Recent Updates

Hakki Na 7

 


🌸🌸🌸🌸🌸

    *HAƘƘI NA*

🌸🌸🌸🌸🌸



 By

_jiddah S Mapi_



*Chapter 7*


*Littafin haƙƙi na na kuɗi ne, 300 ne kacal kiyi transfer ta account nawa 6037523268 hauwa shuaibumapi keystone, turo katin shaidan biya ta nan 08144818849 sai na saki a group ɗin da zan rinƙa posting kullum*



              ~Yana kwance a gefen inna har tayi bacci ta farka, bayan ta farka taji cikin ya É—anyi sauki tashi tayi lokacin mangrib yayi, alwala taje tayi kafin ta dawo ya shimfiÉ—a mata sallaya, salla ta tada saida ta idar ta kalleshi gaba É—aya yayi shiru da alama yana tausaya mata ne "tashi kaje É—akinka kayi wanka kayi salla ina nasirun?"

da hannu yayi mata nuni da yana É—aki yana salla, inda sabo ta saba da halinshi yanzu ya buÉ—e baki yayi mata magana yake ganin aiki ne, ta girgiza kai kawai tace "je kayi salla"

tashi yayi ya tafi É—akinshi, alwala yayi yazo ya tada salla, saida ya idar yace "kaci abinci?"

nas wanda yake shirin tafiya yace "tun É—azu"

"acici"

"oho dai"

rakashi yayi har kofa kana ya dawo ya koma É—akinshi, baiso yaga inna cikin tashin lafiya, yafi son ganinta cikin kwanciyar hankali babu abinda yake damunta, yasan idan inna ta mutu to shima ba zai daÉ—e ba zai bita, wani lokaci idan batada lafiya har rokan Allah yake ya maido cutan kanshi ya cire mata.


haneefa cikin kwana uku tana hanyan zuwa wajenshi siyan rake, idan ta siya wa driver take bawa sabida bata sha, yauma tayi shiri cikin riga da wando tasa dogon hijabi da facemask taje, yana ganinta ya É—ago kai yana murmushi, zuwa yanzu ya fara sabawa da ita, cikin sakin fuska tace "meyasa baka kirani ba tunda banzo da wuri ba?"

hannu yasa a kunne ya kama a hankali yace "sorry"

murmushi tayi ta zauna a gefenshi tace "yau sanda biyar zaka bani"

shiru yayi yana jerawa a leda, saida ya gama yace "duk ke kikesha?"

jijjiga kai tayi kana cikin shagwaɓa tace "duka mana"

ido ya zuba mata ganin yadda shagwaɓa yayi mata kyau sosai, sai kuma ya ɗauke kai yace "ya miki yawa ai"

"a,a nikam baimin yawa ba, ko zan iya shanye duka na wajennan"

dariya yayi jin abinda ta faɗa, ido ta zuba mishi tana ganin yadda gefen kumatunshi yake lotsawa, bata taɓa ganin wanda dariya yayi mishi kyau kamar shi ba, ta kai 10mins tana kallonshi, ganin kallonshi take ya mike yana cewa "to shanye mu gani"

yau taji daÉ—i tunda ya sake sukayi hira, duk zuwan da take baya sake mata fuska sosai, sai yau taga yana mata dariya, kallon agogo tayi sannan ta kalli inda motan yake a fake "na tafi idan na dawo next time zan shanye"

murmushi yayi haka kawai yakejin daÉ—in hira da ita kamar karta tafi, jameel ne yazo wurin yayi sallama yana kallon haneefa wacce take shirin maida facemask, hannu ya mikawa anwar suka gaisa, yace "ya dai? ya jikin inna?"

"da sauki jameel"

haneefa ta gaisheshi ya amsa cikin sakin fuska tareda kallon ledan hannunta yace "wannan raken duk naki ne?"

giÉ—a kai tayi tana murmushi tace "eh"

kallon anwar yayi yasa hannu a waist yace "kai kuma saika bata? ina zata kai wannan raken?"

taɓe baki yayi alaman shima bai saniba, yayi dariya yace "to wannan matan akwai shan zaƙi daga ganinta"

hannu tasa a fuska tana dariya sosai, tsokananta yayi tayi tana dariya, yau kaÉ—ai har sun saba dashi, tace "na tafi"

"to asha kaÉ—an fa kada ya saki ciwon ciki"

dariya kawai tayi sannan ta wuce, anwar ya zauna yana kallon jameel yace "ya dai? ya jikin Abba?"

"toh da sauki"

jikinshi yayi sanyi

"Allah ya bashi lafiya"

"ameen".


Haneefa ta koma gida kamar kullum ta bawa masu gadi raken kafin ta wuce ciki, noor tana zaune a falo itada momy, ta É—aura kai a cinyan mami tana mata tsifa, a hankali ta murÉ—a handle É—in ta shigo fuska É—auke da murmushi, wajensu ta karasa ta zauna, noor ta bita da kallo haka kawai taji bata yadda da inda haneefa taje ba

"sannunku da gida"

"ya ankon an É—inka?"

ciro leda tayi ta nuna musu ankon an É—inka mata dogon riga na zuwa dinner, momy tace "ga É—inkin yayi kyau"

noor dake kwance ta tashi tana kallon É—inkin, kirjinta ne ya bada sautin dum ganin dusan rake a kasan kayan, da mamaki ta kalli haneefa tace "meya kawo rake jikin sabon kaya?"

haneefa tasa hannu ta cire sannan tace "a shagon É—inki ne"

tana faÉ—an haka ta maida kayan keda ta wuce É—aki, noor taji jikinta yana tsuma meke faruwa? kwanan nan saide taga haneefa ta fita ta dawo kuma tana murna tana farin ciki, ba shakka wurin wannan me raken take zuwa, ji tayi kamar ta aza hannu a kai tayi ihu, waya ta É—auka ta kalli Momy tace "ina zuwa"

momy tace "okay"

fita tayi daga É—akin ta wuce can wajen garden, wayan ta cire ta kira wani number, ana É—agawa tace "zan baku task"

amsa mata yayi da "to"

kwatancen me raken tayi musu tace "gobe nakeso ku kamashi ku koya mishi hankali ya fita a harkan haneefa, kunada 2million idan kun gama"

kashe wayan tayi, ta rike a hannunta tana jujjuyawa, saita koya mishi hankali, banda ma rashin hankali da rashin wayo ina haneefa ina wannan bakauyen?.

komawa ciki tayi kaman ba abinda tayi ta kwanta momy taci gaba da kwance mata kitson.


haneefa tana shiga ciki ta kwanta akan gado ta lumshe ido tana tuna yadda ya sake da ita yau yayi hira abin ya birgeta.


da dare noor ta kalleta tace "gobe za'a kawo lefen unty elham?"

jijjiga kai tayi "eh gobe ne zamuje ai idan mun dawo daga school"

"Allah ya kaimu"

wayan noor ne yayi kara ta kalli sunan da sauri ta ɓoye ta mike ta shiga toilet, cikin kasa da murya tace "ya?"

"done"

murmushi tayi sanyi tace "good ku rikeshi har sai nazo"

kashe wayan tayi kana ta koma cikin É—akin fuskanta da murmushi ta zauna, kallonta haneefa tayi "why are you happy?"

girgiza kai tayi "ba komai"

layin anwar ta fara kira, shiru bai É—aga ba kusan 3miss calls, sharewa tayi tasa a caji, fuskanta ba annuri taja bargo ta kwanta, wani irin daÉ—i noor taji ganin yadda yanayin haneefa ya canja alama bata sameshi a waya ba.


washe gari, da sauri haneefa ta shirya kamar yadda ta saba, noor tana kallonta itama har ta shirya suka fito, kamar kullum yauma breakfask sukayi a tare, tana kallonta ta kasan ido yadda take sauri tana cin abinci, murmushi take a ranta wanda ita kaɗai ta san ma'anarsa, bayan sun gama suka yiwa su Abba sallama kana suka fita, shiga mota sukayi driver ya jasu, suna hawa titi haneefa ta sauke glass, bayan sun iso ta inda yake zama ta fara lekawa domin ganinshi, wani murmushi tayi na jin daɗi ganin yana bawa mutane rake yana karɓan kuɗin, dawo da kanta tayi cikin motan tana cigaba da yin murmushi, a tsorace noor ta kalleta sai kuma ta leƙa, ganinshi a zaune yasa taji gabanta ya faɗi, ba sun saceshi ba? ya akayi ya fito?

waya ta ciro daga jaka tayi typing message ta turawa numbern data kira jiya "wa kuka kama?"

ba jimawa ya tura mata "shi wanda kikace mu kama"

"É—au hotonshi ka turon yanzu ta watsapp"

buÉ—e data tayi tana jiran hoton, da sauri ta shiga ciki tana duba hoton da aka tura mata, hannu tasa a baki tana zaro ido ganin hoton wani tsoho yana zaune a galabaice da alama yunwa yayi mishi katutu, ga zufa gashi a useless wuri, da sauri tace "bashi bane ku sakeshi, meyasa bakasa hankali idan an baka task?"

hakuri ya bata, ta kashe wayan ranta kamar wuta, wani kallo ta aikawa anwar wanda yake murmushi yana miƙa ledan rake, da haka har suka wuceshi, suna isa school ta buɗe motan da kanta ta fito ba tareda ta kalli haneefa ba, shiga class tayi ta samu Anee ta zauna gefenta tana huci.

dafata tayi ta É—an juyo, da ido ta mata alama da "ya dai?"

girgiza kai tayi dan wannan abin kunyan batasan ta yaya zata fara mata bayani ba.


wasa-wasa kullum sai haneefa sunyi waya da anwar, tun baya sakewa har ya fara sabawa da ita, yanzu kam wani lokacin shi yake kiranta, sun fara shaƙuwa har haneefa ta fara nuna mishi alamomin soyayya, noor bata nuna mata tasan suna tare dashi, domin idan tayi hakan duk abinda tayi mishi haneefa zata gane da wuri, ita kaɗai ta san abinda zata shuƙa mishi saiya tsani kanshi da kanshi.


zaune take akan stool tana gyara ɗaurin ɗankwalin da aka ɗaura mata, musamman Momy ta kira musu me makeup da ɗauri domin yau ake dinner ɗin elham, haneefa ce ta shigo tana waya tana murmushi, kallon noor tayi wacce tayi kyau cikin dogon riga maroon ɗinkin fited gown, kwalliyan ya maidata kamar ƴar tsanar roba, tayi kyau har ta gaji da kyau, itama haneefa tayi kyau cikin ankon da yake purple ne itama tayi ɗinkin fited gown, kashe wayan tayi tana kallon noor da murmushi a fuskanta tace "ban yadda ba ki goge makeup ɗin nan kada kifi ƙawata kyau"

dariya tayi kana tace "to ai kin fini yin kyau kece zaki goge"

matsowa tayi wajenta tasa hannu tana goge mata bakin eyeshadow daya ɓata mata saman ido kaɗan, saida ta gama tasa hannu biyu ta dafa kafaɗanta, kallonta tayi tace "noor inaso faɗa miki wani abu"

kallon cikin idonta noor tayi, sai kuma taji gabanta ya faÉ—i, ba dai labarin wannan kazamin zata bata ba?

da sauri tasa hannu ta cire hannunta daga dafata da tayi, murmushi tayi ta diro daga kan stool É—in, tazo ta bayanta ta rungumeta tareda zagaye hannunta ta cikinta, "sis we're late, kece bestfreind ya kamata ace yanzu kina wurin"

jijjiga kai tayi "okay let's go, we will talk later"

sakinta tayi suka É—au mayafi, kowa ya É—au wayanshi da jaka, dogayen takalmi suka sa yayi musu kyau suka fito, ido momy ta zuba musu ba ko kyaftawa, yadda taga sunyi kyau, batasan time É—in da suka karaso wajenta ba, noor tace "momy kallonfa?"

hannu tasa ta mareta a fuska kaÉ—an tace "kaniyanki"

addu'a tayi ta shafa musu domin gudun bakin mutane da mayu, "banda rawan kai, ku nutsu a duk inda kuke"

giÉ—a kai sukayi a tare sukace "tom momy mun tafi"

hannu ta É—aga musu "no faruk ne zai kaiku"

waro ido noor tayi "waya gaya mishi momy? gaskiya a bari driver ya kaimu.."

shiru tayi ganin yana saukowa yasha blue black na wani tsadadden yadi sai sheƙi yake, fuskanshi yasha gyara ga sajenshi da yake a kwance lub, hannunshi rike da makullin mota da wayanshi, har ya sauko ya karaso haneefa tana kallonshi, gaskiya bro faruk ajin karshe ne a kyau saide bai kai anwar ba, sallama ya yiwa momy sannan ya wuce gaba, binshi sukayi sum sum, noor ba dan taso ba, babban compound nasu suka tsaya suna kallon motan daya shiga, murmushi noor tayi domin motan yayi mata, a tare suka karaso haneefa ce a gaba sai ita noor a baya, fita sukayi yana tuƙi cikin kwarewa har suka hau titi, babu me magana cikinsu ganin shiru yayi yawa ya kunna waka na turanci, bin wakan noor ta fara a hankali tana lumshe ido, bakin babban hall ɗin da aka tanada domin yin shagalin bikin ya tsaya, hon yayi aka buɗe mishi get, ya shiga ciki tareda yin parking a cikin tulin motocin da suke wajen, fitowa yayi itama haneefa ta fito, noor ma ta fito tana ɗaukan jakanta, kallonsu yayi kana ya wuce gaba, binshi suka fara a baya, noor da ba dan taso ba, ita ta manta ma yah faruk abokin ango ne, cikin nutsuwa suke tafiya har suka isa cikin hall ɗin inda ake gudanar da shagali, ido ne ya dawo kansu lokacin da mutane sukaga sun shigo, murmushi suka fara har suka isa inda aka tanada domin baƙi, Elham ta ɗaga musu hannu tana gefen mijinta tayi kyau har ta gaji kyau, sai glowing take makeup nata da ɗaurin sunyi kyau sosai, manyan mutane ne a wajen daga abokan ango har kawayen amarya, sannu da karasowa aka yiwa babbar kawar amarya wato haneefa, sannan mc ya kirata itace zata bada biography ɗin amarya, haneefa bata son cikin mutane tana ji yana kiran sunanta ta rike hannun yah faruk wanda yake danna waya, ɗagowa yayi ya kalleta, ta marairaice tace "bazan iya zuwa ba ido yayi yawa"

murmushi yayi yasan batason ido, da noor ce data tafi har ta fara, riko hannunta yayi kana ya mike ya fara tafiya da ita, a tsakiyan har tsakiyan fili ya kaita kana yace "ki nutsu kamar babu me ganinki haka zakiyi"

jijjiga kai tayi, ta karɓi mick ta fara da godiya wa ubangiji bayan tayi musu sallama irin na addinin musulunci, cikin nutsuwa ta fara bada biographyn amarya, harshen turanci take magana kamar ƴar kasar america haka take fitar da kowane harafi, tsit wurin yayi sai video ake mata har zuwa time ɗin data fashe da kuka tana cigaba da bada labarin elham wacce ta kasance babbar kawarta, jikin kowa yayi sanyi harda ya faruk da yake zaune a gefe, yadda take kuka tana sunkuyar da kai ya bawa mutane tausayi sosai, a hankali tayi sallama kana ta kai mick ɗin tana share hawaye, tafi akayi mata, kanta kasa har ta karasa inda noor take, hannu tasa ta riko hannun noor, murmushi tayi kana tayi mata raɗa a kunne "gaskiya kin birge na tabbata yau zaki samo mana ɗan babban gida, wow wa yaga noor tana bada biographyn unty haneefan ta"

gaban haneefa ne ya faÉ—a jin abinda noor ta faÉ—a, É—an babban gida?

signal tayi mata tareda kashe ido É—aya tace "Allah kuwa"

sakin hannunta haneefa tayi sannan ta juya ta ciro waya tana duba sakon daya shigo, murmushi tayi jin yace zaizo su gaisa"

dama ita ta tura mishi sako yau ba zatazo siyan rake ba yazo waje kaza suna bikin kawarta  yazo su gaisa, tayi farin ciki da yace zai zo.


ci gaba akayi da gudanar da gagarumin biki, akasa waka noor ta tashi taje tana rawa cikin nutsuwa tana dariya, ɗaga kasan rigan take wanda takeji yana damunta fafaren kafanta suka bayyana cikin bakin kyakkyawan takalmin ta, tana cikin rawa taga Yah faruk yana mata video, a hankali ta karasa wajenshi ta riko hannunshi, kallon abokinshi yayi ya taɓe baki fuska a sake har suka isa fili, rawa ta fara tana rike hannunshi, shima ya biye mata suna rawa, abin ya birge mutane harda amarya suka shigo suna musu liki, kallon haneefa wacce ta zauna tana dariya tana video tayi, taje ta kamo hannunta, tana tirjewa har suka isa filin, ya zama su uku ne, ya faruk ganin haneefa ta tsaya kawai tana kallon kasa yasa hannu ya riko hannunta, rawa ya fara sata yi, nan ya saki jiki da kannen nashi suka rinƙa rawa, noor kana ganinta kasan tana cikin farin ciki domin yaune ranan farko da suka kasance da ya faruk ya sakar musu fuska har suna rawa, mutane sai liƙi suke musu abin ya birge kowa, a hankali amarya da ango suka shigo suma aka fara rawan tare, wayan haneefa ne yayi kara, ta juya tana kallo, ganin sunan Anwar yana yawo a gaban wayan ta juya taga ba me kallonta sannan ta sulale ta fita daga hall ɗin.


noor ce ta bita da ido tana cigaba da rawa tareda amarya, yi tayi kamar zata bita Elham ta rike mata hannu tareda girgiza kai, murmushi tayi suka cigaba da rawan, sun cashe har sun gaji da cashewa, mc yayi musu godiya a hankali suka koma wajensu kowa ya zauna, noor tana latsa waya wani mutum da baƙin kaya da glass yazo wajenta, alama shi ɗin guard ne, cikin girmamawa ya bata waya tareda cewa "ranki daɗe gashi zakuyi magana da Aliyu ɗan gidan tsohon shugaban kasa, zai miki message saboda hayaniya ba zai bari kuyi waya ba"

"alright"

ta faɗa tana karɓan wayan, message ne ya shigo _barka da warhaka, I'm Aliyu Ahmad banga, sorry for disturbing, naga yayarki haneefa ina sonta kuma so da aure, can you please talk to her, inaso muyi magana before I go"

"okay but ta fita saide mu sameta a waje?"

ya amsa da okay, kallon guard É—in tayi "kayi mishi iso"

tafiya yayi daga wurin ta bishi da ido har ya karasa inda Aliyun yake, matashi ne kyakkyawa jikinshi kamar chocolate, daga kayan jikinshi kasan wannan ɗan gidan masu muƙami ne, tashi yayi guard ya mishi iso har zuwa wajenta, hannu yayi mata alama da "barka dai"

murmushi tayi kana ta mike suka nufi waje, ji take kamar tayi tsalle don ba wanda ya kaita son ganin haneefa da manyan yara musamman maganan aure ya shiga.


suna fita a hall É—in yace "ya sunanki?"

"noor"

"nice name itafa yayar taki?"

"haneefa"

"wow haneefa"


"ba zan ɓoye miki ba ina son yayarki har cikin raina, kallo ɗaya na mata naji a raina na samu matar aure, I hope babu wanda yake ciki da maganan aure?"

fuskanta da murmushi tace "eh babu saboda this year zata gana secondary"

tsayawa tayi tana lekawa ko zataga haneefa.


haneefa kuma tana fita ta amsa wayan yace "ina bakin get"

fita tayi har zuwa bakin get ta samu me gadi tayi mishi magana da ya shigo dashi, shigowa akayi da Anwar wanda yayi kyau cikin yadi coffee, ba yadi ne me tsada ba kana gani kasan me arha ne, amma yaji guga kuma ya mishi kyau, sajenshi ya yiwa gyara wanda ya kara fitowa da ainihin kyaunshi, cikin nutsuwa yake tafiya har ya isa inda take, kallonta yayi tayi kyau sosai, lumshe mata ido yayi wanda ya zame mishi ɗabi'a, shagwaɓe fuska tayi "ba zakace nayi kyau ba?"

murmushi yayi "kinyi kyau"

kallon agogon dake É—aure a hannunshi yayi, so yake ya wuce gidansu jameel domin yace jikin Abba ya tashi, a hankali ya É—ago da tsumammun idonshi masu tafiya da zuciyan mutane yace "na gaisheki zan koma"

da sauri ta kalleshi, baki ta turo kana ta fara haɗa fuska cikin murya me cike da sakalci da shagwaɓa tace "nidai ba zaka tafi yanzu ba, yaushe ma kazo?"

kallonta yayi bai taɓa ganin wacce shagwaɓa ya yiwa kyau kamar ita ba, saita koma mishi kamar wata yarinya ƴar shekara 3, haka kawai ya tsinci kanshi da cewa "to bari na kara minti goma"

murmushi tayi kana tace "to muje ciki"

"a,a ba zan shiga ba mu gama gaisawa a waje"

jijjiga kai tayi kana tace "to mu karasa can"

tafiya suka fara a jere tana kallonshi, shi kuma yana kallon agogo, a compound suka tsaya inda aka ajiye motoci, ya tsaya yana kallonta, tsalle tayi ta zauna kan wani kyakkyawan mota red, shikuma ya dafa jikin motan a gefenta yana kallonta, ta lura bashida surutu saide yayi ta kallonta tana magana, a hankali tace "ya inna?"

"inna tana gida"

janshi take da hira banda um da um um, ba abinda yake faɗa, ganin yayi shiru ta zuba mishi ido shima kallonta yake yana murmushi, ji take kamar ta haɗiyeshi, sajenshi yafi tafiya da imaninta, ji take kamar ta janyoshi ta rungume ko zataji sauƙin abinda yake damunta a zuciya, gira ɗaya ya ɗaga mata tareda kashe mata ido yace "kallon fa?"

É—auke kai tayi "shikenan in bakaso na kalleka"

É—abi'anta yana birgeshi gata da rashin manyance, yace "sorry juyo ki kalleni"

kin juyowa tayi, a hankali ya dawo side É—in data kai kanta, zata juya yace "please"

kallonshi ta fara, sannan cikin sanyin murya tace "ko da zan kwana ina kallonka ba zan gaji ba"

daidai time É—in noor suka shawo kwana idata Aliyu wanda yake nuna mata tsananin soyayyan da yake yiwa haneefa wacce ya fara ganinta yau, da sauri tace "gata can"

tayi magana tana nuna mishi haneefa wacce take zaune akan mota ta zubawa wuri É—aya ido tana murmushi, noor batayi zaton tana tare da wani ba dan gani tayi kamar haneefan ta gaji da hayaniya ne ta fito domin samun rest.


murmushi Aliyu yayi kana yace "muje to ko zaki fara mata magana first?"

"a,a muje dai batada matsala"

tafiya suka fara har suka isa inda haneefan take, noor ta É—aga mata hannu tace "hane..."

yawun bakinta ne ya kafe lokacin da taga ya É—ago yana kallon haneefa, da sauri ta koma baya ta kasa sauke hannunta, bakinta buÉ—e ta kalli Aliyu wanda ya zuba musu ido yana kallon yadda suke kallon juna.


hannu yasa a ido yana murzawa dan ji yayi kamar abu ya faÉ—a, da sauri tace "meya sameka?"

idon har ya fara ja yace "ba komai ji nayi kamar abu ya shiga"

bata san lokacin datasa hannu ta riko hannunshi ta matso dashi kusa da ita ba, hannu tasa ta cire hannunshi da yake murza idon dashi, buɗe mishi idon tayi a hankali ta kai bakinta, ta fara hura mishi iskan bakinta, ji yayi jikinshi yayi wani sanyi, jiyo ƙamshin turarenta yasa wani kasala ya sauko mishi, ya rasa kasalan na menene, kamar shauƙi yakeji akanta, tana hura mishi iskan bakinta har taga idon ya daina hawaye.


noor ta runtse ido, Aliyu ya juya baya ganin yadda sukayi kusanci sosai, kallon noor data runtse ido yayi sannan yace "dama tana da wanda take so?"

kasa magana tayi har yanzu idonta a rufe, juyawa yayi "thanks"

buÉ—e ido tayi tana kallonshi har ya kira waya, guard nashi suka fito, buÉ—e mishi wani lafiyayyen rantsatsen mota akayi, har ya shiga suka tafi noor ta kasa magana, a hankali ta juya ta koma ciki, a cikin motan da suke kai aka kawo amarya, elham tana ganinta ta É—aga mata hannu alaman tazo, jikinta kamar wuta har wani rawa jikin yake, taje ta durkusa domin Elham tana high table ne, a kunne tace mata "zan baki makullin mota kije gida ki amso mana sauran snacks É—in"

girgiza kai tayi, ta bata makullin tareda mata kwatancen motan, tabbas shine wanda su haneefa suke kai, a zuciye take tafiya har ta fita zuwa waje tana kaɗa makullin a hannunta, tana fita ta raɓa a hankali ba tareda sun ganta ba ta buɗe motan ta shiga, rufewa tayi a hankali kana ta cikin glass ta kalli haneefa wacce ta tsareshi da ido tana zuba mishi sakalci da shagwaɓa, da wani irin karfi taja motan, haneefa da take kai ta zaro ido, fuskanta ya kalli kasa, noor taja motan zata bar wurin, haneefa ta tsala ihu ganin zata faɗi, kuma idan ta faɗi ba abinda zai hana hakoranta zubewa domin muguwan faɗuwa zatayi, da sauri yasa hannu ya rikota, shi ya faɗi kasa ita kuma ta bishi ta faɗa kanshi, da karfi ta rungumeshi tasa kanta a wuyanshi tana ɓoyewa domin ta matuƙar tsorata, tayi tsammanin yau zata rasa hakoranta, cikin jin zafin da yayi ya cije baki tareda lumshe ido yanajin yadda ta ƙankameshi tana cusa kanta a wuyanshi, hannu yasa zai tashi sai kuma yaji kafarshi kamar ba zai iya takawa ba, da karfi yasa hannu a ƙugunta ya riketa yana cije leɓe dan bayanshi ya wani irin sara, kallonsu tayi ta madubi, badan haneefa tana wurin ba da sai tabi ta kanshi ta take da mota, cikin zafin nama taja motan ta bar wurin, da mugun speed take tuƙi har ta fita daga wurin, haneefa sun kai 10mins a haka, saida yayi ta maza yasa hannu ya ɗagata, tashi tayi har yanzu a tsorace take shima yayi kamar zai tashi sai kuma ya koma ya kwanta dan wani azaba yaji a bayanshi, ba karamin buguwa yayi ba, hannu tasa tana ɗagashi....




*Domin karin bayani 08144818849*

No comments