinta tun safe take ta karatu
har kusan sha biyu bata karya ba, ta rufe
biology text book din dake hannunta ta fito
xuwa falo don neman abinda xata ci a
xuciyarta tana cewa inda wnn mutumin
kirki ne da ba shi xae koya min abubuwan
da na manta a chemistry ba, tayi tsaki ta
shiga kitchen ta tarar safeena ta daura girki
amma bata kitchen din littafin da take
amfani da tana koyan girki na kitchen din a
ajiye da alamar tuwon shinkafa da miyar
egusi xata yi ganin irin kayan miyan da aka
jera a kitchen din ko wanne a cikin dan
plate, inteesar ta girgixa kai tace "dakikiya
kawae ynxu ina dauke littafin nn bbu
abinda xata iya yi a nn," xata daura indomie
kawae wata xuciyar tace ta dauke littafin
kawae ta boye, ba shiri ta dauke littafin ta
ma fasa girkin gaba daya ta fice da sauri ta
haura sama a stairs suka hadu da safeena,
safeena tayi mata wani kallon banxa tana
karairaya, inteesar tayi dariya can ciki ciki a
xuciyarta tace "i jez dey laf," ta shige
dakinta, safeena na shiga kitchen ta nemi
littafi ta rasa ta fito da sauri ta koma sama
ta buga kofar dakin inteesar, inteesar ta fito
tana gyara daurin dankwalinta a walakance
tace "lafiya," safeena tayi mata mugun kallo
tace "maxa fito min da kayana kar na
nakada maki shegen duka a nn," inteesar
tayi dariya tace "meye kuma kayanki,"
safeena na huci ta kasa cewa komai don
wnn ae abun kunya ne a gunta anata
tunanin, inteesar tayi tsaki tana yatsine
fuska xata rufe kofar safeena ta fixgota ta
kai mata mari, ta fasa ihu tace "wayyoo
Abbana, wlh sae na rama," safeena ta kai
mata wani marin, inteesar ta fasa wani
kukan tace "don uwarki me nayi maki xaki
dokeni, bnxa kawae dakikiya, karuwa da
ke," Safeena tayo waje da ido tace "ni kike
ce ma karuwa," Inteesar tace "ance maki din
karuwa yar iska, uban waye bae san kinyi
karuwanci ba," tayi kan Inteesar ta rufeta da
duka dai dai nn Aliyu ya shigo gidan, ya
haura sama da sauri da mamaki yana
kallonsu ya fixge Safeena a fusace yace "ke
jakar wace gari ce" tana huci tace "karuwa
fa tace min Aliyu," ya watsa mata mari yace
"ta ce maki din, sharri tayi maki, ko bakiyi
karuwancin bane.
Safeena ta bude baki da mamaki tana kallon
Aliyu, cikin tsawa yace "get out kar na taka
ki a nn, don uwarki idan kika ji mata ciwo
kice baki sani ba ko me? Yar ki ce xaki
kamata da duka hka ko sharri tayi maki"
tsui tsui Inteesar ta bude dakinta a hankali
ta shige tasa key, Safeena da hawaye ya
gama wanke mata fuska don takaici ta kasa
cewa komai ta juya ta bude dakinta ta shige
da sauri, yyi tsaki ya bude dakinsa shi ma ya
shiga, dariya Inteesar ta dinga yi kmr wata
tababbiya a daki, kai Aliyu bae yi ba ko ke
wacece ya disga ki gaban kowa ba komai
bane a gurinsa, girkin da Inteesar bata yi ba
knn ta ci gaba da karatunta da ta tuna
abinda ya faru sae ta fashe da dariya,
Safeena kam xamanta tayi a daki bayan ta
kira uwarta ta gaya mata abunda ya faru
girki kam ta fasa shi har taje takashe gas
din ta komo sama, tana xaune tana naxarin
abinda uwarta ta gama gaya mata tana
murmushin mugunta Aliyu ya shigo dakin ta
dauke kanta ya karaso kusa da ita ya xauna
yana kallonta cikin lallami yace "haba bbyna,
meyasa xaki kulata bayan nace ki daina, i've
told yhu times wit out nmbr yarinyar nn ba
ishasshen hankali gareta ba wllh, ni kaina
tsoro take bani" Safeena ta mike a fusace
tace "dnt tell me dat Aliyu, ynxu so nake
kawae ka tashi ka maidani gidanmu," ya
mike ya kamo hannunta yace "haba safeena
wllh ina sonki kema kin san da hka, dukan
yarinyar nn da kika yi ynxu baki san xae iya
xaman min jaraba ba,"xata yi magana ya
saka bakinsa cikin nata ya shiga kissin dinta
ya dago kanta yana kallonta yace "yhu knw i
luv yhu dear, ki bari ynxu xanje in mata
magana," ya xaunar da ita ya fice daga
dakin ta bi shi da kallo, ita kam Allah ya
daura mata son Aliyu, tayi shiru xuciyarta na
tafarfasa tanatunanin abinda xata yi masa
taji ddi yau, ta sauke ajiyar xuciya tace
"xanyi maganinka kuwa yau," shi kam yana
fitaya buga kofar dakin Inteesar ta mike da
sauri duk da tasan waye tace "waye," yace
"ni kike tambayr waye," tayi tsaki ta koma
tayi kwanciyarta, yyi shiru yana kallon kofar
snn yyi kwafa ya shiga dakinsa. Ganin
mugun yunwan da take ji yasa inteesar ta
bude kofar a hankali ta fita xuwa falo,
kitchen ta tarda shi tsaye shima yana hada
tea ta juya da sauri xata koma ya fixgota,
tace "wayyoo ni ka kyaleni," ya cakumota
yace "ke kince kunnen kashi gare ki ko?" ta
bata rae kmr xata yi kuka tace "ni ka
kyaleni" yyi kwafa ya saketa yace "ni nasan
maganinki," snn ya fice, itama tean ta hada
taxo ta wucesa a falo tana takunta mai jan
hankali ya bita da kallo, a dae dae stairs ta
hadu da safeena, ta wuceta da sauri kmr
mara gskya, safeena dae bata ce mata
komai ba ta sauko kasa. Ganin ba girki
safeena xata yi ba kuma yasan yyi mata laifi
yasa Aliyu ya fita ya siyo masu abinci da
daddare, bata nuna masa komai ba ta
xauna suka ci abincin bayan ya kaima
Inteesar nata, karfe tara tace masa xata je
tayi wanka ta barsa nn falo ta haura sama
sae da ta fara shiga dakinsa ta bude drawer
dinsa ta dauki kwalin wani magani ta cire
pills har guda hudu tana murmushi sanin ko
na menene ta fice daga dakin ta shiga nata,
tana jin ya bude dakinsa ta fito daga nata
dakin da sauri ta shiga nasa yace "shine
kika bar ni ni daya a falo ko bbyna," ta danyi
murmushi bata ce komai ba ta xauna
gefensa, ta kalli agogo tace "yau baxa ka
sha coffee ba bby," ya duba agogo karfe sha
daya saura yace "to kawo min dear," ta mike
tana rangwada da shegun kayan baccin
dake jikinta tace "ok bby," snn ta fita daga
dakin, tana gama hada coffee din ta watsa
kwayoyin dake hannunta a ciki tana
murmushi ta koma sama ta kai masa, ya
karba ya ajiye yace "tnks dear bari sae nayi
wanka," tayi kwanciyarta kan gado ya mike
ya shiga bathroom yin wanka, tana nn
kwance ya fito yyi shirin kwanciya snn ya
jawo system ya dan yi danne dannensa snn
ya dauki coffee din ya fara sha, sae satan
kallonsa safeena take ta gefen ido, a hankali
ya dinga shan coffeen har ya shanye ya ajiye
cup din, snn yyi rub da cik kan gadon ya
kwanta tare da lumshe idonsa, tana ta
kallonsa har na kusan minti talatin snn taga
ya mike da kyar ya dawo gefenta ya kwanta
ya jawota jikinsa, bata hanasa ba ya shiga
shafata yana kissn wuyarta, ta fara mayar
masa da martani itama, sae da ta bari ya
gama ficewa hayyacinsa gaba daya ya xama
kaman wani mashayi har wani rawa jikinsa
yake yana neman fara aiki snn ta turasa da
karfi tace "me kuma xaka yi da karuwa
banda abinka," ya kankameta kmr wani
tababbe yace "no plss kar kiyi min hka
safeena, plsss," tayi dariya ta turasa da karfi
ta mike ta saka kayanta tace "aa
.
. Duk yanda Aliyu ya so Safeenah ta basa
hadin kai kememe taki yarda da shi sae
dariya take ta tana masa kallon rainin wayo
tace "kaje gun warce ba karuwa ba, ni kam
karuwace," tunda ta shigo gidan dama ta
lura da bbu abinda ke shiga tsakaninsa da
Inteesar don kullum ita kadae ke kwana
dakinsa sae randa baya bukatarta ne xae
hade rae yace tana damunsa ta koma nata
dakin, kuma shi da bakinsa ya taba gaya
mata baya forcin mace ta kwanta da shi,
komin nacinsa gwara ya hakura kuma ta
lura da gskya yake fada mata ba karya ba, ta
mike tsaye tana karairaye tana kallonsa tace
"gud nyt dear," snn ta fice xuciyarta fari tas
ae sae dae ya mutu yau, binta kawae yake
da kallo ya ma rasa abinda xae ce mata ya
mike xaune da kyar ya dafe kansa yana
kiran Allah a xuciyarsa, shi daya kadae yasan
yanda yake ji a jikinsa, ya ma rasa wani
tunanin xae yi, inteesar ta fado masa ya
girgixa kai sanin halinta ya koma kan gado
ya kwanta yana mayar da numfashi, tsam ya
mike kmr wanda aka tsikara ya fice daga
dakin ganin yana neman hallaka kansa yyi
hanyar dakin Inteesar, tana xaune gefen
gado ta kunna bedside lamp chemistry
textbook a hannunta tana karatu don gobe
xata xana jamb, ta mike da sauri jin an bude
kofar dakinta, ta koma da sauri ta xauna
ganin Aliyu don dan karamin kayan bacci ne
jikinta, gani tayi ya xube tsakiyar dakin, ta
mike tsaye da sauri ta dauki xaninta ta
daura ta karasa gabansa da sauri ta
durkusa tana kallonsa da mamaki, a
durkushe kansa yake, nn da nn ta rude kmr
xata yi kuka tace "me ya faru ya Aliyu," ya
dago da kyar ya riketa, idonsa ya kada yyi
jajur da kyar yace "fateema don Allah kar
kice kina tsorona yau, i beg u plss ki tausaya
min," ta yo waje da ido a tsorace ta mike da
sauri xata bar wajen yyi hanxarin fixgota ta
fado kansa ya rungumeta yana mata wani
irin kallo, kuka ta fashe da a rude tace "na
shiga uku, don Allah ka sakeni bana so,"
muryarsa na rawa yace "baki tausayina
fateema," cikin kuka tace "wllh wllh tsoro
nake ji ya Aliyu kayi hakuri," ya mike da kyar
ya fada kan gadonta ta mike tsaye ita ma ta
bisa tana kuka xata yi magana ya jawo ta
jikinsa yace "kar ki ce min komai fateema,
taimakona xaki yi," bae jira tace komai ba ya
shiga rabata da kayanta, duk da rawan da
jikinta ya fara yi kmr ana kada gangi bata
hanasa ba amma kuka ssae take, ganin da
gske ashe yake yasa ta fasa ihu ya toshe
bakinta da sauri ta shiga turasa a gigice
tana cewa "wayyoo wlh bana so ka bari don
Allah nake rokanka baxan iya ba," kuka take
kmr ranta xae fita, ya saketa yana mayar da
numfashi taga ya mike da sauri yyi hanyar
bathroom a nn bakin kofa ya xube kasa ya
kasa karasawa ciki, ta mike da sauri ta
dawo kusa da shi jikinta na rawa tana kuka
tace "kayi hakuri ya Aliyu, gani baxan sake
maka kukan ba," cikin tashin hankali take
maganar, ya rungumota ta runtse idonta da
sauri jikinta na ci gaba da rawa, bata sake
hanasa yi mata komai ba kuma tayi kkrin
hadiye kukan da take sae ajiyar xuciya,
ranar ta ci axaba wajen Aliyu, don bata ga
bambancinsa da ranar da ya fara saninta ba,
tayi kuka tayi rokan amma Aliyu bae sarara
mata ba bae ma san tana yi ba, ya wahalar
da ita ssae ba kadan ba, bae kyaleta ba sae
da yaga numfashinta na neman daukewa,
ya kankameta duk ya rikice mata yana kiran
sunanta, sun fi minti goma a hka snn yyi
namijin kkrin daga ta ya mayar kan gado,
kuka take don tsabar axaba muryarta ma
bae fitowa, duk ya rasa yanda xae yi da ita,
ya rungumeta abun tausayi ya shiga
lallashinta yana bata hakuri, ajiyar xuciya
kawae take tana kwance kan kirjinsa duk ta
wani langwabe don wahala nn da nn jikinta
ya dau xafi, wanka ya fara yi mata snn ya
bata magani ta sha, ya kwantar da ita kan
gado daga nn bacci ya dauketa wajajen
karfe hudu na Asuba.
.
Da kyar Aliyu ya iya tashi yyi sllhn Asuba,
shima duk baya jin ddin jikinsa, har lkcn
bacci Inteesar take ya dawo gefenta ya
xauna yana kallonta cike da tausayinta, a
hankali ya shiga tada ta, ta bude idonta da
ya kumbura don kuka a hankali tana
kallonsa yace "tashi kiyi sllh, xa ki iya?" ta
kauda kanta da sauri bata ce komai ba snn
ta mike xaune, ya daura hannunsa a
goshinta yaji da xafi, yace "xa ki iya kuwa,"
bata ce masa komai ba ta mike da kyar
gabanta na faduwa ko xata ji irin abinda taji
wancan ranar amma bata ji ba sae jiri
kawae da take gani ta shiga bayin ya bita da
kallo, yana nn xaune ta fito ta fara sllh, tana
idarwa, ya dawo kasa kusa da ita ya xauna
yana kallonta ta sunkuyar da kanta, yyi
murmushi yace "mrning," ta hade rae ta
mike xata bar wajen tayi baya xata fadi yyi
saurin rikota ya karasa da ita kan gadon ya
kwantar da ita, kuka ta shiga yi a hankali ya
kwanta gefenta yana kallonta yace "ki fada
min gskya fateema, jiya kin ji xafi ne," ta
dago kai tana kallonsa don takaici ma
kawae sae ta fashe masa da kuka ya dagata
suka mike xaune yace "ni bance kiyi min
kuka ba," ta turasa cikin kuka ssae tace
"tambayata ma kke ko, to wlh daga yau ka
sake min irin hka sae na gaya ka da inna" ya
rungumeta yana murmushi, ta dinga kuka
har da shessheka, a hankali yace "sae kice
ma inna nayi maki me," taki cewa komai sae
dae har lkcn kuka take, ya kwantar da ita ya
rufa mata bargo yace kiyi baccinki, ya koma
daya side din ya xauna, nn da nn bacci ya
dauketa, yana nn xaune har kusan karfe
takwas, yaga ta xabura ta mike xaune ya
juya da sauri yana kallonta, ta kalli agogo ta
mike tsaye da sauri tayi baya xata fadi ya
mike da sauri kan ya karasa kusa da ita har
ta buge da bango ta fadi kasa, ta fashe da
kuka ya durkushe gabanta da sauri ya
dagota, jikinta yyi xafi ssae, ya xaunar da ita
kan gado yace "to da ina xaki," tana kallon
agogo tace "yau ne exams dina," yyi shiru
yana kallonta yace "xaki iya," ta tsaya
kallonsa snn tace "kmr ya," yace "naga baki
jin ddi ki bari nxt yr kawae, kmr gobe..."
bata gama sauraran abinda xae ce ba ta
mike ta shige bathroom abinta tana
daddafa bango, yana nn xaune ta fito ta
shirya, yace "break fst fa," tana rike da
chemistry dinta da kyar tace "tea xan sha
kawae," ta gane xaxxabi ne ke neman
rufeta, da kansa ya hada mata tean ya bata,
ta shiga sha, har ta sha rabi ta ajiye sauran
snn a hankali tana nuna masa wani
calculatn a chemistry textbuk dinta tace "ni
na manta wnn formula din," ya karba yana
kallo abinda take nuna masa, ya dauki
takardar da take calculatns jiya ya shiga
solve din mata questn din yana mata
explanatn, wai daga kan da xae yi sae ganin
ta yyi ta jingina jikin gado tana bacci, yyi
shiru yana kallonta, yasan jiya kam bata
samu baccin kirki ba, a hankali yace
"fateema," ta bude ido da sauri tana
kallonsa tace "kace me," yace "ki bari nxt
tym kiyi jamb," kmr xata yi kuka tace "ni ka
kyaleni, idan baxa ka koya min ba in tashi in
tafi," ya daga kafada ya shiga koya mata har
ya gama yace kin gane tace eh, ta mike ta sa
Hijab dinta ya bi bayanta, sae da ya fara
shiga daki ya dauki makullin motarsa snn ya
fito ya bude mata motar ta shiga shima ya
xaga ya shiga suka bar gidan, hka ta dinga
bacci a motar har suka isa, yace "ke baki jin
magana nace ki bari wani yr din, ki ci gaba
da islamiyya kin ki ko," ko kallonsa bata yi
ba ta bude motar xata fita ya mika mata
dubu biyu yace xan xo daukarki anjima, snn
ya ja motarsa ya wuce, ita kuma ta shiga
ciki. A daddafe ta gama exams din don
xaxxabi ne ssae ya rufeta, ta fito ta nemi
guri ta xauna tana jiransa, jiran minti talatin
tayi masa taga bae xo ba ta tsayar da
tricycle ta hau abinta ta wuce gida, ko da ta
isa gidan bata tarda kowa ba mai gadi yace
mata sun fita shi da Safeena, ta tabe baki ta
koma ciki tayi kwanciyarta, sae kusan
yamma xaxxabin ya sake ta ta sauko kitchen
ta dafa indomie ta koma sama abunta ta ci,
ba su suka shigo gidan ba sae kusan karfe
goma na dare, ya shigo dakin yana kallonta
yace "srry fa, mamar Safeena ce bata da lfya
shine muka je gidan," ta ja dogon tsaki ko
kallonsa bata yi ba ta mike ta bude
bathroom ta shige ta barsa nn tsaye, yyi
kwafa ya fice kawae. Bayan kwana biyu aka
turo mata da scores dinta na Jamb, ya isa
har yyi yawa ta karanta Medicine abunta, a
falo take gaya masa ranar yyi mata mugun
kallo yace "ke ce xaki iya wani karanta
Medicine salon na bata kudi na kawae, wae
an gaya maki cin tuwo ne," ta galla masa
harara tace "to ina ruwanka ka shiga
kwakwalwata ne?," ya mike tsaye yana
kallonta yace "xan fa babbalaki wataran a
gidan nn yarinyar nn," tayi tsaki ta juya ta
koma sama tana cewa "ni wllh abba xanje
na gaya ka da abba, ina ruwanka da abinda
xan karanta, kai wa ya hanaka karanta
medicine" Safeena da aka siyo sabon
takardar koyon girki ana kitchen ana girki
tace "sae hakuri dear, ta xata wasan yara ne
medicine din Honey," yana hararanta yace
"ke kuma wa yasa bakinki a nan,
Bayan sati daya inteesar na kwance ita
kadae a daki wajen karfe sha biyu na rana,
safeena ma na dakinta waka sae tashi yake
kmr xae tsaga gidan, Aliyu ya fita aiki,
inteesar ta gaji da kide kiden da safeena ke
sa wa gashi ba daman tayi mata magana ta
ci ubanta Aliyu baya nn, ta mike ta dauki
Hijab dinta ta fita daga gidan, mai gadi yace
"oga yace kar na bari kowa ya fita," ta yi
shiru tana kallonsa kmr ta shakesa, can dae
tace "bae ce maka xan je duba jarabawa
bne," mai gadi yace "aa ni bae ce min hka
ba," ta galla masa harara ta isa kusa da gate
din tace "to sae ka kirasa kaji," ta bude gate
din ta fice daga gidan, gidan Aneesah ta
shiga, ta tarar tana ta karatun littafin hausa,
taji ddin ganin Inteesar ssae tace "kwana da
yawa 'yar uwa ina kikaboye gashi ba daman
na shiga gidanku,"inteesar tayi dariya tace
"ina nn ke dae, ba nace maki xan xana jamb
ba," Aneesah tace "ohh hka fa ya scores yyi
kyau?" inteesar tace "ehh wllh, shakur fa,"
Aneesah tace "yana bacci wllh, wae meye
sirrin yan mata naga kin kara kyau kinyi
haske" Inteesar ta harareta tace "ban fa son
cin fuska," Aneesah tayi dariya ssae tace
"wllh kuwa da gske, baki duba kanki a
madubi ne? ko dae...." inteesarta tabe baki
tace "ko dae me," Aneesah tayi dariya tace
"oho," ta mike ta kawo mata ruwa da lemo,
nn suka dinga hirar rayuwa, ganin Aneesah
bata boye mata komai game da rayuwarta
yasa inteesar ta bata lbrin nata rayuwan tun
bata yi aure ba har ixuwa aurenta da Aliyu,
da irin xaman da suke da shi har ya auro
safeena, Aneesah tace "tab lallai ba shi da
mutunci, kuma Abba bae kyauta maki ba da
yyi maki hka da ma Haisam din ne, ke ma da
naki ae, taya xaki dinga shiru kina cutar
kanki inteesar, na tabbatar da tuni kin gaya
Abba irin xaman da kuke da ya raba ku
ynxu wllh, to wae ma don me baki son na
shiga gidan naku sbda wata safeena,
tsoranta kike ko me, shi kuma Aliyun ba kiyi
niyar gyara masa xama bne wllh, tab,"
Aneesah tayi kwafa taji kmr ita ce Inteesar,
inteesar tayi murmushi tace "to mu je gidan
namu ynxu, ae ya fita office," Aneesah ta
mike kmr jira take tace "bari na dauko
Hijab," ta wuce sama Inteesar ta bi ta da
kallo tana murmushi, ba ajima ba ta sauko
sanye da Hijab tana rike da Shakur da
kwalban turare a hannunta, ta mika ma
Inteesar tace "mum dita ce ta aiko min da
turaren nn na dibar maki yana da kyau ssae
wlh," Inteesar ta karba tayi mata gdya suka
fita daga gidan, inteesar ta danna bell mai
gadi ya bude masu gate suka shiga, xaune
suka tarar da Safeena da uwarta a falo ta
cika ta da kayan drinks da nama sae hira
suke suna shewa kmr kawaye, safeena ta bi
Aneesah da kallo hka ma uwarta dake kallon
inteesar cike da tsana, Aneesah tace "kai
amma falonki babba ne Inteesar, nake ga
kmr ma yafi nawa," inteesar tayi dariya tace
"kai Aneesah kallon tsoro dae kika ma falon
nawa," safeena ta mike tana hararan
Inteesar tace "falonki? Amma ke jaka ce da
kika yi wnn tunanin uban wa ya baki falo,"
Hajiyarta ta mike tace "wllh kin ban mamaki
safeena da har xaki iya xama yarinya
karama ta raina ki hka, yaushe kika yi laushi
hka safeena, dubi fa kallon da take maki,"
inteesar tace "to falonki kike son nace da, ni
dae naga ko gaban mai gidan kika kira nn
da falonki wllh gwale ki xae yi, dama kun
saba, ni ko sae na fadi hkn ya xauna"
Aneesah ta fashe da dariya, inteesar tace
"Atoh ae gskya ne Aneesah, jiya fa daga tace
kofarta ya fara samun matsala ya hauta da
masifa kmr xae maketa wae ta shigo masa
da kofa gidansa ne da xata ce kofarta, bare
wnn mae gaba daya wae falonta" dariya
Aneesah ta dinga yi ssae, safeena tayi kan
Inteesar ta haura sama da sauri ta bar
Aneesah nn tsaye, safeena ta cakumi
Aneesah tana huci tace "don ubanki me ya
shigo dake gidan nn," Aneesah ta ajiye
shakur ta watsa mata mari tace "meye
hadina dake don uwarki da xaki rikeni hka,"
haba kan kace komai fada ya kaure
tsakaninsu, inteesar ta kasa saukowa don
shegen tsoro, da kyar tayi shahada ta sauko
ganin dambe suke ssae, safeena dake cin
uwarta hannun Aneesah ta fixgo inteesar,
uwarta ma ta taho da gudu xata sa hannu
Aneesah ta jefar da ita gefe daya ji kke
rigijib a kasa, nn inteesar da Aneesah suka
hadu suka nakada ma Safeena shegen duka
sae ihu take shakur ma na ihu, sae da suka
mata laga laga snn inteesar ta ja Aneesah
suka haura sama rike da shakur ganin uwar
safeena tayi kitchen da gudu, inteesar ta
saka key a kofar bayan sun shiga. Ihu
safeena ta dinga rusawa a gidan ta dauki
wayarta ta kira kawayenta gaba daya su xo
wae sae sun kashe Aneesah yau, ita kuma
inteesar mijinta baxae ganeta ba, inteesar
duk ta tsorata ganin kawayen safeena na ta
shigowa gidan, Aneesah kam ko a jikinta,
suka dinga bubbuga kofar kmr xasu cireta,
inteesar kuka shakur kuka, Aneesah tace
"kin ban mamaki wllh inteesar meye abun
tsoro a kishiya, ba dole ta maida ki yar ta ba
tayi ta duka taga kina tsoranta," inteesar
tana goge hawayenta tace "to ko na kira ya
Aliyu ne wllh cire kofar xa suyi," ta fashe da
kuka tana neman wayar Aliyu dake wajenta.
.
Inteesar tadauki wayar jikinta na rawa ta
shiga kiran Aliyu, dontsabar takaici Aneesah
kasa daukar Shakur dake ta tsala ihu tayi,
sae kallon Inteesar take kmr ta maketa, Aliyu
na daga wayar ta fashe masa da kuka, ya
mike tsaye da sauri yace "me ya faru,"
cikinkuka tace "ko ba Safeena bace wae
xata kasheni ta kira kawayenta da yawa a
gidan har da mamarta gasu nn xasu cire
kofar wae su kasheni," Aneesah ta girgixa
kai cike da takaici ta kinkimi danta tayi
hanyar kofa xata fita da gudu inteesar ta
karasa kusa da kofar ta rikota tace "wayyo
so kike su kashemu, don Allah ki bari ya
dawo," da sauri inteesar ta cire makullin,
Aneesah ta ma rasa me xata ce mata, su
safeena har lkcn basu fasa buga kofar da
suke suna xage xage ba, Aneesah ta shiga
mayar masu ita ma, hka suka dinga xage
xage ta uwa ta uba, sum sum inteesar tayi
jikin window har lkcn a tsorace take ta
tsaya tana jiran shigowar Aliyu, ko minti sha
biyar ba ayi ba ya shigo gidan da motarsa,
tayi gun Aneesah da ke ji kmr ta cire kofar
ta fita suyi ta takare tace "Aneesah ya
dawo," Aneesah ta galla mata harara tace
"da'allah ja can kin ban waje, kin ban
mamaki inteesar," Aliyu ya hauro sama yana
kallon safeena da kawayenta kusan su biyar
uwarta ma na tsaye cikinsu, wani mugun
tsawa ya daka ma kawayen nata yace "b4 d
count of 3 duk ku fice min a gida kar na sa
a kulle min ku karuwan bnxa kawae yan
iska nn din gidan ubanku ne ko na uwarku,
kaji min bitches " tuni jikin safeena ya dau
rawa, kawayen nata kuwa sum sum suka
shiga sauka kasa yana binsu da kallo yana
huci, ko kallon uwar safeenar bae yi ba yyi
kan safeena ya fixgota ya kai mata mari
yace "gidan nawa xaki mayar joint din yan
iska? To maxa ke ma dauko gyalenki ki bi su
bana son na bude ido na ganki cikin gidan
nn, get out" cikin tsawa ya karasa maganar,
Hajiya na kallonsa da mamaki tace "Aliyu a
kan idona kke walakanta min 'ya ta," ya juya
yana mata mugun kallo yace "an
walakantata din, ae dama a walakance kika
bani ita, kuma a walakance na sameta ko
kun manta ne," yyi tsaki ya shiga buga kofar
Inteesar, inteesar na hararan kofar
tace"waye?" yace "uwarki ce, kin xo kin
bude min kofa ko sae na taka ki," inteesar
tayi tsaki tace "to baxan bude ba," Aneesah
ta bude baki da mamaki tana kallon kofar, a
lallai wnn gantalallene shi kuma ba shi da
gwani, a fusace ya juya ya shige dakinsa,
safeena ta fito sabe da gyale tana matsar
kwalla tana kallon uwarta, uwar tace "ke ina
xaki maxa koma ita kanta naga ba kyaleta
yyi ba, hka yake dama," safeena tace "hka
yake wllh...." fitowar Aliyu yasa safeena tayi
tsit, ko kallonsu bae yi ba ya isa jikin kofar
inteesar da spare key a hannunsa, inteesar
na jin ya saka key cikin kofar ta mike tsaye
da sauri tana kallon Aneesah ta nuna mata
bathroom murya kasa kasa tace "ki shiga
bayi kafinya shigo," ko kallonta Aneesah
bata yi ba, har ya bude kofar ya shiga dakin,
da sauri inteesar ta juya xata bar wajen ya
fixgota a fusace ta fada kansa ta fasa masa
ihu a tsorace tace "wllh xan gaya ka da
Abba," idonta ya tsaya kallo da alamar
mamaki, ya sa hannu ya dago kanta yana
kallonta da kyau, a hankali ya shiga kare
mata kallo snn taga ya sake ta, Safeena da
uwarta na bakin kofa suna kallon
dukabinda ke faruwa, har ya juya xae fita ya
juya yana mata mugun kallo yace "wnn
wacece," ta hararesa tace "kawata ce," yyi
shiru yana kallonta, shakur ya karaso kusa
da shi yana cewa "daddy," da maganarsa da
bae gama fitowa ba, ya sunkuya yana
kallonsa snn ya shafa kanshi yace "hw re
yhu dan daddy," snn ya juya ya fita shakur
na biye da shia baya, sum sum safeena da
uwarta suka bar wajen, bbu yabo bbu
fallasa Aneesah tace "dauko min yarona na
tafi gida" Inteesar tace "lah har xaki tafi ki
bar anjima mana ko ruwa fa baki sha ba,"
Aneesah ta harareta tace "ae wllh kin bada
mata Inteesar, ni dauko min yaro na na bar
gidan nn," safeena da uwarta na shiga daki
uwartata ta kira Hajiyar Aliyu, tace "maxa
maxa ki taho ki ga irin rikon da danki ke ma
'ya ta Hajiya, hka muka yi dakudama ya
dinga dukan safeena," Hajiya ta bude baki
tana salati tace "wllh Alhaji ya hanani xuwa
gida Aliyu ban san dalili ba, amma kar ki
damu xan kirasa ynxun nn Hajiya" inteesar
na shirin kwanciyawajen karfe goma Aliyu
ya shigo dakin, bata ko kallesa ba ta gama
abinda xata yi ta shige cikin bargo, ya dawo
gefenta ya yaye bargon yana kallonta, ta
hararesa tace "meye hka," ya dan marairaice
mata yace "yau ma tausaya min xaki yi
kanwata," nn da nn ta fara kuka kmr jira
take tace"ni wlh wllh ka fitar min a daki ina
gaya maka," yyi dariya ya dawo gefenta ya
kwanta yana shafa cikinta yana murmushi
xae yi magana sae kuma ya fasa, ta turasa
tace "ni fa bana son iskancin nn ka fitar min
a daki," yana ci gaba da shafa cikinta yace to
wacece wnn yarinyar da na gani daxu a
gidan nn,inteesar ta buge masa hannu tace
"kawata ce," yace "a ina kika samo ta," tayi
masa bnxa, ya rungumota ssae, sae da ya
jagwagwalata snn ya fita daga dakin ganin
irin kukan da take a tsorace
.
Inteesar na kwance a daki tun safe take ta
bacci ta kasa tashi, da ta farka xata koma
taji dae yunwa ya isheta ta mike xaune ba
shiri tana kallon agogo, taga karfe daya, ta
tabe baki ta jingina jikin gadonta bbu
wanda ya damu da ko ta karya ko bata
karya ba a gidan, kuma ranar lahadi ne Aliyu
na gida, ta sauko daga kan gadon da kyar
idonta na juya mata ta dauki xani ta daura
kan rigar baccinta ta bude kofa ta fita tana
jan kafa, xaune ta tarda shi da safeena kan
dinnin suna lunch sae hira take masa tana
dariya, shi kam sae dae yyi murmushi yana
cin abincinsa, da wuya kaga dariyan Aliyu,
inteesar ta tabe baki ta shige kitchen suka
bi ta da kallo, Aliyu ya girgixa kai yace
"yarinyar nn dae bata da amfani a gidan
nn," safeena ta dauke kanta ta ja bakinta
tayi shiru don ta san tana iya magana ya
gwaleta ynxu ba karamin aikinsa bne,
inteesar taji bata jin cin indomie, ta dan
bude tukunyar safeena tana lekar abinda ke
ciki, cous cous ne da miyar hanta, ta dan
yatsina fuska duk da hka kawae taji abincin
ya shiga ranta, ta rufe tukunyar a hankali
tayi xamanta a kitchen din tana tunanin me
xata dafa, indomien dae at lng lst tayi decide
ta dafa ta mike tsaye ta daura ruwan, ta bar
shi ya fara tafasa snn ta shiga xuba
abubuwan da xata xuba, hka kawae taji
bata jin cin kwae, indomien na fara dafuwa
taji xuciyarta na mugun tashi, ta koma baya
da sauri tana rike da cikinta da ya hautsine
nn da nn, ji tayi amai na neman xubo mata
ta toshe bakinta da hannunta da sauri ta
fice daga kitchen din da gudunta tayi
hanyar stairs har tana tuntube, duk suka
bita da kallo Aliyu ya mike ya bi bayanta da
sauri yana tambayarta me ya faru ya ma yi
xaton yankewa tayi, safeena bata yi gigin
binsa ba don tasan halinsa, da kyar Inteesar
ta iya karasawa dakinta ta bude kofar bayi
da sauri ta durkushe nn bakin kofar ta
shiga kwarara amai kmr xata amaye hanjin
cikinta.
Aliyu ya shigo dakin da sauri ya karaso
bakin kofar bayin yana kallonta, har lkcn
amai take ssae gashi bbu komai cikinta, ya
durkusa gabanta a hankali ya dafa ta yana
mata sannu, buge masa hannunsa tayi, tayi
xaman dirshan a bakin kofar tana mayar da
numfashi ta fashe da kuka ta jingina jikin
bango duk ta rasa inda xata sa kanta, juye
juyeta shiga yi a bakin kofar tana kuka tana
kiran Abbanta, ya fixgota ya daka mata
tsawa "kina hauka ne," ko kallonsa bata yi
ba ta rarrafa jikin gado ta xauna ta jinginar
da kanta tana ci gaba da kuka tana mayar
da numfashi, ya mike ya dawo kusa da ita
yana kallonta ya dafa ta xae yi magana ta
mike da sauri ta koma bayin ta durkushe ta
shiga kwararo wani aman kmr xata shide
har wani rawa jikinta yake, lkci daya jikinta
ya dau xafi, ya riketa yana mata sannu, ta
langwabe masa ta fada kansa sae kiran
Abba take tana mayar da numfashi, ta fara
kkrin mikewa ya rikota yace "ina xa ki," tana
girgixa masa kai ta kuma fadawa kansa tace
"wayyo kwanciya xanyi na gaji," ya dago ta
ya shiga da ita bayin ya wanke mata baki ya
dauketa ya maidota cikin dakin ya kwantar
kan gado ya rufa mata bargo yana kallonta
sae rawan sanyi take, ya koma ya gyara
bathroom din, snn ya dawo gefenta ya
xauna yana kallonta duk ya ma rasa wani
tunani xae yi, ya jinginar da kansa jikin
bango a hankali ya lumshe idonsa "no! Wnn
me shegen rakin baxata iya rainon ciki ba
ynxu, nd bae tashi haihuwa da ita ba tukun,
da ma safeena ce wnn kam takuran da yake
samu a gida a kanta xae kara yawa ne ma,
to ma wani moranta yyi har xata dauki ciki
ynxu" yyi tsaki ya bude ido yana kallonta
bacci take amma da gani ba me ddi ba sae
juye juye take, ya girgixa kai ya mike ya fice
daga dakin, makullin motarsa ya dauka ya
sauko falo, safeena da ta fito daga kitchen
knn bayan ta kashe gas din da Inteesar ta
kunna tace "me ya sameta Dear," ya galla
mata harara yace "ban sani ba," ya fice, ta bi
sa da kallo, ita kam halin Aliyu ya isheta a
gidan nn, gashi sae bata kudinsu suke a
banxa a kansa, amma abu sae kara gaba
yake, tayi kwafa ta haura sama, yana shiga
motarsa ya kama hanyar asibiti, bae damu
da gaisuwan da nurses ke masa ba har ma
da patients ya haura sama kawae ya wuce
office dinsa, ya bude glass din da
magunguna suke ya shiga xaban wanda ya
kawosa, tabs kala biyu ya dauka da ruwan
allura daya ya rufe glass din ya fito ya rufe
office din, ya sauko kasa xuwa reception,
sae a snn ya shiga amsa gaisuwan patients
din da ke gaishesa, yyi murmushi ganin
matar da yyi ma theatre kwanakin baya da
yaranta da babansu, ya karasa kusa dasu
yana kallonsu yace "madam me ya sami
twins" matartace "wllh tari suke doctor, ya
aiki?," ya karbi dayan yana masa wasa yace
"aiki Alhmdllh anyi attend din maku ne," tace
"A'a ynxu dae xa a duba mu, madam fa," yyi
murmushi yace "tana lfya," tace "to a gaida
min ita, yau kana wkend ko," yace "wllh
kuwa, Allah ya sauwake, i wil b on my way,"
ya ba mijinta hannu suka yi sllma snn ya
juya, yana isa kofar fita sai da ya juya ya
sake kallon kyawawan yan biyun da suka
girma ssae, ya dauke kansa da sauri ya fice
ya shiga motarsa ya bar asibitin.
.
Aliyu na shiga gida ya tarda Safeena kwance
a falo tana kallo, ta bisa da kallo har ya
haura sama snn ta mike xaune tana
bubbuga kafa a hankali ta shiga maganar
xuci "lallai its high tym she wake up frm her
slumber, ya kamata ta tashi tsaye daga
xaunen da take ynxu, Aliyu ya gama kawota
bango, xata cire sonsa ta ajiye gefe guda
tayi abinda uwarta ta dde tana son tayi taki
yi sbda so ya rufe mata ido, ita kuma
inteesar ynxu suka sa kafar wando da ya da
ita" tayi murmushin mugunta ta mike ta
haura sama xuciyarta na tafarfasa. Aliyu na
shiga dakin ya tarda ta tana bacci ya xauna
gefenta yana kallonta ya ciro magunguna da
alluran da ya dauko a asibiti yana kallonsu,
snn ya juya yana kallonta tayi wani irin
haske ta kuma kara kyau, yyi murmushi ya
shafi gefen fuskarta ya mike ya dauko
syringe a dakinsa ya dawo ya shiga hada
alluran, sunansa yaji ta kira, ya juya da sauri
yana kallonta ta sake maimaitawa "ya Aliyu,"
sae kuma yaga tayi murmushi ta juya, ya
ajiye alluran hannunsa ya dawo dab da ita
ya xauna yana shafa labbanta da yatsa yace
"fateema," cikin baccin ta amsa "na'am," yyi
murmushi ya daura mata kiss a bakinta,
murmushin yaga ita ma tayi, yyi still yana
kallonta, to wae meyasa yake son xubar da
cikin nn, shi dae yana son yara kuma xae so
yaga kyakkyawan bbyn da xata haifa masa
mai kama da ita, ya dauke kansa ya daura
hannu a goshinsa kan na juya masa, y?
Meyasa yake son xubar da bbynsa gudan
jininsa, ya girgixa kai yace "No," da sauri
yaga ta mike xaune ya kamo ta ta fara
turasa xata sauka yaki sakinta yana
tambayarta mene, amai ta shiga kwarara
masa a jiki yana rike da ita har lkcn, sae da
ta gama snn ya dauketa ya shiga da ita bayi,
sae kuka take tana cewa ita ya kaita gida,
wanka yyi mata ya nannadeta cikin towel ya
fito da ita ya cire xanin gadon snn ya
kwantar da ita, shima wankan yyi don duk
ta bata masa jiki ya saka xanin gadon cikin
washn machine da shirt din jikinsa snn ya
fito daure da towel, ranar ce rana ta farko
da ta taba ganinsa daure da towel don ko
singlet Aliyu bae yrda ta gansa da shi bare
short nicker, ta rufe idonta da sauri, shima
bae ce mata komai ba ya kwashi
magunguna da alluran da ya hada ya fita da
su, dai dai lkcn da Safeena ta fito daga
dakinta, ta bi sa da kallon mmki shi kam ko
kallonta bae yi ba shiga dakinsa. Alluran da
yyi mata bayan ya tilasta ta sha tea ne ya
tsayar mata da aman, amma duk da hka sae
da ta gwammace dama aman ta dinga yi taji
ddi, don rasa inda xata sa ranta tayi sae
kuka take tana juye juye, ya rungumota cike
da tausayinta yana lallabata tayi bacci, da
kyar ta samu baccin ya dauketa, yyi shiru
yana kallonta duk ta rame lkci daya, da
yamma wajajen karfe biyar ya fita pharmacy
siyo mata magunguna da drips din da xae
sa mata.Yana fita ko minti goma ba ayi ba
Zainab ta shigo gidan ko kallon safeena
dake ta busar da gashinta da hand dryer
bata yi ba ta wuce sama, safeena ta bi ta da
kallo snn ta ja dogon tsaki, bacci ta tarar
Inteesar ke yi ta shiga tashinta da xolaya
tana cewa "ke kasa kinyi bakuwa maxa
tashi" inteesar ta shiga juye juye ta mike
xaune da kyar tana kallon Zainab, Zainab
tace "hmm lbri na xo maki da mai ban
kunya," inteesar xata yi magana taji yawu
cike bakinta, ta mike tsaye da kyar ta shiga
bayi ta xubar da yawun ta dauraye bakinta
da freshner ta dawo, Zainab tace "meye
hka," Inteesar ta langwabe da kyar tace
"bana jin ddi ne," Zainab ta bude baki "iyye
kar dae bby xa a samo mana," inteesar tayi
shiru da mamaki tana kallonta snn tace "bby
kuma, wani bby," Zainab tayi dariya tace
"lalala kinga yanda kka yi wani irin haske da
kyau kuwa, shknn xa a sama ma yayana
bby," inteesar ta hade rae xata yi magana
taji yawu kuma a bakinta ta mike da sauri
taje ta tofar wnn wani irin jaraba ce, ta
tambayi kanta, kuka ta fashe ma Zainab
ganin Zainab ta kuke sae murna take xa su
samu bby, tace "ni fa bana son hka Zainab
wllh bani da komai," Zainab tace "ki daina
wllh, ga signs a jikinki," kuka ssae take tana
cewa na shiga uku ni Zainab ki bari bani da
komai yarinya da ni xaki ce ina da ciki,
Zainab tayi dariya ssae tace "tunda ko kina
kwana daki daya da yayana ai ke ba yarinya
bace," dai dai nn Aliyu ya shigo yana ma
Zainab mugun kallo yace "ke wae wace irin
mutum ce, ban hanaki shigowa gidana ba,
xo ki fita," cikin daga murya ya karasa
maganar ta mike da sauri tana xumburo
baki ta dauki mayafinta ta bi ta gefensa ta
fice ya kai mata rankwashi, inteesar ta hade
kanta da gwiwa tana kuka, ynxu ciki ne da
ita yar yarinya da ita, to da wani ido ma xata
kalli su inna, ae Allah ma ya kyauta kuma ya
rabata da haihuwa ynxu kuma ma wae dan
Aliyu. Ta mike da sauri tun kan ya shigo
dakin xata yi hanyar bathroom jiri ya debeta
ya shigo dakin da sauri ya kamota ta fada
kansa suka xube kan gado, ya fada gefenta
da sauri ganin ynda take mayar da
numfashi ya dagota ya rungumeta yana
mata sannu, cikin kuka tace "wllh ka cire
min cikin nn bana so," ya toshe bakinta da
sauri yana kallon cikin idonta yace "ni ina
son abu na
.
Kuka ssae Inteesar ta shiga rera masa, shi
kam saekallonta yake yana murmushi, ta
fara kkrin mikewa xata sauka daga kan
gadon ya riketa da sauri yace "ina xaki,"
cikin kuka tace "wllh sae ka cire min cikin
nn bana so," ya rufe bakinta ya hade rae
yace "kar ki sake cewa na cire maki bbyna,
sae kace wani kaya," ta buge masa hannu,
ya harde kafarsa cikin nata tayi yar kara, ya
rungumota yana kallonta ya shiga shafa
mata cikinta yace "me xaki ci, dubi fa yanda
kika rame tun kan ba mu je ko ina ba, a hka
xa muyi rainon cikin kika san ma ko yan
biyu ne kanwata," ta fashe masa da kuka
tana kiran Abbanta, ya rankwashi kanta
yace "ki daina min kmr ihsaan a nn, ke baki
san kin girma ba tunda ga bby nn cikin cikin
ki" bata san lkcn da ita ma ta rama
rankwashin ba tana kukan da xa a iya
kiransa da na shagwaba duk da har ga Allah
ba shagwaba take ba, ya wara ido yana
kallonta, ta koma baya da sauri nn da nn ta
tsorata ya lakaci hancinta ya ja kunnenta
yace "kin ci sa a bbyna na jikinki da yau na
maki shegen bugu, ya Aliyu kike rankwashi
" bae jira me xata ce ba ya kwantar da itaya
mike ya fita, ta mike xaune da sauri ta hade
kanta da gwiwa ta fashe da wani sabon
kukan ynxu wae ciki ne da ita da gske yar
yarinya da ita, ba a dau lkci ba ya dawo
dakin rike da kofin tea yace "maxa tashi ki
sha na saka maki ruwa aman ya tsaya,"
kallon tean kawae tayi taji xuciyarta na tashi
ya kai mata baki ta mike da sauri sae cikin
bayi ta shiga kwarara amae, ya isa kusa da
ita ya durkusa ya dafata yana kallonta yana
mata sannu, sae da ta gama snn ya gyara
mata jiki ya maidota cikin dakin, a hankali ta
kamo hannunsa tana hawaye tace "don
Allah ya Aliyu ka tausayamin ka cire min
cikin nn bana so," ya galla mata harara yace
"wllh idan kika sake gaya min wnn maganar
sae na bata maki rae, ki cire ynxu na gani
mana," tayi shiru tana kallonsa xuciyarta na
tafarfasa, ita ko ta fi sa iskanci xae gani
kuwa, ta juya tayi kwanciyarta tana mayar
da numfashi, tean da bata sha ba knn har
bacci ya dauke, sae kusan sha daya na dare
ta farka yana gefenta a kwance, shima amai
ne ya farkar da ita, ya cire mata ruwan dake
hannunta ganin a gigice ta farka tana
neman sauka ya raka har bayin ta shiga
kwarara amae, gashi dae ba komai cikinta,
ya xuba mata ruwa a kai ya fito da ita, daga
ita har shi ranan basu yi baccin kirki ba,
jikinta yyi xafi ssae ta rasa inda xata sa
ranta sae kuka take masa yana rungume da
ita, da kyar bacci mai nauyi ya dauketa
kusan asuba. Washegari monday bae je aiki
ba sbda ita, tana kwance jikinsa bayan ya
lallabata ta sha tea kadan yyi mata
allurorinta wajen karfe goma safeena ta
kwankwasa kofar tare da sallama, yace ta
shigo, ta bude kofar ta shigo sae da
xuciyarta ya kusan harbawa yanayin da ta
gansu, shi singlet da 3qtre ne jikinsa, ita
kuma rigan bacci iya cinya, ta kirkiro
murmushi ganin allurori a bedside drawer
tace "Ayya bata jin ddi ne dear," ba tare da
ya kalleta ba yace "eh, ya akayi?" tace "Allah
sarki, Allah ya sauwake fateema sannu,"
inteesar ta dago kai da kyar ta watsa mata
harara, ta mayar da kanta, safeena ta dauke
kanta da saurixuciyarta na tafarfasa tace
"yauwa dear Momy ce ciwonta ya tashi
shine xanje ynxu, amma ba ddewa xanyi ba
dan da sauki," yace "ita kuma kullum ciwon
nata ke tashi, baku da abinci ne a gida, ae
yunwa ce ke kawo ulcer " tayi shiru tana
kallonsa ya tabe baki yace "Allah ya
sauwake, ki duba side drawer can bedroom
dina ki dauki dubu goma," tana murmushi
tace "to ngd dear," snn ta juya ta fice tana
murmushin mugunta. Da yamma safeena ta
shigo gidan, har lkcn Aliyu na dakin
Inteesar, lkci lkci yakan yi tunanin ko dae
kawae ya rabata da cikin nn ne ta huta
shima ya huta, don ba karamin wahala yaga
take sha ba tun kan cikin ya kai ko ina, ynxu
ma da kyar ta samu bacci ya dauke, irin
masu shegen laulayin nn ne me wahala, ya
dan yi tsaki, ita ma ragwancinta ne kawae
yyi yawa, duk ta fige lkci daya sai kace
wacce tayi wata tana ciwo, safeena ce ta
bude dakin ta shigo ya daga kai yana
kallonta, tayi murmushi tare da lumshe ido
tace "Aliyu so nake kaje duba mum dita
ynxu, kuma ka tafi mata da wnn maganin
nn da ka bata ranan nn wae taji ddinsa," yyi
shiru yana kallonta,snn taga ya sauke ajiyar
xuciya yace "wae ynxu?" ta dan yi fari da ido
murna fal cikinta, amma ta hade rae tace "to
da yaushe kke tunani," yace "ok," snn ya
kwantar da Inteesar dake jikinsa ya mike
tsaye ya juya yana kallonta bacci take, kan
yace komai safeena tayi saurin cewa "to
kaxo ka wuce," ya juya ya fice daga dakin, ta
bisa da kallo tana murmushi, dakinsa ya
shiga ya shirya snn ya fito da makullin mota,
tana hararansa tace "to haka xaka je mata
hannu rabbana," ya koma ciki sae gashi ya
fito da kudade, ta rakasa har jikin mota snn
ta manna masa kiss a baki, yyi murmushi ya
lumshe idonsa yace "sae na dawo bbyna,"
snn ya ja motar ya fice daga gidan, ta doka
uban tsalle tashiga kiran layin uwarta cikin
murna tace "wayyoo mum, saura naki gashi
nn xuwa.
Aliyu na fita gidan ya wuce wani babban
super market ya yayiwa mum din safeena
siyayya bata wasa ba akalla ya kashe kusan
50k. Ya fito ya shiga motarsa ya dau hanyar
gidan mum xuciarsa duk a cushe ya rasa
dalili,gashi yana son kiran inteesar a waya
ta wayar sa dake hannunsa amma ya kasa a
haka dai ya cigaba da driving har Allah ya
kai shi lpy. Yana isa gidan su safeenar
maigadi ya bude masa get yana washe baki
kasancewar aliyu na hannun damansa ne
yana da yawan kyau,ko kula da gaisuwar da
me gadi yake yi masa bai yi ba ya mika masa
2k aiko maigadi ya hau godia da kiraki
hannu kawai ya daga masa yai hanyar
parkin shade dinsu ya ajiye motarsa ya
duba seat din baya cikin magungunan daya
ajiyewa a a first aid box dinsa ya dauki na
ulcer ya jefa a cikin ledar magunguna da
safeena ta bashi. Sallama yayi cikin nutsuwa
ya shiga falon dai dai lokacin mum ta fito
aiko ganin aliyu yasa ta dan yatsina fuska
shiko jiki na bari kamar yayi gamo ya sauko
dg kan kujera yana kwasar gaisuwa,fuska
ba yabo ba fallasa suka gaisa yai mata ya jiki
sannan ya mika mata ledojin hannunsa ya
mike xai mata sallama kenan tace "aliyu
baxaka tsaya ko ruwa kasha ba?" Sai ya
tsinci kansa ya kasa yi mata musu alhalin bai
taba cin komai na gidan ba. Komawa yai ya
xauna xuciarsa na cikin dumuwa yana
buqatar ya duba inteesar kuma ya san by
nw ta tashi dg baccin da ya barta tanayi.
Tunanin haka yasa ya ajiyar xucia tare da
fesar da iska mai xafi hade da lashe
labbansa da suka bushe. Mum ce ta shigo
riqe da jug a akan tray da cup da roban
ruwan c'est bon,ta tsiyaya masa xobon ta
mika masa ya kai hannu biyu tare da yin
godia.... zai kai bakin shi kenan wayarsa tai
ringing hakan ya dakatar dashi da sauri ya
ajiye xobon ya karkace ya xaro wayar dg
aljihun jeans dinsa duk a tunaninsa ko
inteesar ce ta kira shi...
Sae da Aliyu ya fara xuwa asibiti ya dauki
maganin da xai kai ma mamar safeena snn
ya ja motarsa ya kama hanyar gidan jikinsa
a mace, ya na isa yyi parkin a waje, ya fito
da maganin yana kare ma gidan kallo snn ya
shiga, suka gaisa da mai gadin ya karasa
balcony ya danna bell, yar aiki ta bude masa
kmr jira take ya shiga falon ta nuna masa
kujeran da xae xauna da sauri shima kmr
wnda ake contrl ya xauna inda ta nuna
masa yana bin ko ina na falon da kallo, yar
aikin tayi sama kiran Hajiya, yana kallo
Hajiyar ta shigo falon ya dan dukar da kansa
ya gaisheta ta amsa da fara'a kmr gske snn
yyi mata ya jiki, ya bata maganin da ya kawo
mata, ta amsa tana gdya tana jujjuya
maganin, ya ciro kudin da ya dauko daxu ya
mika mata yace "ni xan koma Hajiya" ta
karba da sauri tana gdya ta mike tace to
bari na kawo maka ruwa kasha mana, yace
"A'a Alhmdlh ae daga gida nke," tace "to
bari na baka sako ka kaima safeena," yace
"to," ta mike ta yi sama, sae ga ta ta sauko
da dan wani parcel, ya karba yyi mata
sallama, ta rakosa har bakin kofa tana sa
masa albarka snn ta koma murna fal cikinta,
yana barin anguwar yaji hka kawae yana
son ganin abinda ke cikin parcel din, parkin
yyi gefen titi snn ya shiga budewa, wani
ruwa ne ya xuba jikinsa ya matsar da parcel
din daga jikinsa da sauri amma duk da hka
sae da ruwan ya taba kayansa da farko wari
yaji, ya yatsine fuska kawae kuma sae yaji
wni mugun kamshi me ddi ya xiyarci
hancinsa, ya rufe da sauri ya ajiye parcel din
ya ci gaba da drivin dinsa. Safeena ta kasa
xaune ta kasa tsaye sae kaiwa take tana
komowa a falo, wayar uwarta ya shigo nata
ta daga da sauri jikinta na rawa tace "ya
xauna kan kujerar mumy, kuma ya karbi
ledan," uwar ta kyalkyale da dariya tace
"wllh kuwa dota, ynxu fatanmu kawae Allah
yasa ya bude," safeena ta doka tsalle tace "
Alhmdllh amma naji ddi momy, budewa
kuma ba matsala bace ko a gida xan sa ya
bude bare ina da yakinin ma ya bude naji
sighn din da mutumin yace xan ji a jiki na,"
budewar gate din da safeena taji yasa tace
"wayyoo momyna ya dawo xamu yi waya
anjima," ta katse kiran tana murmushin
mugunta, shknn ynxu sae yanda tayi da
Aliyu," yana shigowa gidan ta karasa cikin
kissa ta rungumesa ya dagata sama ya
manna mata kiss a goshi yace "bbyna sae
kyau kike karawa kullum," ta hararesa tace
"sae yau ka sani," yace "A'a bbyna ina sane,"
kinsan me bbyna na dan maki barna wllh
momy ta ban turare na kawo maki da
karambani na na bude ya xuba jikina," ta
kankamesa ta rasa inda xata sa kanta don
murna, tace "da gske bbyna, wllh sae ka
biya ni," yyi hanyar stairs da ita yana cewa
"naji xan biya bby nawa ne," inteesar kam
na xaune ta jinginar da kanta jikin gado, ji
take kmr ba ita ba duk ta rasa inda xata sa
ranta taji ddi, ga alluran hana aman da yyi
mata duk ya bi ya dameta, tana neman yin
aman ma ko xata samu sauki amma ta kasa,
yunwa take ji ssae amma bbu abinda ke
ranta, ko wani abinci ta tuna sae taji amai
na taso mata jikinta yyi mugun xafi ga
kishin ruwa da take ji kuma tana tsoron
shan ruwa, ta sauko kasa da kyar ta kwanta
kan tiles din dakin ko xata ji ddin ranta,
kasa daure kishin tayi ta mike xaune tana
mayar da numfashi ta rarrafa ta bude fridge
dinta taga ba ruwa ciki sae lemo, tana
daddafa bango ta fita daga dakin ta sauka
kasa da kyar ta bude fridge ta dauki ruwa ta
sha, snn ta koma sama, dae dae kofar
dakinta taji amai frm no where ta xube
wajen ta shiga kwarara aman kmr ranta xae
fita, suna daki shi da safeena duk ta gama
rikitar da shi, ya turata da karfi ya mike
tsaye ya karasa kofa ya bude ya fita safeena
ta bi bayansa da sauri, durkusawa yyi
gabanta yana kallonta, ta fashe masa da
kuka abun tausayi ta xube jikinsa muryarta
na rawa tace "don Allah ya Aliyu ka kai ni
gida, ni wllh na gaji ko ina ciwo yake min
wayyoo mutuwa xanyi," ya rungumeta cike
da tausayi xae yi magana safeena tace
"dear," ya juya da sauri yana kallonta,
kallonsa kawae ta tsaya yi bata ce komai ba,
ya sauke ajiyar xuciya yana kallon Inteesar
yace "ke kuma mahaukaciyar wace gari ce
xakiyi ma mutane amai a nn, idan kina jin
amai ba sae ki shiga bathroom din ki ba,
wnn ae kaxanta ce," Inteesar ta daga kanta
tana kallonsa, da kyar ta shiga kkrin mikewa
daga inda take wani aman ya taso mata ta
shiga kwarara sa a wajen, kuka ssae ta
fashe da ta jingina jikin bango tace "wayyoo
Abbana," kallonta kawae ya tsaya yi ya kasa
cewa komai, ta rarrafa ta shiga dakinta ta
xube kan tile tana mayar da numfashi,
safeena da sae kallon inteesar take da
mugun mamaki lkci daya jikinta yyi sanyi ta
ma rasa tunanin da xata yi, a xuciyarta tana
cewa amae kuma? to me hkn ke nufi, ta
sauke ajiyar xuciya tana kallon Aliyu tace
"me ke damunta????
.
Aliyu ya mike tsaye yana kallon safeena yace
"bata jin ddi ne," bae jira me xata ce ba ya
bude dakinsa ya shiga sae ga shi ya fito da
mop ya gyara wajen aman, safeena ta koma
daki da sauri hannunta na rawa ta shiga
kiran uwarta, tana dagawa tace "momy wlh
ina ga fa kmr cikine da yarinyar nn," uwar ta
mike daga xaunen da take da sauri tace
"mene? Ke wa ya gaya maki," a rude safeena
tace "gashi nn tana ta amai," uwar tayi salati
tace "bari xan kiraki," ta katse kiran. Da
daddare Inteesar na kwance kan tiles ya
shigo dakin ya durkusa gabanta yana
kallonta yace "tashi ki sha kunu na karbo
maki a gida," ta kasa dagowa ya dagota
yana kallonta ya kauda kansa da sauri, ya
kai mata kofin baki, ta kauda kai da sauri
muryarta na rawa tace "xafi," ya girgixa
mata kai yace "ba xafi," ta maido da kan
jikinta na rawa ta daura hannunta kan kofin
taji ba xafi ta kai bakinta yana rike da kofin
ya shiga bata, da sauri ta cire bakinta tace
"baxan yi amai ba? ya gyada mata kai ya ci
gaba da bata, yunwa take ji ssae don hka
rabi tasha ta koma tayi kwanciyarta kan
tiles, yace "kin koshi ne ta gyada masa kai
tace ruwa xan sha, yace "aa baxa ki sha ba,"
bata ce komai ba ya dago ta mayar kan
gadon duk abinda suke safeena na lekensu,
ta koma da sauri daki har da hawayenta ta
kira uwarta tace "kai ni momy wllh na gaji,
gashi can wajenta yana lallabata yana bata
koko," uwar tace "yi shiru safeena, daxun
nn na dawo daga wurin mutumin, ca yyi
wae duk abinda xa muyi masa a kantabaxae
taba tasiri ba sbda yana mugun son cikin nn
dake jikinta," safeena ta dafe kirji tace "ynxu
ciki ne da ita da gske ina xaune momy,"
uwar tace "ki tsaya ki saurareni mana,"
safeena na share hawaye tace "to ina ji
momy," uwar tace "yauwa, to ynxu ca yyi
dole sae an lalata cikin in har muna son
muga aiki yyi mugun tasiri a kansa, ynxun
ma ba wae bae yi tasiri bane, don xae dinga
lallaba ki kuma sae abinda kika ce masa xe
yi, sae dae fa hankalinsa gaba daya na
gunta sbda wnn shegen cikin, kuma fa baki
isa ki hanasa xuwa gunta ba amma, don
hka kawae ki kwantar da hankalinki jibi ki
xo mu koma kauyen yace yana jiranmu, ciki
kuma kmr ya bare ne," safeena ta share
hawayenta xuciyarta fal murna tace "to
ngdd momyna," ta katse kiran tana
murmushin mugunta. Da safe Aliyu ya bae
ma safeena i.v din bikin Zainab, ta tabe baki
tana hararansa tace "to ca nayi maka ban
sani bane," yyi shiru yana kallonta snn yyi
murmushi yace "to Allah ya baki hkuri
bbyna, amma ni dae ban san me nayi maki
ba kika canxa min kwana biyu," ya mike ya
karasa kusa da ita ya xauna yana shafa
gashinta yace "haba yan matana," ta
hararesa tare da buga masa hannu tace "ni
ka rabu dani," ya rungumeta yace "haba
bbyna," kmr xata yi kuka tace "to ba kai bne
ba baka ma damu dani da lamarina ba a
gidan ba," yace "inji wa yace maki hka,"
kakarin Aman inteesar yaji, ya saketa da
sauri ya mike tsaye ya fice daga dakin,
safeena ta bi sa da kallo xuciyarta na mugun
kuna, kasan dakin ya tarar da ita tana ta
amai ya kamata har ta gama snn ya gyara
mata jikin ya gyara dakin ya kwantar da ita
kan gado, ta rikesa muryarta na rawa tace
"sanyi nake ji yaya," ya lulluba mata bargo
snn ya dauki I.v din da ya ajiye gaban
madubinta xae fita ya juya yaga kallonsa
take, ya dawo yana kallonta yyi murmushi
yace "kina san wani abu ne," ta girgixa
masa kai yace "kinsan bikin Zainab saura
kwana goma ko," ta mike xaune da sauri
tace "da gske yaya, ni ba a gaya min ba to,"
ya kamo hannunta yace "ae sun san baki da
lfya, ki bari nxt wk sae mu tafi gidan kafin
nn jikinki ya kara kwari," ta marairaice kmr
xata yi kuka tace "to ba kila xuwa tayi ranan
ta gaya min ba ka koreta," yace "ba ta ji ne,"
tace "to yaya wa xata aura" yana kallonta
yace "faruuq," ta wara idonta ta fada kansa
cikin jin ddi tace "don Allah da gske yaya, kai
amma naji ddi wllh, ka bani nmbr ya faruuq
din" yace "to anjima xan baki, xanje gida
ynxu me xan ce inna ta girka maki?" tayi
shiru sae kuma ta bata rae ita da ba ma son
cikin take ba, yace kinyi shiru, tana
hararansa tace "kace mata ina da ciki ne," ya
daga hannayensa da sauri yace "A'a" yana
girgixa kai, ta koma ta kwanta tace "dan
wake nake so ni," yace "to, sae na dawo, kar
ki sha ruwa kar amai ya takuraki," bata ce
masa komai ba yayi hanyar kofa, duk wnn
abinda suke safeena na labe tana jinsu, tana
jin xae fito ta bar wajen da sauri ta shige
dakinta tana murmushin mugunta, yana
fitowa ya shiga dakin safeenar
.
Bayan kwana biyu safeena ta samu ta lallaba
Aliyu wae xata gun wata yar uwarta, ya ko
barta har da bata kudi da makullin mota
dayake ta iya drivin tana ta murna a
xuciyarta tana cewa lallai sae yanda tayi da
Aliyu, ynxu kam ta yrda yana tafin hannunta
amma dae ba duka ba, tunda bata isa ta
hanasa xuwa gun Inteesar ba, amma komai
ya kusan xuwa karshe, ta fada a fili tana
murmushi, cikin kwanakin nn Aliyu na da
aiki ssae a clinic don hka ya gwammace da
ya bar Inteesar kadae a gida gwara ya
dinga tafiya da ita don tana bukatar kulawa
ssae, hka ko ya dinga yi kullum shi xae
shiryata da safe yyi ma safeena sallama su
wuce asibiti, hkn yyi mugun tada ma
safeena hankali to ta ya xa'a yi ta aikata
abinda suka sha wahala kafin su samu
bayan baya barinta a gida., ita kam Inteesar
ko kadan abinda Aliyu ke mata baya burgeta
don dai dae da second daya bata son cikin
jikinta, kuma tasan sbda cikin yake mata
hka, wani mugun tashin hankali ke xuwa
mata idan ta tuna cikin Aliyu ne jikinta, Ana
saura kwana uku bikin Zainab ya kai ta gida
duk da ba a son ranta ba don bata son su
san tana da ciki, amma ashe duk ya gaya
masu uwarsa ce kadae be gaya ma ba sae
umma, inna duk ta rikice masa wae cutar
jikarta kawae yake gashi duk ta fige ba kyan
gani, shi dae bae tanka ma inna ba ya fice,
Inteesar dae na kwance falo sae mayar da
numfashi take don da kyar ta iya karasowa
cikin gidan bayan sun sauka daga mota,
kuma da asibiti ne baya barinta ta taka da
kanshi yake daukarta su shiga ciki, inna tace
"to wae wani irin jarababben cikine wnn
dake neman kashe min ke," ta mike xaune
tana hararan inna kmr xata yi kuka tace
"wae ni nace maki ciki gareni ne," bata jira
me inna xata ce ba ta shiga daki tayi
kwanciyarta, inna duk ta daga hankalinta
ganin irin laulayin da Inteesar take mai
tsanani, bbu wanda bae san ciki ne da ita
ba a gidan, ko da yaushe cikin amai da
kasala take, ko maganan kirki bata son yi
sae in Aliyu na yasa ta gaba ko yana
tambayarta me take so, duk tausayinta
kawae yake, Hajiya da hankalinta yyi mugun
tashi bata ga fuskar da xata ma Aliyu
magana ba da ya shigo da ya fice daga
gidan, tab aiko gwara ta nemo yanda xa ayi
da cikin nn, ynxu Aliyu dama sae ya iya
kwana daki daya da yarinyar nn duk cika
bakinsa, hka aka yi biki hankalin inna rabi
na gurin Inteesar rabi na gun bikin, duk aka
yi abubuwa masha Allah, amma inteesar na
kwance tana fama da kanta, safeena ma ta
xo ranar bikin tana daddaga hanci ita matar
Aliyu inna ta kunyatata gaban lodin jama'ar
biki su kursum dariya kmr xasu shide, ko
minti daya bata kara a gidan ba tayi gaba ba
shiri jikinta a sanyaye har ga Allah tsoran
tsohuwar nn take, ran Hajiya yyi mugun baci
amma bbu yanda ta iya da inna, washegarin
ranar da aka kai Amarya da daddare Aliyu ya
shigo falon inna bae ko kalli innar ba ya
durkusa gaban inteesar dake kwance
idonta biyu, ya daura hannu a goshinta yace
"amma yau bakiyi amai ba ko," a fusace inna
tace "kaji gantalalle wani irin bata yi amai
ba, ae hanjin cikinta ne kadae bae xaxxago
ba yau har tsorata nayi nace to ko su ne ke
shirin fitowa" Aliyu yyi mata mugun kallo
yace "to ke kuma wa ya somo bakin ki nn,
iyayi kawae," sae abun ya ba Inteesar dariya
ya dago ta yana kallonta yace "Abba na
neman mu, xaki iya ko na daukeki," ta
marairaice tace ynxu, ya gyada mata kai, ita
mugun kunyan Abba take ji har ma da
momynta, duk shigowar da momy take ta
gaisheta kar inna ta xaxxageta tace taki
xuwa, Inteesar yi take kmr tana bacci, inna
ta mike tsaye da sauri tace "bari kawae na
kama hannunta mu je," Aliyu ya bude baki
yana kallonta yace "wae meyasa kike son
shiga tsabgar da ba taki ba ne," bae jira me
xata ce ba ya harareta ya sa ma Inteesar
hijab dinta ya dauketa suka fice, inna tayi
kmr xata yi kuka tace "ni ban san meyasa
yaron nn ya rainani da tsufa na da furfurata
ba," a hanya ya ajiye ta dalilin rokansa da ta
dinga yi ya ajiyeta suka karaso falon yana
rike da hannunta, da kyar ta iya bude baki
ta gaishe da Abba kanta a kasa, ita kawae
kunyarsa take ji, yace "ya jikin fateema,"
kanta a kasa tace "da sauki Abba," yace "to
Allah ya sauwake, kina son komawa dakin ki
ne ko xaki xauna nn gun inna sbda
condition dinki" ta dago kai a hankali tana
kallon Aliyu, shima kansa a kasa yake, tayi
shiru ta rasa me xata ce don ita kam bata da
burin cikin nn ya kara girma a jikinta, Aliyu
yace "Abba da dae na tafi da ita xan fi kula
da ita a can kuma ba gida ma nake barinta
ba tare da ita nake xuwa clinic, nn ko xae yi
min nisa kuma xan takura kaina," Abba xae
yi magana inna ta fado falon, ashe tana labe
tana jin duk abinda suke cewa tana huci
kmr xata yi kuka tace "amma munafurcinka
dayawa yake Bukar, hka muka yi da kai? To
ni Rahmatu nace bbu inda yarinyar nn xata
je aje a kashe min ita da abinda ke cikinta a
banxa a hofi a barni da wayyo Allah, don
idan an kashe su ma ni nayi hasara ba ku
ba".
.. Aliyu ya dan yi tsaki ya kauda kai, Abba
kam shiru yyi yana ta kallon inna, ita ko ta
tsaya masu kmr soja a bakin kofa, can dae
Abba yace "to ki hada kayanki sae ki bi su,"
tayi kwafa tace "ko da naji," snn ta juya ta
fice da sauri, Abba ya girgixa kai yace "tashi
ka dau matarka ku tafi," Aliyu ya mike yana
kallon Inteesar, ita ma ta mike tsaye suka
ma Abba sallama snn suka fita, yana rike da
hannunta yace "mu je mu gaida momyn
ihsaan ne," tayi kmr bata ji sa ba shima bae
sake ce mata komai ba har suka fita ya bude
mata mota ta shiga shima ya xaga ya shiga
suka kama hanyar gida, ko da suka isa tayi
bacci ya fito da ita daga motar yana rike da
ita kmr bby, safeena na kwance falo ta bi su
da kallo ya sakar mata murmushi yace
"bbyna," tayi tsaki ta dauke kanta tacigaba
da kallonta, sae da ya kai Inteesar sama ya
kwantar da ita snn ya sauko ya sameta, ta
mike tayitsaki ta haura sama ta bar sa nn ya
bita da kallo snn yyi mmrshi yabi bayanta.
Washegari sae da safeena ta sa ya makara
xuwa office, wanka kawae yyi ya shirya ya
dauki makullin motarsa ta rakasa tanai
masa shagwaba ya manna mata kiss ya ja
motarsa ya bar gidan, ta sauke ajiyar
xuciyan jin ddiyau dae ya manta shegiyar
gaba daya, ta koma cikin gida murna fal
cikinta, tana shiga daki ta fito da kullin
maganin da aka basu su sa ma Inteesar a
ruwan sha ta tsura ma maganin ido tana
murmushi,dukiya fa knn a hannunta, ruwan
fridge ta kwashe gaba daya ta bar guda
biyu ta xuxxuba maganin cikisnn ta rufe
fridge din ta koma sama, ta lura kasa
Inteesar ke saukowa shan ruwa bbu ruwa a
dakinta kuma bata ga alamar an siyo ba,
tana ta kwance a daki tana jiran jin
saukowar Inteesar amma shiru, ita ko tana
kwance daki ta rasa inda xata sa ranta sae
juye juye take ga yunwar da take ji tun safe
ta gane Aliyu ya bar gidan hkn yasa ta daure
ta mike ta sa ma kofar ta key, kishin ruwa
duk yabi ya ishetagashi ba karfin sauka
kasa, da kyar ta rarrafa ta shiga bathroom
ta bude tap ta sha ruwa ta dawo tayi
kwanciyarta kan tiles. Washegari ma abinda
ya faru knn Aliyu bae shigo ya ga halin da
take ciki ba ya bar gidan da sassafe, duk da
jiya don ita ya dawoda wuri amma safeena
ta gusar masa da hankalinsa ya manta me
ya dawo da shi, ganin yunwa na neman yi
mata lahani yasa ta dinga daurewa tana
hada tea a nn dakinta da ruwan sanyita sha,
shima tana sha ta amayo, duk ta kara
xabgewa bata da aiki sae na kuka ita daya a
daki, wani lkcn sae taji kmr ta dauki waya ta
kira inna kawae sae ta fasa don bata ga
amfanin kiran ba don rabuwa kawae take
son yi da cikin, ita safeena bbu abinda yafi
daga mata hankali irin yanda taga ruwanta
na nn ajiye ba a taba ba, hkn yasa da
daddare da Aliyu ya dawo ranan tace "anya
kuwa kana shiga duba baiwar Allahn nn
dear, gashi ita bafitowa take ba, na kan
shiga na dubata wllh, amma ba ddewa nake
ba kar ace xan yi mata wani abun ne" Aliyu
ya mike da sauri kmr an tsikaresa yyi hanyar
stairs ta bude fridge ta dauka ruwan da
sauri ta bi sa tana cewa "gashi ka kai mata
ruwa naga kmr jiya ruwan dakinta ya kare
na fanfo take sha, ni kuma kar na kai mata
ta xata wani abun ne," ya karba ya haura
sama ya bude dakin ya shiga rabon da ya
ganta yau kwana uku tun ranar da
sukadawo daga gida, ya karaso gabanta ya
durkusa yana kallonta a hankali yace "ya
jikin fateema, kin daina aman," tayi tsaki ta
juya abinta, ya bude fridge dinta ya ajiye
mata ruwan yace "me xaki ci," tayi bnxa da
shi, yyi shiru yana kallonta, ta juya cikin kuka
tana kallonsa tace "wllh tllh idan baka cire
min wnn shegen cikin ba...." bae jira ya
karasa jin maganarta ba ya xuba mata mari,
"don uwarki kika sake min maganar cire
ciki sae nayi mugun saba maki kina ma da
hankali kuwa, to ki je ki cire tunda ke
mahaukaciya ce," ya mike a fusace ya fice
daga dakin ta bisa da kallo dafe da kuncinta.
Ranar bata yi bacci da daddare ba, kawae
Allah Allah take gari ya waye, gari na
wayewa ya shigo dakin kafin ya tafi aiki, tea
me kauri ya hada mata ya ajiye matagefenta,
snn ya dauko goran ruwan da safeena ta
basa jiya ya ajiye mata gefenta safeena ta
shigo dakin tana murmushi tayi ma Inteesar
ya jiki ko kallonta inteesar bata yi ba suka
fice tare da mijintata rakasa ya shiga mota
ya manna mata kiss snn yaja motar ya bar
gidan, safeena ta koma gidan xuciyarta fari
tasa ganin goran ruwan da ta ba Aliyukusa
da inteesar yau dae xa ayi ta ta kare, ta
shige dakinta tana dariya. Inteesar ta mike
tsaye ta dauki Hijab dinta ta saka, duk irin
wahalan da take sha ko sau daya wanka
bae taba wuce ta da safe ba dole sae ta
daure ta shiga tayi, ta fito tana ganin jiri mai
gadi ya tsaya xae mata maganar bnxa ta
fixgo gate din ta fice abinta ta barsa nn
tsaye, gidan Aneesah ta shiga, tana xaune
tana ba shakur Indomie, tana shigowa ta
kwanta kan kujera tana mayar da numfashi,
Aneesah tace "lah daga ina hka Inteesar
daxun nn nagama xancenki a xuciyata wllh"
Inteesar xata yi magana taji yawu bakin ta
mike da kyar taje bathroom ta xubar
Aneesah tace "A'aah kice oga yyi aiki"
.
Inteesar ta harare Aneesah snn tayi tsaki
tace "ni don Allah taimako naxo kiyi min
Aneesah," Aneesah tayi dariya tace "to
kawas ina jinki amma cikin nn na baki
wahala gskya, kinga yanda kika rame
kuwa," Inteesar ta dawo kasa kusa da ita
tace "don Allah don Annabi Aneesah kinsan
inda ake abortion?" Aneesah tayo waje da
ido da mamaki tana kallonta snn tace "kina
da hankali kuwa inteesar," inteesar ta
jinginar da kanta jikin kujera hawaye ya
cika idonta, Aneesah tace "kinyi shiru,"
inteesar ta share hawayen idonta tace "wllh
xubar da cikin nn xanyi kin dae ji na rantse
in ma xaki gaya min ki gaya min," Aneesah
ta gyada kai tace "to tashi ki fita a gidana, ni
bana hulda da maras tsoran Allah," inteesar
ta juya tana kallonta tayi shiru snn ta mike
tayi hanyar fita daga gidan, Aneesah ta bita
da sauri ta kamo hannunta tace "haba
inteesar bafa kiyi kama da jahila ba," kuka
inteesar ta fashe da tace "baxa ki gane ba
Aneesah wllh bana sonsa bana son cikinsa,
bae damu dani ba sae wahala nke ta sha,"
Aneesah ta xaunar da ita tana kallonta da
tausayi tace "ni na tabbatar maki kina haife
wnn cikin xaki ga tsantsan so gun mijinki,
ni banga rashin son da mijinki yake maki ba
inteesar nafa ga abinda yyi ma kishiyarki
ranar sbda ke, don me xaki walakanta
kyautar da Allah ya baki yar uwa," inteesar
tayi shiru tana ta sauraran Aneesah tana ta
wa'axinta da nasiha, har ta kai Aya snn
inteesar ta kirkiro murmushi tace "to ngdd
Aneesah, ta dauki shakur tana ta wasa da
shi yana mata dariya, tace "amma a gida
kika haife yaron nn ko Aneesah," Aneesah
tace "me kika gani," inteesar tayi yake tace
"aa kawae tambaya ce nayi don ni dae ina
tsoran Haihuwa," Aneesah tayi dariya tace
"A'a a asibiti na haifesa," inteesar tace "wani
asibitn?" Aneesah tace "A'a tender care na
haifesa, ai kin san asibitin bbu wani nisa,"
Inteesar tace "A'a" Aneesah ta gaya mata
inda asibitin yake kuma dama abnda kawae
take son ji knn, ta mike xuciyarta fal murna
ta bar gidan.
.
Inteesar na fita daga gidan Aneesah ta
koma gida cike da jin ddi ta shiga dakinta
tana haki kmr warce tayi gudu, ta tabe baki
jin wakan da ke tashi dakin safeena, sae da
ta huta na kusan minti goma snn ta mike ta
dauki purse dinta ta fita daga dakin, dakin
Aliyu ta bude a hankali ta shiga ta bude
drawer din da taji yace Safeena ta bude ta
dauki kudi ranan, taji ta a kulle, tace "na
shiga uku," ta mike ta fara kalle kallen cikin
dakin kmr xata yi kuka, to ina xata samu
kudin xuwa asibitin ynxu, drawers din
dakin ta dinga bubbudewa gaba daya ko
xata ga kudi amma bbu, duk ta gaji sae haki
take, tuni ta fara kuka tana cewa "Allah ka
taimakeni in ga kudi" ta bude lst bedside
drawer din taga wani babban book an
rubuta my diary a gaba, tayi tsaki ta ajiye ta
mayar da drawern, ta mike ta isa wardrobe
din da yake ajiye kayansa na sawa ta bude
ta lumshe idonta sakamakon wani kamshi
me ddi da ya bugi hancinta, ta gama
bincikenta nn ma ba ta ga kudi ba ta rufe ta
xube kasa ta daura hannu a ka tace
"wayyoo Abbana wllh ni na gaji," ko ina ta
bude daga taga Allura sae taga magunguna
da dae kayan asibiti kmr tsiya wnn wace
irin jaraba ce, kmr ance ta mike ta daga filo
taga dubu daddaya karkashin filon har da
Atm dinsa ta wara ido tace "wayyo Allahna,"
ta kwashi kudin ta shiga kirgasu da sauri
hannunta na rawa taga dubu sha biyu ne, ta
dan marairaice fuska to xae isheta taje
asibitin ma kuwa, tayi tsaki ta bude purse
dinta ta xuba kudin snn ta juya xata fita
daga dakin taje dakinta ta sha ruwa don
mugun kishi take ji don tsabar son taje ta
cire cikin ta nemi xaxxabin dake tattare da
ita ta rasa sae kasala kawae, har ta isa bakin
kofa ta dawo da sauri tuna baxae rasa ruwa
a dakinsa ba da tayi ta bude fridge dina ta
ko ga ruwa ta dauka ta bude ta sha snn ta
rufe fridge din ta dauki sauran ta fita daga
dakin, duk wnn abinda take safeena bata
sani ba, tana daki kwance tana ta shan kida
cike da jin ddi, jiran jin ihun Inteesar kawae
take a ko wani lkci, Inteesar kam har ta fita
daga gidan rike da purse dinta cikin Hijab,
mai gadi dae bae ce mata kala ba ta bude
gate ta fice abinta sae da ta isa bakin titi
snn ta tsayar da tricycle tayi masa
kwatancan asibitin da Aneesah ta gaya
mata yace ta bada dari biyu, ta shiga tace
mu je. Wasa wasa asibitin shegen nisa ne
da shi, yyi parkin dae dae gate din asibitin
ya juyo yana kallonta yace "mun kawo
Hajiya," ta fito tana kare ma asibitin da ma
anguwar kallo, ta bude purse ta ciro dubu
daya cikin kudin ta basa kudin ya rage dubu
sha daya, ya bata canjinta ta karasa cikin
asibitin gabanta na faduwa, wnn dae da
ganin asibitin nn ba na talakawa bne, anya
kuwa xasuyi mata abortion a dubu sha daya
kuwa ta dan karyar da kanta abun tausayi,
da Addu'arta ta shiga asibitin, babba ne
ssae ta karasa cikin reception ta xauna
ganin patients dayawa a xaune, ta shiga
kare ma reception din kallo, ta kai kusan
minti talatin a xaune ba a xo kanta ba duk
ta gaji, taji kwanciya kawae take son yi ga
amai dake taso mata, ta daura kanta a cinya
taji kmr ta rusa ihu duk ta rasa ina xata sa
ranta, wata nurse ce ta dafa ta ta dago da
sauri tana kallonta, Nurse din tace "yhur
card nmbr Madam," inteesar ta shiga kalle
kalle xata yi magana taji yawu ya cika
bakinta, nurse din ta lura da hka ta nuna
mata bayin dake kasan reception ta karasa
ta xubda yawun ta kora ruwa snn ta dawo,
nurse din ta debo vitamin c ta mika mata ta
sa a baki tayi mata gdya ta karba, tana
kallon Nurse din tace "i dnt have a card in
here," Nurse din tace "to dole sae kin yanki
kati," Inteesar tayi shiru snn tace "nawa ake
yankan katin," nurse din tace "family card
dubu biyar, na mutum daya dubu 2 da dari
5," inteesar tayo waje da ido tana kallonta,
ganin xata bata ma nurse din lkci ga kuma
patients dayawa suna jira yasa tace "to ki
yankar min na mutum daya," nurse din tace
"ok" snn tayi gaba, a hankali inteesar tace
"na shiga uku, to ai kudin ya kare," ba ajima
ba nurse din ta fito daga wani dan daki ta
mika mata katin snn wata nurse ta
daddubata ta duba har da weight dinta tayi
rubutu a file tasa nurse ta rakata bayi aka
xuba mata ruwa a kanta don temperature
dinta yyi sama, ita dae binsu kawae take, a
xuciyarta tace ko da yake basu san me ya
kawota ba shiyasa suke bata lkcnsu, ita dae
ynxu likita kawae take son gani, wata nurse
ce ta gwada mata office din doctor din da
xata shiga a sama, tana rike da file dinta ta
haura sama da kyar ta karasa office din tayi
knock.
A hankali Inteesar ta tura kofar bayan an
mata ixinin shigowa office din, cak ta tsaya
daga bakin kofa tana kallon likitar, doctor
din ma ta mike tsaye tana kallon Inteesar da
mamaki tace "fateema," inteesar ta kirkiro
murmushi gabanta na faduwa ta karaso
office din a sanyaye, ta nuna mata kujera ta
xauna, doctor din tace "daga ina kike hka
fateema, me ya kawo ki nn," ta rasa karyan
da xata mata, da kyar bakinta na rawa ta
ce"banda lfya ne," doctor din ta hade rae
tace "shi Aliyun fa," inteesar ta rasa me xata
ce ga xuciyarta sae tashi yake, likitan ta
dawo kusa da ita tana kallonta ta dago
kanta tana kallon cikin idonta tace "ciki gare
ki fateema," inteesar tayi shiru bata ce
komai ba, doctor din ta ciro wayarta ranta a
bace ta shiga neman layin Aliyu, da sauri
inteesar ta dakatar da ita gabanta na
faduwa tace "A'a don Allah doctor kar ki
kirasa wllh ya sani kuma yana dubani nice
dai bana son shi ya duba ni, Allah yana kula
dani doctor kawae ni ce bana so, idan yaji
na xo nn xae bata min rae don bae sani ba,"
doctor din tace "haba fateema, to ma don
me xaki fita ba tare da ixinin mijinki ba,
kuma meyasa baki son ya duba ki," inteesar
ta fashe da kuka tace "wllh ni bana sonsa
doctor," doctor din ta tsaya da mamaki tana
kallonta snn tace "sbda me fateema, gashi
har rabo ya shigo kice baki son mijinki,"
Inteesar ta sunkuyar da kai tana hawaye,
doctor din tayi shiru tana kallonta, can ta
koma sit dinta ta xauna ta shiga yi mata
nasiha kan cewar ta rungumi mijinta ta cire
duk wani rashin sonsa a ranta, ita dae bata
ce komai ba sae kukan da take a hankali,
Doctor din tace "yyi maki scan ne?" inteesar
ta girgixa kanta tace "A'a nace masa bana
so," doctor din ta harareta tace "to karki
sake yi ma mijinki musu baki san aljanarki
na karkashin kafarsa ba," inteesar ta dan
tabe baki kanta a kasa ba tare da ta bari
doctor din ta lura ba, doctor din ta yagi
wani takarda ta danyi rubuce rubuce snn ta
danna bell wata nurse ta xo da sauri, ta
mika mata takardar tace "scan xa ayi yi mata
sisterna ce," doctor din ta kalli Inteesar tace
"tashi ki bita," inteesar ta mike a sanyaye ta
bi bayan nurse din har sun kai bakin kofa ta
juya tana kallon doctor Maryam tace "don
Allah doctor kar ki kirasa wlh xae bata min
rae,"doctorn tayi murmushi tace "baxan
kirasa ba ki kwantar da hankalinki" bayan
kusan awa daya inteesar da nurse din suka
shigo da sakamakon a hannun nurse din, ta
mika ma doctor maryam ta fita, doctorn ta
bude takardar tana dubawa, inteesar dae
kallonta kawae take ranta a hade, ba shiri
taga doctor maryam ta mike tsaye da sauri
tace "waw Ahmdllh, twins 4 Aliyu, Allahu
akbar," ta rungume inteesar tace "Allah ya
raba lfya kanwata, kinga ma yan biyu ne"
inteesar ta sunkuyar da kanta da sauri
hawaye ya cika idonta, hka doctorn ta dinga
mata surutu cike da murna kmr ita xata
haifa ma cikin, ita dae bata ce mata komai
ba daga karshe ta hada mata magunguna,
da allurori a office dinta ta xuba mata su a
leda da takardar scan din tace "to maxa
tashi ki koma gida sae ki kai masa takardar
scan din, sae ya fada maki yanda xaki sha
magungunan yyi maki alluran," Inteesar ta
mike da sauri kmr jira take tace "ngdd ssae
doctor," har gate doctorn ta rakota snn tayi
mata sallama bayan ta kara jaddada mata ta
hakura ta xauna da mijinta, ita dae inteesar
sae gdya take mata har ta koma ciki snn ta
kama hanyar titi inda xata samu tricycle, a
cikin wani flower ta watsar da magungun
da injectns din dake cikin ledar dake
hannunta ta bar takardar scan din kawae, ta
isa titi xuciyarta na suya, ta tsayar da tricycle
tace "malam don Allah idan kasan ko wani
asibiti a nn wajajen ka kai ni," yace "to
shigo muje akwae wani can gaba," ta shiga
da sauri ya ja machine din suka kama
hanyar asibitin, ae ko yan goma ne a cikinta
ba yan biyu ba sae ta xubar da su yau wllh
.
Wani babban Asibitin aka kuma kawota, ta
fito tana kare ma asibitin kallo snn tace
"nawa xan baka," yace "ki bada ko nawa
ne," ta ciro dari biyu ta mika masa tayi
hanyar gate din shiga asibitin, gabanta ya
shiga faduwa ganin asibitin bana wasa
bane don har yafi wanda taje da xu, tana isa
reception bata tarar da patients da yawa ba
aka xo kanta, nurse din tace "yhur card
nmbr madam," Inteesar tace "i dnt have a
card in here, nawa ne katin," nurse din tace
"family card dubu biyar, na mutum daya
dubu uku, na Anti natal, dubu biyu,"
Inteesar ta ciro dubu uku ta mika mata,
matar tace "sunanki fa," inteesar tace
"Fateema Aliyu," matar tace Address fa? Da
date of birth, Inteesar ta bata fake address
da date of birth dinta, matar ta juya ta wuce,
ba ajima ba ta dawo ta mika mata katinta
snn aka dubata wata nurse ta rakata da file
dinta a hannunta xuwa office din doctor,
yana xaune yana ta rubuce rubuce farin
glass a idonsa, sae da gabanta yyi mugun
faduwa don sae taga kmr ya Aliyu barin
yanda ya hade rae da tsukekken bakinsa,
shima kyau kam ba a magana, ta karasa
office din xuciyarta na ci gaba da bugawa ta
ajiye masa file din a gabansa ta xauna kan
kujera a sanyaye tana kallonsa, yana ta
rubuce rubucensa har lkcn bae dago ba,
hkn yasa ta dan marairaice a hankali kmr
me shirin kuka tace "doctor," sae a snn ya
dago yana kallonta yace "srry ina dan abu
ne," ya jawo file dinta gabansa ya bude,
tana kallonsa a sanyaye tace "don Allah don
annabi taimako naxo ka min doctor," ya
dago yana kallonta yace "taimakon me fa,"
nn da nn hawaye ya cika idonta ta rasa me
xata ce, yace "tok 2 me mana yan mata,
taimakon me kike nema, baki da kudine
kika xo a dubaki," ta girgixa kai ta fashe
masa da kuka tace "A'a," ya kauda kansa
yace "ni karkiyi min kuka a nn, ki fadi
abinda ya kawo ki, mijin ki fa?" a hankali
muryarta na rawa tace "ni banda miji," ya
wara ido yana kallonta yace "wat? Amma
kin san kina dauke da juna biyu kuwa," ta
fashe da matsanancin kuka tace "ka taimaka
min ka tausaya min ka cire min don Allah
abinda ya kawo ni knn," yace "kina da
hankali kuwa ca aka maki ana xubar da ciki
a nn," cikin kuka tace "nasan ka iya doctor,
ni taimakona nake son kayi don Allah," ya
girgixa kai yace "me ya aike ki kanwata,
meyasa kika xabi ki..." da sauri ta katsesa
tace "rapin dina aka yi, kuma har yau ba a
sani ba a gida," yace "innalillahi wa
inna'ilaihi raji'un, to don me baki fada ba a
gida" tana kuka tace "ba yrda dani xasu yi
ba wlh," yace "to waye yyi maki," tayi shiru
kmr me tunanin abinda xata ce nn kuma
amai ne ke taso mata, ta daure tace
"saurayina ne," yyi shiru yana kallonta,
mikewa yaga tayi da sauri shima ya mike,
yaga ta toshe bakinta ya bude mata bayi da
sauri ta shiga ta fara kwarara amai, yana
tsaye gefenta tausayinta ya rufesa ganin
yanda take aman kmr xata shide amma bae
taba ta ba har tagama ya bata ruwa ta
wanke bakinta ta xuba ruwa a wajen ta fito
da kyar ta xauna kan kujeran ta kifa
kantakan table dinsa abun tausayi, yace "to
sae mu ce ma Allah me, wllh ban taba xubar
ma mace ciki ba kanwata," ta dago tana
hawaye tace "plss ka taimakeni kuma ka
fadi nawa xan baka ko ba yau ba xan biyaka
don kudin hannuna ya kare," shi dae yyi
shiru bae ce komai ba, har dae daga karshe
ya mike ya fito gabanta yana kallonta yace
"takardar meye a hannunki," ta kalli
takardar snn tace "na scan da nayi ne," ya
karba yanadubawa snn yace "Mrs Aliyu
kuma aka sa," kmr xata yi kuka tace "kunya
nake ji, ace bani da miji kuma gani da ciki,"
bae ce komai ba ya maida idonsa kan
takardar yace "ya salam, yan biyu ne ae," ta
gyada masa kai tana hawaye, ya koma ya
xauna ya dafe kansa, yace "anya kuwa xan
iya taimakon nn kanwata, rae biyu fa kuma
har kusan 2mnth," ta fashe masa da wani
sabon kukan tace "don Allah ka rufa min
asiri," ya mike shima da ganin sa kasan
jikinsa yyi sanyi, ya bude wani show glass
din magunguna ya shiga xaban wasu
magani har kala uku, snn ya dawo yana
kallonta rike da maganin yace "amma xan
maki allura a nn," kai kawae ta gyada masa
tana kallonsa ya hada alluran ya juyo yana
kallonta tace "ni ba kai xaka min ba ka ba
nurse su min," yana kallonta yace "ok ni xan
rufa maki asiri, ke kuma ki tona min nawa
ko," da sauri tace "A'a wllh," ta bude
cinyarta yyi mata snn ya dauko
magungunan ya bata ya gwada mata yanda
xata sha, tayi ta masa gdya har da kuka, nn
dae yyi mata nasiha ssae akan matsalar da
ta tsinci kanta a ciki, ya nuna mata ita ce me
babban laifi, ita dae hawaye kawae take har
yyi mae isar sa, yyi shiru, a hankali tace "to
nawa xan biyaka doctor," yyi shiru yana
kallonta snn ya sauke ajiyar xuciya yace
"bana bukatan komai tunda ba aiki me kyau
nayi ba, kawae dae nmbrki xaki bani don
Allah," da sauri tace "to xan baka amma a
kashe yakesae na koma gida na kunna," ta
basa tsohon layinta, snn ta dada masa gdya
ssae ya rakata har gate, ya koma, ta shiga
ticycle xuciyarta fari tasa kmr an mata
albishir da aljanna ta kama hanyar gida da
magungunanta.
.
A gajiye Inteesar ta shiga gida bayan ta biya
mai adai-daita sahu kudinsa, xaune ta tar da
Safeena a falo tana cin Ayaba da gyada tana
kallon American film sae kyalkyale dariya
take ita daya kmr tababbiya, bata ko kalli
inda safeena take ba ta haura sama da sauri
gabanta na faduwa kar ta biyo ta ta ci
ubanta, don mugun tsoranta take idan su
biyu kadae ne a gida, in ko Aliyu na nn
fitsara sae wanda bata tuna ba, dat was
den, lkcin da take da lafiya knn, ynxu kam ta
kanta take ba ta tsiwa ba, Safeena ta bi ta
da kallon mamaki baki bude, dama yarinyar
nn bata gidan ashe, shine take ta xaune kmr
yar iska tana jiran jin ihunta, to ina ma taje,
ranta yyi mugun baci ta kasa cin ayaban
gabanta, tunawa tayi cewar tunda ta kwaso
rana 1st abinda xata fara bukata shine
ruwa, hankalinta ya kwanta tunanin hkn da
tayi, to amma Allah yasa a fridge ruwan yake
kar taga abinda ke ciki don inda sanyi
baxata taba lura da komai ba, inteesar kam
na shiga daki ta ajiye magunguna da
takardar scan dinta a kan gado, katunan
asibitin dama tun a hanya ta watsar da su,
ta bude fridge dinta da sauri tana haki xata
dauki ruwa ta sha taga bbu ruwa, ta yarfe
hannu kmr xata yi kuka to ynxu ya xata yi
ga wancan mayyar a falo taje tayi mata duka
a bnxa, ta juya xata shiga bayi tasha ruwan
ganin bata da wani alternative ta hango
goran ruwan da safeena ta ba Aliyu ya
kawo mata a bedside drawer, ta karasa da
sauri ta dauki ruwan taji shi kmr ruwan
dumi, bata damu ba ta kai bakinta xata sha
taga abubuwa na yawo a ciki kmr an xuba
kasa, idan ma baka kura ido ba baxa ka lura
da hkn ba, ta dauki dayan ma tana kallon
kasan ruwan ta gansu kwance ta girgije ta
ga suna ta yawo, ta yatsine fuska ta isa
bathroom dinta ta tsiyaye duka ruwan guda
biyu a bath tub snn ta koma daki ta dauko
cup ta dibi ruwa a famfo ta sha ta koma ta
kwanta a gajiye, a hka bacci mai nauyi ya
kwasheta ba tare da ta shirya ba, shafa
cikinta da taji ana yi a hankali ne yasa ta
bude idonta da sauri suka yi ido hudu da
Aliyu xaune gefenta ta shiga kkrin mikewa
xaune ya taimaka mata yana kallonta yace
"kin ci abinci kuwa don yau na xo duba
bbyna ne hope kin shirya?" ta juya ta kalli
agogo da sauri taga karfe takwas na dare,
mikewa tayi da sauri taje ta xubar da yawun
bakinta ya rikota yace "ina xa ki," ta buge
masa hannu ya saketa ta karasa bakin kofar
bayin ta juya tana hararansa,
magungunanta ta gani kan gadon kusa da
shi, ta yo waje da ido a tsorace da ganinta
kasan bata da gskya, ya tsaya kallonta yace
"me ya faru," sanin cewa xae juya ya kalli
inda take kallo ne yasa ta tofar da yawun
bakinta nn bakin kofa da sauri ta fasa wani
raxanannen ihu tana tsalle, har ya juya ya
kalli ledan kan gadon kuwa ya mike da sauri
ya karasa kusa da ita a rude ya riketa yana
tambayarta lfya, jikinta ya dau rawa ta fashe
masa da kuka tace "wayyoo cikina ke min
ciwo har da kaina," da mugun damuwa
yace "cikinki kuma" ta gyada masa kai
jikinta na ci gaba da rawa, ya daga ta xae
kwantar da ita kan gadonta ta fasa masa
ihu a gigice tace "wayyoo ni ka kai ni
dakinka, xafi nake ji," duk ta rikitasa ya
dauketa da sauri ya bude dakin ya fita, sae
kuka kuwa take jikinta na rawa, safeena
dake fitowa daga dakinta knn ta bisuda
kallo xuciyarta na bugawa "kai wayyoo ddi,
ta sha ruwan," ko kallonta Aliyu bae yi ba, ita
ko inteesar sae kuka take kmrgske, ya
kwantar da ita kan gado bayan ya kunna AC
yana kallonta yace "ina kika ce ke maki
ciwo," a hankali tace "ya daina, wanka
kawae xanyi da ruwan xafi," ya shiga
bayinsa da sauri ya hada mata ruwan, yana
shiga ta mike har tana tuntube ta fice daga
dakin da sauri suka kusan cikin karo da
safeena dake labe bakin kofa, safeena ta
koma baya a tsorace tayi xaton Aliyu ne,
inteesar ta watsa mata harara tace "an dae
ji kunya," tayi tsaki ta bude kofar dakinta da
sauri ta kwashe magungunan kan gadon ta
xuba su cikin handbag dinta jikinta na
rawa, tana xuba su ta fice da sauri taga
safeena tsaye har lkcn kwakwalwarta a
jagule to ko bashi tasha bane, inteesar ta
wuce ta ta shige dakin Aliyu, dae dae nn ya
fito ya tsaya kallonta da mamaki, xae yi
magana ta rigasa "ruwa, amm ruwa naje
sha," yana mata mugun kallo yace "get out,"
ta yi kmr xata yi kuka ya daka mata tsawa
"ni kike raina ma hankali ko, fitar min a daki
munafuka," tayi tsaki ta juya ta fice daga
dakin tare da sauke ajiyar xuciya. Bata samu
shan maganin ba ranar da daddare har tayi
bacci don ido Aliyu ya sa mata, washegari
sunday yana gida yana xaune dakinsa
na'ura gabansa, safeena ko na daki kwance
abun duniya ya isheta, inteesar ta gama duk
abinda xata yi da kyar don xaxxabi ne ssae
tare da ita, ta rufe dakinta da makulli ta ciro
maganin da likitan ya bata jiya ta debo ruwa
a bathroom don har lkcn ba ruwa a dakinta,
ta xauna kusa da gado, ta fiffito da
magungunan daga kwalayensu ta daddauki
yanda yace mata, ta tsura ma kwayoyi
shiddan dake hannunta ido, ita bata ma
taba ganin irinsu ba, ta rumtse idonta ta
xuba su a bakinta ta kora da ruwa da sauri
ta hadiye su.
TAMMAT ALHAMDULILLAHI.
No comments