Recent Updates

Al'amarin Maryam Complete Hausa Novel


AL AMARIN MARYAM* 🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻🙆🏻



📝 *FANTASTIC* *STARS* *WRITERS*

           


  *(F,* *S,* *W*)*

   


         👇

         *NA*


*RAHMATULLAH*

 *MUHAMMAD*



Edited by! 

    Mmn khairat 


           

    1⃣



        *BISMILLAHIR* *RAHMANIRRAHIM*



~wannan~ ~qirqirarran~ ~labarine,~ ~banyi dan cin xarafin wani ko wata ba, cin karo da rayuwar wani ko kamanceceniya da yanayin rayuwar wanine wannan~ ~"arashine~

  


''Wasu Yarane guda biyu mata, na hango  a tsakar gidan, sun  takure cikin filin tsakar gidan,  daga can lungu   babu kowa saisu,


Yar babbar bazata fi shekara goma ba   xuwa sha daya, while qaramar yar shekara hudu,  suna gun  Har rana ta fara zafi,   garin ya fara dan zafi zafi, suna takure a wurin,  can  naga wata mata ta fito   ta dubi shashin da yaran suke   ta hade rai,, tace ke fati!  dan munafurci kunanan zaune a wurin nan  salon ki jawowa mutane magana?   Yarinyar da aka kira da fati  ta dago cikin firgita, saboda jin muryar matar da ta kira sunanta,  tace a a  Umma, 

anty ce tace mu fito xata gyara dakinta,  oh...  ta furta tare da yin gaba,  

wacce aka kira da Fati   tai saurin dauke kan qaramar yarinyar daga kan cin yarta, 

tare da cewa Mimi xauna  naje na karbo miki magani gurin Umma, ta miqe tabi bayan umman, tana xuwa  akofar kicin din ta tsaya, cikin jin tsoro,,  tace Umma Mimi ce bata da lfy,   jikinta da kanta yayi xafi  sosai, dan Allah idan kinada magani ki bani  na bata,  umma ta  watso mata harara,  tace to uwar kinibibi,  nida kikaxo wurina kika fadamun chemist gareni?   Ko ni na dora mata ciwon?   Sai ki bari  idan ubanku ya dawo ki fada masa, taja tsaki tace  wuce kiban wuri, fati tace toh 😔    sannan ta koma gurin yar uwarta  ta tallafo kanta ta mayar a cinyarta ta kwantar,   tare da cewa Mimi yi hakuri  kinji  Baffa ya kusa dawowa,  zai kaiki chemist    kinji? 

           

    '' a Haka suka yini a tsakar gidan,  duk inda inuwa take sai su koma can, idan wannan inuwar ta jaye su koma wannan   har xuwa sallar magriba,  Kuma sai lokacin ne  Baffansu  ya shigo gidan,  direct dakinsa ya shiga,  fati da tun rana take dakon shigowarsa   tayi saurin binsa, ta durqusa har qara   tace Baffa sannu da xuwa,yace  yawwa fadimatu, sai tace  Baffa dama Mimi ce bata da lfy,   zazzabi take da ciwon kai,  Ya dago ya kalleta cikin rashin fahimta, 


yace  wacece kuma Mimi? 


 Can ya nisa... sannan yace  au  wai  MARYAMU kike nufi?  Tace eh  Baffa,  sai baffa  yace  wai  yarinya da sunanta  kun saka mata can wani  sunan banxa,  sunan gunki,   yace  tafi gurin ummanku  idan tana da magani ta bata,  sai fati tace  Baffa tun daxu na tambayeta  tace  bata dashi. 

Sai yace  toh  jeki gurin antyn ku,   ya fada tare da shigewa cikin bedroom dinsa,  saita tashi ta tafi  gurin anty, Koda taje gurin daya matar gidan  wacce suke kira da Anty,  ta fada mata saqon Baffan   xaginta ta dungayi, ta uwa ta uwa,, 


kamar wata sa'arta,  kuma dama can tafi tsanar yaran  da saurin daukar xafi akansu ,  yayin dasu kuma suke bala'in tsoronta  tamkar mala'ikan daukar rai,,  da gudu tabar gunta  tadawo ta rumgume   Mimi wacce jikinta ya qara xafi,  ko tuwon da aka miqo musu Sun kasa ci,  duk ta rikice ta shiga damuwa  sosai  sbd halinda Mimi take ciki,  Sam fati takasa  cin tuwon,    


 mimi kuma sbd zafin ciwo  ko bude idonta takasa yi balle taci abinci, 😔

 

          '' Wararen 8:30 pm fati taga jikin  Mimi yayi tsakani, kuma babu wanda keda niyyar taimakonsu  a cikin gidan nan,   hakan yasa  ta goya mimi  ta fita waje,  tana tafiya  cikin anguwar kadan  kadan,  tana cikin tafiya ta  hadu da Ahmad,  (wani maqocinsu ne wanda baifi 15-16 yrs ba) ya tsayar da fati , tare da cewa... Fatima Mesa kika fito a wnn lkcn?  Ta share wahayen dake  fuskarta, sannan tace Mimi ce bata da lfy,  kuma nakasa samun  magani a gidanmu,

 yace to yanxu ina xaki da ita?  Tace chemist xan kaita,  sai yace to kinada kudi  a hannun ki? Tace a a   fadane tana xubar hawaye,  to yi haquri muje inada kudi danake tarawa na makaranta danake ragewa Ina ajiyewa, muje saimu kaita  chemist,  tace to   ya karbi mimi ya dorata a kafada suka qarasa chemist,   mai tsaron chemist din ya dubata   tare da yimata allura,  sannan ya bata magunguna, suka bashi kudi  har suka samu raguwar  canji, dake  lokacin duniya na kwance,  ya rakasu  Har cikin gida,   tare da ledar maganin, 

ya bawa fati sannan ya juya, tayi masa gdy,   ta zauna  ta bude magunguna ta bata kamar yadda yake a rubuce,  sannan suka nemi gurin kwanciya,  Tym to tym fati takan tashi ta duba ta   tataba jikin Mimi, har saida taji  jikin Ya danyi sanyi, sannan tasamu nutsuwa,  daganan bacci yayi awon gaba da ita  tana mai godema Allah, 





~*Mrs* *Muhammad*~ 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🌷AL 'AMARIN MARYAM 🌷

            3⃣

       Fadima xaune ita da yar uwarta khadija wacce take kira da Adda Khadija,  suna tattauna batun auran fadimar da ake shirin yi,  Khadija ta dubeta nidai na fadawa Baba ya qara jaddada masa maganar karatunki kya samu sauqin wani abun inkina ficewa kina barin gidan, ta danyi murmushi ta Kalli Adda Khadija,  Adda dan Allah kar kubari auran nan ya dau lokaci saboda wlh na matsu na koma kusa da yayana Kullum cikin mafarkinsu nake acikin mummunan yanayi.  Khadija tace to fadima in shaa Allah baxai wuce sati ba. 


         Jamila (anty)  kamar yadda yaran gidan ke kiranta  xaune kan kujerar roba a tsakar gida ta harde qafa tana bawa fati wacce ke wanke wanke order, yarinyar jikinta sai rawar sanyi yake ga kuma uban tsoron antyn da takeji uwa uba jibgin wanke wanken da yafi qarfinta gashi koyaya tayi kuskure ko avunda bai gamsar da Anty ba sai ta dako mata tsawa tare da xagin uwarta har ubanta na kabari bai tsiraba daga xagin anty,  ana cikin hakane  Baffa ya shigo gidan da yake yau juma 'a baya fita da wuri sai an sakko daga masallaci. Ya dubi fati sannan ya Kalli shashin da jamila take yace ya haka?  Ina sauran yaran gidan?  Duk wannan aikin ita kadai?  Eh ita xatai ta furta cike da isa,  ko kana nufin ban isa sata aikin bane?  Kafin yakai ga furta wani abun Umma ta fito daga dakinta kamar anjehota ta tsaya tana watsawa mijin nasu harara cike da takaici sannan ta furta kema dai jamila,  ai sabida tsinanniyar uwarsu ta amince da maganar auransa shiyasa yake wannan abun,  ai wlh kaji kunya matar qaninka xaka Aura dan cin amana, itama shegiya yar akuya ta kwanta da qani yanxu tana harin kwanciya da yayansa.  Jamila tayi saurin katseta dakata Hajara itafa bata da laifi, saboda yayanta ta amince da auransa tunda ya hanata yayanta da yabata su ai da ai hakaba,  dama tun dan uwansa na raye yake qulafacinta shiyasa da dan uwan ya mutu ya fake da cewa bazaibar yayan dan uwansa suyi agolanci a wani gidanba,  inkuma tanasan xama da yayanta taxo gidansa a matsayin matar aure ta zauna dasu.  Baki Baffa ya bude jin sharrin da jamila tai masa na cewa yana qulafacin matar Al amin tun yana raye, ransa yayi mutuqar baci da wannan maganar  hakan yasa yace wlh duk matar tada kuma fadar wata magana kuma naji akan aurannan wlh saina saketa.  Sannan ya juya batare daya shiga dakin da yayi niyyar shigaba yayi gaba.  Tsit sukayi saida suka tabbar ya fita sannan jamila ta furta andaiji kunya raqumi ya shanye ruwan dan tsako,  Hajara kuma tace ke kuwa anga jar mace shiyasa yaketa wannan bare baren. (yan iskan qarya da kufada mana agabansa 😂).


      Tun bayan amincewar fadima da auran Baffa yayanta suka kuma shiga takura har abunda ba ayi musu ada yanxu anai musu kamar hanasu abinci da duka xagi kuwa ba a magana domin da yana fitowa da jikinsu ya cika taf da xagi. Yanxu ma hakace ta kasance fati na duqe tana wanke wanke kamar yanda aka dora mata safe da yamma,  Mimi tace yaya fati xanyi fitsari tace to Mimi matsacan kiyi ta nuna mata nesa da inda take wanke wanken tatafi taje ta tsuguna, itadai batasan yanda akaiba sai jitayi anyo jifa da Mimi cikin kayan wanke wanken ta dago a firgice yayin da mimin tasaka wata uwar qara cike da azaba da firgita Zainab ce tsaye akansu tana huci, tace da fatin ke dan kutumar ubanki acikin kayan wanke wanke xakisa tai masa futsari saboda ke jakace? Tace a a anty Zainab wlh acan gurin tayi ba a cikin kayan ba, Zainab ta tsinketa da mari tare da furta qarya nai miki kenan?  (Zainab nada daga cikin yan matan gidan kuma yace a gurin amaryar gidan wato anty)  hayaniyarsu ce ta fito da mutan gidan, Anty Adawiyya ke tambayar meyafaru Zainab ta mayar musu da inda akai, anty tace yayi kyau gara da kika hukuntata ita kuwa umma ko hmm bataceba ta juya daki hakama ragowar yaran gidan sai Adawiyya ce ta tsaya tanaiwa Zainab fadan abunda tayi, zainab cike da fitsara tace kinga malama babu ruwanki ke ko kishin iyayenki bakyayi idan uwarsu ta shigo gidannan mallake Baffa xatai kamar yadda ta mallake uncle, inba dan Umma na taka miki birki ba da ba asan abunda xaki akan wadannan mayun yaranba.  Adawiyya ta bude baki da nufin bata amsa umma dake jinsu daga daki tace wlh Adawiyya inbaki fita harkar yarannan ba saina tsine miki, inaso ki xama yar kallo a harkarsu kamar yadda kowa ya zama, ni duk cikin yayana kece bakisan ciwon kanki ba babbar banxa. 


       Haka fati ta gama wanke waken sannan ta wankewa Mimi jikinta da saboda ruwan daudar wanke wanke ya bata mata kaya tanayi tana shidewa saboda sanyin ruwan ga kuma yanayin sanyin da ake ciki,  tana gamawa tajata suka fita daga gidan,  wannan dalilin yasa koda dangin mahifiyarsu sukazo kafin kayan daki basu gansu har suka gama suka tafi, kuma basu tambayesu ba saboda gudun fitina dan matan gidan da yayansu sai yadda magana suke da waqewaqen habaici nasan a tanka musu ayi tashin hankali, har suka gama gyara mata daki tas suka tafi. Bangaren su fati kuwa sai magriba suka baro gidan maqociyarsu amarya da suke shiga, tunda aka kawota take jansu a jiki kasan cewarsu yara masu gashi takurar da suke ciki tasasu sakin jiki da ita (dan ma tana tsoron masifar su zainab da babu abunda bazatai musuba) iyakacinta dasu ta kunna musu kallo ta basu abinci ko wanka tai yunqurin yiwa Mimi su zainab xasu taso mata da bala'i.  Koda suka shigo gidan babu wanda ya damu dasu balle ya tambayi daga inda suke. 



Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🌷AL 'AMARIN MARYAM 🌷

             2⃣

       Haka rayuwa taci gaba da tafiya babu abunda ya canja na dangane da rayuwar yan marayun Allah Fatima da MARYAM haka suke rayuwar kara xube babu ilimin arabi bare na boko domin makarantar bokon tuni suka dena xuwa  saboda a cewar matan gidan wai makarantar da suke tayi nisa babu me lokacin kaisu, amma nasu yayan suna da me kaisu da dakkosu makarantar islamiyya kuma har yanxu mai gidan baisamu sakasu saboda bai cika xama ba sai dare yake dawowa daga harkar kasuwancinsa bare matan gidan da suka tsani rayuwar yaran a gidan.  Lokaci xuwa lokaci fati ke fakar ido tayi wanka tayiwa Mimi saboda duk gidan babu mai yadda su daukar musu soson wanka, sai kace wasu kutare 😭, wanki kuwa ba a taba hadawa da nasu ba duk da kuwa akwai mai wanki a gidan sai dai suyi tasa kayan suna cirewa suna tarawa, ( dan ma sunada suturar) kansu kuwa wata kalba ce manya manya  da Umma tasa anty Adawiyya tayi musu saboda tun kawosu ba ai musu tsifa ba da fati tagaji da susa ta tsefe nata ta kuma tsefewa Mimi, gashi Allah yayi musu baiwar sumar kai sosai (gashi)  da Umma taga susar da suke tayi yawa tasa aka siyo fiya fiya ta bulbula musu a kansu wai a fadarta kwarkwata garesu sannan tasa anty Adawiyya daya daga cikin yayanta kuma yan matan gidan tai musu kalba, domin itace wacce bata tsananta qiyayyarsu a cikin yayan gidan,  domin duk yaran gidan kyara da hantara ke hadasu dasu mimin kamar yadda suga iyayensu nayi musu, agurin Adawiyya kawai suke samun sauqi sai ko yayan gidan maza wadanda basu cika xama ba balle har su takurasu, abinci kam basu da matsalarsa Sam domin ko almajiran gidan bazasice suna yunwa ba baresu akan basu duk sanda aka gama insuka rage  fati ta ajiyewa Ahmad inya shigo yaci,  batun rashin lfyr Mimi kuwa injiki yayi sauki saiya dawo kuma dama Mimi a halittarta mai yawan laulayice, yau da gobe tasa fati ta koyi ajiye yan kudin da Baffa ke basu kan ya fita kullum, (yakan bawa duk yaran gidan kudin kashewa kullum)  ta saiwa Mimi paracetamol ta dunga jiqa mata tana bata in ciwon ya motsa.  Cikin abunda bai gaxa wata 2 ba yaran sunyi fututu Sun rame sunfita kamaninsu Kai bakace yayan gatane adaba bazaka taba hada kamaninsu da fati da Mimi na wata biyu a baya ba, bazaka taba yarda yayan AL AMIN da FADIMA bane. 

           

            Misalin qarfe biyu da kwata na dare 2:15 am fadima kwance kan gadon dakin mahifaiyarta wacce suke kira da hajia, tana mafarki kamar yadda ta saba a yan kwanakin nan.  Kamar kullum yauma mafarkinta ya nuna mata Mimi ta fada rijiya fati kuma nata ihun a temaka a ciro mimin amma babu wanda ya kalkesu balle yayi yunqurin temaka musu, sai dai yau sabanin sauran Mafarkanta na baya, ayau sai taga AL A MIN ya ciro mimin ya kwantar a gefe ga alamu babu rai a tare da ita,  AL amin din bai furta ko kalma daya ba ya bacewa ganinta. MIMIii! Ta farka a firgice ta sunan mimin a bakinta,  ihunta ne ya tada hajia tayi kanta tana tambayarta lfy?  Wlh hajia Mimi bata da lfy dama Mimi Me yawan laulayice bare ta hadu da rashin kulawa,  nasan duk qarfin xuciyar fati baxata iya kula da Mimi ba uwa itace kawai xata kula da me lalura kamar Mimi,  tana furta wadannan maganganunne cikin tsananin kuka,  ta dora dacewa hajia ki temakeni zasu kashemun yaya anrabani da yayana ankaisu gurin maqiyana an watsar,  😭😭😭

   

        Uwar ta kamata tare da rungumeta yi haquri auta kinji kema da naki lefin da kin amsa buqatar yayan mijinki da tuni kina cikin yayanki duk uwa tana sadaukar da rayuwarta dan ta cece rayuwar yayanta.  Hajiya nasan auran soyayya ya qaremun tunda narasa Al amin, kuma naqi auran Baffa ne saboda inaganin hakan kamar cin amana ga Al amin daga mutuwarsa ko wata 3 beyi a qasa ba Na auri yayansa uwa daya uba daya?  Hajia duniya xata xageni kuma koba a fada ba wannan auran cin amanane.  Hmm yaro dai yaro ne,  fadima banda abunki ai babu abunda xakiyi mutane basu xagekiba, yayin da wani yake ganin kinyi dai dai wani tym din yake gani baki dai dai ba. Kuma inkubuta a wurin ubangijinki basai kin kubuta a wurin mutum ba.  Allah bai haramta auranki da  yayan mijinki ba yakama kijewa wannan auure kodan yayanki. Tunda takabarki ta cika a dalilin haihuwar da kikai babu rai.  Na yarda hajia wlh na amince xanje inkula da yayana bazan bari su wulaqanta ba in ina numfashi  xan xame musu uwa kuma uba.  Yawwa autata kokefa 😊 da wannan suka rufe chapter suka kwanta. 



Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 5⃣


 

NOTE : ina bawa makaranta haquri da kuskuren da nayi wajen sunan yar uwar fadima ADDA KHADIJA,  asanin sunan da tasarin labarin yazo dashi shine ADDA HALIMA. Saboda haka daga yanxu xamuji sunan ya koma Haleema memakon khadija, nagode ayi haquri 😊.


  Yau ta kama Monday Wanda yayi dai dai da kwanan fadima uku a gidan auranta, xuwa wannan lokaci bataga koda giftawar me gidan nata ba balle ya mata magana, matan gidanma babu wacce ta taba nuna tasanta balle ta bata abinci, bata damuba dan babu abunda ba a kawota dashiba na bangaren kayan abinci, da yan kudadenta da yan uwanta suka hada mata dan haka hankalinta kwance yake kamar tsumma a randa.  Tayiwa yayanta shirin makaranta tsaf cikin uniform, 7:00 ta fita ta kulle dakinta da nufin kaisu makaranta, taxi ta tara da yake awancen tym din babu a daidaita sahu, ta kaisu har cikin afoshin shugabar makarantar ta basu haqurin rashin ganinsu ta aka dade ba aiba ta fada musu mahaifinsune ya rasu, tayi mata gaisuwa ta kuma tausayawa yaran dama yaran Sun Shiga ranta saboda tsaftarsu da yalwar gashinsu,  da yake sai shida na yamma suke tashi makarantar hade take da islamiyya tace xata dawo ta daukeso, ta raka Mimi ajinsu nursery 1 sannan ta raka fati dake ajin qarshe na primary. 

       

     Da yamma ta koma ta dakkosu kamar yadda tayi alqawari, ko takan mijin nata batabi ba balle tambayarsa izinin fita, tunda ya kwada mata xaman kanta xatai a gidan itama ta quduri aniyar hakan.  Taxi na saukesu a qofar gidan ta dakko kudi da niyyar bashi saiga motar Baffa da alama dawowarsa daga kasuwa kenan daga kasuwa, ya kalleta cike da mamaki sai kuma duk ya 

diririce ya shige cikin gidan 

,atsakar gidan duk mutanen gidan na tsaye batasan dalilin tsaiwarsuba itadai ta bude dakinta ta shige. 


       Da daddare bayan isha tana tsakiyar yaranta tana koya musu home work,  Ahmad yayi sallama ya shigo, ya gaisheta cike da girmamawa ta amsa itadai tana qaunar yarannan musamman data fuskanci matsalar matar uba da yake fuskanta, uwarsa ta mutu wajen haihuwar qaninsa, mahaifinsa alh Nasir me kudin gaskene kuma dan boko  ya auri wata matar wacce ta mallakeshi tamaida Ahmad bawanta kuma ta rabashi da ubansa,  ta katse tunaninta tare da cewa Ahmad idonka kenan?  Sai yanxu?  Ko makarantar sai yanxu aka tashi?  Ya sunkuyar da kansa tare da cewa a'a mama yau hajiya ce tasani wankinta tun safe sai yanxu nagama ko makarantar ma banjeba (yana nufin matar babansa)  ta kalleshi cikin damuwa tace bakaje makaranta ba Ahmad?  Kayi kokari ka dunga xuwa makaranta inka dawo sai kai mata aikin,  ko bakaso na baka auran Mimi?  😄 inbaka xuwa makaranta bazan baka auran uwata ba,  yayi dariya tare dayin qasa da kansa yace mama ni fati nakeso, Mimi qanwatace, tayi dariya tace toooo 😄, itama fatin inbakai karatu ba bazan bakaba,  fati dake gefe tayi tsagal tace mama ni ko baiyi karatuba ina sansa a haka.  Gaba daya suka saka dariya har Mimi da bata cika dariya ba sai murmushi. Mama tagabarta masa da abinci yaci, har xuwa taran dare sannan yai sallama yatafi, mama tace da safe inyayi shirin makaranta yaxo ya karya , tai shirin bacci suka kwanta tare da yaran a kan gadonta kasancewar tai musu tarbiyyar rashin fitsarin kwance tundaga yaye suke dena fitsari, tuni sukai bacci sai ita ta rage,  taji sallama tare da shigowa cikin dakin,  ssukai ido 4 dame me gidan nata, yayi saurin sunkuyar da kanta ga alamu nauyinta yakeji,  "kixo dakina inasan ganinki yanxu " yana gama fada ya juya ya fice. Taiwa yayanta adduar bacci ta lullubesu da blanket ta dora hijab kan kayan baccinta tanufi dakin mijin nata. Koda taje bayan kwane-kwane na borin kunyar rashin kulata da halin da taga yayanta a cikin gidan, sai maganar ta dunga hada yaran cikin motar gida ana kaisu makaranta bai amince mata qara fita bada ixininsa ba,  da yake namiji dai sunansa namiji sai jin hannunsa tai a jikinsa alamu haqqinsa na aure yake nema, 🙈 tunda ya fara bata dago kanta ta kalkeshiba balle ta tayashi abunda yakeyi,  har yakai ga kwantar da ita akan gadonsa alokacin tayi yinqurin hanashi abunda yake wanda shi kuma alokacin yakai matuqa wajen San cimma burinsa hakan yasa ya samata qarfi ya fiya buqatarsa.  Tayi kuka a wannan dare kuma ta tabbatar da tarasa Al amin har abada, tun kafin asuba tabar dakin nasa takoma nata tai wanka ta kwanta. Tsahon daren intace ta runtsa tayi qarya. 


Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼



Writing & story by rahma Muhammad {hajia}



Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS 

 {F S W }


 

          Page  6⃣



      BAYAN WANI DAN LOKACI. 



        Xuwa wannan lokacin tuni fadima wato (mama)  ta zama yar gida agidan Baffa domin ta ware ta fuskaci qalubalen rayuwar dake tunkaro ta.  Yayanta Kullum suna jikinta, babu abunda ke fitar dasu gidan sai xuwa makaranta,  har Ahmad da yake qaunar yayanta shima ta jima da maidashi dan gida, tana qaunar yaron kamar ita ta haifeshi kuma tana tausaya masa kwarai da gaske,  safe har xuwa dare yana da kwano a wajenta ma ana tana bashi abinci ta dauke hidimar karatunsa tsaf kamarsu bashi kudin makaranta dinka masa uniform da kuma tilasa masa xuwa makarantar.  Da yake dan halak ne yaron, yana mutuqar girmamata da yi mata biyayya kamar ita ta kawoshi duniya.  Duk da baqar maganar da takesha a cikin gidan nacewa ta samu dan daba nata ba tayi ruwa tayi tsaki a harkarsa . Bata taba kulasuba saboda dan Allah takeyi kuma aranta takance Da da dukiya ai ba ai musu mugunta,  kuma da basai wanda ka haifa ne lallai yake jin qankaba .


         Xaman gidan Baffa xamane na kowa kansa ya sani, saboda ko su matan ajunansu ba jituwa sukeba kullum fada suke kamar masu ganin hanjin juna gasu da ido akan yayansu, baki isa koda kauda buta kisa dan wataba sai dai kisa naki.  Amma auro musu fadima da akai sai yasa suka hada kai saboda su yaqeta.  A Kullum cikin goranta mata suke me yawon aure aure ta auri qani ya mutu ta auri yayansa, gashi abun takaicin Sun koyawa yayansu wannan dabi a tayi mata rashin kunya da yi mata habaici,  yayansu maza ne dai babu ruwansu domin bazatace ga ranar da wani aciknsu yayi mata wani abu na batanci ba.  Duk sanda xatai girki a gidan babu mai tayata da koda dauke cokali ne haka xatai girkin ta gama a wahale kasancewar bata saba girkin gidan yawa ba.  Yayanta kuwa ganin idonta baisa anfasa dukansu ko xaginsu da aibatasuba,  amma abun burgewar shine bata taba nunawa tasan anai musu hakan ba balle tayi magana,  wannan ya qara baqanta ransu domin anayine domin tayi magana ko ranta ya baci,  kawai dai abunda tasani shine bata yarda tabar yayanta da qazanta ba ko yunwa ko jahilci ta tsaye musu tsayin daka akan wadannan abubuwan. Agabanta xa a dakesu kuma asakasu aikin da ko ita data haifesu bata sasuba saboda aikin yafi qarfinsu amma saita kau da kai.  A irin hakan wata rana Adda Halima yayar fadiman taxo ta tarar Anty jamila na dukan Mimi kamar xata kasheta wai kawai dan ta aiki mimin siyan omo kanti ita kuma mimin tace Mata mama tace babu kyau mata suje kanti sai dai maza, shine ta kamata tana duka Lamar ita takawota duniya babu wanda yayi yunqurin ceton mimin har uwarta dake can falonta tana dinki a kan keke tayi burus kamar ba yarta ake duka ba, sai Faty daketa kuka tana ihu tare da kiran azo atemaketa Anty xata kashe mata yar uwa. Ana cikin hakan Adda halima ta shigo gidan Kai xaye taje ta angaje jamila ta kwace Mimi tare da dauke Jamilan da Mari, sannan ta dora da cewa me wannan yar ficiciyar yarinyar tai miki kike mata irin wannan dukan?  Shiru Anty jamila tai saboda Marin da akai mata ya shigeta, sai Faty ce ta mayarwa da Adda halima yadda akai . Tace yayi dai dai akan taqi xuwa aikenki kike mata wannan dukan?  In gaskiya ne abun naki meyasa baki aiki naki yayanba?  Ta juya ta kalli ragowar mutanen gidan da suka fito kallo sannan tace wlh tlh ku kiyayi taba yaran nan, marayun Allah kun hanasu sakat,  me suka yimuku?  Magana ta farko kuma ta qarshe wlh duk Randa wani acikin ku da yayanku ya qara sa hannu akan yayan fadima wlh kotuce xata rabamu.  Tana kaiwa nan ta kama hannun Mimi da Faty tayi waje dasu ta xubasu a motar da aka kawota driver yaja suka tafi,  kotakan fadima batabi ba saboda da ranta ya baci kuma tasan fadiman najin abunda akeyi tayi shiru. 


         Bangaren fadima kuwa sukuku tayini Baffa na dawowa da magriba taje ta sameshi da kukanta akan yakaita gidan Adda halima,  ganin tana kuka yasa bai tambayi baasiba saboda ya dauka addan ce ba lfy yasata a mota suka tafi.  Koda sukaje addan kin kulata tai ta hangi su Mimi da Faty a dining Sunayin dinner tare da yaran Adda da kuma dady mijinta tuni Sun sake cikin yara da yake yawanci akwai sa anninsu acikin yaran addan. Fadima taje ta riqe hannun adda tare da saka kuka, tace yi shiru fadima aini bakimun komai ba face amanar yaya da Allah ya baki kika kasa kula dasu kuma na kwashesu inke bakiso ni inaso,  sai alokacin Baffa yaji abunda ke faruwa,  wasa wasa dai adda ta hana fadima Yaya tun ana ganin wasa takeyi har dady da Baffa sukasa baki amma ta qeqashe qasa tahana, da yake ance da uwa sai Allah koda Mimi tagamacin abinci ta kyalla ido taga mamanta ai saitai gurinta da gudu ta kwanta jikinta, da haka Baffa yace tabar yaron ta taso su tafi ta miqe ta yafa gyalenta Mimi ta riqe hannun uwarta xata bita adda ta bita ta dauketa ta saka ihu, ta ajiyeta Tare da cewa maxa bita dan gidanku uwar taki da batasan ciwonki ba tana xaune xa a kasheki tai shiru,  Faty take gefe taga suna shirun fita tace da Adda mummy nima xanbi mama,  ta riqe baki tace au kema? 🤔 to ai kun kunyatani xo kibita in ankasheku ta huta.  Da haka ta bawa fadima yayanta tare da ja mata kunne sosai. 

      

        To tundaga wannan lokaci akasamu sauqin abun domin suna shayin Adda halima sosai domin itadin bata barin ta kwana kuma tsaf Sun san xata aikata abinda ta fadadun koma fiye da haka. Tundaganan babu wanda ya qara yunqurin dukan yayan fadima sai dai kyara da hantara da xagi.  Ni kuwa nace zagi ai zagawa yake kuyi tayi 🙄.

  


Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼


Writing & story by rahama Muhammad {hajia }


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS 

 {F S W } 


            Page7⃣


   ASALINSU 

      

     Mahaifin Maryam su 2 ne a gurin iyayensu wanda suke fulanin gombe usul awani da ake kira kaltungo,  Baffa Buhari shine babba sai AL AMIN wanda yake shine mahaifin su maryam din tun suna yara qanana iyayensi suka rasu, sun taso agurin dangi har xuwa girmansu Buhari secondary skul kawai ya gama ya tsunduma kasuwanci da yake anbar musu gadon dukiya sosai,  dakadan dakadan kasuwancinsa ya bunqasa har ya kasance maxaunin Kano State saboda itane cibiyar kasuwancin arewancin qasarnan. Yana kasuwancinsa a kasuwar singa na sai da kayan abinci da kayan masarufi,  da quruciyarsa sosai yayi aure saboda kudi da yake dashi,  ya auri matarsa Hajara (umma)  kamar yadda yayanta ke kiranta. 

  

     AL amin kuma yafi maida hankali a karatu, duk da yayan nasa yaso kwarai ya tsundumashi harkar kasuwanci ya dunga gocewa har daga baya ya fahimci bayaso ya qyaleshi .

   

     Yayi karatunsa na Law anan ABU zaria ya kammala yaje Law skul dake Lagos ya dawo. AL amin matashin saurayi fari tas kyakykyawan gaske kamar yayan nasa Buhari. Ya dawo xaman gida a inda umma hajara ta dunga yimasa cushen qanwarta husna wadda take gidan a lokacin tana yiwa Umma xaman dabaro a dalilin haihuwar da tayi,  tun be ganeba har ya fuskanta hakan yasa ya dena shigowa cikin gidan sosai indai ba kamawa tayi doleba duk abunda xaiyi yana yi ne iyakar shagonsa dake qofar gidan. Saboda sam husna batai masa badan bata da kyau ba sai dan bata cikin jinsin matan dake burgeshi .


    Ta bangaren mahaifiya kuma asalin mahaifiyar su MARYAM bafulatanar ce domin iyayenta fulanin garko ne ta jihar Kano, su 9 mahaifiyarsu mai suna MARYAM (hajia)  ta haifa da babansu mal SULAIMAN guda 7 maza kuma sune manya sai Adda halima sannan Fadima wato mahaifiyar su MARYAM itace kuma auta mazaunan unguwar tudun maliki. 


     Fadima ta gamu da iftila'in rayuwa tun tana yar shekara 7 wani Mara imanin wanda ba asan ko wanene ba Yayi Maya fyade (rape)  yayi mata kaca kaca  wanda hakan ya jawo mata baqin jini a lokacin yan matancinta dan kaf saida akaiwa sa anninta aure amma ita babu labari har ta shekara 14 (kasancewar ba makarantar boko sukeba, dan mal sulaiman yayansa maza kawai ya yadda suyi ilimin boko ) a zamanin budurwa mai shekaru 14 babbar budurwace sosai kuma da kunya a ganka da yarka a wancan lkcin mai wannan shekaru babu aure,  duk wanda ya fito neman aurenta sai yan unguwa su tareshi su fada masa abunda ya faru kanta, daga haka har aka dena xuwa gaba daya.  Ba tare da shawarar kowa ba Mal Suleiman ya dauki auran fadima ya bawa wani abokinsa direban babbar motar haya (Wanda yake sana arsu daya shima matuqin mota ne) mazaunin qauyen maberaya ta jihar sokoto a wancan lokacin a yanxu kuma zamfara.  Saboda xaman fadima haka ya dameshi kwarai,  yayiwa Mal Ali bayanin abunda ya faru a kan fadima shi kuma yace yaji ya gani ba komai aishi Me rufa masa asirine. 


      Lokacin da yaxo da maganar aurar da fadima ga Mal Ali hajia ta shiga mugun tashin hankali ita da yan uwan fadiman karma Adda halima taji lbr domin tana mugun San fadima,  amma dole sukai haquri saboda sanin halin ubansu mafadacin gaskene. 


    Haka akai biki aka kai fadima gidan Mal Ali dake maberaya, gidan gandu bayan matansa 2 da yaya 17 harya aurar da wasu ma, ga kuma tagowar yan uwansa dake cikin gidan. Haka dai suka baro fadima uwa ta mutu saboda tunda akai maganar aurenta da Mal Ali ta koma wata iri kamar mai tabin hankali, suka rabu suna kuka ita kuma tana binsu da ido kamar zararriya. 


     Saida ta kwana 2 bataga angon nata ba,  anabata abinci agidan irin cimar mutanen qauye wanda ganin bataci suka dena kai mata dan yanda aka kai haka aka dakkoshi,  dan abun motsa baki da kayan fulawa na kayan garar da aka kawota dashine takeci,  bata fitowa sai xata bandaki wanda take mugun kyama domin ko wanka takasayi a ciki.  Arana ta ukun ne ta fito ta wanke bayin cike da tashin xuciya saboda jikinta ya dameta da ciwo tana buqatar wanka tayi wankan tafito tarar da mutan gidan sun cika tsakar gida da daurin qirji suna ganinta aka hau dariya da habaici ko kallo basu ishetaba ta shige dakinta. 


     A daren ne kuma mijin ya shigo dakinta tare da kazarsa ta amarci, alkcin yake fada mata wai tafiya yayi kudu dakko kaya shiyasa taji shiru amma gashi ya dawo suci amarci 😂. Duk yadda yakai da sweet mouth (dadin baki)  fadima taqi amince masa, ya haqura ya kyaleta har kwanakin girkinta suka qare ya bar dakin, girki ya kuma dawowa kanta ya dawo dakin da sam cimma burinsa saboda ya kwaditu kwarai da fadima kyakykyawar mace jajur da ita ga quruciya,  koda taqi yarda dashi yaso kwada mata qarfi ta saka masa ihu dole ya haqura ya kyaleta saboda gidan yawa suke ga yayansa da jikoki cikin gida da kunya aji tanai masa Ihu. 


       Saida aka shafe wata biyu cur a haka xaman gidan sam ya gundureta kwarai, duk sanda ta fito tsakar gidan da nufin yin wani abu zata tadda cincurundun matan gidan a gidin bishiya suna ganinta xa a ce " ritayar birni sai qauye ga gwallin ga shafe shafen amma anrasa miji a birni sai a qauye " sai a tafa a kwashe da dariyar cike da shaqiyanci irin na shegun qauye (shegu qauyawa 😂😂😂) . Duk da tana dakewa ta nuna bata gane da ita sukeba amma abun yana damunta. A bangaren mijin ma dangantaka tsakaninsu tayi tsami, saboda taqi yarda dashi ya dena bata dan kudin kashewa da yake bata da kuma lallabawar da yake mata shima tsakaninsu sai hantara aganinsa hakan zaisa da yadda dashi.  Tayi baqi ta rame ta fita hayyacinta duk ta koma kalar yan can. 


    Ana cikin hakan girki yaxo kanta kuma a daren ya nuna zulamarsa akanta wanda hakan yasa ta dunga kurma ihu har mutan gidan suka tashi suka firfito tsakar gida, kunya ta hanashi fita baqin ciki yasa ya jawo wayar radio ya dunga tsula mata yana kwallo da ita har sai da yaji ya huce ya kyaleta. Anatada sallar asuba a masallaci ya fita itama ta tashi tasa hijabinta tasa takalma ta fita, lokacin data isa tasha gari ya fara shaaa,  tashiga motar Kano bata da ko sisi tayiwa direban motar bayani bata da kudi amma insinje Kano zata bashi ya kaita har gida yayi shiru yana kallonta can yace ke yar Mal manu ce?  Naga Kama,  tai saurin cewa eh ni yarsa ce fadima yace to lfy naganki haka kuma anan?  Tai shiru sannan yace bakomi mun taba aikin mota tare dashi ashe yata ce muje ba komi har gida xan kaiki.  Kafin motar ta cika ya sai mata shayi da bread Shayin kawai ta iya sha tana Allah Allah motar ta cika sutafi dan gani take kamr Mal Ali xai biyo bayanta.  Da haka motar ta cika suka daga. 


Mrs Muhammad 😊



🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            8⃣

    Azahar a cikin gidansu tai mata direban motar daya kawota ne yayiwa Mal sulaiman halin da ya ganta aciki, yayi masa godiya ya shiga da fadiman cikin gida. Ransa ya baci kwarai da yaga kwanciyar bulala ajikin ta kota ina, haka aka dunga biqinta har ta warke yayyunta maza sukace aure anyi angama.  Sai dai har fadima ta share 3wks a gidan Mal Ali bai nemeta ba, hakan yasa Mal sulaiman ya nemshi cikin xafin rai yanuna masa bacin ransa kan abunda yayiwa fadima, shima Mal Ali cikin nasa xafin ran ya balbale Mal sulaiman da nasa fadan tare da cewa yar tasa ragowar wani da bata da mutunci yaje ya saketa. Jikin Mal sulaiman yayi sanyi kwarai ya tara yan uwan fadima ya fada musu kuma ya nemi yafiyarta. Dama duniya makarantace Wannan avun shiya koyawa Mal sulaimn hankali ya lura cewa bada fadima sadaka bashine mafitaba gara yayi haquri har Allah ya kawo mata wanda xai sota a yanda take. Saboda haka ya bawa yan uwanta damar da suka dade suna nema a kanta, suka sakata a makatanta library ta fara xuwa inta tashi ta shiga ajin koyar sana a dinki da saqa. 


    Bayan shekaru 2 fadima ta goge sosai kasancewar ansakar mata mara tana fitsari babu takura, ta goge ta cika ta xama cikakkiyar mace tuni ta kware akan dinki takan dan taba saqa amma tafi maida hankali akan dinki, ta bangaren karatu kuma ta kusa kammala primary. 


        A na cikin hakan suka hadu da AL amin a lokacin yana service (bautar qasa)  ta dawo daga skul suka hadu ahanya ya bita har gida, Sun fara soyayya ya mace akan kyakykyawa fadimatu itama tana qaunar Guy din amma tana dari dari saboda kar yaji abunda ke tare da ita, saboda haka ta kwashe komai ta fada masa kafin asamu wani daga waje ya fada masa. Ga mamakinta saiya tausaya mata tare da bata tabbacin wannan bazai rabasu ba, 


    Bayan dogon dauki ba dadi da kai ruwa rana da aka samu ta bangaren AL amin. Saboda a cewar Baffa Buhari bazai auri bazawara ba sai dai ya samo wata tunda yace bayason husna qanwar hajara, shi kuma AL amin din ya kafe yace ita yakeso, duk da Baffa ba ra ayinsa bane, zugar hajara ce kawai ke aiki dashi kasancewarsa namiji mai daukar xuga, shidai kawai ya tsani fadima tun kafin ya ganta saboda yanda yaga Dan uwansa na qaunarta , wannan ra ayi nasa ya hadu da xugar hajara ya jawowa fadima tsana sosai a gurinsa, a bangaren hajara kuma ji take kamar ta kashe fadima tun kafin ta ganta, gashi alokacin anmata kishiya wato Anty jamila abun ya hadu yayi mata yawa. A karshe dai Allah yayi ikonsa domin AL amin da Fadima sun kasance ma aurata. 


         Ta haifi yarta fari Mace ya maida sunan matarsa, wanda hakan ya kuma janyowa fadima qiyayya a gurin Baffa da matansa, saboda hajara tayi masa famfo cewa kamata yayi AL amin din yasa sunan mahaifiyarsu amma yasa sunan shegiyar matarsa. Xuwa wannan tym din gidan Baffa ya fara cika da yaya kuma arxiqinsa ya bunqasa kwarai da gaske ya gina qaton gida me part 4( gidan da suke ciki yanxu)  gida me kyan gaske ginin irin wancan xamanin da daku 2 asoro na mazan gidan da seat room daga waje da rila xagaye da gidan.  Tun lokacin da aka auro fadima ta tadda yara 7 a gidan 5 na hajara 2 na jamila, daga baya suka fara competition din haihuwa, a inda nan da nan suka cika gidan da yaya maza da mata amma matan sunfi yawa.  


        AL amin yasamu aiki a tun farkon aurensu a inda yasamu aiki a jamiar da yayi karatu wato ABU kuma yana ci gaba da karatunsa, agefe kuma yana taba aiki a wata chamber kasancewarsa lawyer,  suna zaune a unguwar sharada fadima ma tana cigaba da karatunta AL amin ya tsaya mata da kansa inyana gari yakan koyar da ita, ga kuma sana arta ta dinki tanayi. 


        Bayan shekaru 5 da haihuwar Faty ta haifi MARYAM taci sunan mahaifiyar fadima kenan suke kiranta (Mimi). AL amin ya kasance mutum mai mutuqar San iyalinsa yanasan yayansa kwarai,  yakance in Allah ya yarda Faty ma aikaciyar jinya (nurse)  Mimi kuma yakance shixata gada wato lawyer,  in ya fadi haka fadima kance Allah ya rayaka Barrister ya kuma yara maka sister Faty da Barrister Mimi . Yakance amin amin fadimatu. 


       Mimi nada 4yrs ya jefata a skul sai dai ita sabanin yar uwarta miskilace kuma mai yawan lalura da fari Sun sikila ce sai da suka je asibiti sukaji sabanin haka domin bincike ya tabbar da A S ce,  kawai dai Allah ya halicceta me lalura.  Alokacin kuma fadima takuma samun wani cikin, cikinta na wata 6, Allah ya dauki ran AL amin a dalilin hatsari da yayi a hanyarsa ta koma Zaria gurin da yake aiki,  mutuwar ta girgiza fadima da Baffa Buhari kwarai da gaske a dalilin mutuwar fadima tai haihu lokacin haihuwar beyiba ta haifi jariri dan wata 6 babu rai. Bayan 40 Baffa ya buqaci a bashi yayan AL amin,  da farko fadima da danginta sunqi amma daya kafe cewa dole ta bashi domin baza a tafi da yayan dan uwansa wani gidan ba da sunan aure.babu kunya da lokacin da yan uwan fadima maza suka nemi xama sulhu yace in fadima ta matsa tanasan rayuwa da yayanta ta aureshi taje ta riqe yayanta,  lamarin da taqi yarda sam saboda tasan halin matansa da yadda suka tsaneta a matsayin faccala bare kuma ta xama kishiyarsu, sannan kuma ita bazata iya cin amanar AL amin ba ta auri wansa.  Shi kuma yayi amfani da wannan damar ya kwace yayanta yakai gidansa ya watsar.  Kunji yadda lamarin ya kasance. 



Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼


Writing&story by

Rahma Muhammad {hajia} 


Editing by mmn khairat 😍


📝FANTASTIC STARS WRITERS 

{F S W } 

             Pege9⃣





       Maryam (Mimi)  da Faty, Sun taso kai daya kasancewar Mimi mai garun jiki saita xama kamar saar Faty, baxaka taba kallonsu kace Faty tabawa Mimi tazarar shekaru biyar ba. Faty ta kasance fara sol kyakykyawar mace sosai doguwa mara jiki, kamarsu daya da uwarta sak mai yalwar sumar Kai. Yayin da Mimi ta kasance doguwa me murjajjen jiki me cikar halitta, bata da qiba Sam amma duk inda ya kamata ya xamo me cika ajikin mace kamarsu qirjinta da kuma hips to ajikin Mimi dai sai Masha Allah,  dangane da skin colour kuwa Mimi wata irin colour ce ba fara bace kuma ba baqa bace ko kadan, itadai gatanan kamar ruwan xuma ( honey colour)  fatarta me daukar hankalice irin colour din dake matuqar tsada a duniya, a taqaice dai xamu iya kiranta Kalar bargon kaza. Bata da wani shaharren kyau a fuska irin na yar uwarta komai nata a fuska tsaka tsaki ne inka cire manyan iduwanta farare tas, sai kuma haqoranta farare tas dogaye ,itama tana da gashi sosai koma ince duk jikinta gashi a kwance ( irin matannan masu gargasa) har fuskarta gashi ne a kwance tun daga gaban goshinta xuwa sajenta har xuwa qeyarta.  Amma gashin mai qarfin gaske kamar izgar doki ga cika ga tsaho wanda yasa dole mama take mata retouching tun tana qaramarta inba hakaba baya kitsuwa yanka hannu yake.  Itakam tafi kama da AL amin (mahaifinta) inka kalleta tsaf komai nata sai kaga tana kama sosai da SASHA OBAMA ( yar Barrack Obama) kai kace sun hada dangantaka,  babu a bunda ya hadata da yar uwarta Faty ta bangaren kama sai muryarsu da take iri daya sai kuma dimple (beautiful point)  din da suka gada ta bangaren uwarsu, domin yawanci yaya da jikokin gidan sunada shi. Wannan kenan. 


        Sun taso da mutuqar soyayyar junansu, hakan baya raba nasaba da adduar mama domin duk sanda tasa goshinta a qasa tana adduar Allah ya hada matá kan yayan nata kamar yadda ya hada nata da Adda halima, domin su kadai Allah ya bata (bata haihuba a gidan Baffa). Dayake Allah maji roqone ya amsa mata, ita kanta tana alfahari da yayanta inta kallesu tana tasbihi ga Allah, Faty kyakykywa tá qarshe San kowa kin wanda be samu ba, da kuma Mimi wacce da wuya ka dora ido akanta kadauke batare da tasbihi game dukaba musamman inbaka da cutar hassada. Duk da yawan gorin da ake mata a gidan na cewa "duk macen da bata haifi namiji ba bata haihu ba " wannan maganace da Kullum saí Anty ( jamila) ta fada mata ita. Da yake anty kamar yadda yaran gidan ke kiranta, ta kasance mahaukaciyar mace me mutuqar kishin mama ta tsaneta da yayanta, kuma bata iya boye abunda ke xuciyarta baro baro take nuna kiyayyarta ga maman  tana taqama da yayanta kwarai kuma da fifitasu akan komai da take dashi. Yayin da Umma (hajara) ta kasance makirar mace kuma karuwar cikin gida, (fir'auna a xuci Musa a kan sharshe)  wacce da wuya ka gane ainihin abunda ke xuciyarta inba mugun Sani kai mata ba,  bazaka taba cewa ta damu da wanxuwar mama da yayanta a cikin gidanba. Amma a gaskiyar lamari tafi Anty tsanar su,  domin lokacin da aka auro fadima itace ta nemi hadin kan Anty duk da tsananin kishi da fada da suke gwabzawa a lokacin,  ta shawarceta da su ajiye kishi guri guda su yaqi fadiman.  Kuma ta jagoranci Anty suka bi duk wasu hanyoyi suka hana fadima haihauwa domin a cewarsu be kamata taci gadon qani sannan tazo taci gadon yayansa ba.  Shiganan fita can  haka sukai ta xagaye guraren na tsugune (bokaye) har sukai nasarar rufe mahaifar fadima . (nikuwa nace Allah dai be qaddara rabo tsakanin fadima da Buhari ba domin daya qaddara bokaye basu isa hana Allah ikonsa ba). A duk sanda Anty taiwa mama gorin rashin haihuwar yaya maza takance ita haihuwa ai mai albarka kawai ake nema bawai jinsi ba Allah ya yiwa wanda yabani albarka .


       Arziqin Baffa ya bunqasa kwarai domin yanxu har gina gidaje yake yana siyarwa ko ya saka haya ga gidan gonaki da yake dasu wanda yake kiwon kaji, kifi , raguna da kuma shanu. Mutanen da sukecin abinci a qarqashinsa suna da yawa, xuwa wannan lokaci ya aurar da yayansa mata da dama, kuma baya aurar dasu sai ya kaisu sun sauke farali (hajji) kusan ma yarinya tana gama secondry a gidan yake kaita maka, dayake yawanci bibbiyu suke tashi yaran gidan saboda tare Umma da Anty ke haihuwa sai dai tsiran watanni. Duk da cewa baiyi karatun boko mai xurfiba ya bawa yayansa ilimi domin dukkansu sai sun haura secondry yake aurar dasu kina fara jami a level 100 xuwa 200 saiya aurarki kya qarasa agidan mijinki. Kuma bai yarda da bawa karabuti auran yayansa ba, domin yace bazai sayar da akuya ta dawo tana cimasa danga ba, sai wanda ya tara (mai kudi)  komai rufin asiri sosai yake bawa auran yayansa.  Kuma Allah ya dafa masa akan hakan domin wadanda yake muradin yayansa su aura shi Allah yake kawo musu (masu kudi) kasancewar yayan nasa kyawawa gasu da kwalliya da kuma ilimi domin yawanci Baffa suke yowa kuma Baffa kyakykyawan bafullacene. 


       Sai dai ta bangaren yayan mama ba haka lamarinsu ya kasance ba a gidan domin Faty tuni ta gama secondry har ta shiga school of Nursing (makarantar koyan aikin jinya) amma ko airport Baffa bai kaitaba bare saudia dan sauke farali. Da mama taji zafin abun amma daga baya saita barshi abisa ajizanci irin na Dan Adam, musamman data duba alkhairinsa na kaita saudia shekaru 3 abaya, sai ta goge laifin rashin kai Faty, dabeba. Baffa yana muqar San mama domin kuwa bambamci tsakanin mama da sauran matansa a bayyane yake, mama macece mai tsari kwalli tsafta iya girki Kullum cikin kwalliya take yatsunta basa rabuwa da kunshi hakan ya qarawa kyanta armashi da soyayyar miji Baffa a Kullum godewa Allah yake daya qaddara masa auran fadima ,domin shi mutum ne besan gayu da tsafta matansa kuma basu da lokacin wannan saina gasar haihuwa saboda gado. 


       Mama ta dade da samun shaidar karantun NCE a kwalejin horar da malamai ta tarayya (FCE), domin bayan kammala secondry school dinta a gidan galadima taci gaba da karatu bisa shawarar Adda halima wacce a lokacin take B ED (Bachelor in Education)  a FCE din domin mijin Adda (Alh Abdul Aziz)  dan bokone na qarshe saboda haka a hannunsa ta fara karatu tundaga yaqi da jahilci har takai matakin samun degree. Da farko Baffa yaso hana mama karatu, amma ta burkese masa dole ya yarda saboda son da yake mata da kuma tausayinta da yakeji na rashin qara samun haihuwa saboda yana sane Kullum cikin gorin haihuwa take a gidan,  koda komawarta makaranta matan gidan basu wani damuba tunda ba sanin darajar ilimin sukayi ba, sai data kammala mijin Adda halima ya samo mata aiki a wata junior secondry school sannan suka nemi yiwa Baffa bore saboda baqin ciki da hassada, shi kuma yace duk wadda xatai karatu acikinsu kofa abude take kuma intagama da kansa zai sama mata aiki.  Dole sukai shiru domin sunsan basu da tym din karatu. 


    Soyyar dake tsakanin Faty da Mimi baki bai iya fadarta,  Faty yarinyace mai dattako da sanyin hali. Ta bangarenta bata hada San Mimi da komai ba,  za a iya cewa tafisan Mimi da ita kanta, sai kaiwa Faty laifi ta haqura amma in kaiwa Mimi ta yini tana fushi dakai. Mafi yawan qawayenta sunan MARYAM garesu kuma tana qawance dasu ne ta dalilin alaqar sunansu da Mimi.  Bata cika xama a gidan Baffa ba mafi yawan rayuwarta tana yinta ne a gidan mummy (Adda halima) dake rijiyar zaki. Mummy nada yaya 7 maza 3  mata 4. A cikin yayan mummy akwai saar Faty da kuma saar Mimi.  Duk da gidan mummy gidane na yan gayu da daula hakan besa Mimi cika san xaman gidan ba duk kuwa da qaunar da mummy kewa Faty da Mimi, tasamu Faty dai amma Mimi Kullum tana jikin mama. Lokacin da mama ta tafi aikin haji 3yrs back dole tasaka Mimi xaman gidan mummy. Datai duba na tsanaki sai ta gano abunda yasaka Faty San xaman gidan, wato daddy. Mijin mummy mutum ne baisan iyalansa kuma ya sakar musu abunda sukaga dama shi sukeyi, (ba irin sakarwar da xata xama ba tarbiyya ba) Kullum yana cikinsu in dare yayi a hadu ayi karatu ya koya musu sannan a dasa hira har 10 pm sannan kowa ya nemi makwanci, hakan yajawo Faty San xaman cikinsu saboda inda ta taso tsangwama kawai suka Sani daga gurin yan uwansu wato yayan Baffa. 


      Abunda ke daurewa mama kai shine batasan dalilin da yasa anty da Umma suka tsani Mimi fiye da Faty ba, ita a ganinta in qiyayyace Faty ya kamata afi zafafawa ita fiye da Mimi, domin kuwa in kyau ne kaf iyalan gidan Baffa sai dai su xamo a bayan Faty domin babu wanda ya isa ya hada kafadarsa da Faty ta fannin kyau, amma memakon suyiwa Faty hassada kodan kyanta sai ya zamo Mimi akewa. Amma mamakin mama ya qarene a lokacin data fuskanci tsanar Mimi ta samo asaline fisa tsananin soyayyar da Maman da Faty kewa mimin,  sai ya zamo anaiwa Mimi abune kodan mama taji haushi kota tanka musu.  Hakan yasa ta gayyato dauriya ta qara akan wacce take da ita akan Mimi in anmata abu ta kau da kai, duk da ciwon da abun ke mata. 



Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼

AL 'AMARIN MARYAM

🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼



Writing & story by Rahma Muhammad {hajia} 

 


Editing by

 Mmn khairat 😍


📝FANTASTIC STARS WRITERS 

{F S W } 



           Page  1⃣0⃣



     Faty tai sallama dakin mama daga makaranta take,  sanye da fararen kaya Sol (uniform) da dan hijab iyakacin gwiwar hannunta. Mama tana zaune kan sofa tana kallo Mimi na kwance itama kan sofa din ta tada kai da cinyar mama hannun mama cikin gashin mimin tana shafawa ahankali. Ta qaraso ta dafa Mimi sannan ta kalli mama, mama Mimi ba lfy?  Ta tambaya arikice.  Eh ciwon mara take tun safe tasha magani, amma har yanxu be saketa ba. Wayyo inji Faty ta janyo Mimi jikinta ta rungume tana mata sannu mimin ta gyada mata kai cike da galabaita. Ta maida mimin jikin mama ta dau kudi a jakarta tare da cewa ina xuwa ta fita. Can sai gata ta dawo da allura ta bude ta hada, ta kama mimin suka shiga dakinsu dake parlourn ta kwantar da ita a kan gadonsu sannan tai mata allurar. Ko minti biyar bataiba bacci ya dauketa. Taiyi sallah ta canja kaya tazo ta kwanta a bayan mimin bacci ya dauketa itama. Mama taji shirun yayi yawa ta shigo domin kawowa Faty abinci ta tarar dasu kwance kamar yadda suka saba Faty abaya Mimi agaba akan filo daya hannun Faty akan cikin Mimi yayin da mimin ta sa hannunta ta riqe hannun Faty. Wannan shine salon kwanciyar yayanta tun suna qanana wani sa in kuma su rungume juna suna baccin. Tai murmushi ta qarasa ta sumbacesu ta kashe musu fitila taja musu qofa. 


        Tun Faty na secondry skul masoya sukai mata ca kuma manyan masu kudi da yayan manyan mutane harda jinin sarauta, saí dai Baffa yace saita fara makaranta domin haka dokar gidan take, a bangaren Faty kuwa duk basa gabanta domin akwai tsumammiyar soyayyar quruciya aranta, duk kashe kudin da samari keyi akanta baya gabanta hasalima bata kulasu. Tanason Ahmad (yaron maqotansu wanda ke shiga gidansu gurin mama). Tun lokacin da Ahmad ya farga da manyan masu kudin dake kawowa Faty hari ya shiga tashin hankali ba kadan ba,  domin ya mace akan Faty tun tana qanqanuwarta kuma da ita kadai yake tsara rayuwarsa, hakan yasa yaje ya sakawa mama kuka da roqarta ta bashi Faty indai baso ake ya kashe kansa ba. Maman ta bashi tabbaci in shaa Allah Faty bata da miji sai shi domin ta fahimci Faty ma tana qaunar Ahmad shi yasa bata kula kowa cikin manemanta. 



     Duk da Baffa yaso turjewa lokacin da aka gabatar masa da Ahmad a matsayin manemun Faty, domin be tabawa kamar Ahmad (talaka)  auran yarsa ba, amma kafewar Faty da mama akan auran yasa dole ya sakko musamman da yaga irin dukiyar da mahaifin Ahmad din ya kawo a matsayin kudin neman aure.  Domin a lokacin giyar asiri da matarsa ta dena tasiri akansa, ya kuma bawa Ahmad din gida makeke a NNDC sannan ya samar masa aiki saboda a lokacin ya gama karatunsa har yayi service. Hakan yasa Baffa yadan sakko.  Saí dai sabanin yadda Baffa ya saba aurar da yayansa iyayensu matá ko cokali basa siya shiyake komai kuma na bajinta. Amma akan Faty Set din gado kawai ya siya da Set din kujeru daya yaja bakin aljihunsa ya tsuke, abun ya bata mamaki kwarai ganin yadda yake banbanta yayansa da nata kamar ba yayan dan uwansa ba, amma sai ta danganta hakan da rashin San auran Ahmad din da yakeyi hakan yasa ta fitar da kudi maqudai da hadin gwiwar yan uwanta maza da Adda halima sukayi komai na bajinta suka yiwa Faty kayan daki domin na Baffa ma a dakin baqi aka xubasu, (dama dadin nema kenan) . Akayi aure amarya ta tare dakinta, da ike ance dan halak bai manta alkhairi Ahmad ya riqe Faty hannu bibbiyu ya zamo kamar bawa a gareta tana kammala karatu dayake maaikatan lfy basa rasa aiki, Baffa ya samo mata aiki kamar yadda yakeyiwa duk wacce ta gama karatu acikin yayansa, tana aiki a bangaren karbar haihuwa a AKTH wato aikin unguwar xoma (midwifery).




Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼

AL 'AMARIN MARYAM 

🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼



Writing & story by Rahma Muhammad {hajia} 


Editing by 

. Mmn khairat 😍


📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }  

 

   

PAGE 1⃣1⃣





      Kyakykyawar budurwace yar kimanin shekaru 25 da haihuwa,  skin colour dinta kadai ya isa jawo hankalin duk wani lafiyayan namiji fadawa tarkonta bare aje ga dirinta wato structure cikakkiyar fuska gareta me dauke da 👀 darara farare kal,  komai na fuskarta matsakaicine wato mastada 'a  kamar yadda muka siffanta abaya, bakinta dananne kadan dauke da haqora masu kyau farare kal, wanda daka gani kasan ana ziyartar Dental clinic duk bayan wata 6 domin wankesu, koyaya ta motsa bakinta dimple dinta saiya bayyana. Duk da a ganin mutane MARYAM ba wata kyakykyawa bace compared to yar uwarta faty, ni dai anawa ganin MARYAM kyakykyawar gaskece, saboda ba lokaci daya xaka kalleta ka gano kyan nata ba,  nooo sai ka nutsu sosai sannan xaka gano baiwar kyau da Allah ya azurta MARYAM dashi. Bayan haka kuma aiba fuskar mace kadai ake kalla ajikinta asan cewa kyakykyawa ce,  da yake mafi yawan mutanenmu sunfi gane cewa farar fata itace kyau,  wanda Sam ba haka abin yake ba. Hannayen ta dauke suke da wasu irin xara xaran yatsu wadanda aka tara musu farce (kumba) dai dai misali ma ana ba zaqo zaqo ba, gashi an qawatasu da jan lalle hannu da qafa,  qafarta mai ban shawa awa yar dundubus kamar jikinta, yatsun qafarma kamar na hannaye suke zara zara.  Gashin kanta wanda cikar budurci tasa ya qara haukata da tsaho da yawa ya kwanta luf saboda amfani da mayukan gyaran gashi irinsu MEGA GROWTH,  kwanciyar nada nasaba da retouching da yake samu duk bayan 8 wks saboda shampo baya wuce sati 8 akan Mimi zai fita, fuskarta kawai inka kalla kasan tana gashi saboda gashin dayacika gaban goshin hadi da sajenta. MARYAM AL 'AMIN kenan (Mimi).  Wacce yan watanin kadan baya ta kammala degree dinta a fannin sharia (law)  a B U K. 



    AL 'AMARIN MARYAM ya farane tun daga kammala secondry dinta ko ince angane AL amarin ne alokacin da yakamata ace Mimi tana da manema (samari), duk wanda yaji ko yaga Mimi zaiyi mamaki kwarai ace bata da saurayi daya tilo koda na rage dare ne. Duk da cewa Mimi macece mai farin jinin mata a lokacin da take jami a, amma hakan yanada nasaba da kwakwalwa (brain) da Allah ya hore mata, hakan yasa tayi qawaye yayan manyan mutane da kuma dai dai ita yan middle class, wasu sular qawancensu saboda kamun kanta da gayu da kuma kwakwalwar da take dasu wasu kuma sunasan Mimi ne saboda haduwar jini. Sai dai a bangaren samari ba hakan take ba ga Mimi, domin xata iya cewa tunda takai xamanin yan matanci bata taba wata 1 cikakke da saurayi ba, to samarin ma duk gasunanne ma ana yarane qanana masu xaman banxa ko dalibai wanda suke qarqashin kulawar iyayensu balle abasu aure. In saurayi yazo wajen Mimi da wahalar gaske ya dawo inma ya dawo din baya wuce zuwa biyu xai dauke qafa dan kansa, kudan shekaru 6 kenan ana fama da wannan matsala, wadanda suka taso tare a yayan Baffa guda duk anmusu aure hardama yayan dangi na gurin uwa da uba, hakan ya janyo mata gori sosai ita da mama tun anayin abun cikin habaici har takai ana fitowa fili a gotanra musu, musamman inya kasance saurayi yayi musu hidima, (lokacin axumi ko toshin sallah) lamarin dake saka mimin qunci ta shige daki tayi ta kuka ba domin tana musu hassada ba saí dan ta rasa yadda zatasa kanta taji, tunda take bata tabacin ficikar namiji da sunan yana sonta ba to inama samarin suke???  Domin saita shafe shekara ko karen mota be leqo da nufin neman auranta   ba. Ta rasa wani irin al amari ne wannan, ko a dangi anasamun masu goranta mata ta haryar shagube da cewa ah! Kedai Mimi kinqi aure kina jiran me kudi ko? To ai kwayi auran tare da yayanmu, abun takaicin da yawa daga masu goranta mata yan uwantane na jini kuma na jiki wanda ya kamata ace sun jajanta mata sai dai aduk lokacin da irin hakan ta kasance yaya Faty intana gurin takan kare mimin da cewa aure ai lokaci ne,  ita Mimi nata lokacin baiyiba. 


       A bangaren mama AL AMARIN Mimi na mutuqar daure mata kai, domin Mimi macece Abida (mai yawan ibada)  domin da ace ibada tana bada miji da Mimi bata rufe shekaru ashirin ba tare da aure ba, amma da yake aure AL 'AMARI ne na Allah sai gashi shiru, ta bangaren kyau, tsafta,gayu,nutsuwa da gwarjini badan ita ta haifi Mimi ba xata iya cewa ta dade bataga mace irin haka ba.  Ta rasa a inda matsalar take amma ta tattara ta barwa ubangiji lamarinsa itadai kullum goshinta a qasa tana roqawa Mimi da ma masu irin matsalarta Allah ya kawo musu mafita.  Duk da xuciyar mama tasha shawartar maman akan taje ta samu daya daga cikin yan uwanta maxa su hada mimin aure da yayansu kodan saboda matsin lambar da mimin ke fuskanta a gurin Baffa, amma abu daya ke taka mata burki  wannan Abu kuwa shine : kada auren ya tabbata daga baya mijin ya wulaqanta Mimi saboda bashi ya nema ba, bashi ita akai, kuma dama ance matar shige bata daraja.  Kuma inta xurfafa tunani sai taga da daya daga cikin yayan yan uwan nata sunso ai da sun furta San auran Mimi tunda duk Sá anin ta na bangaren jikokin mal SULAIMAN anmusu aure. Tana mutuqar tausayin Mimi, yarinyar bata da qoshin lfy amma tana da qarfin xuciya, indai Mimi na gida to mama aikinta xamane kawai ko kuma tayi dinkinta abunta sai taso xata taya Mimi da aikin girki kona shara amma duk aikin da mace ya kamata tayi a gidan miji Mimi ta daukewa mama hakan ya qara xafafa qiyayyar mimin a gurin Umma da Anty wato kishiyoyin mama matan Baffa, badan basu da yayan da xasuyi musu ba sai dai dan basu yiwa yayan tarbiyar temaka musu ba. 



      A bangaren Baffa kuwa shi babu ruwanshi domin aganinshi iya shegene ya hana Mimi fitar da mijin aure, saboda shi Allah bai taba jarrabashi da dadewar yaya agabansa ba babu aure da sun fara jami a kamar jira suke Allah yake kawo musu miji. Hakan yasa ya dau lamarin Mimi iya shege. " in har baki fitar da miji ba har kika kammala makaranta to tabbas xan cire hannuna daga kanki  domin naga abun naki ya koma iskanci, neman xubarmun da mutunci kikeyi a unguwa gandamemiyar budurwa dake kina yawo a gari ko kunya bakiji tun kina xuwa auran sa anni kin koma xuwa na qanne." wannan shine fadan Baffa Kullum akan Mimi, wanda yau da gobe tasa mimin haddacewa kaf,  kuma hakance ta faru domin bayan graduation din Mimi anyi sallah qarama ba dadewa kuma a wannan sallah Baffa ko sisi baibawa Mimi da sunan kudin kayan sallah ba lamarin da yayiwa matan gidan da yayansu dadi kwarai, kuma wannan alamarce ta nuna tabbas Baffa ya cire hannu akan Mimi kamar yadda ya alqawaranta, ko gaisheshi tai a ciki yake ammasawa shi a lallai yana fushi da ita kan abunda ba ita ta dorawa kanta ba (Allah sarki).  



        A yanxu haka da take shirin tafiya law school,  a gidanma shirin aurar da mutum 3 biyu mata wadanda mimin ta girmesu da shekaru 3 sai namiji 1 yaya Ali, wanda ya kasance da na biyu a jerin yaya mazan gidan, domin dan Baffa namiji na farko (yaya jafar) wanda kuma ya kasance dan Umma yana kaduna yana aiki , kuma da shine yake nuna kamar yanason Mimi duk da bai furtaba amma daga baya maganar tabi ruwa tun bayan samun canjin gurin aiki daga kano xuwa kaduna. A duk lokacin da Baffa zai aurar da yaya mama ce keyi musu labulaye da xannuwan gado na alfarma a matsayin gudummmawa, wanda hakan ya zamewa Baffa jiki a tun bayan Koyan  labulaye da xanin gado da mama tayi  yayi bankwana da siyansu a harkar bikin yayansa, kawai in aure ya tashi xa a bata kalar kayan falon da xa ai wa amarya ita kuma zata zauna ta qure basirarta Ta tsantsara labulaye da bed sheets set uku uku ta bayar da sunan gudummawa kuma a karba bako godia kamar kudin suka bata kuma hakan bazaisa ana jimawa kadan aiwa yarta gorin aureba. Domin matan Baffa hamshaqan jahilai ne, jahilci irin wanda aka denashi saboda sauraran radio koda bakaje makaranta ba to yana existing a gidan tunbama suna fada akan yaya ba sai kaji kamar ka binne kanka, wannan yasa yayansu basu da tarbiyya ko kadan. 


  Gidansu Mimi gidane na kwalliya koma ince competition dinta ake da yake duk wacce ta gama karatu Baffa na samar mata aiki, hakan yasasu qarya daga yan matan gidan har wadanda ke gidan miji, yawancinsu suna da mota koma ince dukkansu wasu su suka siya wasu kuma mazajensu suka saya musu, acikinsu kuwa harda yaya Faty wacce ya Ahmad ya siya mata tun kafin ya siyawa kansa. Hakan yasa gidan ake gasar saka suttura da kwalliya da kuma shiga mota.  Ta bangaren sutura Mimi kan sai hamdala tufa dai akwaita mama tayi mata, yaya Faty tayi mata, hajia kakarta ta wajen uwa wacce taci sunanta itama Kullum a hanyar yiwa takwararta sutura take , sannan mummy (Adda halima) yayar mama tayi mata sutura kam sai dai ta jira Mimi, ba Mimi ta jira ba.  Hakan yasa koda Baffa bai mataba bata damuba. 


Ana saura sati biyu bikin gidan ta tafi law school wanda yan gidan suka danganta haka da baqin ciki suka dunga sakin maganganu marasa dadi,  domin Anty cewa tai ai dole aqirqiri tafiya law school domin da kunya a xauna to!  za ayiwa yara aure ga gyatuma xaube ajabe agida. 



Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼

AL' AMARIN MARYAM

🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼


📝FANTASTIC STARS WRITERS

 {F S W } 


Writing & story by

 Rahma Muhammad {hajia}



Editing by

 mmn khairat 😍




           Page 1⃣2⃣

    Yammacin ranar juma a ne rana gaf take da faduwa,  a zaune akan tabar rila ta gidansu Mimi matasa ne guda biyu zaune akan tabarma suna jiran Baffa dake daga cikin sitroom din yana sallamar wasu baqi.  Badaru sunan babban mai shekaru 33 sai Badamasi qaramin kenan me kimanin shekaru 30 a duniya,  yayan abokin Baffa ne ya turosu gaida Baffa kamar yadda yake a al adar mahaifinsu (alh Inuwa)  yakan turosu gaida abokin nasa aduk sanda ya kasance Badamasi na gari, saboda ba a garin kano yake aiki ba.  Fararene tas kana ganinsu kaga fulani amma babban wato Badaru yafi Badamasi haske sai dai Badamasin yafishi jiki da kuma cikar zati irin ta maxa,  sannan kuma yafishi alamar wayewa da kuma kwarjini, kodan hakan yanada nasaba da ilimin boko da Badamasin yafi Badaru oho. 

 

         Tafe take cike da gajiya saboda tafiyar da tayi daga Law skul (makarantar koyar da aikin lauya)  xuwa gida sakamon samun hutu 1 wk da sukayi tazo gida domin yin hutun,  sanye dake cikin suit baqaqe riga da skirt kamar yanda yake ga dokar makarantarsu,  sai dan Baby hijab dake maqale a wuyanta kayan sun mata cif sun fito da surarta,  qafarta sanye cikin rufaffen takalmi (cover shoe)  baqi sai jakar goyo irinta dalibai itama baqa, ataqaice dai hijab dintane kawai fari a jikinta,  jakar na goye a bayanta wacce ke dauke da yan kayan da xata iya buqata kamarsu brush,  charger da kuma system din ta ( wato laptop) sai wayar dake riqe a hannunta. Duk da gajiyar da tayi hakan bai hana kyanta fitowa ba, babu kwalliya ko digo a fuskarta sai gashin gaban goshinta wanda baya iya rufuwa koda ta kwatanta rufeshi fatarta tayi tas ta kuma yin kyau saboda zama guri daya data samu.  Mimin mama da Yaya Faty kenan .


       Harta qaraso cikin rilar wacce xata sadata da sorayen gidansu bata kula da wanxuwar su Badaru a cikin gurin ba, wanda su kuma tunda ta tunkaro gidan suke kallonta harta shigo cikin rilar shigowarta yasa suka sauke ajiyar xuciya atare suka kuma shagala da kallonta ganin tana shirin shigewa cikin gidan yasa Badamasi tashi da hanxari ya qarasa inda take tare da cewa "Assalamu alaikum" . Yayin da Badaru ya kashingida ya cigaba da kallonta bako qiftawa.  Bayan sun dan gaisa da Badamasi sama sama saboda ta qagu ta qarasa gida,  ya kalleta a karo na barkatai sannan yace kamar daga makaranta kike ko?  Taqanyi yaqe tace eh, ok wace skul kike?  Ina Law skul ne dake nan jihar kano, ta bashi amsa a gajarce. Kai 😳 kice da Barrister nake tare,  yasunan  malamar?  Maryam ta bashi amsa tana murmushi 😊. Barrister maryam gaskiya kin burgeni inason inga mace tayi karatu me xurfi haka.  Well naga a gajiye kike ni sunana Badamasi wancan na kwance yayanane sunansa Badaru munxo gurin Babanki ne, kuma ina fata daga yanxu xumunci ya shiga tsakaninmu.  Tace to nagode bari na qarasa,  Ok to Mimi sai nazo karki manta sunan Badamasi da haka suka rabu ta shige gida. 



           Bayan ta kwana biyu da xuwa ne kuma ta shirya xuwa gidan Rashida da Rahana (wato amaren gidan da akai biki bayan batanan)  ta Ware 10k da nufin ta bawa ko wacce 5k a cikinsu.  Mama sam batazo xuwan Mimi gidan Rashida ba saboda Rashida (yar Anty jamila)  tafi tsananta qiyayyar Mimi akan kowane mahaluqi dake gidan Baffa,  qiyayyar Rashida ga Mimi a bayyane take kowa yasan Rashida ta tsani Mimi tsana ta qarshe,  domin anshayin taro acikin gidan ko a wajen gidan Rashida tayiwa Mimi gorin aure (tun kafin ita Rashida tayi auren kenan) ko kuma ta duxgata agaban mutane ko qawatenta.  Dan akwai lokacin da yaya Zainab yar ita Rashidan wato yar dakin Anty ta haihu ranar suna duk antaru anata aikin dambun shinkafa a gate din gidan Anty Zainab din anata hira kowa na tofa albarkacin bakinsa,  hirar dai akan karatune da kuma wahalar samun aiki,  Mimi tasa baki acikin hirar da cewa " ai aiki kam na wahala akasar nan indai baka da wanda kasani saika gama karatunma ka xama jobless Allah dai ya kyara qasarnan,  sai kuwa tsulum Rashida tasa baki tare da cewa "ai koba aiki inkanada mashinshini sai kai auranka ka huta, damuwa akan aiki ai Sai irinki wadanda kukai kwantai kuka kai matakin bandaro (🤣🤣🤣🤣) ,ta fada tare da kwashewa da dariya.  Kowa agurin yayi qim maganar ta bashi mamaki domin bata taba fitowa fili ta fadawa mimin magana ga da ga hakaba,  maganar ta daki Mimi kuma tai mata ciwo saboda ganin yadda gurin yake acike da mutane daga na gida har qawayen Anty Zainab da dangin mijinta,  ta rasa abunda ta tsarewa Rashida take mata wannan muguwar qiyayyar, duk da tasan cewa a yayan Baffa wadanda suke santa basu wuce 4 ba xuwa 5 amma ba wanda yake mata qiyayya kwatan kwacin wadda Rashida ke mata tasha goranta mata abunda ba ita ta dorawa kanta ba (jinkirin aure) hawaye ya wanke mata fuska ta kasa dago kanta ta kalli kowa a gurin saboda jitayi duk ta muzanta,  qarar marin ta tajine ya dawo da ita daga tunanin da take,  tai saurin dagowa taga wanda aka mara tai toxali da Rashida riqe da kunci gefe kuma ga yaya Faty tana huci da alama itace ta mari Rashida.  Dai dai lokacin kuma Rashida ta yunquro cike da fitsara ta fara nuna Faty tana cewa akan wannan 👈🏼 ta nuna Mimi kika mareni?  Dan ance tayi kwantai?  Qarya nai batai kwantan bane?  Shekararta nawa batai aure ba?  Age mate dinta hardame yaya 4 amma ita ta gaza samun even tsayayyen saurayi  saboda rashin kamun kai, duk wanda yaxo sai tabashi ya dana, ya za ai kuwa ya aureta?  Kema Faty (yau ko yaya fatyn babu 😄) duk randa kika kuma taba fuskata da sunan duka wlh sai..  Adaidai lokacin Anty Adawiyya wacce akaje cikin gida aka fada mata abunda ke faruwa ta sharawa Rashida mari ta kuma kifa mata wani,  sannan ta dora da xagin Rashida da yimata gargadi cikin kakkausan lafaxi kasancewarta Principal din makaranta kusan tasan takan iya shege (kusan principals ba wasa 😜 akwai displine) . Ko takansu Faty bata kuma bi ba taja hannun Mimi ta bude motarta dake cikin gate din tasaka mimin aciki sannan ta koma cikin gidan ta debo duk wani abu nata da taxo dashi da na mimin ta xuba a Mota Anty Adawiyya na kiranta ko juyawa bataiba bare ta nuna taji, duk kuwa  da tsanin girmamawar da sukewa Anty Adawiyya sabida itace babbar yar Baffa (mai haquri bai iya fushi ba) amota suna tafe Faty kuka take kamar Mimi koma fiye da ita,  fuskar tayi jajur kan Hancinta har Pink yake saboda kuka.  Wannan shine dalilin da Mimi ta daina xuwa taro domin intaje sai anmata abunda akasan ranta zai baci koda cikin hirane, kuma shine dalinlin da yasa bata xauna bikin su Rashida ba kar atara mutane aci mata mutunci.  Duk da Anty tasan da duk abunda Rashida kewa Mimi amma ko afuska bata tava nunawa Rashida tayi lefi ba. 


         Mimi nikam da xaki haqura da xuwa gidan Rashida duk abunda ki kai niyyar bata ki aika mata dashi sabida gudun fitina.  Mimi tayi murmushi tare da dafa cinyar mama tace mama duk lalacewar Rashida duk qiyayyarta gareni yar uwata ce jininmu daya kuma innaje gidan Rahana banje gidan Rashida ba bakya ganin hakan xai xama abun magana?  Mama tadan nisa kana tace eh hakane kam kuma ai duk tsiyarta tunda gidanta kikaje ai batayi miki ba,  yawwa mama kingane kenan. Mimi ta fada.  Mama ta kalli yar tata, sanye take da riga da skirt na atamafar nouvo dark blue me adon Yellow ta saka veil (mayafi)  Yellow tasha daurinta me steps ta bude tsakiyar daurin inda gashinta da tai dunnot dashi ya fito, Mimi ta taba mama tace mama kodai infasa xuwa naga hankalinki bai kwantaba,  Maman tai saurin cewa a a wlh uwata kyau kikayi shiyasa nake ta kallonki,  Allah ya kiyaye hanya Allah ya sa asamon suruki. Mimin tayi murmushi ta sunkui da kai cike da kunya sannan ta fita. 


        Duk da ba wani good time suke da Rahana ba, amma ta karbeta da girmamawa ba kamar a gida ba da suka rainata dan batai aureba,  hakan kuwa yayiwa mimin dadi sosai Rahana ta zagaya da ita taga gidan ya tsaru komai tsaf mijin nata nada yan canji (kudi) 😄 har ta kirashi ya sunkuya har qasa ya gaida ta, itama kuma taja girmanta ko 30mnt bataiba a gidan ta bata 5k taita godia. 


       A gidan Rashida kam to abun babu dadi domin Mimi na shigowa falon tahauyin wayar qarya tana cewa "kedai bari ai duk macen da batai aure da wuriba ta cuci kanta domin kinsan in mace ta wuce 25 yrs ance ita damai haihuwa goma duk daya namiji yake jinsu,  nikam na dace inkinga yanda my Adams ya dunga tarairayata ba har pant wankemun yake yanxu hakama yaban kyautar Mota,  abun Allah tana cikin wannan maganar ne wayarta tai qara alamar kira ya shigo, wanda hakan shiya fallasa wayar qaryar da take dan taciwa baiwar Allah mutunci, nan danan kuwa ta dibibice ta wayance da cewa wata wayar ta shigo.  Suka gaisa tana wani daga kai ita adole madam saboda ta auri me kudi da gidan alfarma, batacewa mimin tashiga taga gidaba itama batai gigin leqa ko ina a gidan ba,  tadai kira kukunsu tace ya kawo mimin pure wata (ruwan leda)  ita kuma tace ya dakko mata gorar ruwan Faro, yaje ya kawo kamar yadda tace Mimi ta dauki ruwan tasha ita abunma dariya ya bata dan ita ba baquwar ruwan roba bace,  ta bata kudin da ta kawo mata tare da cewa ta gaida me gidan inya dawo ta karbi kudin a yatsine ta watsasu kan centre table din dake dakin cike da ixxa tare da cewa xan fada masa kina gaidashi inban manta ba 😏 ko tashi bataiba balle ta raka mimin tana daganan tace ki gaida gida.  


             Ta tafi tana qissima kyan gidan Rashida a ranta,  Allah me yadda yaso dama Rashida macece mesan qawa da fantamawa da kuma rayuwar kece raini gashi kuma Allah ya bata.  Koda taje gida babu wanda ta fadawa abunda Rashidan tai mata sabida fadar bata da amfani, da haka ta qarasa kwanakin da xatai a gidan dagan tai gidan yaya Faty ta qarasa kwanakinta sukasha hirarsu ta xumunci,  daga can ta koma skul cike da kewar yan uwanta danma ta kusa gamawa. 


       

  Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼

AL AMARIN MARYAM

🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼





📝FANTASTIC STARS WRITE

 {F S W } 


WRITING & STORY BY

rahma Muhammad {hajia}


Editing by

Maman khairat 😍



          Page 1⃣3⃣


       Alh Inuwa da Haj Kaltume wato mahaifan su Badaru yan asalin misaune da jahar bauchi harkar kasuwanci ta kawoshi garin kano, kuma harkar kasuwancin ce ta hadashi da Baffa (alh Buhari) yayan biyar biyu maxa Badaru sannan Badamasi sai mata guda 3 kuma sune qanana yanxu haka kowacce tai aure tana gidanta kasancewar ba ba karatu suke me xurfi ba iya secondry suke tsaya saboda alh inuwa bashi da wayewa irinta Baffa, haka ma kuma a fagen kasuwanci Baffa yayi masa fintunkau, duk da cewa shima dai baza a kirashi talaka ba yana sahun masu rufin asiri.  Badaru sam baiyi wani karatun boko mai zurfiba domin yana gama secondry skul yayi nufin ajiye karatu sai dai kuma abbansu yanason yayansa maxa suyi karatu me xurfi,  ala dole Badaru yayi applying a AMINU kano college of islamic (legal)  tunda result dinsa baiyi kyan da xai shiga jamia ba  kuma dama yafi qarfi a bangaren arabic saboda ko secondry dinsa ma arabic skul yayi.  Ko da ya shiga legal din ba wani maida hankali yayi ba domin hankalinsa yafi karkata kan kasuwancin mahaifinsa da yake a kasuwar singa yana saida kayan masarufi. Da kyar da sudin goshi ya kammala diploma a legal saboda shi dama can karatun boko be dameshi ba ko kadan kuma yana daukan duk wanda ya zaqe da neman ilimin boko a matsayin Bayahude be bautawa turawa,  awani bangaren ma yana yimasa kallo kafiri kafiri (waiyazubillah).  A bangaren halitta farine tsamurmuri bashi da tsaho ko kadan sai yar qiba daya fara bayan kammala karatunsa,  hakan yasa yayi tumbi kamar dan yaye 😄, ga dukkan alamu inyasamu Jin dadi anan kusa zaiyi qiba wacce xata qarawa xubin halittarsa muni sosai.  Irin mutanenne masu zafin aqida da taurin kai da kuma kafewa akan abunda suke ganin dai dai ne koda kuwa sauran jamaa suna kallon abun a matsayin kuskure,  a fuska bashi da muni duk da kuwa karan hancinsa da yaso ya shafe wanxuwar idanunsa 👀 a fuskar ma 'ana idanunsa qananane sosai ya tara qasumba har xuwa dan madaidaicin gemunsa. Saboda burkitaccen ra'ayin Badaru yasa bai cika abokai ba,  saboda kallon kowa yake a matsayin bayahude daya shagala da bautar masu jajayen kunnuwa (turawa),  sai dayake bahaushe yace ba a rasa nono a ruga hakan yasa Badaru bai rasa dai daikun abokai ba masu irin ra'ayinsa.  A fagen soyayya kuwa ya dade da fadawa tarkon wata yarinya Nafeesa yarinyace batafi 16-17 years ba, dominshi a ra'ayinsa babu auran babba aciki yafison yara wacce zaiyi tarbiyyarta ya juyata san ransa, amma fa a ganinsa (ni kuwa nace banda irin yaran yanxu, domin sunfi manyan iya shege)  😊 yanason Nafee wajen shekararsu 2 tare da ita.  Nafeesa kyakykyawar gaskece fara wanda hanken fatar tata yasamu tagomashi da bleaching (dama ance yanxu farare ne ke bleaching) yar siririya sosai ko ince shapeless, duk da cewa Badaru yafison yaga mace dirarriya wato 8 figure, amma a kan Nafeesa wannan raayi nasa ya kasa tasiri saboda san dayake mata.  Itama a bangarenta babu kamar Badaru duk duniya 😳 ( wai ina ruwan kucaka 😂) saboda hidimar da yake mata,  biyayya take masa sau da qafa kamar mijin auranta ko ince kamar ubanta wanda hakan ya qara janyo mata soyayyar gurinsa.  Qiriri Nafee ta tsaida karatu tun tana JS 3 saboda Badaru bayaso tai ilimin boko dan kartafi qarfinsa , iyayenta kuma suka xuba mata ido saboda kar suce lallai sai tayi Badaru ya daina yimata hidima  ta koma xaman kashe pant ( xaman banxa da yawon bin gidajen maqota) kasancewar iyayen nata masu qaramin qarfi kwarai,  tun shekarar data gabata Badaru ya kai kudin aure kuma akai musu engage ana jira ya gama ginin gidansa asaka rana kuma gaf yake da gama ginin. 


     

       A bangaren halayen Badamasi qanin Badaru kuwa xan iya kiran lamarin da bil akasi,  domin duk da kasancewarsu uwa daya uba daya halayensu kishiyoyin junane,  Badamasi yayi karatunsa har xuwa jamia inda ya jika burin mahaifinsu na xama cikakken likitan qashi kuma yasamu aiki a babban asibitin Dutse ta jahar jigawa,  duk da suna kama da Badaru a fuska hakan be hana Badamasi cikar kamala da cikar halitta fiye da Badaruba shikam yana da tsaho fiye dana dan uwansa ga saje da ya tsayar kuma yake gyarashi, dan bokone sosai kallo daya inkai masa xaka iya gano hakan daga yanayin shigarsa,  atsarinsa ya fison mace matashiya ba yarinya ba ba kuma over age ba (tsaka tsaki) kuma mai ilimin addini dana boko sannan wayayyiya wacce xata iya kula dashi,  baiyi katarin samun macen data hada wannan abubuwa ba sai kuma yanxu daya ga Mimi,  tundaga lokacin da suka hadu xuwa yau kimanin 5 wks kenan Kullum tana maqale a ransa da wata irin faduwar gaba da yake a duk lokacin daya tunata,  ya rasa dalilin dayasa har yanxu ya kasa komawa gidan ko no wayarta ya karba dik da cewa kuwa takanas yake baro dutse duk sati da nufin xuwa gidansu amma yana zuwa saí xancen ya shiririce ko wani abun ya sha gabansa.  Da yayi tunanin fara yiwa abba maganarta dan anemar masa auranta in da hali ma so yake a hada bikin dana Badaru,  amma sai yaga gara ya fara neman soyayyarta yanda xasu gina gidansu cikin soyayya da fahimtar juna.  



        Yau asabar xaune suke a falo su 4 abba, Umma, Badaru da Badamasi. Sun gama breakfast kamar yadda suka saba,  Badaru ya sunkuyar da kansa ya fuskanci iyayen nasa dake saman kujera sannan yace " Abba xuwan da mukai na qarshe gidan abokinka Alh Buhari naga wata yarinya a gidan ta kwantamun araina sosai, tunda na ganta nake addua kimanin wata 2 kenan nayi istikhara naji lamarinta ya kwantamun kwarai shine nace bara nai maka magana a neman izinin zuwa neman auranta kamar yadda addini ya tanada " iyayen sukai quri suna kallonsa,  Badamasi dake gefe can akan kujera gabansa yayi wata irin muguwar faduwa wayar dake hannunsa ta subuce ta fado, abunda ya janyo hankalinsu kansa yai saurin daukar wayar tare da saita kansa kana ya kasa kunne yaji amsar da abba zai bashi, amma sai Umma ta riga Abban magana da cewa " Badaru 😳 kana da hankali kuwa?  Ita kuma Nafeesan da ka kaiwa kudin aure take xaman jiranka kayi yaya da ita kenan?  Ko fasa aurenta kayi??.  Yayi qasa da kansa cikin sigar ladabin da yake yaudarar mutane dashi sannan yace " a a  Umma ban fasa aurenta ba itama xan aureta inna kammala ginina tunda da sunanta nake ginin kuma itace ta tsara yadda takeso,,,,,..  Uwarka Badaru naci Uwarka nace ta fada tare da yimasa daquwa sannan ta dora da cewa an fada maka kowa mahaukacine irinka?  A gidan uwarka xaka iya hada mata 2? . Abba dake zaune yana nazarin Badaru ya dakatar da ita da cewa ya isa haka Kaltume ✋🏽 shin ba namiji bane mata 4 aka halasta masa aure meye dan ya hada biyu lokaci daya ya aura?.  Ya juya ga Badaru kai kana sonta ko?  Yai saurin gyada kai, to abu yayi kyau dama nadade ina burin hada xuria da Alh Buhari ashe Allah ya rubuta hakan, ya fada yana murmushi.  Sannan ya juya kan matar tasa tare da cewa ke kuma abunda nakeso dake kisawa abun albarka ai bazai kasa ruqe mace biyuba ke ko hudu zai iya riqewa in shaa Allah,  sannan ya ciro waya daga aljihunsa yana cewa bara muji wacece acikin yayan na Buhari kakeso don alkhairi akewa hanzari. 


      Bangaren Badamasi kuwa yanaji abba ya goyi bayan mahangurbar da Badaru yayi masa ya saddaqar maryam ba matarsa bace yasan cewa xurfin ciki ya kaishi ya baro,  abari ya huce shike kawo rabon wani, kuma yasan Badaru yafishi fada a gurin abba nesa ba kusa ba yasan koda shiya fara farta yanasob maryam sannan Badaru ya fada daga baya wlh abba Badaru zai nemawa auren,  dan haka ya sulale yabar falon a lokacin ya hada komai nasa yayi ya kama hanyar Dutse da nufin xuwa yayi jinyar xuciyarsa ba tare da yayiwa kowa sallama ba dan bayason asan halin da yake ciki,  ya bar abun a xuciyarsa dagashi sai ubangijin daya halicceshi. 


      Bayan gaishe gaishe da tambayar iyali tsakanin Baffa da abba ta cikin waya sannnan abba ya tambayeshi da cewa " ai dankane yaga yarinyar gurinka yakeso, to kasan ni bana gane yaran naka sabida suna da yawa,  Baffa yadan nisa kadan sannan yace " eh to yanxu dai ai ba yan mata a gidan duk na aurarsu yaran da suka rage yanxu qananane basufi shekaru 9-10 ba. Abba yace a wannan dai inaga babba ce dan har yana cewa bayaso auran ya dau lokaci,  toh?  Cewar Baffa kuma a gidana ya ganta?  Eh tabbas yace nan yaga ta shiga da alama ma wai aikin jarida take dan ya ganta da baqaqen kaya.  Baffa ya chafe maganar da cewa auhoooo 🤔 MARYAM ce ai yar gurin Aminu qaninace da ya rasu,  tana can makarantar Horas da lauyoyi amma befi sati 6 ya rage ta kammala ba.  Wanne acikin yaran yake sonta?  Abba ya amsa da cewa Badaru ne,  to mashaallah abun yayimun dadi wlh,  aikai mai aurar da MARYAM ne saboda haka kawai inkun shirya kukawo dukiyar aure.  Lar lah lah Alh haka da sauri inji abba yana murmushin Jin dadi,  Baffa ya amsa masa da tome xa a jira tunda ansan asali aishine dama abun nema a aure.  To shikenan nagode da wannan karamci kuma in shaa Allah xaka jini kafin muxo.  Da haka sukai sallama suka kashe wayar.  



  Mrs Muhammad 😊[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 1⃣7⃣


Dedicated to 

Maryam Baita



    Tun fauxa qawar Mimi,  na jiran xuwan tawagar ango da sunan siyan baki har ta gaji da xaman jiran. Wajen 8:30 pm tai shirin tafiya,  ta miqe ta dau mayafinta dake gefen Mimi ta yafa, tace "qawata nikam xan tafi tunda har yanxu angon be qaraso ba, kuma kinga layin naku da nisa daga titi kar dare ya qarayi inrasa abun hawa". 


Mimi ta marairaice cikin zubda kwallah 😪 tace fauxa kema tafiya xaki kibarni kamar yadda kowa ya tafi yabarni?  Fauxa qawancenmu yace haka?. 


Ta xauna gefen Mimi tare da cewa qawata haquri xakiyi, kinsan nabar Aslam a gida gurin mama, kuma nasan yanxu yanacan yana kuka, indai har Baba ya dawo ya datta bananan nabarshi yana rigima fada xaimun.  Wlh dana taho dashi sai najira xuwan su Badaru inyaso sa maidani gida. 


Ta riqe hannun mimin sannan tace "qawata kiyi haquri komai yayi farko xaiyi qarshe, ikon Allah ne kawai bashi da farko bashi da qarshe,  Allah ya sa alkhairi acikin aurenki. Kimaida AL AMARINKI gurin ubangiji,  in shaa Allahu zakiyi alfahari da wannan aure, karki bari rashin son mijinki ya taba biyayyarki gareshi har irin tawa ta sameki (mutuwar aure),  bana fatan haka Mimi.  Ki tuna ba duk abunda kakeso kake samu ba. Kiyi biyayya, kiyi ibada,  abu na qarshe da xan fada miki shine kada ki sake ki zauna da yunwa ".  Na sanki Jan wuya ce ke wurin ibada,  to qira akai". 


Tana kaiwa nan ta juya ta tafi ita kuka Mimi kuka.  


Tun bayan tafiyar fauxa take xaune a tsorace, koya taji motsi sai ta firgita duk kuwa da cewa ita din ba gwanar tsoro bace,  amma yau sai tasami kanta cikin mugun jin tsoro,  ji take kamar ta tashi ta xura da gudu, kasancewar ba wuta a unguwar sai chaja aka kunna. 


Batasan iya lokacin data dauka a haka ba, sai ji tayi ana bude kofar gidan ta waje, alamar me gidanne. Shigowarsa parlon ya xowa Mimi da wata irin faduwar gaba matsananciya, gumi ya dunga karyo mata. 


Sam bazata iya tantance ko yayi sallama ko beyi ba,  domin ko yayi bataji ba balle ta amsa. Direct yayo kanta tare da cire mayafin data rufe kanta dashi yana huci kamar a fagen daga (filin yaqi) duk da a tsorace dake da abunda yayi hakan baisa ta motsa ba, ya qare mata kallo tare da hadiye wani mugun yawu duk da ramar da tayi hakan bai hana surarta bayyana ba,  ya dure kallon nasa akan fuskarta ya qura mata ido yana mata kallon qurullah,  abunda bai taba lura tana dashi ba kafin ya aureta yau ya ganshi wato tabon sallah take goshinta da danannen bakinta,  sannan kwantancen gashin dake gaban goshinta,  hakan yasa ya cire mata dan kwalin kanta,  kyakykyawan gashin kanta dashi sampoo yake tashin qamshin mega growth ya bayyana, " SUBHANALLAH " ya furta afili sannan a zuciyarsa yace dama anasamun macen bahaushe da irin wannan gashin?  Ya shafa gashin,  sannan ya tura hannunsa cikin wuyar rigarta ya cafko qirjinta, abunda yayi tsananin firgigita tai saurin yin baya ta maqure jikinta. 



Taso muyi sallah,  ya fada ransa a hade cikin sigar bada umarni,  sanin cewa batai sallar ishaba yasa ta tashi ta bishi inda yabi wato toilet tayi alwala suka fito, ya jasu Sallah sukayi isha,  sallar ma aurata ta biyo baya. Tasan akwai adduar da manxon tsira (s a w) ya umarci miji ya dafa kan matarsa yayi mata ita kam baiyi mata,  ya tashi yaje kitchen ya dakko cup ya tuttula L&Z Milk ya shanye sannan ya kuma cika kofin ya miqa mata a hankali ta girgiza kai alamar bata sha,  ya bude ledar kazarsa ya cirota sai tashin qamshi take ya dora kan plate " zo muci " abunda ya cemata kenan, bayan ya fara yagar kazarsa yana hadawa da madarar yana kurba, alamar an dade ba a hadu ba 🤣 (lol), ko kallonsa bataiba balle ya samu amsa. 


Bayan ya tashi da kaza guda da liter daya na gorar madarar l&z, ya ture ragowar   kayan da yaci gefe ya cire rigar shaddar jikinsa tulelen cikinsa ya bayyana alamar anyiwa cikin loding da yafi qarfinsa,  ko singlet babu ajikinsa. Babu batun yin brush domin tsaftace baki kafin kwanciyar bacci balle aje ga dan yin tattaki domin narka abinci daya loda kamar yadda addini ya hana kwanciya bayan cin abinci. 


Ya hayo gadon tare da janyo Mimi jikinsa ya saki ajiyar zuciya, cikin zaquwa ya fara cire mata kayan jikinta,  lamarin da yayi matuqar tsoratata domin Sam babu nitsuwa a tattare da abunda Badarun keyi,  lokacin da yazo cire mata riga ne ta riqe riga qam ta hanashi cirewa, yayi yunqure kwacewa ta qara riqewa gam,  hakan yasa yayi amfani da qarfinsa wajen rabata da rigar, tuni ta sakar masa ganin yana shirin yaga  atamfar super wax mallakar kamfanin Sheraton ( Sheraton super wax).


A haukace yake tsotsar qirjinta duk ya rude,  ya kuma rudata,  kuka take me hade da ihu 😭 , Jin yadda yake matsa mata nono ba tare da tausayi ba kamar ba jikin me rai yake latsawa ba. Ya cire hannunsa ya shinfideta a kan gadon sannan ya xare wandon jikinsa,  ita kam ya dade da rabata da nata kayan,  ya rankwafo kanta da nufin hada bakinsa da nata,  tai saurin kauda kanta, domin a tunaninta ai sai da soyayya akeyin kiss,  ita kuma batason Badaru kuma tayi alqawarin bazai taba shan bakinta na,  kuma bayan haka ma ai Badaru bashi da tsaftar da xata hada baki dashi,  ita kuma macece me tsaftar gaske,  yanxun hakama daya kifu a kanta qarnin gumi yake alamar tun rana rabon jikinsa da ganin ruwa (wanka). 



Sucking din nononta yake tun qarfinsa kamar me shirin xugo ruwa,  radadin da takeji ya zarce faduwa da baki.  Ana cikin hakan ne taji ya danna yatsansa a matancinta,  ta kwallah wani irin ihu tare da miqewa zaune a kan gadon ba tare da tasan tayi hakanba. Xuwa wannan lokaci shikam ya zaqu wajen San cimma burinsa,  ya kalleta cikin fita hayyaci yace "ke meye haka?  Dare na fa kike ihu maqota xasu iya jiwo ki,  hanya nake nema shiyasa,  in kuma kinsan gurin nunamun."  ya qara janyota ya kwantar tana ihu tana bashi haquri da cewa "Dan Allah Badaru kayi haquri na dena,  na tuba da xafi Dan darajar iyayenka."



Yayi murmushin mugunta yace "ba kince bakya sona na ba?  nima ance miki ina sonki ne?  Kinga wannan abun da nake miki shine dalilin aure na dake,  domin MARYAM tun randa na fara ganinki Allah ya jarrabeni da muguwar sha 'awarki,  wlh ko yarinyar da nakeso kamar raina bana sha'awarta kamar ke, tundaga ranar Kullum na kwanta sai nayi mafarkin ina saduwa dake,  komai na halittar jikinki yayimun, amma fa bawai Love ba,  no Just sha'awa ".  Yana kaiwa nan ya kuma danna hannunsa a gabanta tare da tambayarta nanne?  Gara fa in kinsan gurin ki nunamun dan karna shiga inda ba nanba,  Dan wlh saina sadu dake ayau ko mutuwa zaki ".



Shigewar da gaba daya ta ya tsan hannunsa tayi ya tabbar masa da nanne hanyar kuma a take ya fara qoqarin shigarta iya qarfinsa yana wani irin ihu da sambatun ambaton sunan Nafeesa tare da yiwa Nafeesan wasu alqawura na soyayya,  alamar dake nuna cewa itace a ransa.  Muryar Mimi ta katse masa sambatun da yake. 



Cikin kuka wurjanjan take furta "ka dubi Allah kayimun a hankali wlh ban taba yiba,  kayi haquri xata jimun ciwo 😭" . Kalamanta suka sanyaya masa jiki kwarai, ya shafi gefen fuskarta yace "maryam wlh nasan ke ba mazinaciya bace, domin kedin duk wanda ya kalleki zega alamar kamewa a tare da ke koda maqiyinki ne, sai dai mutum yaqi Allah ya yi miki sharri" 


Yana kaiwa nan yaci gaba da abunda yake,  amma ala tilas ya haqura bayan ya dan samu nutsuwa, saboda ya gane baxai taba iya kauda budurcin Mimi a dare daya ba, saboda tana cikin jerin mata masu qaramar halitta, sannan masu kwarin tantanin budurci.  



Bacci kona 1 minute Mimi bata samuba a daren saboda a tsorace take ga ciwon jiki,  ga muguwar yunwar take addabarta,  wacce ta haifar mata da tsananin ciwon kai.



Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 1⃣8⃣


Dedicated to 

Maryam Baita



   Har garin Allah ya waye bata rintsaba saboda axabar ciwon kai,  ta kalli agogon dakin dai dai lokacin 7:45am. Amma ta kasa tashi tayi wanka tai sallah.


Shikam Badaru kiran farko ya miqe yaje ya tsarkake jikinsa yayi nafilfili tana kallonsa, har akai kiran assalatu yayi sallah yaci gaba da karatun qur ani,  da taga bashi da niyyar taimaka matane tace " Dan Allah taimakamun intashi lokacin sallah yana qurewa". 


Ya kalleta shagarai "wai nufinki dan wannan abun da ya faru shine ya hanaki tashi? 😏 lallai ke muguwar yar rainin hankalice,  sai ki tanadi ambulance ranar da mai gaba dayan zai kasance,  tashi kuma karki tashi ai da kindamu dayin sallah akan lokaci da baki tsaya langwai ba,  hakan ya nuna ko acan gidan iyayenki haka kike wasarere da harkar addini abunda kuma bazan dauka ba kenan,  dan ni natsani mutum din dabe damu da addini ba"



Ta runtse ido kalamansa sunfi abunda yayi mata daren jiya muni a gareta, domin ita mutum ce me tsananin kiyaye lokutan sallah,  yan gidansu har cewa suke mata "mayyar sallah" amma rayuwa yau ita ake qalubalanta akan sallah. 



Tana kaiwa nan a tunaninta ta qara kallon agogo a karo na biyu 8:03 agogon ya nuna,  tai wani irin nishi cike da qarfin hali ta yunqura ta miqe,  ta wuce ta gabansa tanajan qafa saboda axaba,  taje kitchen ta kunna gas ta tari ruwa famfon kitchen ta cika tukunya ta dora.



Tananan tsugune a qofar kitchen din ruwan ya fara shuuuu alamun ya kusa tafasa taje toilet ta dakko bokiti ta juye ta daga dakyar ta kai toilet,  naya kallonta dan rashin tausayi ko ajikinsa. 



Bayan tayi wankan zarki dana sabulu ta xuba ragowar ruwan zafin a baho tasa gishiri ta shiga ciki ta zauna dakyar.


Koda ta fito daga wanka ta sameshi xaune yana shan tea da bread din daya shigo dashi jiya,  kuma ga dukkan alamu iya cikinsa ya dafa ruwan tea din banda ita. 



Tuni Badaru ya fita,  ita kuwa tunda ta idar da sallah tana kan daddumar a zaune saboda kabaitar da ita da yunwa tayi ga wani mugun amai da yake taso mata.



Ta rarrafa da dakko wayarta dake kan bed side,  ta kira yaya Faty,  bugu daya ta dauka,  "bazaku zo bane yaya Faty"?  Shine maganar da Mimi ta fara fada bayan Faty ta daga wayar.


Ta danyi jum,  cikin dauri ta danne kukan dake shirin taso mata,  sannan tace "kinga Mimi na tashine da ciwon kai,  ko sallah ma a zaune nayi,  bazan samu xuwa ba sai kin dan kwana biyu,  ya mijin naki kun tashi lfy?. 



Duk da Mimi tasan cewa abunda ya Faty ta fada ba haka bane,  saboda ta fuskanci yaya Faty batasan xuwa gidan Sam dan jiya ma batazo kawota ba,  kuma tasan tausayinta da Faty keji shi ya haifar da haka. Ta daure tace "ayyah sannu sister Allah ya baki lfy,  agaida ya Ahmad. 


Bata qara gigin kiran wani ba,  duk da tasan a al adar gidansu washegarin biki sai sun hadu duk yan gidan anje gidan amarya,  amma ga dukkan alamu ita bata Sami hakan ba tunda gashi har goma tayi amma ko kare baixo wajenta ba. 



Tananan zaune cikin ciwon kai da yunwa wanda tun qarfi suke shirin tayar mata da ciwonta na sarqewar numfashi,  tunani take irin rayuwar auren tada ke shirin faruwa a kanta,  ita dai tasha ji a fili da kuma littattafan soyayya yacce namiji ke tattalin mace a daren farko da kuma washe garin ranar musamman inya sameta virgin,  amma ita sai yunqurin fyade da Badaru yayi mata (to fyade mana tunda bataso kuma bebi a hankali ba) duk da yasani kuma ya tabbatar da cewa ita din virgin dince. Sai kuma dan karen wulaqanci da tasha yau da safe ta hanayar yin halin ko in kula da ita.  Afili ta furta "ALLAH KAINE KA JARRABENI,  KUMA KASAN XAN IYA SHIYASA KA JARRABENI DAN KA GWADA IMANINA,  ALLAH KA BANI IKON CIN JARRABAWA,  KA BANI IKON BIYAYYA GA MIJINA."



Tananan zaune cikin yunwa da nauyin qirji, amma kuma sam batasan koda hadiyar ruwa balle abinci,  taji ana buga gidan. 


Ta tashi dakyar cikin jiri, ta fita ta bude. Little ta gani wato autar momy yar mama, sunanta na gaskiya MARYAM wato sunansu daya da Mimi, kasan cewar sunan hajja gareta babar su momy Lima itace auta a gidan momy shiyasa ake ce mata little (wato  qarama),  yarinyace da bazata gaza shekaru 13 ba,  doguwa fara sol siririya kamar ka harareta ta karye saboda siranta kyakykyawa irin kyan su yaya Faty tunda dama tafi kama da yayan momy.  



Little akwai kafirin iyayi da son nuna iyawa saboda rayuwar da ta taso ciki kasancewarta auta yasa aka sakar mata take sangarta son ranta ga kuma gatan yayye dana iyaye. 



Tsaye take a qofar gidan alamar itace da buga qofar sanye take cikin riga da skirt yan kanti (kamar yadda yake ga dabiarta bata cikasa natives ba indai ba biki ba) kanta ba dankwali sai siririn gyale datai yane kanta dashi, fuskar nan tasha make up ga kuma wani qaton glass data kwama wanda ya shafe rabin fuskarta. Daga can bayanta kuma Huxaifa ne (Dan gidan Baffa)  ke gyara parking din mota da alama shiya kawo Little din. 



Mimi farin ciki ya rufe ta daka tsalle ta rungume Little din kamar ta shekara bata ga na gida ba haka takeji,  tace "autar momy kece 😊" ku shigo ciki Huxaifa,  


Little tace " name sake kamar yadda take kiran Mimi ko kuma tace mata ya Mimi,  wlh mama ce ta tasoni,  wai duk wanda tace yaxo ta aiko shi sai ya zame, waisu tausayinki sukeji,  shine suka hadu ita da momy suka tattgoni " 



Ta kalli gidan ta yatsine fuska sannan ta dora da cewa " nima fa name sake da nasan haka zanxo in tadda gidannan bazanzo ba,  no wonder kowa yaqi xuwa, tai tsaki,  ta dora da cewa duk yanda ake fadar munin gidannan banxaci abun yakai haka ba,  gida sai kace xuciyar kafiri, gaskiya guy dinnan ya kwafsa mana " 



Dai dai nan Huxaifa ya shigo da kaya niqi niqi,  ya ajiye ya fita yace bari in jiraki a waje Little,  Mimi tayi tayi ya zauna yaqi ko saboda qanqantar parlon ne oho. 



Mimi ta fara fito da kayan daja ajiye tana gani, yawanci kayanta ne na amfanin yau da kullum, kamarsu system da chajar waya sai kuma pos 👛 dinta, wacce ke qunshe dasu ATM dinta da I D cards. 



Little ta matso tana bude ragowar kayan data shigo dasu yanxu tana cigaba da mita " ai wlh wannan anguwar kwata kwata batai ba duk ba Local champions ne a unguwar muna kawo kai naga ana kiwon shanu da raquma sai kace a ruga "


Mimi tai murmushi tare da cewa to ya za ai Little kowa da qaddararsa a rayuwa kuma mutum baya kaucewa qaddararsa ni tawa qadddarar kenan 😊.


Ta fito da leda da wani ruwa a ciki me sanyi tace wai gashi Maltina ce da madara mama ta hada miki tace ki shanye yanxu, Mimi tai tsai tana jinjina soyayyar uwa ga danta, wato tasan tana cikin yunwa sannan kuma dan tsabar soyayy sai data hada mata, sannan ta bayar a kawo mata lallai agaida uwa (Allah ya sakawa uwa da gidan aljannah).  



Atake kuwa ta bula ta shanye,  wani sanyi yana ratsata ta balli maganinta da aka hado mata dashi yanxu cikin kaya ta hadiya saboda nauyin da qirjin ke mata. Little taci gaba da nuna mata kayayyakin ta miqo mata miya cikin tukunya da taji naman kaji ta soyu tai shar sai qamshi take tace gashi inji momy,  sannan qanqara guru guru ta pure wata cikin leda tace wannan kuma inji mama ga kuma soyayyan naman shanu cikin bokitin roba inji yaya Faty. 



Haka dai abun alheri niqi niqi ta dunga kukan murna da jinjina soyayyar uwa da dangin uwa akan dá. 



Nan da nan kuwa taji kwarin jikinta ta tashi Little ta tayata suka gyara gidan ta bawa Huxaifa kudi acikin wanda mama ta kawo mata ta riqe a hannunta ya siyo mata ruwan pure wata leda daya da maltina rabin dozin ta xuba a cooler ta fasa qanqara akai,  sabida gidan fridge be samu shiga ba.  




Taga kayan abinci a kitchen sai dai kayan miyane babu   hakan yasa ta dafa farar taliya da nufin aci da miyar da momy ta kawo. 


Suka bade gidan da room freshners masu sanyin qamshi,  gidan yayi fes tayi wanka ta canja kaya harda make up dan qarfin hali. 



Koda Little ta tashi tafiya Mimi ta bude akwatin lefenta ta dakko mata atamfar súper collection me kyau da sabulu da mai,  domin taji dadin xuwansu sosai,  shi kuma Huxaifa ta bashi turare da sabulai,  sannan ta bawa little ragowar kajin da Badaru ya kawo guda biyu tace ta kaiwa mama.


Har mota ta rakasu tana ta godia tace da Little sai yaushe autarmu?  Ta daure fuska sannan tace " Allah name sake baxan kuma xuwa ba saboda daga gidan har me gidan basuyimun ba,  wlh kinfi qarfin auran wannan bagidajen kawai dai akwai abunda Allah yake nufi da hakan" 


Huxaifa ya jinjina kai cikin mamakin qarfin hali Iron na Little, sannan yayi saurin katseta da cewa "ya isa uwar iyayi in banda shirmenki mutum yana auran matar da ba tasa ba"?


Sukaja Mota suka tafi suna dagawa juna hannu. 






Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 1⃣9⃣


Dedicated to 

Maryam Baita



Tafiyarsu bada jimawa ba akai kiran sallar zuhr,  bayan tayi sallah tana zaune kan kujera so take tadan runtsa ko tasami saukin ciwon kai,  amma abun ya gagara sai tunani take. 


A irin hakan ta tunano rayuwarta acan baya.  Akwai wani lokaci da AL AMARINTA ya damu mama har ta dau shawarar wata qawarta yar gurin aikinsu wacce suke kira da Anty saude.


Anty saude ta dade tana fadawa mama ta nemi taimakon malamai akan LAMARIN Mimi amma maman tanayin burus da zancen, sai dai a lokacin da matsin lambar Baffa Yayi qamari akan Mimi dole tasa mama amsa gayyatar Anty saude. 


Anty saude ta tasa Mimi gaba babu san ranta ko kadan dandai mama ta dage ne,  sukaje gidan wani malami acan wajen kurna babban layi.


Duk da bayanin da Anty saude taiwa malamin akan matsalar Mimi sai da ya buqaci Mimi ta qara yi masa bayani da kanta,  wanda hakan yasa Mimi kuka domin batasan abunda zatace masa ba.  Cewa xatai ta kasa daukan qaddarar da Allah ya dora ko yaya?  Ko cewa xatai ya jawo mata mijin aure koda lokacinta beyi ba?. Sam ita batasan bin malamai. 



Ganin Mimi na kuka yasa ya haqura dajin lamarin daga bakinta sannan ya dora da yimata tambayoyi kamarsu : kina mafarki ana saduwa dake?  Tace gyada kai,  alamar eh.  Kina jin bacin rai haka kawai?  Tace eh. Kina tsanin ciwon mara lokacin al ada?  Tace eh. 


Ya kalli anty saude yace da alama baqin aljani ya auri yarinyar nan,  kuma indai ba a rabata dashiba to wlh ita da aure har abada.


Mimi ta tsorata dajin cewar wai itadin aljani ya aureta. 


Ya basu turaren hayaqi ya fada musu yanda xatai amfani dashi,  Anty saude ta bashi sadaka yace "a a dauki aimu sai buqata ta biya ake biyanmu."


Koda suka dawo ta mayarwa da mama yacce akai tabata turaren daya bata,  mama tasata gaba tayi saida tayi duk turaren. 



Kafin wa adin daya dibar musu na komawa gurinsa yayi,  cikin ikon Allah Mimi ta sami saukin mafarkan da take yawanyi har ta fadawa mama ta dunga murna da cewa " Allah ya sa qarshen baqin cikinmu kenan,  dama saude ta dade tanamun tayin neman taimako ina sharewa ashe akwai waraka aciki "


Ranar komawarsu gurin Anty saude bata samu xuwa ba saboda wani uxuri da yazo mata,  Mimi ita kadai taje gidan. 


Tai sa ar samunsa shi kadai acikin dakinsa da yake sallamar baqi, ta fada masa irin nasarar data samu akan maganin, yace yau ina maman taki?   Tace taje asibiti gurin me haihuwa. 


Yawwa dama nasarar aikin mukeso mu fara gani tunda yanxu anyi nasara akan wannan sai mutafi mataki na gaba.  Ya kalleta sannan ya dan rage murya "kinsan tunda aljanin ya ruga ya sadu dake dole sai anyi miki wani dan gajeren aiki,  wato sai an tsarkake gabanki saboda shafar da aljani yayi miki,  sanyi rubutu a gabana sai in dan shigeki  da nufin haramtawa aljanin qara kusantarki anan gaba." 


Yana kaiwa nan ya matso kusa da ita da nufin tabata tai wufff ta miqe tsaye ta nufi qofar fita yayi saurin riqota da cewa ke taimakonki xanyi,  inkuma bakiso shikenan ki biyani kudin aikin da nayi miki rannan.  Kafin ya qarasa tai masa wata muguwar kutufo wanda ita kanta batasan ta iyaba, sai yanxu da taga ana shirin keta mata haddi.  Nan take kuwa sai gashi a qasa wanwar.  Sannan ta dora da cewa "in abunda kai nufin yimun alkhairine Allah ya saka maka da alkhairi in kuma sharrine Allah ya kawo me kwatantashi akan yar cikinka" sannan ta bude jaka ta watsa masa kudi,  tace ga ladan aikinka nan, domin ni banacin haqqin mutum. 



A burkice ta shiga gida, saboda har yanxu tsoron abunda akai mata bai bartaba idonta jawur,  umma take tsakar gidan tace "lfy Mimi?  Naganki wata iri ko hatsari kikai " ko ta kanta batabi ba ta shige dakin mama. 


Har bedroom din maman ta isketa cikin kuka ta fara magana " mama meyasa bazaki dau qaddarar Allah akaina ba?  Shin na dameki da yawon bin mazane shiyasa kika damu nai aure?  Bakya ganin takurawarmu ga lamarina ba shishshigine ga Allah ba?  Indan Allah ya kyalemu da kanmu xamuji dadi?  Akwai wanda xai mana abu ba Allah ba? Wlh tun farko banso xuwa gurinnan ba Allah ya gani kece kika takura. Wlh!  Wlh!!  Wlh!!!  Da inbawa malamin tsibbu jikina da nufin zaimun aikin da zan samu miji gara nayi ta xama ba miji har abada , domin nasan Allah baya mantuwa kuma bai manta daniba "


Jikin mama na rawa,  cikin razana ta kamo mimin sannan ta zaunar da ita kusa da ita tace " meya faru mamana?  Kinsani a duhu waye yayi yunqurin keta miki mutunci? "


Ta mayarwa da mama yadda sukai da malamin,  mama ta tsorota da lalacewar zamani,  ta yadda malami zai nemi mace dan kawai taje neman taimako,  sannan ta godewa Allah daya bata nutsatstsiyar ya.  Tace yi haquri Mimi bansan haka lamarin yakeba wlh da bazan soma ba.  Da haka aka rufe chapter neman taimakon malamai akan LAMARIN MARYAM. 



Badaru bai dawo gidanba sai magariba,  gidan yayi baqiqirin saboda rashin wutar Nepa kuma duk fitilolin babu chaji.  Ga xafi kasancewar ana tsaka da xafi,  ya qudure dole ya samo injin generator koda qaramine saboda bayason zafi.



Yayi amfani da fitilar wayarsa wajen haska parlon ya ganta a xaune akan pray mat alamar sallah tayi. 


Tayi masa sannu da xuwa, ya amsa direct ya wuce kitchen ya xubo abinci a tray (ina ruwan khadimul ci,  bama a plate ba 🤣) taliyar da ya xubo xatai guda daya, lafto miyar kafin dama kajin, ya faraci ba tare da tambayar inda ta samu kayan miyan da tayi girkin ba ganin cewa baibata ko asi ba kuma bai kawo kayan miya ba. 


Tayi mamaki da taga ya cinye Raliya tas ya dora da gwangwanin maltina, kamar shi ya siya.  Yayi gyatsa. Sunanan zaune ita tana jan carbi shi kuma na danna waya aka kira isha ya tashi ya tafi masallaci. 


Bayan idar da shafa'i  da wuturi ta je kitchen ta debo red meat din da aka kawo mata dazu soyayye ta zauna taci tasha maltina,  sannan taje tayi wanka da brush ta gyara jikinta da turarurka masu sanyi ta sanya riga da wandon bacci cotton,  ta fito parlo ta xauna tana charting duk kuwa da cewa babu chaji a wayar,  jira kawai take abunda taci ya fada taje ta kwanta dan bacci takeji. 


Yau dai ansamu cigaba domin Badaru yayi wanka bayan dawowar daga masallaci, brush ne dai beyiba alamar be saba yiba. 



Beyi mata magana ba, kawai dai yazo yaja hannunta kamar tunkiya ya shiga da ita bedroom din ya cillata akan gado tare da cewa " gara mu fara da wuri mu gama don yau bacci nakeji" babu xancen wani romance a cikin tsarinsa kawai dai ya hau wasa da qirjinta da kuma tsotsa kamar tababbe,  tun tana daurewa har ta gaza ta fara yunqurin ture kansa daga jikin nipple dinta, lamarin da yasa ya gartsa mata cixo a nipple din,  ta kwalla qara.  Ya fara yunqurin cinma burinsa, amma sai dai yauma kamar jiya ya kasa duk iya nacinsa dole ya haqura domin shima ya fara jiwa kansa rauni.


Ya kwanta cike da baqin cikin kasa cimma burinsa,  sannan na kukan da Mimi ke masa,  a xuciyarsa yace kin kusa kiyi me dalili dan wlh gobe gurin Mekudi (abokinsa) xanje ya nemomin maganin qarfin maza. 



Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 2⃣0⃣


Dedicated to 

Maryam Baita



Washegari bai samu kansaba sai wajen qarfe hudu na yamma,  saboda yaje kasuwa daga can kuma ya wuce ya sayi inji (generator) ya kai gida ya kira masu hadawa suka hada, sannan yayi sallah ya tafi majalisarsu dake unguwarsu unguwar da iyayensa suke.


Ya samu Maikudi yace yawwa wlh kai nake nema tun safe nake kiran wayarka a rufe,  Maikudi yace wlh babu chajine.  Sannan suka kebe daga can qarshen tabarmar dake gurin. Yan gurin sunata zolayarsa da ango meya fito da kai yanxu,  ba mun baka hutu ba. 



Mekudi abokin Badaru ne,  duk da cewa halinsu ba daya ba, domin mekudi irin mazannan mayun mata bashi da aikinyi sai yawan yaudarar yayan mutane duk da cewa yana da mata har yaya biyu,  gashi Dan duniya na qarshe.



Bayan Badaru ya gama fada masa abunda ke faruwa na kasa kauda budurcin Mimi (kuji rashin sanin ciwon kai 😒). Mekudi yace " to kodai tayi cushe cushe nan nasu na mata a wajen?  Kasan hakan nasa irin hakan" 



Badaru yace "banajin hakan,  domin yarinyar bata da rawar kai irinta yan matan yanxu,  bayan haka kuma bata sona banaji zatai wannan abun da nufin burgeni,  nafi dauka dai halittartace hakan.  Yarinya fa yar baiwa ce ya fada yana dariya,  sannan ya dora da cewa ta hadu dan kawai banasonta ne"



Yace to shikenan  yanxu inada wani ragowar magani yana Mota ka hadiya tunda naga amatse kake,  kafin in samo maka wani.  Yawwa mutumina cewar Badaru wlh na matsu inji ya lamarin yake 🙈.



 

Suna tsaye kofar gidan su Nafee,  hira suke,  awanni 3 kenan da shan maganin da Mekudi ya bashi, amma ga dukkan alamu maganin ya fara aiki a jikinsa,  dan ji yake kamar cafko Nafee.



Yace mata "ni bara in tafi Nafee"  ta marairaice tace kace baka santa amma tunda ka aureta inkazo Allah Allah kake ka koma gunta,  me hakan ke nufi? 



Yace "yi haquri yau kam banajin dadi ne,  amma gobe innazo xan dade kinji" yana kaiwa nan ya fice ko takanta be kuma bi ba.


Yana xuwa ya ganta a duhu ga zafi saboda qanqantar gidan,  wayarta babu chaji dan haka take zaune a duhu. 



Yaje ya tada inji, kunna fankar parlon . Ta saki ajiyar xuciya dan zafi ya dameta kuma zafi kan iya tayar da ciwonta. Yaje yayi wanka ya xuba abinci yaci. 



"Zo" yace da ita yana kashingide a jikin kujera, yanajin wani irin feelings.  


Ta marairaice cikin zubar da kwallah tace "Badaru kayi haquri wlh kaina ciwo yake tun renda aka kawoni gidannan" 


Yayi dariyar mugunta yace to aini ba kanki xan taba jikinki kawai nakeso,  saboda haka kixo kafin na tashi nayi miki abunda xakiyi nadama.  


Tai saurin qarasawa inda yake da rarrafe Jin abunda yace, "cire rigarki" ta zaro ido 😳. Haka dai saida yasata tai tik ta hanyar tsoratar da ita. 



Sannan ya buqaci ta tashi tayi tafiya a gabansa a hakan, lamarin da ita kuma taqi yarda duk kuwa da yadda yakai da naci dole ya haqura,  ganin tana bata masa lokaci kuma ga magani na aiki a jikinsa yasa ya huqara ya haye kanta anan kan centre carpet din parlon da kuma fitila akunne (Dan tsabar rashin sanin ciwon kai da rashin kunya). 



Ashe kuwa gaskiyar Badaru da yake cewa ta tanadi ambulance,  domin kuwa bata tabajin labarin daren farko me wahala irin nata ba. 



Tun tana yunqurin kwatar kanta harta gaza ta xuba ikon Allah ido,  ta gurxu iya gurxuwa cikin mugunta da wutar ciki ya kauda budurcinta.



Ya dunga kuka wiwi yana sambatun kiran sunanta ( dan rainin wayo ashe kasan sunanta🤔) tare da alqawarin riqeta iya rayuwarsa.



Wannan dare ma bata runtsaba saboda ji take kamar an tsagata da reza an mata tsarki da attaruhu.  Yayin da Badaru yake bacci harda munshari alamar cikar buri,  kuma munsharinsa ya temaka kwarai wajen hanata bacci.



Sai gab da asuba ta samu baccin shedan ya kwasheta (na shedan mana tunda zai hanaka sallar akan lokaci).



Sanyin ruwan daya shafa matane yasa ta farka,  "sannu maryam, kin hadu ni nasan bada banxa na gigice akanki ba,  gaskiya xan huta,  fatana ki koyi dauriya dan naga kedin raguwa ce" kalaman Badaru kenan. Kuma yana gama fadar hakan yasa kai ya fice,  ba tare da la akarin yayi mata tagargazar da xata buqaci temako ba.



Yauma kamar ranar itace ta gyara kanta tayi sallah, ta nade xanin gadon da ya baci da wani abu chakal .kamar jirwaye da kuma ruwan ciwo. Amma babu jini sam. Ta shinfida wani.



Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 2⃣1⃣


Dedicated to 

Maryam Baita



A hankali rayuwa taci gaba da tafiya, lokuta na gudu tunda gashi Mimi ta samu kimanin wata daya da rabi a gidan miji. 


Ixuwa yanxu yan gidansu kaf babu wacce bataxo mata ba inka dauke Faty,  domin ta kasa xuwa gidan Mimi,  ko meye dalili oho.


Kuma duk wanda yaxo tanajin dadi sosai,  kusan ma ince duk takun saqar da suke da wasu daga cikin yan gidansu xuwansu gidanta ya goge mata komai aranta, duk da cewa in anxo sai anyi habaici da kushe gidanta da kuma jajanta mata irin mijin data samu. 


Fauxa kam xuwanta daya gidan duk kuwa da nacin da Mimi ke damunta dashi a waya na rashin xuwanta. Takance "Mimi ni bamai aure ba aga ina yawan xuwa gidanki sai ace naqi zaman aure inaso inkashe miki naki "


Dake ita din ba gwanar qawaye bace,  sannan kuma mafi yawan qawayen basusan tayi aure ba,  sai ya xamana babu wata qawa inka dauke fauxa da taxo gidanta.  Lamarin da yayiwa Badaru dadi,  domin shi a tunaninsa qawaye na iyasa Mimi tayi masa bore kan axabar da yake mata. 



A fannin kwanciyar aure dai Mimi ta kasa sabawa da salon Badaru,  domin ita dai ixuwa wannan lokaci Kullum abun sabo yake gareta.  Mekudi ya riga ya bata Badaru da shan maganin qarfin maza, kawai dan aganawa yar mutane azaba.



Saboda da haka Kullum Badaru cikin buqata yake,  baya duba cewa ita din abun Sam be qarbeta ba duba da yanda take jigata aduk sanda ya kusanceta,  wataran ma har rasa numfashi take na wucin gadi (ciwonta). 



 Yau laraba,  kuma tun 7:30  Badaru ya fita a cewarsa akwai wadanda zasuzo siyan kaya shagonsa a kasuwa zaije ya sallamesu.



Bai dawo gidan ba sai yanxu,  11:45 am, ya datta Mimi duke a qofar kitchen tana shirya kayan wanke2 da tayi. Tana cemasa sannu da xuwa bebi takanta ba,  kawai hannunta ya kama kiiiii yayi daki da ita.



Yana xuwa ya axata kan gado ya cire wandonsa,  yana me cewa "kinga abunda ya dawo dani,  wata nagani yanxu a kasuwa shedan ya qawatamun ita shine na dawo insamu nutsuwa"



Yana fadar haka ya farmata ya fara yunqurin shigarta,  babu batun romance a salon kwanciyar Badaru sam,  yanayin kwanciyarsa dai tafi kama da kwanciyar da manxon Allah (s w a)  ya siffata masu yinta da dabbobi,  wadan da suke farwa mace batare da tayar mata da tata sha'awar ba.



Sai da ya biyawa kansa buqata,  sannan ya lura da pink din janbakin data fente bakinta dashi,  ya bashi sha'awa kwarai,  dan haka ya nufi bakinta da nufin kissing dinta, tai saurin kauda kanta. 



Ya tsaya,  yana qare mata kallo da Jin haushin ta hanashi tsotsarta yace " wai ke kina nufin bazan sha bakinki ba?  Inafa lura dake duk sanda nazo shan bakinki sai ki kauda kanki,  sai kiyi tayi kinwa kanki,  tunda nasamu abunda yafi baki ajikinki kuma ina yanda naso dashi ai shikenan"



Bayan yayi shirin fita ya sameta akan gadon har yanxu bata gama wartsakewa ba da dirxar da yayi mata,  yace " ni xan fita inason inbiya gidane in duba Abba yau be fita kasuwa ba wai kansa ke ciwo"  tace to  Allah ya sawaqe,  kai mai sannu. 



Sannan tace " Dan Allah ka siyo wake so nake inyi wake da shinkafa" sai da yakai qofar fita sannan ya cillo mata 30 naira yace gashinan ki sayi waken,  yasa kai ya fice.



Tai tsam tana tunani,  naira talatin ai ko wake gwangwani daya baxata sai mata ba duba da yacce rayuwa tai tsada yanxu. 


Tunda aka kawota gidan Badaru bai taba daukan ko naira biyar ya bata ba,  da sunan kudin cefane ko kudin wani abun daban.  Duk da cewa baya kawo kayan miya ko nama,  tunda ya aciye abinci da maggi me star sai jarkar mai kings sai gishiri be kuma kawo komai ba. 



Tunda miyar da momy ta kawo mata ta qare,  bata qara sa kayan miya a idonta ba, sai da ta gaji dan kanta da cin abinci da mai da yaji (duk da cewa ada tana marmarin mai da yaji,  lokacin tana cikin gata) taga cewa kanta take cuta tundashi bai cika cin abincin rana a gidan ba,  na dare ma inyaga bai masa ba sai ya fita wajen mai shayi a hada masa da kwai,  ko ya siyo tsire iya cikinsa yaci a gabanta babu tayi,  duk da ko yayi mata tayinma baci take ba.



Da yake gidan amarya baya rabo da yara a hankali yaran unguwar suka fara shiga gidan,  ita kuma tasa hannu bibbiyu ta karbesu bata nuna musu kyama ba,  dan sune yan uwanta yanxu,  cikin shirinta na karbar rayuwa aduk inda tazo mata. 


Wadannan yara su take aika su siyo mata duk abunda take buqata acikin yan kudinta da mama ta bata, wanda little ta kawo mata. Wanda kuma tun daga su maman bata kuma aiko mata da kudiba saboda rashin dan aike.


Amma ta da wata yaxo qarshe akai salary ta saka mata kudi a acctn dinta, kamar yadda suka saba ita da yaya Faty duk wata in sukayi albashi sukan tura mata kudi ta acct dinta,  hakan yasa da wuya ta rasa kudi. Amma yanxu abu 2 yayi mata togaciya daga daukan kudin da suke tura mata. 


Na farko,  ATM dinta da yayi expire wanda dole sai taje ta gyara kafin ta samu hurumin fidda kudi. Na biyu kuma shine takunkumin da Badaru ya qaqaba mata,  domin tun sati 2 da xuwanta gidansa ta tambayi xuwa kitso yace mata baya cikin tsarinsa fitar matarsa daga gidan aure inbada lalura ba,  kuma koda xata fita ma yanaga sai ta shekara a gidansa.  Wannan shine dalilin da yasa ko daxu da yace zashi gida duba Abbansa batace xata bishi ba,  saboda yace wannan shine tsarinsa. 



Da yake ance me dá wawa, saboda jan yayansu da take ajiki yasa be kitson take xuwa har gida tai mata kitson da baya wuce kwana 5 ya tuje saboda Kullum cikin xubawa kai ruwa take da kuma yanayin halittar gashinta, domin kanta shampoo din da tayi da biki ya dade da fita,  kuma bata da wani man shammpoo din da take amfani dashi (mega growth) domin kaf cosmetics din lefenta ba irin wanda take amfani dasu bane,  kuma yawanci anrabar dasu ga dangi (kamar yadda akeyi a al adance).



Kudin hannunta sune kayan miya, siyan salak in buqatar cin salak din ta taso,  sune biyan kudin kitso da kuma siyan sabulun wanki. Domin akan idonta Badaru kan hada wankinsa ya bayar a wanko a gogo masa, amma bai taba hadawa da nata ba.  Gashi ita kuma bata iya wanki ba zata iya cewa tunda take bata taba wanke kayanta na sawa ba,  iyakacin wankinta undis suma a washing machine take watsasu ta wanke.



Duk da cewa Badaru yasan bai taba kawo kayan miya gidansa ba,  hakan baya hana in yaga anyi abinci da miya koma har da nama ya zauna ya take tumbinsa,  kusan ma bayacin abincin gidan sai yaga Cima da canja maana anyi me dadi,  Ko kunya bayaji ko kuma ya tambayi ina akasamu kayan girkin saboda tsabar San banxa (san banxa mesa gidan yari cika 🙄😄). 



Yau da gobe tafi qarfin wasa kuma xara bata barin dami dan haka kudin hannunta bai gaxa 800 ba, dan haka ta tambayeshi ya bada kudin wake (abunda bata taba yiba, wato tambayar Badaru abu koda kuwa haqqinsa ne yayi).  Acikin wannan 800 din data rage mata tanason siyan pad dan lokacinta ya kusa,  ga siyan sabulun wanki ga, ga kudin wankin,  sannan ga kanta ya dameta ya cika ya sarsarqe alamun yana buqatar shampoo, amma da yake hakan bata samuwa dole ta biya kudi a kitse matashi. Gashi tanason siyan wake ta hada a dahuwar shinkafa dan tagaji dacin fara da mai. 



Atake a gurin ta samowa kanta solution,  domin kudin bazasu isheta ba,  saboda haka ta yanke shawarar siyan always (pad) tunda ita dole ce,  kasancewarta mace me xubar da jini a lokacin al ada yasa sinqi daya bata isarta sai daya da rabi ko biyu.   Yanxu da rayuwa taxo mata a haka ta yanke shawarar hadawa da tsumma, ragowar kudin xata sai sabulun wanki tai wankin da kanta tunda ba kudin kai wankau, sannnan ta bada kudin kitso ai mata kitso ragowar kudin ta sai wake ta dafa a shinkafa. 



Rayuwa kenan abar tsoro wai yau maryam ce da wanki. Ahankali ta furta "rayuwa ce wataran sai lbr, dama aure a 2 ne ko kaci gaba ko kaci baya." 


Tana kaiwa nan a tunaninta ta miqe ta fara aiwatar da abunda ta shirya.



Badaru bayan ya isa gidansu ya duba jikin Abbansa,  yana zaune suna dan taba hira da Abban ummansu take gefe sai kallonsa take asace,  saboda kunya irin ta dan fari.  


Can dai ta kalleshi tace ina wajen su maryam din?  Yace ko lfy,  ai canake da ita xakuxo duba alh? 


Yayi saurin cewa tananan qalau tace ma a gaisheshi da jiki,  ni banason gantaline a tsarina banason matata ta fita. 



To sannu me mata hakan yayi dai dai mara kunya inji Umma.  Sannan ta dora da cewa " ai wannan yarinya Allah ya saka mata da alkhairi,  ta gyaraka kayi tas kayi jajur da kai har wata teba ka ajiye.  Wannan yarinya ta samu tarbiyyar Allah ya sakawa iyayenta da alkhairi" ta kalli abbansu Badarun sannan tace "wlh Alh tunda mukaje yarinyar nan take hidima damu ta kawo wannan ta kawo wancan,  sannan ta samu hijabi ta saka a jikinta har muka taho bata cire ba,  muna kan kujera tana qasa idanunta a qasa. Aini Alh banzaci acikin yaran yanxu masu xurfin karatun boko akwai irin maryam ba,  haka in su Aisha (yayanta mata) sukaje mata take hidima dasu da yayansu inzasu taho,  tabawa wannan mayafi wannan takalmi kai gashinan dai abun sai San barka"



Alh inuwa ya dubeta yayi murmushi sannan yace lallai kaltume wannan suruka taki tayi miki 😊 dan naga kullum in muka zauna sai kinyi bitar ahalayenta. 


Tai saurin cafewa da cewa wlh kam tayimun,  ai maryama ta haifu yarinyar yar halak ce,  ni da Xaiji shawara ma ai daya haqura da Nafeesan yayi xamansa da wannan dan ni kam maryam tafi kwantamun.



Badaru yaji maganar kamar saukar aradu ya dago a razane 😳, yace Umma in haqura fa kikace?  Shekara nawa Nafee na jirana?  Innaqi auranta na yaudareta,  Kuma bayan haka ma ina sonta baxan iya haqura da itaba. 



Umman ta watsa masa harara tare da cewa "ai tare aka hallicceku shiyasa bazaka iya haquri ba"



Abba yayi saurin katsesu kafin maganar tayi nisa yace "ya isa kaltume,  ki gyaleshi tunda yana sonta.  Maryam din ma da za a aurota ai saida kika nuna turjiya,  amma yanxu kinfi kowa yaban halinta.  Itama wannan kikasan nata kyawun halin?" 


Umma dai ta tabe baki tare da cewa Allah ya bada sa a 😏




Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 2⃣2⃣


Dedicated to 

Maryam Baita



Watanta biyu dai-dai a gidan, xuwa wannan lokaci ta saba da wahala,  duk cewa ance ba'a sabo da wuya.



A bangare guda kuma tana cikin matsananciyar wahalar  auratayya da Badaru. Irin yanda duk wata amarya da takai budurcinta gidan miji ke fuskanta a farkon aure. Ta wahala iya wahala saboda kwanciyar aure da Badaru tafi komai jigatar da Mimi.



Ga wani irin ciwon qirji da yake yawan fyadeta,  saboda bacin rai da rashin cima mai dadi (mai da yaji). Tuni maganinta na numfashi ya qare,  kuma tun kafin maganin ya qare intasha baya yimata aiki.  Ga uwa uba zafi dakesa koda yaushe cikin daukewar numfashi take,  saboda Sam yanayin ciwonta bayason zafi. Badaru kuma baya tada inji saiya dawo kuma duk inda 11 tai zai kashe yayi baccinsa inda ita kuma xata kwana fiffita da hand fan dan kiyaye lfy ta.



Babban abunda yafi damunta kuma shine; duk wannan hali da take ciki baisa Badaru ya tausaya mata yace taje asibiti ba, ko ya kaita.  Hasali ma haka yake shafe tsawon lokaci yana auratayya da ita cikin shauqi da sambatu.  Baya gajiya da abu daya wani lokacin sai yaga bata numfashi sannan yake saurara mata.



Bacin rai,  yunwa,  zafi da rashin kwanciyar hankali ya hadu ya saukar mata da wani irin matsanancin ciwon qirji. Wanda ya kwantar da ita wanwar ko sallah sai dai tayi zaune,  aikin gida kuma in su abuwa (yaran maqota dake shigo mata) sunxo suke yimata,  babban abin takaicin shine bata da ko naira 5 din siyan ruwan pure water.  Wayarta ma kona plashing babu. 



Yau monday,  wanda ta kama kwananta 3 da kwanciya wanwar saboda nauyin qirji da daukewar numfashi.  Ya xamana ko kwanciyar ta gagara sai dai tai ruf da ciki ta danne qirjinta saboda ji take kamar inbata danne dinba zai tarwatse. Daga waje kuwa kana iya jiyo hakin da take.



A haka Badaru yazo cikin shirin fita, yana balle botiran rigarsa, ya kalleta a wulaqance tana kwance ruf da ciki a kan centre carpet din parlon yace 'bakisan wannan kwanciyar babu kyau ba a musulunce?' sannan ya dora "nifa banason langwai kin cika gida da gurnani sai kace tsohuwar kafura wai ke ciwo ko?  To wlh wannan ciwon da kike rashin dogaro da Allah ya kawo miki shi"  (kunji jahili 😒). Yana ida fadar haka ya sa kai ya fice dan tsabar rashin tausayi da tsaurin xuciya.



Ta share hawayenta, aranta tana ayyana ko maqiyinta bazata so Allah ya jarrabeshi da qaddarar abokin zama me taurin zuciya irin Badaru ba.  Kansa kawai ya sani gashi da manmaqo da masifar rowa.



Tananan kwance har yamma,  xuwa lokacin ta ida jigata.  Sai dai in lokacin sallah yayi takan samu sauqi a dabi ance,  saboda tasa sallar aranta.  



Bayan idar da sallah ta jawo wayarta cikin qarfin hali da jan numfashi dakyar. Tana tunanin wanda xata kira,  shin mama xata kira ta fada bata da lfy,  ta daga mata hankali?  Ko yaya Faty data watsar da ita ta nuna batayinta xata kira? (duk kuwa da cewa Faty na kiranta a waya itace bata dauka saboda ta gaji da jin uxurin Faty akan rashin xuwanta gidanta, kawai ta dauki Faty a matsayin wacce bata santa a yanxu)  dole dai mama da Faty sune dolenta (ranar naka sai naka) 



Yaya Ahmad mijin Faty yayi saurin fado mata ta jawo wayarta tai masa pls call me,  kafin ta aje wayar ya kirata. 



Ta dauka "assalamu alaikum ya Ahmad " ya amsa sallamar "mimina kina lfy?  Ya naji muryarki haka? " ya fada agigice.  "bani da lfy ne shine nace dan Allah ko zaka taimakamun kaiwa Badaru magana ya kaini asibiti" ta fada a wahale.  "subhanallah sannu Mimi bari muga ya za ai?   Sannu autarmu" da haka ya kashe wayar.  



Ya tashi ya shiga bedroom gurin Faty dake zaune (yau aikin safe tayi shiyasa take gida a wannan lokacin) ya kalleta tare da cewa "fadima meyasa bakyajin maganata ne?  Inashan fada miki kece babba karkiyi abunda zai bata xumuncinku da Mimi,  na fada miki mama har fushi tayi dake akan rashin zuwa kiga halin da Mimi ke ciki,  amma duk kinqi ji ko?  To yanxu Mimi ta kirani bata da lfy kuma ga dukkan alamu tanajin jiki,  babban abun takaicin shine: mijinta yaqi kaita asibiti,  daya takaicin shine;  ko zancenki batai ba a wayar, wanda hakan ke nuna cewa ta watsar dake kamar yadda kikai mata" yana kaiwa nan a maganarsa yasa kai ya fita. 




Tunda ya furta Mimi babu lfy  kuma ta kirashi a waya,  Faty take a fingice. Ta tashi tabi bayan Ahmad da gudu ta fada jikinsa ta baya ta rumgumeshi tare da sakin kuka "yaya kace Mimi bata tambayeni ba?  Kace Mimi bata da lfy?  Yaya wlh tausayin Mimi da halin da xan ganta ciki ya hanani xuwa gurinta, bawai bijerewa umarninka dana mama ba. Yaya banason mijin Mimi tunda Mimi bata sonsa" ya dagota ya juyo da ita yana share mata hawaye,  yace "my luv, bata wannan hanyar xaki nuna tausayin Mimi ba,  neman kusanci da ita da maganta mata matsalarta da kwantar mata da hankali shine hanyar tausayinki da soyayyarki gareta" tace naji kuma xanyi yadda kace "  duk a rude take wannan magana. 



Ta shiga daki ta dakko mayafinta da key din mota ta fito,  ya kalleta ina zaki?  "Gidan Mimi " ta bashi amsa direct.  Yace a a bari insa ta turo no mijin nata infara yi masa magana tukun.  Tai rau -rau  tace 'yaya Mimi babu lfy kace in tsaya injira ayiwa wannan wawan waya?  Mimita cefa ba lfy?  Ka bari inje xanyi duk abunda ya dace" yace "to my luv sai kin dawo kibi komai a hankali karki abunda xaki xubar da mutuncinki a gurinsa,  kuma matarsa ce ya fimu iko akanta"  ta gyada kai tare da ficewa. 




Lokacin da ta isa gidan Mimi yamma tayi sosai,  domin har Badaru ya dawo. Ta dunga kwada sallama Mimi na parlo a kwance tana jinta tai mata shiru,  yayin da Badaru dake cikin bedroom yaji sallmar kuma yaji Mimi bata amsa ba ya fito.  Lokacin Faty ta gaji da jiran a amsa mata sallama har ta shigo parlon,  Mimi kuwa tanajin ta shigo ta juya baya tabar kallon qofa,  ta fuskanci kujerar parlon.  Badaru yana tsaye yana ganin ikon Allah,  shidai yasan Faty yar uwar Mimi ce,  kuma a dan iya xamansu da Mimi bai taba ganin tayiwa wani haka ba koda kuwa batasanshi ba,  balle Faty yar uwarta. 



Faty bata kula da wanxuwar Badaru ba dake kofar bedroom riqe da cotton (labule) ba, saboda gigitar halin ko in kula da Faty tai akanta. 



Jikinta a sanyaye tasa gwiwarta kan centre carpet din dake parlon ta marairaice tace "Mimi na tuba,  karkiyimun hukunci irin wannan,  bazan iya jure rashinki gareni ba. 




Mimi ba tare da ta juyo ba,  tace "ai tunda kika iya jure 2 month baki ganni ba kuma baki damuba hakan na nuna kin yanke alaqa tsakaninmu,  shiyasa nima na cireki a raina kuma ban nemi taimakonki ba.  Duk mutumin daka rayu tsahon wata biyu babushi wannan sheda ce dake nuna cewa ko babushi xaka iya rayuwa"



Faty ta fashe da kuka "MARYAM karki bari shedan yayi tasiri a xuciyarki,  kinfi kowa sanin cewa duk halin da kike bazan gujeki ba.  Kuma duk tsahon lokacinnan wlh dake nake kwana nake tsahi,  Mimi kinsan dalilin da yasa banxo gurinki ba,  sai dai kiqi gasgata dalilin nawa.  Mimi wallahil azim ko yayan dana haifa banai musu soyayyar da nake miki, saboda duk duniya bani da yar uwa uwa daya uba daya saike" 



Mimi taji wani irin mugun tausayin Faty ya kamata amma ta danne saboda tanason hora Faty akan karta qara yimata haka anan gaba tace "yaya Faty ki tashi kije gidanki,  nasan dake na naimi yaya Ahmad ban nemeki ba kuma da nasan ke zai turo da ban nemi ya taimakamun ba" duk tana wannan maganar ne a juye (ta bawa Faty baya). 



Parlon yayi tsit na tsawon 5 minutes.  Mimi da taji shirun yayi yawa ta juyo a zatonta Faty tayi fushi ta tafi.  Amma me?   Sai tayi arba da Faty tana tsugune tana hawaye. 



Ta qura fatyn ido itama tana hawayen,  ita kuwa Faty ganin yadda Mimi ta lalace ta kade yasa ta qara sautin kukanta cike da nadamar rashin xuwa taga lfyr mimin. 



Cikin kuma Faty tace "#FATIMARYAM# bazasu taba rabuwa ba,  bazasuyi fushi da junansu ba,  matsalar Faty ta Maryam ce,  matsalar maryam ta Faty ce. Mimi wannan shine alwashin mama akanmu,  karki karya alqawarinnan tun yanxu 😪" 




Mimi najin haka ta taho da rarrafe domin babu qarfin tashi,  taje ta rungume Faty.  Faty ma qanqame Mimi tayi kamar xata maidata ciki.



Suka dunga a jiyar xuciya xuciya a tare,  Faty ta dunga sharewa Mimi hawayenta sannan ta kwantar da Mimi a qirjinta kamar yarinya tana shafa kanta alamar lallashi. 



Badaru yana tsaye,  yana kallon dramar su,  kamar masu shirin film.  Aransa yace dama akwai irin wannan soyayyar yan uwantaka?  Lallai yarannan suna san junansu. 



Ya juya da nufin komawa daki,  motsinsa ya sanar dasu wanxuwarsa a gurin,  yayi saurin cewa da Faty "haj Faty barka da xuwa,  ina wuni? " dan haka kawai yaji ta masa kwarjini duk da cewa xai girmeta da kadan ko kuma suyi sa anni. 



Ta kalleshi cikin tsana, sannan ta kalli yar uwarta dake kwance kan cinyarta.  Yayi tas yayi qiba yayin da Mimi ta tsummace da qare kamar me jinyar shekaru da yawa. Ta amsa gaisuwarsa sannan ta dora da cewa " ranka ya dade ya akai akabar Mimi ciwo yaci qarfinta haka?  Ciwon Mimi fa ciwone me hadarin gaske kuma yana da alaqa da xuciya,  duk sanda ciwonta ya tashi inbai samu kulawar gaggawa ba hakan kan iya jawowa arasa rai.  Kuma babbar abunda ke motsa lalurar Mimi bacin rai"



Yayi wuqi wuqi, yana kame kame da bawa Faty haquri.  Tace to gobe da sassafe xanxo in kaita asibiti dan naga abun yayi worst,  xansa ayi mata booking tun yanxu. 



Cikin kunya yace "to Allah ya kaimu,  Allah ya bata lfy kuma za a kiyaye in shaa Allahu"



Ganin magariba ta kawo kai yasa Faty tai nufin tafiya,  ta karanci matsalar Mimi harda yunwa aciki. Sannan ko zafin wannan gidan ya isa ya tashi ciwon Mimi. 



Mimi kamar tabi Faty takeji,  kuma ganin yar uwarta da daidaitawarsu yasa tasamu rangwamen ciwon. Faty ta lallabata da cewa tayi haquri gobe da asuba xataxo kuma,  tayi wanka ta shirya kafin taxo din. 




Fitar Faty befi da minti 15 ba wani yaro ya shigo da leda yace gashi inji wata mata fara a mota tace abawa maryam.  Ta karba ta bude taga freshyoo me sanyi qarara guda uku. 



Atake ta bude ta shanye daya,  sanyin ya ratsata ta kuma bude wani tasha rabi sannan taji ta qoshi.  Tayi hamdala tare da cewa "Allah sarki dan uwa rabin jiki"



Da xumudi ta kwana, saboda tana murna gobe xata fita bayan wata biyu a kulle a gida. 



Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 2⃣3⃣


Dedicated to 

Maryam Baita


    Asubar fari Faty ta gama shirinta na tafiya, har breakfast ta hadawa Mimi. Taiwa Ahmad sallama ya kawo kudi ya bata da nufin taiwa Mimi amfani dasu a asibiti.



5:30 AM agidan Mimi tai mata,  ta samu Mimi tayi wanka amma tana zaune bakin gado bata shirya ba saboda jikin ya motsa mata.  Suka gaisa da Badaru ta shiga cikin daki.



Haka ta dunga bincika drawern Mimi da nufin dubo mata kayan da zata saka, domin duk kayan sun yamutse (anyi wanki babu guga). Gashi kayan sai qarnin sabulun wanki suke.  Dakyar ta samowa Mimi zani da dankwalin atamfar dutch wax (holland) da shirt (domin rigar atamfar tayi mata yawa saboda ramar da tayi) ta saka. Ta dakko humra ta zazzga ta murxa a jikinta (domin humrar kadai take dashi,  turarurrukanta tuni sun qare,  dan bata saka turare daya tafi gane ta hada kaloli da yawa.  Kuma da Badaru suka hadu suka qarar tunda shikam baya siyan turare ya saka  sai da yaga Mimi dashi ya tayata suka qarar anga banxa 🤣) ta dan gyara fuskarta, ta hade kitson kanta tasa ribbon. Ta yafa mayafi kumar suka fito. 


Suka tadda Badaru a parlour ya dakko 500 ya bawa Mimi tare da cewa "ga wannan ku riqe ko za'a buqaci wani abun" Faty tai saurin cewa "no bashshi babu abunda xai gagara da ixinin Allah" .



Bakwai a AKTH (Aminu kano teaching hospital) tai musu inda Faty ke aiki. koda likita yaxo ita ya fara gani saboda sanayya da kuma booking din da sukai.



Suka gaisa da Faty likitan mai barkwanci,  yana duban Mimi ya duba file dinta dake gabansa yace " fatima kina da wannan African queen din shine baki bani na aura ba? "  Faty tai murmushi tace "Dr babu rabone shiyasa baku taba haduwa ba, amma Mimi ai tana xuwa nan"



Ya duba record din ciwon Mimi,  yace "maryam meyasa kike sa damuwa a ranki?  Bakisan ciwonki bayason damuwa ba? ". Mimi dai shiru tai masa kanta na qasa.



Ya rubuta allura yace Faty taje ta karbo yanxu a pharmacy  ta kawo masa xai mata.  Allurar 9k ce saboda haka ya rubuta note,  dan acikin albashinsa xa a cire. Faty ta dunga yi masa godiyar karamcin da yayi mata,  yace bakomi ai zaman tare ne ya kawo.



Bayan fitarta, nasiha ya dunga yiwa Mimi cikin hikima. Duk cewa baisan matsalarta ba. Suna haka Faty ta dawo,  ya fasa allurar ya nemi jijiyar hannu yayi mata,  sannan ya buqaci ta zauna ta huta xuwa 10 minute saboda allurar nada qarfi.




Cikin qanqanin lokaci,  Mimi taji nauyin da qirjinta yayi ya sauka,  numfashinta ya koma fita normal.  Ta dago ta dubi likitan tace "nagode Allah ya biyaka da gidan aljannah naji dadi". Yayi murmushi yawwa maryam nagode da addu a Allah ya qara sauqi,  suka dauki takardar magunguna suka fita.



Suka tsaya cikin asibitin suka sai magunguna. Sannan Faty ta tsaya ATM ta ciri kudi suka tafi.  Ta miqawa Mimi travelling mug cike da tea murtuk dashi (hadin kauri inji Mal kabiru dadin kowa 😂) tace shanye.  Mimi ba musu ta shanye domin tana ganin shayin yawunta ya tsinke domin rabonta da shayi da madara tun madarar amarci. Bayan ta gama sha ta miqa mata food warmer cike da soyayyar doya da kwai da miyar qoda a gefe. Tace "kici ki qoshi dan ba gida xan 

kaiki ba". Taci doyar ta qoshi nak,  atake wata nutsuwa ta saukar mata.  Lallai ta yarda matsalarta harda yunwa a ciki. 



Direct zoo road ta tsaya inda Mimi keyin saloon,  ta ajeta tace a gyara gashinta a wanke mata qafa, sannan ta tafi tace xataje ta dawo.



Suka taya Mimi ta tsefe kan,  aka shamfe shi,  sannan aka dora da steaming. Akai mata gyaran fuska (cire gashin fuska)  ba abunda bai buqatar gyara,  nan da nan saiga Mimi tayi tar fuskar ta washe. 



Ana wanke mata qafa Faty ta dawo, ana gamawa ta biya kudin suka tafi. Direct shoprite suka nufa,  suka fara da gurin electronics Faty ta sayi reachargable fan (fankan da akewa chaji).  Sannan suka shiga gurin provision tace Mimi ta dau duk abunda take buqata,  dake Mimi tasan ko bata dauka ba Faty fada xatai mata shiyasa tadau duk abunda tasan tana da buqatarsu, kamarsu : mayan robobin madara da milo,  omo,  sugar, pads, toothpaste, cookies da sauran kayan amfanin gida. Faty ta qara mata da wasu kayan shayin irin na sachet da catoon din cake da caton din freshyo da su malt da exotic duk catons.  Ta kalli Faty cikin soyayyar yan uwantaka tace "ya Faty basu yawa ba kuwa?  Karba ki dorawa kanki wahala" ta kalleta tace "Mimi yanxu dan na miki abu ya xama wahala kenan? Yaushe muka fara haka dake? Ta dafa kafadarta tace,  Mimi ina qaunarki mu kadai mama ta haifa,  ina roqon Allah indai xai bani abunda bazan Mora miki ba kada ya bani shi ko menene" Mimi tai saurin fadawa jikin Faty suka qanqame juna. Kudi sosai ta biya na siyayyar da sukai,  sannan suka dau hanya. 



Lokacin da suka isa gidan Faty qarfe biyun rana, adaddafe tayi sallah sabida yunwa dake damunta.  Tana idar da sallah taje kan dining table,  ta cika plate da jellof din macaroni da hadin salad tayi tai qat ta dora da pepper soup.  Duk abunda take Faty na ankare da ita,  tabbas Badaru yana yiwa Mimi horon yunwa domin ada Mimi bata cikin jerin mata masu cin abinci, amma yanxu har mamakin cin da Mimi tayi take. 



Abincin yana fada mata ta nutse akan royal bed din Faty wanda yasha shinfidu tausasa na alfarma, sanyin AC na ratsata tayi bacci me dadin gaske.


Bata farka ba sai 5:16 pm tayi salati,  tare da miqa.  A gaggauce ta shiga bandaki ganin lokacin sallah ya qure.  Sai dai tana cire pant dinta da nufin yin wanka ta tarar period dinta yaxo,  duk kuwa da cewa lokacinta yayi har ya wuce batai ba.  Tai mamakin xuwan period din ba tare da ciwon mara ba,  ko hakan yana nasaba da allurar da akai mata oho? Ta dakko shaving cream (veet) ta shafa a jikinta ta qalqale gashin. Ta salla wankanta da mayukan wanka da subulai, ta dauki sabon pant a drawer ta manna pad ta saka.  Ta gyare jikinta da mayuka da perfumes masu sanyin qamshi, ta dauki doguwar rigar atamfa a kayan Faty ta saka.  Tai mata cif sakamakon ramar da tayi, ta danyi simple make up ta fito tas da ita. 



Ta iske Faty da Ahmad da yaran zaune a parlour suna kallon drama (madhubala) a mbcbollywood.  Tace "ya Faty har lokaci yaja haka baki tasheni ba? Tace "sry Mimi shigata biyu da nufin in tasheki saina tarar baccin ya muki dadi shiyasa na gyaleki.  Ta samu guri kusa da Faty ta zauna,  suka gaisa da Ahmad, ya jajanta mata jikin sannan ya zarce da yi mata nasiha.  Dan har ga Allah yanason Mimi ganinta yake kamar uwa daya uba daya suke, tunda shi bashi da yan uwa.  



Taje fridge ta dakko robar ice cream ta dawo ta xauna tanasha suna hira.  Ji take kamar karta tafi dan xaman yayi mata dadi.  Ahmad ya kalli Faty yace,  tashi ki kaita gida kada muyi rashin hankali.  Faty ta yunqura tare da miqawa Mimi wata leda tace kinga a siyayyar da mukai kin manta baki dauki masuka da turare ba shine na koma na siyo miki" Mimi ta leqa ledar taga muyakan da take amfani dasu ne cocoa butter (palmers)  Set dinsa har sabulunsa sai turaren da take amfani dashi da sure na feshi da sauran spray.  Ta dunga godia.



Sai da Ahmad ya bata 10k,  sannan ya jaddada mata duk sanda take buqatar taimako ta fada,  kada ta qara zama ciwo yaci jikinta haka.  Saida Ahmad ya temaka suka saka kayan a mota saboda kayan da yawa.  Har sun fara tafiya Faty ta tuna da fankar da tasa chaji,  ta dawo ta dauka. Suna tafiya suna hira cikin nishadi ta dauki jakar Mimi ta saka mata ledar magungunan da suka siya tare da kudi sannan ta qara da cewa gashinan ki kula,  ki rabu da namiji ki dainasa baqin cikinsa a ranki, lfy tafi komai kuma shi kansa inbaki da lfy bazai zauna dake ba,  so dat ki lallaba lfyarki.  



Suka tsaya yahuxa suya dake kabuga ta sai mata kaza da furar habib.  Kafin suje gida anyi sallar magruba saboda sun tarar da hold up.  



Suna gama shiga da kayan Faty ta juya gida.  Mimi da bata sallah xataiba da kimtsa kayan takai kowanne muhallin daya dace. Tana zaune tana lazimi aka kira sallar isha ta tashi tasa kayan bacci dan jikinta fes yake bata buqatar wanka.  Bata damu da dawowar Badaru ba domin ya kunna inji,  ta kunna fankarta wacce tai chaji full.  Iskar fankar na kada ta tana danna waya (chating)  a zuciyarta cewa take "Allah ya sakawa yaya Faty da alkhairi badan taimakonta ba da tuni ina zaune cikin zafi. 



Takwas nayi ta balli maganinta tasha dama tana timing. Ta janyo kazarta ta bude ta fara ci da bisimillah. Qarar injin da taji ya tabbatar mata da dawowar Badaru, ya shigo dakin yayi tozali da Mimi.  Idonsa fes akanta saboda hasken wutar lantarki,  tayi masa kyau ainun kamar sake masa ita akai. 



Yayi saurin qarasawa gabanta tare da cewa "maryam sauki ne ya samu haka da wuri? Sannu" ta danyi murmushi tare da gaisheshi.  Ya amsa idonsa na kan ledar gabanta wanda qamshin kazar ya cika dakin,  yace " harda hidima haka? " ta amsa da cewa "eh yaya Faty ce tasaimun da wannan fankar (ta nuna masa fankar) yace " to madallah haj Faty kenan bataso kudi su zauna lfy" (kuji banxa🤣)



Ba kunya ya tayata suka cinye kazar sukasha furar,  lamarin da yayiwa Mimi dadi.  Domin yaune rana ta farko da suka taba cin abinci kwano daya da Badaru. 



Yana ta kallon Mimi wai ta burgeshi qarshe,  ya kalli qafarta yar dundubus da ita har tafi jikinta haske yatsunta kansu abun kallone be taba lura Mimi takai haka ba sai yau (dama ya xa ai kasani?  Wahalar gidanka tasa tayi kaushi) ya ruqo hannunta yana murxawa cikin shauqi "maryam tashi muyi shirin kwanciya" ya fada yana mai qura mata ido.  Azuciyarta tai masa dariyar mugunta,  saboda tasan bata da tsarki. 



Ba musu ta miqe taje tai brush,  shima ganin tayi yaje yayi amma ba batun wanka duk kuwa da tsamin ranar da yake.  Ta feshe jikinta da turare ta kwanta hankalita kwance yau ba kawo farmaki 😜. 



Tayi mamaki kwarai da taji ya kashe inji,  ya shigo dakin yana me cewa tunda ga fanka ai sai man injin ya huta. Yana hawa gadon ya kamata ya rungume yana shafar gashin kanta yana cewa "maryam kinada shiga rai,  komai naki me kyau ne" tadan motsa bakinta cikin sigar murmushi har dimple dinta ya lotsa.  Lamarin da Badaru yaji ba abunda yake muradi illah ya hada bakinsa da nata.  Amma yasan bazata yadda ba shiyasa beyi yunqurun hakan ba,  domin yau hakanan yaji bayason batawa maryam rai. 



Ganin abun nasa yana nisa yasa tace masa bata da tsarki,  atake ya saki wani mugun tsaki tare da tureta daga Jikinsa,  ya koma gefe ya kwanta.  Dama hakan take jira dan haka ta gyara kwanciyarta ta maida fankar dai dai saitinta tai adduar kwanciya bacci.




Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 2⃣4⃣


Dedicated to 

Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Tasamu canjin rayuwa saboda taimakon Faty,  ta rabu da matsalar zafi saboda fankar da Faty ta sai mata. Koda babu wuta takan bada fankar da 50 naira akai mata wani company dake bayan gidanta kadan mai gadin gurin ya karbi hamsin din yasamata caji,  saboda company ne basa rabo da wuta.  



Sai dai da yake rayuwa indai kai imani baka rasa jarrabawar ubangiji,  sai wata sabuwar matsalar da bullo mata.  Matsalar kuwa itace;  kawo abokai da Badaru ya tsiriyi cikin gidan saboda yaga cimar gidansa ta canja (ansamu mai dadi).



Ba kawo abokan nasa ne problem dinba ko kuma abunda zasuci,  cin mutunci da toxarcin da Badaru keyi mata agaban abokan nasa shine babbar matsalar. 



Sau tari zai cika gidan da abokansa duk kuwa da qanqantar gidan,  wanda hakan ke hanata sakewa sai dai ta takure kanta adaki.  In fita parlour ta kamata ko duba girki sai dai ta saka hijabi, har mamakin inda ilimin addininsa yake take domin babu addini sam acikin abunda yake, kodan ya takura mata yake hakan?  Sannan bayan tayi hidima dasu da jikinta da aljihunta (domin babu ko sisinsa aciki) sai kuma ya dunga zaburarta yana daka mata tsawa agabansu,  a qoqarinsa na nunawa abokansa cewa ita din bata isa komai ba. 



Yauma hakace ta kasance,  domin tare suka shigo da wani abokinsa sani around 5;30 pm.  Suka taddata zaune parlour ta tasa fanka agaba tana shan iska,  a xuciyarta bata gajiya da yiwa wacce ta sai mata fankar adduar alkhairi (ya Faty) 



Tai saurin miqewa ta shige daki da nufin suturta jikinta,  domin shimice kawai a jikin nata.  "kinaji ana sallama dan rainin hankali baxaki amsaba" cewar Badaru.  Sani abokinsa yayi saurin tareshi da cewa "bakaga hijabi zata dakko ba,  laifinane dana shigo kai tsaye ban tunanin halin da xan taddata ba" ta fito sanye da jihab me hannu tana cewa "sannunku da xuwa" ta gaishe da Sani, sannan ta nufi kitchen ta qara sanwar abinci dan ganin baqo,  ta debo musu ruwa da kwalin exotic ta dora akan tray ta glass cups ta kawo ta koma daki ta zauna. 



Tananan zaune tana yan danne dannen waya taji xuwan wasu abokan nasa har su 3 domin taji ya ambaci sunayensu.  A xuciyarta tace yau kuma anan xa ai mana zaman majalisar kenan. 



Ta tashi domin ta duba abincin data dora,  ta gaishesu ta wuce kitchen.  Ta gama komai ta maida miyar kan gas domin ta qara dumamata ta jiyo Badaru na kwala mata kira,  ta fito parlour ta dan durqusa gefensa "gani" ya dubeta yana wani daga hanci yace " ke wace irin mahaukaciyar mace ce mara tsari?  Bakiga nayi baqi bane?  Ko sai nace ki qaro wasu kofunan da lemon? Banason dabbanci."  Ba tare da tace komai ba ta miqe taje ta kawo  wani kwalin lemon da kofuna ta ajiye,  tana shirin juyawa yace " abincin ma sai nace ki kawo ko?  To karki kawo" tai saurin xuba abincin a warmers har tana qonewa saboda kar wani cin mutuncin ya biyo baya.  Domin tana jiwo shewar abokan nasa,  suna yaba masa yadda yake tafi da ita.  Har wani a cikinsu wanda bazata iya gane kowaye ba yana cewa "da kyau mutumina haka akeson mutum ya xama jan wuya a gidansa"




Ta hada musu komai na abincin a gabansu, sai da ta tabbatar ta hada komai sannan ta nufi daki.  Badaru yayi saurin katseta da cewa "waye bawan gidanku anan dazai zuba musu? " ta duqa a takure take saboda kallon da wasu acikinsu suke mata,  xata fara xubawa Sani yayi saurin katseta da cewa "a a jeki maryam mungode  kowa zai xuba nasa" dan ya lura a kunyace takeyin komai. 



Badaru yace "a a ta xubawa kowa umarnina ne,  ni naga damar haka.  Tana gama xubawa ta miqe ta shige daki.  Sani ya dubeshi ransa adan bace " ka daina haka Badaru,  wannan yarinyar kyautace Allah ya baka ka riqeta da amana ku zauna lfy.  Yawanci yaran yanxu basu cika bin miji haka ba,  bare ita da take da xurfin ilimi" Badaru ya daga murya,  domin yanaso Mimi ta jiyo abunda zaice "yo ni ina ruwana da ilimin mutum,  ko parpesa ce ita bai dameni ba domin miji ta rasa na taimaka mata na aureta,  inba dan nidinba da tuni tanacan a jabe gidan ubanta"  





Yayi sa a kuwa domin duk maganar da suke akan kunnen mimin sukayi saboda tana da ji sosai,  kuma dakin bashi da xurfi. Hawaye ya wanke mata fuska,  lallai yau wulaqancin na Badaru yafi na koyaushe.  Muryar daya daga cikinsu ta katse mata tunani inda yake cewa "au wai kana nufin tana da ilimi? " Badaru ya bashi amsa da cewa "degree      ne da ita akan fannin sharia" wanda yayi tambayar yace "Tab ai wlh gwanda daka riqe mata wuta daka sake mata rainaka zatayi musamman intasan tafika ilimi mata yan boko mugayen yan rainin wayo ne.  Kai kuma sani da kake wani xance ai mata xuma ne da wuta ake cinsu" Sani ya balla masa harara yace "inkasan ba shawarar arziqi zaka bayar ba ka daina xuga xugagge yana ciwa yar mutane mutunci"




Badaru yayi saurin tareshi cikin hargowa "kaga sani ya isa,  ni ba wani wanda yake zugani haka nayi niyyar tafi da gidana kuma haka nakeyi.  Intaga xata iya xama dani a haka ta zauna, in kuma bazata iya ba sai in mata saki daya taje gidan nasu ta dandana xama taji.  Ai tasan rufa mata asiri nayi,  kaf gidansu ita kadaice budurwar data rage. Sannan tace xata kawomun wani fi ili?  Bokon banxa bokon wofi  meyasa bokon nata be bata mijin aure ba.  Wlh ko shugabar qasa ce ita dole ta bini yadda nakeso intaqi ga hanya nan.  Nasan kina jina MARYAM in bazaki iyaba kixo ki tafi gidan ubanki."



Duk yanda taso danne xuciyarta abun ya gagara kuka take wurjanjan,  batasan yadda akaiba sai ganinta tayi a parlourn adai dai lokacin da yake cewa "ai kinsan yadda kika sha wuya kika zaunu kafin Allah ya kawo miki ni na aureki,  ki qoqari ki kashe auran kina budurwa ma kin rasa miji bare kina BAZAWARA."





Sai a lokacin ya ankara da wanxuwarta a parlourn,  ya kalli idonta da fuskarta gabansa yayi mugun faduwa  domin bai taba ganinta cikin wannan yanayin ba duk abunda yake mata.  




Sani yayi saurin shan gabanta ganin ta nufi qofar fita, a qoqarinsa na dai daitawa,  yace MARYAM Dan Allah dan darajar iyayenki kiyi haquri kar fita.  Ta tsaya cak! Badaru dake gefe ya saukewa boyayyar ajiyar xuciya ganin ta tsaya. 




Sani yace Badaru,  beye lefin yarinyar nan?  Saboda ni kayi haka? Daga gaya maka gaskiya xaka ci mata mutunci haka?  Lefin me tayi maka? 



Mimi ta matso kusa dashi ta kalleshi, yai saurin yin qasa da kansa.  Tace  cikin nutsuwa da qarfin zuciya " kayi haquri qaddarace ta hadamu, amma karka manta kai ka ganni kace kanaso ba talla aka kawo maka niba.  Kuma tabbas miji na rasa shiyasa na aureka,  inba dan haka ba ai babu wacce xataso xama da  namiji irinka.  Kuma da Allah ya hanani miji daga baya ai yabani kai?   To haka nake sakaran duk renda Allah ya sa ka rabu da ni Allah xai bani wani mijin.  Gari da yawa ai maye bayacin kansa Badaru. In shaa Allahu yadda Allah ya doramun jarrabawar xama da kai xai bani ikon cin jarrabawar, wlh nima ba Jin dadin xama dakai nake ba.  Allah ya na madakata yana jiranmu kuma zai mana sharia"




Simi simi daya bayan daya abokan nasa suka fice,  kodan kada aure ya mutu ace ta sillarsu ne.  Ya rage sai Sani kawai,  ya kalleshi yace "yanxu wannan abun da kayi me gari ya waya?  Burgewa kayi? Ka tauna asirin gidanka a idon duniya.   Allah ne kadai yasan inda wannan zancen zai tsaya,  kuma tunda da wata niyya kake kawo abokai gida daga yau babu abokin da xai kuma xuwa gidanka.  Ya juya ga Mimi yace MARYAM kiyi haquri,  anbata miki Allah ya baki haquri ya huci xuciyarki." ya juya ya fita. 





Tunda ta shiga daki bata qara fitowa ba sai da akai kiran magriba ta fito alwala,  ta taddashi zaune a yayi tagumi.  Daganan bata qara fitowa ba har wajen 9:03 taji ya tada inji tayi shirin kwanciya ko wanka bataiba bare cin abinci dan ranta har yanxu a bace yake.  



Tanajin lokacin da yaxo ya kwanta kusa da ita,  tai saurin rintse ido.  Dan jitayi wata irin tsanarsa ta taso mata.  Bata tabbatar da Badaru bashi da kunya ba sai da taji hannunsa a jikinta  yana lalubarta.  A tunaninta yau zai haqura tunda sunyi sabani,  amma ina mayen ya kasa haquri duk kuwa da ya gwada yin haqurin ya kasa.  Tai masa banza taqi bashi fuska,  take banxa ne sai ya fara qoqarin gwada mata qarfi zai shigeta,  a salonsa na kwanciyar awakai.  Ta qanqame jikinta ta hanashi yin hakan,  dole qanwar naqi yayi amfani da lallashi ta hanyar cewa "maryam dan daure ki barni nayi,  na kasa bacci kinsan na riga na saba" sama sama ya samu nutsuwa ba kamar yadda ya saba ba. 





Ya koma gefe ya kwanta yana tunanin da maryam din ta tafi dazu da ya zaiyi?  Dole ya sake taku,  kodan lalurarsa ya xama dole ya zauna da maryam dan bayajin xai iya haqura da buqatarsa koda ta kwana daya ne.  Dan yana sahun mabuqata ga kuma qarin magunguna da yake sha,  bayan haka kuma bai gama more kudinsa ajikin maryam dinba.  




Duk da bata taba turje masa a gurin kwanciya ba sai yau,  amma yana mamakin duk sanda ya batawa maryam rai to ranar baya samun yadda yakeso ajikinta.  Duk da kuwa ba hanashi takeyi ba,  amma duk qoqarinsa baya gamsuwa.  A fili yace dole in gyara lamura na da maryam kodan shimfidata. 



Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 2⃣5⃣


Dedicated to 

Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)




Su 3 ne kawai zaune a majalisar,  Badaru,  Mekudi sai wani abokinsu da suke kira KB.  Hira suke yayin da KB ke daga gefensu kadan yana karatun news paper.  Badaru ya kalli Mekudi yace "ya babu lbr ne?  Na jika kwana biyu shiru? " Mekudi yayi wani shu'umin murmushi sannan yace "yo ni ana raba ni da lbr ne? Kamar ka shiga xuciyata ansamo wani be zafi,  amma fa a tube yake ita zaka matsa ka cusawa kafin ka shiga,  sauran bayani kuma xaka bani lbr da kanka.  Ya fada yana daga gira" 



Badaru ya washe baki tare da cewa "Allah mutumina 😄? Yana ina?  Bani " mekudi yadan muskuta tare da cewa " sai dai fa yana da illah,  yakan bata mahaifa ko hana haihuwa gaba daya,  saboda haka ka kula,  amma dadi kam xakaji dadi kamar ka mutu 😜"  Badaru ya miqa masa hannu suka tafa yace " yo ni ina ruwana,  ai dama bandamu in haihu da ita ba,  amfanin ta kashe qishirwata da ita".



KB da tunda suka fara maganar hankalinsa na kansu ya magantu "Badaru me kake shirin aikatawa?  Sirin shimfidarku kake budewa anan? Har kake shirin batawa yarinya mahaifa? to wlh karka soma.  Kai kuma mekudi kaji tsoron Allah ka tuna kana da yaya mata in akaiwa yarka haka xakaji dadi? "  sukai tsit suka sunkuyar da kai,  saboda suna respecting KB dan ya girme musu. 



Suna idar da sallar magriba Mekudi ya tashi tafiya Badaru ya miqe shima tare da cewa " Bari in koma gida nasan tana zaune a duhu ba wuta." 




Yayi saurin tadda mekudi a motar sa yana shirin tashin motar ya bude ya shiga,  ya miqa masa hannu "Bani maganin" mekudi ya sheqe da dariya yace "shege baka haqura ba" shima yayi dariyar tare da cewa "aimu bama wasa da kayan aiki". Ya miqa masa maganin a kwalinsa tare da cewa "ka kula". Badaru ya fito ya shiga tasa motar,  yayi gida yau ko gurin Nafee baya son xuwa tunda ya samu......... 




Mimi tayi mamakin barin jikin da Badaru keyi a kanta yau,  duk da ba sabon abu bane a gurinta sambatunsa a shimfidarsu.  Tana jin lokacin da ya cusa mata wani abu a gabanta.  Tai saurin yunqurawa xata tashi,  yasa hannu ya danneta.  Tace "meka sakamun a jikina?"  cikin rashin nuna kulawa ya bata amsa "xan cuceki ne? To vaseline na saka saboda kin matse da yawa na kasa shigarki" daren ranar ta gurxu a hannun Badaru,  ga wani irin ihu da sambatu da yake tana tsammanin maqota na kusa zasu iya jiyoshi. 




A dan wannan tsakanin Badaru ya xama wani irin qasurgumin jarababbe,  kullum cikin yin abu daya yake.  Ba dare ba rana,  domin da ranar Allah xai baro kasuwa yazo gida ya shafe awanni yana dirxarta.  Kuma in dare yayi ma babu hutu,  sai yayi aqallah sau 3. Ita har mamaki take sam baya gajiya,  zata iya cewa tunda aka kawota gidan Badaru yau kimanin wata hudu kenan (4 month)  bai taba fashin kwanciya da ita ba,  sai dai in period take. 



Lokaci guda ta qare ta lalace,  a xuciyarta take cewa ashe da ba wahala nakesha ba,  yanxu ne nake ainihin wahala.  Gashi dai bata nemi komai ta rasa ba (Faty ta tsaya mata)  amma jarabar Badaru tasa ta xama kamar tsumma.  A gefe guda kuma ga rashin mutuncinsa domin babu abunda ya fasa,  sai ma qaruwa da yayi.  



Sau tari takanyi tunanin matan da suke cewa aure da dadi,  sai ta rasa ta inda sukejin dadin auran, ta xaman takewar gida kota kwamciyar aure?  Domin ita dai tunda suke da Badaru ko na second daya bata tabajin dadin kwanciya ba,  hasali ma axaba takeci ba kadan ba.  Da farkon aurenta tana danganta hakan da rashin sabo,   amma yanxu data dan kwan biyu sai take ganin halittar tace haka.  Ita dai tasan in azabar da takeji ce jin dadin aure sai take ganin ba macen da xatace aure da dadi. 




A lokacin sai takejin babu abunda ta tsana a duk duniya irin sex life (kwanciyar aure).  Duk da gori da qalubale data fuskanta a rayuwarta ta yan matanci sai ta kwammace gara rayuwarta ta gida da wannan rayuwar da take yanxu. 




***    ***       ***     ***



Yau babban baqo garesu,  Badamasi qanin Badaru wanda tunda akai auren bai taba xuwa gidan ba.  Yauma yaxo ne bisa takurawar ummansu. 




Tunda yaxo Mimi keta hidima dashi dakko wannan,  kawo wannan.  Duk da batasan da xuwansa ba, tai masa tarba ta musamman da girkin alfarma.  Tana ta xarya tsakanin parlour da kitchen,  cikin tsawa da umarnin Badaru,  wanda duk fitowar da tayi sai ya nemi wani abun da zaice batai dai dai ba. 



Yanxu ma tafito ne dauke da qaramin tray wanda ta doro cups da lemon happy hour na kwali ta taho,  ya daka mata tsawa da cewa "wai ke komai sai anyi jiranki ne?  Kinsa wani hijabi na munafurci,  wazai kalleki anan?  Ni da babu abunda bansani ba a jikin ki, ko Badamasi dake dan uwana uwa daya uba daya? "   Badamasi ya runtse ido cikin takaicin abunda Badaru yakewa yarinya,  tana qoqarin kare masa mutunci ta hanyar suturta kanta yana kwaye mata baya.  A dan xaman da yayi yanxu ya fuskanci inda aurensu yasa gaba. Shiyasa yaga maryam din duk ta canja,  mace qayatacciya kyakykyawar gaske me fasali amma cikin lokaci kadan ji inda Badaru ya kwararrabata.  Ya gyara xaman wayarsa dake kan hannun kujera, wacce yake recording din duk abunda ke faruwa tun daxu,  da nufin in yakoma gida ya sakawa iyayensu suji yadda Badaru kewa yar mutane. 



Tunaninsa ya katse lokacin da yaji Mimi na ajiye lemon da ta kawo a kusa dashi.  Badaru ya tsai da ita, tare da daka mata wata muguwar tsawa "ke dauke Badamasi bayashan irin wannan lemon na kanti, sai zobo kije ki kawo masa zobo" (kunji fa kamar ya siya ya ajiye)  ta dauki tray din lemon tare da cewa "to bara na dafa zobon sai dai babu qanqara...... " maganar ta dauke lokacin da taga Badaru ya daga hannu da nufin kai mata mari.  Tai saurin saka tray din hannunta ta kare fuskarta,  hakan yasa dukan ya sauka kan farantin kayan ciki suka watse.  Badamasi yayi saurin miqewa tsaye cikin razana 😳. Badaru ya dora da cewa "Dan ubanki harni xan saki aiki kice babu qanqara?  Meyasa baki siya kin ajiye ba?"  idon Mimi qurrr akansa tana kallonsa cikin mamaki Dan yaune karon farko da yakai hannu jikinta da sunan duka,  kuma yaune karon farko da ya xagi ubanta dake qarqashin qasa. 




Cinkin dinbin mamaki da razana Badamasi yace "Badaru 😳dukan mace?  Kamar jahili,  metai maka?  Dama abunda nakiji na cewa kana tara abokai kaci mata mutunci gaskiya ne? Me tayi maka? " Badaru ya tare Badamasin cinkin hargowa kamar xai dakeshi,  "baka ga abunda tai ba?  Yar iska mara mutunci,  duk abunda xata xubarmun da mutunci ta iya, banxa jaka" 




Idanunta jajur suna digar hawaye take kallon Badaru ba komai yayi mata ciwo ba irin zagin ubanta.  Cikin qarfin zuciya tace" karka kuma zagarmun uba,  domin yana kabari akwance".  Yayi saurin cewa "an zageshi uban ubanki ma yaci ubansa,  kiyi abunda xakiyi"  ta mayar masa da martanin cewa "babu abinda xanyi domin xagi xagawa yake, kuma duk abunda kakemun Allah ya na jinka, yana ganinka kuma zaimun sakayya." 




Ya watsa mata wani kallo sannan ya funciko hannunta ya hankadata bakin qofa tare da cewa "fita ki tafi gidan ubanki shegiya mara tarbiyya gayyar tsiya." Badamasi ya daka tsalle tare da dakawa Badaru tsawa kamar shine gaba da Badarun yace "wlh Badaru ka kiyaye ni, na rantse da Allah xaka tarkowa kanka bala'i,  domin yanxu xanje na fada Abba abunda gidanka yake ciki"  yana kaiwa nan ya figi muqullin motar Badaru dake kan kujerar parlourn (domin shi baixo da mota ba) ya fita. Mimi ma tasa kai ta fita yayi saurin cewa " ban baki izinin fita ba" ko takansa bata biba tai waje ya bita da gudu ya jawo ta ya dawo da ita tare da furta "maryam akanki ake shirin hadani da iyayena,  kowa nawa sai ya rabu dani a kanki. Abokaina, yan uwana, yanxu kuma iyayena?  Meyasa haka?"



Acikin motar Badaru kuwa Badamasi ne a kifa kansa a sitiyari yana jin quna a ransa, wlh da yasan yacce xai tarar da Mimi kenan da bai zoba.  Bazai juri ganin Mimi cikin wannan halin ba,  yanxu meye abunyi?  Yayi dan gajeran tunani,  baxai fadawa iyayensu abunda gidan Badaru ke ciki ba yanxu.  Domin inyayi silar mutuwar auren Mimi sannan daga baya yazo yace yana sonta cewa xa ai ya kashe mata aure dan ya aureta.  Ya dakko wayarsa yayi saving recording din da yayi saboda wata rana. 




Hannunsa yakai kan aljihun motar ya jawoshi,  saiga kwalayen magani guda 4 duk iri daya (maganin da mekudi ya bawa Badaru,  yake ajiyarsa amota saboda kar Mimi ta gani) ya dakko ya duba kwalin hotunane ajiki na mace da namiji tsirara suna xxx kala kala hutunan abun ba kyan gani.  Ya duba rubutun jikin maganin,  yaga illar da yake,   a qa'idar maganin ma matan banxa masu blue films akewa amfani dashi dan su fita hayyacinsu, kuma suma din sai anyi aggrement.  Amma dan zalunci da son zuciya Badaru yakewa yar mutane amfani dashi, kuma bama kwali daya ba,  alamu sun nuna ya dade yana mata amfani dashi tunda ga kwalaye nan har guda 4. 



Ya share hawayensa ya dauke ragowar maganin a fili yace "MARYAM Allah ya saka miki,  Allah ya miki canjin alkhairi domin Badaru ba miji bane. 




Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 2⃣6⃣


Dedicated to 

Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)




Cikin kwanakin da suka biyo baya tai wata irin ramewa kamar me ciwon SIDA (AIDS). Ta fita hayyacinta kwarai,  ga wani irin mugun qaiqaiyi dake addabarta a qasanta,  ga dukkan alamu ciwon sanyi infection yayi mata mugun kamu. Domin har gari gari take gani a gabanta a memakon danshi da akasan ya mace dashi, ga wani irin wari danma bata ramo da inserting almuski. 



Badaru tsakaninta dashi dangantaka tayi tsami kwarai da gaske,  domin sai suyi 3 dayz koma fiye da hakan bai mata magana ba, kuma inma tayi masa baya amsawa. Walau kuwa koda gaisuwa ce,  sai dai tagaji da tsuguno ta tashi.  Wanda hakan shiyasa kawo mugun koma baya a lfyarta,  sau da yawa sai dai ta ganta a kwance kamar gawa batasan abunda ya faru ba tunda babu kowa a kusa balle ya karanta ta mata abunda ya faru kafin ta tsinci kanta a hakan. 




Babban abun takaicin shine : duk wannan takun saqa da suke da shi,  hakan baya hana in dare yayi yazo ya mutsutstsuketa da sunan yazo neman haqqinsa na aure.  Sakamakon ciwon sanyi da yayi mata illah yasa ko yazo baya samun komai (babbar illar ciwon sanyi kenan,  wato qafar da ni'imar mace) wanda hakan ke jawowa ya fusata yayi ta xaginta da aibatata. 




Data kula sosai sai ta gano cewa ba ita kadai ciwon ke damu ba,  saboda Badaru ma Kullum cikin sosa al aurarsa yake,  alamu shima ciwon na addabarsa. 



Dan lfyar kanta da kuma maganin wulaqancin da Badaru kemata a shimfida (domin tana kyauta zaton rashin samun biyan buqatarsa na daga abunda ya sa wulaqancinsa ya kuma ta azzara) yasa ta tunkareshi da sunan ya barta taje asibiti domin ciwon sanyi ke damunta.  Da farko be kulata da maganar ba,  sai daga baya ya jiyo qanshin gaskiya a maganarta.  Domin ciwon da tai masa bayani yayi kama da wanda masu magani ke bayani a kasuwa.  Hakan yasa ya sameta har daki yace "kawai kinje kin kwaso ciwon sanyi kinxo kin gogamun,  wlh in hakan yayi sanadiyar raguwar qarfin mazantakata bazan yafe miki ba"(🤣🤣🤣).



Ta dago arazane jin abunda yace,  cikin sanyin murya tace "ni kuma Badaru?  Ni ina fita ne?  Canake tunda nazo gidannan fitata daya?  A ina xan kwaso ciwon?  Nafi zaton kaine ka dakko mana a kasuwa" yasan tana da gaskiya shiyasa bece komai ba ya kada kai yayi gaba. 



Da yamma kuwa sai gashi da ledar magani,  ya siyo a irin gurin masu saida maganin hausar nan na kasuwa.  Wadanda ke yawo da mota suna tallah a speaker.  Ya miqo mata wani qaramin qulli "wannan gashi ki juyeshi a madara yanxu ki shanye,  ya miqo dayan wannan kuma ki dunga turare dashi kina tsugunawa akai" (kunji fa!  Mtsew komai aka hada da jaki sai yaci kara) tace  "to" ta karba,  azuciyarta take tunanin shidai asibiti ne bayaso arayuwarsa.  Ta qudure bazatai amfani da wandannan magungunan da batasan ingancinsu ba haka kawai ita ba qoshin lfy suje su illatata.




Tofa! Abu fa ya kacame, komai ya xama chocolate 😂. Iskancin Badaru da wulaqancinsa kanta ya kazanta,  ko alabari bata taba jin inda ake cin mutuncin matar sunnah yadda Badaru kecin mutuncinta ba.  "Banxa jaka,  na tsaneki" sune kalaman da Badaru ke fada mata adun sanda suka hada shimfida dashi saboda baya samun biyan buqata Sam.  Gashi ita a kanta tanajin yadda tai wata irin budewa tai sako sako,  kamar matar data haihu bata gyara kanta ba. 



Bama sai sun hada shimfida ba,  a rana daya yakan ce mata "na tsaneki" yafi sau cikin carbi. Sunanta kuwa a gurinsa ya koma "jaka" dan sau tari zai sata aiki sai yace "ke jaka yimun abu kaza" yayin da agefe guda kuma ya dage da aikin ginin da yake,  domin ya auro Nafee wacce yanxu Kullum a gurinta yake kai 11 dare. 




Mimi,  yar kwalisa yanxu ta xama wata muguwar siriri mara fasali,  tayi fari fau kamar me amfani da mayunkan kwaile fata (bleaching) yar kewayayyar fuskarta ta koma tsuru sai manyan idanuwa 👁👁 da hancinta 👃🏾 wanda rama tasa yayi bodardar.  A taqaice dai ta xama mummunar qarfi da yaji. 




Babbar matsalar dake addabarta itace rashin ganin al adarta (period) rabonta dayi tun tana wata biyu a gidan, wato lokacin da taje asibiti ta biya gidan Faty.  Tayi tayi Badaru ya barta taje taga likita ko wata matsalar ce yaqi.  Data dameshi da xancen saboda ciwon marar dake addabarta  sai yace karta dameshi,  saboda ba akanta aka soma CIKI ba.   Tunda daganan itama bata qara xancen ba,  saboda itama data duba cikinta sai taga tafi kama da masu qaramin ciki. 




Kuma wani ikon Allah sai ta tsinci kanta cikin farinciki da cikin,  saboda kasancewarta meson yara tunda basu taso sunga kowa a dakin mama ba sai su biyu.  A fili tace " Baby ki rasa lokacin da xakixo sai lokacin da ake sa toka sa katsi?  Allah ka rabamu lfy,  Allah ya miki albarka yata😊" ta fada hannunta na dafe akan cikin. 




Badaru dake gefe yana sauraranta yayi saurin matsowa kusa da ita yace "au mace kikeso ki haifa?  To ai se ki roqi Allah kada ya baki me irin BAQIN JININKI,  domin in ta rasa miji wlh sadakarta xan bayar"  ta dago ta kalleshi tayi murmushi 😊 tace " Badaru in tayoka ai bazatai baqin jini ba, tunda ka ganni ka taimaka ka aureni itama sai Allah ya dubi kyakykyawan aikin da kayi a kaina ya kawo me auranta 😊"




Yasan magana ta fada masa dan haka yayi tsit. 


*******       ********    ******


Tun jiya cikin dare take murqususun ciwon mara,  har xuwa yanxu 9:43 na safe.  Tun tana iya yunquri har qarfinta ya qare ta kasa.  Badaru tun shekaran jiya yayi tafiya Lagos akan harkar kasuwancinsa, kuma gashi bata da lambarshi kamar yadda bashi da tata.



Badamasi da yau ya shigo kano yazo daga inda yake aiki (Dutse) tunkan ya qarasa gida hankalinsa yake akan maryam.  Tun rabuwar da sukai da Badaru akan ciwa maryam mutunci hankalinsa ya kasa kwanciya,  dan haka direct ya wuce unguwar su Badaru. 



Tun daga soro yake kwada sallama amma ba amsa,  ta bangaren Mimi ta dakko waya da nufin kiran Faty ta fada mata halin datake ciki sallamar ta rusketa.  Kuma tana amsawa amma dake muryar a shaqe take saboda wuyar ciwo shiyasa bayaji. Ya sako kai parlour tai miqe daga kwanciyar cikin qarfin hali tana haki tace "inata amsawa bakaji" ya dubeta a razane yace "maryam badai ba lfy ba? Ina mai gidan ya fita ya barki cikin wannan halin?" 



Tai murmushi tace "yayi tafiya tun Lagos,  bayan tafiyar ne ciwon ya riskeni shi......" bai qarasa jinta ba ya dakko waya a aljihu.  Sai ji tayi yana xancen rashin lfyrta kuma ga dukkan alamu da Badaru yake.  Can yaji yana cewa "babu batun ragonta,  dan mace na da ciki bazatai ciwo ba sai ace tacika ragonta?  Nidai yanxu xan kaita asibiti ya kashe wayar"




"Tashi ki shirya muje asibiti, " ya bawa maryam umarni.  Sannan ya zarce da mitar cewa kasan lalurar ciki ne?  Inda kai Allah ya dorawa wayasan kwakwazon da zakai?  Kaiwa yar mutane ciki ka tafi kabarta da wahala.   Itadai ta yunqura dakyar ta miqe tayi hanyar toilet tana godewa Allah da ya kawo me temakonta. 




Cikin qarfin xuciya tai brush da wanka suka tafi.  Ganin yadau hanyar yan kaba yasa tace "Aminu kano nake ganin likita ai" ya waiwayo ya dubeta yace " rana tayi shiyasa xan kaiki asibitin wani abokina da mukai karatu tare,  amma shi likitan mata ne"  tace ai a Aminu kano akwai yayata dake aiki acan,  inka kaini ko likitan yamma ne sai nagani" 




Yana kallon titi yace "sry bari na kaiki private din xaki fi samun kulawa inyaso har awo da haihuwa sai kije can. Yasan aikinsa sosai" ta sunkuyar da kai cikin kunya jin yayi maganar cikin jikinta.  Ya qura mata ido cikin burgewa dan yanason mace me kunya. Aransa yana aiyana rashin imanin Badaru dan kowa yaga maryam yasan ba a dadi take ba kuma ga ciki na wahalar da ita. 



Sun tadda layi kasancewar safiya ce. Badamasi yayi masa waya da kansa ya fito ya shiga dasu bayan ya nemi alfarmar na kan layi. 




Yana dubata suna dan taba hirar yaushe gamo da Badamasi,  ya kalleta yace maryam alamu sun nuna kina da qarancin jini a jikin ki,  shiyasa kika dashe kikai haske.  Badamasi yace " ba ciki bane ya kawo hasken?"  Dr yace "bazan iya cewa da ciki ba ko babu,  amma dai bari nayiwa sister sarah magana ta tafi da ita can nursing station tayi mata checking sosai akan hakan" 



Ya kirata a waya nan da nan sai gata yace "kuje da wannan yayi mata bayani" Mimi ta bita yayin da Badamasi ya koma reception dan bawa ragowar marasa lfyar damar ganin likita. 




Acan gurin nursing din sun dubata sosai taji wacce ta dubata na fadawa dayar cewa,  tana buqatar aimata wankin ciki. Lamarin da yasa Mimi tsorata, domin tasha ji ana fadar wahalar wankin ciki. Dan haka ko takan mayafinta da jakar bata biba ta ranta ana kare 🏃🏽‍♀.



Badamasi na zaune yaga fitowarta daga dakin a harkitse,  tana tafiya tana waiwayen bayanta taga ko nurse din ta biyo ta.  Ya taho gurinta da sauri cikin rashin sani suka gabxa karo. Tai qasa xata fadi yayi saurin tarota jikinsa,  jinta jikin mutum yasa ta qanqameshi tana cewa "Badaru kaji wai wankin ciki zasuyimun,  kuma da xafi sannan xasu wankemun Baby dan Allah karka bari suyimun." shidai Badamasi tunda yaji maryam ajikinsa ya tafi wata duniyar,  ya xaci irin mafarkan da yasa ba yine akanta dan haka ya rungumeta jikinsa tsam yana sauke ajiyar xuciya. Akayi sa a itama ta xaci mijintane ta kwanta lub.



Nurse din data biyo Mimi da jakarta da mayafi ce ta dawo dasu hayyacinsu.  "oga gashi ta gudo dakaji ance xa ai mata wankin ciki"  yai saurin rabata da jikinsa daya farga ba mafarki yake ba,  a xuciyarsa ya dunga cewa astagfirullah Badaru kai ka jawomun da ka kula da matarka da ban kawota asibiti ba balle harna rumgumeta.   Itama Mimi sai yanxu ta dawo hayyacinta,  ta dunga jero neman gafarar Allah.  




Suka koma office din Dr,  nurse din tayi masa bayanin matsalar Mimi da kuma qin yadda ai mata wankin cikin.  Ala dole ya rubuta mata maganin ciwon mara dana qarin jini. Badamasi ya tambayeshi akan cikin.  Yace "yanxu kam bazan iya cewa da ciki ba ko babu tunda akwai lalura da yawa a tare da ita, sai dai ko in kun kuma dawowa ayi scanning.  Ga maganin ta dage da cin abinci da shansu kuma basu da qarfi koda da cikin baxasu illatashi ba" sukai sallama suka tafi. 




A hanya suna tafiya tace masa "dan Allah karka maidani gidannan na kwana ni kadai jiya nasha wahala,  bansan abunda hali xaiyi ba yau." ya dubeta yace "to Maryam ai bani da ikon kaiki wani gurin bada ixinin mijinki ba,  amma bari in masa magana saboda akwai hatsari abari ki kwana ke kadai" ya dakko waya ya kirashi tanaji yana masa bayani,  can ya miqo mata wayar yana cewa gata.  Tai sallama be amsa ba bare ya saurari gaisuwar da take masa ya hau masifa " kince bazaki kwana gidanki ba ko?   Uwar langwai to kitafi duk inda xaki tunda kinsa anmun titsiye inna dawo kya dawo." yana kaiwa nan ya kashe wayar, itama ta kashe ta miqa masa tare da cewa kaini yahya gusau gidan yaya Faty.  




Koda suka isa gidan sun samu ya Ahmad na nan,  dan haka koda yaya Faty ta fito domin temakamata su shiga ciki yaga bata lokaci ne dan haka ya dauketa cak yakaita har cikin parlourn.  Badamasi ya dunga kallonsu cikin birgewa,  domin sai ka xata Ahmad ne dan uwan Mimi ba Faty ba. 



Badamasi ya dade a gidan suna hira, saboda family din sun burgeshi.  Faty ta dunga jerawa Mimi sannu ta duba magungunan da aka bata.  Tare sukayi dinner sannan tasha maganin kana Badamasi ya tafi. 



Yau dadi takeji xata kwana gidan yaya Faty,  har dare sunata hirarsu cikin nishadi sannan suka nemi makwanci,  yaya Faty ta dunga mitar ramar da Mimi tayi amma koda mimin ta fada mata ciki ke wahalar da ita sai mitar ta koma murna.  Suka raba dare suna hirarsu sannan sukai bacci. 




Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 2⃣7⃣


Dedicated to 

Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)




Kwanaki uku da tayi gidan Faty yazo mata da wani irin canji,  har mamakin nishadin da take ciki takeyi. Sai take ganin rayuwarsu kamar lokacin da suke gida kafin suyi aure.  Suci abinci tare,  bacci tare,  sannan gashi ya Ahmad duk sanda xai shigo saiya shigo mata da abun kwadayi,  yakance me ciki ba a rabata da kwadayi, sai kace shi xa a haifawa dan.  Amma aduk sanda ta tuna xata koma gidan Badaru sai jikinta yayi mugun sanyi sannan gabanta yayi ta faduwa. 



Rana ta biyar a gidan Faty wanda ya kama da satin Badaru daya a Lagos,  da yammaci suna zaune ana hirar da aka saba anata dariya.  Mimi zaune a gefen Faty akan kujera 3 sitter tanacin guava,  yayin da ya Ahmad ke gefensu akan kujera 1 sitter yana basu lbr sai dariya suke. 




Badamasi yayi sallama ya shigo,  Mimi na ganinsa gabanta ya yanke ya fadi.  Nan take nishadin da take ya qare kuma duk wanda ke parlourn ya lura da wannan canjin na Mimi.  Ko Badamasi bai fada ba tasan Badaru ya dawo kuma xuwa yayi ya maida ita kamar yadda ya alqawaranta. 



Suna gama gaisawa ya fada musu labarin dawowar Badaru tun safe,  kuma yace yaxone ya maidata gidan.  Ya Ahmad ya katseshi da cewa "shi maiyasa bazaizo ya dauki matarsa ba?  Sati daya baka gari?  Inka dawo ai iyalinka ya dace ka nema kaji lfyarsu,  ko akuya ka bari da ciki sati daya inka dawo ai ka binciki lfyarta.  Wannan abunda yakeyi sam babu tsari a cikinsa,  na kuma gaji dab nake da indau mataki akai " ya qare maganar cikin bacin rai 😔. Badamasi ya bude baki da nufin kareshi ya Ahmad ya tsai dashi "karkace komai,  nasan halinsa kuma shirun da akai masa baya yana nufin Mimi bata da gata bane, kawai muna kau da kaine saboda iyayenmu" Faty na gefe na share hawaye .




Sha tara ta arxiqi suka hada mata,  kamar wacce xatai tafiyar shekara.  Har Badamasi ya dunga jinjina soyayyarsu ga Mimi. Faty bata fito rako Mimi ba saboda kuka da take bataso tasa mimin kuka itama,  sai ya Ahmad ne ya tsaya aka loda kayan a bayan motar sannan ya kawo kudi ya bawa Mimi,  har anrufe motar ta fito da gundu ta fada jikin ya Ahmad tasa kuka ya kamo fuskarta ya share mata hawaye yace "maryam kici gaba da haquri Allah ya na tare dake,  baxaki taba tabewa ba a rayuwarki" ya bude motar ya sakata suka tafi. 





*****       *****        ******


Bata canja xani ba rayuwar da suke a baya itace dai,  gashinan abun babu tsari kamar a jahiliyya period.  




Kimanin kwana 11 da dawowarsa daga Lagos kenan daren ranar suna kwance,  ya hauro kanta yasa qarfi ya danneta.  Kimanin sau uku kenan yana  yin hakan,  inya gama buqatarsa yaji bai gamsuba yayita zaginta yana ci mata mutunci. 




Yanxun ma hakace ta kasance,  ya shigeta da dukkan qarfin da Allah ya bashi.  Taji xafi kwarai harta kwallah qara,  yaja dogon tsaki yace "qarar me kikemun?  Wai nufinki xafi kikaji?  Abunda duk kin bude kin tale,  innaxo shigarki kawai ji nake na rufta babu wata madatsa 😳🙈 shine har xakice kinji xafi?" 



Tai qasa da murya"wlh Badaru tun lokacin da ciwon sanyin nan ya samemu inkanayi ji nake kamar kana xubamun yaji daurewa kawai nakeyi,  da kabari naje asibiti da tuni mun warke."  cikin hargowa da daga murya yace "ya sameki dai, dan ni tuni na warke,  ai nakawo miki magani kikaqi amfani dashi ke lallai sai na asibiti ko Baturiyya? To wlh baki isa ba dan mugunta kin hanani inji dadi dake?  Wlh wlh whl yau ko xanyi sau dari sai naji dadi xan kyakeki ya rage naki"




Yana kaiwa nan ya farmata kota ina juyata yake yayi,  tun tana jin xafi harta denaji.  Numfashinta ya fara gazawa. Batasan iya lokacin da ya shafe yana durxarta ba,  ita dai tasan yayi mugun dadewa yana abu daya.  Sannan ya sauka ya koma gefe ga dukkan alamu gajiya yayi bawai biyan buqatar ya samu ba. 




Kukansa ya dawo da ita hayyacinta,  inda cikin kukan takaici yake cewa "maryam kin cuceni, kin xalunceni,  ni zakiyiwa haka ko?  Ni zaki hana jin dadi dake ko?  Kimanin wata daya kenan Kullum cikin buqata nake kin kasa biyamun ita.  Kije Allah ya isa ban yafe miki ba,  in Allah ya yadda bazaki gama da duniya lfy ba. KE MARYAM ALLAH YA TSINE MIKI." 😳😳😳😳




Jin furucin Badaru na qarshe yasa tai xunbur ta miqe,  tare da cewa "Badaru me yayi zafi haka??? 😳" ya bata amsa da cewa "ubanki ne yayi zafi" yana fadar haka ya fita daga bedroom din. 




Wani irin yanayi ta shiga ita ba matacciya ba ita ba rayayya ba.  Kukan ma ta kasa,  tsinuwa daga mijin aurenta?  Akan abunda bata da iko akai? Tab akwai matsala.  Saboda da gajiyar dirxar da Badaru yayi mata batasan sanda bacci ya kwasheta ba.  Sai ana kiran sallatu ta farka,  qasanta wani irin xugi yake mata kamar ansa reza an ketata taje tai wanka tai sallah ta roqi Allah sauki da gaggawa kan halin da take ciki. 



Sukuku ta yini saboda tsinuwar da Badaru yayi mata ta taba xuciyarta sosai, ta qudure a ranta inya kunna inji da dare ta samu chajin waya xataiwa ya Faty maganar infection din ta kawo mata Magani, domin wulaqancin ya isheta haka gara ta naimi magani ya dunga samun biyan buqata axauna lfy domin ita batasan tashin hankali (Allah sarki rayuwar ya mace,  Kullum cikin sadaukarwa namiji take.) babu abunda ta iyaci ranar illa ruwan lipton da lemon tsami. 




Ta idar da sallar laasar,  tadan kwanta kan sallayar tana azkar,  ta qudure aranta yau laraba intasamu dan aike xata bashi kudi yayi mata sadaka domin yau yini tayi gabanta na faduwa. Bazai wuce hudu da rabi ba 4:30 lokacin da taji dawowar Badaru, tayi mamaki kwarai dan bai cika dawowa haka ba sai inda muhimmin abu da xaiyi. 




Ya wuce daki fuu sai gashi da tulin kayansa masu dauda. Ya fita tsakar gida,  sai gashi ya dawo ya danqi gashin kanta ya fita da ita,  ya nuna mata tulin kayan wankinsa yace "ga wanki nan kiyimun,  tunda baki iya biyamun buqata ba kimun wanki,  dan baxan dunga baki abinci a banxa ba" tai tsam sannan tace "to kayi haquri kaga nawa ma bayi nake amma in ya Faty ta aiko karbar nawa wankin in shaa Allah xan hada maka da naka." 




Ya danqi wuyanta ya hadata da bango, sannan cikin huci da tsabar tsanar yace "ke kin isa insaki aiki kice baki ba? Wlh baki isa ba,  na tsaneki wlh da inka kashe rai babu wani hukunci a kanka da kece mutum ta farko da xan fara kashewa,  maryam ban taba tsanar wata halitta a duniya kamar ki ba.  Saboda haka dole kimun wanki dan ubanki"  ta fusge wuyanta tayi gefe ganin yana shirin kaita lahira, tana maida numfashi tace "wanki bazanyi ba kisa kuma bisimillah ka kasheni." cikin bacin rai take furta wadannan maganganun domin ranta yakai matuqar baci da xagin da Badaru kewa ubanta.  




Kafin ta ankara ya tsinka mata mari ji kike kau! 😳 tayi baya cikin azama ya dora da cewa "lallai wuyanki ya isa yanka? Yauni kike maidawa magana?  To dan ubanki...... "ta tari numfashinsa kafin ya qarasa. "karka kuma xagin ubana domin nasan darajarsa,  kuma da yana raye wlh bazan auri wanda besan darajar iyaye kamar ka ba,  maraicine ya jawomun"



Ya kuma dauketa da wani gigitaccen mari,  "na xagi uban naki bayan xagima na dakeki dan haka kije ki haqoshi daga kabari yazo ya rama miki."  ta dago idonta jajur " ka mareni?  Wlh komai daren dadewa saina rama,  wannan alqawarine na yiwa kaina." 




Ya ja hannunta qiiiiii ya bude gidan ya turata waje ta fadi dabas.  Sannan yace "ai basai andade ba kije yanxu ki tasoshi daga kabari kuxo ke dashi ku hadu ku dakeni,  kije na sakeki kuma Allah ya isa tsakanina dake in shaa Allahu bazaki gama da duniya lfy ba." 




Ya maida gidansa ya rufe,  yabarta zaune babu takalmi babu mayafi. Kuma dai dai lokacin hankalin mutane ya fara dawowa kanta, aka zagayeta ana kallonta tai qasa da kanta taji duk ta muxanta. Ya qara bude gidan ya wullo mata hijabi da wayarta,  jehowar da yayi tasa wayar taci screen. Ta miqe tasa hijabin qafarta babu takalmi gashi bai bari ta dakko kudi ba dan shiga Mota. 





Har ta fara tafiya wata maqociyarta yar dattijuwa wacce yayanta ke shiga gidan Mimi ta biyota a baya ta tsai da ita,  tace "maryam yanxu akaje aka sanar dani abunda ke faruwa, kiyi haquri indai baki cuceshi ba Allah saiya saka miki AURAN BAYA SADAKIN NA GABA." ta cire takalmin qafarta ta bawa Mimi tace saka ki tafi Allah ya hada fuskokinmu da alkhairi,  ta juya ta tafi tana kuka dan tana qaunar Mimi.




Cikin wani irin yanayi take tafiya,  tafi kama da mahaukaciya sabon kamu sam ba kuka take ba, idonta da xuciyarta sun bushe qaraf.  Jinta take ita ba matacciya ba ita ba rayayya ba,  abun kamar almara aurenta ya mutu cikin wata biyar da kwana shida kacal da yin auren.  Batasan mutuwar aure sam koda akan maqiyinta bare a gida irin nasu wanda bata taba ganin ko yaji anyi a gidanba.  Ita kuma haka QADDARARTA take,  andade ba ai aure ba,  anyi ba a dade ba ya mutu.  Tasan qalubalene a rayuwarta qatoto,  wlh duk ixayar da take ciki gara ta haqura ta xauna da Badaru da ace aurenta ya mutu. Koda kuwa takata zai dungayi yana wucewa. Kuma da tasan zai dauki matakin saki akanta wlh da gara tayi masa wankin. 




Saboda tashin hankalin da take ciki yasa bataga nisan tafiyar gidan Badaru xuwa titi ba, kawai ta tsinci kanta a bakin titi.  Ta tare dan sahu tace kaini yahya gusau (gidan ya Faty) dan koda wasa tasan bazata iya tunkarar gidan Baffa ba (gidansu) 




Har bakin gate din gidan ya kaita kasancewar gidan a bakin titi yake.  Ta sauka tace bari in kawo maka kudin. 




Faty na zaune a parlour tanashan golden morn taga fadowar Mimi parlour kamar an jehota,  ta miqe a razane tace "lfy Mimi,  jikin naki ne ya tashi?" nabar dan sahu a waje ban bashi kudin ba" itace amsar da Mimi ta bawa Faty,  tana fadar haka ta shige bedroom din ya Faty. 




Bayan Faty ta sallami dan sahun,  ta riski Mimi a bedroom dinta kwance kan gadonta tace "Mimi ki fadamun abunda ke faruwa na ganki a hargitse haka" dakyar ta daga ido saboda tsabar ciwon da kanta ke mata,  a taqaice tace da Faty "ya sake ni" ko kalma daya bata qara akan haka ba ta koma ta kwanta kan Royal bed din Faty.  Sama sama ta dunga jiyo salati da sallallamin fatyn.  




Har akai sallar magriba ana gab dayin ta isha suna zaune a gurin da sukai sallah jugum jugum.  Suna idda sallar isha Mimi ta kuma hayewa gado ta qudundune mugun sanyi takeji saboda zazzbin da ya rufar mata. 




Duk yadda Faty tayi da Mimi taci abinci taqi ci,  domin batajin ko maqogaronta abinci zai wuce,  saboda wani irin malolo takeji a maqogaron shi beyi gaba ba shi beyi baya ba.  Kuma itama Faty da take maganar itama bataci abincinba. Ta hado tea ta miqawa Mimi tace "karbi kisha kodan abunda ke cikin ki" ba musu ta karba tasha. 




A haka Ahmad ya riskesu,  dawowarsa kenan.  Ya shiga har bedroom din yace "lfy Faty?  Mimi jikin ne ya kuma tashi?" duk sukai masa shiru, Mimi tacigaba da shan tea din ya kalli Mimi " Mimina lfy?  Ko muje asibiti?" nan ma shiru ya kuma kallon Faty yace " Faty na kiyi magana mana lfy?" a hankali Faty ta furta "sakinta Badaru yayi".




Ga mamakinsu sai sukaji Ahmad yace "ALHAMDULILLAH " nan take fuskarta ta nuna tsantsar farin ciki,  dukkansu suka saki baki suna kallonsa. 




Ya ajiye jakarsa ta office akan side bed, sannan ya haura kan gadon ya kwantar da kan Mimi a kafadarsa yace "maryam ki godewa Allah da ya rabaki da Badaru,  domin bai dace da samun salihar mace irinki ba,  MARYAM keep praying in shaa Allah sai kinsamu mijin da baki taba mafarkin samu ba haqurinki bazai tashi a baxan ba" 





Ita dai bin kowa take da ido ga alama ta samu kurumta ta wucin gadi.  Haka suka kwana gado daya da Faty,  inta fara bacci sai ta farka a furgice sai dai Faty ta tofa mata addua ta maida ita ta kwantar.  Ya Ahmad kuma kwana yayi yana nafila yana roqawa Mimi waraka gurin ubangiji,  in yai sallama ya shiga dakin da suke kwance,  yaga halin da suke ciki,  a duk sanda ya shiga Mimi kanyi xunbur ta miqe zaune alamun a firgice take sai dai ya maida ita ya kwantar ya tofa mata addua.  Da haka har suka wayi gari. 





HAPPY EIDIL FITR,  TAQABBALALLAHU MINNA WA MINKUM.  


Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 2⃣8⃣


Dedicated to 

Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



A bangaren Badaru kuwa,  sai bayan ya saki maryam sannan fargabar abunda zai biyo ta bangaren Abbansa ya shige shi. Amma daya tuna yanda ya tsani maryam da yacce ya suqe da xama da ita sai yaga ai yanci bana rago bane.  gara kawai da ya saketa komai xai faru ma ya faru. 



Ana iddar da sallar isha, ya hada tea murtuk ya soya kwai 5, kamar shi ya siya.  Ya dake cikinsa sannan ya sheqa wanka ya xaba shadda,  ya samu turaren Mimi ya feshe jikinsa da shi.  Ko lura da cewa turaren mata ne bayi ba. Yaywa gidan su Nafee tsinke. 



Tare suka fito da dan aiken da yaje kiranta kamar jira take,  ko gaisawa bata bari sunyi ba ta fara qorafi "Badaru anya kuwa kana sona?  Anya kuwa xaka aure ni?  Nifa na fara yadda da maganar mutane da suke cewa yaudara kake"



Ya danyi dariya 😄 yace "Nafee ko gaisuwa babu za a fara da qorafi" tace da maganar na yini tana damuna.



Yace to "ki fara shirin bikin ki nan da wata biyu masu xuwa" ta waro ido tace "bayan sallah fa kenan" yace kwarai kuwa tace "wace sallah?  Yace wacce sallah ke gabanmu yanxu? "  tace in nayi lissafi dai dai qaramar sallah kake nufi domin yau kwana 8 ko 7 ya rage a fara axumi"



Yace yawwa yar gari,  kin gane kenan.  Ta daka tsalle tace "da gaske?" yace "wlh da gaske nake"  ya qara murmusawa yace "kuma daya albishir din da xan miki shine : ke kadai ce dani yanxu" tai far 🙄 tace "kamar yaya?" yace "mun rabu da maryam daxu" 




Wannan karon tanayin tsallen ta fada jikinsa (kuji rashin kamun kai) ta qanqameshi duk kuwa da cewa basu taba hakan ba.  Yayi saurin cireta a jikinsa jin yana shirin loosing control.  Wannan dare haka suka sha hirar soyayya cikin nishadi saboda matsalarsu ta tafi (maryam) tare da hirar yadda aurensu xai kasance. 


*****   ******    ******    *****



Karfe taran safe 9:00 am a gidan kakanninsu tayi musu bisa shawarar Ahmad da kuma rakiyarsa,  domin ita kanta bai yadda da nutsuwar Faty ba a lokacin shi yasa ya hanata driving.  Yasan tunkarar Baffa da lamarin mutuwar auren Mimi ba karamin balli zai tayar ba,  shiyasa yace abi abun takan surukan Baffa ko zai zo da sauki. 




Babba gidane me cike da kango a da,  amma yanxu da yayansa suka xama wasu sun bigeshi sun maidashi na tsamani da tsari.  A katafaren parlourn gidan sukai masauki hajja na kan kujera, yayinda mal manu kekan well chair ( saboda girma baya iya tafiya)




Tiryan tiryan Faty tai musu bayanin lamarin tun rashin lfyar maryam da kuma halin data tsinceta a gidan Badaru  har xuwa jiya da auren ya qare.  



Hajja tunda aka fara take share kwallah,  mal manu kuwa baice komai ba sai wayarsa daya dakko ya kirawo mama yace ta sameshi gida yanxu,  sannan ya kira Baffa ma ya fada masa. 




Tana gurin aiki kiran ya risketa,  dan haka ta kasa nutsuwa. Tasan ba qaramin abu bane zaisa Baba kiranta a wannan lokacin,  sai ta barwa kanta kawai Hajja ce ba lfy. Taje office din Principal din ta naimi excuse ganin bata taba hakan ba kuma da alama a rude take yasa ya barta. 




Kusan tare suka iso da Baffa,  domin shigarsa kenan taxo.  Ganin motarsa a kofar gida yasa ta qara rudewa.  Tana saka kai parlourn gabanta ya yanke ya fadi,  dan ganin Mimi ta tsummace rabonta da ita tun randa aka kaita gidan miji (halayyar uwa ta gari bata xuwa gidan yayanta sai da babban dalili) ta samu gefen centre carpet ta xauna. 



Faty ta kuma yi musu bitar abunda ya faru tas (dan ma Mimi bata fada musu waye haqiqanin Badaru ba da irin azabar da yayi mata). Baffa ya miqe ya watsawa Mimi kallon kinwa kanki,  dagani akwai magana a bakinsa kuma bai yarda da abunda Faty ta fada ba,  amma ganin idon surukansa yasa bece komai ba.  Yace "ni natafi kasuwa dan nakusa makara"




Mama ta kasa dauriya da abunda ya samu Mimi tasa kuka,  hajja da tun dazu take kukan itama ta qara volume  Faty itama tasaka nata kukan.  Mimi ganin mama da Faty na kuka (mutanen data fiso fiye da komai) itama ta saka nata kukan (tunda abun ya faru sai yanxu tayi kuka.



Kamar jiran nata kukan suke, kowa yayi shiru da nasa kukan parlourn yayi tsit  sai sautin kukanta.  Faty ta yunqura xata tashi taje gurinta mal manu yayi mata alama ta zauna.  Sai da tayi 43 minutes tana kuka baji ba gani,  sannan tayi shiru dan kanta.  



Mal manu ya garo kujerarsa yaxo kusa da ita ya dafa kanta "MARYAMU kiyi haquri kinji, wata rana sai lbr,  haqiqa mijinki ya cutar dake,  amma kiyi haquri wlh duk wanda ya toxarta aure saiya wulaqanta, sakayyar aure a duniya Allah ya ke yinta. Allah ya baki wanda ya fishi,  in shaa Allah wannan hawayen da kika xubar a dalilin baqin cikin aure sai Allah ya sa kin xubar da hawayen farin ciki fiye da wannan, Allah ya albarkaci rayuwarki" duk suka amsa da Aminnnnnnnn




Faty ta miqe xata tafi gurin aiki,  mama ma ta miqe.  Mimi tai saurin tashi tabi bayan mama. Hajja tace "maryam da kunyi xamanki anan kin dan murmure bakyaje wannan gidan naku  haka ba suyi ta kasaki a fefe ana tallanki.  



Mama tace "Hajja barni intafi da ita,  hankalina sai yafi kwanciya" Mal manu yana jinsu yayi musu shiru domin daga uwar (mama) har yar (Mimi) tausayi suke bashi. Sai yake ganin rayuwar Mimi kamar ta mama acan lokacin da ya wuce,  tabbas tarihi yana shirin maimaita kansa akan Mimi.  Yana fata itama nata qarshen labarin yayi kyau (Mimi) kamar inda na fadimarsa yayi kyau. Yanason yarinya fiye da duk jikokin da yake dasu, yana ganin wasu halayyar MARYAM (matarsa Hajja) a tare da Mimi kamar haquri da sanyin hali,  biyayya da kuma ibada. Kai hatta tafiya Mimi irin ta hajja take yi,  afuskane kawai basa kama (tafi kama da mahaifinta AL AMIN,  kamar photocopy dinsa ce) yana wannan tunanin har suka fita tsakar gida.  Ya kwalawa mama kira "Fadimatu" ta amsa "naam Baba"




Ta sameshi yace "duk sanda kikaga tana kuka karki hanata, kibarta tayi ya isheta,  baqin cikin zai ragu. Rashin kuka alokacin da abun kuka ya sameka kan illata lfyar kwakwalwa,  shiyasa daxu na barta tayi kukanta,  tashi kije Allah ya yi muku albarka ke da zuri ar ki" tace amin Baba Allah ya saka da khairan.



Umma kawai suka samu a tsakar gida tana yanka salak,  ta tashi ta bisu har daki tana cewa "maryam meya sameki haka duk kika tsummace?  Jiya nake cewa baffanku ya kamata aje a ganoki, tunda aka kaiki babu wanda yaje (kuji qarya)"  sukai mata shiru har ta gama surutunta.  Daga dakinsu gurin Anty ta nufa ta kai mata kanun labarai,  tun kafin a gama fada mata ta nufi dakin mama. 



Tana xuwa tace "maryam!😳 yanxu cikin ne yasa kika tarkato kika taho gida? Yara qannan bayanki suna gidan miji a zaune inma cikin ne sai dai mugansu dashi ya girma? Koda yake da alama cikin na wahalar dake duba da yadda duk kika qare,  yo uwarki ce har yanxu bata daina abun mutanen da ba,  wai ita kunya bata xuwa gidanku mu ba haka muke xarya gidan namu yayan ba" itama har ta gama haukanta basu tanka musu ba.  Mama ta tashi tana tunanin hali irin na matan gidan wai ai wata biyar ba a ga mutum ba, amma in anganshi ko irin nuna murna nan ta yaushe gamo. 




Mama ta dumamawa Mimi tuwon shinkafa miyar kuka tasa yajin daddawa ta isketa har bedroom kwance a saman gado ta kai mata "mimina tashi kici" ta girgixa kai alamar bataci mama ta hayo gadon ta dagata ta zaunar da ita tace "nasan mutuwar aure Mimi, nasan ciwon sakin aure.  Musamman saki irin naki na wulaqanci amma babu yadda zaki da hukuncin Allah,  barin kanki da yunwa bashine solution ba." ta karbi tuwon ta faraci,  mama ta qura mata ido tana kallonta,  tana son gano cikin da akace Mimi tana dashi.  Ita sam abun bai mata dadi ba,  dan dai babu yacce xatai da hukuncin Allah ne. 




Acan kasuwa kuwa Baffa yini yayi yana xirga xirgar neman Badaru, tun yana xuwa da kansa har ya gaji ya dunga aika yaransa.  Sai dai amsar dayace baixo kasuwa ba yau,  kuma abun kamar hadin baki shima abban Badaru yau be zoba. Kuma Badaru yaqi xuwa kasuwar ne saboda yasan sai Baffa ya nemeshi. 




Koda ya koma gida bai nemi mama ba duk kuwa da cewa ita keda girki,  ta karbi girki da yamma.  Wanda hakan ke nuna laifin Mimi ya shafeta,  itama ta fison haka.  Tasa yarta da jikanta (Dady dan Faty wanda ke xama a hannun Maman) agaba sukai kwanciyarsu. 



Sai dai yadda Mimi ta kwana jiya, haka ta kwana yau.  Ta dunga farkawa a firgice, kuma duk farkawar da tayi xataga mama xaune tana kalkonta. Farkawa ta qarshe da tayi tasamu mama tana sallah. Ita sai yanxu ta tuna in masifa ta sameka kana addua.  Dan haka ta miqe taje tayo alwala ta fara sallah kamar motsatstsiya,  duk sujjadar da tayi takance "ALLAH HUKUNCINKA NE WANNAN BANYI FUSHI BA,  ALLAH KA QARAMUN JURIYA"




Da sassafe Baffa ya yiwa gidan alh inuwa tsinke,  yana bacci xuwan kiran Baffa ya iskeshi. Sama sama suka gaisa Baffa ya karanta masa abunda Badaru yayiwa Mimi.  (saboda da abun ya tayar masa da hankali, abunka da wanda ba a taba sakarwa ya ba). Wata irin kunya kunya ta rufe alh inuwa,  ya tashi ya shiga gida yace da Baffa yana xuwa. 



Yasamu Umma a kitchen ya labarta mata abunda Badaru yayi,  gabanta ya yanke ya fadi ta xauna dabas a qasa tana sallallami tace "alh meye abunyi yanxu?  Har Badaru yayi saki ba tare da saninmu ba. Maxa kirawoshi yazo ya maida ita tunkan abu yayi nisa" ba musu ya dakko waya,  dan shima abunda yake shirin yi kenan.  



Dajin kiran ABBA da sigar da yayi masa magana, yasan lbrin sakin ya ruskesu.  Saboda haka ko wanka beyi ba ya tashi ya nufi gidansu yana qudurce cewa sai dai ayi duk wacce xa ai amma wlh ya gama xama da maryam. 




Dake Bahaushe yace baya bata da kadan,  be dade da fita ba mumy (Adda halima) yayar mama da Faty suka yiwa gidan tsinke.  Sukai sa a yabar muqullin a gurin wani me shagon kofar gidan,  suka shiga suka kwashe duk wata kayan sakawa na Mimi (suturu)  mumy taiwa wani me furniture waya yaxo ya kwashe kayan dakin ya siya kuma ya siya da daraja tunda sababbi ne kuma sun samu kulawar Mimi.  Kayan Badaru dake drawer mumy tasa Faty ta dau akwatin Mimi daya ta loda masa kayansa a ciki.  Kayan da tayi amfani da su kuwa kamarsu tukwane,  tea flask da food waemers, jugs cups plates duk tasa aka dunga rabawa maqota. Kayan abinci kuwa dana tea da lemuka duk tace a bar masa duk da kuwa Faty ta fada mata bashi ya siya ba, shinkafa kawai yake siya a gidan,  mumy tace duk hada ki bar masa Faty shine matsiyaci,  mukam ai bamu gaji tsiya ba. Ai mun auna arziqi tunda ya sakar mana yar. Dan ni dama gaba daya Badaru be mun ba a mijin Mimi.  



Maqota da aka basu kaya suka dunga shigowa godia,  suna yaba hallayar kirki irinta Mimi da alhinin rabuwa da ita,  wasu harda kuka sunai mata fatan alkhairi.  Wanda ya sayi Kayan yana gama fita dasu suma suka fito hannun Faty dauke da system (laptop) din Mimi da fos dinta suka qulla gidan suka bawa mai shagon muqullin,  drivern mumy ya loda kayan a mota dake seinna ce tas ta dauke suka shiga suka tafi. 




Badaru kuwa yana xuwa bai shiga gidansu ba,  saboda kar Umma ta takura masa ya mayar da maryam,  direct sitroom ya nufa gurin abbansa da Baffa ya gaishesu cikin daure fuska dan karsuce lallai ya maida Mimi.  Abbansa cikin fada ya fara yi masa jawabin abunda Baffa yazo dashi,  bayan ya gama ya bashi umarni da ya maida Mimi dakinta.  Badaru ya motsa ya qara daure fuska yace "gaskiya abba kayi haquri nagaji da xama da ita,  yarinyar Sam bata ganin girmana duk tsawon wannan lokacin haquri nake da ita" Baffa da yazo da nufin ciwa Badaru mutunci akan sakin Mimi yayi saurin sakkowa jin Badaru yace bazai maida Mimi ba. Cikin sanyin murya yace "haquri xakai Badaru duk matan haka suke duk wanda ka ganshi da matarsa sun dade haquri yake da ita" ya fada cikin qanqan dakai.



Badaru ya qarayin fuskar shanu yayi burus da lallashin da Baffa ke masa yace "Baffa tunda na auri maryam ban isa insata abu tayi ba,  Kullum cikin yimun gorin ilimi take wai ta fini ilimi.  Yanxu kuma akan bautar qasa ta tada balli wai sun kusa tafiya,  nace ta bari lokacin yayi inga yacce za ai sai kawai tahau xagina wai bansan darajar ilimi ba.  Dan haka ni na haqura da ita taje can ta auri wanda yasan darajar ilimi" hmmmmm (ni kuwa nace kuji qarya)  ya ciro takadda daga aljihunsa ya miqawa Baffa ga takaddarta nan,  dan Allah suyi gaggawar xuwa su kwashe kaya saboda xan saki gidan in karbe ragowar kudina. 





Baffa ya bishi da kallo har ya bar gurin, cikin yaba rashin kunyar Badaru.  Amma kuma baiga laifinsa ba tunda ya xayyano abunda Mimi tayi masa dole ya fusata.  Abbansa ya dubi Baffa "to alh kaji abunda maryam tayi masa, bata kyauta ba sam inai mata kallon mai hankali.  Inaga yanxu muyi haquri da batun kome tunda ya ruga ya fusata,  inda rabon xama gaba a sasanta."(kuji tsabar san kai)  Baffa bece komai ba sai gyada kai yayi ya tashi ya fita. 




Badaru na shiga gida,  ya tarar da ummansu a kofar sitroom din a tsaye idonta cike da kwallah.  Ga dukkan alamu taji duk abunda ya wakana.  Yana shiga ta fidda hannu ta tsinka masa mari,  wanda hakan yayi dai dai da shigowar abbansa. Ta kalkeshi tace " wlh tallahi nasan maryam bazata taba aikata abunda ya fada ba,  sharri yayi mata.  Ai suffar macen da xatayi hakan daban take.  Maryam ka saka ko Badaru?  Macen arziqi,  baka kyautawa kanka ba inajin kamar yar cikina aka saka,  inason maryam.  Kuma wlh sai kayi nadamar rabuwa da maryam. Kaje duniya ce" Abban ya daka mata tsawa "ke!  Karkiwa dana baki akan wata maryam, ko shi kadaine ya taba sakin aure?" itam ta daka masa tsawa cikin fusata tace anyi masa,  ko ka fini sansa ne.  Badaru sum sum ya fice ganin abun nasu zai zama fada. 



Ko daya koma gida yaga gidan fayau kuma yaga tulin kayan abincin da suka bar masa harda kyautar akwati sai duk jikinsa yayi sanyi,  amma daya tuna da Nafee da kuma soyayyarsu sai yaji wani kwarin gwiwa ya shigeshi. 


******** ********************




Baffa ya riga su mumy isa gida,  ya iske mama a gida bata fita aiki ba dan bata da kwarin gwiwar yin hakan.  Lokacin wajen 10:30 na safe,  yaran gidan duk sun tafi makaranta sai masu aikin gidan tsofaffi guda biyu wadan da ke wanke wanke da shara. Ya tsaya a tsakar gida ya kwallawa mama da Mimi kira, gabansu ya fadi a tare dan yanayin kiran kawai xai fada musu abunda kiran ya qunsa. Suka fito Mimi ta tsuguna mama ta tsaya daga gefensa,  matan gidan ma duk suka fito.  Ya kalli Mimi ya daka mata tsawa "keee!  Kinwa kanki daga gidan iyayen mijinki nake naje naji irin rashin mutuncin da kika shuka har ya sakeki,  kin cuce ni kin batamun tarihin gida,  ba a taba bazawara a gidana ba sai a kanki, wai har kece kike zagin mijinki na aure akan xaki tafi hidimar qasa.  Irin tarbiyar da nai miki kenan?  To tunda kinqi xaman gidan aure akan bautar qasa bazakije bautar qasar ba in anfara tafiya,  kuma tunda kika dawomun gida a matsayin bazawara bazaki huta ba.  Ya kalli shashin da yan aikin ke tsaye cirko cirko yace ku! Na hutar daku,  kuma xanci gaba da biyanku albashinku,  kubar mata aikin daga yau na maidashi doka tayi shara tayi wanke wanke kuma tayi girki, ya wulla mata takardar sakin a fuskarta yace ga certifacate dinki nan na xaman gida kitashi ki fara aikinki tun daga yanxu.  Ya kalli shashin da mama take yace kuma duk wanda ya sabamun doka akan aikin dana sakata Allah ya isa"




Kowa ya watse wasu cikin farin ciki wasu akasin haka,  Mimi ta nufi bakin famfo ta tara ruwa ta fara tulin wanke wanken,  sam idonta babu digon kwallah. 




Bai dade da fita ba,  su Faty suka shigo.  Drivern ne ya shigar musu da tulin a kwatinan Mimi,  sannan suka zauna ana gaisawa.  Faty tace "mama ina Mimi xan bata fos dinta" Maman tace tana waje tana wanke wanke,  mumy da Faty suka hada baki sukace "wanke wanke kuma 😳" Faty taci gaba da cewa waya sata wanke wanke ina masu aikin gidannan? " 



Baffanku ne ya sakata,  yanxu yazo yana fada yaje gidan su Badaru har sun bashi takaddar ta,  shine ya dora mata aikin gidannan gaba daya.  Faty najin haka ta dau jakar xata tafi,  mumy tace mata "Faty ki zauna ki huta mana"  ta kalli mummy idonta taf da hawaye tace " me xan xauna nayi mumy Baffa na shirin kashemun yar uwa.  Kuma wai mama tanaji tana gani baxatai magana ba" tasakai ta fice. 




Mumy ma ta miqe,  ta kalli mama kanta a sunkuye,  ta miqa mata tulin kudi "gashi kudin kayan dakin Mimi ne dana siyar ki ajiye mata" mama tace to akwai na sadakinta ma a hannu sai inhada mata. 



Mummy ta nisa ta fesar da iska cikin bacin rai tace "lokaci yayi da xan hada alh Buhari da human right akan abusing din maryam da yake yi (qungiyar kare haqqin Dan Adam)" mama ta xaro ido jin abunda da Adda halima tace.  Cikin sanyin jiki tace "Adda kiyi haquri ku gyaleshi yarsa ce yana da iko akanta" mummy ta daka mata tsawa " daallah yimun shiru shashasha ki zauna ya kashe miki yaya da bakin ciki sukenan kike dasu,  shi bashi da asara.  Wlh fadima inbaki tashi kin kwatarwa yayanki yanci ba wlh saina hadashi da human right" itama ta juya ta fice. 





Har inda maryam ke wanke wanke taje ta dafa bayanta,  ta dago ganin mumy yasata yin murmushi,  mumy tace "mamana kiyi haquri na ya qare akan lamarinki acikin gidannan na kusa in kwatar miki yanci kinji."  tace " to mumy ai ba komai ma wata rana bazan ba, wata rana ko ganina saiya gagara sai dai aje kabarina ayimun addua"  tace hakane Mamana Allah ya saka miki,  Allah ya albarkaci rayiwarki amma kafin ki mutu in shaa Allah sai kinji dadin rayuwa. 




Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 2⃣9⃣


Dedicated to 

Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



A hankali aikin da Baffa ya dora mata ya fara xamar mata jiki,  duk kuwa da farko tana ganin wahalar aikin.  Gidansu babban gidane wanda shararsa kawai aikine,  sannan ga uban wanke wanke saboda yini ake da fita da abinci daga gidan domin adadin mutanen dake karbar abinci a gidan suna da yawa. Ko dattijan da suke aiki a gidan (masu wanke wanke da shara) sau tari aikin yawa yake musu, sannan ga wanke toilets din dake tsakar gidan.  Batun girki kuwa dama da coal suke yinsa bisa manyan tukwanen tasa,  kuma me girki ita keyin girki sai dai masu aikin su tayata da wanke wannan yanka wancan.  To lokaci daya Baffa ya dorawa Mimi duk wannan aiki. ( qalubalenku iyaye, miji ya wulaqanta yarinya ko kuma ya korota ku iyaye memakon ku karbi qaddara ku kwantarwa da yarinya hankali,  a a sai a tsiri muzguna mata da sunan hukuncin ta naqin xaman aure. Wlh kuji tsoron Allah irin haka inba a samu me hangen nesa ba kome haquri sai ta gudu ta shiga duniya.  Haba ai abun yayi yawa gidan miji ba dadi gidan iyayema ba dadi) Da yake tana da qarfin zuciya duk sai aikin yaxo mata da sauki. Takan tashi tun asubar fari ta fara shara,  ana kira taje tai sallah da azkar sannan ta dora breakfast ta zauna wanke wanke.  Bakwai da rabi na safe ta gama breakfast sannan ta rabawa yan makaranta ta wanke bandakuna, taje gaida Baffa wanda intaje baya amsawa sai dai cin mutunci da gorin zawarci da yake biyo baya. Kafin taje gyara dakin mama takan tarar Maman ta gyara ta wanke toilet a qoqarinta na ragewa Mimi aiki.  



In mama ta tafi aiki takanji gidan yayi mata xafi bata samun sukuni sai 11 tayi lokacin da take dora abincin rana ko kuma in dady ya dawo daga skul ya zauna yayi tayi mata shirmen yara ko kuma tayi masa homework. 



Kafin kace meye wannan lbrin mutuwar aurenta yayi fitar dango,  ta hanyar Anty da Umma.  Karma Anty taji lbr domin gida gida take aiken mutuwar auren Mimi,  kamar me rabon katin biki.  Inda kuma baxata iya xuwa ba ta buga waya ta fada.  Har gara Umma takan boye farin cikinta akan mutuwar auren, amma Anty a fili take nuna murnarta.   



A irin hakan lbr ya riski fauxa  qawar Mimi wacce suke maqota na kusa,  da farko bata yarda ba a ganinta in hakane Mimi xata fada mata.  Dan haka taje gidan da kanta,  ta iske mugun lbr kuwa domin ganin da taiwa Mimi tana tulluqar aiki ya tabbatar mata da ingancin maganar. 



Can cikin dakin Mimi (dakinta na yan matanci) suka qule. Fauxa ta riqo hannunta Mimi ta bude baki xatayi magana fauxan ta tsaidata tace "basai kince komai ba qawata,  nasan halin da kike ciki ni da ke qadadarar da Allah ya dora mana kenan. Allah ya sa muci jarrabawa" ta fada tana share hawaye, Mimi ta goge mata hawaye tace "kiyi haquri fauxa,  bakiji daga bakina ba ganinayi kyakykyawan lbr ake fada" tace nagane Mimi kuma  banyi fushi ba,  Allah ya bamu haqurin jure halin da muke ciki" Mimi tana murmushi tace amin qawata. 



Tun daga ranar Kullum sai fauxa da shigo debewa Mimi kewa,  in ta dawo daga aiki (tana aiki a wata private skul). A duk sanda ta shigo Anty kan saki shewa tace " ayyuririri bazawara qawar bazawara 🤣 Allah ya sa a dade anayi zaurawan asali." babu wanda ya taba tanka mata.  Kuma daya abun takaicin shine : Baffa yasan tana haka amma bai taba hanata ba ko ya tsawatar mata,  wanda hakan yasa ta qara qaimi wajen cin fuskar Mimi.  Ga kwanuka da ake batawa da gangan da kuma bata gida duk dan a qara mata aiki. A duk sanda fauxa ta shigo taga Mimi na aiki takan Sabe mayafinta ta taya Mimi aiki. 




Bayan haka kuma,  Anty Kullum cikin gayyato mutane take dan suxo suga Mimi,  kuma takan yi musu jagora har dakin mama a cewarta wai suxo suga gyatumar da tai wata 5 a gidan miji auren ya mutu.  Ko kunyar idon mama bataji,  kuma abun sha awa daga mana har Mimi babu wanda ke tanka mata,  ko ya nuna damuwa kan abunda tayi.  Wanda hakan shike baqanta mata rai kwarai,  domin ta fiso su tanka mata. 



Abun na Anty sam babu shaawa,  kamar ba mace ko kuma bata da yaya mata.  Ko tayi alqawari da nata mijin bazai taba sakinta ba.  




Daya matsalar itace : muguwar rashin kunyar da Mimi ke fuskanta daga qananan yaran gidan yan mata,  dan sau tari sukan bangajeta su wuce sai dai ta kauda kanta tayi kamar bata ganiba.  Domin suna yine fisa umarnin iyayensu, wadanda ke zaman shirin ta tanka su cimata mutunci.  Dan tashaji Umma na cewa " mutum bazai kasa xaman gidan aure ba, sannan ya dawo gida ya takurawa qananan yayanmu."



Duk mai imani inyaga Mimi a wannan lokaci saiya tausaya mata,  domin ta qare ta mole tayi wani yagwal da ita.  Babu rashin ci babu rashin sha, amma duniya ta juya mata baya.  A wannan lokacin sai ta kwammace xaman gidan Badaru akan mazan gida.  Wai dama haka mutuwar aure take?  Tambayar da take yawan yiwa kanta kenan.  Kota ina babu sauqi, sai a gurin ubangiji.  Ta haqiqance babu mai santa yanxu sai mama da fauxa da kuma uwa uba ya Faty. 




Faty tun daga ranar da suka debo kayan Mimi bata kuma xuwa gidan ba,  domin sam batasan ganin Mimi cikin halin da Baffa ya sakata.



Mama ce ta lura da soshe soshen da Mimi takeyi,  ta turketa ta tambayeta babu kwana kwana ta fadawa mama infection ke damunta.  Dan haka mama ta bugawa Faty waya tace gobe tazo ta tafi da Mimi asibiti,  qaiqayin bandaki na damunta. 




Saboda tasan da xuwa asibitin tun qarfe hudun asuba ta tashi ta fara aikinta,  bakwai dai dai ta gama Faty taxo suka dau hanya.  



Likitan mata ta gani, ya basu kwaje kwaje,  saboda Faty ya sa basubi layi ba suka gama da wuri suka kai masa result din.  Ya duba yace "nikam banga ciki a jikin result dinta ba,  amma ta iya yiwuwa akwaishi,  matsalar magungunan da tayi ta amfani dasu suka cushe mata mahaifarta ya kuma haifar da rashin xuwan period dinta.  Ya kalli Mimi yace ko anan gaba ki kiyayi cusa abu a gabanki,  gurin yana da rauni kuma yana da saurin karbar kwayoyin cuta.  Kinga dalilin cushe cushen da kikayi yasa ciwon qaiqaiyin tsanani a jikin ki.  Amma yanxu ga magani nan  da allura inkikayi amfani dasu yadda ya dace duk qarfin ciwon sanyi zai rabu dake, kuma suna da qarfi sosai kici abinci sosai kafin kisha" sannan ya rubuta wani abu a takadda ya bawa Faty yace " wannan maganin kinsan yadda ake amfani dashi,  duk sanda jinin al adarta yaxo shedar ta warke daga ciwon kenan sai ki siya ki saka mata acan ciki ki tabbatar ya taba mahaifarta,  tunda kince sister dinki ce xaki iya yi mata a gida basai kun dawo ba" 




Suna kan hanyar xuwa gida daga asibitin Faty ta gallawa Mimi harara tace "Mimi har magani kike cusawa a jikin ki dan ki burge Badaru ko?  Mutumin da baisan mutuncinki ba?"  Mimi ta marairaice tace " wlh ya Faty ban taba shan komai ko cusa wani abu a jikina ba,  kinaga kazar da kuka yimun ma kafin a kaini ko dandanata banyi ba. Kawai dai lalura ce Allah ya doramun"  Faty ta sauke fushinta dajin abunda Mimi tace,  kuma tasan tabbas hakan ne domin kazar ma itace ta cinyeta bayan Mimi taqi ci.  Dan haka ta sauke murya tace "ko kuma Badaru ya debo ya goga miki ba."




Da xuwansu gida tayiwa Mimi alluran tasha maganin sannan Faty ta daura mata drip (qarin ruwa) domin a cewarta Mimi ta dashe da yawa jikinta na buqatar ruwa da gaggawa. 




Kwana 8 da sakin Mimi aka tashi da azumin watan ramadan. Kuma suka tashi ta baquncin Baba Saude (wata yar uwa a gurin Baffa, wacce ke xuwa daga can garinsu Gombe duk azumi da kuma sallah ta karbi kayan azumi ko kuma kayan sallah da Baffa ke bawa yan uwansa nacan taje ta raba)  Baba saude irin mutanenne masu fadar gaskiya,  dan haka take da baqin jini gurin matan Baffa (Umma da Anty) bayan haka kuma suna baqin cikin abunda take karba a gurin Baffa ta kaiwa yan uwansa na qauye. 



Mama dai babu ruwanta cikin wannan shaani,  tsakaninta da Baba saude kyakykyawar muamala ce.  Duk sanda tazo takan tsinci kwancen kayanta kona Mimi dana dady ta bayar akai qauye a rabar,  sannan kuma takan bata yan kudi ta qara akan na Mota.  Ko kunsan alheri kan saka qauna,  dan haka tafi sauran matan Baffa daraja a gurin Baba saude.



Wannan xuwa da tayi ta tarar da baqin lbrin mutuwar auren Mimi,  ta jimanta kwarai domin ta sauyawa halin da taga mimin aciki.  Basai anfada ba kasan xaman gidan baya mata dadi,  ga uwarta me haquri tasan duk cin kashin da xa aiwa Mimi mama bazatai magana ba.  




Ana haka Anty ta fito tana kumfar baki cewar Mimi bata dora abincin shan ruwa da wuri ba.  Baba saude ta cafe maganar da cewa "ke yanxu jamila dan yaya buhari ya dorawa maryam aiki sai ku sakar mata har abincin azumi?  Ai aikin azumi yafi qarfin hannu daya " 


Umma ta shiga cikin maganar da cewa " ai bamu muka sakata ba,  ubanta ne ya sakata kuma dole tayi, sannan bamu mukaje taje tai rashin mutunci a saketa ba"  Anty ta qara da cewa "kemadai Hajara kike bata bakinki,  ai abunda uwa tayi shi yar take maimaitawa,  inbaki manta ba ai haka uwar ta dunga yawan aure aure kafin Allah ya hadata da Aminu ta maqale masa sannan daga baya aka dawo kan mijinmu.  Waya sanima ko garin yawan asiri akan korarmu abun ya koma kan yarta?  Ai maryam gadan aure aure tayi da mugun abu a gurin uwarta,  Alhmdl Allah ya mayar mata da mugun abunta kanta kuma in shaa Allahu mutuwar aure yanxu kika fara,  da yardar Allah sai kin auri maza goma" 



Mimi najin haka ta fashe da kuka me cin rai,  mama ta fito daga daki taja hannun Mimi.  Baba saude ta harxuqa ta tofa Anty yawu tare da cewa " aniyarki ta biki,  kuma ki tuna kina da yaya mata,  fata nagari kuma lamiri.  Saboda haka wlh ki kiyayi Allah, harshenki zai jawo miki bala in da yafi qarfinki,  ba a yiwa Allah ixgili" Anty tace kema taki aniyar ta biki.  Baba saude tai saurin cewa "amin,  ai duk wanda kikaji ance aniyarsa ta bishi yaji haushi wlh aniyar ba me kyau bace.  Kuma indai ana gadon mugun abu ke hana zaman aure da naki yayan basu xauna ba."



Taci gaba da mita ita kadai a tsakar gida,  haka al amuran gidannan suka dame? Lallai yaya Buhari inbewa tufkar hanci ba tabbas jamila xata watsa masa gida.  Taja tsaki mtsewww.  Inbanda abunsa ma meye na damuwa da mutuwar auren maryam?  Sama da yaya goma suna gidan miji a xaune dan Allah ya dora masa qaddara akan daya ya kasa dauka.  Bare inda mutuwar aure ta zama gama gari,  aimu ko acan qauye ba a tsangwamar mace dan aurenta ya mutu. 



Umma ta leqo ta taga tace da Baba saude "karki kuma cewa yarsa ce,  domin shi duk nasa yayan na gidan miji a zaune basu taba zawarci ba saboda basu ga munayiba"  Baba saude ta katseta da cewa "to saiki zuqe jinin maryam daga jikin Buhari domin sharia ta riga ta bashi ya" Umma tace ai shi da kansa yace ba jininsa bace,  shi jininsa basa mutuwar aure.  Taje can ta nemi inda tayo gadan aure aure. 




Baba saude bata kuma cewa komai ba,  sai daga murya tayi yanda Mimi xata jiyota tace "ke maryamu kiyi shiru kinji,  Allah ya na tare dake,  shi dora miki kuma in shaa Allah xai baki mafita"



Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 3⃣0⃣


Dedicated to 

Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



A haka ta fara axumi wanda ya qarasa ramarta ta qazanta,  domin sam abinci baya ciyuwa a gurinta. Ta dage da adduar neman sauki gurin ubangiji,  kuma duk wani masoyinta na tayata.  Kullum in ansha ruwa Mimi ke xuwa gidansu fauxa su tafi masallaci yin sallar tarawih domin gidansu fauxa yafi kusa da masallacin.  Sau tari a masallacin ma bata rasa masu yin zundenta da qusqus din mutuwar aurenta. 



A al adar gidan Baffa duk goma ga watan Ramadan yayansa kaf maza da mata, masu aure da marasa aure har na wani garin ana haduwa asha ruwa agida saboda sada xumunci.  Kuma uku ga kowacce sallah (sallah babba da sallah qarama) suna kuma taruwa shima aci abinci a sada xumunci ayi hotuna.



To wannan karon ba ai shan ruwan goma ga azumin ba kamar yadda aka saba,  saboda ya jafar bezo daga kaduna ba inda yake aiki.  Sai da azumi yayi rabi (15) sannan yaxo kuma a ranar aka fara shirin shan ruwan.  Yawanci duk yayan gidan mata sukanxo tun azahar a hadu ayi aikin abincin shan ruwa.  To yau dinma hakance ta kasance,  wadanda ke farin ciki da mutuwar auren Mimi da wuri sukazo sukaga dahir sannan suka dunga shewa suna sakin habaici. Masu hankalin ciki kuwa,  abun bai musu dadi ba saboda haka Anty Adawiyya ta jagorancesu sukaje dakin mama suka jajanta mata mutuwar auren sannan suka taushi Mimi tare da bata haquri akan abunda yan uwansu ke mata.  Mama taji dadin wannan karamci da sukayi mata ta dunga godia kamar sun bata wani abun.  




Azahar kowa ya hallara inka cire ya Faty da bata taso daga aiki ba,  duk suna baje a tsakar gidan suna aiki, masu gyara kaji nayi, masu hada zobo nayi masu gyara ayar kunun aya sunayi da masu gere dankali.  Baby tai sallama ta shigo jikinta sanye da uniform da alama daga skul take. Baby itace ya ta tara a dakin Anty,  shekarunta bazasu wuce 15 ba,  tana aji 1 a babbar sakandire (senior secondry).



Tana shigowa wani almajiri ya biyota,  "wai ana kiran wacce ta shigo yanxu" inji almajirin.  Baby ta murguda baki cikin tsabar fitsara da tashen balaga tace " wlh na tsani naci, tundaga makaranta yake bina maye."  



Anty tai saurin fitowa daga kitchen tace "je kace yarinya ce bata tsaiwa da samari" yaron ya fita fadar abunda aka aikeshi. 



Anty ta ruqe haba cikin sigar al ajabi tace "kai wadannan yara da farin jini suke,  babu dama su fita sai an biyosu.  Wlh bari Baffa ya dawo mu xauna ayi magana,  gara tanayin candy a aurar da ita inyaso jamiar tayi a gidan mijinta.  Aini nadau darasi da barin da ya dade a gabanka, qarshe kwantai yakeyi.  Wlh tana candy xan aurar da ita" (kunji fa kamar auren a hannunta yake,  mudai munsan koda miji a hannu aure sai Allah yayi tunda aure lokaci ne.)



Rashida ta kalli shashin da Baby take tsaye tana murmushi saboda jin abunda uwarta tace na cewar tana da farin jini,  tace "aike Baby ki godewa Allah tun yanxu anfara kawo miki hari,  alamar cewa ba zaki Bandaro ba.  Saboda wlh in mutum yayi kwantai ko yaje gidan mijin ba iya xama yake ba" ragowar yan jam iyar Rashida (masu qin Mimi) suka saki dariya tare da cewa "wlh kuwa 🤣🤣🤣"



Anty Adawiyya dake gefe ta cije lebe saboda duk wanda ke gurin ya fuskanci inda maganar Anty da Rashida ta nufa,  Anty Halima ta kalli Adawiyya cikin takaicin abunda uwarta da yar uwarta sukai (halima yar Anty ce) tace Anty wai haka zamu zuba ido abubuwannan suci gaba a gidannan,  infa akaci gaba da haka nan gaba kadan xumunci xai watse mune manya ya dace mu gyara abun.  Anty Adawiyya tace " Halima mexance?  Ai baka canja mutum kina ganin kwanaki da nai hukunci akan abunda Rashida kewa Mimi qarshe abun fada ya xama tsakanin Umma da Anty.  Saboda haka duk wanda aka fada masa yaqiji sai a kyaleshi duniya tai masa nata karatun"




Suna zaune akan qatuwar tabarma da aka malala a tsakar gidan,  kayan abinci ne jibgi a gabansu kowa na diban abunda yake so yana ci.  Duk zuriar gidan sun hallara tundaga kan Baffa, matansa, yayansa da surukarsa (matar yaya Ali) da kuma jikokinsa.  Anata hira ana jin abinci cikin raha,  ya jafar ya kalli Baby yace "ke jeki kice Mimi ta fito,  inna kuma aiko ta fito bata fito ba sai ranta ya baci." wannan shine karo na 3 da yake aikawa kiran Mimi amma taqi fitowa,  kuma ba wani abu ke hanata fitowar ba sai gudun abunda ka iya faruwa inta zauna a cikinsu.  



Umma tai tsaki ta dan harari jafar,  tace "to kai ina ruwanka da rashin fitowarta,  ai dan ta nuna muku mugun halinta ne yasa bata fito ba,  tayi abu yazo ya dameta ya hanata shiga cikin mutane." 




Wannan karon Mimi tare suka fito da Baby,  sanye take da hijab me hannu.  Faty bataso tilastawar da ya jafar yayi Mimi ta fito ba saboda tasan dole sai anyi abunda xa aci xarafin Mimi.  




Ganin babu guri a inda Baby ta xauna yasa Mimi tayi nufin tsallakewa can kusa da Anty safiyya (matar ya Ali) . Ganin da Rashida tayi Mimi na shirin tsallaketa yasa ta miqe qasa tare turo qatan cikinta,  Mimi ta daga qafa xata tsallaka a hankalce saboda kar ace tayi wani abun ko ta buge mai ciki Rashida tasa daya qafar ta tade Mimin. Ai kuwa ta yanke jiki ta fada kan Sumayya take zaune da jaririnta dan 4 month akan cinya, sannan ga kofin shayi sai tururi yake a gabanta.  Cikin axama Sumayya ta ture Mimi daga kan jaririnta ta tura mimin kan ruwan shayin tare da cewa "bakya ganine zaki kashemun da?" 


Zafin ruwan shayin bai gama ratsa Mimi ba taji saukar mari a kuncinta.  Tai dafe kunci tare da dagowa taga wanda ya mareta tai arba da Baffa sai huci yake yana kallonta cike da tsana yace "dan bakisan ciwon haihuwa ba shine xaki fado mata akan jariri?  Ke dan kin gaza xama a naki gidan ki haifi naki dan zakixo ki fado musu ka?  Ke wace irin muguwar yarinya ce". 



Umma tace ai dama tunda aka tilasa mata fitowa batai niyya ba nasan saitayi abunda xata sosa mana rai kuma shine muguntar taki xata qare akan jikana?  Rashida na gefe sai murmushin jin dadi take. 



Duk wanda ke gurin ya lura da abunda ya faru saboda hasken nefa tanyar a tsakar gidan.  Mimi abun yayi mata yawa ga zafin qonewa ga zafin maganganun Baffa,  ta fashe da kuka tace " Dan Allah kuyi haquri,  inwani laifin nai muku kuka tsaneni dan Allah ku fadamun in gyara" tana kaiwa nan ta shige daki.



Ya jafar da tausayin Mimi ya hanashi daurewa ya kalli Baffa yace "Baffa wannan wane irin hukunci ne?  Wlh ina kallon abunda ya faru, Rashida ce ta turota dan me xaka goyi bayansu qonata fa sukayi" Anty tai saurin kare Rashida da cewa karkai mata sharri, kawai dai ta shirya mugutar fadawa kan Rashida tasa ta naqudar dole ita kuma Allah ya bata sa a ta tureta.  Baffa ya hau borin kunya da "yimun shiru jafar, kaine ka haifeni?  Ko kai xakaimun hukunci a gidana"




Faty tabi bayan Mimi itama tana kuka. Jafar ya kalli shashin da mama ke zaune yaga tananan inda take ko motsawa batai ba sai dai ta kasa cin abincin sai juya tea take da spoon.  Anty Adawiyya ta dakko qaramin try ta xuba duk nau in abincin dake gurin ta bawa Anty safiyya tace "kaiwa su Faty daki"  Faty na zaune kan kujera tana kuka tana shafawa Mimi jelly a dantsen hannunta inda ruwan shayin ya xaba.  Anty safiyya ta bata abincin tace ki tabbatar Mimi taci. Kuyi haquri Allah baya zalunci kuma ya haramtashi garemu in shaa Allah xakuga sakamako. 




Faty ta dunga diban abincin da hannu tana bawa Mimi,  ita kuwa ba musu ta dunga karba tanaci.




Tun jiya da abun ya faru har ixuwa yanxu da gari ya waye tunani take. Wai shin meyasa indai aure ya mutu a Society dinmu laifin kan zama na ya mace ita kadai?  Wai yaushe YA MACE xata samu yanci a Society namu?  Wadannan sune tambayoyin da ta rasa me amsa mata. 



Kanta ke mugun ciwo,  wanda tasan tunani ne ya haddasa matashi.  Ga kuma yanxu mararta ta daure,  alamu kamar period pain.  Tananan kwance,  taji ciwon marar ya fara tsananta kuma taji danshi a qasanta.  A fili tace "babu ciki a jikina kenan kamar yadda Dr yace" gudun kar ciwon mara ya galabaitar da ita gashi mama ta tafi aiki yasa ta tashi taje parlour ta dakko gwangwanin maltina a fridge tazo ta balli maganin ciwon mara tasha.  Lokacin ko ganin gabanta bata iyayi saboda tsananin ciwon kai. 



Tana kwance tana murqususun ciwon mara da ciwon abunda Baffa Yayi mata,  itadai tun take da Baffa bata taba gani ya dora hannunsa akan wani da a gidan ba sai ita.  Koda yake itakam a gidan tana da banbanci da kowa,  domin Baffa ya mata abubuwa da yawa da bata taba gani yayiwa wani ba. 



Da farko bayan qin biya mata ko sisi a cikin hidimar karatunta,  yazo ya takura mata da sunan taqi aure,  yayi mata auren dole sannan auren babu dadi bai taba taka gidanta da sunan yaje ganinta ba,  duk kuwa da cewa dabiar sa ce xuwa gidan yayansa yaga halin da suke ciki kuma ya musu alheri.  Amma ita tunda aka kaita ko waya bai taba yimata ba.  Abu na qarshe shine: anyi mata sakin wulaqanci ta dawo gida ya kuma takura mata,  takurar da tafi ta farko,  ga kuma duka anfara jiya.  




A wannan gaba taga ya dace ta karbi shawarar da xuciyarta tasha bata a kwanakin baya,  dan haka ta miqe ta dauki kudi ta fita ta tsaya a soro ta aiki wani almajiri ya siyo mata abunda take buqata.  Tananan tsaye yaron yaje ya kawo mata aiken,  ta bar masa ragowar canjin. 




Da magriba ta gama duk wani aikinta ta shige daki tunda ba azumi tayi ba, tabar mama tana shan ruwa a parlour. 




Fauxa da tagaji da zaman jiran Mimi ta biyo mata zuwa sallar tarawih bata zoba ta tashi domin biyawa Mimi,  dan taji har an tayar. 



Ta sami mama a parlour suka gaisa Maman na shirin shiga bedroom tace "qawartaki na dakinta tun dazu kinga ma ko ruwa bata sha ba" tace to bari in dubata. 




Shigar Fauxa dakin tayi dai dai da lokacin da Mimi ta daga kwalbar FIYA FIYA (abunda aka siyo mata daxu) xata kai bakinta.  Fauxa ta kwala kiran "MIMI" a razane 😳 tare da doke hannun mimin.  Kwallah kiran da tayi ya janyo hankalin mama daga bedroom, taiwa dakin tsinke tana tambayar lfy?.  Fauxa batabi takan tambayar da mama keyi ba.  Ta qarasa ta riqe kafadun Mimi tana girgixata cikin kuka tana cewa "Mimi kashe kanki xakiyi akan mutuwar aure?  Shin in kashe kanki wanda ya sakeki yana da asara ne?  Mesa xakiyi haka?  Duk fa abunda xai faru ya riga ya faru.  Ansake ki,  an takura miki,  anyi gulmarki,  anmiki sharri.  Inbaki sani ba maganganu da yawa ke yawo akan mutuwar aurenki.  Akwai masu cewa cukumar mijinki kikayi kina zaginsa ya sakeki,  wasu kuma suce wai sata kikai masa ya sakeki,  ke harda masu cewa ya kamaki ne kina lesbian (neman mata) ya sakeki.  Amma duk wandannan maganganu da nakeji bana fada miki saboda kar in daga miki hankali. Amma shine yanxu xaki kashe kanki Mimi?  Why Mimi,  Why. Wlh indai akan baqin cikin namiji kike haka gara ki dena,  shin ni ba a sakeni ba?  Ni harda Da aka sakeni mutu nayi?  Ko takurar da aka yi miki ba ita akemun ba,  kafin Baba ya gane gaskiya ya sakarmun mara?"




Maganganun da Fauxa keyi yabawa mama amsar tambayar da take yi,  dan haka cikin kuka ta juya tabar dakin.  Mimi ta gigice ganin kukan mama dan tasan ba qaramin abu kesa mama kuka ba,  tai gargawar biyo bayan mama tana cewa "mama ki yafemun na tuba 😪"  



Fitowar mama tai dai dai da shigowar Faty parlourn, ya Ahmad na biye da ita.  Dan bata gamsu da yacce tabar Mimi a jiya ba shiyasa ta kuma xuwa ta taushi Mimi.  Ta iske wannan mugun lbr, fauxa ta fada mata tace "WHAT" kalmar data janyo hakalin matan gidan, nan da nan kuwa suka cika qofar dakin mama suna kallo.  Ya Ahmad kuwa gurin mama yaje ya tsuguna gefenta yana nemarwa Mimi yafiyar abunda tayi. 




Faty kallon Mimi take da wata irin fuska 😡 wacce babu wanda ya taba ganinta da ita.  Mimi tana rabe jikin bango,  cikin kuka take furta "am sry,  am so sry sister"  Faty batabi takan haqurin da Mimi ke bata ba,  ta kifawa Mimi mari,  ta kuma kifa mata wani,  ta qara mata.  Ataqaice dai sai da tayiwa Mimi mari guda 6 xafafa.  Mimi idanunta a runtse,  bata dauke kanta ba, ba kuma ta fasa furta "am sorry sister"  



Wadanda ke bakin kofa suna kallo abun yayi matuqar girgizasu,  domin ba qaramin abu zaisa Faty ta daki Mimi, bama su taba gani ko fada Faty taiwa Mimi ba bare duka.  Dan haka kansu ya qulle suka rasa lefin da Mimi ta aikata Faty ke mata wannan hukunci.  Kuma ta wani barin abun ya burgesu domin daga Anty har Umma babu wacce daya daga cikin yayanta na sama ya isa yayiwa na qasa hukunci haka,  ba ai gagarumin yaqi ba. Kuma daya abun burgewar har wanda akaiwa hukuncin yana bada haquri. 




Faty na gama marin Mimi itama ta fashe da kuka, ta janyo mimin ta rungumeta tsam suka xube qasa tana shafa kan Mimi tare da cewa "is Ok sister" Fauxa ma ta matso kusa tana lallashin Mimi cike da yabawa hukuncin da ya Faty tayi mata.  A xuciyarta tana aiyana duk renda Allah ya bata yaya mata xatayi iya yinta ta hada kansu kamar yadda mama ta hada kan Faty da Mimi. 




Yan kallo kuwa dole suka watse ganin film ya qare.  Ya Ahmad ya tafi ya bar Faty ta kwana,  saboda halin da mama ke ciki.  




Can tsakiyar dare suna kwance kan doguwar kujera,  mama dauke da Dady kan cinyarta,  sai Faty dake zaune tana bacci Mimi kuma ta tada kai da tata cinyar.  Tun faruwar abun Mimi ke bawa mama haquri amma mama tayi kunnan uwar shegu kamar batajin abunda Mimi ke fada,  yanxu ma sai kuka take tana qara neman gafarar mama.  Mama ta shafa fuskarta tace "na haqura Mimi, amma ko wane irin hali xaki shiga karki qara yunqurin halaka kanki,  kinga ku kadai nake daku in kintafi kinbar yar uwarki ni da ita ya xamuyi?  Bakisan rayuwarki nada matuqar mahimmacin a gurin mu ba?  Danme xaki kashe kanki akan wadanda mutuwarki sukafi so akan rayuwarki?  Mimi kiyimun alqawari daga yau zaki cire duk wata damuwa a ranki ki fuskanci abunda ke gabanki.  Da ace mutane suna riqe abunda ya riga ya wuce wlh da baqin cikin ya kashe rabin mutanen duniya.  Saboda haka past is gone forever, ki gyara present dinki,  future kuma ki barwa Allah shi yasan abunda future xata xo miki dashi." 




Mimi ta gyada kai cike da gamsuwa da kalaman mama, sannnan ta qudure yin aiki da abunda maman tace mata.  



Ta yunqura ta miqe xataje toilet domin canja pad din jikinta da ta jiqe,  mama tai saurin cewa ina xaki?  Tace " xan canja pad ne"  wani farin ciki ya xiyarci mama,  jin Mimi taga jini wanda hakan ke nuna babu ciki kenan.  Ta dunga godia ga Allah domin batason Mimi ta haihu da Badaru.  Tace da mimin muje in rakaki,  Mimi ta zaro ido 😳 tace "mama toilet din xaki rakani?" mama na tafiya tace "eh nasani ko ki kuma yunqurin halaka kanki"  Mimi ta marairaice tace " mama zargina kike wlh bazan kuma ba na baya ma da nayi kuskure ne."




Yan kwanakin da suka biyo baya ta dan samu sauki,  amma fa ba sauqin aikin gida ba saukin damuwar dake xuciyarta a bisa amfani da shawarar mama.  Ta kuma yardarwa kanta xatai karbi rayuwa a duk inda taxo mata. 




Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 3⃣1⃣


Dedicated to 

Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)




Ranar da Mimi tayi wankan tsarki ranar Faty tazo gidan,  ta tasa Mimi a gaba harda yan kayanta set 2. Mimi tace "ya Faty Baffa inyaxo ya tadda banyi aiki ba xaimun fada." Faty ta fallara mata harara "xan dura miki xagi Mimi,  ana xancen lfyarki kina xancen fadan Baffa?  Ko kin manta abunda Dr yace in kinga jini insamiki wani magani?" Mimi ta marairaice tace "ya Faty ai na warke ko sati banyi ina amfani da maganin ba na daina qaiqaiyin, wlh kamar ban taba yiba." Faty ta kuma watsa mata harara tace " ke wlh sai kin bini in yaso in kin dawo Baffa ya kasheki bashi kikejin tsoro ba?" tace tuba nake sis muje 😊




Bayan sunsha ruwa sun huta,  Faty ta dakko maganin tasa safar hannu tace da mimin kwanta.  Mimi ta waro ido tace "ya Faty😳 yanxu wai saina bude jikina?"  Faty tace "a a karki bude insa miki magani, amma ai kin budewa Badaru ko? Mimi najin haka ta kwanta ta bude jiki,  Faty ta gama yi mata gwaje gwaje tasa mata magani.  Tanata tsaki tare da cewa " wannan mutumin ya cuceki Mimi dole sai anmuki stitches (dinki)" Mimi ta zaro ido cikin kidima 😳😳😳 tace "ya Faty na samu qari ne? Naga masu haihuwa akewa dinki" tayi tsaki tace "ba gara wacce ta haihu dake ba, ita tasan haihuwa tayi.  Kuma ba sai lallai masu haihuwa akewa dinki ba. Ba qari kika samuba amma ya miki barna a jikin ki ya nuna mugunta wajen kusantarki, gara ma da Allah yasa nagani amma wannan in kikayi aure ai sai kiji kunya, wata 5 a gidan miji amma wani mijin ya sameki sakwakwa haka ai sai yace qarya ake cutarsa akai."



Washegari kuwa tana dawowa daga aiki tace da Mimi ki shirya in ansha ruwa xamuyi aikin, na siyo kayan aikin masu kyau wanda in anyi basai an ware ba zaibi jikin ki. 



Kafin asha ruwa Mimi ta tsure,  mugun tsoron dinkin takeji kamar tace a fasa.  Haka dai ta haqura aka fara dinkin,  tunda aka fara ta runtse idonta tare da cije lebenta saboda azaba.  Har akayi stitches din aka gama ko tari bataiba,  Faty ta dunga yabawa dauriyar da Mimi tayi.  Mimi ta kalleta tace "ya Faty xai kai kwana nawa kafin ya warke?" Faty tace "kayan aikin da nayi miki amfani dasu masu kyau ne,  amma duk da haka ya danganta da irin jikin ki da kuma irin kulawar da kikayi dashi." ta bata magani ta hadiya saboda ya kashe xafin gurin, ta qara da cewa indai jikinki me kyaune gurin zai koma fresh kamar baayi dinki ba. 




Kwananta biyar a gidan Faty, ta samu nutsuwa da kuma sakewa ga kulawa da shiga ruwan dumi saboda stitches din. Nan da nan kuwa ya kame kamar bame dinki ba tafiyarta ta koma normal.  Kuma a ranar ne Baffa ya lura ko kuma aka kai masa gulmar Mimi bata gidan.  Shima daya lura sai yaga baya ganin kai kawonta a tsakar gida, kuma tsaftar gidanma ta ragu saboda masu aikin sun karbi aikinsu, lokacin da Mimi  na aiki gidan yafi tsafta.




Dan haka ya bugawa Mimi waya yace ta taho kafin ranta yayi mugun baci,  a cewarsa tunda batai zaman nata gidanba bazataje ta kashewa wata nata auren ba. 



Sai wajen goman dare ya Ahmad ya maidota gida.  Ta dunga lallaba jikinta saboda kar stitches din ya samu matsala,  duk abunda xatai tana kula sannan ko mama batasan da xancen dinkin ba.  




Azumi ya tasamma qarewa anata shirin sallah,  a wannan lokaci ita kanta tasan ta samu sauki.  Domin tana jin jikinta a matse kamar lokacin da tana 15 years, ita kanta tasan ta samu canji a jikinta.  Gashi ta dan murmure saboda kwanciyar hankali data samu.




Ranar 3 ga sallah gida ya cika kamar yadda suka saba zuwa, kowa cikin kwalliya ta burgewa da qoqarin nuna tattalin arziqin mijinsa. 😄




Mimi bata fita tsakar gidanba inda aketa photuna ake shewa, saboda tayi alqawarin dena shiga cikinsu duk rintsi.  Tana zaune parlour tana karatun wani novel da aka turo a grp,  Rashida da tawagarta suka shigo.  Rashida tace ina mama?  Xuwa nayi inyi kallo a dakinnan parlourn Umma yara sunyi yawa.  Ta xauna akan kujerar kusa da Mimi,  ragowar wadanda suka shigo tare ma duk suka nemi gurin xama.  Ta kunna kayan kallon sannan tasa fefen CD na film din ZAURAWA na AISHA DANKANO,  wanda takanas Rashida ta taho dashi daga gidanta dan kawai taci zarafin Mimi.  Ana kallon film din su Rashida na hira tare da aibata zaurawa da tsine musu,  wai a cewar Rashidan "duk wata bazawara karuwa ce,  suna fakewa da xawarci suna neman maxa. Kuma da mijinki ya auro miki bazawara gara ya auro miki visites domin bazawara saita nuna miki tasan namiji.  Ta kuma gyara xama tace,  ai duk macen da ta fara mutuwar aure to wlh haka take qare rayuwarta a aure aure yo dama mutum dakyar ya shiga bare yanxu." 



Mimi tayi banxa dasu tana danna waya, saboda ta kasa karatun novel din dan maganganun Rashida sun tabata.  A zuciyarta kuwa cewa take "rashin fita cikin nasu ma ban tsira ba tunda har dakin uwata anbiyo ni ana zagina" tana wannan tunanin har film din yazo dai dai inda Aisha Dankano ke cewa "ZAURAWA" nan take kuwa Rashida ta saita babban yatsanta saitin Mimi 👍🏼 tare da cewa "SUNE" ragowar suka saka dariya sukace Rashida baki da M. 




Anty safiyya dake dakin Mimi a kwance duk abunda suke tana jinsu,  kuma babu wanda yasan tana dakin.  Ta fara tunanin dalilin da yasa yan gidannan suke haka sai kace ba yan boko ba,  kawai dan aure ya mutu sai a takurawa yarinya. Itakam bataga laifin Mimi ba,  yarinyar tanada haquri da shiga rai.  Ta tashi ta fito ta riqe labulen dakin tace "tace meye haka nakeji Rashida?  Waike wace irin yarinyace mai neman fitina? Ki biyota har dakin uwarta kina insulting dinta?"  Rashida ta murguda baki cikin fitsara tace "babu ruwanki malama,  muna abunmu iya yan gida kinxo kinsa baki,  wannan aiba abunda ya shafeki bane" Anty safiyya ta nunota da yatsa tace "ke!  Kikiyayeni,  in kinsaba iskanci a kyaleki ni inkaimun Ali (mijinta) xansa ya casaki." Rashida najin haka tayi shiru dan tasan yaya Ali babu ruwansa ubanta zaici. 




********   ********      *******


Kwana goma dayin sallah ta kuma tsintar kanta cikin jini,  wanda ke maxaunin jini na biyu bayan sakinta. Kuma hakan ya nuna saura jini daya kenan ta tashi daga matar Badaru,  tunda munsan cewa iddah jini 3 ce.  Ba wata uku ba kamar yadda wasu ke fada,  sabida ba kowace mace ke jini duk wata ba.  Wata tanayin sati 3 wata kuma 25 dayz (kamar Mimi kenan). 




Haka al amura sukaci gaba da tafiya,  tasamu saukin rayuwa sosai saboda aikin da Baffa ya dora mata ya xamar mata jiki inbataiba batajin dadi.  Sai dai surutun mutane akan mutuwar aurenta har yanxu abun be sauki ba,  wannan kuma ta kance suyi su gama watan kwaram daya ne, na biyu sai gagara. Mutane kan bata mamaki,  inbakai aure ba a dameka inkayi balain gidan auren ya hanaka xama nanma asaka agaba. 



Duk magribar duniya fauxa kan shigo susha hira sai goman dare take tafiya.  Wanda hakan kan yiwa Mimi dadi,  kuma yakan debe mata kewa.  Dan ita Baffa ya hanata fita ko kofar gida.  A cewarsa kunya yakeji aganta ace yarsace kuma bazawara ce.  Dan haka suka qara shaquwa sosai da fauxa.  Duk wani abu da take buqata fauxa take bawa ta siyo mata. 




Sati hudu dayin qaramar sallah katin bikin Badaru yazo gidansu.  Kuma a lokacinne mate din Mimi suka fara registration din tafiya service domin an bude musu portal,  ta dunga kuka saboda Baffa ya hanata.  Sam bikin Badaru baya gabanta bata sansa balle tai kishinsa dan haka in mata 100 zai aura wlh baxata damu ba. 




Ranar asabar data kasance ranar yinin bikin Badaru matan gidansu Anty da Umma suka shirya suka tafi duk kuwa da cewa ba wani xumunci ke tsakaninsu da Umman su Badaru ba,  amma saboda a cuzgunawa Mimi suka tafi,  mama kuwa dama ba a gayyaceta ba. 




Ai kuwa suka dawo da lbrin irin gidan da Badaru ya qera domin sunje kai amarya,  da kuma irin bushashar da yayi a bikin.  Sukaita fadar magana wai ai yanxu yayi aurenso domin ya nunawa duniya yanason Nafee.




Ranar da aka kai masa Nafee a daren ya tumurmusheta, saboda yana yunwar abun. Amma ga mamakinsa a daren ya shigeta tsaf,  sabanin Mimi da sai da yayi kwana biyu dan ma tagomashin maganin kuzari.  Abun ya daure masa kai,  gadai Nafee danya shataf (mai qarancin shekaru) amma Mimi ta fita qaramar halitta.  Ashe abun ba shekaru bane.  Amma duk da haka ya yaba mata kwarai  tunda ya sameta cikakkiyar mace wacce ta kawo masa mutuncinta dan haka ta kuma samun gurbi sosai a zuciyar Badaru. 



Itama ta bangarenta tasha wuya sosai,  amma ta daure ne saboda soyayyar da takewa Badarun. 




Ranar da Mimi taga jini na uku (ranar cikar iddarta) har sadaka tayi saboda farin cikin sun rabu da Badaru har abada (abunda take fata). Mama kamar ta xuba ruwa a qasa tasha,  ta dunga sallar Nafila tana roqawa Mimi da duk wata ya mace samun miji nagari da ingantacciyar rayuwa. 




Daf ake da babbar sallah. Cikin wata guda da aurensu suka fara samun sabani da Badaru a dalilin yawan buqatarsa,  ita kuma tagaji da juriya.  Abunda kuwa ya faru shine: dake ance me hali baya fasa halinsa Badaru yaci gaba da bankar magungunan qara kuzari,  wanda ya qara yawan buqata akan tasa,  ita kuma Nafee taga sam bazata jura ba.  Duk kuwa da cewar Badaru baya ware mata qarfi kamar yadda yakewa Mimi.  Sabanin haka ita yakan yi romancing dinta ya lallabata kafin yakai gaci.  Kuma yanayin hakanne saboda soyayya da kuma duba qarancin shekarunta. 



A bangare guda kuma bata samun yacce takeso ta wajen cima, sabida ta gama sawa a ranta inta auri Badaru zaman jin dadi xatai saboda yana da kudi, ga kuma gida daya qera mata.  Shi kuma Badaru baisaba siyan komai a gidansa ba, amma duk da haka yasan xaman da yayi da Mimi babu macen da xata yadda da haka.  Dan haka yake sassauta wasu al amuran.  Yana siyan komai na cefanen gida dai dai gwargwado saboda har yanxu gushirin yana kan kaxa.  Sada nama da kayan shayi da bai taba saiwa Mimi ba yakan saiwa Nafee da sun qare,  sai dai kudi ne kwandala bata taba shiga tsakaninsu ba.  Wanda Nafee taga bazata lamunta ba.  




Abunda ya fara kawo musu sabani kuwa shine : tara qawayen da takeyi danta nuna musu itafa yanxu ta kere sa a ta auri mai kudi.  Wanda shi Badaru sam baya qaunar yaga anshiga gidansa,  kuma in sukaxo inyananan sai tace ya basu kudin mota inma bayanan saita ciwo bashi a maqota inya dawo ya biya.  Kuma duk wani nama da ya siya a gidan in qawayenta sukaxo sai sun cinyeshi.  A irin haka wata rana qawayenta sunxo dayar ta buqaci Nafee ta bata always ta canja,  Nafee da son gwaninta ta dakko ledar always ultra gaba daya ta bata.  Wacce dakyar Badaru ya siyo mata ita  domin cewa yayi bai taba siya ba,  kuma tai masa kudi da yawa harda cewa abar da za asa ayar har sai ansa 500 ansiya?  A taqaice dai sai da aka kai ruwa rana kafin ya siyo gashi Nafee ta bada ita lokaci daya. 




Yana dawowa kuwa ko sannu da xuwa batai masa ba ballantana ta bari yaci abinci tace "kaje ka siyomun always" ta fada cikin sigar rashin mutunci dan kar yace bazai siyo ba.  Ya kalleta a kaikaice yace "amma kyabari inci abinci ko"  ta qara tsuke fuska tace "ai babu abincin domin nayi baqi sun cinye kuma kafin na dora wani ka dawo"  ya jinjina kai cikin qosawa da halinta domin ba wannan ne karo na farko da tayi mai haka ba yace "ba shekaran jiya na siyo miki ba? Harta qare kenan?"  cike da isa tace "na bayar da ita daxu,  domin da kunya axo a ganni a wannan makeken gidan inkasa bada ledar always ai wlh kamata yayi ka dunga saimun sunqi guda saboda qawaye na"  yace "ok haka ya dace kiyi?  Kinyi dai dai"




Ala tilas yaje ya siyo mata always din,  domin da yaqi siyowa xama ta dunga yi ko ina tana batawa da jini daga qarshe ma da taga bai dauki abunda tayi da mahimmaci ba saita zauna akan cinyarsa ta batashi da Jinin (su Nafee yan iska🤣) dan haka ya yi saurin tashi yaje ya siyo tun kafin ta haram ta masa xama a gidan saboda qazantar jini,  domin shi Allah ya yi masa kyankyamin jini.  




Ranar alhamis suka tashi cikin tashin hankali, fada kacucur suke da Nafee yana fada tana mayar masa kamar ba sune masoyan da suka shafe shekaru suna soyayya ba.  Dalilin fadan kuwa shine: Nafee tace ya siyo mata kaza domin ta dade bataciba a fadarta rabonta dacin kaza tun ta daren amarci,  kuma wannan danqareren gidan kamata yayi ace Kullum da farfesun kaza ake breakfast 🤣. Shi kuma ya bata amsa da bazai siyo ba,  domin a gidansu ma ai ba kazar take ciba,  naman kasuwar ma da ta samu ta godewa Allah (abunki da wanda ya saba da fadar baqar magana) ai kuwa yana fadar haka Nafee ta taso masa kamar xata dakeshi tanayi masa warning din karya kuma sa gidansu acikin rashin mutuncinsa domin inya kuma xatayi babban rashin mutunci. 




Da haka ya tarkata ya fita saboda karya zauna zuciya ta xugashi ayi batacciya. A kasuwa tunani ya yini yi na mamakin halin Nafee. Shidai a iya zamansu baisan haka halinta yake ba ashe lambu lambu tai masa,  to kodai qawaye ke xugata?  Wata xuciyar tace ba wasu qawaye halintane hakan ta boye makane sai daka aureta.  Wannan shine ana zaton wuta a maqera ansameta a masaqa,  yana zaton a gurin ruqaqqun yan mata masu ilimi irinsu MARYAM ake samun fitsara da rashin kunya wa miji ashe abun ba haka yake ba,  sai gashi yar qaramar yarinya Nafee da ko secondry bata gama ba tanayi masa abunda bai taba tsammani ba.  Ada ya dauka xai juya Nafee yacce yakeso ya koya mata irin aqidunsa sai yaga labari yasha banban domin tun kafin aje ko ina Nafee na neman fin qarfinsa.  




Haka ya yini tunani a kasuwa, da dare ya dawo batai abinci ba. A cewarta wai ya bata mata rai saboda haka bazatai girki ba. Sai gurin me shayi yaje yaci indomie 😂.



Dake tsohon jarababbene,  a wajen kwanciya sai ya nemi haqqinsa.  Ai kuwa tace "kai ka isama?  Bakaban nama naci ba kazo ka mutstsukeni? Aikin banxa jarababbe kawai bakasan komai ba sai dare yayi ka danne mace" qiri qiri ta hanashi abunda yakeso kuma dole ya haqura. 




A daren ya gama yanke shawarar abunda zaiyi, domin ya gaji da rashin kunyar Nafee da iskancinta.  Kuma gashi ta fara hanashi haqqinsa shi kuma bashi da juriya a wannan fanni.  Dama kuma cikin yunwar abun yake domin sam baya samun gamsuwa da Nafee yacce yake samu da maryam,  ya saba da xagaye daya ya gamsu amma itakam Nafee sai yayi biyu xuwa uku yake samun biyan buqata lamarin da Nafeen taqi yarda dashi domin tace ita ba shinkafa bace dazaita sasuqarta. 




Dawo da MARYAM xaiyi domin ya fara gane kuskurensa na saurin rabuwa da ita.  Saboda haka xai dawo da ita ta zabe masa ruwan kashe shaawarsa a duk sanda ya buqata. Ita kuma Nafee yaci gaba da ajiyeta a matsayin matar so ya kuma ci gaba da haquri da halinta domin har yanxu yana sonta,  dan San tsakani da Allah ya ke mata itace dai ta rufeshi.  Dan haka ko gida daya bazai hadata da Nafee ba kartaga irin abunda Nafee take masa itama tace xatayi,  wani gidan zai kama mata haya anan kusa da Nafee.  




Yana kaiwa nan a tunaninsa wani farin ciki ya shigeshi, 😄 harya fara hangosu shi da MARYAM cikin yanayin auratayya.  Yasan xuwa yanxu ta nemi maganin ciwonta na sanyi, sannan kuma gata da qaramin ciki yasan xai shana kwarai dan MARYAM yar baiwa ce ko babu ciki bare da ciki. Sai yanxu yaji yana son cikin jikinta kuma yanason ganinta da cikin yasan cikin zaiyi mutuqar kyau ajikinta dan komai nata me kyau ne (Dan rainin sense 😏) da wannan tunani bacci ya daukeshi cike da mafarkin MARYAM wanda ya kaishi ga wanka.




Ganin kansa a jiqe yasa Nafee fallara masa harara, tace ina ruwan dan anace mafarki kai kenan?  Bai kulata ba saboda  bayason ta bata masa mood,  dan daga masallacin asuba gidansu zai tafi gurin Abbansa suje bikon MARYAM. 




Mrs 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 3⃣2⃣


Dedicated to 

Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)




Bakwai saura kwata (6:45 AM) a gidansu tai masa. Yasha shadda fara sol yar ciki da babbar riga, ya dankwafa hula kamar kansilan qauye.  🤣




Har cikin dakin Abbansu ya shiga, ya samu Umma tana hadawa Abban shayi. Ya tsuguna har qasa ya gaishesu, Abba ya gama shirinsa tsaf da alama fita xaiyi.  




Badaru ya qara sunkuyar dakai cikin sigar neman alfarma yace "Abba dama nazone dan Allah muje mu dawo da MARYAM,  Na janye sakin da nayi mata. Naga gara ta dawo mucigaba da xama ta haihu a dakinta, na huce da fushin da nake da ita."  Umma ta ware ido tace 😳 au dama MARYAM din ciki gareta amma ka saketa?  Kuma shine baka taba fada ba?  Wannan yaro ka jawo mana abun kunya wlh,  ai da munsan da ciki da mun dunga xuwa dubata."  yayi dan murmushin alamun samun nasara yace "Umma kuyi haquri lokacin rainane a bace shiyasa ban fada muku ba."  tace " eh ai yayi kyau hakan,  yaro yarone, yaro bakasan wuta ba saika taka.  Yanxu kuma da xaka dawo da ita ka manta da xagin naka da kace tanayi? Ka sheqa kaji babu kwaya kenan.Hmmm to wlh bakayi  

daya ba kaji dadi duk randa ka kuma sakin wata mace bama MARYAM ba daga ranar ka canja uwa domin ni bazan xama uwar mai auri saki ba"




Abba yayi gyaran murya yace "tunda dai yayi kuskure kuma ya gane kuskurensa shikenan,  kuma itama MARYAM din nasan yanxu tayi nadamar abubuwan da tayi masa. Yanxu xanje Dawaki daurin aure amma in shaa Allahu bazan kai sallar juma a acan ba.  Yanxu xanje insamu kawunka in fada masa,  inyaso ina dawowa daga masallaci sai mu wuce dashi muje gidansu MARYAM din."




Badaru ya dunga murmushin farin ciki, sai yakeji a ransa kamar ta dawo ta gama.  Dan haka yace "Abba inaga gobe kawai su dawo da ita,  yanxu xanje inga inda xata zauna acan gurin Nafee kafin in samar mata gida" Abban yace to hakan yayi, bari intashi kar inyi rana. 




Bayan komawarsa gida,  yana kashingide yana tunanin maryam har wani lumshe ido yake inya tuno sweet moment dinsu. Ya gama tsara cewa dakinsa da yake ciki zai bawa maryam din kafin ya samu gida ya sai mata, bazai qara sakinta ba zai zauna da ita saboda buqatarsa.  




Yana cikin tunanin ne Nafee tazo ta dangwarar masa da baqin shayi (lipton) da breadi.  Tace gashinan babu madarar.Bai ce mata komai ba, sai dariya da yake mata a xuciyarsa. Tanai masa kallon biri yana mata kallon ayaba,  domin bazai fada mata xai dawo da maryam ba sai dai taganta.  Ya qudure suna dawowa daga gidansu Maryam din zaije yayo mata shoping na komai da komai ita kadai, Nafee kuwa taji a salansa, dan yagaji da barnar da Nafee keyi masa. 




Kamar yadda Abban Badaru ya alqawaranta tare sukayi sallah da Baffa a masallacin jumaar gidan sarki,  kuma daganan yabi Baffa gida yace suje zasuyi magana me hamimmanci. Baffa dajin haka yasan maganar Komece farinciki ya cika zuciyarsa. Abba tare da qaninsa da Baffa sukaci abinci tare a gidan Baffa.  Kuma dama ga al adar Baffa ranar juma a daga sallar juma a gida yake tahowa baya komawa kasuwa. 




Suna gama cin abinci suka labartawa Baffa maqasudin xuwansu da kuma saqon Badaru na amaida maryam din gobe (kunji fa kamar wata yarsa) harda labarin cikin Mimi sai da suka fadawa Baffa. Babu wani nuna ja ko tauna tsakuwa dan aya taji tsoro ko kuma tsawatarwa dan kar Badaru ya kuma yin saki anan gaba Baffa ya yadda da komen maryam gidansa (dan Allah ku duba inda ake wulaqanta ya mace. Ba dole namiji yayiwa mace wulaqanci ba dan yasan inma ya saketa bazai sha estalar dawo da ita ba) suka sha hirarsu cikin nishadi ya basu tabbacin gobe ana magriba A dar uma yaxo ya dau maryam su tafi. 




Suna tafiya Baffa ya shiga gida,  a lokacin qarfe uku na yamma.  Tunda tsakar gida ya dunga kwallawa mama da Mimi kira,  har ya bude parlourn Sá ya shiga bai fasa kiransu ba.  Mama ta fito ta bishi dakinsa, yace jeki ki rawomun maryam yana fara a. Taje ta taso Mimi take bacci,  Umma da Anty jin kiran da Baffa kewa Mimi yasa suka fito suka shiga dakin Baffa kamar an gayyacesu. Dan Susan tunda ya kira Mimi watace ta taso dan inba haka ba sai yayi sati bai kirata ba.  Ya jafar ma yanxu ya shigo gidan xuwansa kenan daga kaduna yazo weekend kuma yana xuwane saboda Mimi, jin kiran da Baffa yake mata yasa ya tsaya daga gefen kitchen kusa da dakin Baffa dan yaji dalilin kiran, babu wanda ya lura da xuwansa. 




Baffa ya kallesu,  Umma, mama, Anty sai kuma Mimi dake gefe daya.  Ya fadada faraarsa tare da cewa "ALHAMDULILLAHI,  Allah ya sani tunda abunnan ya faru nake adduar Allah ya sa a daidaita, to Allah maji roqon bawa yanxu Alh Inuwa da qaninsa suka xomun da xancen mayar da auren maryam da Badaru.  Domin shi Badarun da kansa yau yace ya janye sakin ta koma dakinta. Dan haka maryam sai ki hada kayanki gobe zaizo da almuru ya daukeki, basai nace miki komai ba in aurenki ya kuma mutuwa karki dawomun gida"




Mimi ta kwalolo 👀, jin abunda Baffa yace wai Badaru ya maida ita.  Ta juya ta kalli da nufin mama tayi magana, domin ita bazata iya cewa da Baffa ta gama iddah ba.




Ai kuwa mama ta magantu "Alh wani irin kome kuma?  Ai aure ya qare, tunda yau kwanan Mimi 6 da gama iddar Badaru." 




Baffa ya dakawa mama tsawa tare da cewa "Faduma karki kawomun zancen banxa mana,  yarinya da akace tana da ciki itace xakice ta gama idda?"



Mama ta hade rai cikin shirin ko ta kwana😡. Umma tai saurin sa musu baki a maganar da cewa "a ciki kuwa akwaishi dan ko mu munsan dashi, sai dai in Faty ce ta jagoranci " maganar ta katse a dalilin hararar da mama ta watsa mata.  Abun ya bata mamaki domin ko da wasa mama bata taba harararta ba,  dan haka yau da taga fadiman na shirin canjawa taja bakinta ta tsuke saboda kar girmanta ya xube. 




Baffa shima ganin mama tayi fuskar shanu tana hararar Umma yasa ya bar maganar ciki. Yace "to shikenan ai duk da haka akwai mafita bara in kirawo Alh inuwan suxo da daddare a daura aure ya wuce da matarsa"




Mimi da mama suka kalli juna a razane. Mimi ta dago kanta cikin dakiya tace "Baffa karka kirawoshi,  nikam nagama auren Badaru in shaa Allah,  Allah ya hada kowa da rabonsa na alkhairi"




Baffa ya taso mata cikin hargowa yace "ke ki kiyayeni kuma aure dole ki koma,  kina zaton akwai wanda zai aureki inyaji abunda kika shukawa tsohon mijinki ya sakeki a wata 5? Kinsa ana zagina a gari kamar ni ace inada bazawara a gidana? Kin batamun record din gida.  Saboda haka dole ki koma gidansa ayau basai gobe ba"




Ba tare da wani shayi ba ko shakka, domin xuciyarta ta gama bushewa.  Ta dago kanta tace "Baffa bazan koma ba wlh,  saboda ni kadai nasan irin wahalar da nasha a gidansa"




Baffa ya dauketa da wasu irin maruka guda 2, tare da cewa "ni xance kiyi abu maryam kice baxakiyi ba? Lallai na yadda Badaru yayi haqurin zama dake.  Kuma wlh sai an mayar da aurenki ayau, inyaso ni dake aga wanda ya haifi wani"  




Idonta jajur saboda zafin marin da Baffa yayi mata, ta kuma dagowa ta kalleshi tace "wallhil azeem bazan koma gidan Badaru ba,  da inkoma aurensa gara inshiga duniya." 



Umma da Anty dake gefe suna kallo tun abun na burgesu har ya koma basu tsoro, suka kwalalo ido dan yau Mimi ta shayar dasu mamaki. 



Baffa kuwa baiyi wata wata ba ya tashi yasa hannu ya rufe mimin da duka kota ina. Nan take kuwa jini ya fara fita ta hancinta wato habo. Mama ganin jini na xuba a hancin Mimi ta runtse ido,  xuciyarta na tafasa tana kai kawo.  Mimi kuwa duk dukan da Baffa ke mata bata fasa fadar "wlh ko kasheni xa ai bazan koma gidansa ba" Baffa yaje ya ciro wayar receiver ya nufi Mimi da niyyar sake dukanta dan yagaji da dukanta da hannu, yana cewa "to ayau kuwa xaki barmun gidana bayan na gama fasa miki duk jikinki da duka dan ban haifi dan da zai fada in fada ba"



Mama tai saurin tashi tasha gabansa (ta shiga tsakaninsa da Mimi) tare da cewa Alh Buhari karka qara dukarmun ya, domin baka tayani naqudar kawota duniya ba.  Haka kawai kasa marainiyar Allah a gaba sai jibga kakeyi kamar kana dukan namiji dan uwanka. Ai ko musulunci bai baka dama kai mata auren dole ba a matsayinta na bazawara"




Umma da Anty dake gefe abun ya basu mamaki kwarai,  Anty ta kasa haquri ta miqe tare da cewa "amma kam kedai fadima baki da kunya baki da kara, yanxu sunan mijin naki kike ambata tare da yi masa tsawar ya daina dukar miki ya? Ai ab" kafin ta qarasa abunda tai niyyar fada mama ta dauketa da mari, tare da nunata "👉🏼 ke! Na kasa dake balle ki dauka?  Da wanda ya ajiyeki nakeyi" Anty da tasha mari ta dafe kunci tana kallon mama cikin kidima, Umma kuwa nan take ta kuma shiga taitaiyinta. 



Mama ta maida kallonta ga Baffa da ke tsaye nayi mata kallon mamakin abunda takeyi taci gaba da cewa "ni har a fadamun kara akan yayana?  Nagaji nagaji da abunda kake jagorantar matanka kukemun haqurina ya qare.  Kuma yau na tabbatar da AL AMIN baya duniya, domin da yana raye da ko cikin shege maryam tayi zai karba ya rufa mata asiri.  Duk cikin yayanka wa kayiwa auren dole?  Sai yata, saboda qasa ta rufe idanun ubanta ko?  Nagaji da abunda kakemun nagaji da wariya akan yayana,  ai koda ace ba yayan dan  uwanka bane kayimun kara.  A karatu ka fifita yayanka akan nawa,  a wajen tarbiya da nuna soyayya ka fifita naka akan nawa,  a wajen aurar da yayama salon auren yayanka daban da nawa,  sannan ka debi yayanka ka dunga kaisu saudia kabar nawa, to shin ubansu bashi da gado a dukiyar da kake facaka da itane ko kuma sudin shegu ne?  Duk abubuwan da kakeyi ina sane kuma ina ganewa domin ni ba mahaukaciya bace kamar yadda kuke xata.  Sannan akan wani banxa Badaru ka mayarmun da ya baiwa me aikin gidanka,  sannan kuma yanxu kana nema kasa yata ta shiga duniya saboda Badaru? Shin wai maryam yar dan uwanka ko Badaru?  To tunda kana qaunar Badaru ka dauki daya daga cikin yayanka ka aura masa. Tunda anyi ruwa qofar dakin kowa ta jiqe (ma ana kowa yana da yaya) duk cikin yayanka wacece take maka biyayyar da Mimi take maka? Amma duk da haka kafi tsanarta kafi wulaqantata bansan abunda ta tsare maka da kai da yayanka da matanka ba kun tsangwamarmun ya kun takurata, to wlh duk wanda ya qaramun abunda bai gamsheni ba akan yayana sai yaga tashin hankali. Ko kasan cewa akan takurar da kaiwa Mimi har yunqurin kashe kanta tayi? To wlh Buhari duk randa maryam ta kashe kanta saboda takurar da kake mata wlh sai nayi sharia da kai daga nan har kotun duniya. Kamar yadda kasha fada kuma kake nunawa a aikace cewa Mimi ba yarka bace to yau na tabbatar maka cewa FATIMARYAM ba yayanka bane yayan AL AMIN da FADIMA ne.  Saboda haka na yanta yayana daga barin yi maka bauta. Abu na qarshe dazan fada maka shine : kamar yadda kace Mimi tabar gidanka xata bari,  amma ni da ita xamu barmaka gidan tare domin saboda su nake zaune a gidannan inkuma ankore su banga xaman da xanyi ba." 



Ta juya ta kama hannun Mimi tare da cewa "taho maryamu daga yau na yanta ki" Baffa yayi sakato kamar an dasashi jikinsa yayi mugun sanyi  wata irin kunya wacce bai taba zato akwaita ba yakeji. Ashe duk abunda yakewa fadima tana sane? Lallai ya dade yana zaluntar wannan baiwar Allah da yayanta, yau ta fada masa abunda bai taba tunani ba kuma shi kansa baisan hujjarsa ta nuna banbanci tsakanin yayansa da yayan dan uwansa Al amin ba.  Lallai mai haquri bai iya fushi ba yau fadima ta zame musu horo, yasan tabbas abunda ta fada gaskiyace tsantsan duk yayansa babu mai masa biyayyar da Mimi keyi masa kuma babu wacce yayiwa auren wulaqanci irinta. Kuma wlh baisan abunda yasa yakewa Mimi haka ba, kuma yasan da Anty ko Umma yakewa yayansu abunda yakewa Mimi wlh da sai anyi yaqin duniya na uku. Muryarsa a tausashe yace da mama dake shirin fita daga parlourn "ban baki izinin fita daga gidannan ba daga ke har maryam" Umma da Anty suka kalleshi jin abunda yace suka jinjina kai.  Domin sun dauka zai saki fadima ne nan take, da daya daga cikinsu ce da tuni ya sender ta gida.




Mama na fitowa daga dakin Baffa ta tsugunar da Mimi a bakin fanfo da nufin wanke mata jinin daya bata jikinta.  Jafar da ya gamajin abunda ke wakana yayi saurin xuwa kitchen ya dakko mata ruwa a freezer ya miqa mata, ta karba ta wankewa Mimi fuska dashi.  Nan take habon ya tsaya, taja hannun Mimi suka shige dakinta. 



Jafar ya furta "jarumar uwa" ta jure abubuwa da yawa akan yayanta sannan lokaci daya ta kwatarwa Mimi yancinta.  Ya dunga farin cikin jin Mimi ta gama iddah yace "in shaa Allah maryam matata ce"




Har magruba tayi mama bata fito ta dora girkin dare ba duk kuwa da cewa ita ke da girkin. Anty ta samu Baffa har daki yayi tagumi tanayi masa mitar cewa,  mama bata dora girki ba mai zasu bawa yara suci?  Ya dago ya kalleta yace "ku masu yaya bakuje kun girka kun basu ba sai ita me ya guda daya? Saboda haka karku dameni" Anty ta ruqe haba cikin ranta na jinjina soyayyar fadima a gurin Baffa,  wato duk abunda tayi batai laifi ba kenan? Har marin da tayi mata 🤣. Ala tilas taje ta dora jellof din taliya dan lokaci ya qure kuma itace me qananan yaya. 



Bayan ta gama ta hana kowa sai Baffa kawai ta xubawa ta kaima masa daki,  shi kuma ya tambayeta da cewa kin kaiwa fadima? Ta harzuqa tace "aini bata shanye ni ba kamar yadda ta shanyeka ba, saboda haka ban kai mata ba dan ba xamanta nake ba.  Ana cikin hakan Umma ta shigo tana tambayar Anty ina nata abincin?  Tace nima dafawa nayi ni da yayana kema kije ki dafa dan ba baiwarku bace ni.  Umma tace dakata karkiyimun fitsara inba haka ba yanxu in wanka miki mari dan naga sai anmareki kike samun nutsuwa 😂. Anty da jin haka ta harzuqo suka fara cacar baki ita da Umma.  Baffa ya katsesu da cewa ko suyi shiru su bashi guri ko kuma kowacce ta tafi gidansu.  Anty ta cije lebe da cewa ai dole kace mu tafi gida,  ita wacce  ta qare maka zagi daxu ai ta kwana lfy saboda ta iya bun malamai. 



Daya fita sallar isha ya biya ya siyowa mama da Mimi qatuwar kaza da fura roba biyu, jin cewa ba a basu abinci ba. (lallai mama ta motsa kwanji 😄) ya shigo Anty na alwala a tsakar gida kuma taga ledar daya shiga da ita dakin mama.  Har ta miqe xata bishi sai ta tuna marin da tasha daxu dan haka ta koma ta xauna.



Yasameta xauna akan kujera ita da Dady suna kallon mbc 3 Mimi kuma tana kujera zaman mutum daya da digital casbaha a hannunta tana dannawa.  Baice musu komaiba sai ajiye ledar da yayi kan qafar mama ya fita.  



Dimin da taji shiya tabbatar mata abinci ya kawo musu,  kuma dama shiri take ta tashi ta samar musu abunda xasuci.  Dan yau jin ranta take sawai,  abunda yake ranta shekara da shekaru yau ta amayar dashi.  Dan haka ta dakko musu faranti da cups sukaci kazar suka sha fura suka qulle dakinsu suka kwanta,  daga ita har Mimi basu garka ba sai asuba sun sami bacci me nauyi. (dole tunda anraba xuciya da damuwa)



Mrs

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 3⃣3⃣


Dedicated to 

Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)




Baffa kwana yayi yana tunani,  haqiqa yayi kuskure yayiwa fadima abubuwa da yawa kuma babu wanda ya taba fada masa yayi ba daidaiba.  Tabbas yaci amanar Al amin,  yayansa kwaya biyu yakasa hadawa cikin nasa yayan ya rike.  Kuma dole su Faty sunada gado a dukiyarsa domin tunda Al amin ya mutu ya tattara abunda yabari ya riqe,  ko mama bai sallama ya bata tumunin takaba.  Su bai basu dukiyarsu sun mora ba su baiyi masa da tasa ba.  Dole zaisan abunyi akan dukiyarsu,  ko bebawa su Faty tasu ba dole zai sallami mama da tumuninta.




Ta bangaren Mimi kuwa,  baisan dalilin tsanar da yayi mata ba.  Amma yasan akwai tagomashin matansa wadanda Kullum cikin kawo masa sukar Mimi suke.  In yayi kallo xuwa hallayyar yarinya sai yaga yarinyace sassanya wacce ko acikin gida ake hira da wahala kaji harshenta, sai dai in anyi abun dariya tayi.  Gata da kirki da qarfin xuciya,  duk da bata cika lfy ba Kullum xaka sameta cikin aiki ko a tsakar gida ko a dakin uwarta.  Bata da qashin cewar bazatai aiki ba saboda akwai yan aiki a gidan kamar yacce yayansa keyi.  In kuma yanason ai masa abu misalin gyaran daki ko wani aiki to Mimi yake sakawa domin tana tsayawa ta yishi babu hainci wanda ko matansa basu iya yimasa shi tsaf kamar nata.  



Dan haka ya fuskanci xuga ce jigon tsanar da yakewa Mimi,  sai kuma issue din rashin aurenta da wuri wanda ya dauki hakan iya shege.  Dole ya kawo canji domin yanason fadima kuma bazai iya rabuwa da itaba,  yanxu gashi tana shirin rabuwa dashi saboda Mimi. Nan take yaji rabin tsanar da yakewa Mimi ta tafi. Afili ya furta Fadima nagode da kika karantar dani kuskurena da wuri tunkan in mutu Allah ya kamani da haqqin xumunta dana marayu.  Kuma daga yau xan sakarwa yarki mara tayi irin rayuwar da take so. 



Lokacin da yafito domin tafiya masallacin asuba ya kirawo masu aikin gidan  yace su karbi aikinsu yau sannan ya fita. 



Mimi kuwa bayan ta iddar da sallar asuba ta gaida mama,  mama tace mata kije kiyi registration din tafiya service din yau.  Mimi tayi rau rau tace " mama ai anrufe sun kusama tafiya camp domin har call up dinsu ta fito" mama tace to kiyi haquri haka Allah ya shirya kaje wata shekarar"

Anan kitchen din cikin parlour suka hada break fast sukaci,  domin mama ta quduri aniyar kwatar yanci. Tunda ya hanata tafiya ai sai tayi yajin a dakinta.



Badaru yadda suka kwana da Nafee jiya yauma haka suka kwana,  domin shima ya bar mata abunta yace ta jiqa tasha.  Aransa kuwa cewa yake ni da xan kwana da maryam yau dan anhanani wannan ruwan daurayar ai ba wani abu bane.  




Wajen qarfe goman safe yaje gidansu,  dake asabar ce kuma basa fita kasuwa weekend da wuri duk ya samesu a parlour.  Har Badamasi da yazo weekend. 



Ya zauna ya kwashi gaisuwa gurin iyayensa,  ya juya suka gaisa da Badamasi sama sama domin Badamasin yanxu yake samun lbrin saki da kuma maida maryam da Badaru yayi sannan da zancen auran da yayi.  Dan haka yaji yayi mugun tsanar Badaru sabida maryam. 



Badaru ya kalli Abbansu yace "Abba inaga da yamma xanje in dauko maryam din,  saboda inason inkaita store tayi shoping din kayan abincinta da kanta inyaso sai mu wuce gida daga can" 



Abban yace to babu laifi,  bari na fadawa Alh Buharin saboda karkaje bata kimtsa ba" Umma dake gefe tana murmushi aranta taji dadi ga dukkan alamu Badaru ya gane mahimmancin maryam, dan haka tace "Alh ai da ya kira maryam din da kansa yace ta shirya da wuri zaizo da yamma" 



Badaru ya sunkuyar da kai cikin kunyar abunda xai fada yace "ai bani da lambarta" babu wanda yace masa komai sai Badamasi dake watsa masa harara kamar ya tashi ya dakeshi. 



Abba ya ciro wayarsa yace bari na fada masa da kaina. Lokacin da kiran Abba ya shigo Baffa na xaune yana karyawa Umma na gefensa ga dukkan alamu itace tayi girkin tunda mama tayi bore. 



Ya daga suka gaisa,  har yanxu jikin Baffa a sanyaye yake.  Abba ya fada masa buqatar Badaru.  Baffa yace "ai Alh inaga sai dai mu haqura domin yarinyar har ta gama iddah, kaga babu maganar kome kenan?"



Abba dajin abunda Baffa ke fada yasa wayar a hands free domin Badaru yaji abunda Baffa yace.  Abba ya maimaita abunda Baffa yace "ta gama idda?" Baffa yace "eh"



Badaru ya dafe qirji yace "to cikin jikinta fa?  Xubarwa tai?" Baffa da yaji abunda Badaru yace saboda hands free din da aka saka yace "ita dai tace babu ciki kuma iddarta ta cuka tun kwana 6 baya" 



Abba yayi saurin cewa "to ai abun bai baci ba har yanxu,  tunda yayi nufin maidata sai mu kawo sadaki in anjima a maida auren" Badaru yayi saurin gyada kai cikin gamsuwa da abunda Abba yace"



Sai dai muryar Baffa ta katse masa hanxari inda yake cewa "Alh sai dai muyi haquri inaga iyakacin xaman da Allah ya rubuta musu kenan, domin nima na kawo batun maida auren maryam ta nuna bata da raayin kuma xama dashi dana takura sai anmaida auren adalilin hakan nima xaman lfyar gidana ya tabu,  domin uwarta tace baza a kuma yiwa yarta auren dole ba har tana barazanar dauke yarta su barmun gidana.  Ni kuma inason matata kaga garin gyara kuskuren Badaru aurena zai mutu,  gara kawai a haqura." 




Abba ya kashe wayar cike da jin haushin Baffa, yana mitar kamar Buhari ya zauna mace na juya shi?  To kada Allah ya sa maryam din ta dawo,  metafi Badarun ai Badaru ba illah ce dashi ba babu inda xaije neman aure ba a bashi ba (kuji san kai?)  



Badaru tunda ya gama jin abunda Baffa ya fada gabansa ya yake ya fadi,  qirjinsa ya dunga bugawa sai yanxu ya tabbatar ya tafka kuskure.  Tabbas yasan maryam bata sansa,  wlh da yasan haka xata kasance da bai saketa ba.  Ta xubar masa da cikin da yake ganin shine tsanin da xai dunga hadasu. Umma kuwa hawaye takeyi jin maryam ta bar xuriar ta, tasan Badaru yayi rashi.  



Badamasi kuwa dake gefe fuskarsa a washe sai murmushi yake.  Ya dunga godewa Allah a xuciyarsa,  yace lokacin aurena yayi, maryam ta dawo.  Jin fadan abba yaqi qarewa kuma Abban baya blaming kowa sai Mimi,  shiyasa ya matsa gaban Abban,  baice komai ba sai wayarsa da ya ciro ya kunna recording din da ya tabayi wanda Badaru ke tsagin Mimi da korarta daga gidansa.  Yace Abba ku saurari wannan"




Sukayi tsit har Badaru suna sauraran recording din harya qare sannan Badamasi ya dora musu da sauran abunda yagani na zamantakewar auren da kai Mimi asibiti da yayi da kuma abunda yakeji lbr gurin abokan Badaru. 




Jikinsu yayi mugun sanyi, Umma kuwa kuka take tana kallon Badaru a razane.  Ta kalli Abba cikin kuka tace "Alh kaji abunda nake fada maka ko? Kake goyon bayansa,  wlh nasan sharri yayiwa yarinyar nan,  ai dole tace baxata xauna dashi ba saboda ya azabtar da ita,  inma cikin ne ai baqin cikinka ma ya isa ya xubar da cikin.  Kuma wlh indai nadama ce baka fara ba,  ka cuceni ina qaunar yarinyar nan ka rabani da ita"  ta qara fashewa da kuka.  Abba ma ya kalleshi yace "baka cuci maryam ba,  ba kuma ka cuceni ba kanka ka cuta.  Na yarda da kai kasa ina jin haushin yar mutane ashe kaine babban dan iska,  sabida haka kajira sakamako wlh sai Allah ya saka mata"




Badamasi ya matsa kusa da qafar Umma ya riqo hannunta yace "Umma share wahayenki,  baki rabu da maryam ba,  maryam xata dawo cikin xuriar ki kuma a matsayin surukarki,  domin xan auro maryam.  Idon kowa a gurin ya dawo kansa.  Yaci gaba da cewa tun farko ni naga maryam, ni na fara sonta,  ni nafara yi mata magana.  Ina shirin inje innemi soyayyarta Badaru yazowa Abba da maganar aurenta ganin haka yasa na haqura,  amma wlh da nasan Badaru haka zai maltreating maryam wlh bazan haqura in bar masa ba.  Saboda haka Umma ban taba neman abu a wajenku ba yanxu nazo da alfarmar neman goyon bayanku akan neman auren maryam,  ba haram bane dan Allah ku kauda kai a magoar mutane ku goyamun baya." 



Umma ta share wahayen farin ciki,  ta shafa fuskar Badamasi tace "na baka goyon baya 100%, nasan bazaka wulaqanta maryam yanda Badaru yayiba Allah ya sa rabonka ce"  ya juya gurin Abba yace "Abbana inkace in haqura xan haqura"  Abba ya kalli Badamasi a nutse yace " na baka goyon baya likita,  indai har kun daidaita kanku da kaina xanje gurin Alh Buhari a karo na biyu in nai mar maka aurenta" ya dunga godia yana dariya ji yake indai Mimi ta amince nan da 2 wks xa ayi komai a gama.  Yau yana da daurin auren abokinsa a Danbatta amma gobe in shaa Allah zaije su gana. 




Badaru da tunda Badamasi ya fara magana yake kallonshi har ya gama,  ya tashi idanunsa jajur da tsabar kishi ya tari gaban Badamasi cikin sigar rigima yace "oh dama ashe san maryam kake?  Shiyasa ka hure mata kunne ta ciremun ciki ta gujemun sannan ka nado sirrinmu ka kawo ko?  To wlh baka isa ka auri maryam ba indai ina numfashi,  kai ko kunya bakaji ka auri tsohuwar matata? Ban taba neman abu na rasa ba, na auri maryam da farko kuma yanxu ma xan kuma aurenta domin wlh saina kasa ka,  ka rubuta ka ajiye,  inkuma ban aureta wlh sai dai ayi biyu babu kowa ya rasa."



Badamasi yaja da baya ya kalleshi yana dariya yace "ka saba yiwa kanka kirarin duk abunda ka nema kana samu,  amma inkasamu baka iya alkinta abun,  kaga kodan haka Allah xai iya jarrabarka,  saboda haka maryam dai yanxu rabonace in shaa Allah gara kaje ka lallaba kucakar matarka ku zauna lfy.  Kuma ni bazan fada da kai ba domin yau cikin farin ciki nake dan haka kaje ka nemi irinka looser  kuyi " 



Badaru yakai masa duka Badamasi ya tare tare da cewa kasan in dambe xamuyi wlh karyaka xanyi ka wani tara teba sai kace me ciki.  Abba ya daka musu tsawa tare da ja musu warning.  Kowanne ya fita yana hararar dan uwansa.  Umma tace "Alh baraka fa xata bullo idan bamu tashi tsaye ba"



Abba yayi shirin fita kasuwa ya leqa dakin Badamasi yace "Bani wayarka ka saitamun gurin maganar nan, gara insami Alh Buhari in wanke yarinyarnan a gurinsa." Badamasi ya bashi wayar tare da bude masa recording din,  yana xuwa play kawai xai danna. 




Baffa naganin Alh Inuwa a shagonsa ya hade fuska,  don a xatonsa xuwa yayi ya qara neman alfarmar mayar da Mimi.  Amma sabanin haka sai yaji yana bashi haquri tare da neman itama Mimi abata haqurin, kana ya budewa Baffa recording din ya saurara.  



Baffa yayi matuqar tsorata da lamarin Badaru,  ya kalli Alh inuwa yace " kace dan iska ka kawomun cikin manyan kaya ni kuma banyi bincike ba na dauki salihar mace na bashi" Alh inuwa yace "wlh Alh bansan abunda Badaru ya aikata ba kenan, shiyasa na kawo maka abunda yayi kaji.  Amma dan Allah kayi haquri  kuma ka bawa maryama haquri babu hannuna a abunda aka aikata mata kuma wlh da nasan haka zaiyi da ban nema mishi auranta ba"  Baffa yace " shikenan nagode da sanar dani da kayi shi kuma ya je dan kansa ya cuci marainiyar Allah"



Baffa yayi sakato yana tunani,  lallai ya tafka kuskure a baya.  Ya dauki ya yabawa dan iska yana zaginta da goranta mata,  amma kuma duk abunda Badaru yayi bashi da laifi, shine babban mai lefi da bai riqe su da daraja ba kuma ya nuna maryam din ba wata bace.  



Tausayin Mimi da soyayyarta ta dirar masa nan take,  dole Mimi tace bazata koma gidan Badaru ba saboda ya zalunceta sannan ya biyota da sharri shi kuma ba bincike yahau ya xauna.  Jin soyayyar Mimi yake har cikin bargonsa kuma yaji yana kunyar hada ido da ita da uwarta. 




Badaru na zuwa gida ya samu Nafee a parlour tana kallo, ya kalli parlour komai kaca kaca ya kalleta da yake a kusa yake neman masifa yake sai yace "ke haka ya dace kibar guri ki xauna kina kallo dake ke jaka ce?"



 Ta kalleshi sheqeqe tayi dariya tace " jakai dai,  ni da kai in ban gyara ba kai baka da hannun gyarawa?"  kafin ta ida fada ya kifa mata mari.  




Batai wata wata ba ta dakko plate din da ta gama cin indomie yanxu ta jefa masa tana huci, sannan ta dora da cewa "ga dukkan alamu ka saba ganin tsohonka na jibgar gyatumarka shine kazo xaga gwada a kaina,  to wlh duk randa ka qara dukana wlh saina sake maka kaciya 😳"




Ya tsorata da mutuqa da maganar Nafee,  bece uffan ba ya shige bedroom dinsa,  ya rasa abunda yake masa dadi.  Shi yanxu yasan duk wanda ya fadawa abunda Nafee ke masa dariya zaiyi saboda yacce ya daukaki Nafee.  Ya dunga juyi akan gado ya kasa bacci,  har akai sallar laasar bai fito ba ga yunwa na addabarsa kuma yasan Nafee yau bazata bashi abinci ba.  Ya tashi yayi wanka yayi sallah,  ya zabo kayansa na qure adaka yasa.  Gurin maryam xaije ya bata haquri ya nemi yafiyarta,  yasanta da sauqin kai xata haqura su koma aurensu. 



Ya samu Nafee zaune ta cokala dauri ture kaga tsiya tana sanaar (kallo), ya tsaya domin yayi mata magana,  ta dauki remote ta qure volume alama batason jin abunda xaice, dan haka ya fice. 




Ya dade a qofar gidan Baffa babu dan aike kuma bashi da no Mimi. Mimi ta fito domin zuwa gurin fauxa,  tana sawo kai waje idonta cikin na Badaru gabanta ya yanke ya fadi ta diririce,  ta juya da nufin komawa gida yayi wuf ya damqe hannunta yajata cikin sit room din dake soron farko. 




Cikani, baka da hankaline xaka riqe mani hannu? "ta fada cikin fita hayyaci.  Ya sassauta riqon da yayi mata, amma still yana riqe da ita karta gudu ya fara magana murya a kwance " maryam dan Allah kiyi haquri nasan na bata miki naci zarafinki na hadaki da iyayenki na tauye haqqinki na kuma toxarta ki. Amma wlh nagane kuskurena abaya na aureki ne dan shaawa amma xaman da mukai da ke nagane kyawawan halayenki da son addininki hakan ya jawo miki soyayya a gurina." Mimi tayi sakato tana kallonsa wai dama Badaru ya iya magana a hankali?  Kuma dama yasan duk abunda yake ba dai dai yake ba? Tambayar da takewa kanta kenan. 



A bangare guda kuma Baffa dake azumi (azumin kaffarar rantsuwar da yayi ta Mimi saita koma gidan Badaru, ya fara yau) ya dawo gida da wuri domin ya kawo salad din da yakeso a kwada masa yayi buda baki dashi.  Yana xuwa soro aci burki dan jin maganganun dake fitowa daga sitroom.  Da farko bai gane mai maganar ba,  amma jin an ambaci sunan maryam ya gane me maganar da inda maganar ta dosa.  A fili yace lallai wannan yaron bashi da kunya bari inje inyi masa tsakani da yata. 




Sai dai muryar Badaru ta katse masa hanxari inda yaci gaba da cewa "maryam ki tunano rayuwar auratayyarmu me dadi 🙈, ke bakya tunawa? Wlh kullum cikin kewarki nake da mafarkinki,  ki dawo muje mu zauna duk abunda kikeso zan miki   duk yan uwanki na gidan miji ke kadaice kika rage,  kin wuce xaman gida ki dawo dakinki shine rufin asirinki"





Ta katseshi da cewa "xaman gidanmu yafiyemun zaman gidanka,  kuma lokacin da sakeni ka wurgoni kofar gida baka duba cewa na wuce xaman gida ba sai yanxu? Rayuwar auratayya kuma da kake fada kaika santa har take maka dadi,  abunda kawai zan iya dorarwa aciki shine: fyaden da kakemun duk daren duniya.  Abubuwan kuma da kayimun a duk xamanmu na barka da mahaliccinka shi zaimun sakayya." tana kaiwa nan ta fusge hannunta ta kifawa Badaru mari,  kafin ya gama mamaki ta kifa masa wani 😳. 




Ta dora da cewa " yau alqawari ya cika, lokacin daka mareni a gidanka na fada maka cewa wlh saina rama gashi kuma na rama din.  Zagin ubana kuma da kayi kace inje in haqoshi a kabari,  bazan rama ba,  domin nasan darajar iyayena sannan nasan duk daren dadewa naka uban xaije inda nawa yaje.  Gida kuma basai nace karka kuma xuwa ba,  saboda bata dalilina ka fara xuwa gidanba."




Baffa dake sauraransu yayi murmushi cikin jin dadin abunda Mimi tayi yace "yar halak kenan, tayi alqawari ta kuma cika maryam jinin Al amin ce domin ga halinsa nan a jikinta. 


Ta fito ta koma gida memakon gidansu fauxa da tayi niyyar xuwa,  shiyasa bata kula da Baffa ba dake tsaye a qofar fita.  Badaru ya gama mamaki ya jawo qafafuwansa jiki babu kwari yayi hanyar waje,  yaci karo da Baffa. Baffa ya nunashi da yatsa yace "karka kuma xuwarmun gida,  in kuma ka kuma xuwa xan hadaka da hukuma" yana fadar haka ya shige gida.  




Washe gari lahadi da yammaci aka aiko kiran Mimi,  har taqi fita mama tace taje in Badaru ne taxo ta fada mata.  Sai dai me tana fita taga Badamasi a tsaye. Tana ganin mutuncinsa dan haka tai masa iso sit room. 



Ya xauna suka gaisa a mutunce ta tambayeshi mutan gida da gurin aikinsa. Yayi farin ciki ganin maryam din ta fara dawowa hayyacinta ba kamar lokacin da tana gidan Badaru ba, ya dunga hasketa da murmushi yana kuma jinta a xuciyarsa.   Yayi mata jajan mutuwar aurenta,  tace ba komai iyakacin xaman da Allah ya nufa kenan. 



Ya karanto mata abunda ke cikin xuciyarsa,  ta dunga kallonsa a kidime ba tace komai ba ta miqe da nufi fita.  Yayi saurin shan gabanta yace "maryam wlh babu inda xaki sai kin fadamun matsayina a xuciyarki,  inbaki manta ba nina fara sonki Badaru furtawa ya rigani indai ba so kike inyi hauka a kanki ba ki amshi soyayyta" itadai babu baka sai kunne,  domin kanta ya daure da yawa. 



Da yaga taqi magana saiya kamota ya sata a bango yayi mata rumfa da qirjinsa yasa hannu ya katangeta ta inda duk motsin da tayi saita taba jikinsa.  Yakai fuskarsa dab da tata ya fara magana "Mimi ki laluba xuciyarki bazaki rasa soyayyata aciki ba,  ba halinmu daya da Badaru ba soyayyar da nake miki bazata bari in cutar dake ba,  xan kula dake xan baki yancinki,  xakiyi duk abunda kikeso, bazan tauyeki ba irin rayuwar da kike mafarki xakiyi. Maryam fargabar me kikeyi?  Bazan akiyeki kusa ba balle a dunga yi miki surutu,  can gurin aikina xan tafi dake sai dai kixo da yawo." 



Ganin cewa kamar baya cikin hayyacinsa yasa tayi niyyar yimasa dabara.  Dan haka tadan dauke kanta daga fuskarsa,  yayi saurin dawo da fuskarta kusa da tasa har tanajin numfashinsa,  yace "yimun magana a haka in san cewa mafarkina ya kusa xama gsskiya."  tayi qasa da murya tace "kadan bani lokaci inyi tunani inkuma yi istikhara" 



Tunda ta fara magana, ya lumshe ido yana shaqar hucin bakinta.  Sai data gama sannan yace "to shikenan,  xanso hakan nima kuma nima zanje inyi sallatul istikhara.  Saboda haka wani satin xan dawo saboda gobe xan koma Dutse" ya dakko kudin da ya ware zai bata 10k ya lalubi hannunta ya manna mata.



Ta kalli kudin ta kalleshi tace "ai basai ka bani kudi zan soka ba."  ya kalleta hankalinsa ya kuma kwanciya da ita yace nasani maryam amma ai kyauta ce.  Tace "nasani amma ka riqe wata rana ka bani"  yayi murmushin cin nasara yace "to my soul"


Ya nemi ta bashi no dinta tace wayar na gida kuma bata ruqe no dinba,  dan haka ya bata tasa xata kirashi.  Dake ya makance a soyayya be gane cewa wayo taimasa ba,  ba musu ya dakko katinsa na gurin aiki ya bata. 



Mama tayi matuqar kaduwa dajin wai Badamsi keson Mimi,  tace "duk da ba haramun bane ai ana barin halak dan kunya,  kuma naji dadi shine gari.  In shaa Allah ko wanda sunansa ya fara daga BA bazaki auraba. Yazaki qara fita yayi haukansa ya gama"




Ranar litinin ranar Baffa ya dau azuminsa na qarshe,  kuma yau ya shirya tunkarar mama akan fushin da take dashi. 



Da yamma ya shiga har dakinta,  ya sameta xaune a kan kujera Mimi tana kwance tayi pilo da cinyarta tanacin chocolate.  Tana ganinsa ta miqe daga kwanciyar,  mama tace mata Mimi shiga ciki.  Ba musu ta shige bedroom din. 




Baffa ya xauna ya fara da bata haquri akan dukkan abunda ya dade yana yimata da kuma godia akan tunasar dashi da tayi, kana ya dora mata da abunda baban Badaru ya kawo masa yaji a waya da kuma abunda yaji da kunnensa Badaru na fadawa Mimi.  Yace yagane kuskurensa kuma ya canja daga yanxu,  kuma Dan Allah ko anan gaba taga yana nufin kauce hanya a wani abun tayi gaggawar tunasar dashi, domin yagane itadin macen arxiqice.  Sannan yayi mata xancen tumunin takabarta yasa an fitar mata a kotu tasamu gidaje biyu da wajen miliyan biyu (saboda andade ana juya kudaden) ya karbi acct no ta da nufin tura mata kudaden ya kuma danqamata takaddun gidajenta.  



Ya kwallah Mimi kira,  ta fito ta tsuguna. Rayuwa kenan duk wanda yayi haquri zaiga haske domin wai yau Baffa ke neman yafiyar Mimi da kuma bata haquri akan abunda duk ya faru a baya.  



Mimi tana hawaye tace "komai ya wuce Baffa,  kai ubanane duk duniya bani da wanda ya fika,  nima ka yafemun abunda nayi maka rannan saboda bani da xabi sai hakan shiyasa nayi" yace baki komai ba MARYAMU  Allah ya miki albarka ya baki abokin xama nagari sakamon biyayyar da kikaimun. 



Mama na gefe na share hawayen farin ciki,  ta dunga godewa Allah.  Tace da Baffa nagode da kulamana da dukiya da kayi.  Amma inaganin wadannan ka karba ka riqemun."



Yace "riqe abunki Haj Fadima,  nadai riqe na yayana Faty da maryam kuma suma na rubuta da shedu saboda halin rayuwa, gidajen dai xantsaya a xuba yan haya."  tace to duk yadda kayi nagode.  




Yace " to ai bazan yadda kin huce ba sai kin karbi girki,  ga cefane can nakawo inaso aimun special girki dan azumin nake kuma nadade banci delicious dinki ba."




Mama ta miqe tabi bayanshi tana dariya tace " yau kuwa xakici domin xan tabbatar maka na huce." Umma da Anty da tunda ya shiga dakin mama suke tsaye suna jiran suga abunda xa ai suka qiqim qiqim ganin mama da Baffa tare suna dariya.  Mimi ma ta biyo bayansu da nufin taya mama girki itama tana tata dariyar. 



Mrs 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼

AL AMARIN MARYAM 

🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼



📝FANTASTIC STARS WRITERS 

 {F S W }

 

Writing & story by 

Rahma Muhammad {hajia} 


Editing by

Mmn khairat 😍


 

   Page 1⃣4⃣



     Cike da farin ciki Baffa ya shiga gidan,  gami da kwalawa mama kira tunda daga tsakar gida,  ta fito a gigice saboda Jin kiran farautar da yake mata ta iskeshi daki gami da yimasa sannu da xuwa.  Ya amsa yana washe baki kamar bebe yaga wawan zama (Lol) sannan ya dora da cewa wani abun farinciki ne ya samemu fadima shiyasa ki ganni gida yanxu,  wato yaronnan dan wajen Alh Inuwa shine yaga Maryamu yace yanaso, kuma ga dukkan alamu akusa sukesan auren dan Alh inuwa da kansa yayimun maganar ni kuma nayi dattako nace kawai in sun shirya su kawo kayan aure kawai ayi.  Mama ta kalleshi shagarai tare da daure fuska tace,  Alh wannan wane irin neman aure ne sai kace auren yar tsana?   Daga yaro yaga Mimi yace yanaso sai ace ya fito anbashi?  Ita mimin baza aji raayinta ba?  Kuma banaji ma Mimi tasan maganar domin da tasani xata fadamun, sannan shin kayi bincike akan yaron?  Ko kuma dan ansan mahaifinsa shikenan?  Aure fa in anaso a zauna lfy sai anyi da yardar maauratan,  kuma naga ai bakai da Alh inuwa ne zakuyi xaman auren ba,  yaran ne masu xama  saboda haka inaga ku basu dama su fahimci juna inyaso daga baya insun dai daita kwa shiga lamarin. Baffa dake kallon mama tun da ta fara magana a dage tare da fallara mata harara wacce ita sam bata kula ba,  ya magantu da cewa sai yanxu nasan ke babbar mahaukaciya ce fadima.  Ta miqe tsaye tare da qara daure fuska tamau tace hauka kuma?  Yau kuma nice mahaukaciyar?  Nan da nan kuwa ya dai daita nutsuwar domin ya farga da kasassabar da yayi (ya tuna da fadima yake magana wacce Sam bata daukar irin cin mutuncin da yakewa ragowar matansa, ta nuna masa tasan ciwan kanta dan haka ko fada xai mata yakan tausasa kalamansa)  dan haka yanxu ma sai yayi saurin yin kwana da cewa ai kece naji kina qoqarin yiwa Allah butulci,  shekarar maryam din nawa ana neman miji?  Ba a taba budurwa mai shekarunta ba kaf danginki da nawa,  sai yanxu Allah ya kawo kice ga xance ga magana.  Ta kalkeshi tace ni ba butulu bace kuma ba butulcewa nai ba inaso ne dai a gina auren akan fahimtar juna da soyayya,  amma tunda haka kace shikenan Mimi yarka ce kana da ikon xaba mata miji, Allah ya sanya alkhairi yasa tsohuwar gida ce.  Yawwa yanxu kikayi magana fadima da tun farko abunda kikace kenan ai da ba a tsaya sa insa ba, amin Allah ya yi miki albarka cewar Baffa. 


       Maryam kwance saman gadonta acan hostel na law skul rubda ciki take tana danna system,  qarar Waya ya katseta daga typing din da take a system din, ta tsurawa screen din wayar ido gabanta na dukan 3 3 , tun tana qanqanuwarta ta tashi da tsananin tsoron Baffa da kuma dison qiyayyarsa acan qasan zuciyarta saboda halin ko inkula da yake da al amarinsu, duk da cewa mahaifiyarsu awancan lokacin tana boye musu lamarin baffan garesu kafun su girma su gane,  sai kuma alokacin mama take yawan cemusu halin Baffa garesu ajixanci ne irin na Dan Adam.  Amma AL AMARIN MARYAM na jinkirin aure da kuma takura gami da gorin Baffa akanta yasa dison qiyayyar Baffa ta samu girma a zuciyar maryam wanda takai tayi yado ta zama tamkar bishiya mai rassa,  domin ji takeyi kamar ta raba auren Baffa da mahaifiyarta domin auren Baffa ba abunda ya qari mama dashi sai muzgunawa da gori daga gurin matansa daga gareshi kuma xa a iya kiran abun da yaudara domin kulawar da take kwadayin yayanta su samu inta aureshi basu sameta ba.  Wayar ta sakeyin qara akaro na wajen 4 wanda hakan ya yankewa maryam tunaninta,  tai shahada ta daga wayar.  Ta gaisheshi cike da tsoro da firgici,  ya amsa farai farai tare da tambayar karatunta da kuma lokacin kammalawa,  lamarin daya daure kan maryam tamau,  acikin ranta ta farta Baffa da tambayar karatuna? 😳 first in history.  


         Bayan hakanne kuma ya zayyano mata dalilin kiranta a waya akan maganar Badaru,  sai da ta nutsu kwarai sannan ta gane wadanda yake nufi domin ita tamanta da haduwarsu,  amma kuma tayi mamaki dajin cewa wai har ana zancen qarbar kudi ba tare da sun zanta da wanda ya nuna raayin a kanta ba, (domin ita a zatonta wanda yayi mata magana shike sonta wato Badamasi) amma da yake mama batai musu tarbiyyar ja da maganar Baffa ba sai kawai tace masa to Baffa Allah ya xaba mana abunda yafi alkhairi, yaji dadin furucinta kwarai ya dunga samata albarka.  Koda ta kashe wayar tunani ya cikata to meyasa yaya Faty da mama babu wanda ya mata maganar ko dai suma basu sani ba? Sannan ta shiga wassafa siffar guy din da azatonta shine Badarun,  ta dan tabe baki 😏 tare da furtawa a fili "yayi babu laifi he is handsome " amma ba irin mijin da nake mafarkin samu bane  duk da bashi da muni amma bashi da tsahon da nakeso daga da namiji " 🙈 ta rufe idonta cike da kunya kamar wani yana ganin.  Wannan dare dai haka ta qareshi cikin tunanin irin nata salon neman auren cikin gaggawa wato haka Allah ya shirya mata kuma dama fauxa (wata qawarta yar unguwarsu)  tasha fada mata in Allah ya tashi bata miji in shaa Allah gaba daya zai fito jinkiri zai kawo mata alkhairi,   ta miqe cike da farin ciki da kwarin gwiwa ta dauro alwala ta tada sallah aranta tana cewa ashe nima zanga ranar aurena,  ashe ankusa a daina yimun gorin aure 😊. 

  

        Ranar jumaar data kasance aranar aka karbi kudin auren Mimi da kuma lefe,  da misalin qarfe 2:30 pm Faty ta shiga dakin babarta afujajan, daga gurin aiki take.  Yau dinnan zancen kawo kayan lefen ya isketa daga bakin Ahmad mijinta. Tai sallama danta na fari dady (AL Amin)  wanda yaci sunan babanta yazo da gudu ya rungume qafafunta da yake a gurin mama yake tun daga yaye,  na biyun kuma wato Muhsin dan kimanin shekara 2 tun safe suke gurin mama dashi dame rainonsa.  Ta sunkuya ta sumbaci dady tare da cewa sannu babana,  muhsin ma ya gangaro ta daukeshi tana shafa kansa.  Ta zauna akan kujera gefen mama tare da bawa laure (mai rainon muhsin)  umarnin ta dakko mata maltina a fridge,  da kyar ta ida bari suka gaisa da mama saboda xance na cinta, suka qule uwar daki.  Ta kalli mama da alamar tambaya tace mama wanene mijin Mimi?  Wane irin neaman aure ne wannan bamuji neman aure ba banusan mijin ba sai kawo lefe mukaji da sa rana? 😒 . Mama ta gyara xama cikin hikimar uwa ta gari da sigar lallashi ta kwashe zancen tas ta fadawa Faty sannan ta dora da cewa kuma shima Baffa besan har lefe zasu kawo ba,  shi kudi sukace masa kawai sai gasu da kayan lefe.  Kuma banaso ki dau dumi a lamarinnan tunda baffanku yace yayiwa Mimi maganar ta bada goyon baya kinga hakan ya nuna tanason yaron,  kuma kodan mutan gidannan inaso ku karbi lamarinnan haka Allah ya tsara muyi mata addua da fatan alkhairi.  Tace to mama ai tunda kince mimin tanaso shikenan 😊 dama ni banaso a danne haqqinta ne,  yanxu ina kayan lefen?  Suna can dakin ummanku.  Ta miqe ta nufi dakin Umman, tanasa qafa a falon ta fara cin karo da cosmetic din kayan lefen alamar angani duk an watsar ba a gyara ba. Umman na ganin Faty ta dan saki fuska da yake makira ce tare da cewa a a Faty har kin qaraso?  Tace eh suka gaisa tare da yiwa juna murna akan auren na Mimi, ana cikin hakan ne anty ta shigo baqin cikinta sam be boyuba akan fuskarta,  ta kalli Faty tare da cewa sai kuma kikaji abu babu zato?  Ai bana dai yan kwantai sai aure suke,  Faty da maganar ta bata ranta tayi murmushi da cewa aishi aure lamarine na Allah in lokaci yayi sai kikaga duk hassadar mutum sai anyi kuma sai kiga duk dadewarka babu aure abun ya zama tarihi.  Ta fada tana duba kayan Anty da taga Faty ta dagota sai tai saurin sakin zancen tare da kama wani gadai lefenan akwati 4  da kit ne kaya kala 30, takalma qafa 5, jaka guda 3, 

 Sai mayafai 6. Kodan gold qaramin Set babu,  babbar atamfa a cikin lefen itace cote d voire,  leshi bafi tsada acikin kayan kwanaki  Safna (yar antyn ce)  ta saimun irinsa a gurin aikinsu biya 2 8k  kinga a kasuwa baifi 6k  kenan? Ai wlh a tarihin gidannan ba a taba matsiyacin lefe irin wannan ba, wai lefen mai kwalin degree a hannu kenan ta qarasa fada tare da sheqewa da dariyar mugunta 🤣, sannan ta dora da cewa ana cewa jinkiri na kawo alkhairi ni dai banga alamun alkhairi ga wannan auren ba nashaji ana cewa in guga ya dade a rijiya yana jawo ruwa tsullum amma shikam gugan gidannan yayi shekaru aru aru a ruwa ya dago fayau.  Faty ta dago tai qayataccen murmushi cikin qoshi da ilimi da wayewa tace "mashaallah kaya kam sunyi mu sun ishemu haka duba da babu irin tufar da Mimi bata saba indai a duniya take kuma da kudi ake siyanta, to kinga kuwa indai ka saba saka sutura me tsada ai ta lefe baxata dameka ba,  kuma ai lefe bashine xaman aure ba mu alkhairin abun muke nema,  kuma bamusan arxiqin da Allah ya yiwa Mimi ba anan gaba kinga kuwa be dace mu sare tundaga kan lefe ba.  Tana gama fadar haka ta tattara kayan ta maida komai muhallinsa ta dubi umma wacce ke kan kujera tana kada qafa ga dukkan alamu xancen Anty akan Mimi yayi mata dadi domin ga fuskarta nan ta nuna alamar hakan.  Tace Umma Allah ya sanya alkhairi ya kuma kaimu lokacin sannan ta fice . Haka sukaci gaba da shirin biki wanda xa ayishi da zarar Mimi ta gama law skul da sati daya. 




Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼

AL AMARIN MARYAM

🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼 



📝FANTASTIC STARS WRITERS 

{F S W }        


Page 1⃣5⃣



NA RAHMATULLAH (Hajia) 





       Kammaluwar karatun Mimi da kawo IV din bikinta abune da ya kasance a tare,  kuma aranar data dawo ne Badaru yaxo domin suga juna tare da tattauna al amuran biki ( kuji fa kamar auran qauye), da taimakon yaya Faty wacce kullum sai tazo gidan saboda shirin biki  ta shirya kanta cikin atamfar súper wax ja ta yafa mayafi kalar atamfar da dan takalminta shima ja plat, fuskarta tasha make up wanda ya fito da idanunta sukai tar saboda eye liner da mascara da akai amfani dasu wajan qayata idanunta.   Jikinta na tashin qamshin turarurukan companyn Al rehab, domin ita a raayinta tafison Arabian perfume .


           Zaune ta iskoshi a sitroom din gidan,  qamshinta ya fara sanar masa ta iso, ya dago ya qura mata ido tare da hadiye wani irin abu da ya tsirga masa maqogaro ya saki murmushi aransa yana qisima bai taba ganin macen da ta birkita masa hankali ba, idan aka dauki lokaci bai samu maryam a matsayin mata ba tabbas zai iya sabawa ubangijinsa akanta,  duk wani abu da ake buqata ajikin mace maryam tana dashi , wata irin muguwar sha awa yakeji akanta, feelings din dabe taba sanin yana dashi ba akan mace maryam tasa yana jinsa , shiyasa ya yanke shawarar auranta duk da baya sonta kuma baya raayin mace me shekaru da wayewarta,  zai ajeta amatsayin wacce zai dunga kashe qishirwar shaawarsa akanta,  sannan gefe kuma ga burin ransa wato Nafeesa a matsayin matar so.  A bangaren Mimi kuwa tana hada ido da Badaru gabanta ya yanke ya fadi a fili ta furta "innalillahi wa innah ilaihi raju un " saboda tsananin firgici data shiga na ganin Badaru amatsayin mijin auranta nan da yan kwanaki,  ashe wanda take zato ba shi bane?  Ashe ita duk hauka take?  Ashe Badamasin ma da take ganin be cika irin sharadin mijin da takeso ba , ba shine mijinta ba?  Ashe kasan Badamasin ne? Shin meyasa ta dauri kanta ta cewa Baffa ta yarda da mijin da ya bata tunkan taga kalar mijin?  Yanxu fisabillah ina ita ina wannan dan tsamurmurin bafillacen wanda tasan tafi tsaho nesa ba kusa ba???  Tambayoyi burjik ta dunga yiwa kanta a xuci a fili kuma tana hawaye,  wata irin muguwar tsanar Badaru ta shiga xuciyarta nan take.  Badaru da tun daxu yake kallon Mimi cikin mamaki, ya magantu " yanaji da ganina kin furta adduar da sai anga masifa ko abin qi ake yinta? " cikin baqin ciki da bacin rai idanunta jazur ta kalleshi tare da cewa meyasa kaimun haka?  Dan me baka nemi yardata ba ko Jin raayina akanka kakai maganar gurin Baba na?  Wane irin neman aure ne haka?  Ya bata amsa da cewa irin neman auren da addini ya tsara,  batare da tunanin komai ba tace to kasani ni Banasonka wlh 😪  shima cikin nasa sigar bacin ran da tsantsar rashin mutunci yace to nima anfada miki ina sonki ne?  Kawai dai xan aureki ne saboda bani da xabin da ya wuce auran naki,  xancen rashin neman yarsarki kuma sai kije ki tuhumi babanki wanda daga ganin sarkin power yasa miya tai zaqi,  dagaji ance ina sonki yace in fito wanda hakan ya nuna baki da wani sai ni din danake shirin rufa miki asiri shine xakimun iskanci,  wlh maryam bani da auran mace me shekaru kamarki kawai qaddara Allah ya doramun akanki.  Ance inxo ne in mutsara lamarin biki to ni kisani bani da raayin wasu bidi 'o'i saboda haka sisina baxan bayarba nayi abunda yake wajibi wato sadaqi.  Yana fadar haka yasa kai ya fice. 


       Jage jage fuska duk ta dame saboda make up daya hade da hawaye ta shiga dakin mama,  Faty ce kawai ta kula da shigowarta dakin ta sauri tashi ta tareta ta fada jikin Faty tare da qara fashewa da kuka,  yaya Faty dama irin mijin da Baffa ya zabamun kenan?  Sam be dace dani ba wlh banasonsa na tsaneshi bana raayin auren mutum irin wannan.  Faty ta dago kanta cikin rashin fahimta tace Mimi yimun bayani yanda xan gane,  ba ance kun taba haduwa ba?   Tace ba shi bane sister wanda nake zato ba shi bane 😭😭 wannan mugune wanda baya qaunata kuma ya furtamun da bakinsa,  bazan aureshi ba sai dai in duk abunda za ayi ayi.  Mama ta iso kansu ta tsaya cike da al ajabin abunda mimin ke fada,  ta durqusa a gabansu tace Mimi babu abunda za ai wanda ya wuce ki yarda da qaddara kinsan wlh auren nan babu mai hana faruwarsa sai Allah tunda baffa ya tsaya akai,  kuma turjiyarki ga wannan lamari yana nufin tashin hankalina acikin gidannan.  Ta share kwalla tare da cewa mama yanxu auren dole kike nuna goyon baya ayimun?  Tai saurin tareta da cewa a a wlh Mimi ko maqiyina bazanso auren dole akansa tunda anyimun banji dadi ba,  bare ke yar cikina, amma inaso kiyi haquri ki dauki wannan aure a matsayin qaddara mutum baya taba gujewa qaddararsa wlh tun kan nasan waye mijin da Baffa ya xaba miki naji Sam lamarin bai munba, MARYAM indai ni na haifeki bazaki kaucewa umarnina ba,  umarnina kuma gareki ki karbi wannan aure,  in shaa Allah bazaki danasani ba.  Ta dafa mimin tare da cewa kin yarda xakibi umarnina MARYAM?  Tai saurin kwada kai tare da cewa yar halak ce ni mama bazan taba kaucewa umarninki ba,  naji nagani na yarda.  Kukan da take yasa dady dan yaya Faty shima yasa kuka tare da xuwa ya rungume Mimi yana share mata hawaye da cewa Anty yi shiru ki dena kuka Anty,  ta kalli yaron soyayya ce me qarfi tsakaninta da dady ko uwarsa be shaqu da ita ba yadda ya shaqu da Mimi saboda a hannunsu ya tashi,  tayi dariyar yaqe cike da qaunar dady tace nayi shiru Baba na ta rungumeshi suka kwanta akan cinyar yaya Faty.


      Badaru tsaye qofar gidan su Nafee,  yafi 30 minutes a wajen yana dakon fitowar ta amma shiru,  har ya fidda rai ya juya zai tafi sai kuma gata ta fito tana yatsina wacce take nuna dab take da tayi rashin mutunci. 


 Ya dan matsa kusa da ita tare da cewa ranki ya dade yana washe baki 😁. Tai far da ido 🙄 sannan tace meya kawo ka?  Ai canake kanacan gurin masoyiyarka?  

 

Yayi saurin tareta da cewa ai bani da wata masoyiya da ta wuce ki,  ai ban zaci ma zaki fito ba kusan fa sati 2 ina xuwa bakya fitowa.  Ta fallara masa harara sannan tace ai dole ce tasa na fito,  tunda naga rashin fitowar tawa be hanaka abunda kake niyya ba wato auren Maryam. Ta fada tare da 

fashewa da kuka 😪.


 Tausayin Nafeesa da sonta ya qara qamari a xuciyarsa cikin sigar lallashi yace yi haquri Nafee wlh auren maryam qaddarace a guri..... Dakatamun ✋🏽 ta tsai dashi a hassale,  Kullum abunda kake fada kenan a matsayin abunda xaka kare kanka a wajena kuma nagaji dajin hakan,  ai wlh Badaru ka cuceni, ingama jiranka inbar karatuna sabida kai amma yanxu kaimun haka.  Yanxu bani da ikon fita sai aita nunani ana zundena,  wasu har cewa suke ka fasa aurena. 


 Nafee kiyi haquri wlh babu abunda xai hanani aurenki sai mutuwa,  kuma duk masu yi miki dariya a sannu zasusha mamaki domin aurenmu na barshi daganan xuwa bayan sallah in shaa Allah. 


 Amma dai kasan bazan zauna da ita ba ko?  Saboda haka ka nemar mun gurin zama tun wuri saboda na tabbatar bazan iya hada kishi da wata ba a kanka. 


Nasani Nafee shiyasa ma na nemar mata gurin xama shi kuma wancan gidan dama nakine ke kadai keda yayan da zamu haifa. 


 Nafeesa ta dan sakko jin wannan furuci na badaru kuma ta tabbar har yanxu yana sonta,  tace wai muga photon ta kyau ta finine naga kanata rawar kai a kanta?   Yayi murmushin cin nasara yace wlh bani da photon ta amma wlh ko kama qafarki batai ba Nafeesa. Wai shin kinsan ma dalilin auranta?       Nan ya kwashe abunda ke ransa game da Mimi ya fadawa Nafeesa ba tare da tunanin illar da hakan kan iya haifarwa ba nan gaba. 


Lamarin da yayiwa Nafeesa dadi kwarai da gaske,  domin tasan halin Badaru baya qarya hasali ma ya tsani maqaryacin mutum,  kuma tasan abunda ya fada mata harga Allah hakane a xuciyarsa.  Shiyasa ta saki jiki sukaci gaba da hirarsu ta soyayya kamar ba abunda ya faru. 


Mrs Muhammad 😊

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼

AL AMARIN MARYAM 

 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼          


📝FANTASTIC STARS WRITERS 

                  {F, S, W}


Written by 

RAHMTULLAH (Hajia) 



Dedicated to 

MARYAM BAITA 



Page 1⃣6⃣


   Kwanaki kadan bayan hakan Mimi tai wata irin muguwar rama ta fita hayyacinta,  kallo daya xakai mata kasan akwai abunda ke cinta a xuci. Duk da ba fita tayi rabon i v ba,  acewarta a turawa kowa ta waya inda hali ma a haqura da shagali a bikin a daura aure a kaita.


Abubuwa da yawa sun taru sun cudewa mama da yaya Faty da duk ma wani masoyinsu,  ta bangaren mama dai abu da yawa na damunta,  babban abunda yafi damunta kuwa shine damuwar halin da Mimi take ciki,  na biyu kuma abunda Baffa Yayi mata.  Abunda ya faru dai shine : abunda yayi a bikin Faty shi ya maimaita akan Mimi koma ince har gara Faty akan Mimi domin kuwa tunda ya sai set din kayan gado guda 1 da saitin kujeru yaja bakin aljihunsa ya tsuke daga haka ko tsinke be kuma siya ba,  abunda yayi mugun baqanta ran mama da duk yan uwanta,  domin a xaton mama Baffa xai saki jiki yayiwa Mimi kayan daki kamar yadda yake yiwa yayansa kodan albarkacin biyayyar da tai masa akan mijin da ya bata.  Ita tunaninta abunda yasa yayiwa Faty haka a lokacin aurenta dan bayasan auren da Ahmad ne,  amma sai taga sabanin haka domin har gara kayan Faty akan na Mimi, kenan Baffa ya na nuna mata yayan Al amin daban da nasa tunda ga banbancinnan yana nunawa qiriri,  amma duk cikin lamarin Baffa wannan yafi bata mata rai fiye da rashin kai yayanta sauke farali kamar yadda yakewa yayansa domin a cewarta xuwa maka lokacinsu ne bayi ba. Ta kuma qudure a ranta cewa lokaci yayi da xata takawa Baffa burki akan yayanta. 


Ita kanta Faty da bata cika daukan abu da xafi ba wannan karon taji zafin Baffa kwarai akan abunda yayi. 


Da yake dangin mama ba matsiyata bane da ita kanta maman da Faty suka fidda kudi naqudai Adda halima da yaya Faty sukaje suka lafto siyayya daga kan kayan kicin da kayan qayata falo komai acan acan,  sukaxo suka lafce kayan a tsakar gidan Baffa,  duk girman tsakar gidan sai da kayan sukai ragowa aka dora wasu kan wasu.  Cikin falon mama kuma danginta ne cike taf tunda da kan Adda halima (momy)  har xuwa kan matan yayyensu da kuma yayansu, bakajin komai sai tashin hira da shewa cike da nishadi.


A dai dai wannan lokacin kuma matan gidan na cikin dakunansu cike da baqin ciki. Umma dai anata bangaren tun lokacin da aka kawo lefen Mimi har xuwa kayan auren da Baffa yayi mata tana cikin farin ciki,  domin ita macece wadda bataso taga anfi yayanta,  to ganin komai na Mimi tsiya tsiya yasa hankalinta mugun kwanciya, domin taga Mimi batafi yayanta ba, amma ganin wannan uban Kaya da dangin uwar Mimi suka kawo yasa murnarta komawa ciki. 



Bangaren Anty kuwa kusan tafi Umma shiga tashin hankali akan wannan kaya,  domin ita Sam batason cigaban wani koda kuwa dan uwanta uwa daya uba daya,  bare kuma Mimi yar kishiyarta wacce tafi tsana a duniya.


Ana cikin hakanne saiga Baffa ya dawo diban wani katin daurin aure domin wanda ya fita dashi ya qare, ya tsaya turus ganin kaya sun cika gida ya kwallawa Umma kira suka fito tare da Anty (kamar ita aka kira),  yace mata wannan kayan fa?  Momy wacce ta fito daga dakin mama tace sannu Baffa ya juya tare da cewa haj halima ashe Kina ciki? Suka gaisa tai masa Murnar qaratowar biki sannan ta dora da cewa, dama kayane ta fada tare nuna kayan,  muka kawo tamu gudumnawar babu yawa.  Wata irin kunya ta rufe Baffa wacce tunda yake bai taba jiba, nan take ya fara nadamar abunda yakewa fadima akan yayanta,  har yake tambayar kansa shin meyasa yayi haka kuma meye ribar nuna bambamcin da yake tsakanin yayansa da yayan dan uwansa guda daya da ya mutu yabar masa,  gashinan dai abunda beyi ba danginta sunyi mata kamar yadda sukai a bikin Faty,  yasan acikin matansa duk wacce za aiwa yarta aure ko cokali bata siya,  amma fadima abikin Faty dana Mimi ta nunka abunda ya kashe wajan sau 3, baiji ragowar abunda momy take fada ba saboda tunanin da yake,  sai dai kawai ya tsinci kansa da yi mata godiyar kayan da suka kawo. 


Ba yanda yaya Faty batai da Mimi ba taje wankin kai da qunshi amma taqi,  da kyar fauxa qawar mimin maqociyarsu ta lallami mimin suka tafi saloon akayi mata shampoo aka gyara gashin, qunshi kuwa qiri qiri taqi zuwa dole sai yaya Faty ce tasa me kunshin tazo har gida tayi mata.  Duk da cewa Badaru be bada kudin event din yan mata ba, yan uwanta sun kama gidan dan hausa inda xa ayi luncheon kawai,  domin ko sun qara wani event din Mimi bazataje ba,  dan luncheon dinma cewa tai ba inda xata. 


Ana gobe kamune akaje kafi (jere) gidan amarya ko 2 hours masu jeren basuyiba suka dawo jiki a sanyaye,  domin kuwa wata yar qaramar gida Badaru ya kama haya a wani Geto area da nufin nanne gidan Mimi.  Gidan dai yafi kama da gidan student wanda suke kamawa inbabu guri a hostel,  domin dan qaramin tsakar gida ne sai qofa daya wacce inka shiga xaka tadda falon da ko Set din kujeru baxai ci ba sai bedroom daya da toilet aciki sai dan kicin dan qarami daga hagun falon,  irin kitchen da in kin shiga bazaki iya tsgunawa ba saboda qanqantarsa. 


Wannan gida ya faranta ran maqiyan Mimi na gida (irinsu Umma da Anty da kuma wasu daga cikin yayansu) da na waje. Anty ta dunga murna tana cewa yarinya dai ko FARHAN kitchen aka sai mata a banxa tunda babu gurin xubawa,  domin kuwa ala dole aka juyo da kayan Mimi gida dan abunda ya samu shiga cikin gidan ba wani yawane dashi ba,  don ko fridge da cooker gas basu samu shiga ba sai dan qaramin gas aka siya mata irin na yan hostel.  Direct aka wuce da kayan gidan kakakannin Mimi (gidan mal SULAIMAN)  aka jibge. 


Matar babban yayan su mama (Umma)  da momy suka dunga masifa akan wulaqancin da gidan su badaru sukaiwa Mimi akan gida kuma haka suka samu Baffa da xancen, shima da yake bayason harkar qaranta a take ya nemi mahaifin Badaru da zancen,  har yana barazanar inbasu da wuri ajiye maryam a fasa auren dan ransa ya baci shima,  alh inuwa ya dunga bawa Baffa haquri da cewa wlh suma sai a qurarren lokaci Badaru ya nuna musu inda zai saka maryam kuma basu so hakan ba, amma su kwantar da hankalinsu ya kusa gama gininsa.  Wannan ne yadan kwantar da hankalin masoyan Mimi, amma duk da haka qananan maganganu sunyi ta kai kawo a tsakanin mutane akan auren.


Ranar alhamis itace ranar da aka fara bikin ko ince ranar luncheon,  duk yanda aka kai da lallaba Mimi ta tashi tai shirin tafiya Gidan Dan hausa gurin luncheon Sam taqi anyi fadan anyi nasihar anyi waazin duk taqi ga dukkan alamu halinta na kafiya ya motsa,  ala dole aka kyaleta ganin ciwonta na daukewar numfashi na alamun tashi domin qirjinta sai bugawa yake wanda shine alamun ciwonta yana gab da tashi,  duk ta yankwane tayi wata irin migues rama duk wannan cikar jikin ta xube a 10 dayz,  sai idanuwa xuru xuru da qasusun wuya. 


Haka dai aka dade aka barta a gida daga ita sai kakarta (hajja maryam)  wacce taci sunanta kenan sai kuma mama da tace ina xata yarta babu lfy?  Hajja ce ketaiwa Mimi nasiha da falalar yadda da qaddara mama na gefe tana shafawa hajja mai a qafarta saboda wankan da tayi,  nasihar ta shigi Mimi sosai saboda kwatancen da hajja tai mata da mama mahaifiyarta da kuma irin quncin da ta shiga a dalilin damuwarta,  a fili hajja ke nuna San Mimi fiye da duk wasu jikokinta tanason yarinya fiye da tinanin me karatu.


Mama kuwa ko kallon Mimi batason yi saboda kwantsamewar da Mimin tayi, kuma sau tari in ta kalli Mimi sai taga kamar tana kallon hoton rayuwarta ne ta baya, domin itama haka ce ta kasance gareta lokacin aurenta na fari.  Ta maida hankalinta kacokan kan kula da hajja ( mamanta)  wacce tazo bikin Mimi da nufin sai angama xata tafi. 


Bayan magriba yan bikin da babu amarya suka dawo,  atsakar gida suka jiwo muryar anty na cewa wannan wane irin biki ne kamar na bagudajiyar qauye?  Biki lami kuma dan abun kunya event daya? Neman kudi anan dai beyi rana ba wlh,  shiyasa amaryar taqi xuwa ta qirqiri ciwon qarya 😄. Ai wlh ba a taba abun kunya a gidannan irin wannan ba domin ko taron suna ake a gidannan anayin shagalin da yaci uban wannan kai andaiji kunya wlh,  lallai kwantai beyi ba, 😂 dama haka bikin yan kwantai yake komai tsiya 2 ? Allah ka cigaba da bawa yayanmu miji da wuri tun suna da quruciyarsu.  Babu wanda ya kulata a dangin mama da suka cika gidan domin hajja ta hana a tanka mata a cewarta wanda ya tara jama a baya fushi ko fada in yayi fushi to ya bata taronsa. 



Washegari juma a aka daura auren MARYAM AL AMIN da BADARU MOHD INUWA akan sadaki 50k,  kuma a take Baffa ya kirata ya bata sadakinta kamar yadda addini ya tanada,  tana shiga daki ta wullar da kudin sadakin ta sa kuka,  sai mama ce ta dauke kudin.  Washegari akai yini anan gidan  babu wani armashi qarfe biyar aka tafi kai amarya kasancewar unguwar da xa a kaita da nisa sosai da kyar aka fito da ita daga gidan domin ta qanqame mama tana kuka da kyar momy ta banbareta daga jikin Maman tai waje da ita tasata a mota, momy da wata yar uwar su Baffa (qanwace a gurinsu baffan)  mama saude suka shiga aka tafi kaita. 



Mrs😊[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 1⃣7⃣


Dedicated to 

Maryam Baita



    Tun fauxa qawar Mimi,  na jiran xuwan tawagar ango da sunan siyan baki har ta gaji da xaman jiran. Wajen 8:30 pm tai shirin tafiya,  ta miqe ta dau mayafinta dake gefen Mimi ta yafa, tace "qawata nikam xan tafi tunda har yanxu angon be qaraso ba, kuma kinga layin naku da nisa daga titi kar dare ya qarayi inrasa abun hawa". 


Mimi ta marairaice cikin zubda kwallah 😪 tace fauxa kema tafiya xaki kibarni kamar yadda kowa ya tafi yabarni?  Fauxa qawancenmu yace haka?. 


Ta xauna gefen Mimi tare da cewa qawata haquri xakiyi, kinsan nabar Aslam a gida gurin mama, kuma nasan yanxu yanacan yana kuka, indai har Baba ya dawo ya datta bananan nabarshi yana rigima fada xaimun.  Wlh dana taho dashi sai najira xuwan su Badaru inyaso sa maidani gida. 


Ta riqe hannun mimin sannan tace "qawata kiyi haquri komai yayi farko xaiyi qarshe, ikon Allah ne kawai bashi da farko bashi da qarshe,  Allah ya sa alkhairi acikin aurenki. Kimaida AL AMARINKI gurin ubangiji,  in shaa Allahu zakiyi alfahari da wannan aure, karki bari rashin son mijinki ya taba biyayyarki gareshi har irin tawa ta sameki (mutuwar aure),  bana fatan haka Mimi.  Ki tuna ba duk abunda kakeso kake samu ba. Kiyi biyayya, kiyi ibada,  abu na qarshe da xan fada miki shine kada ki sake ki zauna da yunwa ".  Na sanki Jan wuya ce ke wurin ibada,  to qira akai". 


Tana kaiwa nan ta juya ta tafi ita kuka Mimi kuka.  


Tun bayan tafiyar fauxa take xaune a tsorace, koya taji motsi sai ta firgita duk kuwa da cewa ita din ba gwanar tsoro bace,  amma yau sai tasami kanta cikin mugun jin tsoro,  ji take kamar ta tashi ta xura da gudu, kasancewar ba wuta a unguwar sai chaja aka kunna. 


Batasan iya lokacin data dauka a haka ba, sai ji tayi ana bude kofar gidan ta waje, alamar me gidanne. Shigowarsa parlon ya xowa Mimi da wata irin faduwar gaba matsananciya, gumi ya dunga karyo mata. 


Sam bazata iya tantance ko yayi sallama ko beyi ba,  domin ko yayi bataji ba balle ta amsa. Direct yayo kanta tare da cire mayafin data rufe kanta dashi yana huci kamar a fagen daga (filin yaqi) duk da a tsorace dake da abunda yayi hakan baisa ta motsa ba, ya qare mata kallo tare da hadiye wani mugun yawu duk da ramar da tayi hakan bai hana surarta bayyana ba,  ya dure kallon nasa akan fuskarta ya qura mata ido yana mata kallon qurullah,  abunda bai taba lura tana dashi ba kafin ya aureta yau ya ganshi wato tabon sallah take goshinta da danannen bakinta,  sannan kwantancen gashin dake gaban goshinta,  hakan yasa ya cire mata dan kwalin kanta,  kyakykyawan gashin kanta dashi sampoo yake tashin qamshin mega growth ya bayyana, " SUBHANALLAH " ya furta afili sannan a zuciyarsa yace dama anasamun macen bahaushe da irin wannan gashin?  Ya shafa gashin,  sannan ya tura hannunsa cikin wuyar rigarta ya cafko qirjinta, abunda yayi tsananin firgigita tai saurin yin baya ta maqure jikinta. 



Taso muyi sallah,  ya fada ransa a hade cikin sigar bada umarni,  sanin cewa batai sallar ishaba yasa ta tashi ta bishi inda yabi wato toilet tayi alwala suka fito, ya jasu Sallah sukayi isha,  sallar ma aurata ta biyo baya. Tasan akwai adduar da manxon tsira (s a w) ya umarci miji ya dafa kan matarsa yayi mata ita kam baiyi mata,  ya tashi yaje kitchen ya dakko cup ya tuttula L&Z Milk ya shanye sannan ya kuma cika kofin ya miqa mata a hankali ta girgiza kai alamar bata sha,  ya bude ledar kazarsa ya cirota sai tashin qamshi take ya dora kan plate " zo muci " abunda ya cemata kenan, bayan ya fara yagar kazarsa yana hadawa da madarar yana kurba, alamar an dade ba a hadu ba 🤣 (lol), ko kallonsa bataiba balle ya samu amsa. 


Bayan ya tashi da kaza guda da liter daya na gorar madarar l&z, ya ture ragowar   kayan da yaci gefe ya cire rigar shaddar jikinsa tulelen cikinsa ya bayyana alamar anyiwa cikin loding da yafi qarfinsa,  ko singlet babu ajikinsa. Babu batun yin brush domin tsaftace baki kafin kwanciyar bacci balle aje ga dan yin tattaki domin narka abinci daya loda kamar yadda addini ya hana kwanciya bayan cin abinci. 


Ya hayo gadon tare da janyo Mimi jikinsa ya saki ajiyar zuciya, cikin zaquwa ya fara cire mata kayan jikinta,  lamarin da yayi matuqar tsoratata domin Sam babu nitsuwa a tattare da abunda Badarun keyi,  lokacin da yazo cire mata riga ne ta riqe riga qam ta hanashi cirewa, yayi yunqure kwacewa ta qara riqewa gam,  hakan yasa yayi amfani da qarfinsa wajen rabata da rigar, tuni ta sakar masa ganin yana shirin yaga  atamfar super wax mallakar kamfanin Sheraton ( Sheraton super wax).


A haukace yake tsotsar qirjinta duk ya rude,  ya kuma rudata,  kuka take me hade da ihu 😭 , Jin yadda yake matsa mata nono ba tare da tausayi ba kamar ba jikin me rai yake latsawa ba. Ya cire hannunsa ya shinfideta a kan gadon sannan ya xare wandon jikinsa,  ita kam ya dade da rabata da nata kayan,  ya rankwafo kanta da nufin hada bakinsa da nata,  tai saurin kauda kanta, domin a tunaninta ai sai da soyayya akeyin kiss,  ita kuma batason Badaru kuma tayi alqawarin bazai taba shan bakinta na,  kuma bayan haka ma ai Badaru bashi da tsaftar da xata hada baki dashi,  ita kuma macece me tsaftar gaske,  yanxun hakama daya kifu a kanta qarnin gumi yake alamar tun rana rabon jikinsa da ganin ruwa (wanka). 



Sucking din nononta yake tun qarfinsa kamar me shirin xugo ruwa,  radadin da takeji ya zarce faduwa da baki.  Ana cikin hakan ne taji ya danna yatsansa a matancinta,  ta kwallah wani irin ihu tare da miqewa zaune a kan gadon ba tare da tasan tayi hakanba. Xuwa wannan lokaci shikam ya zaqu wajen San cimma burinsa,  ya kalleta cikin fita hayyaci yace "ke meye haka?  Dare na fa kike ihu maqota xasu iya jiwo ki,  hanya nake nema shiyasa,  in kuma kinsan gurin nunamun."  ya qara janyota ya kwantar tana ihu tana bashi haquri da cewa "Dan Allah Badaru kayi haquri na dena,  na tuba da xafi Dan darajar iyayenka."



Yayi murmushin mugunta yace "ba kince bakya sona na ba?  nima ance miki ina sonki ne?  Kinga wannan abun da nake miki shine dalilin aure na dake,  domin MARYAM tun randa na fara ganinki Allah ya jarrabeni da muguwar sha 'awarki,  wlh ko yarinyar da nakeso kamar raina bana sha'awarta kamar ke, tundaga ranar Kullum na kwanta sai nayi mafarkin ina saduwa dake,  komai na halittar jikinki yayimun, amma fa bawai Love ba,  no Just sha'awa ".  Yana kaiwa nan ya kuma danna hannunsa a gabanta tare da tambayarta nanne?  Gara fa in kinsan gurin ki nunamun dan karna shiga inda ba nanba,  Dan wlh saina sadu dake ayau ko mutuwa zaki ".



Shigewar da gaba daya ta ya tsan hannunsa tayi ya tabbar masa da nanne hanyar kuma a take ya fara qoqarin shigarta iya qarfinsa yana wani irin ihu da sambatun ambaton sunan Nafeesa tare da yiwa Nafeesan wasu alqawura na soyayya,  alamar dake nuna cewa itace a ransa.  Muryar Mimi ta katse masa sambatun da yake. 



Cikin kuka wurjanjan take furta "ka dubi Allah kayimun a hankali wlh ban taba yiba,  kayi haquri xata jimun ciwo 😭" . Kalamanta suka sanyaya masa jiki kwarai, ya shafi gefen fuskarta yace "maryam wlh nasan ke ba mazinaciya bace, domin kedin duk wanda ya kalleki zega alamar kamewa a tare da ke koda maqiyinki ne, sai dai mutum yaqi Allah ya yi miki sharri" 


Yana kaiwa nan yaci gaba da abunda yake,  amma ala tilas ya haqura bayan ya dan samu nutsuwa, saboda ya gane baxai taba iya kauda budurcin Mimi a dare daya ba, saboda tana cikin jerin mata masu qaramar halitta, sannan masu kwarin tantanin budurci.  



Bacci kona 1 minute Mimi bata samuba a daren saboda a tsorace take ga ciwon jiki,  ga muguwar yunwar take addabarta,  wacce ta haifar mata da tsananin ciwon kai.



Mrs 😊

[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼

            


Writing & story by rahman Mohammed (hajia)


Editing by mmn khairat 

📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }


Page 1⃣8⃣


Dedicated to 

Maryam Baita



   Har garin Allah ya waye bata rintsaba saboda axabar ciwon kai,  ta kalli agogon dakin dai dai lokacin 7:45am. Amma ta kasa tashi tayi wanka tai sallah.


Shikam Badaru kiran farko ya miqe yaje ya tsarkake jikinsa yayi nafilfili tana kallonsa, har akai kiran assalatu yayi sallah yaci gaba da karatun qur ani,  da taga bashi da niyyar taimaka matane tace " Dan Allah taimakamun intashi lokacin sallah yana qurewa". 


Ya kalleta shagarai "wai nufinki dan wannan abun da ya faru shine ya hanaki tashi? 😏 lallai ke muguwar yar rainin hankalice,  sai ki tanadi ambulance ranar da mai gaba dayan zai kasance,  tashi kuma karki tashi ai da kindamu dayin sallah akan lokaci da baki tsaya langwai ba,  hakan ya nuna ko acan gidan iyayenki haka kike wasarere da harkar addini abunda kuma bazan dauka ba kenan,  dan ni natsani mutum din dabe damu da addini ba"



Ta runtse ido kalamansa sunfi abunda yayi mata daren jiya muni a gareta, domin ita mutum ce me tsananin kiyaye lokutan sallah,  yan gidansu har cewa suke mata "mayyar sallah" amma rayuwa yau ita ake qalubalanta akan sallah. 



Tana kaiwa nan a tunaninta ta qara kallon agogo a karo na biyu 8:03 agogon ya nuna,  tai wani irin nishi cike da qarfin hali ta yunqura ta miqe,  ta wuce ta gabansa tanajan qafa saboda axaba,  taje kitchen ta kunna gas ta tari ruwa famfon kitchen ta cika tukunya ta dora.



Tananan tsugune a qofar kitchen din ruwan ya fara shuuuu alamun ya kusa tafasa taje toilet ta dakko bokiti ta juye ta daga dakyar ta kai toilet,  naya kallonta dan rashin tausayi ko ajikinsa. 



Bayan tayi wankan zarki dana sabulu ta xuba ragowar ruwan zafin a baho tasa gishiri ta shiga ciki ta zauna dakyar.


Koda ta fito daga wanka ta sameshi xaune yana shan tea da bread din daya shigo dashi jiya,  kuma ga dukkan alamu iya cikinsa ya dafa ruwan tea din banda ita. 



Tuni Badaru ya fita,  ita kuwa tunda ta idar da sallah tana kan daddumar a zaune saboda kabaitar da ita da yunwa tayi ga wani mugun amai da yake taso mata.



Ta rarrafa da dakko wayarta dake kan bed side,  ta kira yaya Faty,  bugu daya ta dauka,  "bazaku zo bane yaya Faty"?  Shine maganar da Mimi ta fara fada bayan Faty ta daga wayar.


Ta danyi jum,  cikin dauri ta danne kukan dake shirin taso mata,  sannan tace "kinga Mimi na tashine da ciwon kai,  ko sallah ma a zaune nayi,  bazan samu xuwa ba sai kin dan kwana biyu,  ya mijin naki kun tashi lfy?. 



Duk da Mimi tasan cewa abunda ya Faty ta fada ba haka bane,  saboda ta fuskanci yaya Faty batasan xuwa gidan Sam dan jiya ma batazo kawota ba,  kuma tasan tausayinta da Faty keji shi ya haifar da haka. Ta daure tace "ayyah sannu sister Allah ya baki lfy,  agaida ya Ahmad. 


Bata qara gigin kiran wani ba,  duk da tasan a al adar gidansu washegarin biki sai sun hadu duk yan gidan anje gidan amarya,  amma ga dukkan alamu ita bata Sami hakan ba tunda gashi har goma tayi amma ko kare baixo wajenta ba. 



Tananan zaune cikin ciwon kai da yunwa wanda tun qarfi suke shirin tayar mata da ciwonta na sarqewar numfashi,  tunani take irin rayuwar auren tada ke shirin faruwa a kanta,  ita dai tasha ji a fili da kuma littattafan soyayya yacce namiji ke tattalin mace a daren farko da kuma washe garin ranar musamman inya sameta virgin,  amma ita sai yunqurin fyade da Badaru yayi mata (to fyade mana tunda bataso kuma bebi a hankali ba) duk da yasani kuma ya tabbatar da cewa ita din virgin dince. Sai kuma dan karen wulaqanci da tasha yau da safe ta hanayar yin halin ko in kula da ita.  Afili ta furta "ALLAH KAINE KA JARRABENI,  KUMA KASAN XAN IYA SHIYASA KA JARRABENI DAN KA GWADA IMANINA,  ALLAH KA BANI IKON CIN JARRABAWA,  KA BANI IKON BIYAYYA GA MIJINA."



Tananan zaune cikin yunwa da nauyin qirji, amma kuma sam batasan koda hadiyar ruwa balle abinci,  taji ana buga gidan. 


Ta tashi dakyar cikin jiri, ta fita ta bude. Little ta gani wato autar momy yar mama, sunanta na gaskiya MARYAM wato sunansu daya da Mimi, kasan cewar sunan hajja gareta babar su momy Lima itace auta a gidan momy shiyasa ake ce mata little (wato  qarama),  yarinyace da bazata gaza shekaru 13 ba,  doguwa fara sol siririya kamar ka harareta ta karye saboda siranta kyakykyawa irin kyan su yaya Faty tunda dama tafi kama da yayan momy.  



Little akwai kafirin iyayi da son nuna iyawa saboda rayuwar da ta taso ciki kasancewarta auta yasa aka sakar mata take sangarta son ranta ga kuma gatan yayye dana iyaye. 



Tsaye take a qofar gidan alamar itace da buga qofar sanye take cikin riga da skirt yan kanti (kamar yadda yake ga dabiarta bata cikasa natives ba indai ba biki ba) kanta ba dankwali sai siririn gyale datai yane kanta dashi, fuskar nan tasha make up ga kuma wani qaton glass data kwama wanda ya shafe rabin fuskarta. Daga can bayanta kuma Huxaifa ne (Dan gidan Baffa)  ke gyara parking din mota da alama shiya kawo Little din. 



Mimi farin ciki ya rufe ta daka tsalle ta rungume Little din kamar ta shekara bata ga na gida ba haka takeji,  tace "autar momy kece 😊" ku shigo ciki Huxaifa,  


Little tace " name sake kamar yadda take kiran Mimi ko kuma tace mata ya Mimi,  wlh mama ce ta tasoni,  wai duk wanda tace yaxo ta aiko shi sai ya zame, waisu tausayinki sukeji,  shine suka hadu ita da momy suka tattgoni " 



Ta kalli gidan ta yatsine fuska sannan ta dora da cewa " nima fa name sake da nasan haka zanxo in tadda gidannan bazanzo ba,  no wonder kowa yaqi xuwa, tai tsaki,  ta dora da cewa duk yanda ake fadar munin gidannan banxaci abun yakai haka ba,  gida sai kace xuciyar kafiri, gaskiya guy dinnan ya kwafsa mana " 



Dai dai nan Huxaifa ya shigo da kaya niqi niqi,  ya ajiye ya fita yace bari in jiraki a waje Little,  Mimi tayi tayi ya zauna yaqi ko saboda qanqantar parlon ne oho. 



Mimi ta fara fito da kayan daja ajiye tana gani, yawanci kayanta ne na amfanin yau da kullum, kamarsu system da chajar waya sai kuma pos 👛 dinta, wacce ke qunshe dasu ATM dinta da I D cards. 



Little ta matso tana bude ragowar kayan data shigo dasu yanxu tana cigaba da mita " ai wlh wannan anguwar kwata kwata batai ba duk ba Local champions ne a unguwar muna kawo kai naga ana kiwon shanu da raquma sai kace a ruga "


Mimi tai murmushi tare da cewa to ya za ai Little kowa da qaddararsa a rayuwa kuma mutum baya kaucewa qaddararsa ni tawa qadddarar kenan 😊.


Ta fito da leda da wani ruwa a ciki me sanyi tace wai gashi Maltina ce da madara mama ta hada miki tace ki shanye yanxu, Mimi tai tsai tana jinjina soyayyar uwa ga danta, wato tasan tana cikin yunwa sannan kuma dan tsabar soyayy sai data hada mata, sannan ta bayar a kawo mata lallai agaida uwa (Allah ya sakawa uwa da gidan aljannah).  



Atake kuwa ta bula ta shanye,  wani sanyi yana ratsata ta balli maganinta da aka hado mata dashi yanxu cikin kaya ta hadiya saboda nauyin da qirjin ke mata. Little taci gaba da nuna mata kayayyakin ta miqo mata miya cikin tukunya da taji naman kaji ta soyu tai shar sai qamshi take tace gashi inji momy,  sannan qanqara guru guru ta pure wata cikin leda tace wannan kuma inji mama ga kuma soyayyan naman shanu cikin bokitin roba inji yaya Faty. 



Haka dai abun alheri niqi niqi ta dunga kukan murna da jinjina soyayyar uwa da dangin uwa akan dá. 



Nan da nan kuwa taji kwarin jikinta ta tashi Little ta tayata suka gyara gidan ta bawa Huxaifa kudi acikin wanda mama ta kawo mata ta riqe a hannunta ya siyo mata ruwan pure wata leda daya da maltina rabin dozin ta xuba a cooler ta fasa qanqara akai,  sabida gidan fridge be samu shiga ba.  




Taga kayan abinci a kitchen sai dai kayan miyane babu   hakan yasa ta dafa farar taliya da nufin aci da miyar da momy ta kawo. 


Suka bade gidan da room freshners masu sanyin qamshi,  gidan yayi fes tayi wanka ta canja kaya harda make up dan qarfin hali. 



Koda Little ta tashi tafiya Mimi ta bude akwatin lefenta ta dakko mata atamfar súper collection me kyau da sabulu da mai,  domin taji dadin xuwansu sosai,  shi kuma Huxaifa ta bashi turare da sabulai,  sannan ta bawa little ragowar kajin da Badaru ya kawo guda biyu tace ta kaiwa mama.


Har mota ta rakasu tana ta godia tace da Little sai yaushe autarmu?  Ta daure fuska sannan tace " Allah name sake baxan kuma xuwa ba saboda daga gidan har me gidan basuyimun ba,  wlh kinfi qarfin auran wannan bagidajen kawai dai akwai abunda Allah yake nufi da hakan" 


Huxaifa ya jinjina kai cikin mamakin qarfin hali Iron na Little, sannan yayi saurin katseta da cewa "ya isa uwar iyayi in banda shirmenki mutum yana auran matar da ba tasa ba"?


Sukaja Mota suka tafi suna dagawa juna hannu. 

[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏻 *






Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 1⃣9⃣

Dedicated to 
Maryam Baita


Tafiyarsu bada jimawa ba akai kiran sallar zuhr,  bayan tayi sallah tana zaune kan kujera so take tadan runtsa ko tasami saukin ciwon kai,  amma abun ya gagara sai tunani take. 

A irin hakan ta tunano rayuwarta acan baya.  Akwai wani lokaci da AL AMARINTA ya damu mama har ta dau shawarar wata qawarta yar gurin aikinsu wacce suke kira da Anty saude.

Anty saude ta dade tana fadawa mama ta nemi taimakon malamai akan LAMARIN Mimi amma maman tanayin burus da zancen, sai dai a lokacin da matsin lambar Baffa Yayi qamari akan Mimi dole tasa mama amsa gayyatar Anty saude. 

Anty saude ta tasa Mimi gaba babu san ranta ko kadan dandai mama ta dage ne,  sukaje gidan wani malami acan wajen kurna babban layi.

Duk da bayanin da Anty saude taiwa malamin akan matsalar Mimi sai da ya buqaci Mimi ta qara yi masa bayani da kanta,  wanda hakan yasa Mimi kuka domin batasan abunda zatace masa ba.  Cewa xatai ta kasa daukan qaddarar da Allah ya dora ko yaya?  Ko cewa xatai ya jawo mata mijin aure koda lokacinta beyi ba?. Sam ita batasan bin malamai. 


Ganin Mimi na kuka yasa ya haqura dajin lamarin daga bakinta sannan ya dora da yimata tambayoyi kamarsu : kina mafarki ana saduwa dake?  Tace gyada kai,  alamar eh.  Kina jin bacin rai haka kawai?  Tace eh. Kina tsanin ciwon mara lokacin al ada?  Tace eh. 

Ya kalli anty saude yace da alama baqin aljani ya auri yarinyar nan,  kuma indai ba a rabata dashiba to wlh ita da aure har abada.

Mimi ta tsorata dajin cewar wai itadin aljani ya aureta. 

Ya basu turaren hayaqi ya fada musu yanda xatai amfani dashi,  Anty saude ta bashi sadaka yace "a a dauki aimu sai buqata ta biya ake biyanmu."

Koda suka dawo ta mayarwa da mama yacce akai tabata turaren daya bata,  mama tasata gaba tayi saida tayi duk turaren. 


Kafin wa adin daya dibar musu na komawa gurinsa yayi,  cikin ikon Allah Mimi ta sami saukin mafarkan da take yawanyi har ta fadawa mama ta dunga murna da cewa " Allah ya sa qarshen baqin cikinmu kenan,  dama saude ta dade tanamun tayin neman taimako ina sharewa ashe akwai waraka aciki "

Ranar komawarsu gurin Anty saude bata samu xuwa ba saboda wani uxuri da yazo mata,  Mimi ita kadai taje gidan. 

Tai sa ar samunsa shi kadai acikin dakinsa da yake sallamar baqi, ta fada masa irin nasarar data samu akan maganin, yace yau ina maman taki?   Tace taje asibiti gurin me haihuwa. 

Yawwa dama nasarar aikin mukeso mu fara gani tunda yanxu anyi nasara akan wannan sai mutafi mataki na gaba.  Ya kalleta sannan ya dan rage murya "kinsan tunda aljanin ya ruga ya sadu dake dole sai anyi miki wani dan gajeren aiki,  wato sai an tsarkake gabanki saboda shafar da aljani yayi miki,  sanyi rubutu a gabana sai in dan shigeki  da nufin haramtawa aljanin qara kusantarki anan gaba." 

Yana kaiwa nan ya matso kusa da ita da nufin tabata tai wufff ta miqe tsaye ta nufi qofar fita yayi saurin riqota da cewa ke taimakonki xanyi,  inkuma bakiso shikenan ki biyani kudin aikin da nayi miki rannan.  Kafin ya qarasa tai masa wata muguwar kutufo wanda ita kanta batasan ta iyaba, sai yanxu da taga ana shirin keta mata haddi.  Nan take kuwa sai gashi a qasa wanwar.  Sannan ta dora da cewa "in abunda kai nufin yimun alkhairine Allah ya saka maka da alkhairi in kuma sharrine Allah ya kawo me kwatantashi akan yar cikinka" sannan ta bude jaka ta watsa masa kudi,  tace ga ladan aikinka nan, domin ni banacin haqqin mutum. 


A burkice ta shiga gida, saboda har yanxu tsoron abunda akai mata bai bartaba idonta jawur,  umma take tsakar gidan tace "lfy Mimi?  Naganki wata iri ko hatsari kikai " ko ta kanta batabi ba ta shige dakin mama. 

Har bedroom din maman ta isketa cikin kuka ta fara magana " mama meyasa bazaki dau qaddarar Allah akaina ba?  Shin na dameki da yawon bin mazane shiyasa kika damu nai aure?  Bakya ganin takurawarmu ga lamarina ba shishshigine ga Allah ba?  Indan Allah ya kyalemu da kanmu xamuji dadi?  Akwai wanda xai mana abu ba Allah ba? Wlh tun farko banso xuwa gurinnan ba Allah ya gani kece kika takura. Wlh!  Wlh!!  Wlh!!!  Da inbawa malamin tsibbu jikina da nufin zaimun aikin da zan samu miji gara nayi ta xama ba miji har abada , domin nasan Allah baya mantuwa kuma bai manta daniba "

Jikin mama na rawa,  cikin razana ta kamo mimin sannan ta zaunar da ita kusa da ita tace " meya faru mamana?  Kinsani a duhu waye yayi yunqurin keta miki mutunci? "

Ta mayarwa da mama yadda sukai da malamin,  mama ta tsorota da lalacewar zamani,  ta yadda malami zai nemi mace dan kawai taje neman taimako,  sannan ta godewa Allah daya bata nutsatstsiyar ya.  Tace yi haquri Mimi bansan haka lamarin yakeba wlh da bazan soma ba.  Da haka aka rufe chapter neman taimakon malamai akan LAMARIN MARYAM. 


Badaru bai dawo gidanba sai magariba,  gidan yayi baqiqirin saboda rashin wutar Nepa kuma duk fitilolin babu chaji.  Ga xafi kasancewar ana tsaka da xafi,  ya qudure dole ya samo injin generator koda qaramine saboda bayason zafi.


Yayi amfani da fitilar wayarsa wajen haska parlon ya ganta a xaune akan pray mat alamar sallah tayi. 

Tayi masa sannu da xuwa, ya amsa direct ya wuce kitchen ya xubo abinci a tray (ina ruwan khadimul ci,  bama a plate ba 🤣) taliyar da ya xubo xatai guda daya, lafto miyar kafin dama kajin, ya faraci ba tare da tambayar inda ta samu kayan miyan da tayi girkin ba ganin cewa baibata ko asi ba kuma bai kawo kayan miya ba. 

Tayi mamaki da taga ya cinye Raliya tas ya dora da gwangwanin maltina, kamar shi ya siya.  Yayi gyatsa. Sunanan zaune ita tana jan carbi shi kuma na danna waya aka kira isha ya tashi ya tafi masallaci. 

Bayan idar da shafa'i  da wuturi ta je kitchen ta debo red meat din da aka kawo mata dazu soyayye ta zauna taci tasha maltina,  sannan taje tayi wanka da brush ta gyara jikinta da turarurka masu sanyi ta sanya riga da wandon bacci cotton,  ta fito parlo ta xauna tana charting duk kuwa da cewa babu chaji a wayar,  jira kawai take abunda taci ya fada taje ta kwanta dan bacci takeji. 

Yau dai ansamu cigaba domin Badaru yayi wanka bayan dawowar daga masallaci, brush ne dai beyiba alamar be saba yiba. 


Beyi mata magana ba, kawai dai yazo yaja hannunta kamar tunkiya ya shiga da ita bedroom din ya cillata akan gado tare da cewa " gara mu fara da wuri mu gama don yau bacci nakeji" babu xancen wani romance a cikin tsarinsa kawai dai ya hau wasa da qirjinta da kuma tsotsa kamar tababbe,  tun tana daurewa har ta gaza ta fara yunqurin ture kansa daga jikin nipple dinta, lamarin da yasa ya gartsa mata cixo a nipple din,  ta kwalla qara.  Ya fara yunqurin cinma burinsa, amma sai dai yauma kamar jiya ya kasa duk iya nacinsa dole ya haqura domin shima ya fara jiwa kansa rauni.

Ya kwanta cike da baqin cikin kasa cimma burinsa,  sannan na kukan da Mimi ke masa,  a xuciyarsa yace kin kusa kiyi me dalili dan wlh gobe gurin Mekudi (abokinsa) xanje ya nemomin maganin qarfin maza. 


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣0⃣

Dedicated to 
Maryam Baita


Washegari bai samu kansaba sai wajen qarfe hudu na yamma,  saboda yaje kasuwa daga can kuma ya wuce ya sayi inji (generator) ya kai gida ya kira masu hadawa suka hada, sannan yayi sallah ya tafi majalisarsu dake unguwarsu unguwar da iyayensa suke.

Ya samu Maikudi yace yawwa wlh kai nake nema tun safe nake kiran wayarka a rufe,  Maikudi yace wlh babu chajine.  Sannan suka kebe daga can qarshen tabarmar dake gurin. Yan gurin sunata zolayarsa da ango meya fito da kai yanxu,  ba mun baka hutu ba. 


Mekudi abokin Badaru ne,  duk da cewa halinsu ba daya ba, domin mekudi irin mazannan mayun mata bashi da aikinyi sai yawan yaudarar yayan mutane duk da cewa yana da mata har yaya biyu,  gashi Dan duniya na qarshe.


Bayan Badaru ya gama fada masa abunda ke faruwa na kasa kauda budurcin Mimi (kuji rashin sanin ciwon kai 😒). Mekudi yace " to kodai tayi cushe cushe nan nasu na mata a wajen?  Kasan hakan nasa irin hakan" 


Badaru yace "banajin hakan,  domin yarinyar bata da rawar kai irinta yan matan yanxu,  bayan haka kuma bata sona banaji zatai wannan abun da nufin burgeni,  nafi dauka dai halittartace hakan.  Yarinya fa yar baiwa ce ya fada yana dariya,  sannan ya dora da cewa ta hadu dan kawai banasonta ne"


Yace to shikenan  yanxu inada wani ragowar magani yana Mota ka hadiya tunda naga amatse kake,  kafin in samo maka wani.  Yawwa mutumina cewar Badaru wlh na matsu inji ya lamarin yake 🙈.


 
Suna tsaye kofar gidan su Nafee,  hira suke,  awanni 3 kenan da shan maganin da Mekudi ya bashi, amma ga dukkan alamu maganin ya fara aiki a jikinsa,  dan ji yake kamar cafko Nafee.


Yace mata "ni bara in tafi Nafee"  ta marairaice tace kace baka santa amma tunda ka aureta inkazo Allah Allah kake ka koma gunta,  me hakan ke nufi? 


Yace "yi haquri yau kam banajin dadi ne,  amma gobe innazo xan dade kinji" yana kaiwa nan ya fice ko takanta be kuma bi ba.

Yana xuwa ya ganta a duhu ga zafi saboda qanqantar gidan,  wayarta babu chaji dan haka take zaune a duhu. 


Yaje ya tada inji, kunna fankar parlon . Ta saki ajiyar xuciya dan zafi ya dameta kuma zafi kan iya tayar da ciwonta. Yaje yayi wanka ya xuba abinci yaci. 


"Zo" yace da ita yana kashingide a jikin kujera, yanajin wani irin feelings.  

Ta marairaice cikin zubar da kwallah tace "Badaru kayi haquri wlh kaina ciwo yake tun renda aka kawoni gidannan" 

Yayi dariyar mugunta yace to aini ba kanki xan taba jikinki kawai nakeso,  saboda haka kixo kafin na tashi nayi miki abunda xakiyi nadama.  

Tai saurin qarasawa inda yake da rarrafe Jin abunda yace, "cire rigarki" ta zaro ido 😳. Haka dai saida yasata tai tik ta hanyar tsoratar da ita. 


Sannan ya buqaci ta tashi tayi tafiya a gabansa a hakan, lamarin da ita kuma taqi yarda duk kuwa da yadda yakai da naci dole ya haqura,  ganin tana bata masa lokaci kuma ga magani na aiki a jikinsa yasa ya huqara ya haye kanta anan kan centre carpet din parlon da kuma fitila akunne (Dan tsabar rashin sanin ciwon kai da rashin kunya). 


Ashe kuwa gaskiyar Badaru da yake cewa ta tanadi ambulance,  domin kuwa bata tabajin labarin daren farko me wahala irin nata ba. 


Tun tana yunqurin kwatar kanta harta gaza ta xuba ikon Allah ido,  ta gurxu iya gurxuwa cikin mugunta da wutar ciki ya kauda budurcinta.


Ya dunga kuka wiwi yana sambatun kiran sunanta ( dan rainin wayo ashe kasan sunanta🤔) tare da alqawarin riqeta iya rayuwarsa.


Wannan dare ma bata runtsaba saboda ji take kamar an tsagata da reza an mata tsarki da attaruhu.  Yayin da Badaru yake bacci harda munshari alamar cikar buri,  kuma munsharinsa ya temaka kwarai wajen hanata bacci.


Sai gab da asuba ta samu baccin shedan ya kwasheta (na shedan mana tunda zai hanaka sallar akan lokaci).


Sanyin ruwan daya shafa matane yasa ta farka,  "sannu maryam, kin hadu ni nasan bada banxa na gigice akanki ba,  gaskiya xan huta,  fatana ki koyi dauriya dan naga kedin raguwa ce" kalaman Badaru kenan. Kuma yana gama fadar hakan yasa kai ya fice,  ba tare da la akarin yayi mata tagargazar da xata buqaci temako ba.


Yauma kamar ranar itace ta gyara kanta tayi sallah, ta nade xanin gadon da ya baci da wani abu chakal .kamar jirwaye da kuma ruwan ciwo. Amma babu jini sam. Ta shinfida wani.


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣1⃣

Dedicated to 
Maryam Baita


A hankali rayuwa taci gaba da tafiya, lokuta na gudu tunda gashi Mimi ta samu kimanin wata daya da rabi a gidan miji. 

Ixuwa yanxu yan gidansu kaf babu wacce bataxo mata ba inka dauke Faty,  domin ta kasa xuwa gidan Mimi,  ko meye dalili oho.

Kuma duk wanda yaxo tanajin dadi sosai,  kusan ma ince duk takun saqar da suke da wasu daga cikin yan gidansu xuwansu gidanta ya goge mata komai aranta, duk da cewa in anxo sai anyi habaici da kushe gidanta da kuma jajanta mata irin mijin data samu. 

Fauxa kam xuwanta daya gidan duk kuwa da nacin da Mimi ke damunta dashi a waya na rashin xuwanta. Takance "Mimi ni bamai aure ba aga ina yawan xuwa gidanki sai ace naqi zaman aure inaso inkashe miki naki "

Dake ita din ba gwanar qawaye bace,  sannan kuma mafi yawan qawayen basusan tayi aure ba,  sai ya xamana babu wata qawa inka dauke fauxa da taxo gidanta.  Lamarin da yayiwa Badaru dadi,  domin shi a tunaninsa qawaye na iyasa Mimi tayi masa bore kan axabar da yake mata. 


A fannin kwanciyar aure dai Mimi ta kasa sabawa da salon Badaru,  domin ita dai ixuwa wannan lokaci Kullum abun sabo yake gareta.  Mekudi ya riga ya bata Badaru da shan maganin qarfin maza, kawai dan aganawa yar mutane azaba.


Saboda da haka Kullum Badaru cikin buqata yake,  baya duba cewa ita din abun Sam be qarbeta ba duba da yanda take jigata aduk sanda ya kusanceta,  wataran ma har rasa numfashi take na wucin gadi (ciwonta). 


 Yau laraba,  kuma tun 7:30  Badaru ya fita a cewarsa akwai wadanda zasuzo siyan kaya shagonsa a kasuwa zaije ya sallamesu.


Bai dawo gidan ba sai yanxu,  11:45 am, ya datta Mimi duke a qofar kitchen tana shirya kayan wanke2 da tayi. Tana cemasa sannu da xuwa bebi takanta ba,  kawai hannunta ya kama kiiiii yayi daki da ita.


Yana xuwa ya axata kan gado ya cire wandonsa,  yana me cewa "kinga abunda ya dawo dani,  wata nagani yanxu a kasuwa shedan ya qawatamun ita shine na dawo insamu nutsuwa"


Yana fadar haka ya farmata ya fara yunqurin shigarta,  babu batun romance a salon kwanciyar Badaru sam,  yanayin kwanciyarsa dai tafi kama da kwanciyar da manxon Allah (s w a)  ya siffata masu yinta da dabbobi,  wadan da suke farwa mace batare da tayar mata da tata sha'awar ba.


Sai da ya biyawa kansa buqata,  sannan ya lura da pink din janbakin data fente bakinta dashi,  ya bashi sha'awa kwarai,  dan haka ya nufi bakinta da nufin kissing dinta, tai saurin kauda kanta. 


Ya tsaya,  yana qare mata kallo da Jin haushin ta hanashi tsotsarta yace " wai ke kina nufin bazan sha bakinki ba?  Inafa lura dake duk sanda nazo shan bakinki sai ki kauda kanki,  sai kiyi tayi kinwa kanki,  tunda nasamu abunda yafi baki ajikinki kuma ina yanda naso dashi ai shikenan"


Bayan yayi shirin fita ya sameta akan gadon har yanxu bata gama wartsakewa ba da dirxar da yayi mata,  yace " ni xan fita inason inbiya gidane in duba Abba yau be fita kasuwa ba wai kansa ke ciwo"  tace to  Allah ya sawaqe,  kai mai sannu. 


Sannan tace " Dan Allah ka siyo wake so nake inyi wake da shinkafa" sai da yakai qofar fita sannan ya cillo mata 30 naira yace gashinan ki sayi waken,  yasa kai ya fice.


Tai tsam tana tunani,  naira talatin ai ko wake gwangwani daya baxata sai mata ba duba da yacce rayuwa tai tsada yanxu. 

Tunda aka kawota gidan Badaru bai taba daukan ko naira biyar ya bata ba,  da sunan kudin cefane ko kudin wani abun daban.  Duk da cewa baya kawo kayan miya ko nama,  tunda ya aciye abinci da maggi me star sai jarkar mai kings sai gishiri be kuma kawo komai ba. 


Tunda miyar da momy ta kawo mata ta qare,  bata qara sa kayan miya a idonta ba, sai da ta gaji dan kanta da cin abinci da mai da yaji (duk da cewa ada tana marmarin mai da yaji,  lokacin tana cikin gata) taga cewa kanta take cuta tundashi bai cika cin abincin rana a gidan ba,  na dare ma inyaga bai masa ba sai ya fita wajen mai shayi a hada masa da kwai,  ko ya siyo tsire iya cikinsa yaci a gabanta babu tayi,  duk da ko yayi mata tayinma baci take ba.


Da yake gidan amarya baya rabo da yara a hankali yaran unguwar suka fara shiga gidan,  ita kuma tasa hannu bibbiyu ta karbesu bata nuna musu kyama ba,  dan sune yan uwanta yanxu,  cikin shirinta na karbar rayuwa aduk inda tazo mata. 

Wadannan yara su take aika su siyo mata duk abunda take buqata acikin yan kudinta da mama ta bata, wanda little ta kawo mata. Wanda kuma tun daga su maman bata kuma aiko mata da kudiba saboda rashin dan aike.

Amma ta da wata yaxo qarshe akai salary ta saka mata kudi a acctn dinta, kamar yadda suka saba ita da yaya Faty duk wata in sukayi albashi sukan tura mata kudi ta acct dinta,  hakan yasa da wuya ta rasa kudi. Amma yanxu abu 2 yayi mata togaciya daga daukan kudin da suke tura mata. 

Na farko,  ATM dinta da yayi expire wanda dole sai taje ta gyara kafin ta samu hurumin fidda kudi. Na biyu kuma shine takunkumin da Badaru ya qaqaba mata,  domin tun sati 2 da xuwanta gidansa ta tambayi xuwa kitso yace mata baya cikin tsarinsa fitar matarsa daga gidan aure inbada lalura ba,  kuma koda xata fita ma yanaga sai ta shekara a gidansa.  Wannan shine dalilin da yasa ko daxu da yace zashi gida duba Abbansa batace xata bishi ba,  saboda yace wannan shine tsarinsa. 


Da yake ance me dá wawa, saboda jan yayansu da take ajiki yasa be kitson take xuwa har gida tai mata kitson da baya wuce kwana 5 ya tuje saboda Kullum cikin xubawa kai ruwa take da kuma yanayin halittar gashinta, domin kanta shampoo din da tayi da biki ya dade da fita,  kuma bata da wani man shammpoo din da take amfani dashi (mega growth) domin kaf cosmetics din lefenta ba irin wanda take amfani dasu bane,  kuma yawanci anrabar dasu ga dangi (kamar yadda akeyi a al adance).


Kudin hannunta sune kayan miya, siyan salak in buqatar cin salak din ta taso,  sune biyan kudin kitso da kuma siyan sabulun wanki. Domin akan idonta Badaru kan hada wankinsa ya bayar a wanko a gogo masa, amma bai taba hadawa da nata ba.  Gashi ita kuma bata iya wanki ba zata iya cewa tunda take bata taba wanke kayanta na sawa ba,  iyakacin wankinta undis suma a washing machine take watsasu ta wanke.


Duk da cewa Badaru yasan bai taba kawo kayan miya gidansa ba,  hakan baya hana in yaga anyi abinci da miya koma har da nama ya zauna ya take tumbinsa,  kusan ma bayacin abincin gidan sai yaga Cima da canja maana anyi me dadi,  Ko kunya bayaji ko kuma ya tambayi ina akasamu kayan girkin saboda tsabar San banxa (san banxa mesa gidan yari cika 🙄😄). 


Yau da gobe tafi qarfin wasa kuma xara bata barin dami dan haka kudin hannunta bai gaxa 800 ba, dan haka ta tambayeshi ya bada kudin wake (abunda bata taba yiba, wato tambayar Badaru abu koda kuwa haqqinsa ne yayi).  Acikin wannan 800 din data rage mata tanason siyan pad dan lokacinta ya kusa,  ga siyan sabulun wanki ga, ga kudin wankin,  sannan ga kanta ya dameta ya cika ya sarsarqe alamun yana buqatar shampoo, amma da yake hakan bata samuwa dole ta biya kudi a kitse matashi. Gashi tanason siyan wake ta hada a dahuwar shinkafa dan tagaji dacin fara da mai. 


Atake a gurin ta samowa kanta solution,  domin kudin bazasu isheta ba,  saboda haka ta yanke shawarar siyan always (pad) tunda ita dole ce,  kasancewarta mace me xubar da jini a lokacin al ada yasa sinqi daya bata isarta sai daya da rabi ko biyu.   Yanxu da rayuwa taxo mata a haka ta yanke shawarar hadawa da tsumma, ragowar kudin xata sai sabulun wanki tai wankin da kanta tunda ba kudin kai wankau, sannnan ta bada kudin kitso ai mata kitso ragowar kudin ta sai wake ta dafa a shinkafa. 


Rayuwa kenan abar tsoro wai yau maryam ce da wanki. Ahankali ta furta "rayuwa ce wataran sai lbr, dama aure a 2 ne ko kaci gaba ko kaci baya." 

Tana kaiwa nan a tunaninta ta miqe ta fara aiwatar da abunda ta shirya.


Badaru bayan ya isa gidansu ya duba jikin Abbansa,  yana zaune suna dan taba hira da Abban ummansu take gefe sai kallonsa take asace,  saboda kunya irin ta dan fari.  

Can dai ta kalleshi tace ina wajen su maryam din?  Yace ko lfy,  ai canake da ita xakuxo duba alh? 

Yayi saurin cewa tananan qalau tace ma a gaisheshi da jiki,  ni banason gantaline a tsarina banason matata ta fita. 


To sannu me mata hakan yayi dai dai mara kunya inji Umma.  Sannan ta dora da cewa " ai wannan yarinya Allah ya saka mata da alkhairi,  ta gyaraka kayi tas kayi jajur da kai har wata teba ka ajiye.  Wannan yarinya ta samu tarbiyyar Allah ya sakawa iyayenta da alkhairi" ta kalli abbansu Badarun sannan tace "wlh Alh tunda mukaje yarinyar nan take hidima damu ta kawo wannan ta kawo wancan,  sannan ta samu hijabi ta saka a jikinta har muka taho bata cire ba,  muna kan kujera tana qasa idanunta a qasa. Aini Alh banzaci acikin yaran yanxu masu xurfin karatun boko akwai irin maryam ba,  haka in su Aisha (yayanta mata) sukaje mata take hidima dasu da yayansu inzasu taho,  tabawa wannan mayafi wannan takalmi kai gashinan dai abun sai San barka"


Alh inuwa ya dubeta yayi murmushi sannan yace lallai kaltume wannan suruka taki tayi miki 😊 dan naga kullum in muka zauna sai kinyi bitar ahalayenta. 

Tai saurin cafewa da cewa wlh kam tayimun,  ai maryama ta haifu yarinyar yar halak ce,  ni da Xaiji shawara ma ai daya haqura da Nafeesan yayi xamansa da wannan dan ni kam maryam tafi kwantamun.


Badaru yaji maganar kamar saukar aradu ya dago a razane 😳, yace Umma in haqura fa kikace?  Shekara nawa Nafee na jirana?  Innaqi auranta na yaudareta,  Kuma bayan haka ma ina sonta baxan iya haqura da itaba. 


Umman ta watsa masa harara tare da cewa "ai tare aka hallicceku shiyasa bazaka iya haquri ba"


Abba yayi saurin katsesu kafin maganar tayi nisa yace "ya isa kaltume,  ki gyaleshi tunda yana sonta.  Maryam din ma da za a aurota ai saida kika nuna turjiya,  amma yanxu kinfi kowa yaban halinta.  Itama wannan kikasan nata kyawun halin?" 

Umma dai ta tabe baki tare da cewa Allah ya bada sa a 😏



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣2⃣

Dedicated to 
Maryam Baita


Watanta biyu dai-dai a gidan, xuwa wannan lokaci ta saba da wahala,  duk cewa ance ba'a sabo da wuya.


A bangare guda kuma tana cikin matsananciyar wahalar  auratayya da Badaru. Irin yanda duk wata amarya da takai budurcinta gidan miji ke fuskanta a farkon aure. Ta wahala iya wahala saboda kwanciyar aure da Badaru tafi komai jigatar da Mimi.


Ga wani irin ciwon qirji da yake yawan fyadeta,  saboda bacin rai da rashin cima mai dadi (mai da yaji). Tuni maganinta na numfashi ya qare,  kuma tun kafin maganin ya qare intasha baya yimata aiki.  Ga uwa uba zafi dakesa koda yaushe cikin daukewar numfashi take,  saboda Sam yanayin ciwonta bayason zafi. Badaru kuma baya tada inji saiya dawo kuma duk inda 11 tai zai kashe yayi baccinsa inda ita kuma xata kwana fiffita da hand fan dan kiyaye lfy ta.


Babban abunda yafi damunta kuma shine; duk wannan hali da take ciki baisa Badaru ya tausaya mata yace taje asibiti ba, ko ya kaita.  Hasali ma haka yake shafe tsawon lokaci yana auratayya da ita cikin shauqi da sambatu.  Baya gajiya da abu daya wani lokacin sai yaga bata numfashi sannan yake saurara mata.


Bacin rai,  yunwa,  zafi da rashin kwanciyar hankali ya hadu ya saukar mata da wani irin matsanancin ciwon qirji. Wanda ya kwantar da ita wanwar ko sallah sai dai tayi zaune,  aikin gida kuma in su abuwa (yaran maqota dake shigo mata) sunxo suke yimata,  babban abin takaicin shine bata da ko naira 5 din siyan ruwan pure water.  Wayarta ma kona plashing babu. 


Yau monday,  wanda ta kama kwananta 3 da kwanciya wanwar saboda nauyin qirji da daukewar numfashi.  Ya xamana ko kwanciyar ta gagara sai dai tai ruf da ciki ta danne qirjinta saboda ji take kamar inbata danne dinba zai tarwatse. Daga waje kuwa kana iya jiyo hakin da take.


A haka Badaru yazo cikin shirin fita, yana balle botiran rigarsa, ya kalleta a wulaqance tana kwance ruf da ciki a kan centre carpet din parlon yace 'bakisan wannan kwanciyar babu kyau ba a musulunce?' sannan ya dora "nifa banason langwai kin cika gida da gurnani sai kace tsohuwar kafura wai ke ciwo ko?  To wlh wannan ciwon da kike rashin dogaro da Allah ya kawo miki shi"  (kunji jahili 😒). Yana ida fadar haka ya sa kai ya fice dan tsabar rashin tausayi da tsaurin xuciya.


Ta share hawayenta, aranta tana ayyana ko maqiyinta bazata so Allah ya jarrabeshi da qaddarar abokin zama me taurin zuciya irin Badaru ba.  Kansa kawai ya sani gashi da manmaqo da masifar rowa.


Tananan kwance har yamma,  xuwa lokacin ta ida jigata.  Sai dai in lokacin sallah yayi takan samu sauqi a dabi ance,  saboda tasa sallar aranta.  


Bayan idar da sallah ta jawo wayarta cikin qarfin hali da jan numfashi dakyar. Tana tunanin wanda xata kira,  shin mama xata kira ta fada bata da lfy,  ta daga mata hankali?  Ko yaya Faty data watsar da ita ta nuna batayinta xata kira? (duk kuwa da cewa Faty na kiranta a waya itace bata dauka saboda ta gaji da jin uxurin Faty akan rashin xuwanta gidanta, kawai ta dauki Faty a matsayin wacce bata santa a yanxu)  dole dai mama da Faty sune dolenta (ranar naka sai naka) 


Yaya Ahmad mijin Faty yayi saurin fado mata ta jawo wayarta tai masa pls call me,  kafin ta aje wayar ya kirata. 


Ta dauka "assalamu alaikum ya Ahmad " ya amsa sallamar "mimina kina lfy?  Ya naji muryarki haka? " ya fada agigice.  "bani da lfy ne shine nace dan Allah ko zaka taimakamun kaiwa Badaru magana ya kaini asibiti" ta fada a wahale.  "subhanallah sannu Mimi bari muga ya za ai?   Sannu autarmu" da haka ya kashe wayar.  


Ya tashi ya shiga bedroom gurin Faty dake zaune (yau aikin safe tayi shiyasa take gida a wannan lokacin) ya kalleta tare da cewa "fadima meyasa bakyajin maganata ne?  Inashan fada miki kece babba karkiyi abunda zai bata xumuncinku da Mimi,  na fada miki mama har fushi tayi dake akan rashin zuwa kiga halin da Mimi ke ciki,  amma duk kinqi ji ko?  To yanxu Mimi ta kirani bata da lfy kuma ga dukkan alamu tanajin jiki,  babban abun takaicin shine: mijinta yaqi kaita asibiti,  daya takaicin shine;  ko zancenki batai ba a wayar, wanda hakan ke nuna cewa ta watsar dake kamar yadda kikai mata" yana kaiwa nan a maganarsa yasa kai ya fita. 



Tunda ya furta Mimi babu lfy  kuma ta kirashi a waya,  Faty take a fingice. Ta tashi tabi bayan Ahmad da gudu ta fada jikinsa ta baya ta rumgumeshi tare da sakin kuka "yaya kace Mimi bata tambayeni ba?  Kace Mimi bata da lfy?  Yaya wlh tausayin Mimi da halin da xan ganta ciki ya hanani xuwa gurinta, bawai bijerewa umarninka dana mama ba. Yaya banason mijin Mimi tunda Mimi bata sonsa" ya dagota ya juyo da ita yana share mata hawaye,  yace "my luv, bata wannan hanyar xaki nuna tausayin Mimi ba,  neman kusanci da ita da maganta mata matsalarta da kwantar mata da hankali shine hanyar tausayinki da soyayyarki gareta" tace naji kuma xanyi yadda kace "  duk a rude take wannan magana. 


Ta shiga daki ta dakko mayafinta da key din mota ta fito,  ya kalleta ina zaki?  "Gidan Mimi " ta bashi amsa direct.  Yace a a bari insa ta turo no mijin nata infara yi masa magana tukun.  Tai rau -rau  tace 'yaya Mimi babu lfy kace in tsaya injira ayiwa wannan wawan waya?  Mimita cefa ba lfy?  Ka bari inje xanyi duk abunda ya dace" yace "to my luv sai kin dawo kibi komai a hankali karki abunda xaki xubar da mutuncinki a gurinsa,  kuma matarsa ce ya fimu iko akanta"  ta gyada kai tare da ficewa. 



Lokacin da ta isa gidan Mimi yamma tayi sosai,  domin har Badaru ya dawo. Ta dunga kwada sallama Mimi na parlo a kwance tana jinta tai mata shiru,  yayin da Badaru dake cikin bedroom yaji sallmar kuma yaji Mimi bata amsa ba ya fito.  Lokacin Faty ta gaji da jiran a amsa mata sallama har ta shigo parlon,  Mimi kuwa tanajin ta shigo ta juya baya tabar kallon qofa,  ta fuskanci kujerar parlon.  Badaru yana tsaye yana ganin ikon Allah,  shidai yasan Faty yar uwar Mimi ce,  kuma a dan iya xamansu da Mimi bai taba ganin tayiwa wani haka ba koda kuwa batasanshi ba,  balle Faty yar uwarta. 


Faty bata kula da wanxuwar Badaru ba dake kofar bedroom riqe da cotton (labule) ba, saboda gigitar halin ko in kula da Faty tai akanta. 


Jikinta a sanyaye tasa gwiwarta kan centre carpet din dake parlon ta marairaice tace "Mimi na tuba,  karkiyimun hukunci irin wannan,  bazan iya jure rashinki gareni ba. 



Mimi ba tare da ta juyo ba,  tace "ai tunda kika iya jure 2 month baki ganni ba kuma baki damuba hakan na nuna kin yanke alaqa tsakaninmu,  shiyasa nima na cireki a raina kuma ban nemi taimakonki ba.  Duk mutumin daka rayu tsahon wata biyu babushi wannan sheda ce dake nuna cewa ko babushi xaka iya rayuwa"


Faty ta fashe da kuka "MARYAM karki bari shedan yayi tasiri a xuciyarki,  kinfi kowa sanin cewa duk halin da kike bazan gujeki ba.  Kuma duk tsahon lokacinnan wlh dake nake kwana nake tsahi,  Mimi kinsan dalilin da yasa banxo gurinki ba,  sai dai kiqi gasgata dalilin nawa.  Mimi wallahil azim ko yayan dana haifa banai musu soyayyar da nake miki, saboda duk duniya bani da yar uwa uwa daya uba daya saike" 


Mimi taji wani irin mugun tausayin Faty ya kamata amma ta danne saboda tanason hora Faty akan karta qara yimata haka anan gaba tace "yaya Faty ki tashi kije gidanki,  nasan dake na naimi yaya Ahmad ban nemeki ba kuma da nasan ke zai turo da ban nemi ya taimakamun ba" duk tana wannan maganar ne a juye (ta bawa Faty baya). 


Parlon yayi tsit na tsawon 5 minutes.  Mimi da taji shirun yayi yawa ta juyo a zatonta Faty tayi fushi ta tafi.  Amma me?   Sai tayi arba da Faty tana tsugune tana hawaye. 


Ta qura fatyn ido itama tana hawayen,  ita kuwa Faty ganin yadda Mimi ta lalace ta kade yasa ta qara sautin kukanta cike da nadamar rashin xuwa taga lfyr mimin. 


Cikin kuma Faty tace "#FATIMARYAM# bazasu taba rabuwa ba,  bazasuyi fushi da junansu ba,  matsalar Faty ta Maryam ce,  matsalar maryam ta Faty ce. Mimi wannan shine alwashin mama akanmu,  karki karya alqawarinnan tun yanxu 😪" 



Mimi najin haka ta taho da rarrafe domin babu qarfin tashi,  taje ta rungume Faty.  Faty ma qanqame Mimi tayi kamar xata maidata ciki.


Suka dunga a jiyar xuciya xuciya a tare,  Faty ta dunga sharewa Mimi hawayenta sannan ta kwantar da Mimi a qirjinta kamar yarinya tana shafa kanta alamar lallashi. 


Badaru yana tsaye,  yana kallon dramar su,  kamar masu shirin film.  Aransa yace dama akwai irin wannan soyayyar yan uwantaka?  Lallai yarannan suna san junansu. 


Ya juya da nufin komawa daki,  motsinsa ya sanar dasu wanxuwarsa a gurin,  yayi saurin cewa da Faty "haj Faty barka da xuwa,  ina wuni? " dan haka kawai yaji ta masa kwarjini duk da cewa xai girmeta da kadan ko kuma suyi sa anni. 


Ta kalleshi cikin tsana, sannan ta kalli yar uwarta dake kwance kan cinyarta.  Yayi tas yayi qiba yayin da Mimi ta tsummace da qare kamar me jinyar shekaru da yawa. Ta amsa gaisuwarsa sannan ta dora da cewa " ranka ya dade ya akai akabar Mimi ciwo yaci qarfinta haka?  Ciwon Mimi fa ciwone me hadarin gaske kuma yana da alaqa da xuciya,  duk sanda ciwonta ya tashi inbai samu kulawar gaggawa ba hakan kan iya jawowa arasa rai.  Kuma babbar abunda ke motsa lalurar Mimi bacin rai"


Yayi wuqi wuqi, yana kame kame da bawa Faty haquri.  Tace to gobe da sassafe xanxo in kaita asibiti dan naga abun yayi worst,  xansa ayi mata booking tun yanxu. 


Cikin kunya yace "to Allah ya kaimu,  Allah ya bata lfy kuma za a kiyaye in shaa Allahu"


Ganin magariba ta kawo kai yasa Faty tai nufin tafiya,  ta karanci matsalar Mimi harda yunwa aciki. Sannan ko zafin wannan gidan ya isa ya tashi ciwon Mimi. 


Mimi kamar tabi Faty takeji,  kuma ganin yar uwarta da daidaitawarsu yasa tasamu rangwamen ciwon. Faty ta lallabata da cewa tayi haquri gobe da asuba xataxo kuma,  tayi wanka ta shirya kafin taxo din. 



Fitar Faty befi da minti 15 ba wani yaro ya shigo da leda yace gashi inji wata mata fara a mota tace abawa maryam.  Ta karba ta bude taga freshyoo me sanyi qarara guda uku. 


Atake ta bude ta shanye daya,  sanyin ya ratsata ta kuma bude wani tasha rabi sannan taji ta qoshi.  Tayi hamdala tare da cewa "Allah sarki dan uwa rabin jiki"


Da xumudi ta kwana, saboda tana murna gobe xata fita bayan wata biyu a kulle a gida. 


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣3⃣

Dedicated to 
Maryam Baita

    Asubar fari Faty ta gama shirinta na tafiya, har breakfast ta hadawa Mimi. Taiwa Ahmad sallama ya kawo kudi ya bata da nufin taiwa Mimi amfani dasu a asibiti.


5:30 AM agidan Mimi tai mata,  ta samu Mimi tayi wanka amma tana zaune bakin gado bata shirya ba saboda jikin ya motsa mata.  Suka gaisa da Badaru ta shiga cikin daki.


Haka ta dunga bincika drawern Mimi da nufin dubo mata kayan da zata saka, domin duk kayan sun yamutse (anyi wanki babu guga). Gashi kayan sai qarnin sabulun wanki suke.  Dakyar ta samowa Mimi zani da dankwalin atamfar dutch wax (holland) da shirt (domin rigar atamfar tayi mata yawa saboda ramar da tayi) ta saka. Ta dakko humra ta zazzga ta murxa a jikinta (domin humrar kadai take dashi,  turarurrukanta tuni sun qare,  dan bata saka turare daya tafi gane ta hada kaloli da yawa.  Kuma da Badaru suka hadu suka qarar tunda shikam baya siyan turare ya saka  sai da yaga Mimi dashi ya tayata suka qarar anga banxa 🤣) ta dan gyara fuskarta, ta hade kitson kanta tasa ribbon. Ta yafa mayafi kumar suka fito. 

Suka tadda Badaru a parlour ya dakko 500 ya bawa Mimi tare da cewa "ga wannan ku riqe ko za'a buqaci wani abun" Faty tai saurin cewa "no bashshi babu abunda xai gagara da ixinin Allah" .


Bakwai a AKTH (Aminu kano teaching hospital) tai musu inda Faty ke aiki. koda likita yaxo ita ya fara gani saboda sanayya da kuma booking din da sukai.


Suka gaisa da Faty likitan mai barkwanci,  yana duban Mimi ya duba file dinta dake gabansa yace " fatima kina da wannan African queen din shine baki bani na aura ba? "  Faty tai murmushi tace "Dr babu rabone shiyasa baku taba haduwa ba, amma Mimi ai tana xuwa nan"


Ya duba record din ciwon Mimi,  yace "maryam meyasa kike sa damuwa a ranki?  Bakisan ciwonki bayason damuwa ba? ". Mimi dai shiru tai masa kanta na qasa.


Ya rubuta allura yace Faty taje ta karbo yanxu a pharmacy  ta kawo masa xai mata.  Allurar 9k ce saboda haka ya rubuta note,  dan acikin albashinsa xa a cire. Faty ta dunga yi masa godiyar karamcin da yayi mata,  yace bakomi ai zaman tare ne ya kawo.


Bayan fitarta, nasiha ya dunga yiwa Mimi cikin hikima. Duk cewa baisan matsalarta ba. Suna haka Faty ta dawo,  ya fasa allurar ya nemi jijiyar hannu yayi mata,  sannan ya buqaci ta zauna ta huta xuwa 10 minute saboda allurar nada qarfi.



Cikin qanqanin lokaci,  Mimi taji nauyin da qirjinta yayi ya sauka,  numfashinta ya koma fita normal.  Ta dago ta dubi likitan tace "nagode Allah ya biyaka da gidan aljannah naji dadi". Yayi murmushi yawwa maryam nagode da addu a Allah ya qara sauqi,  suka dauki takardar magunguna suka fita.


Suka tsaya cikin asibitin suka sai magunguna. Sannan Faty ta tsaya ATM ta ciri kudi suka tafi.  Ta miqawa Mimi travelling mug cike da tea murtuk dashi (hadin kauri inji Mal kabiru dadin kowa 😂) tace shanye.  Mimi ba musu ta shanye domin tana ganin shayin yawunta ya tsinke domin rabonta da shayi da madara tun madarar amarci. Bayan ta gama sha ta miqa mata food warmer cike da soyayyar doya da kwai da miyar qoda a gefe. Tace "kici ki qoshi dan ba gida xan 
kaiki ba". Taci doyar ta qoshi nak,  atake wata nutsuwa ta saukar mata.  Lallai ta yarda matsalarta harda yunwa a ciki. 


Direct zoo road ta tsaya inda Mimi keyin saloon,  ta ajeta tace a gyara gashinta a wanke mata qafa, sannan ta tafi tace xataje ta dawo.


Suka taya Mimi ta tsefe kan,  aka shamfe shi,  sannan aka dora da steaming. Akai mata gyaran fuska (cire gashin fuska)  ba abunda bai buqatar gyara,  nan da nan saiga Mimi tayi tar fuskar ta washe. 


Ana wanke mata qafa Faty ta dawo, ana gamawa ta biya kudin suka tafi. Direct shoprite suka nufa,  suka fara da gurin electronics Faty ta sayi reachargable fan (fankan da akewa chaji).  Sannan suka shiga gurin provision tace Mimi ta dau duk abunda take buqata,  dake Mimi tasan ko bata dauka ba Faty fada xatai mata shiyasa tadau duk abunda tasan tana da buqatarsu, kamarsu : mayan robobin madara da milo,  omo,  sugar, pads, toothpaste, cookies da sauran kayan amfanin gida. Faty ta qara mata da wasu kayan shayin irin na sachet da catoon din cake da caton din freshyo da su malt da exotic duk catons.  Ta kalli Faty cikin soyayyar yan uwantaka tace "ya Faty basu yawa ba kuwa?  Karba ki dorawa kanki wahala" ta kalleta tace "Mimi yanxu dan na miki abu ya xama wahala kenan? Yaushe muka fara haka dake? Ta dafa kafadarta tace,  Mimi ina qaunarki mu kadai mama ta haifa,  ina roqon Allah indai xai bani abunda bazan Mora miki ba kada ya bani shi ko menene" Mimi tai saurin fadawa jikin Faty suka qanqame juna. Kudi sosai ta biya na siyayyar da sukai,  sannan suka dau hanya. 


Lokacin da suka isa gidan Faty qarfe biyun rana, adaddafe tayi sallah sabida yunwa dake damunta.  Tana idar da sallah taje kan dining table,  ta cika plate da jellof din macaroni da hadin salad tayi tai qat ta dora da pepper soup.  Duk abunda take Faty na ankare da ita,  tabbas Badaru yana yiwa Mimi horon yunwa domin ada Mimi bata cikin jerin mata masu cin abinci, amma yanxu har mamakin cin da Mimi tayi take. 


Abincin yana fada mata ta nutse akan royal bed din Faty wanda yasha shinfidu tausasa na alfarma, sanyin AC na ratsata tayi bacci me dadin gaske.

Bata farka ba sai 5:16 pm tayi salati,  tare da miqa.  A gaggauce ta shiga bandaki ganin lokacin sallah ya qure.  Sai dai tana cire pant dinta da nufin yin wanka ta tarar period dinta yaxo,  duk kuwa da cewa lokacinta yayi har ya wuce batai ba.  Tai mamakin xuwan period din ba tare da ciwon mara ba,  ko hakan yana nasaba da allurar da akai mata oho? Ta dakko shaving cream (veet) ta shafa a jikinta ta qalqale gashin. Ta salla wankanta da mayukan wanka da subulai, ta dauki sabon pant a drawer ta manna pad ta saka.  Ta gyare jikinta da mayuka da perfumes masu sanyin qamshi, ta dauki doguwar rigar atamfa a kayan Faty ta saka.  Tai mata cif sakamakon ramar da tayi, ta danyi simple make up ta fito tas da ita. 


Ta iske Faty da Ahmad da yaran zaune a parlour suna kallon drama (madhubala) a mbcbollywood.  Tace "ya Faty har lokaci yaja haka baki tasheni ba? Tace "sry Mimi shigata biyu da nufin in tasheki saina tarar baccin ya muki dadi shiyasa na gyaleki.  Ta samu guri kusa da Faty ta zauna,  suka gaisa da Ahmad, ya jajanta mata jikin sannan ya zarce da yi mata nasiha.  Dan har ga Allah yanason Mimi ganinta yake kamar uwa daya uba daya suke, tunda shi bashi da yan uwa.  


Taje fridge ta dakko robar ice cream ta dawo ta xauna tanasha suna hira.  Ji take kamar karta tafi dan xaman yayi mata dadi.  Ahmad ya kalli Faty yace,  tashi ki kaita gida kada muyi rashin hankali.  Faty ta yunqura tare da miqawa Mimi wata leda tace kinga a siyayyar da mukai kin manta baki dauki masuka da turare ba shine na koma na siyo miki" Mimi ta leqa ledar taga muyakan da take amfani dasu ne cocoa butter (palmers)  Set dinsa har sabulunsa sai turaren da take amfani dashi da sure na feshi da sauran spray.  Ta dunga godia.


Sai da Ahmad ya bata 10k,  sannan ya jaddada mata duk sanda take buqatar taimako ta fada,  kada ta qara zama ciwo yaci jikinta haka.  Saida Ahmad ya temaka suka saka kayan a mota saboda kayan da yawa.  Har sun fara tafiya Faty ta tuna da fankar da tasa chaji,  ta dawo ta dauka. Suna tafiya suna hira cikin nishadi ta dauki jakar Mimi ta saka mata ledar magungunan da suka siya tare da kudi sannan ta qara da cewa gashinan ki kula,  ki rabu da namiji ki dainasa baqin cikinsa a ranki, lfy tafi komai kuma shi kansa inbaki da lfy bazai zauna dake ba,  so dat ki lallaba lfyarki.  


Suka tsaya yahuxa suya dake kabuga ta sai mata kaza da furar habib.  Kafin suje gida anyi sallar magruba saboda sun tarar da hold up.  


Suna gama shiga da kayan Faty ta juya gida.  Mimi da bata sallah xataiba da kimtsa kayan takai kowanne muhallin daya dace. Tana zaune tana lazimi aka kira sallar isha ta tashi tasa kayan bacci dan jikinta fes yake bata buqatar wanka.  Bata damu da dawowar Badaru ba domin ya kunna inji,  ta kunna fankarta wacce tai chaji full.  Iskar fankar na kada ta tana danna waya (chating)  a zuciyarta cewa take "Allah ya sakawa yaya Faty da alkhairi badan taimakonta ba da tuni ina zaune cikin zafi. 


Takwas nayi ta balli maganinta tasha dama tana timing. Ta janyo kazarta ta bude ta fara ci da bisimillah. Qarar injin da taji ya tabbatar mata da dawowar Badaru, ya shigo dakin yayi tozali da Mimi.  Idonsa fes akanta saboda hasken wutar lantarki,  tayi masa kyau ainun kamar sake masa ita akai. 


Yayi saurin qarasawa gabanta tare da cewa "maryam sauki ne ya samu haka da wuri? Sannu" ta danyi murmushi tare da gaisheshi.  Ya amsa idonsa na kan ledar gabanta wanda qamshin kazar ya cika dakin,  yace " harda hidima haka? " ta amsa da cewa "eh yaya Faty ce tasaimun da wannan fankar (ta nuna masa fankar) yace " to madallah haj Faty kenan bataso kudi su zauna lfy" (kuji banxa🤣)


Ba kunya ya tayata suka cinye kazar sukasha furar,  lamarin da yayiwa Mimi dadi.  Domin yaune rana ta farko da suka taba cin abinci kwano daya da Badaru. 


Yana ta kallon Mimi wai ta burgeshi qarshe,  ya kalli qafarta yar dundubus da ita har tafi jikinta haske yatsunta kansu abun kallone be taba lura Mimi takai haka ba sai yau (dama ya xa ai kasani?  Wahalar gidanka tasa tayi kaushi) ya ruqo hannunta yana murxawa cikin shauqi "maryam tashi muyi shirin kwanciya" ya fada yana mai qura mata ido.  Azuciyarta tai masa dariyar mugunta,  saboda tasan bata da tsarki. 


Ba musu ta miqe taje tai brush,  shima ganin tayi yaje yayi amma ba batun wanka duk kuwa da tsamin ranar da yake.  Ta feshe jikinta da turare ta kwanta hankalita kwance yau ba kawo farmaki 😜. 


Tayi mamaki kwarai da taji ya kashe inji,  ya shigo dakin yana me cewa tunda ga fanka ai sai man injin ya huta. Yana hawa gadon ya kamata ya rungume yana shafar gashin kanta yana cewa "maryam kinada shiga rai,  komai naki me kyau ne" tadan motsa bakinta cikin sigar murmushi har dimple dinta ya lotsa.  Lamarin da Badaru yaji ba abunda yake muradi illah ya hada bakinsa da nata.  Amma yasan bazata yadda ba shiyasa beyi yunqurun hakan ba,  domin yau hakanan yaji bayason batawa maryam rai. 


Ganin abun nasa yana nisa yasa tace masa bata da tsarki,  atake ya saki wani mugun tsaki tare da tureta daga Jikinsa,  ya koma gefe ya kwanta.  Dama hakan take jira dan haka ta gyara kwanciyarta ta maida fankar dai dai saitinta tai adduar kwanciya bacci.



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣4⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)


Tasamu canjin rayuwa saboda taimakon Faty,  ta rabu da matsalar zafi saboda fankar da Faty ta sai mata. Koda babu wuta takan bada fankar da 50 naira akai mata wani company dake bayan gidanta kadan mai gadin gurin ya karbi hamsin din yasamata caji,  saboda company ne basa rabo da wuta.  


Sai dai da yake rayuwa indai kai imani baka rasa jarrabawar ubangiji,  sai wata sabuwar matsalar da bullo mata.  Matsalar kuwa itace;  kawo abokai da Badaru ya tsiriyi cikin gidan saboda yaga cimar gidansa ta canja (ansamu mai dadi).


Ba kawo abokan nasa ne problem dinba ko kuma abunda zasuci,  cin mutunci da toxarcin da Badaru keyi mata agaban abokan nasa shine babbar matsalar. 


Sau tari zai cika gidan da abokansa duk kuwa da qanqantar gidan,  wanda hakan ke hanata sakewa sai dai ta takure kanta adaki.  In fita parlour ta kamata ko duba girki sai dai ta saka hijabi, har mamakin inda ilimin addininsa yake take domin babu addini sam acikin abunda yake, kodan ya takura mata yake hakan?  Sannan bayan tayi hidima dasu da jikinta da aljihunta (domin babu ko sisinsa aciki) sai kuma ya dunga zaburarta yana daka mata tsawa agabansu,  a qoqarinsa na nunawa abokansa cewa ita din bata isa komai ba. 


Yauma hakace ta kasance,  domin tare suka shigo da wani abokinsa sani around 5;30 pm.  Suka taddata zaune parlour ta tasa fanka agaba tana shan iska,  a xuciyarta bata gajiya da yiwa wacce ta sai mata fankar adduar alkhairi (ya Faty) 


Tai saurin miqewa ta shige daki da nufin suturta jikinta,  domin shimice kawai a jikin nata.  "kinaji ana sallama dan rainin hankali baxaki amsaba" cewar Badaru.  Sani abokinsa yayi saurin tareshi da cewa "bakaga hijabi zata dakko ba,  laifinane dana shigo kai tsaye ban tunanin halin da xan taddata ba" ta fito sanye da jihab me hannu tana cewa "sannunku da xuwa" ta gaishe da Sani, sannan ta nufi kitchen ta qara sanwar abinci dan ganin baqo,  ta debo musu ruwa da kwalin exotic ta dora akan tray ta glass cups ta kawo ta koma daki ta zauna. 


Tananan zaune tana yan danne dannen waya taji xuwan wasu abokan nasa har su 3 domin taji ya ambaci sunayensu.  A xuciyarta tace yau kuma anan xa ai mana zaman majalisar kenan. 


Ta tashi domin ta duba abincin data dora,  ta gaishesu ta wuce kitchen.  Ta gama komai ta maida miyar kan gas domin ta qara dumamata ta jiyo Badaru na kwala mata kira,  ta fito parlour ta dan durqusa gefensa "gani" ya dubeta yana wani daga hanci yace " ke wace irin mahaukaciyar mace ce mara tsari?  Bakiga nayi baqi bane?  Ko sai nace ki qaro wasu kofunan da lemon? Banason dabbanci."  Ba tare da tace komai ba ta miqe taje ta kawo  wani kwalin lemon da kofuna ta ajiye,  tana shirin juyawa yace " abincin ma sai nace ki kawo ko?  To karki kawo" tai saurin xuba abincin a warmers har tana qonewa saboda kar wani cin mutuncin ya biyo baya.  Domin tana jiwo shewar abokan nasa,  suna yaba masa yadda yake tafi da ita.  Har wani a cikinsu wanda bazata iya gane kowaye ba yana cewa "da kyau mutumina haka akeson mutum ya xama jan wuya a gidansa"



Ta hada musu komai na abincin a gabansu, sai da ta tabbatar ta hada komai sannan ta nufi daki.  Badaru yayi saurin katseta da cewa "waye bawan gidanku anan dazai zuba musu? " ta duqa a takure take saboda kallon da wasu acikinsu suke mata,  xata fara xubawa Sani yayi saurin katseta da cewa "a a jeki maryam mungode  kowa zai xuba nasa" dan ya lura a kunyace takeyin komai. 


Badaru yace "a a ta xubawa kowa umarnina ne,  ni naga damar haka.  Tana gama xubawa ta miqe ta shige daki.  Sani ya dubeshi ransa adan bace " ka daina haka Badaru,  wannan yarinyar kyautace Allah ya baka ka riqeta da amana ku zauna lfy.  Yawanci yaran yanxu basu cika bin miji haka ba,  bare ita da take da xurfin ilimi" Badaru ya daga murya,  domin yanaso Mimi ta jiyo abunda zaice "yo ni ina ruwana da ilimin mutum,  ko parpesa ce ita bai dameni ba domin miji ta rasa na taimaka mata na aureta,  inba dan nidinba da tuni tanacan a jabe gidan ubanta"  




Yayi sa a kuwa domin duk maganar da suke akan kunnen mimin sukayi saboda tana da ji sosai,  kuma dakin bashi da xurfi. Hawaye ya wanke mata fuska,  lallai yau wulaqancin na Badaru yafi na koyaushe.  Muryar daya daga cikinsu ta katse mata tunani inda yake cewa "au wai kana nufin tana da ilimi? " Badaru ya bashi amsa da cewa "degree      ne da ita akan fannin sharia" wanda yayi tambayar yace "Tab ai wlh gwanda daka riqe mata wuta daka sake mata rainaka zatayi musamman intasan tafika ilimi mata yan boko mugayen yan rainin wayo ne.  Kai kuma sani da kake wani xance ai mata xuma ne da wuta ake cinsu" Sani ya balla masa harara yace "inkasan ba shawarar arziqi zaka bayar ba ka daina xuga xugagge yana ciwa yar mutane mutunci"



Badaru yayi saurin tareshi cikin hargowa "kaga sani ya isa,  ni ba wani wanda yake zugani haka nayi niyyar tafi da gidana kuma haka nakeyi.  Intaga xata iya xama dani a haka ta zauna, in kuma bazata iya ba sai in mata saki daya taje gidan nasu ta dandana xama taji.  Ai tasan rufa mata asiri nayi,  kaf gidansu ita kadaice budurwar data rage. Sannan tace xata kawomun wani fi ili?  Bokon banxa bokon wofi  meyasa bokon nata be bata mijin aure ba.  Wlh ko shugabar qasa ce ita dole ta bini yadda nakeso intaqi ga hanya nan.  Nasan kina jina MARYAM in bazaki iyaba kixo ki tafi gidan ubanki."


Duk yanda taso danne xuciyarta abun ya gagara kuka take wurjanjan,  batasan yadda akaiba sai ganinta tayi a parlourn adai dai lokacin da yake cewa "ai kinsan yadda kika sha wuya kika zaunu kafin Allah ya kawo miki ni na aureki,  ki qoqari ki kashe auran kina budurwa ma kin rasa miji bare kina BAZAWARA."




Sai a lokacin ya ankara da wanxuwarta a parlourn,  ya kalli idonta da fuskarta gabansa yayi mugun faduwa  domin bai taba ganinta cikin wannan yanayin ba duk abunda yake mata.  



Sani yayi saurin shan gabanta ganin ta nufi qofar fita, a qoqarinsa na dai daitawa,  yace MARYAM Dan Allah dan darajar iyayenki kiyi haquri kar fita.  Ta tsaya cak! Badaru dake gefe ya saukewa boyayyar ajiyar xuciya ganin ta tsaya. 



Sani yace Badaru,  beye lefin yarinyar nan?  Saboda ni kayi haka? Daga gaya maka gaskiya xaka ci mata mutunci haka?  Lefin me tayi maka? 


Mimi ta matso kusa dashi ta kalleshi, yai saurin yin qasa da kansa.  Tace  cikin nutsuwa da qarfin zuciya " kayi haquri qaddarace ta hadamu, amma karka manta kai ka ganni kace kanaso ba talla aka kawo maka niba.  Kuma tabbas miji na rasa shiyasa na aureka,  inba dan haka ba ai babu wacce xataso xama da  namiji irinka.  Kuma da Allah ya hanani miji daga baya ai yabani kai?   To haka nake sakaran duk renda Allah ya sa ka rabu da ni Allah xai bani wani mijin.  Gari da yawa ai maye bayacin kansa Badaru. In shaa Allahu yadda Allah ya doramun jarrabawar xama da kai xai bani ikon cin jarrabawar, wlh nima ba Jin dadin xama dakai nake ba.  Allah ya na madakata yana jiranmu kuma zai mana sharia"



Simi simi daya bayan daya abokan nasa suka fice,  kodan kada aure ya mutu ace ta sillarsu ne.  Ya rage sai Sani kawai,  ya kalleshi yace "yanxu wannan abun da kayi me gari ya waya?  Burgewa kayi? Ka tauna asirin gidanka a idon duniya.   Allah ne kadai yasan inda wannan zancen zai tsaya,  kuma tunda da wata niyya kake kawo abokai gida daga yau babu abokin da xai kuma xuwa gidanka.  Ya juya ga Mimi yace MARYAM kiyi haquri,  anbata miki Allah ya baki haquri ya huci xuciyarki." ya juya ya fita. 




Tunda ta shiga daki bata qara fitowa ba sai da akai kiran magriba ta fito alwala,  ta taddashi zaune a yayi tagumi.  Daganan bata qara fitowa ba har wajen 9:03 taji ya tada inji tayi shirin kwanciya ko wanka bataiba bare cin abinci dan ranta har yanxu a bace yake.  


Tanajin lokacin da yaxo ya kwanta kusa da ita,  tai saurin rintse ido.  Dan jitayi wata irin tsanarsa ta taso mata.  Bata tabbatar da Badaru bashi da kunya ba sai da taji hannunsa a jikinta  yana lalubarta.  A tunaninta yau zai haqura tunda sunyi sabani,  amma ina mayen ya kasa haquri duk kuwa da ya gwada yin haqurin ya kasa.  Tai masa banza taqi bashi fuska,  take banxa ne sai ya fara qoqarin gwada mata qarfi zai shigeta,  a salonsa na kwanciyar awakai.  Ta qanqame jikinta ta hanashi yin hakan,  dole qanwar naqi yayi amfani da lallashi ta hanyar cewa "maryam dan daure ki barni nayi,  na kasa bacci kinsan na riga na saba" sama sama ya samu nutsuwa ba kamar yadda ya saba ba. 




Ya koma gefe ya kwanta yana tunanin da maryam din ta tafi dazu da ya zaiyi?  Dole ya sake taku,  kodan lalurarsa ya xama dole ya zauna da maryam dan bayajin xai iya haqura da buqatarsa koda ta kwana daya ne.  Dan yana sahun mabuqata ga kuma qarin magunguna da yake sha,  bayan haka kuma bai gama more kudinsa ajikin maryam dinba.  



Duk da bata taba turje masa a gurin kwanciya ba sai yau,  amma yana mamakin duk sanda ya batawa maryam rai to ranar baya samun yadda yakeso ajikinta.  Duk da kuwa ba hanashi takeyi ba,  amma duk qoqarinsa baya gamsuwa.  A fili yace dole in gyara lamura na da maryam kodan shimfidata. 


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣5⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Su 3 ne kawai zaune a majalisar,  Badaru,  Mekudi sai wani abokinsu da suke kira KB.  Hira suke yayin da KB ke daga gefensu kadan yana karatun news paper.  Badaru ya kalli Mekudi yace "ya babu lbr ne?  Na jika kwana biyu shiru? " Mekudi yayi wani shu'umin murmushi sannan yace "yo ni ana raba ni da lbr ne? Kamar ka shiga xuciyata ansamo wani be zafi,  amma fa a tube yake ita zaka matsa ka cusawa kafin ka shiga,  sauran bayani kuma xaka bani lbr da kanka.  Ya fada yana daga gira" 


Badaru ya washe baki tare da cewa "Allah mutumina 😄? Yana ina?  Bani " mekudi yadan muskuta tare da cewa " sai dai fa yana da illah,  yakan bata mahaifa ko hana haihuwa gaba daya,  saboda haka ka kula,  amma dadi kam xakaji dadi kamar ka mutu 😜"  Badaru ya miqa masa hannu suka tafa yace " yo ni ina ruwana,  ai dama bandamu in haihu da ita ba,  amfanin ta kashe qishirwata da ita".


KB da tunda suka fara maganar hankalinsa na kansu ya magantu "Badaru me kake shirin aikatawa?  Sirin shimfidarku kake budewa anan? Har kake shirin batawa yarinya mahaifa? to wlh karka soma.  Kai kuma mekudi kaji tsoron Allah ka tuna kana da yaya mata in akaiwa yarka haka xakaji dadi? "  sukai tsit suka sunkuyar da kai,  saboda suna respecting KB dan ya girme musu. 


Suna idar da sallar magriba Mekudi ya tashi tafiya Badaru ya miqe shima tare da cewa " Bari in koma gida nasan tana zaune a duhu ba wuta." 



Yayi saurin tadda mekudi a motar sa yana shirin tashin motar ya bude ya shiga,  ya miqa masa hannu "Bani maganin" mekudi ya sheqe da dariya yace "shege baka haqura ba" shima yayi dariyar tare da cewa "aimu bama wasa da kayan aiki". Ya miqa masa maganin a kwalinsa tare da cewa "ka kula". Badaru ya fito ya shiga tasa motar,  yayi gida yau ko gurin Nafee baya son xuwa tunda ya samu......... 



Mimi tayi mamakin barin jikin da Badaru keyi a kanta yau,  duk da ba sabon abu bane a gurinta sambatunsa a shimfidarsu.  Tana jin lokacin da ya cusa mata wani abu a gabanta.  Tai saurin yunqurawa xata tashi,  yasa hannu ya danneta.  Tace "meka sakamun a jikina?"  cikin rashin nuna kulawa ya bata amsa "xan cuceki ne? To vaseline na saka saboda kin matse da yawa na kasa shigarki" daren ranar ta gurxu a hannun Badaru,  ga wani irin ihu da sambatu da yake tana tsammanin maqota na kusa zasu iya jiyoshi. 



A dan wannan tsakanin Badaru ya xama wani irin qasurgumin jarababbe,  kullum cikin yin abu daya yake.  Ba dare ba rana,  domin da ranar Allah xai baro kasuwa yazo gida ya shafe awanni yana dirxarta.  Kuma in dare yayi ma babu hutu,  sai yayi aqallah sau 3. Ita har mamaki take sam baya gajiya,  zata iya cewa tunda aka kawota gidan Badaru yau kimanin wata hudu kenan (4 month)  bai taba fashin kwanciya da ita ba,  sai dai in period take. 


Lokaci guda ta qare ta lalace,  a xuciyarta take cewa ashe da ba wahala nakesha ba,  yanxu ne nake ainihin wahala.  Gashi dai bata nemi komai ta rasa ba (Faty ta tsaya mata)  amma jarabar Badaru tasa ta xama kamar tsumma.  A gefe guda kuma ga rashin mutuncinsa domin babu abunda ya fasa,  sai ma qaruwa da yayi.  


Sau tari takanyi tunanin matan da suke cewa aure da dadi,  sai ta rasa ta inda sukejin dadin auran, ta xaman takewar gida kota kwamciyar aure?  Domin ita dai tunda suke da Badaru ko na second daya bata tabajin dadin kwanciya ba,  hasali ma axaba takeci ba kadan ba.  Da farkon aurenta tana danganta hakan da rashin sabo,   amma yanxu data dan kwan biyu sai take ganin halittar tace haka.  Ita dai tasan in azabar da takeji ce jin dadin aure sai take ganin ba macen da xatace aure da dadi. 



A lokacin sai takejin babu abunda ta tsana a duk duniya irin sex life (kwanciyar aure).  Duk da gori da qalubale data fuskanta a rayuwarta ta yan matanci sai ta kwammace gara rayuwarta ta gida da wannan rayuwar da take yanxu. 



***    ***       ***     ***


Yau babban baqo garesu,  Badamasi qanin Badaru wanda tunda akai auren bai taba xuwa gidan ba.  Yauma yaxo ne bisa takurawar ummansu. 



Tunda yaxo Mimi keta hidima dashi dakko wannan,  kawo wannan.  Duk da batasan da xuwansa ba, tai masa tarba ta musamman da girkin alfarma.  Tana ta xarya tsakanin parlour da kitchen,  cikin tsawa da umarnin Badaru,  wanda duk fitowar da tayi sai ya nemi wani abun da zaice batai dai dai ba. 


Yanxu ma tafito ne dauke da qaramin tray wanda ta doro cups da lemon happy hour na kwali ta taho,  ya daka mata tsawa da cewa "wai ke komai sai anyi jiranki ne?  Kinsa wani hijabi na munafurci,  wazai kalleki anan?  Ni da babu abunda bansani ba a jikin ki, ko Badamasi dake dan uwana uwa daya uba daya? "   Badamasi ya runtse ido cikin takaicin abunda Badaru yakewa yarinya,  tana qoqarin kare masa mutunci ta hanyar suturta kanta yana kwaye mata baya.  A dan xaman da yayi yanxu ya fuskanci inda aurensu yasa gaba. Shiyasa yaga maryam din duk ta canja,  mace qayatacciya kyakykyawar gaske me fasali amma cikin lokaci kadan ji inda Badaru ya kwararrabata.  Ya gyara xaman wayarsa dake kan hannun kujera, wacce yake recording din duk abunda ke faruwa tun daxu,  da nufin in yakoma gida ya sakawa iyayensu suji yadda Badaru kewa yar mutane. 


Tunaninsa ya katse lokacin da yaji Mimi na ajiye lemon da ta kawo a kusa dashi.  Badaru ya tsai da ita, tare da daka mata wata muguwar tsawa "ke dauke Badamasi bayashan irin wannan lemon na kanti, sai zobo kije ki kawo masa zobo" (kunji fa kamar ya siya ya ajiye)  ta dauki tray din lemon tare da cewa "to bara na dafa zobon sai dai babu qanqara...... " maganar ta dauke lokacin da taga Badaru ya daga hannu da nufin kai mata mari.  Tai saurin saka tray din hannunta ta kare fuskarta,  hakan yasa dukan ya sauka kan farantin kayan ciki suka watse.  Badamasi yayi saurin miqewa tsaye cikin razana 😳. Badaru ya dora da cewa "Dan ubanki harni xan saki aiki kice babu qanqara?  Meyasa baki siya kin ajiye ba?"  idon Mimi qurrr akansa tana kallonsa cikin mamaki Dan yaune karon farko da yakai hannu jikinta da sunan duka,  kuma yaune karon farko da ya xagi ubanta dake qarqashin qasa. 



Cinkin dinbin mamaki da razana Badamasi yace "Badaru 😳dukan mace?  Kamar jahili,  metai maka?  Dama abunda nakiji na cewa kana tara abokai kaci mata mutunci gaskiya ne? Me tayi maka? " Badaru ya tare Badamasin cinkin hargowa kamar xai dakeshi,  "baka ga abunda tai ba?  Yar iska mara mutunci,  duk abunda xata xubarmun da mutunci ta iya, banxa jaka" 



Idanunta jajur suna digar hawaye take kallon Badaru ba komai yayi mata ciwo ba irin zagin ubanta.  Cikin qarfin zuciya tace" karka kuma zagarmun uba,  domin yana kabari akwance".  Yayi saurin cewa "an zageshi uban ubanki ma yaci ubansa,  kiyi abunda xakiyi"  ta mayar masa da martanin cewa "babu abinda xanyi domin xagi xagawa yake, kuma duk abunda kakemun Allah ya na jinka, yana ganinka kuma zaimun sakayya." 



Ya watsa mata wani kallo sannan ya funciko hannunta ya hankadata bakin qofa tare da cewa "fita ki tafi gidan ubanki shegiya mara tarbiyya gayyar tsiya." Badamasi ya daka tsalle tare da dakawa Badaru tsawa kamar shine gaba da Badarun yace "wlh Badaru ka kiyaye ni, na rantse da Allah xaka tarkowa kanka bala'i,  domin yanxu xanje na fada Abba abunda gidanka yake ciki"  yana kaiwa nan ya figi muqullin motar Badaru dake kan kujerar parlourn (domin shi baixo da mota ba) ya fita. Mimi ma tasa kai ta fita yayi saurin cewa " ban baki izinin fita ba" ko takansa bata biba tai waje ya bita da gudu ya jawo ta ya dawo da ita tare da furta "maryam akanki ake shirin hadani da iyayena,  kowa nawa sai ya rabu dani a kanki. Abokaina, yan uwana, yanxu kuma iyayena?  Meyasa haka?"


Acikin motar Badaru kuwa Badamasi ne a kifa kansa a sitiyari yana jin quna a ransa, wlh da yasan yacce xai tarar da Mimi kenan da bai zoba.  Bazai juri ganin Mimi cikin wannan halin ba,  yanxu meye abunyi?  Yayi dan gajeran tunani,  baxai fadawa iyayensu abunda gidan Badaru ke ciki ba yanxu.  Domin inyayi silar mutuwar auren Mimi sannan daga baya yazo yace yana sonta cewa xa ai ya kashe mata aure dan ya aureta.  Ya dakko wayarsa yayi saving recording din da yayi saboda wata rana. 



Hannunsa yakai kan aljihun motar ya jawoshi,  saiga kwalayen magani guda 4 duk iri daya (maganin da mekudi ya bawa Badaru,  yake ajiyarsa amota saboda kar Mimi ta gani) ya dakko ya duba kwalin hotunane ajiki na mace da namiji tsirara suna xxx kala kala hutunan abun ba kyan gani.  Ya duba rubutun jikin maganin,  yaga illar da yake,   a qa'idar maganin ma matan banxa masu blue films akewa amfani dashi dan su fita hayyacinsu, kuma suma din sai anyi aggrement.  Amma dan zalunci da son zuciya Badaru yakewa yar mutane amfani dashi, kuma bama kwali daya ba,  alamu sun nuna ya dade yana mata amfani dashi tunda ga kwalaye nan har guda 4. 


Ya share hawayensa ya dauke ragowar maganin a fili yace "MARYAM Allah ya saka miki,  Allah ya miki canjin alkhairi domin Badaru ba miji bane. 



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣6⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Cikin kwanakin da suka biyo baya tai wata irin ramewa kamar me ciwon SIDA (AIDS). Ta fita hayyacinta kwarai,  ga wani irin mugun qaiqaiyi dake addabarta a qasanta,  ga dukkan alamu ciwon sanyi infection yayi mata mugun kamu. Domin har gari gari take gani a gabanta a memakon danshi da akasan ya mace dashi, ga wani irin wari danma bata ramo da inserting almuski. 


Badaru tsakaninta dashi dangantaka tayi tsami kwarai da gaske,  domin sai suyi 3 dayz koma fiye da hakan bai mata magana ba, kuma inma tayi masa baya amsawa. Walau kuwa koda gaisuwa ce,  sai dai tagaji da tsuguno ta tashi.  Wanda hakan shiyasa kawo mugun koma baya a lfyarta,  sau da yawa sai dai ta ganta a kwance kamar gawa batasan abunda ya faru ba tunda babu kowa a kusa balle ya karanta ta mata abunda ya faru kafin ta tsinci kanta a hakan. 



Babban abun takaicin shine : duk wannan takun saqa da suke da shi,  hakan baya hana in dare yayi yazo ya mutsutstsuketa da sunan yazo neman haqqinsa na aure.  Sakamakon ciwon sanyi da yayi mata illah yasa ko yazo baya samun komai (babbar illar ciwon sanyi kenan,  wato qafar da ni'imar mace) wanda hakan ke jawowa ya fusata yayi ta xaginta da aibatata. 



Data kula sosai sai ta gano cewa ba ita kadai ciwon ke damu ba,  saboda Badaru ma Kullum cikin sosa al aurarsa yake,  alamu shima ciwon na addabarsa. 


Dan lfyar kanta da kuma maganin wulaqancin da Badaru kemata a shimfida (domin tana kyauta zaton rashin samun biyan buqatarsa na daga abunda ya sa wulaqancinsa ya kuma ta azzara) yasa ta tunkareshi da sunan ya barta taje asibiti domin ciwon sanyi ke damunta.  Da farko be kulata da maganar ba,  sai daga baya ya jiyo qanshin gaskiya a maganarta.  Domin ciwon da tai masa bayani yayi kama da wanda masu magani ke bayani a kasuwa.  Hakan yasa ya sameta har daki yace "kawai kinje kin kwaso ciwon sanyi kinxo kin gogamun,  wlh in hakan yayi sanadiyar raguwar qarfin mazantakata bazan yafe miki ba"(🤣🤣🤣).


Ta dago arazane jin abunda yace,  cikin sanyin murya tace "ni kuma Badaru?  Ni ina fita ne?  Canake tunda nazo gidannan fitata daya?  A ina xan kwaso ciwon?  Nafi zaton kaine ka dakko mana a kasuwa" yasan tana da gaskiya shiyasa bece komai ba ya kada kai yayi gaba. 


Da yamma kuwa sai gashi da ledar magani,  ya siyo a irin gurin masu saida maganin hausar nan na kasuwa.  Wadanda ke yawo da mota suna tallah a speaker.  Ya miqo mata wani qaramin qulli "wannan gashi ki juyeshi a madara yanxu ki shanye,  ya miqo dayan wannan kuma ki dunga turare dashi kina tsugunawa akai" (kunji fa!  Mtsew komai aka hada da jaki sai yaci kara) tace  "to" ta karba,  azuciyarta take tunanin shidai asibiti ne bayaso arayuwarsa.  Ta qudure bazatai amfani da wandannan magungunan da batasan ingancinsu ba haka kawai ita ba qoshin lfy suje su illatata.



Tofa! Abu fa ya kacame, komai ya xama chocolate 😂. Iskancin Badaru da wulaqancinsa kanta ya kazanta,  ko alabari bata taba jin inda ake cin mutuncin matar sunnah yadda Badaru kecin mutuncinta ba.  "Banxa jaka,  na tsaneki" sune kalaman da Badaru ke fada mata adun sanda suka hada shimfida dashi saboda baya samun biyan buqata Sam.  Gashi ita a kanta tanajin yadda tai wata irin budewa tai sako sako,  kamar matar data haihu bata gyara kanta ba. 


Bama sai sun hada shimfida ba,  a rana daya yakan ce mata "na tsaneki" yafi sau cikin carbi. Sunanta kuwa a gurinsa ya koma "jaka" dan sau tari zai sata aiki sai yace "ke jaka yimun abu kaza" yayin da agefe guda kuma ya dage da aikin ginin da yake,  domin ya auro Nafee wacce yanxu Kullum a gurinta yake kai 11 dare. 



Mimi,  yar kwalisa yanxu ta xama wata muguwar siriri mara fasali,  tayi fari fau kamar me amfani da mayunkan kwaile fata (bleaching) yar kewayayyar fuskarta ta koma tsuru sai manyan idanuwa 👁👁 da hancinta 👃🏾 wanda rama tasa yayi bodardar.  A taqaice dai ta xama mummunar qarfi da yaji. 



Babbar matsalar dake addabarta itace rashin ganin al adarta (period) rabonta dayi tun tana wata biyu a gidan, wato lokacin da taje asibiti ta biya gidan Faty.  Tayi tayi Badaru ya barta taje taga likita ko wata matsalar ce yaqi.  Data dameshi da xancen saboda ciwon marar dake addabarta  sai yace karta dameshi,  saboda ba akanta aka soma CIKI ba.   Tunda daganan itama bata qara xancen ba,  saboda itama data duba cikinta sai taga tafi kama da masu qaramin ciki. 



Kuma wani ikon Allah sai ta tsinci kanta cikin farinciki da cikin,  saboda kasancewarta meson yara tunda basu taso sunga kowa a dakin mama ba sai su biyu.  A fili tace " Baby ki rasa lokacin da xakixo sai lokacin da ake sa toka sa katsi?  Allah ka rabamu lfy,  Allah ya miki albarka yata😊" ta fada hannunta na dafe akan cikin. 



Badaru dake gefe yana sauraranta yayi saurin matsowa kusa da ita yace "au mace kikeso ki haifa?  To ai se ki roqi Allah kada ya baki me irin BAQIN JININKI,  domin in ta rasa miji wlh sadakarta xan bayar"  ta dago ta kalleshi tayi murmushi 😊 tace " Badaru in tayoka ai bazatai baqin jini ba, tunda ka ganni ka taimaka ka aureni itama sai Allah ya dubi kyakykyawan aikin da kayi a kaina ya kawo me auranta 😊"



Yasan magana ta fada masa dan haka yayi tsit. 

*******       ********    ******

Tun jiya cikin dare take murqususun ciwon mara,  har xuwa yanxu 9:43 na safe.  Tun tana iya yunquri har qarfinta ya qare ta kasa.  Badaru tun shekaran jiya yayi tafiya Lagos akan harkar kasuwancinsa, kuma gashi bata da lambarshi kamar yadda bashi da tata.


Badamasi da yau ya shigo kano yazo daga inda yake aiki (Dutse) tunkan ya qarasa gida hankalinsa yake akan maryam.  Tun rabuwar da sukai da Badaru akan ciwa maryam mutunci hankalinsa ya kasa kwanciya,  dan haka direct ya wuce unguwar su Badaru. 


Tun daga soro yake kwada sallama amma ba amsa,  ta bangaren Mimi ta dakko waya da nufin kiran Faty ta fada mata halin datake ciki sallamar ta rusketa.  Kuma tana amsawa amma dake muryar a shaqe take saboda wuyar ciwo shiyasa bayaji. Ya sako kai parlour tai miqe daga kwanciyar cikin qarfin hali tana haki tace "inata amsawa bakaji" ya dubeta a razane yace "maryam badai ba lfy ba? Ina mai gidan ya fita ya barki cikin wannan halin?" 


Tai murmushi tace "yayi tafiya tun Lagos,  bayan tafiyar ne ciwon ya riskeni shi......" bai qarasa jinta ba ya dakko waya a aljihu.  Sai ji tayi yana xancen rashin lfyrta kuma ga dukkan alamu da Badaru yake.  Can yaji yana cewa "babu batun ragonta,  dan mace na da ciki bazatai ciwo ba sai ace tacika ragonta?  Nidai yanxu xan kaita asibiti ya kashe wayar"



"Tashi ki shirya muje asibiti, " ya bawa maryam umarni.  Sannan ya zarce da mitar cewa kasan lalurar ciki ne?  Inda kai Allah ya dorawa wayasan kwakwazon da zakai?  Kaiwa yar mutane ciki ka tafi kabarta da wahala.   Itadai ta yunqura dakyar ta miqe tayi hanyar toilet tana godewa Allah da ya kawo me temakonta. 



Cikin qarfin xuciya tai brush da wanka suka tafi.  Ganin yadau hanyar yan kaba yasa tace "Aminu kano nake ganin likita ai" ya waiwayo ya dubeta yace " rana tayi shiyasa xan kaiki asibitin wani abokina da mukai karatu tare,  amma shi likitan mata ne"  tace ai a Aminu kano akwai yayata dake aiki acan,  inka kaini ko likitan yamma ne sai nagani" 



Yana kallon titi yace "sry bari na kaiki private din xaki fi samun kulawa inyaso har awo da haihuwa sai kije can. Yasan aikinsa sosai" ta sunkuyar da kai cikin kunya jin yayi maganar cikin jikinta.  Ya qura mata ido cikin burgewa dan yanason mace me kunya. Aransa yana aiyana rashin imanin Badaru dan kowa yaga maryam yasan ba a dadi take ba kuma ga ciki na wahalar da ita. 


Sun tadda layi kasancewar safiya ce. Badamasi yayi masa waya da kansa ya fito ya shiga dasu bayan ya nemi alfarmar na kan layi. 



Yana dubata suna dan taba hirar yaushe gamo da Badamasi,  ya kalleta yace maryam alamu sun nuna kina da qarancin jini a jikin ki,  shiyasa kika dashe kikai haske.  Badamasi yace " ba ciki bane ya kawo hasken?"  Dr yace "bazan iya cewa da ciki ba ko babu,  amma dai bari nayiwa sister sarah magana ta tafi da ita can nursing station tayi mata checking sosai akan hakan" 


Ya kirata a waya nan da nan sai gata yace "kuje da wannan yayi mata bayani" Mimi ta bita yayin da Badamasi ya koma reception dan bawa ragowar marasa lfyar damar ganin likita. 



Acan gurin nursing din sun dubata sosai taji wacce ta dubata na fadawa dayar cewa,  tana buqatar aimata wankin ciki. Lamarin da yasa Mimi tsorata, domin tasha ji ana fadar wahalar wankin ciki. Dan haka ko takan mayafinta da jakar bata biba ta ranta ana kare 🏃🏽‍♀.


Badamasi na zaune yaga fitowarta daga dakin a harkitse,  tana tafiya tana waiwayen bayanta taga ko nurse din ta biyo ta.  Ya taho gurinta da sauri cikin rashin sani suka gabxa karo. Tai qasa xata fadi yayi saurin tarota jikinsa,  jinta jikin mutum yasa ta qanqameshi tana cewa "Badaru kaji wai wankin ciki zasuyimun,  kuma da xafi sannan xasu wankemun Baby dan Allah karka bari suyimun." shidai Badamasi tunda yaji maryam ajikinsa ya tafi wata duniyar,  ya xaci irin mafarkan da yasa ba yine akanta dan haka ya rungumeta jikinsa tsam yana sauke ajiyar xuciya. Akayi sa a itama ta xaci mijintane ta kwanta lub.


Nurse din data biyo Mimi da jakarta da mayafi ce ta dawo dasu hayyacinsu.  "oga gashi ta gudo dakaji ance xa ai mata wankin ciki"  yai saurin rabata da jikinsa daya farga ba mafarki yake ba,  a xuciyarsa ya dunga cewa astagfirullah Badaru kai ka jawomun da ka kula da matarka da ban kawota asibiti ba balle harna rumgumeta.   Itama Mimi sai yanxu ta dawo hayyacinta,  ta dunga jero neman gafarar Allah.  



Suka koma office din Dr,  nurse din tayi masa bayanin matsalar Mimi da kuma qin yadda ai mata wankin cikin.  Ala dole ya rubuta mata maganin ciwon mara dana qarin jini. Badamasi ya tambayeshi akan cikin.  Yace "yanxu kam bazan iya cewa da ciki ba ko babu tunda akwai lalura da yawa a tare da ita, sai dai ko in kun kuma dawowa ayi scanning.  Ga maganin ta dage da cin abinci da shansu kuma basu da qarfi koda da cikin baxasu illatashi ba" sukai sallama suka tafi. 



A hanya suna tafiya tace masa "dan Allah karka maidani gidannan na kwana ni kadai jiya nasha wahala,  bansan abunda hali xaiyi ba yau." ya dubeta yace "to Maryam ai bani da ikon kaiki wani gurin bada ixinin mijinki ba,  amma bari in masa magana saboda akwai hatsari abari ki kwana ke kadai" ya dakko waya ya kirashi tanaji yana masa bayani,  can ya miqo mata wayar yana cewa gata.  Tai sallama be amsa ba bare ya saurari gaisuwar da take masa ya hau masifa " kince bazaki kwana gidanki ba ko?   Uwar langwai to kitafi duk inda xaki tunda kinsa anmun titsiye inna dawo kya dawo." yana kaiwa nan ya kashe wayar, itama ta kashe ta miqa masa tare da cewa kaini yahya gusau gidan yaya Faty.  



Koda suka isa gidan sun samu ya Ahmad na nan,  dan haka koda yaya Faty ta fito domin temakamata su shiga ciki yaga bata lokaci ne dan haka ya dauketa cak yakaita har cikin parlourn.  Badamasi ya dunga kallonsu cikin birgewa,  domin sai ka xata Ahmad ne dan uwan Mimi ba Faty ba. 


Badamasi ya dade a gidan suna hira, saboda family din sun burgeshi.  Faty ta dunga jerawa Mimi sannu ta duba magungunan da aka bata.  Tare sukayi dinner sannan tasha maganin kana Badamasi ya tafi. 


Yau dadi takeji xata kwana gidan yaya Faty,  har dare sunata hirarsu cikin nishadi sannan suka nemi makwanci,  yaya Faty ta dunga mitar ramar da Mimi tayi amma koda mimin ta fada mata ciki ke wahalar da ita sai mitar ta koma murna.  Suka raba dare suna hirarsu sannan sukai bacci. 



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣7⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Kwanaki uku da tayi gidan Faty yazo mata da wani irin canji,  har mamakin nishadin da take ciki takeyi. Sai take ganin rayuwarsu kamar lokacin da suke gida kafin suyi aure.  Suci abinci tare,  bacci tare,  sannan gashi ya Ahmad duk sanda xai shigo saiya shigo mata da abun kwadayi,  yakance me ciki ba a rabata da kwadayi, sai kace shi xa a haifawa dan.  Amma aduk sanda ta tuna xata koma gidan Badaru sai jikinta yayi mugun sanyi sannan gabanta yayi ta faduwa. 


Rana ta biyar a gidan Faty wanda ya kama da satin Badaru daya a Lagos,  da yammaci suna zaune ana hirar da aka saba anata dariya.  Mimi zaune a gefen Faty akan kujera 3 sitter tanacin guava,  yayin da ya Ahmad ke gefensu akan kujera 1 sitter yana basu lbr sai dariya suke. 



Badamasi yayi sallama ya shigo,  Mimi na ganinsa gabanta ya yanke ya fadi.  Nan take nishadin da take ya qare kuma duk wanda ke parlourn ya lura da wannan canjin na Mimi.  Ko Badamasi bai fada ba tasan Badaru ya dawo kuma xuwa yayi ya maida ita kamar yadda ya alqawaranta. 


Suna gama gaisawa ya fada musu labarin dawowar Badaru tun safe,  kuma yace yaxone ya maidata gidan.  Ya Ahmad ya katseshi da cewa "shi maiyasa bazaizo ya dauki matarsa ba?  Sati daya baka gari?  Inka dawo ai iyalinka ya dace ka nema kaji lfyarsu,  ko akuya ka bari da ciki sati daya inka dawo ai ka binciki lfyarta.  Wannan abunda yakeyi sam babu tsari a cikinsa,  na kuma gaji dab nake da indau mataki akai " ya qare maganar cikin bacin rai 😔. Badamasi ya bude baki da nufin kareshi ya Ahmad ya tsai dashi "karkace komai,  nasan halinsa kuma shirun da akai masa baya yana nufin Mimi bata da gata bane, kawai muna kau da kaine saboda iyayenmu" Faty na gefe na share hawaye .



Sha tara ta arxiqi suka hada mata,  kamar wacce xatai tafiyar shekara.  Har Badamasi ya dunga jinjina soyayyarsu ga Mimi. Faty bata fito rako Mimi ba saboda kuka da take bataso tasa mimin kuka itama,  sai ya Ahmad ne ya tsaya aka loda kayan a bayan motar sannan ya kawo kudi ya bawa Mimi,  har anrufe motar ta fito da gundu ta fada jikin ya Ahmad tasa kuka ya kamo fuskarta ya share mata hawaye yace "maryam kici gaba da haquri Allah ya na tare dake,  baxaki taba tabewa ba a rayuwarki" ya bude motar ya sakata suka tafi. 




*****       *****        ******

Bata canja xani ba rayuwar da suke a baya itace dai,  gashinan abun babu tsari kamar a jahiliyya period.  



Kimanin kwana 11 da dawowarsa daga Lagos kenan daren ranar suna kwance,  ya hauro kanta yasa qarfi ya danneta.  Kimanin sau uku kenan yana  yin hakan,  inya gama buqatarsa yaji bai gamsuba yayita zaginta yana ci mata mutunci. 



Yanxun ma hakace ta kasance,  ya shigeta da dukkan qarfin da Allah ya bashi.  Taji xafi kwarai harta kwallah qara,  yaja dogon tsaki yace "qarar me kikemun?  Wai nufinki xafi kikaji?  Abunda duk kin bude kin tale,  innaxo shigarki kawai ji nake na rufta babu wata madatsa 😳🙈 shine har xakice kinji xafi?" 


Tai qasa da murya"wlh Badaru tun lokacin da ciwon sanyin nan ya samemu inkanayi ji nake kamar kana xubamun yaji daurewa kawai nakeyi,  da kabari naje asibiti da tuni mun warke."  cikin hargowa da daga murya yace "ya sameki dai, dan ni tuni na warke,  ai nakawo miki magani kikaqi amfani dashi ke lallai sai na asibiti ko Baturiyya? To wlh baki isa ba dan mugunta kin hanani inji dadi dake?  Wlh wlh whl yau ko xanyi sau dari sai naji dadi xan kyakeki ya rage naki"



Yana kaiwa nan ya farmata kota ina juyata yake yayi,  tun tana jin xafi harta denaji.  Numfashinta ya fara gazawa. Batasan iya lokacin da ya shafe yana durxarta ba,  ita dai tasan yayi mugun dadewa yana abu daya.  Sannan ya sauka ya koma gefe ga dukkan alamu gajiya yayi bawai biyan buqatar ya samu ba. 



Kukansa ya dawo da ita hayyacinta,  inda cikin kukan takaici yake cewa "maryam kin cuceni, kin xalunceni,  ni zakiyiwa haka ko?  Ni zaki hana jin dadi dake ko?  Kimanin wata daya kenan Kullum cikin buqata nake kin kasa biyamun ita.  Kije Allah ya isa ban yafe miki ba,  in Allah ya yadda bazaki gama da duniya lfy ba. KE MARYAM ALLAH YA TSINE MIKI." 😳😳😳😳



Jin furucin Badaru na qarshe yasa tai xunbur ta miqe,  tare da cewa "Badaru me yayi zafi haka??? 😳" ya bata amsa da cewa "ubanki ne yayi zafi" yana fadar haka ya fita daga bedroom din. 



Wani irin yanayi ta shiga ita ba matacciya ba ita ba rayayya ba.  Kukan ma ta kasa,  tsinuwa daga mijin aurenta?  Akan abunda bata da iko akai? Tab akwai matsala.  Saboda da gajiyar dirxar da Badaru yayi mata batasan sanda bacci ya kwasheta ba.  Sai ana kiran sallatu ta farka,  qasanta wani irin xugi yake mata kamar ansa reza an ketata taje tai wanka tai sallah ta roqi Allah sauki da gaggawa kan halin da take ciki. 


Sukuku ta yini saboda tsinuwar da Badaru yayi mata ta taba xuciyarta sosai, ta qudure a ranta inya kunna inji da dare ta samu chajin waya xataiwa ya Faty maganar infection din ta kawo mata Magani, domin wulaqancin ya isheta haka gara ta naimi magani ya dunga samun biyan buqata axauna lfy domin ita batasan tashin hankali (Allah sarki rayuwar ya mace,  Kullum cikin sadaukarwa namiji take.) babu abunda ta iyaci ranar illa ruwan lipton da lemon tsami. 



Ta idar da sallar laasar,  tadan kwanta kan sallayar tana azkar,  ta qudure aranta yau laraba intasamu dan aike xata bashi kudi yayi mata sadaka domin yau yini tayi gabanta na faduwa. Bazai wuce hudu da rabi ba 4:30 lokacin da taji dawowar Badaru, tayi mamaki kwarai dan bai cika dawowa haka ba sai inda muhimmin abu da xaiyi. 



Ya wuce daki fuu sai gashi da tulin kayansa masu dauda. Ya fita tsakar gida,  sai gashi ya dawo ya danqi gashin kanta ya fita da ita,  ya nuna mata tulin kayan wankinsa yace "ga wanki nan kiyimun,  tunda baki iya biyamun buqata ba kimun wanki,  dan baxan dunga baki abinci a banxa ba" tai tsam sannan tace "to kayi haquri kaga nawa ma bayi nake amma in ya Faty ta aiko karbar nawa wankin in shaa Allah xan hada maka da naka." 



Ya danqi wuyanta ya hadata da bango, sannan cikin huci da tsabar tsanar yace "ke kin isa insaki aiki kice baki ba? Wlh baki isa ba,  na tsaneki wlh da inka kashe rai babu wani hukunci a kanka da kece mutum ta farko da xan fara kashewa,  maryam ban taba tsanar wata halitta a duniya kamar ki ba.  Saboda haka dole kimun wanki dan ubanki"  ta fusge wuyanta tayi gefe ganin yana shirin kaita lahira, tana maida numfashi tace "wanki bazanyi ba kisa kuma bisimillah ka kasheni." cikin bacin rai take furta wadannan maganganun domin ranta yakai matuqar baci da xagin da Badaru kewa ubanta.  



Kafin ta ankara ya tsinka mata mari ji kike kau! 😳 tayi baya cikin azama ya dora da cewa "lallai wuyanki ya isa yanka? Yauni kike maidawa magana?  To dan ubanki...... "ta tari numfashinsa kafin ya qarasa. "karka kuma xagin ubana domin nasan darajarsa,  kuma da yana raye wlh bazan auri wanda besan darajar iyaye kamar ka ba,  maraicine ya jawomun"


Ya kuma dauketa da wani gigitaccen mari,  "na xagi uban naki bayan xagima na dakeki dan haka kije ki haqoshi daga kabari yazo ya rama miki."  ta dago idonta jajur " ka mareni?  Wlh komai daren dadewa saina rama,  wannan alqawarine na yiwa kaina." 



Ya ja hannunta qiiiiii ya bude gidan ya turata waje ta fadi dabas.  Sannan yace "ai basai andade ba kije yanxu ki tasoshi daga kabari kuxo ke dashi ku hadu ku dakeni,  kije na sakeki kuma Allah ya isa tsakanina dake in shaa Allahu bazaki gama da duniya lfy ba." 



Ya maida gidansa ya rufe,  yabarta zaune babu takalmi babu mayafi. Kuma dai dai lokacin hankalin mutane ya fara dawowa kanta, aka zagayeta ana kallonta tai qasa da kanta taji duk ta muxanta. Ya qara bude gidan ya wullo mata hijabi da wayarta,  jehowar da yayi tasa wayar taci screen. Ta miqe tasa hijabin qafarta babu takalmi gashi bai bari ta dakko kudi ba dan shiga Mota. 




Har ta fara tafiya wata maqociyarta yar dattijuwa wacce yayanta ke shiga gidan Mimi ta biyota a baya ta tsai da ita,  tace "maryam yanxu akaje aka sanar dani abunda ke faruwa, kiyi haquri indai baki cuceshi ba Allah saiya saka miki AURAN BAYA SADAKIN NA GABA." ta cire takalmin qafarta ta bawa Mimi tace saka ki tafi Allah ya hada fuskokinmu da alkhairi,  ta juya ta tafi tana kuka dan tana qaunar Mimi.



Cikin wani irin yanayi take tafiya,  tafi kama da mahaukaciya sabon kamu sam ba kuka take ba, idonta da xuciyarta sun bushe qaraf.  Jinta take ita ba matacciya ba ita ba rayayya ba,  abun kamar almara aurenta ya mutu cikin wata biyar da kwana shida kacal da yin auren.  Batasan mutuwar aure sam koda akan maqiyinta bare a gida irin nasu wanda bata taba ganin ko yaji anyi a gidanba.  Ita kuma haka QADDARARTA take,  andade ba ai aure ba,  anyi ba a dade ba ya mutu.  Tasan qalubalene a rayuwarta qatoto,  wlh duk ixayar da take ciki gara ta haqura ta xauna da Badaru da ace aurenta ya mutu. Koda kuwa takata zai dungayi yana wucewa. Kuma da tasan zai dauki matakin saki akanta wlh da gara tayi masa wankin. 



Saboda tashin hankalin da take ciki yasa bataga nisan tafiyar gidan Badaru xuwa titi ba, kawai ta tsinci kanta a bakin titi.  Ta tare dan sahu tace kaini yahya gusau (gidan ya Faty) dan koda wasa tasan bazata iya tunkarar gidan Baffa ba (gidansu) 



Har bakin gate din gidan ya kaita kasancewar gidan a bakin titi yake.  Ta sauka tace bari in kawo maka kudin. 



Faty na zaune a parlour tanashan golden morn taga fadowar Mimi parlour kamar an jehota,  ta miqe a razane tace "lfy Mimi,  jikin naki ne ya tashi?" nabar dan sahu a waje ban bashi kudin ba" itace amsar da Mimi ta bawa Faty,  tana fadar haka ta shige bedroom din ya Faty. 



Bayan Faty ta sallami dan sahun,  ta riski Mimi a bedroom dinta kwance kan gadonta tace "Mimi ki fadamun abunda ke faruwa na ganki a hargitse haka" dakyar ta daga ido saboda tsabar ciwon da kanta ke mata,  a taqaice tace da Faty "ya sake ni" ko kalma daya bata qara akan haka ba ta koma ta kwanta kan Royal bed din Faty.  Sama sama ta dunga jiyo salati da sallallamin fatyn.  



Har akai sallar magriba ana gab dayin ta isha suna zaune a gurin da sukai sallah jugum jugum.  Suna idda sallar isha Mimi ta kuma hayewa gado ta qudundune mugun sanyi takeji saboda zazzbin da ya rufar mata. 



Duk yadda Faty tayi da Mimi taci abinci taqi ci,  domin batajin ko maqogaronta abinci zai wuce,  saboda wani irin malolo takeji a maqogaron shi beyi gaba ba shi beyi baya ba.  Kuma itama Faty da take maganar itama bataci abincinba. Ta hado tea ta miqawa Mimi tace "karbi kisha kodan abunda ke cikin ki" ba musu ta karba tasha. 



A haka Ahmad ya riskesu,  dawowarsa kenan.  Ya shiga har bedroom din yace "lfy Faty?  Mimi jikin ne ya kuma tashi?" duk sukai masa shiru, Mimi tacigaba da shan tea din ya kalli Mimi " Mimina lfy?  Ko muje asibiti?" nan ma shiru ya kuma kallon Faty yace " Faty na kiyi magana mana lfy?" a hankali Faty ta furta "sakinta Badaru yayi".



Ga mamakinsu sai sukaji Ahmad yace "ALHAMDULILLAH " nan take fuskarta ta nuna tsantsar farin ciki,  dukkansu suka saki baki suna kallonsa. 



Ya ajiye jakarsa ta office akan side bed, sannan ya haura kan gadon ya kwantar da kan Mimi a kafadarsa yace "maryam ki godewa Allah da ya rabaki da Badaru,  domin bai dace da samun salihar mace irinki ba,  MARYAM keep praying in shaa Allah sai kinsamu mijin da baki taba mafarkin samu ba haqurinki bazai tashi a baxan ba" 




Ita dai bin kowa take da ido ga alama ta samu kurumta ta wucin gadi.  Haka suka kwana gado daya da Faty,  inta fara bacci sai ta farka a furgice sai dai Faty ta tofa mata addua ta maida ita ta kwantar.  Ya Ahmad kuma kwana yayi yana nafila yana roqawa Mimi waraka gurin ubangiji,  in yai sallama ya shiga dakin da suke kwance,  yaga halin da suke ciki,  a duk sanda ya shiga Mimi kanyi xunbur ta miqe zaune alamun a firgice take sai dai ya maida ita ya kwantar ya tofa mata addua.  Da haka har suka wayi gari. 




HAPPY EIDIL FITR,  TAQABBALALLAHU MINNA WA MINKUM.  

Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣8⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)


A bangaren Badaru kuwa,  sai bayan ya saki maryam sannan fargabar abunda zai biyo ta bangaren Abbansa ya shige shi. Amma daya tuna yanda ya tsani maryam da yacce ya suqe da xama da ita sai yaga ai yanci bana rago bane.  gara kawai da ya saketa komai xai faru ma ya faru. 


Ana iddar da sallar isha, ya hada tea murtuk ya soya kwai 5, kamar shi ya siya.  Ya dake cikinsa sannan ya sheqa wanka ya xaba shadda,  ya samu turaren Mimi ya feshe jikinsa da shi.  Ko lura da cewa turaren mata ne bayi ba. Yaywa gidan su Nafee tsinke. 


Tare suka fito da dan aiken da yaje kiranta kamar jira take,  ko gaisawa bata bari sunyi ba ta fara qorafi "Badaru anya kuwa kana sona?  Anya kuwa xaka aure ni?  Nifa na fara yadda da maganar mutane da suke cewa yaudara kake"


Ya danyi dariya 😄 yace "Nafee ko gaisuwa babu za a fara da qorafi" tace da maganar na yini tana damuna.


Yace to "ki fara shirin bikin ki nan da wata biyu masu xuwa" ta waro ido tace "bayan sallah fa kenan" yace kwarai kuwa tace "wace sallah?  Yace wacce sallah ke gabanmu yanxu? "  tace in nayi lissafi dai dai qaramar sallah kake nufi domin yau kwana 8 ko 7 ya rage a fara axumi"


Yace yawwa yar gari,  kin gane kenan.  Ta daka tsalle tace "da gaske?" yace "wlh da gaske nake"  ya qara murmusawa yace "kuma daya albishir din da xan miki shine : ke kadai ce dani yanxu" tai far 🙄 tace "kamar yaya?" yace "mun rabu da maryam daxu" 



Wannan karon tanayin tsallen ta fada jikinsa (kuji rashin kamun kai) ta qanqameshi duk kuwa da cewa basu taba hakan ba.  Yayi saurin cireta a jikinsa jin yana shirin loosing control.  Wannan dare haka suka sha hirar soyayya cikin nishadi saboda matsalarsu ta tafi (maryam) tare da hirar yadda aurensu xai kasance. 

*****   ******    ******    *****


Karfe taran safe 9:00 am a gidan kakanninsu tayi musu bisa shawarar Ahmad da kuma rakiyarsa,  domin ita kanta bai yadda da nutsuwar Faty ba a lokacin shi yasa ya hanata driving.  Yasan tunkarar Baffa da lamarin mutuwar auren Mimi ba karamin balli zai tayar ba,  shiyasa yace abi abun takan surukan Baffa ko zai zo da sauki. 



Babba gidane me cike da kango a da,  amma yanxu da yayansa suka xama wasu sun bigeshi sun maidashi na tsamani da tsari.  A katafaren parlourn gidan sukai masauki hajja na kan kujera, yayinda mal manu kekan well chair ( saboda girma baya iya tafiya)



Tiryan tiryan Faty tai musu bayanin lamarin tun rashin lfyar maryam da kuma halin data tsinceta a gidan Badaru  har xuwa jiya da auren ya qare.  


Hajja tunda aka fara take share kwallah,  mal manu kuwa baice komai ba sai wayarsa daya dakko ya kirawo mama yace ta sameshi gida yanxu,  sannan ya kira Baffa ma ya fada masa. 



Tana gurin aiki kiran ya risketa,  dan haka ta kasa nutsuwa. Tasan ba qaramin abu bane zaisa Baba kiranta a wannan lokacin,  sai ta barwa kanta kawai Hajja ce ba lfy. Taje office din Principal din ta naimi excuse ganin bata taba hakan ba kuma da alama a rude take yasa ya barta. 



Kusan tare suka iso da Baffa,  domin shigarsa kenan taxo.  Ganin motarsa a kofar gida yasa ta qara rudewa.  Tana saka kai parlourn gabanta ya yanke ya fadi,  dan ganin Mimi ta tsummace rabonta da ita tun randa aka kaita gidan miji (halayyar uwa ta gari bata xuwa gidan yayanta sai da babban dalili) ta samu gefen centre carpet ta xauna. 


Faty ta kuma yi musu bitar abunda ya faru tas (dan ma Mimi bata fada musu waye haqiqanin Badaru ba da irin azabar da yayi mata). Baffa ya miqe ya watsawa Mimi kallon kinwa kanki,  dagani akwai magana a bakinsa kuma bai yarda da abunda Faty ta fada ba,  amma ganin idon surukansa yasa bece komai ba.  Yace "ni natafi kasuwa dan nakusa makara"



Mama ta kasa dauriya da abunda ya samu Mimi tasa kuka,  hajja da tun dazu take kukan itama ta qara volume  Faty itama tasaka nata kukan.  Mimi ganin mama da Faty na kuka (mutanen data fiso fiye da komai) itama ta saka nata kukan (tunda abun ya faru sai yanxu tayi kuka.


Kamar jiran nata kukan suke, kowa yayi shiru da nasa kukan parlourn yayi tsit  sai sautin kukanta.  Faty ta yunqura xata tashi taje gurinta mal manu yayi mata alama ta zauna.  Sai da tayi 43 minutes tana kuka baji ba gani,  sannan tayi shiru dan kanta.  


Mal manu ya garo kujerarsa yaxo kusa da ita ya dafa kanta "MARYAMU kiyi haquri kinji, wata rana sai lbr,  haqiqa mijinki ya cutar dake,  amma kiyi haquri wlh duk wanda ya toxarta aure saiya wulaqanta, sakayyar aure a duniya Allah ya ke yinta. Allah ya baki wanda ya fishi,  in shaa Allah wannan hawayen da kika xubar a dalilin baqin cikin aure sai Allah ya sa kin xubar da hawayen farin ciki fiye da wannan, Allah ya albarkaci rayuwarki" duk suka amsa da Aminnnnnnnn



Faty ta miqe xata tafi gurin aiki,  mama ma ta miqe.  Mimi tai saurin tashi tabi bayan mama. Hajja tace "maryam da kunyi xamanki anan kin dan murmure bakyaje wannan gidan naku  haka ba suyi ta kasaki a fefe ana tallanki.  


Mama tace "Hajja barni intafi da ita,  hankalina sai yafi kwanciya" Mal manu yana jinsu yayi musu shiru domin daga uwar (mama) har yar (Mimi) tausayi suke bashi. Sai yake ganin rayuwar Mimi kamar ta mama acan lokacin da ya wuce,  tabbas tarihi yana shirin maimaita kansa akan Mimi.  Yana fata itama nata qarshen labarin yayi kyau (Mimi) kamar inda na fadimarsa yayi kyau. Yanason yarinya fiye da duk jikokin da yake dasu, yana ganin wasu halayyar MARYAM (matarsa Hajja) a tare da Mimi kamar haquri da sanyin hali,  biyayya da kuma ibada. Kai hatta tafiya Mimi irin ta hajja take yi,  afuskane kawai basa kama (tafi kama da mahaifinta AL AMIN,  kamar photocopy dinsa ce) yana wannan tunanin har suka fita tsakar gida.  Ya kwalawa mama kira "Fadimatu" ta amsa "naam Baba"



Ta sameshi yace "duk sanda kikaga tana kuka karki hanata, kibarta tayi ya isheta,  baqin cikin zai ragu. Rashin kuka alokacin da abun kuka ya sameka kan illata lfyar kwakwalwa,  shiyasa daxu na barta tayi kukanta,  tashi kije Allah ya yi muku albarka ke da zuri ar ki" tace amin Baba Allah ya saka da khairan.


Umma kawai suka samu a tsakar gida tana yanka salak,  ta tashi ta bisu har daki tana cewa "maryam meya sameki haka duk kika tsummace?  Jiya nake cewa baffanku ya kamata aje a ganoki, tunda aka kaiki babu wanda yaje (kuji qarya)"  sukai mata shiru har ta gama surutunta.  Daga dakinsu gurin Anty ta nufa ta kai mata kanun labarai,  tun kafin a gama fada mata ta nufi dakin mama. 


Tana xuwa tace "maryam!😳 yanxu cikin ne yasa kika tarkato kika taho gida? Yara qannan bayanki suna gidan miji a zaune inma cikin ne sai dai mugansu dashi ya girma? Koda yake da alama cikin na wahalar dake duba da yadda duk kika qare,  yo uwarki ce har yanxu bata daina abun mutanen da ba,  wai ita kunya bata xuwa gidanku mu ba haka muke xarya gidan namu yayan ba" itama har ta gama haukanta basu tanka musu ba.  Mama ta tashi tana tunanin hali irin na matan gidan wai ai wata biyar ba a ga mutum ba, amma in anganshi ko irin nuna murna nan ta yaushe gamo. 



Mama ta dumamawa Mimi tuwon shinkafa miyar kuka tasa yajin daddawa ta isketa har bedroom kwance a saman gado ta kai mata "mimina tashi kici" ta girgixa kai alamar bataci mama ta hayo gadon ta dagata ta zaunar da ita tace "nasan mutuwar aure Mimi, nasan ciwon sakin aure.  Musamman saki irin naki na wulaqanci amma babu yadda zaki da hukuncin Allah,  barin kanki da yunwa bashine solution ba." ta karbi tuwon ta faraci,  mama ta qura mata ido tana kallonta,  tana son gano cikin da akace Mimi tana dashi.  Ita sam abun bai mata dadi ba,  dan dai babu yacce xatai da hukuncin Allah ne. 



Acan kasuwa kuwa Baffa yini yayi yana xirga xirgar neman Badaru, tun yana xuwa da kansa har ya gaji ya dunga aika yaransa.  Sai dai amsar dayace baixo kasuwa ba yau,  kuma abun kamar hadin baki shima abban Badaru yau be zoba. Kuma Badaru yaqi xuwa kasuwar ne saboda yasan sai Baffa ya nemeshi. 



Koda ya koma gida bai nemi mama ba duk kuwa da cewa ita keda girki,  ta karbi girki da yamma.  Wanda hakan ke nuna laifin Mimi ya shafeta,  itama ta fison haka.  Tasa yarta da jikanta (Dady dan Faty wanda ke xama a hannun Maman) agaba sukai kwanciyarsu. 


Sai dai yadda Mimi ta kwana jiya, haka ta kwana yau.  Ta dunga farkawa a firgice, kuma duk farkawar da tayi xataga mama xaune tana kalkonta. Farkawa ta qarshe da tayi tasamu mama tana sallah. Ita sai yanxu ta tuna in masifa ta sameka kana addua.  Dan haka ta miqe taje tayo alwala ta fara sallah kamar motsatstsiya,  duk sujjadar da tayi takance "ALLAH HUKUNCINKA NE WANNAN BANYI FUSHI BA,  ALLAH KA QARAMUN JURIYA"



Da sassafe Baffa ya yiwa gidan alh inuwa tsinke,  yana bacci xuwan kiran Baffa ya iskeshi. Sama sama suka gaisa Baffa ya karanta masa abunda Badaru yayiwa Mimi.  (saboda da abun ya tayar masa da hankali, abunka da wanda ba a taba sakarwa ya ba). Wata irin kunya kunya ta rufe alh inuwa,  ya tashi ya shiga gida yace da Baffa yana xuwa. 


Yasamu Umma a kitchen ya labarta mata abunda Badaru yayi,  gabanta ya yanke ya fadi ta xauna dabas a qasa tana sallallami tace "alh meye abunyi yanxu?  Har Badaru yayi saki ba tare da saninmu ba. Maxa kirawoshi yazo ya maida ita tunkan abu yayi nisa" ba musu ya dakko waya,  dan shima abunda yake shirin yi kenan.  


Dajin kiran ABBA da sigar da yayi masa magana, yasan lbrin sakin ya ruskesu.  Saboda haka ko wanka beyi ba ya tashi ya nufi gidansu yana qudurce cewa sai dai ayi duk wacce xa ai amma wlh ya gama xama da maryam. 



Dake Bahaushe yace baya bata da kadan,  be dade da fita ba mumy (Adda halima) yayar mama da Faty suka yiwa gidan tsinke.  Sukai sa a yabar muqullin a gurin wani me shagon kofar gidan,  suka shiga suka kwashe duk wata kayan sakawa na Mimi (suturu)  mumy taiwa wani me furniture waya yaxo ya kwashe kayan dakin ya siya kuma ya siya da daraja tunda sababbi ne kuma sun samu kulawar Mimi.  Kayan Badaru dake drawer mumy tasa Faty ta dau akwatin Mimi daya ta loda masa kayansa a ciki.  Kayan da tayi amfani da su kuwa kamarsu tukwane,  tea flask da food waemers, jugs cups plates duk tasa aka dunga rabawa maqota. Kayan abinci kuwa dana tea da lemuka duk tace a bar masa duk da kuwa Faty ta fada mata bashi ya siya ba, shinkafa kawai yake siya a gidan,  mumy tace duk hada ki bar masa Faty shine matsiyaci,  mukam ai bamu gaji tsiya ba. Ai mun auna arziqi tunda ya sakar mana yar. Dan ni dama gaba daya Badaru be mun ba a mijin Mimi.  


Maqota da aka basu kaya suka dunga shigowa godia,  suna yaba hallayar kirki irinta Mimi da alhinin rabuwa da ita,  wasu harda kuka sunai mata fatan alkhairi.  Wanda ya sayi Kayan yana gama fita dasu suma suka fito hannun Faty dauke da system (laptop) din Mimi da fos dinta suka qulla gidan suka bawa mai shagon muqullin,  drivern mumy ya loda kayan a mota dake seinna ce tas ta dauke suka shiga suka tafi. 



Badaru kuwa yana xuwa bai shiga gidansu ba,  saboda kar Umma ta takura masa ya mayar da maryam,  direct sitroom ya nufa gurin abbansa da Baffa ya gaishesu cikin daure fuska dan karsuce lallai ya maida Mimi.  Abbansa cikin fada ya fara yi masa jawabin abunda Baffa yazo dashi,  bayan ya gama ya bashi umarni da ya maida Mimi dakinta.  Badaru ya motsa ya qara daure fuska yace "gaskiya abba kayi haquri nagaji da xama da ita,  yarinyar Sam bata ganin girmana duk tsawon wannan lokacin haquri nake da ita" Baffa da yazo da nufin ciwa Badaru mutunci akan sakin Mimi yayi saurin sakkowa jin Badaru yace bazai maida Mimi ba. Cikin sanyin murya yace "haquri xakai Badaru duk matan haka suke duk wanda ka ganshi da matarsa sun dade haquri yake da ita" ya fada cikin qanqan dakai.


Badaru ya qarayin fuskar shanu yayi burus da lallashin da Baffa ke masa yace "Baffa tunda na auri maryam ban isa insata abu tayi ba,  Kullum cikin yimun gorin ilimi take wai ta fini ilimi.  Yanxu kuma akan bautar qasa ta tada balli wai sun kusa tafiya,  nace ta bari lokacin yayi inga yacce za ai sai kawai tahau xagina wai bansan darajar ilimi ba.  Dan haka ni na haqura da ita taje can ta auri wanda yasan darajar ilimi" hmmmmm (ni kuwa nace kuji qarya)  ya ciro takadda daga aljihunsa ya miqawa Baffa ga takaddarta nan,  dan Allah suyi gaggawar xuwa su kwashe kaya saboda xan saki gidan in karbe ragowar kudina. 




Baffa ya bishi da kallo har ya bar gurin, cikin yaba rashin kunyar Badaru.  Amma kuma baiga laifinsa ba tunda ya xayyano abunda Mimi tayi masa dole ya fusata.  Abbansa ya dubi Baffa "to alh kaji abunda maryam tayi masa, bata kyauta ba sam inai mata kallon mai hankali.  Inaga yanxu muyi haquri da batun kome tunda ya ruga ya fusata,  inda rabon xama gaba a sasanta."(kuji tsabar san kai)  Baffa bece komai ba sai gyada kai yayi ya tashi ya fita. 



Badaru na shiga gida,  ya tarar da ummansu a kofar sitroom din a tsaye idonta cike da kwallah.  Ga dukkan alamu taji duk abunda ya wakana.  Yana shiga ta fidda hannu ta tsinka masa mari,  wanda hakan yayi dai dai da shigowar abbansa. Ta kalkeshi tace " wlh tallahi nasan maryam bazata taba aikata abunda ya fada ba,  sharri yayi mata.  Ai suffar macen da xatayi hakan daban take.  Maryam ka saka ko Badaru?  Macen arziqi,  baka kyautawa kanka ba inajin kamar yar cikina aka saka,  inason maryam.  Kuma wlh sai kayi nadamar rabuwa da maryam. Kaje duniya ce" Abban ya daka mata tsawa "ke!  Karkiwa dana baki akan wata maryam, ko shi kadaine ya taba sakin aure?" itam ta daka masa tsawa cikin fusata tace anyi masa,  ko ka fini sansa ne.  Badaru sum sum ya fice ganin abun nasu zai zama fada. 


Ko daya koma gida yaga gidan fayau kuma yaga tulin kayan abincin da suka bar masa harda kyautar akwati sai duk jikinsa yayi sanyi,  amma daya tuna da Nafee da kuma soyayyarsu sai yaji wani kwarin gwiwa ya shigeshi. 

******** ********************



Baffa ya riga su mumy isa gida,  ya iske mama a gida bata fita aiki ba dan bata da kwarin gwiwar yin hakan.  Lokacin wajen 10:30 na safe,  yaran gidan duk sun tafi makaranta sai masu aikin gidan tsofaffi guda biyu wadan da ke wanke wanke da shara. Ya tsaya a tsakar gida ya kwallawa mama da Mimi kira, gabansu ya fadi a tare dan yanayin kiran kawai xai fada musu abunda kiran ya qunsa. Suka fito Mimi ta tsuguna mama ta tsaya daga gefensa,  matan gidan ma duk suka fito.  Ya kalli Mimi ya daka mata tsawa "keee!  Kinwa kanki daga gidan iyayen mijinki nake naje naji irin rashin mutuncin da kika shuka har ya sakeki,  kin cuce ni kin batamun tarihin gida,  ba a taba bazawara a gidana ba sai a kanki, wai har kece kike zagin mijinki na aure akan xaki tafi hidimar qasa.  Irin tarbiyar da nai miki kenan?  To tunda kinqi xaman gidan aure akan bautar qasa bazakije bautar qasar ba in anfara tafiya,  kuma tunda kika dawomun gida a matsayin bazawara bazaki huta ba.  Ya kalli shashin da yan aikin ke tsaye cirko cirko yace ku! Na hutar daku,  kuma xanci gaba da biyanku albashinku,  kubar mata aikin daga yau na maidashi doka tayi shara tayi wanke wanke kuma tayi girki, ya wulla mata takardar sakin a fuskarta yace ga certifacate dinki nan na xaman gida kitashi ki fara aikinki tun daga yanxu.  Ya kalli shashin da mama take yace kuma duk wanda ya sabamun doka akan aikin dana sakata Allah ya isa"



Kowa ya watse wasu cikin farin ciki wasu akasin haka,  Mimi ta nufi bakin famfo ta tara ruwa ta fara tulin wanke wanken,  sam idonta babu digon kwallah. 



Bai dade da fita ba,  su Faty suka shigo.  Drivern ne ya shigar musu da tulin a kwatinan Mimi,  sannan suka zauna ana gaisawa.  Faty tace "mama ina Mimi xan bata fos dinta" Maman tace tana waje tana wanke wanke,  mumy da Faty suka hada baki sukace "wanke wanke kuma 😳" Faty taci gaba da cewa waya sata wanke wanke ina masu aikin gidannan? " 


Baffanku ne ya sakata,  yanxu yazo yana fada yaje gidan su Badaru har sun bashi takaddar ta,  shine ya dora mata aikin gidannan gaba daya.  Faty najin haka ta dau jakar xata tafi,  mumy tace mata "Faty ki zauna ki huta mana"  ta kalli mummy idonta taf da hawaye tace " me xan xauna nayi mumy Baffa na shirin kashemun yar uwa.  Kuma wai mama tanaji tana gani baxatai magana ba" tasakai ta fice. 



Mumy ma ta miqe,  ta kalli mama kanta a sunkuye,  ta miqa mata tulin kudi "gashi kudin kayan dakin Mimi ne dana siyar ki ajiye mata" mama tace to akwai na sadakinta ma a hannu sai inhada mata. 


Mummy ta nisa ta fesar da iska cikin bacin rai tace "lokaci yayi da xan hada alh Buhari da human right akan abusing din maryam da yake yi (qungiyar kare haqqin Dan Adam)" mama ta xaro ido jin abunda da Adda halima tace.  Cikin sanyin jiki tace "Adda kiyi haquri ku gyaleshi yarsa ce yana da iko akanta" mummy ta daka mata tsawa " daallah yimun shiru shashasha ki zauna ya kashe miki yaya da bakin ciki sukenan kike dasu,  shi bashi da asara.  Wlh fadima inbaki tashi kin kwatarwa yayanki yanci ba wlh saina hadashi da human right" itama ta juya ta fice. 




Har inda maryam ke wanke wanke taje ta dafa bayanta,  ta dago ganin mumy yasata yin murmushi,  mumy tace "mamana kiyi haquri na ya qare akan lamarinki acikin gidannan na kusa in kwatar miki yanci kinji."  tace " to mumy ai ba komai ma wata rana bazan ba, wata rana ko ganina saiya gagara sai dai aje kabarina ayimun addua"  tace hakane Mamana Allah ya saka miki,  Allah ya albarkaci rayiwarki amma kafin ki mutu in shaa Allah sai kinji dadin rayuwa. 



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣9⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)


A hankali aikin da Baffa ya dora mata ya fara xamar mata jiki,  duk kuwa da farko tana ganin wahalar aikin.  Gidansu babban gidane wanda shararsa kawai aikine,  sannan ga uban wanke wanke saboda yini ake da fita da abinci daga gidan domin adadin mutanen dake karbar abinci a gidan suna da yawa. Ko dattijan da suke aiki a gidan (masu wanke wanke da shara) sau tari aikin yawa yake musu, sannan ga wanke toilets din dake tsakar gidan.  Batun girki kuwa dama da coal suke yinsa bisa manyan tukwanen tasa,  kuma me girki ita keyin girki sai dai masu aikin su tayata da wanke wannan yanka wancan.  To lokaci daya Baffa ya dorawa Mimi duk wannan aiki. ( qalubalenku iyaye, miji ya wulaqanta yarinya ko kuma ya korota ku iyaye memakon ku karbi qaddara ku kwantarwa da yarinya hankali,  a a sai a tsiri muzguna mata da sunan hukuncin ta naqin xaman aure. Wlh kuji tsoron Allah irin haka inba a samu me hangen nesa ba kome haquri sai ta gudu ta shiga duniya.  Haba ai abun yayi yawa gidan miji ba dadi gidan iyayema ba dadi) Da yake tana da qarfin zuciya duk sai aikin yaxo mata da sauki. Takan tashi tun asubar fari ta fara shara,  ana kira taje tai sallah da azkar sannan ta dora breakfast ta zauna wanke wanke.  Bakwai da rabi na safe ta gama breakfast sannan ta rabawa yan makaranta ta wanke bandakuna, taje gaida Baffa wanda intaje baya amsawa sai dai cin mutunci da gorin zawarci da yake biyo baya. Kafin taje gyara dakin mama takan tarar Maman ta gyara ta wanke toilet a qoqarinta na ragewa Mimi aiki.  


In mama ta tafi aiki takanji gidan yayi mata xafi bata samun sukuni sai 11 tayi lokacin da take dora abincin rana ko kuma in dady ya dawo daga skul ya zauna yayi tayi mata shirmen yara ko kuma tayi masa homework. 


Kafin kace meye wannan lbrin mutuwar aurenta yayi fitar dango,  ta hanyar Anty da Umma.  Karma Anty taji lbr domin gida gida take aiken mutuwar auren Mimi,  kamar me rabon katin biki.  Inda kuma baxata iya xuwa ba ta buga waya ta fada.  Har gara Umma takan boye farin cikinta akan mutuwar auren, amma Anty a fili take nuna murnarta.   


A irin hakan lbr ya riski fauxa  qawar Mimi wacce suke maqota na kusa,  da farko bata yarda ba a ganinta in hakane Mimi xata fada mata.  Dan haka taje gidan da kanta,  ta iske mugun lbr kuwa domin ganin da taiwa Mimi tana tulluqar aiki ya tabbatar mata da ingancin maganar. 


Can cikin dakin Mimi (dakinta na yan matanci) suka qule. Fauxa ta riqo hannunta Mimi ta bude baki xatayi magana fauxan ta tsaidata tace "basai kince komai ba qawata,  nasan halin da kike ciki ni da ke qadadarar da Allah ya dora mana kenan. Allah ya sa muci jarrabawa" ta fada tana share hawaye, Mimi ta goge mata hawaye tace "kiyi haquri fauxa,  bakiji daga bakina ba ganinayi kyakykyawan lbr ake fada" tace nagane Mimi kuma  banyi fushi ba,  Allah ya bamu haqurin jure halin da muke ciki" Mimi tana murmushi tace amin qawata. 


Tun daga ranar Kullum sai fauxa da shigo debewa Mimi kewa,  in ta dawo daga aiki (tana aiki a wata private skul). A duk sanda ta shigo Anty kan saki shewa tace " ayyuririri bazawara qawar bazawara 🤣 Allah ya sa a dade anayi zaurawan asali." babu wanda ya taba tanka mata.  Kuma daya abun takaicin shine : Baffa yasan tana haka amma bai taba hanata ba ko ya tsawatar mata,  wanda hakan yasa ta qara qaimi wajen cin fuskar Mimi.  Ga kwanuka da ake batawa da gangan da kuma bata gida duk dan a qara mata aiki. A duk sanda fauxa ta shigo taga Mimi na aiki takan Sabe mayafinta ta taya Mimi aiki. 



Bayan haka kuma,  Anty Kullum cikin gayyato mutane take dan suxo suga Mimi,  kuma takan yi musu jagora har dakin mama a cewarta wai suxo suga gyatumar da tai wata 5 a gidan miji auren ya mutu.  Ko kunyar idon mama bataji,  kuma abun sha awa daga mana har Mimi babu wanda ke tanka mata,  ko ya nuna damuwa kan abunda tayi.  Wanda hakan shike baqanta mata rai kwarai,  domin ta fiso su tanka mata. 


Abun na Anty sam babu shaawa,  kamar ba mace ko kuma bata da yaya mata.  Ko tayi alqawari da nata mijin bazai taba sakinta ba.  



Daya matsalar itace : muguwar rashin kunyar da Mimi ke fuskanta daga qananan yaran gidan yan mata,  dan sau tari sukan bangajeta su wuce sai dai ta kauda kanta tayi kamar bata ganiba.  Domin suna yine fisa umarnin iyayensu, wadanda ke zaman shirin ta tanka su cimata mutunci.  Dan tashaji Umma na cewa " mutum bazai kasa xaman gidan aure ba, sannan ya dawo gida ya takurawa qananan yayanmu."


Duk mai imani inyaga Mimi a wannan lokaci saiya tausaya mata,  domin ta qare ta mole tayi wani yagwal da ita.  Babu rashin ci babu rashin sha, amma duniya ta juya mata baya.  A wannan lokacin sai ta kwammace xaman gidan Badaru akan mazan gida.  Wai dama haka mutuwar aure take?  Tambayar da take yawan yiwa kanta kenan.  Kota ina babu sauqi, sai a gurin ubangiji.  Ta haqiqance babu mai santa yanxu sai mama da fauxa da kuma uwa uba ya Faty. 



Faty tun daga ranar da suka debo kayan Mimi bata kuma xuwa gidan ba,  domin sam batasan ganin Mimi cikin halin da Baffa ya sakata.


Mama ce ta lura da soshe soshen da Mimi takeyi,  ta turketa ta tambayeta babu kwana kwana ta fadawa mama infection ke damunta.  Dan haka mama ta bugawa Faty waya tace gobe tazo ta tafi da Mimi asibiti,  qaiqayin bandaki na damunta. 



Saboda tasan da xuwa asibitin tun qarfe hudun asuba ta tashi ta fara aikinta,  bakwai dai dai ta gama Faty taxo suka dau hanya.  


Likitan mata ta gani, ya basu kwaje kwaje,  saboda Faty ya sa basubi layi ba suka gama da wuri suka kai masa result din.  Ya duba yace "nikam banga ciki a jikin result dinta ba,  amma ta iya yiwuwa akwaishi,  matsalar magungunan da tayi ta amfani dasu suka cushe mata mahaifarta ya kuma haifar da rashin xuwan period dinta.  Ya kalli Mimi yace ko anan gaba ki kiyayi cusa abu a gabanki,  gurin yana da rauni kuma yana da saurin karbar kwayoyin cuta.  Kinga dalilin cushe cushen da kikayi yasa ciwon qaiqaiyin tsanani a jikin ki.  Amma yanxu ga magani nan  da allura inkikayi amfani dasu yadda ya dace duk qarfin ciwon sanyi zai rabu dake, kuma suna da qarfi sosai kici abinci sosai kafin kisha" sannan ya rubuta wani abu a takadda ya bawa Faty yace " wannan maganin kinsan yadda ake amfani dashi,  duk sanda jinin al adarta yaxo shedar ta warke daga ciwon kenan sai ki siya ki saka mata acan ciki ki tabbatar ya taba mahaifarta,  tunda kince sister dinki ce xaki iya yi mata a gida basai kun dawo ba" 



Suna kan hanyar xuwa gida daga asibitin Faty ta gallawa Mimi harara tace "Mimi har magani kike cusawa a jikin ki dan ki burge Badaru ko?  Mutumin da baisan mutuncinki ba?"  Mimi ta marairaice tace " wlh ya Faty ban taba shan komai ko cusa wani abu a jikina ba,  kinaga kazar da kuka yimun ma kafin a kaini ko dandanata banyi ba. Kawai dai lalura ce Allah ya doramun"  Faty ta sauke fushinta dajin abunda Mimi tace,  kuma tasan tabbas hakan ne domin kazar ma itace ta cinyeta bayan Mimi taqi ci.  Dan haka ta sauke murya tace "ko kuma Badaru ya debo ya goga miki ba."



Da xuwansu gida tayiwa Mimi alluran tasha maganin sannan Faty ta daura mata drip (qarin ruwa) domin a cewarta Mimi ta dashe da yawa jikinta na buqatar ruwa da gaggawa. 



Kwana 8 da sakin Mimi aka tashi da azumin watan ramadan. Kuma suka tashi ta baquncin Baba Saude (wata yar uwa a gurin Baffa, wacce ke xuwa daga can garinsu Gombe duk azumi da kuma sallah ta karbi kayan azumi ko kuma kayan sallah da Baffa ke bawa yan uwansa nacan taje ta raba)  Baba saude irin mutanenne masu fadar gaskiya,  dan haka take da baqin jini gurin matan Baffa (Umma da Anty) bayan haka kuma suna baqin cikin abunda take karba a gurin Baffa ta kaiwa yan uwansa na qauye. 


Mama dai babu ruwanta cikin wannan shaani,  tsakaninta da Baba saude kyakykyawar muamala ce.  Duk sanda tazo takan tsinci kwancen kayanta kona Mimi dana dady ta bayar akai qauye a rabar,  sannan kuma takan bata yan kudi ta qara akan na Mota.  Ko kunsan alheri kan saka qauna,  dan haka tafi sauran matan Baffa daraja a gurin Baba saude.


Wannan xuwa da tayi ta tarar da baqin lbrin mutuwar auren Mimi,  ta jimanta kwarai domin ta sauyawa halin da taga mimin aciki.  Basai anfada ba kasan xaman gidan baya mata dadi,  ga uwarta me haquri tasan duk cin kashin da xa aiwa Mimi mama bazatai magana ba.  



Ana haka Anty ta fito tana kumfar baki cewar Mimi bata dora abincin shan ruwa da wuri ba.  Baba saude ta cafe maganar da cewa "ke yanxu jamila dan yaya buhari ya dorawa maryam aiki sai ku sakar mata har abincin azumi?  Ai aikin azumi yafi qarfin hannu daya " 

Umma ta shiga cikin maganar da cewa " ai bamu muka sakata ba,  ubanta ne ya sakata kuma dole tayi, sannan bamu mukaje taje tai rashin mutunci a saketa ba"  Anty ta qara da cewa "kemadai Hajara kike bata bakinki,  ai abunda uwa tayi shi yar take maimaitawa,  inbaki manta ba ai haka uwar ta dunga yawan aure aure kafin Allah ya hadata da Aminu ta maqale masa sannan daga baya aka dawo kan mijinmu.  Waya sanima ko garin yawan asiri akan korarmu abun ya koma kan yarta?  Ai maryam gadan aure aure tayi da mugun abu a gurin uwarta,  Alhmdl Allah ya mayar mata da mugun abunta kanta kuma in shaa Allahu mutuwar aure yanxu kika fara,  da yardar Allah sai kin auri maza goma" 


Mimi najin haka ta fashe da kuka me cin rai,  mama ta fito daga daki taja hannun Mimi.  Baba saude ta harxuqa ta tofa Anty yawu tare da cewa " aniyarki ta biki,  kuma ki tuna kina da yaya mata,  fata nagari kuma lamiri.  Saboda haka wlh ki kiyayi Allah, harshenki zai jawo miki bala in da yafi qarfinki,  ba a yiwa Allah ixgili" Anty tace kema taki aniyar ta biki.  Baba saude tai saurin cewa "amin,  ai duk wanda kikaji ance aniyarsa ta bishi yaji haushi wlh aniyar ba me kyau bace.  Kuma indai ana gadon mugun abu ke hana zaman aure da naki yayan basu xauna ba."


Taci gaba da mita ita kadai a tsakar gida,  haka al amuran gidannan suka dame? Lallai yaya Buhari inbewa tufkar hanci ba tabbas jamila xata watsa masa gida.  Taja tsaki mtsewww.  Inbanda abunsa ma meye na damuwa da mutuwar auren maryam?  Sama da yaya goma suna gidan miji a xaune dan Allah ya dora masa qaddara akan daya ya kasa dauka.  Bare inda mutuwar aure ta zama gama gari,  aimu ko acan qauye ba a tsangwamar mace dan aurenta ya mutu. 


Umma ta leqo ta taga tace da Baba saude "karki kuma cewa yarsa ce,  domin shi duk nasa yayan na gidan miji a zaune basu taba zawarci ba saboda basu ga munayiba"  Baba saude ta katseta da cewa "to saiki zuqe jinin maryam daga jikin Buhari domin sharia ta riga ta bashi ya" Umma tace ai shi da kansa yace ba jininsa bace,  shi jininsa basa mutuwar aure.  Taje can ta nemi inda tayo gadan aure aure. 



Baba saude bata kuma cewa komai ba,  sai daga murya tayi yanda Mimi xata jiyota tace "ke maryamu kiyi shiru kinji,  Allah ya na tare dake,  shi dora miki kuma in shaa Allah xai baki mafita"


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 3⃣0⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)


A haka ta fara axumi wanda ya qarasa ramarta ta qazanta,  domin sam abinci baya ciyuwa a gurinta. Ta dage da adduar neman sauki gurin ubangiji,  kuma duk wani masoyinta na tayata.  Kullum in ansha ruwa Mimi ke xuwa gidansu fauxa su tafi masallaci yin sallar tarawih domin gidansu fauxa yafi kusa da masallacin.  Sau tari a masallacin ma bata rasa masu yin zundenta da qusqus din mutuwar aurenta. 


A al adar gidan Baffa duk goma ga watan Ramadan yayansa kaf maza da mata, masu aure da marasa aure har na wani garin ana haduwa asha ruwa agida saboda sada xumunci.  Kuma uku ga kowacce sallah (sallah babba da sallah qarama) suna kuma taruwa shima aci abinci a sada xumunci ayi hotuna.


To wannan karon ba ai shan ruwan goma ga azumin ba kamar yadda aka saba,  saboda ya jafar bezo daga kaduna ba inda yake aiki.  Sai da azumi yayi rabi (15) sannan yaxo kuma a ranar aka fara shirin shan ruwan.  Yawanci duk yayan gidan mata sukanxo tun azahar a hadu ayi aikin abincin shan ruwa.  To yau dinma hakance ta kasance,  wadanda ke farin ciki da mutuwar auren Mimi da wuri sukazo sukaga dahir sannan suka dunga shewa suna sakin habaici. Masu hankalin ciki kuwa,  abun bai musu dadi ba saboda haka Anty Adawiyya ta jagorancesu sukaje dakin mama suka jajanta mata mutuwar auren sannan suka taushi Mimi tare da bata haquri akan abunda yan uwansu ke mata.  Mama taji dadin wannan karamci da sukayi mata ta dunga godia kamar sun bata wani abun.  



Azahar kowa ya hallara inka cire ya Faty da bata taso daga aiki ba,  duk suna baje a tsakar gidan suna aiki, masu gyara kaji nayi, masu hada zobo nayi masu gyara ayar kunun aya sunayi da masu gere dankali.  Baby tai sallama ta shigo jikinta sanye da uniform da alama daga skul take. Baby itace ya ta tara a dakin Anty,  shekarunta bazasu wuce 15 ba,  tana aji 1 a babbar sakandire (senior secondry).


Tana shigowa wani almajiri ya biyota,  "wai ana kiran wacce ta shigo yanxu" inji almajirin.  Baby ta murguda baki cikin tsabar fitsara da tashen balaga tace " wlh na tsani naci, tundaga makaranta yake bina maye."  


Anty tai saurin fitowa daga kitchen tace "je kace yarinya ce bata tsaiwa da samari" yaron ya fita fadar abunda aka aikeshi. 


Anty ta ruqe haba cikin sigar al ajabi tace "kai wadannan yara da farin jini suke,  babu dama su fita sai an biyosu.  Wlh bari Baffa ya dawo mu xauna ayi magana,  gara tanayin candy a aurar da ita inyaso jamiar tayi a gidan mijinta.  Aini nadau darasi da barin da ya dade a gabanka, qarshe kwantai yakeyi.  Wlh tana candy xan aurar da ita" (kunji fa kamar auren a hannunta yake,  mudai munsan koda miji a hannu aure sai Allah yayi tunda aure lokaci ne.)


Rashida ta kalli shashin da Baby take tsaye tana murmushi saboda jin abunda uwarta tace na cewar tana da farin jini,  tace "aike Baby ki godewa Allah tun yanxu anfara kawo miki hari,  alamar cewa ba zaki Bandaro ba.  Saboda wlh in mutum yayi kwantai ko yaje gidan mijin ba iya xama yake ba" ragowar yan jam iyar Rashida (masu qin Mimi) suka saki dariya tare da cewa "wlh kuwa 🤣🤣🤣"


Anty Adawiyya dake gefe ta cije lebe saboda duk wanda ke gurin ya fuskanci inda maganar Anty da Rashida ta nufa,  Anty Halima ta kalli Adawiyya cikin takaicin abunda uwarta da yar uwarta sukai (halima yar Anty ce) tace Anty wai haka zamu zuba ido abubuwannan suci gaba a gidannan,  infa akaci gaba da haka nan gaba kadan xumunci xai watse mune manya ya dace mu gyara abun.  Anty Adawiyya tace " Halima mexance?  Ai baka canja mutum kina ganin kwanaki da nai hukunci akan abunda Rashida kewa Mimi qarshe abun fada ya xama tsakanin Umma da Anty.  Saboda haka duk wanda aka fada masa yaqiji sai a kyaleshi duniya tai masa nata karatun"



Suna zaune akan qatuwar tabarma da aka malala a tsakar gidan,  kayan abinci ne jibgi a gabansu kowa na diban abunda yake so yana ci.  Duk zuriar gidan sun hallara tundaga kan Baffa, matansa, yayansa da surukarsa (matar yaya Ali) da kuma jikokinsa.  Anata hira ana jin abinci cikin raha,  ya jafar ya kalli Baby yace "ke jeki kice Mimi ta fito,  inna kuma aiko ta fito bata fito ba sai ranta ya baci." wannan shine karo na 3 da yake aikawa kiran Mimi amma taqi fitowa,  kuma ba wani abu ke hanata fitowar ba sai gudun abunda ka iya faruwa inta zauna a cikinsu.  


Umma tai tsaki ta dan harari jafar,  tace "to kai ina ruwanka da rashin fitowarta,  ai dan ta nuna muku mugun halinta ne yasa bata fito ba,  tayi abu yazo ya dameta ya hanata shiga cikin mutane." 



Wannan karon Mimi tare suka fito da Baby,  sanye take da hijab me hannu.  Faty bataso tilastawar da ya jafar yayi Mimi ta fito ba saboda tasan dole sai anyi abunda xa aci xarafin Mimi.  



Ganin babu guri a inda Baby ta xauna yasa Mimi tayi nufin tsallakewa can kusa da Anty safiyya (matar ya Ali) . Ganin da Rashida tayi Mimi na shirin tsallaketa yasa ta miqe qasa tare turo qatan cikinta,  Mimi ta daga qafa xata tsallaka a hankalce saboda kar ace tayi wani abun ko ta buge mai ciki Rashida tasa daya qafar ta tade Mimin. Ai kuwa ta yanke jiki ta fada kan Sumayya take zaune da jaririnta dan 4 month akan cinya, sannan ga kofin shayi sai tururi yake a gabanta.  Cikin axama Sumayya ta ture Mimi daga kan jaririnta ta tura mimin kan ruwan shayin tare da cewa "bakya ganine zaki kashemun da?" 

Zafin ruwan shayin bai gama ratsa Mimi ba taji saukar mari a kuncinta.  Tai dafe kunci tare da dagowa taga wanda ya mareta tai arba da Baffa sai huci yake yana kallonta cike da tsana yace "dan bakisan ciwon haihuwa ba shine xaki fado mata akan jariri?  Ke dan kin gaza xama a naki gidan ki haifi naki dan zakixo ki fado musu ka?  Ke wace irin muguwar yarinya ce". 


Umma tace ai dama tunda aka tilasa mata fitowa batai niyya ba nasan saitayi abunda xata sosa mana rai kuma shine muguntar taki xata qare akan jikana?  Rashida na gefe sai murmushin jin dadi take. 


Duk wanda ke gurin ya lura da abunda ya faru saboda hasken nefa tanyar a tsakar gidan.  Mimi abun yayi mata yawa ga zafin qonewa ga zafin maganganun Baffa,  ta fashe da kuka tace " Dan Allah kuyi haquri,  inwani laifin nai muku kuka tsaneni dan Allah ku fadamun in gyara" tana kaiwa nan ta shige daki.


Ya jafar da tausayin Mimi ya hanashi daurewa ya kalli Baffa yace "Baffa wannan wane irin hukunci ne?  Wlh ina kallon abunda ya faru, Rashida ce ta turota dan me xaka goyi bayansu qonata fa sukayi" Anty tai saurin kare Rashida da cewa karkai mata sharri, kawai dai ta shirya mugutar fadawa kan Rashida tasa ta naqudar dole ita kuma Allah ya bata sa a ta tureta.  Baffa ya hau borin kunya da "yimun shiru jafar, kaine ka haifeni?  Ko kai xakaimun hukunci a gidana"



Faty tabi bayan Mimi itama tana kuka. Jafar ya kalli shashin da mama ke zaune yaga tananan inda take ko motsawa batai ba sai dai ta kasa cin abincin sai juya tea take da spoon.  Anty Adawiyya ta dakko qaramin try ta xuba duk nau in abincin dake gurin ta bawa Anty safiyya tace "kaiwa su Faty daki"  Faty na zaune kan kujera tana kuka tana shafawa Mimi jelly a dantsen hannunta inda ruwan shayin ya xaba.  Anty safiyya ta bata abincin tace ki tabbatar Mimi taci. Kuyi haquri Allah baya zalunci kuma ya haramtashi garemu in shaa Allah xakuga sakamako. 



Faty ta dunga diban abincin da hannu tana bawa Mimi,  ita kuwa ba musu ta dunga karba tanaci.



Tun jiya da abun ya faru har ixuwa yanxu da gari ya waye tunani take. Wai shin meyasa indai aure ya mutu a Society dinmu laifin kan zama na ya mace ita kadai?  Wai yaushe YA MACE xata samu yanci a Society namu?  Wadannan sune tambayoyin da ta rasa me amsa mata. 


Kanta ke mugun ciwo,  wanda tasan tunani ne ya haddasa matashi.  Ga kuma yanxu mararta ta daure,  alamu kamar period pain.  Tananan kwance,  taji ciwon marar ya fara tsananta kuma taji danshi a qasanta.  A fili tace "babu ciki a jikina kenan kamar yadda Dr yace" gudun kar ciwon mara ya galabaitar da ita gashi mama ta tafi aiki yasa ta tashi taje parlour ta dakko gwangwanin maltina a fridge tazo ta balli maganin ciwon mara tasha.  Lokacin ko ganin gabanta bata iyayi saboda tsananin ciwon kai. 


Tana kwance tana murqususun ciwon mara da ciwon abunda Baffa Yayi mata,  itadai tun take da Baffa bata taba gani ya dora hannunsa akan wani da a gidan ba sai ita.  Koda yake itakam a gidan tana da banbanci da kowa,  domin Baffa ya mata abubuwa da yawa da bata taba gani yayiwa wani ba. 


Da farko bayan qin biya mata ko sisi a cikin hidimar karatunta,  yazo ya takura mata da sunan taqi aure,  yayi mata auren dole sannan auren babu dadi bai taba taka gidanta da sunan yaje ganinta ba,  duk kuwa da cewa dabiar sa ce xuwa gidan yayansa yaga halin da suke ciki kuma ya musu alheri.  Amma ita tunda aka kaita ko waya bai taba yimata ba.  Abu na qarshe shine: anyi mata sakin wulaqanci ta dawo gida ya kuma takura mata,  takurar da tafi ta farko,  ga kuma duka anfara jiya.  



A wannan gaba taga ya dace ta karbi shawarar da xuciyarta tasha bata a kwanakin baya,  dan haka ta miqe ta dauki kudi ta fita ta tsaya a soro ta aiki wani almajiri ya siyo mata abunda take buqata.  Tananan tsaye yaron yaje ya kawo mata aiken,  ta bar masa ragowar canjin. 



Da magriba ta gama duk wani aikinta ta shige daki tunda ba azumi tayi ba, tabar mama tana shan ruwa a parlour. 



Fauxa da tagaji da zaman jiran Mimi ta biyo mata zuwa sallar tarawih bata zoba ta tashi domin biyawa Mimi,  dan taji har an tayar. 


Ta sami mama a parlour suka gaisa Maman na shirin shiga bedroom tace "qawartaki na dakinta tun dazu kinga ma ko ruwa bata sha ba" tace to bari in dubata. 



Shigar Fauxa dakin tayi dai dai da lokacin da Mimi ta daga kwalbar FIYA FIYA (abunda aka siyo mata daxu) xata kai bakinta.  Fauxa ta kwala kiran "MIMI" a razane 😳 tare da doke hannun mimin.  Kwallah kiran da tayi ya janyo hankalin mama daga bedroom, taiwa dakin tsinke tana tambayar lfy?.  Fauxa batabi takan tambayar da mama keyi ba.  Ta qarasa ta riqe kafadun Mimi tana girgixata cikin kuka tana cewa "Mimi kashe kanki xakiyi akan mutuwar aure?  Shin in kashe kanki wanda ya sakeki yana da asara ne?  Mesa xakiyi haka?  Duk fa abunda xai faru ya riga ya faru.  Ansake ki,  an takura miki,  anyi gulmarki,  anmiki sharri.  Inbaki sani ba maganganu da yawa ke yawo akan mutuwar aurenki.  Akwai masu cewa cukumar mijinki kikayi kina zaginsa ya sakeki,  wasu kuma suce wai sata kikai masa ya sakeki,  ke harda masu cewa ya kamaki ne kina lesbian (neman mata) ya sakeki.  Amma duk wandannan maganganu da nakeji bana fada miki saboda kar in daga miki hankali. Amma shine yanxu xaki kashe kanki Mimi?  Why Mimi,  Why. Wlh indai akan baqin cikin namiji kike haka gara ki dena,  shin ni ba a sakeni ba?  Ni harda Da aka sakeni mutu nayi?  Ko takurar da aka yi miki ba ita akemun ba,  kafin Baba ya gane gaskiya ya sakarmun mara?"



Maganganun da Fauxa keyi yabawa mama amsar tambayar da take yi,  dan haka cikin kuka ta juya tabar dakin.  Mimi ta gigice ganin kukan mama dan tasan ba qaramin abu kesa mama kuka ba,  tai gargawar biyo bayan mama tana cewa "mama ki yafemun na tuba 😪"  


Fitowar mama tai dai dai da shigowar Faty parlourn, ya Ahmad na biye da ita.  Dan bata gamsu da yacce tabar Mimi a jiya ba shiyasa ta kuma xuwa ta taushi Mimi.  Ta iske wannan mugun lbr, fauxa ta fada mata tace "WHAT" kalmar data janyo hakalin matan gidan, nan da nan kuwa suka cika qofar dakin mama suna kallo.  Ya Ahmad kuwa gurin mama yaje ya tsuguna gefenta yana nemarwa Mimi yafiyar abunda tayi. 



Faty kallon Mimi take da wata irin fuska 😡 wacce babu wanda ya taba ganinta da ita.  Mimi tana rabe jikin bango,  cikin kuka take furta "am sry,  am so sry sister"  Faty batabi takan haqurin da Mimi ke bata ba,  ta kifawa Mimi mari,  ta kuma kifa mata wani,  ta qara mata.  Ataqaice dai sai da tayiwa Mimi mari guda 6 xafafa.  Mimi idanunta a runtse,  bata dauke kanta ba, ba kuma ta fasa furta "am sorry sister"  


Wadanda ke bakin kofa suna kallo abun yayi matuqar girgizasu,  domin ba qaramin abu zaisa Faty ta daki Mimi, bama su taba gani ko fada Faty taiwa Mimi ba bare duka.  Dan haka kansu ya qulle suka rasa lefin da Mimi ta aikata Faty ke mata wannan hukunci.  Kuma ta wani barin abun ya burgesu domin daga Anty har Umma babu wacce daya daga cikin yayanta na sama ya isa yayiwa na qasa hukunci haka,  ba ai gagarumin yaqi ba. Kuma daya abun burgewar har wanda akaiwa hukuncin yana bada haquri. 



Faty na gama marin Mimi itama ta fashe da kuka, ta janyo mimin ta rungumeta tsam suka xube qasa tana shafa kan Mimi tare da cewa "is Ok sister" Fauxa ma ta matso kusa tana lallashin Mimi cike da yabawa hukuncin da ya Faty tayi mata.  A xuciyarta tana aiyana duk renda Allah ya bata yaya mata xatayi iya yinta ta hada kansu kamar yadda mama ta hada kan Faty da Mimi. 



Yan kallo kuwa dole suka watse ganin film ya qare.  Ya Ahmad ya tafi ya bar Faty ta kwana,  saboda halin da mama ke ciki.  



Can tsakiyar dare suna kwance kan doguwar kujera,  mama dauke da Dady kan cinyarta,  sai Faty dake zaune tana bacci Mimi kuma ta tada kai da tata cinyar.  Tun faruwar abun Mimi ke bawa mama haquri amma mama tayi kunnan uwar shegu kamar batajin abunda Mimi ke fada,  yanxu ma sai kuka take tana qara neman gafarar mama.  Mama ta shafa fuskarta tace "na haqura Mimi, amma ko wane irin hali xaki shiga karki qara yunqurin halaka kanki,  kinga ku kadai nake daku in kintafi kinbar yar uwarki ni da ita ya xamuyi?  Bakisan rayuwarki nada matuqar mahimmacin a gurin mu ba?  Danme xaki kashe kanki akan wadanda mutuwarki sukafi so akan rayuwarki?  Mimi kiyimun alqawari daga yau zaki cire duk wata damuwa a ranki ki fuskanci abunda ke gabanki.  Da ace mutane suna riqe abunda ya riga ya wuce wlh da baqin cikin ya kashe rabin mutanen duniya.  Saboda haka past is gone forever, ki gyara present dinki,  future kuma ki barwa Allah shi yasan abunda future xata xo miki dashi." 



Mimi ta gyada kai cike da gamsuwa da kalaman mama, sannnan ta qudure yin aiki da abunda maman tace mata.  


Ta yunqura ta miqe xataje toilet domin canja pad din jikinta da ta jiqe,  mama tai saurin cewa ina xaki?  Tace " xan canja pad ne"  wani farin ciki ya xiyarci mama,  jin Mimi taga jini wanda hakan ke nuna babu ciki kenan.  Ta dunga godia ga Allah domin batason Mimi ta haihu da Badaru.  Tace da mimin muje in rakaki,  Mimi ta zaro ido 😳 tace "mama toilet din xaki rakani?" mama na tafiya tace "eh nasani ko ki kuma yunqurin halaka kanki"  Mimi ta marairaice tace " mama zargina kike wlh bazan kuma ba na baya ma da nayi kuskure ne."



Yan kwanakin da suka biyo baya ta dan samu sauki,  amma fa ba sauqin aikin gida ba saukin damuwar dake xuciyarta a bisa amfani da shawarar mama.  Ta kuma yardarwa kanta xatai karbi rayuwa a duk inda taxo mata. 



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 3⃣1⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Ranar da Mimi tayi wankan tsarki ranar Faty tazo gidan,  ta tasa Mimi a gaba harda yan kayanta set 2. Mimi tace "ya Faty Baffa inyaxo ya tadda banyi aiki ba xaimun fada." Faty ta fallara mata harara "xan dura miki xagi Mimi,  ana xancen lfyarki kina xancen fadan Baffa?  Ko kin manta abunda Dr yace in kinga jini insamiki wani magani?" Mimi ta marairaice tace "ya Faty ai na warke ko sati banyi ina amfani da maganin ba na daina qaiqaiyin, wlh kamar ban taba yiba." Faty ta kuma watsa mata harara tace " ke wlh sai kin bini in yaso in kin dawo Baffa ya kasheki bashi kikejin tsoro ba?" tace tuba nake sis muje 😊



Bayan sunsha ruwa sun huta,  Faty ta dakko maganin tasa safar hannu tace da mimin kwanta.  Mimi ta waro ido tace "ya Faty😳 yanxu wai saina bude jikina?"  Faty tace "a a karki bude insa miki magani, amma ai kin budewa Badaru ko? Mimi najin haka ta kwanta ta bude jiki,  Faty ta gama yi mata gwaje gwaje tasa mata magani.  Tanata tsaki tare da cewa " wannan mutumin ya cuceki Mimi dole sai anmuki stitches (dinki)" Mimi ta zaro ido cikin kidima 😳😳😳 tace "ya Faty na samu qari ne? Naga masu haihuwa akewa dinki" tayi tsaki tace "ba gara wacce ta haihu dake ba, ita tasan haihuwa tayi.  Kuma ba sai lallai masu haihuwa akewa dinki ba. Ba qari kika samuba amma ya miki barna a jikin ki ya nuna mugunta wajen kusantarki, gara ma da Allah yasa nagani amma wannan in kikayi aure ai sai kiji kunya, wata 5 a gidan miji amma wani mijin ya sameki sakwakwa haka ai sai yace qarya ake cutarsa akai."


Washegari kuwa tana dawowa daga aiki tace da Mimi ki shirya in ansha ruwa xamuyi aikin, na siyo kayan aikin masu kyau wanda in anyi basai an ware ba zaibi jikin ki. 


Kafin asha ruwa Mimi ta tsure,  mugun tsoron dinkin takeji kamar tace a fasa.  Haka dai ta haqura aka fara dinkin,  tunda aka fara ta runtse idonta tare da cije lebenta saboda azaba.  Har akayi stitches din aka gama ko tari bataiba,  Faty ta dunga yabawa dauriyar da Mimi tayi.  Mimi ta kalleta tace "ya Faty xai kai kwana nawa kafin ya warke?" Faty tace "kayan aikin da nayi miki amfani dasu masu kyau ne,  amma duk da haka ya danganta da irin jikin ki da kuma irin kulawar da kikayi dashi." ta bata magani ta hadiya saboda ya kashe xafin gurin, ta qara da cewa indai jikinki me kyaune gurin zai koma fresh kamar baayi dinki ba. 



Kwananta biyar a gidan Faty, ta samu nutsuwa da kuma sakewa ga kulawa da shiga ruwan dumi saboda stitches din. Nan da nan kuwa ya kame kamar bame dinki ba tafiyarta ta koma normal.  Kuma a ranar ne Baffa ya lura ko kuma aka kai masa gulmar Mimi bata gidan.  Shima daya lura sai yaga baya ganin kai kawonta a tsakar gida, kuma tsaftar gidanma ta ragu saboda masu aikin sun karbi aikinsu, lokacin da Mimi  na aiki gidan yafi tsafta.



Dan haka ya bugawa Mimi waya yace ta taho kafin ranta yayi mugun baci,  a cewarsa tunda batai zaman nata gidanba bazataje ta kashewa wata nata auren ba. 


Sai wajen goman dare ya Ahmad ya maidota gida.  Ta dunga lallaba jikinta saboda kar stitches din ya samu matsala,  duk abunda xatai tana kula sannan ko mama batasan da xancen dinkin ba.  



Azumi ya tasamma qarewa anata shirin sallah,  a wannan lokaci ita kanta tasan ta samu sauki.  Domin tana jin jikinta a matse kamar lokacin da tana 15 years, ita kanta tasan ta samu canji a jikinta.  Gashi ta dan murmure saboda kwanciyar hankali data samu.



Ranar 3 ga sallah gida ya cika kamar yadda suka saba zuwa, kowa cikin kwalliya ta burgewa da qoqarin nuna tattalin arziqin mijinsa. 😄



Mimi bata fita tsakar gidanba inda aketa photuna ake shewa, saboda tayi alqawarin dena shiga cikinsu duk rintsi.  Tana zaune parlour tana karatun wani novel da aka turo a grp,  Rashida da tawagarta suka shigo.  Rashida tace ina mama?  Xuwa nayi inyi kallo a dakinnan parlourn Umma yara sunyi yawa.  Ta xauna akan kujerar kusa da Mimi,  ragowar wadanda suka shigo tare ma duk suka nemi gurin xama.  Ta kunna kayan kallon sannan tasa fefen CD na film din ZAURAWA na AISHA DANKANO,  wanda takanas Rashida ta taho dashi daga gidanta dan kawai taci zarafin Mimi.  Ana kallon film din su Rashida na hira tare da aibata zaurawa da tsine musu,  wai a cewar Rashidan "duk wata bazawara karuwa ce,  suna fakewa da xawarci suna neman maxa. Kuma da mijinki ya auro miki bazawara gara ya auro miki visites domin bazawara saita nuna miki tasan namiji.  Ta kuma gyara xama tace,  ai duk macen da ta fara mutuwar aure to wlh haka take qare rayuwarta a aure aure yo dama mutum dakyar ya shiga bare yanxu." 


Mimi tayi banxa dasu tana danna waya, saboda ta kasa karatun novel din dan maganganun Rashida sun tabata.  A zuciyarta kuwa cewa take "rashin fita cikin nasu ma ban tsira ba tunda har dakin uwata anbiyo ni ana zagina" tana wannan tunanin har film din yazo dai dai inda Aisha Dankano ke cewa "ZAURAWA" nan take kuwa Rashida ta saita babban yatsanta saitin Mimi 👍🏼 tare da cewa "SUNE" ragowar suka saka dariya sukace Rashida baki da M. 



Anty safiyya dake dakin Mimi a kwance duk abunda suke tana jinsu,  kuma babu wanda yasan tana dakin.  Ta fara tunanin dalilin da yasa yan gidannan suke haka sai kace ba yan boko ba,  kawai dan aure ya mutu sai a takurawa yarinya. Itakam bataga laifin Mimi ba,  yarinyar tanada haquri da shiga rai.  Ta tashi ta fito ta riqe labulen dakin tace "tace meye haka nakeji Rashida?  Waike wace irin yarinyace mai neman fitina? Ki biyota har dakin uwarta kina insulting dinta?"  Rashida ta murguda baki cikin fitsara tace "babu ruwanki malama,  muna abunmu iya yan gida kinxo kinsa baki,  wannan aiba abunda ya shafeki bane" Anty safiyya ta nunota da yatsa tace "ke!  Kikiyayeni,  in kinsaba iskanci a kyaleki ni inkaimun Ali (mijinta) xansa ya casaki." Rashida najin haka tayi shiru dan tasan yaya Ali babu ruwansa ubanta zaici. 



********   ********      *******

Kwana goma dayin sallah ta kuma tsintar kanta cikin jini,  wanda ke maxaunin jini na biyu bayan sakinta. Kuma hakan ya nuna saura jini daya kenan ta tashi daga matar Badaru,  tunda munsan cewa iddah jini 3 ce.  Ba wata uku ba kamar yadda wasu ke fada,  sabida ba kowace mace ke jini duk wata ba.  Wata tanayin sati 3 wata kuma 25 dayz (kamar Mimi kenan). 



Haka al amura sukaci gaba da tafiya,  tasamu saukin rayuwa sosai saboda aikin da Baffa ya dora mata ya xamar mata jiki inbataiba batajin dadi.  Sai dai surutun mutane akan mutuwar aurenta har yanxu abun be sauki ba,  wannan kuma ta kance suyi su gama watan kwaram daya ne, na biyu sai gagara. Mutane kan bata mamaki,  inbakai aure ba a dameka inkayi balain gidan auren ya hanaka xama nanma asaka agaba. 


Duk magribar duniya fauxa kan shigo susha hira sai goman dare take tafiya.  Wanda hakan kan yiwa Mimi dadi,  kuma yakan debe mata kewa.  Dan ita Baffa ya hanata fita ko kofar gida.  A cewarsa kunya yakeji aganta ace yarsace kuma bazawara ce.  Dan haka suka qara shaquwa sosai da fauxa.  Duk wani abu da take buqata fauxa take bawa ta siyo mata. 



Sati hudu dayin qaramar sallah katin bikin Badaru yazo gidansu.  Kuma a lokacinne mate din Mimi suka fara registration din tafiya service domin an bude musu portal,  ta dunga kuka saboda Baffa ya hanata.  Sam bikin Badaru baya gabanta bata sansa balle tai kishinsa dan haka in mata 100 zai aura wlh baxata damu ba. 



Ranar asabar data kasance ranar yinin bikin Badaru matan gidansu Anty da Umma suka shirya suka tafi duk kuwa da cewa ba wani xumunci ke tsakaninsu da Umman su Badaru ba,  amma saboda a cuzgunawa Mimi suka tafi,  mama kuwa dama ba a gayyaceta ba. 



Ai kuwa suka dawo da lbrin irin gidan da Badaru ya qera domin sunje kai amarya,  da kuma irin bushashar da yayi a bikin.  Sukaita fadar magana wai ai yanxu yayi aurenso domin ya nunawa duniya yanason Nafee.



Ranar da aka kai masa Nafee a daren ya tumurmusheta, saboda yana yunwar abun. Amma ga mamakinsa a daren ya shigeta tsaf,  sabanin Mimi da sai da yayi kwana biyu dan ma tagomashin maganin kuzari.  Abun ya daure masa kai,  gadai Nafee danya shataf (mai qarancin shekaru) amma Mimi ta fita qaramar halitta.  Ashe abun ba shekaru bane.  Amma duk da haka ya yaba mata kwarai  tunda ya sameta cikakkiyar mace wacce ta kawo masa mutuncinta dan haka ta kuma samun gurbi sosai a zuciyar Badaru. 


Itama ta bangarenta tasha wuya sosai,  amma ta daure ne saboda soyayyar da takewa Badarun. 



Ranar da Mimi taga jini na uku (ranar cikar iddarta) har sadaka tayi saboda farin cikin sun rabu da Badaru har abada (abunda take fata). Mama kamar ta xuba ruwa a qasa tasha,  ta dunga sallar Nafila tana roqawa Mimi da duk wata ya mace samun miji nagari da ingantacciyar rayuwa. 



Daf ake da babbar sallah. Cikin wata guda da aurensu suka fara samun sabani da Badaru a dalilin yawan buqatarsa,  ita kuma tagaji da juriya.  Abunda kuwa ya faru shine: dake ance me hali baya fasa halinsa Badaru yaci gaba da bankar magungunan qara kuzari,  wanda ya qara yawan buqata akan tasa,  ita kuma Nafee taga sam bazata jura ba.  Duk kuwa da cewar Badaru baya ware mata qarfi kamar yadda yakewa Mimi.  Sabanin haka ita yakan yi romancing dinta ya lallabata kafin yakai gaci.  Kuma yanayin hakanne saboda soyayya da kuma duba qarancin shekarunta. 


A bangare guda kuma bata samun yacce takeso ta wajen cima, sabida ta gama sawa a ranta inta auri Badaru zaman jin dadi xatai saboda yana da kudi, ga kuma gida daya qera mata.  Shi kuma Badaru baisaba siyan komai a gidansa ba, amma duk da haka yasan xaman da yayi da Mimi babu macen da xata yadda da haka.  Dan haka yake sassauta wasu al amuran.  Yana siyan komai na cefanen gida dai dai gwargwado saboda har yanxu gushirin yana kan kaxa.  Sada nama da kayan shayi da bai taba saiwa Mimi ba yakan saiwa Nafee da sun qare,  sai dai kudi ne kwandala bata taba shiga tsakaninsu ba.  Wanda Nafee taga bazata lamunta ba.  



Abunda ya fara kawo musu sabani kuwa shine : tara qawayen da takeyi danta nuna musu itafa yanxu ta kere sa a ta auri mai kudi.  Wanda shi Badaru sam baya qaunar yaga anshiga gidansa,  kuma in sukaxo inyananan sai tace ya basu kudin mota inma bayanan saita ciwo bashi a maqota inya dawo ya biya.  Kuma duk wani nama da ya siya a gidan in qawayenta sukaxo sai sun cinyeshi.  A irin haka wata rana qawayenta sunxo dayar ta buqaci Nafee ta bata always ta canja,  Nafee da son gwaninta ta dakko ledar always ultra gaba daya ta bata.  Wacce dakyar Badaru ya siyo mata ita  domin cewa yayi bai taba siya ba,  kuma tai masa kudi da yawa harda cewa abar da za asa ayar har sai ansa 500 ansiya?  A taqaice dai sai da aka kai ruwa rana kafin ya siyo gashi Nafee ta bada ita lokaci daya. 



Yana dawowa kuwa ko sannu da xuwa batai masa ba ballantana ta bari yaci abinci tace "kaje ka siyomun always" ta fada cikin sigar rashin mutunci dan kar yace bazai siyo ba.  Ya kalleta a kaikaice yace "amma kyabari inci abinci ko"  ta qara tsuke fuska tace "ai babu abincin domin nayi baqi sun cinye kuma kafin na dora wani ka dawo"  ya jinjina kai cikin qosawa da halinta domin ba wannan ne karo na farko da tayi mai haka ba yace "ba shekaran jiya na siyo miki ba? Harta qare kenan?"  cike da isa tace "na bayar da ita daxu,  domin da kunya axo a ganni a wannan makeken gidan inkasa bada ledar always ai wlh kamata yayi ka dunga saimun sunqi guda saboda qawaye na"  yace "ok haka ya dace kiyi?  Kinyi dai dai"



Ala tilas yaje ya siyo mata always din,  domin da yaqi siyowa xama ta dunga yi ko ina tana batawa da jini daga qarshe ma da taga bai dauki abunda tayi da mahimmaci ba saita zauna akan cinyarsa ta batashi da Jinin (su Nafee yan iska🤣) dan haka ya yi saurin tashi yaje ya siyo tun kafin ta haram ta masa xama a gidan saboda qazantar jini,  domin shi Allah ya yi masa kyankyamin jini.  



Ranar alhamis suka tashi cikin tashin hankali, fada kacucur suke da Nafee yana fada tana mayar masa kamar ba sune masoyan da suka shafe shekaru suna soyayya ba.  Dalilin fadan kuwa shine: Nafee tace ya siyo mata kaza domin ta dade bataciba a fadarta rabonta dacin kaza tun ta daren amarci,  kuma wannan danqareren gidan kamata yayi ace Kullum da farfesun kaza ake breakfast 🤣. Shi kuma ya bata amsa da bazai siyo ba,  domin a gidansu ma ai ba kazar take ciba,  naman kasuwar ma da ta samu ta godewa Allah (abunki da wanda ya saba da fadar baqar magana) ai kuwa yana fadar haka Nafee ta taso masa kamar xata dakeshi tanayi masa warning din karya kuma sa gidansu acikin rashin mutuncinsa domin inya kuma xatayi babban rashin mutunci. 



Da haka ya tarkata ya fita saboda karya zauna zuciya ta xugashi ayi batacciya. A kasuwa tunani ya yini yi na mamakin halin Nafee. Shidai a iya zamansu baisan haka halinta yake ba ashe lambu lambu tai masa,  to kodai qawaye ke xugata?  Wata xuciyar tace ba wasu qawaye halintane hakan ta boye makane sai daka aureta.  Wannan shine ana zaton wuta a maqera ansameta a masaqa,  yana zaton a gurin ruqaqqun yan mata masu ilimi irinsu MARYAM ake samun fitsara da rashin kunya wa miji ashe abun ba haka yake ba,  sai gashi yar qaramar yarinya Nafee da ko secondry bata gama ba tanayi masa abunda bai taba tsammani ba.  Ada ya dauka xai juya Nafee yacce yakeso ya koya mata irin aqidunsa sai yaga labari yasha banban domin tun kafin aje ko ina Nafee na neman fin qarfinsa.  



Haka ya yini tunani a kasuwa, da dare ya dawo batai abinci ba. A cewarta wai ya bata mata rai saboda haka bazatai girki ba. Sai gurin me shayi yaje yaci indomie 😂.


Dake tsohon jarababbene,  a wajen kwanciya sai ya nemi haqqinsa.  Ai kuwa tace "kai ka isama?  Bakaban nama naci ba kazo ka mutstsukeni? Aikin banxa jarababbe kawai bakasan komai ba sai dare yayi ka danne mace" qiri qiri ta hanashi abunda yakeso kuma dole ya haqura. 



A daren ya gama yanke shawarar abunda zaiyi, domin ya gaji da rashin kunyar Nafee da iskancinta.  Kuma gashi ta fara hanashi haqqinsa shi kuma bashi da juriya a wannan fanni.  Dama kuma cikin yunwar abun yake domin sam baya samun gamsuwa da Nafee yacce yake samu da maryam,  ya saba da xagaye daya ya gamsu amma itakam Nafee sai yayi biyu xuwa uku yake samun biyan buqata lamarin da Nafeen taqi yarda dashi domin tace ita ba shinkafa bace dazaita sasuqarta. 



Dawo da MARYAM xaiyi domin ya fara gane kuskurensa na saurin rabuwa da ita.  Saboda haka xai dawo da ita ta zabe masa ruwan kashe shaawarsa a duk sanda ya buqata. Ita kuma Nafee yaci gaba da ajiyeta a matsayin matar so ya kuma ci gaba da haquri da halinta domin har yanxu yana sonta,  dan San tsakani da Allah ya ke mata itace dai ta rufeshi.  Dan haka ko gida daya bazai hadata da Nafee ba kartaga irin abunda Nafee take masa itama tace xatayi,  wani gidan zai kama mata haya anan kusa da Nafee.  



Yana kaiwa nan a tunaninsa wani farin ciki ya shigeshi, 😄 harya fara hangosu shi da MARYAM cikin yanayin auratayya.  Yasan xuwa yanxu ta nemi maganin ciwonta na sanyi, sannan kuma gata da qaramin ciki yasan xai shana kwarai dan MARYAM yar baiwa ce ko babu ciki bare da ciki. Sai yanxu yaji yana son cikin jikinta kuma yanason ganinta da cikin yasan cikin zaiyi mutuqar kyau ajikinta dan komai nata me kyau ne (Dan rainin sense 😏) da wannan tunani bacci ya daukeshi cike da mafarkin MARYAM wanda ya kaishi ga wanka.



Ganin kansa a jiqe yasa Nafee fallara masa harara, tace ina ruwan dan anace mafarki kai kenan?  Bai kulata ba saboda  bayason ta bata masa mood,  dan daga masallacin asuba gidansu zai tafi gurin Abbansa suje bikon MARYAM. 



Mrs 😊
[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 3⃣2⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Bakwai saura kwata (6:45 AM) a gidansu tai masa. Yasha shadda fara sol yar ciki da babbar riga, ya dankwafa hula kamar kansilan qauye.  🤣



Har cikin dakin Abbansu ya shiga, ya samu Umma tana hadawa Abban shayi. Ya tsuguna har qasa ya gaishesu, Abba ya gama shirinsa tsaf da alama fita xaiyi.  



Badaru ya qara sunkuyar dakai cikin sigar neman alfarma yace "Abba dama nazone dan Allah muje mu dawo da MARYAM,  Na janye sakin da nayi mata. Naga gara ta dawo mucigaba da xama ta haihu a dakinta, na huce da fushin da nake da ita."  Umma ta ware ido tace 😳 au dama MARYAM din ciki gareta amma ka saketa?  Kuma shine baka taba fada ba?  Wannan yaro ka jawo mana abun kunya wlh,  ai da munsan da ciki da mun dunga xuwa dubata."  yayi dan murmushin alamun samun nasara yace "Umma kuyi haquri lokacin rainane a bace shiyasa ban fada muku ba."  tace " eh ai yayi kyau hakan,  yaro yarone, yaro bakasan wuta ba saika taka.  Yanxu kuma da xaka dawo da ita ka manta da xagin naka da kace tanayi? Ka sheqa kaji babu kwaya kenan.Hmmm to wlh bakayi  
daya ba kaji dadi duk randa ka kuma sakin wata mace bama MARYAM ba daga ranar ka canja uwa domin ni bazan xama uwar mai auri saki ba"



Abba yayi gyaran murya yace "tunda dai yayi kuskure kuma ya gane kuskurensa shikenan,  kuma itama MARYAM din nasan yanxu tayi nadamar abubuwan da tayi masa. Yanxu xanje Dawaki daurin aure amma in shaa Allahu bazan kai sallar juma a acan ba.  Yanxu xanje insamu kawunka in fada masa,  inyaso ina dawowa daga masallaci sai mu wuce dashi muje gidansu MARYAM din."



Badaru ya dunga murmushin farin ciki, sai yakeji a ransa kamar ta dawo ta gama.  Dan haka yace "Abba inaga gobe kawai su dawo da ita,  yanxu xanje inga inda xata zauna acan gurin Nafee kafin in samar mata gida" Abban yace to hakan yayi, bari intashi kar inyi rana. 



Bayan komawarsa gida,  yana kashingide yana tunanin maryam har wani lumshe ido yake inya tuno sweet moment dinsu. Ya gama tsara cewa dakinsa da yake ciki zai bawa maryam din kafin ya samu gida ya sai mata, bazai qara sakinta ba zai zauna da ita saboda buqatarsa.  



Yana cikin tunanin ne Nafee tazo ta dangwarar masa da baqin shayi (lipton) da breadi.  Tace gashinan babu madarar.Bai ce mata komai ba, sai dariya da yake mata a xuciyarsa. Tanai masa kallon biri yana mata kallon ayaba,  domin bazai fada mata xai dawo da maryam ba sai dai taganta.  Ya qudure suna dawowa daga gidansu Maryam din zaije yayo mata shoping na komai da komai ita kadai, Nafee kuwa taji a salansa, dan yagaji da barnar da Nafee keyi masa. 



Kamar yadda Abban Badaru ya alqawaranta tare sukayi sallah da Baffa a masallacin jumaar gidan sarki,  kuma daganan yabi Baffa gida yace suje zasuyi magana me hamimmanci. Baffa dajin haka yasan maganar Komece farinciki ya cika zuciyarsa. Abba tare da qaninsa da Baffa sukaci abinci tare a gidan Baffa.  Kuma dama ga al adar Baffa ranar juma a daga sallar juma a gida yake tahowa baya komawa kasuwa. 



Suna gama cin abinci suka labartawa Baffa maqasudin xuwansu da kuma saqon Badaru na amaida maryam din gobe (kunji fa kamar wata yarsa) harda labarin cikin Mimi sai da suka fadawa Baffa. Babu wani nuna ja ko tauna tsakuwa dan aya taji tsoro ko kuma tsawatarwa dan kar Badaru ya kuma yin saki anan gaba Baffa ya yadda da komen maryam gidansa (dan Allah ku duba inda ake wulaqanta ya mace. Ba dole namiji yayiwa mace wulaqanci ba dan yasan inma ya saketa bazai sha estalar dawo da ita ba) suka sha hirarsu cikin nishadi ya basu tabbacin gobe ana magriba A dar uma yaxo ya dau maryam su tafi. 



Suna tafiya Baffa ya shiga gida,  a lokacin qarfe uku na yamma.  Tunda tsakar gida ya dunga kwallawa mama da Mimi kira,  har ya bude parlourn Sá ya shiga bai fasa kiransu ba.  Mama ta fito ta bishi dakinsa, yace jeki ki rawomun maryam yana fara a. Taje ta taso Mimi take bacci,  Umma da Anty jin kiran da Baffa kewa Mimi yasa suka fito suka shiga dakin Baffa kamar an gayyacesu. Dan Susan tunda ya kira Mimi watace ta taso dan inba haka ba sai yayi sati bai kirata ba.  Ya jafar ma yanxu ya shigo gidan xuwansa kenan daga kaduna yazo weekend kuma yana xuwane saboda Mimi, jin kiran da Baffa yake mata yasa ya tsaya daga gefen kitchen kusa da dakin Baffa dan yaji dalilin kiran, babu wanda ya lura da xuwansa. 



Baffa ya kallesu,  Umma, mama, Anty sai kuma Mimi dake gefe daya.  Ya fadada faraarsa tare da cewa "ALHAMDULILLAHI,  Allah ya sani tunda abunnan ya faru nake adduar Allah ya sa a daidaita, to Allah maji roqon bawa yanxu Alh Inuwa da qaninsa suka xomun da xancen mayar da auren maryam da Badaru.  Domin shi Badarun da kansa yau yace ya janye sakin ta koma dakinta. Dan haka maryam sai ki hada kayanki gobe zaizo da almuru ya daukeki, basai nace miki komai ba in aurenki ya kuma mutuwa karki dawomun gida"



Mimi ta kwalolo 👀, jin abunda Baffa yace wai Badaru ya maida ita.  Ta juya ta kalli da nufin mama tayi magana, domin ita bazata iya cewa da Baffa ta gama iddah ba.



Ai kuwa mama ta magantu "Alh wani irin kome kuma?  Ai aure ya qare, tunda yau kwanan Mimi 6 da gama iddar Badaru." 



Baffa ya dakawa mama tsawa tare da cewa "Faduma karki kawomun zancen banxa mana,  yarinya da akace tana da ciki itace xakice ta gama idda?"


Mama ta hade rai cikin shirin ko ta kwana😡. Umma tai saurin sa musu baki a maganar da cewa "a ciki kuwa akwaishi dan ko mu munsan dashi, sai dai in Faty ce ta jagoranci " maganar ta katse a dalilin hararar da mama ta watsa mata.  Abun ya bata mamaki domin ko da wasa mama bata taba harararta ba,  dan haka yau da taga fadiman na shirin canjawa taja bakinta ta tsuke saboda kar girmanta ya xube. 



Baffa shima ganin mama tayi fuskar shanu tana hararar Umma yasa ya bar maganar ciki. Yace "to shikenan ai duk da haka akwai mafita bara in kirawo Alh inuwan suxo da daddare a daura aure ya wuce da matarsa"



Mimi da mama suka kalli juna a razane. Mimi ta dago kanta cikin dakiya tace "Baffa karka kirawoshi,  nikam nagama auren Badaru in shaa Allah,  Allah ya hada kowa da rabonsa na alkhairi"



Baffa ya taso mata cikin hargowa yace "ke ki kiyayeni kuma aure dole ki koma,  kina zaton akwai wanda zai aureki inyaji abunda kika shukawa tsohon mijinki ya sakeki a wata 5? Kinsa ana zagina a gari kamar ni ace inada bazawara a gidana? Kin batamun record din gida.  Saboda haka dole ki koma gidansa ayau basai gobe ba"



Ba tare da wani shayi ba ko shakka, domin xuciyarta ta gama bushewa.  Ta dago kanta tace "Baffa bazan koma ba wlh,  saboda ni kadai nasan irin wahalar da nasha a gidansa"



Baffa ya dauketa da wasu irin maruka guda 2, tare da cewa "ni xance kiyi abu maryam kice baxakiyi ba? Lallai na yadda Badaru yayi haqurin zama dake.  Kuma wlh sai an mayar da aurenki ayau, inyaso ni dake aga wanda ya haifi wani"  



Idonta jajur saboda zafin marin da Baffa yayi mata, ta kuma dagowa ta kalleshi tace "wallhil azeem bazan koma gidan Badaru ba,  da inkoma aurensa gara inshiga duniya." 


Umma da Anty dake gefe suna kallo tun abun na burgesu har ya koma basu tsoro, suka kwalalo ido dan yau Mimi ta shayar dasu mamaki. 


Baffa kuwa baiyi wata wata ba ya tashi yasa hannu ya rufe mimin da duka kota ina. Nan take kuwa jini ya fara fita ta hancinta wato habo. Mama ganin jini na xuba a hancin Mimi ta runtse ido,  xuciyarta na tafasa tana kai kawo.  Mimi kuwa duk dukan da Baffa ke mata bata fasa fadar "wlh ko kasheni xa ai bazan koma gidansa ba" Baffa yaje ya ciro wayar receiver ya nufi Mimi da niyyar sake dukanta dan yagaji da dukanta da hannu, yana cewa "to ayau kuwa xaki barmun gidana bayan na gama fasa miki duk jikinki da duka dan ban haifi dan da zai fada in fada ba"


Mama tai saurin tashi tasha gabansa (ta shiga tsakaninsa da Mimi) tare da cewa Alh Buhari karka qara dukarmun ya, domin baka tayani naqudar kawota duniya ba.  Haka kawai kasa marainiyar Allah a gaba sai jibga kakeyi kamar kana dukan namiji dan uwanka. Ai ko musulunci bai baka dama kai mata auren dole ba a matsayinta na bazawara"



Umma da Anty dake gefe abun ya basu mamaki kwarai,  Anty ta kasa haquri ta miqe tare da cewa "amma kam kedai fadima baki da kunya baki da kara, yanxu sunan mijin naki kike ambata tare da yi masa tsawar ya daina dukar miki ya? Ai ab" kafin ta qarasa abunda tai niyyar fada mama ta dauketa da mari, tare da nunata "👉🏼 ke! Na kasa dake balle ki dauka?  Da wanda ya ajiyeki nakeyi" Anty da tasha mari ta dafe kunci tana kallon mama cikin kidima, Umma kuwa nan take ta kuma shiga taitaiyinta. 


Mama ta maida kallonta ga Baffa da ke tsaye nayi mata kallon mamakin abunda takeyi taci gaba da cewa "ni har a fadamun kara akan yayana?  Nagaji nagaji da abunda kake jagorantar matanka kukemun haqurina ya qare.  Kuma yau na tabbatar da AL AMIN baya duniya, domin da yana raye da ko cikin shege maryam tayi zai karba ya rufa mata asiri.  Duk cikin yayanka wa kayiwa auren dole?  Sai yata, saboda qasa ta rufe idanun ubanta ko?  Nagaji da abunda kakemun nagaji da wariya akan yayana,  ai koda ace ba yayan dan  uwanka bane kayimun kara.  A karatu ka fifita yayanka akan nawa,  a wajen tarbiya da nuna soyayya ka fifita naka akan nawa,  a wajen aurar da yayama salon auren yayanka daban da nawa,  sannan ka debi yayanka ka dunga kaisu saudia kabar nawa, to shin ubansu bashi da gado a dukiyar da kake facaka da itane ko kuma sudin shegu ne?  Duk abubuwan da kakeyi ina sane kuma ina ganewa domin ni ba mahaukaciya bace kamar yadda kuke xata.  Sannan akan wani banxa Badaru ka mayarmun da ya baiwa me aikin gidanka,  sannan kuma yanxu kana nema kasa yata ta shiga duniya saboda Badaru? Shin wai maryam yar dan uwanka ko Badaru?  To tunda kana qaunar Badaru ka dauki daya daga cikin yayanka ka aura masa. Tunda anyi ruwa qofar dakin kowa ta jiqe (ma ana kowa yana da yaya) duk cikin yayanka wacece take maka biyayyar da Mimi take maka? Amma duk da haka kafi tsanarta kafi wulaqantata bansan abunda ta tsare maka da kai da yayanka da matanka ba kun tsangwamarmun ya kun takurata, to wlh duk wanda ya qaramun abunda bai gamsheni ba akan yayana sai yaga tashin hankali. Ko kasan cewa akan takurar da kaiwa Mimi har yunqurin kashe kanta tayi? To wlh Buhari duk randa maryam ta kashe kanta saboda takurar da kake mata wlh sai nayi sharia da kai daga nan har kotun duniya. Kamar yadda kasha fada kuma kake nunawa a aikace cewa Mimi ba yarka bace to yau na tabbatar maka cewa FATIMARYAM ba yayanka bane yayan AL AMIN da FADIMA ne.  Saboda haka na yanta yayana daga barin yi maka bauta. Abu na qarshe dazan fada maka shine : kamar yadda kace Mimi tabar gidanka xata bari,  amma ni da ita xamu barmaka gidan tare domin saboda su nake zaune a gidannan inkuma ankore su banga xaman da xanyi ba." 


Ta juya ta kama hannun Mimi tare da cewa "taho maryamu daga yau na yanta ki" Baffa yayi sakato kamar an dasashi jikinsa yayi mugun sanyi  wata irin kunya wacce bai taba zato akwaita ba yakeji. Ashe duk abunda yakewa fadima tana sane? Lallai ya dade yana zaluntar wannan baiwar Allah da yayanta, yau ta fada masa abunda bai taba tunani ba kuma shi kansa baisan hujjarsa ta nuna banbanci tsakanin yayansa da yayan dan uwansa Al amin ba.  Lallai mai haquri bai iya fushi ba yau fadima ta zame musu horo, yasan tabbas abunda ta fada gaskiyace tsantsan duk yayansa babu mai masa biyayyar da Mimi keyi masa kuma babu wacce yayiwa auren wulaqanci irinta. Kuma wlh baisan abunda yasa yakewa Mimi haka ba, kuma yasan da Anty ko Umma yakewa yayansu abunda yakewa Mimi wlh da sai anyi yaqin duniya na uku. Muryarsa a tausashe yace da mama dake shirin fita daga parlourn "ban baki izinin fita daga gidannan ba daga ke har maryam" Umma da Anty suka kalleshi jin abunda yace suka jinjina kai.  Domin sun dauka zai saki fadima ne nan take, da daya daga cikinsu ce da tuni ya sender ta gida.



Mama na fitowa daga dakin Baffa ta tsugunar da Mimi a bakin fanfo da nufin wanke mata jinin daya bata jikinta.  Jafar da ya gamajin abunda ke wakana yayi saurin xuwa kitchen ya dakko mata ruwa a freezer ya miqa mata, ta karba ta wankewa Mimi fuska dashi.  Nan take habon ya tsaya, taja hannun Mimi suka shige dakinta. 


Jafar ya furta "jarumar uwa" ta jure abubuwa da yawa akan yayanta sannan lokaci daya ta kwatarwa Mimi yancinta.  Ya dunga farin cikin jin Mimi ta gama iddah yace "in shaa Allah maryam matata ce"



Har magruba tayi mama bata fito ta dora girkin dare ba duk kuwa da cewa ita ke da girkin. Anty ta samu Baffa har daki yayi tagumi tanayi masa mitar cewa,  mama bata dora girki ba mai zasu bawa yara suci?  Ya dago ya kalleta yace "ku masu yaya bakuje kun girka kun basu ba sai ita me ya guda daya? Saboda haka karku dameni" Anty ta ruqe haba cikin ranta na jinjina soyayyar fadima a gurin Baffa,  wato duk abunda tayi batai laifi ba kenan? Har marin da tayi mata 🤣. Ala tilas taje ta dora jellof din taliya dan lokaci ya qure kuma itace me qananan yaya. 


Bayan ta gama ta hana kowa sai Baffa kawai ta xubawa ta kaima masa daki,  shi kuma ya tambayeta da cewa kin kaiwa fadima? Ta harzuqa tace "aini bata shanye ni ba kamar yadda ta shanyeka ba, saboda haka ban kai mata ba dan ba xamanta nake ba.  Ana cikin hakan Umma ta shigo tana tambayar Anty ina nata abincin?  Tace nima dafawa nayi ni da yayana kema kije ki dafa dan ba baiwarku bace ni.  Umma tace dakata karkiyimun fitsara inba haka ba yanxu in wanka miki mari dan naga sai anmareki kike samun nutsuwa 😂. Anty da jin haka ta harzuqo suka fara cacar baki ita da Umma.  Baffa ya katsesu da cewa ko suyi shiru su bashi guri ko kuma kowacce ta tafi gidansu.  Anty ta cije lebe da cewa ai dole kace mu tafi gida,  ita wacce  ta qare maka zagi daxu ai ta kwana lfy saboda ta iya bun malamai. 


Daya fita sallar isha ya biya ya siyowa mama da Mimi qatuwar kaza da fura roba biyu, jin cewa ba a basu abinci ba. (lallai mama ta motsa kwanji 😄) ya shigo Anty na alwala a tsakar gida kuma taga ledar daya shiga da ita dakin mama.  Har ta miqe xata bishi sai ta tuna marin da tasha daxu dan haka ta koma ta xauna.


Yasameta xauna akan kujera ita da Dady suna kallon mbc 3 Mimi kuma tana kujera zaman mutum daya da digital casbaha a hannunta tana dannawa.  Baice musu komaiba sai ajiye ledar da yayi kan qafar mama ya fita.  


Dimin da taji shiya tabbatar mata abinci ya kawo musu,  kuma dama shiri take ta tashi ta samar musu abunda xasuci.  Dan yau jin ranta take sawai,  abunda yake ranta shekara da shekaru yau ta amayar dashi.  Dan haka ta dakko musu faranti da cups sukaci kazar suka sha fura suka qulle dakinsu suka kwanta,  daga ita har Mimi basu garka ba sai asuba sun sami bacci me nauyi. (dole tunda anraba xuciya da damuwa)


Mrs
[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 3⃣3⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Baffa kwana yayi yana tunani,  haqiqa yayi kuskure yayiwa fadima abubuwa da yawa kuma babu wanda ya taba fada masa yayi ba daidaiba.  Tabbas yaci amanar Al amin,  yayansa kwaya biyu yakasa hadawa cikin nasa yayan ya rike.  Kuma dole su Faty sunada gado a dukiyarsa domin tunda Al amin ya mutu ya tattara abunda yabari ya riqe,  ko mama bai sallama ya bata tumunin takaba.  Su bai basu dukiyarsu sun mora ba su baiyi masa da tasa ba.  Dole zaisan abunyi akan dukiyarsu,  ko bebawa su Faty tasu ba dole zai sallami mama da tumuninta.



Ta bangaren Mimi kuwa,  baisan dalilin tsanar da yayi mata ba.  Amma yasan akwai tagomashin matansa wadanda Kullum cikin kawo masa sukar Mimi suke.  In yayi kallo xuwa hallayyar yarinya sai yaga yarinyace sassanya wacce ko acikin gida ake hira da wahala kaji harshenta, sai dai in anyi abun dariya tayi.  Gata da kirki da qarfin xuciya,  duk da bata cika lfy ba Kullum xaka sameta cikin aiki ko a tsakar gida ko a dakin uwarta.  Bata da qashin cewar bazatai aiki ba saboda akwai yan aiki a gidan kamar yacce yayansa keyi.  In kuma yanason ai masa abu misalin gyaran daki ko wani aiki to Mimi yake sakawa domin tana tsayawa ta yishi babu hainci wanda ko matansa basu iya yimasa shi tsaf kamar nata.  


Dan haka ya fuskanci xuga ce jigon tsanar da yakewa Mimi,  sai kuma issue din rashin aurenta da wuri wanda ya dauki hakan iya shege.  Dole ya kawo canji domin yanason fadima kuma bazai iya rabuwa da itaba,  yanxu gashi tana shirin rabuwa dashi saboda Mimi. Nan take yaji rabin tsanar da yakewa Mimi ta tafi. Afili ya furta Fadima nagode da kika karantar dani kuskurena da wuri tunkan in mutu Allah ya kamani da haqqin xumunta dana marayu.  Kuma daga yau xan sakarwa yarki mara tayi irin rayuwar da take so. 


Lokacin da yafito domin tafiya masallacin asuba ya kirawo masu aikin gidan  yace su karbi aikinsu yau sannan ya fita. 


Mimi kuwa bayan ta iddar da sallar asuba ta gaida mama,  mama tace mata kije kiyi registration din tafiya service din yau.  Mimi tayi rau rau tace " mama ai anrufe sun kusama tafiya camp domin har call up dinsu ta fito" mama tace to kiyi haquri haka Allah ya shirya kaje wata shekarar"
Anan kitchen din cikin parlour suka hada break fast sukaci,  domin mama ta quduri aniyar kwatar yanci. Tunda ya hanata tafiya ai sai tayi yajin a dakinta.


Badaru yadda suka kwana da Nafee jiya yauma haka suka kwana,  domin shima ya bar mata abunta yace ta jiqa tasha.  Aransa kuwa cewa yake ni da xan kwana da maryam yau dan anhanani wannan ruwan daurayar ai ba wani abu bane.  



Wajen qarfe goman safe yaje gidansu,  dake asabar ce kuma basa fita kasuwa weekend da wuri duk ya samesu a parlour.  Har Badamasi da yazo weekend. 


Ya zauna ya kwashi gaisuwa gurin iyayensa,  ya juya suka gaisa da Badamasi sama sama domin Badamasin yanxu yake samun lbrin saki da kuma maida maryam da Badaru yayi sannan da zancen auran da yayi.  Dan haka yaji yayi mugun tsanar Badaru sabida maryam. 


Badaru ya kalli Abbansu yace "Abba inaga da yamma xanje in dauko maryam din,  saboda inason inkaita store tayi shoping din kayan abincinta da kanta inyaso sai mu wuce gida daga can" 


Abban yace to babu laifi,  bari na fadawa Alh Buharin saboda karkaje bata kimtsa ba" Umma dake gefe tana murmushi aranta taji dadi ga dukkan alamu Badaru ya gane mahimmancin maryam, dan haka tace "Alh ai da ya kira maryam din da kansa yace ta shirya da wuri zaizo da yamma" 


Badaru ya sunkuyar da kai cikin kunyar abunda xai fada yace "ai bani da lambarta" babu wanda yace masa komai sai Badamasi dake watsa masa harara kamar ya tashi ya dakeshi. 


Abba ya ciro wayarsa yace bari na fada masa da kaina. Lokacin da kiran Abba ya shigo Baffa na xaune yana karyawa Umma na gefensa ga dukkan alamu itace tayi girkin tunda mama tayi bore. 


Ya daga suka gaisa,  har yanxu jikin Baffa a sanyaye yake.  Abba ya fada masa buqatar Badaru.  Baffa yace "ai Alh inaga sai dai mu haqura domin yarinyar har ta gama iddah, kaga babu maganar kome kenan?"


Abba dajin abunda Baffa ke fada yasa wayar a hands free domin Badaru yaji abunda Baffa yace.  Abba ya maimaita abunda Baffa yace "ta gama idda?" Baffa yace "eh"


Badaru ya dafe qirji yace "to cikin jikinta fa?  Xubarwa tai?" Baffa da yaji abunda Badaru yace saboda hands free din da aka saka yace "ita dai tace babu ciki kuma iddarta ta cuka tun kwana 6 baya" 


Abba yayi saurin cewa "to ai abun bai baci ba har yanxu,  tunda yayi nufin maidata sai mu kawo sadaki in anjima a maida auren" Badaru yayi saurin gyada kai cikin gamsuwa da abunda Abba yace"


Sai dai muryar Baffa ta katse masa hanxari inda yake cewa "Alh sai dai muyi haquri inaga iyakacin xaman da Allah ya rubuta musu kenan, domin nima na kawo batun maida auren maryam ta nuna bata da raayin kuma xama dashi dana takura sai anmaida auren adalilin hakan nima xaman lfyar gidana ya tabu,  domin uwarta tace baza a kuma yiwa yarta auren dole ba har tana barazanar dauke yarta su barmun gidana.  Ni kuma inason matata kaga garin gyara kuskuren Badaru aurena zai mutu,  gara kawai a haqura." 



Abba ya kashe wayar cike da jin haushin Baffa, yana mitar kamar Buhari ya zauna mace na juya shi?  To kada Allah ya sa maryam din ta dawo,  metafi Badarun ai Badaru ba illah ce dashi ba babu inda xaije neman aure ba a bashi ba (kuji san kai?)  


Badaru tunda ya gama jin abunda Baffa ya fada gabansa ya yake ya fadi,  qirjinsa ya dunga bugawa sai yanxu ya tabbatar ya tafka kuskure.  Tabbas yasan maryam bata sansa,  wlh da yasan haka xata kasance da bai saketa ba.  Ta xubar masa da cikin da yake ganin shine tsanin da xai dunga hadasu. Umma kuwa hawaye takeyi jin maryam ta bar xuriar ta, tasan Badaru yayi rashi.  


Badamasi kuwa dake gefe fuskarsa a washe sai murmushi yake.  Ya dunga godewa Allah a xuciyarsa,  yace lokacin aurena yayi, maryam ta dawo.  Jin fadan abba yaqi qarewa kuma Abban baya blaming kowa sai Mimi,  shiyasa ya matsa gaban Abban,  baice komai ba sai wayarsa da ya ciro ya kunna recording din da ya tabayi wanda Badaru ke tsagin Mimi da korarta daga gidansa.  Yace Abba ku saurari wannan"



Sukayi tsit har Badaru suna sauraran recording din harya qare sannan Badamasi ya dora musu da sauran abunda yagani na zamantakewar auren da kai Mimi asibiti da yayi da kuma abunda yakeji lbr gurin abokan Badaru. 



Jikinsu yayi mugun sanyi, Umma kuwa kuka take tana kallon Badaru a razane.  Ta kalli Abba cikin kuka tace "Alh kaji abunda nake fada maka ko? Kake goyon bayansa,  wlh nasan sharri yayiwa yarinyar nan,  ai dole tace baxata xauna dashi ba saboda ya azabtar da ita,  inma cikin ne ai baqin cikinka ma ya isa ya xubar da cikin.  Kuma wlh indai nadama ce baka fara ba,  ka cuceni ina qaunar yarinyar nan ka rabani da ita"  ta qara fashewa da kuka.  Abba ma ya kalleshi yace "baka cuci maryam ba,  ba kuma ka cuceni ba kanka ka cuta.  Na yarda da kai kasa ina jin haushin yar mutane ashe kaine babban dan iska,  sabida haka kajira sakamako wlh sai Allah ya saka mata"



Badamasi ya matsa kusa da qafar Umma ya riqo hannunta yace "Umma share wahayenki,  baki rabu da maryam ba,  maryam xata dawo cikin xuriar ki kuma a matsayin surukarki,  domin xan auro maryam.  Idon kowa a gurin ya dawo kansa.  Yaci gaba da cewa tun farko ni naga maryam, ni na fara sonta,  ni nafara yi mata magana.  Ina shirin inje innemi soyayyarta Badaru yazowa Abba da maganar aurenta ganin haka yasa na haqura,  amma wlh da nasan Badaru haka zai maltreating maryam wlh bazan haqura in bar masa ba.  Saboda haka Umma ban taba neman abu a wajenku ba yanxu nazo da alfarmar neman goyon bayanku akan neman auren maryam,  ba haram bane dan Allah ku kauda kai a magoar mutane ku goyamun baya." 


Umma ta share wahayen farin ciki,  ta shafa fuskar Badamasi tace "na baka goyon baya 100%, nasan bazaka wulaqanta maryam yanda Badaru yayiba Allah ya sa rabonka ce"  ya juya gurin Abba yace "Abbana inkace in haqura xan haqura"  Abba ya kalli Badamasi a nutse yace " na baka goyon baya likita,  indai har kun daidaita kanku da kaina xanje gurin Alh Buhari a karo na biyu in nai mar maka aurenta" ya dunga godia yana dariya ji yake indai Mimi ta amince nan da 2 wks xa ayi komai a gama.  Yau yana da daurin auren abokinsa a Danbatta amma gobe in shaa Allah zaije su gana. 



Badaru da tunda Badamasi ya fara magana yake kallonshi har ya gama,  ya tashi idanunsa jajur da tsabar kishi ya tari gaban Badamasi cikin sigar rigima yace "oh dama ashe san maryam kake?  Shiyasa ka hure mata kunne ta ciremun ciki ta gujemun sannan ka nado sirrinmu ka kawo ko?  To wlh baka isa ka auri maryam ba indai ina numfashi,  kai ko kunya bakaji ka auri tsohuwar matata? Ban taba neman abu na rasa ba, na auri maryam da farko kuma yanxu ma xan kuma aurenta domin wlh saina kasa ka,  ka rubuta ka ajiye,  inkuma ban aureta wlh sai dai ayi biyu babu kowa ya rasa."


Badamasi yaja da baya ya kalleshi yana dariya yace "ka saba yiwa kanka kirarin duk abunda ka nema kana samu,  amma inkasamu baka iya alkinta abun,  kaga kodan haka Allah xai iya jarrabarka,  saboda haka maryam dai yanxu rabonace in shaa Allah gara kaje ka lallaba kucakar matarka ku zauna lfy.  Kuma ni bazan fada da kai ba domin yau cikin farin ciki nake dan haka kaje ka nemi irinka looser  kuyi " 


Badaru yakai masa duka Badamasi ya tare tare da cewa kasan in dambe xamuyi wlh karyaka xanyi ka wani tara teba sai kace me ciki.  Abba ya daka musu tsawa tare da ja musu warning.  Kowanne ya fita yana hararar dan uwansa.  Umma tace "Alh baraka fa xata bullo idan bamu tashi tsaye ba"


Abba yayi shirin fita kasuwa ya leqa dakin Badamasi yace "Bani wayarka ka saitamun gurin maganar nan, gara insami Alh Buhari in wanke yarinyarnan a gurinsa." Badamasi ya bashi wayar tare da bude masa recording din,  yana xuwa play kawai xai danna. 



Baffa naganin Alh Inuwa a shagonsa ya hade fuska,  don a xatonsa xuwa yayi ya qara neman alfarmar mayar da Mimi.  Amma sabanin haka sai yaji yana bashi haquri tare da neman itama Mimi abata haqurin, kana ya budewa Baffa recording din ya saurara.  


Baffa yayi matuqar tsorata da lamarin Badaru,  ya kalli Alh inuwa yace " kace dan iska ka kawomun cikin manyan kaya ni kuma banyi bincike ba na dauki salihar mace na bashi" Alh inuwa yace "wlh Alh bansan abunda Badaru ya aikata ba kenan, shiyasa na kawo maka abunda yayi kaji.  Amma dan Allah kayi haquri  kuma ka bawa maryama haquri babu hannuna a abunda aka aikata mata kuma wlh da nasan haka zaiyi da ban nema mishi auranta ba"  Baffa yace " shikenan nagode da sanar dani da kayi shi kuma ya je dan kansa ya cuci marainiyar Allah"


Baffa yayi sakato yana tunani,  lallai ya tafka kuskure a baya.  Ya dauki ya yabawa dan iska yana zaginta da goranta mata,  amma kuma duk abunda Badaru yayi bashi da laifi, shine babban mai lefi da bai riqe su da daraja ba kuma ya nuna maryam din ba wata bace.  


Tausayin Mimi da soyayyarta ta dirar masa nan take,  dole Mimi tace bazata koma gidan Badaru ba saboda ya zalunceta sannan ya biyota da sharri shi kuma ba bincike yahau ya xauna.  Jin soyayyar Mimi yake har cikin bargonsa kuma yaji yana kunyar hada ido da ita da uwarta. 



Badaru na zuwa gida ya samu Nafee a parlour tana kallo, ya kalli parlour komai kaca kaca ya kalleta da yake a kusa yake neman masifa yake sai yace "ke haka ya dace kibar guri ki xauna kina kallo dake ke jaka ce?"


 Ta kalleshi sheqeqe tayi dariya tace " jakai dai,  ni da kai in ban gyara ba kai baka da hannun gyarawa?"  kafin ta ida fada ya kifa mata mari.  



Batai wata wata ba ta dakko plate din da ta gama cin indomie yanxu ta jefa masa tana huci, sannan ta dora da cewa "ga dukkan alamu ka saba ganin tsohonka na jibgar gyatumarka shine kazo xaga gwada a kaina,  to wlh duk randa ka qara dukana wlh saina sake maka kaciya 😳"



Ya tsorata da mutuqa da maganar Nafee,  bece uffan ba ya shige bedroom dinsa,  ya rasa abunda yake masa dadi.  Shi yanxu yasan duk wanda ya fadawa abunda Nafee ke masa dariya zaiyi saboda yacce ya daukaki Nafee.  Ya dunga juyi akan gado ya kasa bacci,  har akai sallar laasar bai fito ba ga yunwa na addabarsa kuma yasan Nafee yau bazata bashi abinci ba.  Ya tashi yayi wanka yayi sallah,  ya zabo kayansa na qure adaka yasa.  Gurin maryam xaije ya bata haquri ya nemi yafiyarta,  yasanta da sauqin kai xata haqura su koma aurensu. 


Ya samu Nafee zaune ta cokala dauri ture kaga tsiya tana sanaar (kallo), ya tsaya domin yayi mata magana,  ta dauki remote ta qure volume alama batason jin abunda xaice, dan haka ya fice. 



Ya dade a qofar gidan Baffa babu dan aike kuma bashi da no Mimi. Mimi ta fito domin zuwa gurin fauxa,  tana sawo kai waje idonta cikin na Badaru gabanta ya yanke ya fadi ta diririce,  ta juya da nufin komawa gida yayi wuf ya damqe hannunta yajata cikin sit room din dake soron farko. 



Cikani, baka da hankaline xaka riqe mani hannu? "ta fada cikin fita hayyaci.  Ya sassauta riqon da yayi mata, amma still yana riqe da ita karta gudu ya fara magana murya a kwance " maryam dan Allah kiyi haquri nasan na bata miki naci zarafinki na hadaki da iyayenki na tauye haqqinki na kuma toxarta ki. Amma wlh nagane kuskurena abaya na aureki ne dan shaawa amma xaman da mukai da ke nagane kyawawan halayenki da son addininki hakan ya jawo miki soyayya a gurina." Mimi tayi sakato tana kallonsa wai dama Badaru ya iya magana a hankali?  Kuma dama yasan duk abunda yake ba dai dai yake ba? Tambayar da takewa kanta kenan. 


A bangare guda kuma Baffa dake azumi (azumin kaffarar rantsuwar da yayi ta Mimi saita koma gidan Badaru, ya fara yau) ya dawo gida da wuri domin ya kawo salad din da yakeso a kwada masa yayi buda baki dashi.  Yana xuwa soro aci burki dan jin maganganun dake fitowa daga sitroom.  Da farko bai gane mai maganar ba,  amma jin an ambaci sunan maryam ya gane me maganar da inda maganar ta dosa.  A fili yace lallai wannan yaron bashi da kunya bari inje inyi masa tsakani da yata. 



Sai dai muryar Badaru ta katse masa hanxari inda yaci gaba da cewa "maryam ki tunano rayuwar auratayyarmu me dadi 🙈, ke bakya tunawa? Wlh kullum cikin kewarki nake da mafarkinki,  ki dawo muje mu zauna duk abunda kikeso zan miki   duk yan uwanki na gidan miji ke kadaice kika rage,  kin wuce xaman gida ki dawo dakinki shine rufin asirinki"




Ta katseshi da cewa "xaman gidanmu yafiyemun zaman gidanka,  kuma lokacin da sakeni ka wurgoni kofar gida baka duba cewa na wuce xaman gida ba sai yanxu? Rayuwar auratayya kuma da kake fada kaika santa har take maka dadi,  abunda kawai zan iya dorarwa aciki shine: fyaden da kakemun duk daren duniya.  Abubuwan kuma da kayimun a duk xamanmu na barka da mahaliccinka shi zaimun sakayya." tana kaiwa nan ta fusge hannunta ta kifawa Badaru mari,  kafin ya gama mamaki ta kifa masa wani 😳. 



Ta dora da cewa " yau alqawari ya cika, lokacin daka mareni a gidanka na fada maka cewa wlh saina rama gashi kuma na rama din.  Zagin ubana kuma da kayi kace inje in haqoshi a kabari,  bazan rama ba,  domin nasan darajar iyayena sannan nasan duk daren dadewa naka uban xaije inda nawa yaje.  Gida kuma basai nace karka kuma xuwa ba,  saboda bata dalilina ka fara xuwa gidanba."



Baffa dake sauraransu yayi murmushi cikin jin dadin abunda Mimi tayi yace "yar halak kenan, tayi alqawari ta kuma cika maryam jinin Al amin ce domin ga halinsa nan a jikinta. 

Ta fito ta koma gida memakon gidansu fauxa da tayi niyyar xuwa,  shiyasa bata kula da Baffa ba dake tsaye a qofar fita.  Badaru ya gama mamaki ya jawo qafafuwansa jiki babu kwari yayi hanyar waje,  yaci karo da Baffa. Baffa ya nunashi da yatsa yace "karka kuma xuwarmun gida,  in kuma ka kuma xuwa xan hadaka da hukuma" yana fadar haka ya shige gida.  



Washe gari lahadi da yammaci aka aiko kiran Mimi,  har taqi fita mama tace taje in Badaru ne taxo ta fada mata.  Sai dai me tana fita taga Badamasi a tsaye. Tana ganin mutuncinsa dan haka tai masa iso sit room. 


Ya xauna suka gaisa a mutunce ta tambayeshi mutan gida da gurin aikinsa. Yayi farin ciki ganin maryam din ta fara dawowa hayyacinta ba kamar lokacin da tana gidan Badaru ba, ya dunga hasketa da murmushi yana kuma jinta a xuciyarsa.   Yayi mata jajan mutuwar aurenta,  tace ba komai iyakacin xaman da Allah ya nufa kenan. 


Ya karanto mata abunda ke cikin xuciyarsa,  ta dunga kallonsa a kidime ba tace komai ba ta miqe da nufi fita.  Yayi saurin shan gabanta yace "maryam wlh babu inda xaki sai kin fadamun matsayina a xuciyarki,  inbaki manta ba nina fara sonki Badaru furtawa ya rigani indai ba so kike inyi hauka a kanki ba ki amshi soyayyta" itadai babu baka sai kunne,  domin kanta ya daure da yawa. 


Da yaga taqi magana saiya kamota ya sata a bango yayi mata rumfa da qirjinsa yasa hannu ya katangeta ta inda duk motsin da tayi saita taba jikinsa.  Yakai fuskarsa dab da tata ya fara magana "Mimi ki laluba xuciyarki bazaki rasa soyayyata aciki ba,  ba halinmu daya da Badaru ba soyayyar da nake miki bazata bari in cutar dake ba,  xan kula dake xan baki yancinki,  xakiyi duk abunda kikeso, bazan tauyeki ba irin rayuwar da kike mafarki xakiyi. Maryam fargabar me kikeyi?  Bazan akiyeki kusa ba balle a dunga yi miki surutu,  can gurin aikina xan tafi dake sai dai kixo da yawo." 


Ganin cewa kamar baya cikin hayyacinsa yasa tayi niyyar yimasa dabara.  Dan haka tadan dauke kanta daga fuskarsa,  yayi saurin dawo da fuskarta kusa da tasa har tanajin numfashinsa,  yace "yimun magana a haka in san cewa mafarkina ya kusa xama gsskiya."  tayi qasa da murya tace "kadan bani lokaci inyi tunani inkuma yi istikhara" 


Tunda ta fara magana, ya lumshe ido yana shaqar hucin bakinta.  Sai data gama sannan yace "to shikenan,  xanso hakan nima kuma nima zanje inyi sallatul istikhara.  Saboda haka wani satin xan dawo saboda gobe xan koma Dutse" ya dakko kudin da ya ware zai bata 10k ya lalubi hannunta ya manna mata.


Ta kalli kudin ta kalleshi tace "ai basai ka bani kudi zan soka ba."  ya kalleta hankalinsa ya kuma kwanciya da ita yace nasani maryam amma ai kyauta ce.  Tace "nasani amma ka riqe wata rana ka bani"  yayi murmushin cin nasara yace "to my soul"

Ya nemi ta bashi no dinta tace wayar na gida kuma bata ruqe no dinba,  dan haka ya bata tasa xata kirashi.  Dake ya makance a soyayya be gane cewa wayo taimasa ba,  ba musu ya dakko katinsa na gurin aiki ya bata. 


Mama tayi matuqar kaduwa dajin wai Badamsi keson Mimi,  tace "duk da ba haramun bane ai ana barin halak dan kunya,  kuma naji dadi shine gari.  In shaa Allah ko wanda sunansa ya fara daga BA bazaki auraba. Yazaki qara fita yayi haukansa ya gama"



Ranar litinin ranar Baffa ya dau azuminsa na qarshe,  kuma yau ya shirya tunkarar mama akan fushin da take dashi. 


Da yamma ya shiga har dakinta,  ya sameta xaune a kan kujera Mimi tana kwance tayi pilo da cinyarta tanacin chocolate.  Tana ganinsa ta miqe daga kwanciyar,  mama tace mata Mimi shiga ciki.  Ba musu ta shige bedroom din. 



Baffa ya xauna ya fara da bata haquri akan dukkan abunda ya dade yana yimata da kuma godia akan tunasar dashi da tayi, kana ya dora mata da abunda baban Badaru ya kawo masa yaji a waya da kuma abunda yaji da kunnensa Badaru na fadawa Mimi.  Yace yagane kuskurensa kuma ya canja daga yanxu,  kuma Dan Allah ko anan gaba taga yana nufin kauce hanya a wani abun tayi gaggawar tunasar dashi, domin yagane itadin macen arxiqice.  Sannan yayi mata xancen tumunin takabarta yasa an fitar mata a kotu tasamu gidaje biyu da wajen miliyan biyu (saboda andade ana juya kudaden) ya karbi acct no ta da nufin tura mata kudaden ya kuma danqamata takaddun gidajenta.  


Ya kwallah Mimi kira,  ta fito ta tsuguna. Rayuwa kenan duk wanda yayi haquri zaiga haske domin wai yau Baffa ke neman yafiyar Mimi da kuma bata haquri akan abunda duk ya faru a baya.  


Mimi tana hawaye tace "komai ya wuce Baffa,  kai ubanane duk duniya bani da wanda ya fika,  nima ka yafemun abunda nayi maka rannan saboda bani da xabi sai hakan shiyasa nayi" yace baki komai ba MARYAMU  Allah ya miki albarka ya baki abokin xama nagari sakamon biyayyar da kikaimun. 


Mama na gefe na share hawayen farin ciki,  ta dunga godewa Allah.  Tace da Baffa nagode da kulamana da dukiya da kayi.  Amma inaganin wadannan ka karba ka riqemun."


Yace "riqe abunki Haj Fadima,  nadai riqe na yayana Faty da maryam kuma suma na rubuta da shedu saboda halin rayuwa, gidajen dai xantsaya a xuba yan haya."  tace to duk yadda kayi nagode.  



Yace " to ai bazan yadda kin huce ba sai kin karbi girki,  ga cefane can nakawo inaso aimun special girki dan azumin nake kuma nadade banci delicious dinki ba."



Mama ta miqe tabi bayanshi tana dariya tace " yau kuwa xakici domin xan tabbatar maka na huce." Umma da Anty da tunda ya shiga dakin mama suke tsaye suna jiran suga abunda xa ai suka qiqim qiqim ganin mama da Baffa tare suna dariya.  Mimi ma ta biyo bayansu da nufin taya mama girki itama tana tata dariyar. 


Mrs 😊
[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼
AL AMARIN MARYAM 
🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼


📝FANTASTIC STARS WRITERS 
 {F S W }
 
Writing & story by 
Rahma Muhammad {hajia} 

Editing by
Mmn khairat 😍

 
   Page 1⃣4⃣


     Cike da farin ciki Baffa ya shiga gidan,  gami da kwalawa mama kira tunda daga tsakar gida,  ta fito a gigice saboda Jin kiran farautar da yake mata ta iskeshi daki gami da yimasa sannu da xuwa.  Ya amsa yana washe baki kamar bebe yaga wawan zama (Lol) sannan ya dora da cewa wani abun farinciki ne ya samemu fadima shiyasa ki ganni gida yanxu,  wato yaronnan dan wajen Alh Inuwa shine yaga Maryamu yace yanaso, kuma ga dukkan alamu akusa sukesan auren dan Alh inuwa da kansa yayimun maganar ni kuma nayi dattako nace kawai in sun shirya su kawo kayan aure kawai ayi.  Mama ta kalleshi shagarai tare da daure fuska tace,  Alh wannan wane irin neman aure ne sai kace auren yar tsana?   Daga yaro yaga Mimi yace yanaso sai ace ya fito anbashi?  Ita mimin baza aji raayinta ba?  Kuma banaji ma Mimi tasan maganar domin da tasani xata fadamun, sannan shin kayi bincike akan yaron?  Ko kuma dan ansan mahaifinsa shikenan?  Aure fa in anaso a zauna lfy sai anyi da yardar maauratan,  kuma naga ai bakai da Alh inuwa ne zakuyi xaman auren ba,  yaran ne masu xama  saboda haka inaga ku basu dama su fahimci juna inyaso daga baya insun dai daita kwa shiga lamarin. Baffa dake kallon mama tun da ta fara magana a dage tare da fallara mata harara wacce ita sam bata kula ba,  ya magantu da cewa sai yanxu nasan ke babbar mahaukaciya ce fadima.  Ta miqe tsaye tare da qara daure fuska tamau tace hauka kuma?  Yau kuma nice mahaukaciyar?  Nan da nan kuwa ya dai daita nutsuwar domin ya farga da kasassabar da yayi (ya tuna da fadima yake magana wacce Sam bata daukar irin cin mutuncin da yakewa ragowar matansa, ta nuna masa tasan ciwan kanta dan haka ko fada xai mata yakan tausasa kalamansa)  dan haka yanxu ma sai yayi saurin yin kwana da cewa ai kece naji kina qoqarin yiwa Allah butulci,  shekarar maryam din nawa ana neman miji?  Ba a taba budurwa mai shekarunta ba kaf danginki da nawa,  sai yanxu Allah ya kawo kice ga xance ga magana.  Ta kalkeshi tace ni ba butulu bace kuma ba butulcewa nai ba inaso ne dai a gina auren akan fahimtar juna da soyayya,  amma tunda haka kace shikenan Mimi yarka ce kana da ikon xaba mata miji, Allah ya sanya alkhairi yasa tsohuwar gida ce.  Yawwa yanxu kikayi magana fadima da tun farko abunda kikace kenan ai da ba a tsaya sa insa ba, amin Allah ya yi miki albarka cewar Baffa. 

       Maryam kwance saman gadonta acan hostel na law skul rubda ciki take tana danna system,  qarar Waya ya katseta daga typing din da take a system din, ta tsurawa screen din wayar ido gabanta na dukan 3 3 , tun tana qanqanuwarta ta tashi da tsananin tsoron Baffa da kuma dison qiyayyarsa acan qasan zuciyarta saboda halin ko inkula da yake da al amarinsu, duk da cewa mahaifiyarsu awancan lokacin tana boye musu lamarin baffan garesu kafun su girma su gane,  sai kuma alokacin mama take yawan cemusu halin Baffa garesu ajixanci ne irin na Dan Adam.  Amma AL AMARIN MARYAM na jinkirin aure da kuma takura gami da gorin Baffa akanta yasa dison qiyayyar Baffa ta samu girma a zuciyar maryam wanda takai tayi yado ta zama tamkar bishiya mai rassa,  domin ji takeyi kamar ta raba auren Baffa da mahaifiyarta domin auren Baffa ba abunda ya qari mama dashi sai muzgunawa da gori daga gurin matansa daga gareshi kuma xa a iya kiran abun da yaudara domin kulawar da take kwadayin yayanta su samu inta aureshi basu sameta ba.  Wayar ta sakeyin qara akaro na wajen 4 wanda hakan ya yankewa maryam tunaninta,  tai shahada ta daga wayar.  Ta gaisheshi cike da tsoro da firgici,  ya amsa farai farai tare da tambayar karatunta da kuma lokacin kammalawa,  lamarin daya daure kan maryam tamau,  acikin ranta ta farta Baffa da tambayar karatuna? 😳 first in history.  

         Bayan hakanne kuma ya zayyano mata dalilin kiranta a waya akan maganar Badaru,  sai da ta nutsu kwarai sannan ta gane wadanda yake nufi domin ita tamanta da haduwarsu,  amma kuma tayi mamaki dajin cewa wai har ana zancen qarbar kudi ba tare da sun zanta da wanda ya nuna raayin a kanta ba, (domin ita a zatonta wanda yayi mata magana shike sonta wato Badamasi) amma da yake mama batai musu tarbiyyar ja da maganar Baffa ba sai kawai tace masa to Baffa Allah ya xaba mana abunda yafi alkhairi, yaji dadin furucinta kwarai ya dunga samata albarka.  Koda ta kashe wayar tunani ya cikata to meyasa yaya Faty da mama babu wanda ya mata maganar ko dai suma basu sani ba? Sannan ta shiga wassafa siffar guy din da azatonta shine Badarun,  ta dan tabe baki 😏 tare da furtawa a fili "yayi babu laifi he is handsome " amma ba irin mijin da nake mafarkin samu bane  duk da bashi da muni amma bashi da tsahon da nakeso daga da namiji " 🙈 ta rufe idonta cike da kunya kamar wani yana ganin.  Wannan dare dai haka ta qareshi cikin tunanin irin nata salon neman auren cikin gaggawa wato haka Allah ya shirya mata kuma dama fauxa (wata qawarta yar unguwarsu)  tasha fada mata in Allah ya tashi bata miji in shaa Allah gaba daya zai fito jinkiri zai kawo mata alkhairi,   ta miqe cike da farin ciki da kwarin gwiwa ta dauro alwala ta tada sallah aranta tana cewa ashe nima zanga ranar aurena,  ashe ankusa a daina yimun gorin aure 😊. 
  
        Ranar jumaar data kasance aranar aka karbi kudin auren Mimi da kuma lefe,  da misalin qarfe 2:30 pm Faty ta shiga dakin babarta afujajan, daga gurin aiki take.  Yau dinnan zancen kawo kayan lefen ya isketa daga bakin Ahmad mijinta. Tai sallama danta na fari dady (AL Amin)  wanda yaci sunan babanta yazo da gudu ya rungume qafafunta da yake a gurin mama yake tun daga yaye,  na biyun kuma wato Muhsin dan kimanin shekara 2 tun safe suke gurin mama dashi dame rainonsa.  Ta sunkuya ta sumbaci dady tare da cewa sannu babana,  muhsin ma ya gangaro ta daukeshi tana shafa kansa.  Ta zauna akan kujera gefen mama tare da bawa laure (mai rainon muhsin)  umarnin ta dakko mata maltina a fridge,  da kyar ta ida bari suka gaisa da mama saboda xance na cinta, suka qule uwar daki.  Ta kalli mama da alamar tambaya tace mama wanene mijin Mimi?  Wane irin neaman aure ne wannan bamuji neman aure ba banusan mijin ba sai kawo lefe mukaji da sa rana? 😒 . Mama ta gyara xama cikin hikimar uwa ta gari da sigar lallashi ta kwashe zancen tas ta fadawa Faty sannan ta dora da cewa kuma shima Baffa besan har lefe zasu kawo ba,  shi kudi sukace masa kawai sai gasu da kayan lefe.  Kuma banaso ki dau dumi a lamarinnan tunda baffanku yace yayiwa Mimi maganar ta bada goyon baya kinga hakan ya nuna tanason yaron,  kuma kodan mutan gidannan inaso ku karbi lamarinnan haka Allah ya tsara muyi mata addua da fatan alkhairi.  Tace to mama ai tunda kince mimin tanaso shikenan 😊 dama ni banaso a danne haqqinta ne,  yanxu ina kayan lefen?  Suna can dakin ummanku.  Ta miqe ta nufi dakin Umman, tanasa qafa a falon ta fara cin karo da cosmetic din kayan lefen alamar angani duk an watsar ba a gyara ba. Umman na ganin Faty ta dan saki fuska da yake makira ce tare da cewa a a Faty har kin qaraso?  Tace eh suka gaisa tare da yiwa juna murna akan auren na Mimi, ana cikin hakan ne anty ta shigo baqin cikinta sam be boyuba akan fuskarta,  ta kalli Faty tare da cewa sai kuma kikaji abu babu zato?  Ai bana dai yan kwantai sai aure suke,  Faty da maganar ta bata ranta tayi murmushi da cewa aishi aure lamarine na Allah in lokaci yayi sai kikaga duk hassadar mutum sai anyi kuma sai kiga duk dadewarka babu aure abun ya zama tarihi.  Ta fada tana duba kayan Anty da taga Faty ta dagota sai tai saurin sakin zancen tare da kama wani gadai lefenan akwati 4  da kit ne kaya kala 30, takalma qafa 5, jaka guda 3, 
 Sai mayafai 6. Kodan gold qaramin Set babu,  babbar atamfa a cikin lefen itace cote d voire,  leshi bafi tsada acikin kayan kwanaki  Safna (yar antyn ce)  ta saimun irinsa a gurin aikinsu biya 2 8k  kinga a kasuwa baifi 6k  kenan? Ai wlh a tarihin gidannan ba a taba matsiyacin lefe irin wannan ba, wai lefen mai kwalin degree a hannu kenan ta qarasa fada tare da sheqewa da dariyar mugunta 🤣, sannan ta dora da cewa ana cewa jinkiri na kawo alkhairi ni dai banga alamun alkhairi ga wannan auren ba nashaji ana cewa in guga ya dade a rijiya yana jawo ruwa tsullum amma shikam gugan gidannan yayi shekaru aru aru a ruwa ya dago fayau.  Faty ta dago tai qayataccen murmushi cikin qoshi da ilimi da wayewa tace "mashaallah kaya kam sunyi mu sun ishemu haka duba da babu irin tufar da Mimi bata saba indai a duniya take kuma da kudi ake siyanta, to kinga kuwa indai ka saba saka sutura me tsada ai ta lefe baxata dameka ba,  kuma ai lefe bashine xaman aure ba mu alkhairin abun muke nema,  kuma bamusan arxiqin da Allah ya yiwa Mimi ba anan gaba kinga kuwa be dace mu sare tundaga kan lefe ba.  Tana gama fadar haka ta tattara kayan ta maida komai muhallinsa ta dubi umma wacce ke kan kujera tana kada qafa ga dukkan alamu xancen Anty akan Mimi yayi mata dadi domin ga fuskarta nan ta nuna alamar hakan.  Tace Umma Allah ya sanya alkhairi ya kuma kaimu lokacin sannan ta fice . Haka sukaci gaba da shirin biki wanda xa ayishi da zarar Mimi ta gama law skul da sati daya. 



Mrs Muhammad 😊
[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼
AL AMARIN MARYAM
🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼 


📝FANTASTIC STARS WRITERS 
{F S W }        

Page 1⃣5⃣


NA RAHMATULLAH (Hajia) 




       Kammaluwar karatun Mimi da kawo IV din bikinta abune da ya kasance a tare,  kuma aranar data dawo ne Badaru yaxo domin suga juna tare da tattauna al amuran biki ( kuji fa kamar auran qauye), da taimakon yaya Faty wacce kullum sai tazo gidan saboda shirin biki  ta shirya kanta cikin atamfar súper wax ja ta yafa mayafi kalar atamfar da dan takalminta shima ja plat, fuskarta tasha make up wanda ya fito da idanunta sukai tar saboda eye liner da mascara da akai amfani dasu wajan qayata idanunta.   Jikinta na tashin qamshin turarurukan companyn Al rehab, domin ita a raayinta tafison Arabian perfume .

           Zaune ta iskoshi a sitroom din gidan,  qamshinta ya fara sanar masa ta iso, ya dago ya qura mata ido tare da hadiye wani irin abu da ya tsirga masa maqogaro ya saki murmushi aransa yana qisima bai taba ganin macen da ta birkita masa hankali ba, idan aka dauki lokaci bai samu maryam a matsayin mata ba tabbas zai iya sabawa ubangijinsa akanta,  duk wani abu da ake buqata ajikin mace maryam tana dashi , wata irin muguwar sha awa yakeji akanta, feelings din dabe taba sanin yana dashi ba akan mace maryam tasa yana jinsa , shiyasa ya yanke shawarar auranta duk da baya sonta kuma baya raayin mace me shekaru da wayewarta,  zai ajeta amatsayin wacce zai dunga kashe qishirwar shaawarsa akanta,  sannan gefe kuma ga burin ransa wato Nafeesa a matsayin matar so.  A bangaren Mimi kuwa tana hada ido da Badaru gabanta ya yanke ya fadi a fili ta furta "innalillahi wa innah ilaihi raju un " saboda tsananin firgici data shiga na ganin Badaru amatsayin mijin auranta nan da yan kwanaki,  ashe wanda take zato ba shi bane?  Ashe ita duk hauka take?  Ashe Badamasin ma da take ganin be cika irin sharadin mijin da takeso ba , ba shine mijinta ba?  Ashe kasan Badamasin ne? Shin meyasa ta dauri kanta ta cewa Baffa ta yarda da mijin da ya bata tunkan taga kalar mijin?  Yanxu fisabillah ina ita ina wannan dan tsamurmurin bafillacen wanda tasan tafi tsaho nesa ba kusa ba???  Tambayoyi burjik ta dunga yiwa kanta a xuci a fili kuma tana hawaye,  wata irin muguwar tsanar Badaru ta shiga xuciyarta nan take.  Badaru da tun daxu yake kallon Mimi cikin mamaki, ya magantu " yanaji da ganina kin furta adduar da sai anga masifa ko abin qi ake yinta? " cikin baqin ciki da bacin rai idanunta jazur ta kalleshi tare da cewa meyasa kaimun haka?  Dan me baka nemi yardata ba ko Jin raayina akanka kakai maganar gurin Baba na?  Wane irin neman aure ne haka?  Ya bata amsa da cewa irin neman auren da addini ya tsara,  batare da tunanin komai ba tace to kasani ni Banasonka wlh 😪  shima cikin nasa sigar bacin ran da tsantsar rashin mutunci yace to nima anfada miki ina sonki ne?  Kawai dai xan aureki ne saboda bani da xabin da ya wuce auran naki,  xancen rashin neman yarsarki kuma sai kije ki tuhumi babanki wanda daga ganin sarkin power yasa miya tai zaqi,  dagaji ance ina sonki yace in fito wanda hakan ya nuna baki da wani sai ni din danake shirin rufa miki asiri shine xakimun iskanci,  wlh maryam bani da auran mace me shekaru kamarki kawai qaddara Allah ya doramun akanki.  Ance inxo ne in mutsara lamarin biki to ni kisani bani da raayin wasu bidi 'o'i saboda haka sisina baxan bayarba nayi abunda yake wajibi wato sadaqi.  Yana fadar haka yasa kai ya fice. 

       Jage jage fuska duk ta dame saboda make up daya hade da hawaye ta shiga dakin mama,  Faty ce kawai ta kula da shigowarta dakin ta sauri tashi ta tareta ta fada jikin Faty tare da qara fashewa da kuka,  yaya Faty dama irin mijin da Baffa ya zabamun kenan?  Sam be dace dani ba wlh banasonsa na tsaneshi bana raayin auren mutum irin wannan.  Faty ta dago kanta cikin rashin fahimta tace Mimi yimun bayani yanda xan gane,  ba ance kun taba haduwa ba?   Tace ba shi bane sister wanda nake zato ba shi bane 😭😭 wannan mugune wanda baya qaunata kuma ya furtamun da bakinsa,  bazan aureshi ba sai dai in duk abunda za ayi ayi.  Mama ta iso kansu ta tsaya cike da al ajabin abunda mimin ke fada,  ta durqusa a gabansu tace Mimi babu abunda za ai wanda ya wuce ki yarda da qaddara kinsan wlh auren nan babu mai hana faruwarsa sai Allah tunda baffa ya tsaya akai,  kuma turjiyarki ga wannan lamari yana nufin tashin hankalina acikin gidannan.  Ta share kwalla tare da cewa mama yanxu auren dole kike nuna goyon baya ayimun?  Tai saurin tareta da cewa a a wlh Mimi ko maqiyina bazanso auren dole akansa tunda anyimun banji dadi ba,  bare ke yar cikina, amma inaso kiyi haquri ki dauki wannan aure a matsayin qaddara mutum baya taba gujewa qaddararsa wlh tun kan nasan waye mijin da Baffa ya xaba miki naji Sam lamarin bai munba, MARYAM indai ni na haifeki bazaki kaucewa umarnina ba,  umarnina kuma gareki ki karbi wannan aure,  in shaa Allah bazaki danasani ba.  Ta dafa mimin tare da cewa kin yarda xakibi umarnina MARYAM?  Tai saurin kwada kai tare da cewa yar halak ce ni mama bazan taba kaucewa umarninki ba,  naji nagani na yarda.  Kukan da take yasa dady dan yaya Faty shima yasa kuka tare da xuwa ya rungume Mimi yana share mata hawaye da cewa Anty yi shiru ki dena kuka Anty,  ta kalli yaron soyayya ce me qarfi tsakaninta da dady ko uwarsa be shaqu da ita ba yadda ya shaqu da Mimi saboda a hannunsu ya tashi,  tayi dariyar yaqe cike da qaunar dady tace nayi shiru Baba na ta rungumeshi suka kwanta akan cinyar yaya Faty.

      Badaru tsaye qofar gidan su Nafee,  yafi 30 minutes a wajen yana dakon fitowar ta amma shiru,  har ya fidda rai ya juya zai tafi sai kuma gata ta fito tana yatsina wacce take nuna dab take da tayi rashin mutunci. 

 Ya dan matsa kusa da ita tare da cewa ranki ya dade yana washe baki 😁. Tai far da ido 🙄 sannan tace meya kawo ka?  Ai canake kanacan gurin masoyiyarka?  
 
Yayi saurin tareta da cewa ai bani da wata masoyiya da ta wuce ki,  ai ban zaci ma zaki fito ba kusan fa sati 2 ina xuwa bakya fitowa.  Ta fallara masa harara sannan tace ai dole ce tasa na fito,  tunda naga rashin fitowar tawa be hanaka abunda kake niyya ba wato auren Maryam. Ta fada tare da 
fashewa da kuka 😪.

 Tausayin Nafeesa da sonta ya qara qamari a xuciyarsa cikin sigar lallashi yace yi haquri Nafee wlh auren maryam qaddarace a guri..... Dakatamun ✋🏽 ta tsai dashi a hassale,  Kullum abunda kake fada kenan a matsayin abunda xaka kare kanka a wajena kuma nagaji dajin hakan,  ai wlh Badaru ka cuceni, ingama jiranka inbar karatuna sabida kai amma yanxu kaimun haka.  Yanxu bani da ikon fita sai aita nunani ana zundena,  wasu har cewa suke ka fasa aurena. 

 Nafee kiyi haquri wlh babu abunda xai hanani aurenki sai mutuwa,  kuma duk masu yi miki dariya a sannu zasusha mamaki domin aurenmu na barshi daganan xuwa bayan sallah in shaa Allah. 

 Amma dai kasan bazan zauna da ita ba ko?  Saboda haka ka nemar mun gurin zama tun wuri saboda na tabbatar bazan iya hada kishi da wata ba a kanka. 

Nasani Nafee shiyasa ma na nemar mata gurin xama shi kuma wancan gidan dama nakine ke kadai keda yayan da zamu haifa. 

 Nafeesa ta dan sakko jin wannan furuci na badaru kuma ta tabbar har yanxu yana sonta,  tace wai muga photon ta kyau ta finine naga kanata rawar kai a kanta?   Yayi murmushin cin nasara yace wlh bani da photon ta amma wlh ko kama qafarki batai ba Nafeesa. Wai shin kinsan ma dalilin auranta?       Nan ya kwashe abunda ke ransa game da Mimi ya fadawa Nafeesa ba tare da tunanin illar da hakan kan iya haifarwa ba nan gaba. 

Lamarin da yayiwa Nafeesa dadi kwarai da gaske,  domin tasan halin Badaru baya qarya hasali ma ya tsani maqaryacin mutum,  kuma tasan abunda ya fada mata harga Allah hakane a xuciyarsa.  Shiyasa ta saki jiki sukaci gaba da hirarsu ta soyayya kamar ba abunda ya faru. 

Mrs Muhammad 😊
[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼
AL AMARIN MARYAM 
 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼          

📝FANTASTIC STARS WRITERS 
                  {F, S, W}

Written by 
RAHMTULLAH (Hajia) 


Dedicated to 
MARYAM BAITA 


Page 1⃣6⃣

   Kwanaki kadan bayan hakan Mimi tai wata irin muguwar rama ta fita hayyacinta,  kallo daya xakai mata kasan akwai abunda ke cinta a xuci. Duk da ba fita tayi rabon i v ba,  acewarta a turawa kowa ta waya inda hali ma a haqura da shagali a bikin a daura aure a kaita.

Abubuwa da yawa sun taru sun cudewa mama da yaya Faty da duk ma wani masoyinsu,  ta bangaren mama dai abu da yawa na damunta,  babban abunda yafi damunta kuwa shine damuwar halin da Mimi take ciki,  na biyu kuma abunda Baffa Yayi mata.  Abunda ya faru dai shine : abunda yayi a bikin Faty shi ya maimaita akan Mimi koma ince har gara Faty akan Mimi domin kuwa tunda ya sai set din kayan gado guda 1 da saitin kujeru yaja bakin aljihunsa ya tsuke daga haka ko tsinke be kuma siya ba,  abunda yayi mugun baqanta ran mama da duk yan uwanta,  domin a xaton mama Baffa xai saki jiki yayiwa Mimi kayan daki kamar yadda yake yiwa yayansa kodan albarkacin biyayyar da tai masa akan mijin da ya bata.  Ita tunaninta abunda yasa yayiwa Faty haka a lokacin aurenta dan bayasan auren da Ahmad ne,  amma sai taga sabanin haka domin har gara kayan Faty akan na Mimi, kenan Baffa ya na nuna mata yayan Al amin daban da nasa tunda ga banbancinnan yana nunawa qiriri,  amma duk cikin lamarin Baffa wannan yafi bata mata rai fiye da rashin kai yayanta sauke farali kamar yadda yakewa yayansa domin a cewarta xuwa maka lokacinsu ne bayi ba. Ta kuma qudure a ranta cewa lokaci yayi da xata takawa Baffa burki akan yayanta. 

Ita kanta Faty da bata cika daukan abu da xafi ba wannan karon taji zafin Baffa kwarai akan abunda yayi. 

Da yake dangin mama ba matsiyata bane da ita kanta maman da Faty suka fidda kudi naqudai Adda halima da yaya Faty sukaje suka lafto siyayya daga kan kayan kicin da kayan qayata falo komai acan acan,  sukaxo suka lafce kayan a tsakar gidan Baffa,  duk girman tsakar gidan sai da kayan sukai ragowa aka dora wasu kan wasu.  Cikin falon mama kuma danginta ne cike taf tunda da kan Adda halima (momy)  har xuwa kan matan yayyensu da kuma yayansu, bakajin komai sai tashin hira da shewa cike da nishadi.

A dai dai wannan lokacin kuma matan gidan na cikin dakunansu cike da baqin ciki. Umma dai anata bangaren tun lokacin da aka kawo lefen Mimi har xuwa kayan auren da Baffa yayi mata tana cikin farin ciki,  domin ita macece wadda bataso taga anfi yayanta,  to ganin komai na Mimi tsiya tsiya yasa hankalinta mugun kwanciya, domin taga Mimi batafi yayanta ba, amma ganin wannan uban Kaya da dangin uwar Mimi suka kawo yasa murnarta komawa ciki. 


Bangaren Anty kuwa kusan tafi Umma shiga tashin hankali akan wannan kaya,  domin ita Sam batason cigaban wani koda kuwa dan uwanta uwa daya uba daya,  bare kuma Mimi yar kishiyarta wacce tafi tsana a duniya.

Ana cikin hakanne saiga Baffa ya dawo diban wani katin daurin aure domin wanda ya fita dashi ya qare, ya tsaya turus ganin kaya sun cika gida ya kwallawa Umma kira suka fito tare da Anty (kamar ita aka kira),  yace mata wannan kayan fa?  Momy wacce ta fito daga dakin mama tace sannu Baffa ya juya tare da cewa haj halima ashe Kina ciki? Suka gaisa tai masa Murnar qaratowar biki sannan ta dora da cewa, dama kayane ta fada tare nuna kayan,  muka kawo tamu gudumnawar babu yawa.  Wata irin kunya ta rufe Baffa wacce tunda yake bai taba jiba, nan take ya fara nadamar abunda yakewa fadima akan yayanta,  har yake tambayar kansa shin meyasa yayi haka kuma meye ribar nuna bambamcin da yake tsakanin yayansa da yayan dan uwansa guda daya da ya mutu yabar masa,  gashinan dai abunda beyi ba danginta sunyi mata kamar yadda sukai a bikin Faty,  yasan acikin matansa duk wacce za aiwa yarta aure ko cokali bata siya,  amma fadima abikin Faty dana Mimi ta nunka abunda ya kashe wajan sau 3, baiji ragowar abunda momy take fada ba saboda tunanin da yake,  sai dai kawai ya tsinci kansa da yi mata godiyar kayan da suka kawo. 

Ba yanda yaya Faty batai da Mimi ba taje wankin kai da qunshi amma taqi,  da kyar fauxa qawar mimin maqociyarsu ta lallami mimin suka tafi saloon akayi mata shampoo aka gyara gashin, qunshi kuwa qiri qiri taqi zuwa dole sai yaya Faty ce tasa me kunshin tazo har gida tayi mata.  Duk da cewa Badaru be bada kudin event din yan mata ba, yan uwanta sun kama gidan dan hausa inda xa ayi luncheon kawai,  domin ko sun qara wani event din Mimi bazataje ba,  dan luncheon dinma cewa tai ba inda xata. 

Ana gobe kamune akaje kafi (jere) gidan amarya ko 2 hours masu jeren basuyiba suka dawo jiki a sanyaye,  domin kuwa wata yar qaramar gida Badaru ya kama haya a wani Geto area da nufin nanne gidan Mimi.  Gidan dai yafi kama da gidan student wanda suke kamawa inbabu guri a hostel,  domin dan qaramin tsakar gida ne sai qofa daya wacce inka shiga xaka tadda falon da ko Set din kujeru baxai ci ba sai bedroom daya da toilet aciki sai dan kicin dan qarami daga hagun falon,  irin kitchen da in kin shiga bazaki iya tsgunawa ba saboda qanqantarsa. 

Wannan gida ya faranta ran maqiyan Mimi na gida (irinsu Umma da Anty da kuma wasu daga cikin yayansu) da na waje. Anty ta dunga murna tana cewa yarinya dai ko FARHAN kitchen aka sai mata a banxa tunda babu gurin xubawa,  domin kuwa ala dole aka juyo da kayan Mimi gida dan abunda ya samu shiga cikin gidan ba wani yawane dashi ba,  don ko fridge da cooker gas basu samu shiga ba sai dan qaramin gas aka siya mata irin na yan hostel.  Direct aka wuce da kayan gidan kakakannin Mimi (gidan mal SULAIMAN)  aka jibge. 

Matar babban yayan su mama (Umma)  da momy suka dunga masifa akan wulaqancin da gidan su badaru sukaiwa Mimi akan gida kuma haka suka samu Baffa da xancen, shima da yake bayason harkar qaranta a take ya nemi mahaifin Badaru da zancen,  har yana barazanar inbasu da wuri ajiye maryam a fasa auren dan ransa ya baci shima,  alh inuwa ya dunga bawa Baffa haquri da cewa wlh suma sai a qurarren lokaci Badaru ya nuna musu inda zai saka maryam kuma basu so hakan ba, amma su kwantar da hankalinsu ya kusa gama gininsa.  Wannan ne yadan kwantar da hankalin masoyan Mimi, amma duk da haka qananan maganganu sunyi ta kai kawo a tsakanin mutane akan auren.

Ranar alhamis itace ranar da aka fara bikin ko ince ranar luncheon,  duk yanda aka kai da lallaba Mimi ta tashi tai shirin tafiya Gidan Dan hausa gurin luncheon Sam taqi anyi fadan anyi nasihar anyi waazin duk taqi ga dukkan alamu halinta na kafiya ya motsa,  ala dole aka kyaleta ganin ciwonta na daukewar numfashi na alamun tashi domin qirjinta sai bugawa yake wanda shine alamun ciwonta yana gab da tashi,  duk ta yankwane tayi wata irin migues rama duk wannan cikar jikin ta xube a 10 dayz,  sai idanuwa xuru xuru da qasusun wuya. 

Haka dai aka dade aka barta a gida daga ita sai kakarta (hajja maryam)  wacce taci sunanta kenan sai kuma mama da tace ina xata yarta babu lfy?  Hajja ce ketaiwa Mimi nasiha da falalar yadda da qaddara mama na gefe tana shafawa hajja mai a qafarta saboda wankan da tayi,  nasihar ta shigi Mimi sosai saboda kwatancen da hajja tai mata da mama mahaifiyarta da kuma irin quncin da ta shiga a dalilin damuwarta,  a fili hajja ke nuna San Mimi fiye da duk wasu jikokinta tanason yarinya fiye da tinanin me karatu.

Mama kuwa ko kallon Mimi batason yi saboda kwantsamewar da Mimin tayi, kuma sau tari in ta kalli Mimi sai taga kamar tana kallon hoton rayuwarta ne ta baya, domin itama haka ce ta kasance gareta lokacin aurenta na fari.  Ta maida hankalinta kacokan kan kula da hajja ( mamanta)  wacce tazo bikin Mimi da nufin sai angama xata tafi. 

Bayan magriba yan bikin da babu amarya suka dawo,  atsakar gida suka jiwo muryar anty na cewa wannan wane irin biki ne kamar na bagudajiyar qauye?  Biki lami kuma dan abun kunya event daya? Neman kudi anan dai beyi rana ba wlh,  shiyasa amaryar taqi xuwa ta qirqiri ciwon qarya 😄. Ai wlh ba a taba abun kunya a gidannan irin wannan ba domin ko taron suna ake a gidannan anayin shagalin da yaci uban wannan kai andaiji kunya wlh,  lallai kwantai beyi ba, 😂 dama haka bikin yan kwantai yake komai tsiya 2 ? Allah ka cigaba da bawa yayanmu miji da wuri tun suna da quruciyarsu.  Babu wanda ya kulata a dangin mama da suka cika gidan domin hajja ta hana a tanka mata a cewarta wanda ya tara jama a baya fushi ko fada in yayi fushi to ya bata taronsa. 


Washegari juma a aka daura auren MARYAM AL AMIN da BADARU MOHD INUWA akan sadaki 50k,  kuma a take Baffa ya kirata ya bata sadakinta kamar yadda addini ya tanada,  tana shiga daki ta wullar da kudin sadakin ta sa kuka,  sai mama ce ta dauke kudin.  Washegari akai yini anan gidan  babu wani armashi qarfe biyar aka tafi kai amarya kasancewar unguwar da xa a kaita da nisa sosai da kyar aka fito da ita daga gidan domin ta qanqame mama tana kuka da kyar momy ta banbareta daga jikin Maman tai waje da ita tasata a mota, momy da wata yar uwar su Baffa (qanwace a gurinsu baffan)  mama saude suka shiga aka tafi kaita. 


Mrs😊[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 1⃣7⃣

Dedicated to 
Maryam Baita


    Tun fauxa qawar Mimi,  na jiran xuwan tawagar ango da sunan siyan baki har ta gaji da xaman jiran. Wajen 8:30 pm tai shirin tafiya,  ta miqe ta dau mayafinta dake gefen Mimi ta yafa, tace "qawata nikam xan tafi tunda har yanxu angon be qaraso ba, kuma kinga layin naku da nisa daga titi kar dare ya qarayi inrasa abun hawa". 

Mimi ta marairaice cikin zubda kwallah 😪 tace fauxa kema tafiya xaki kibarni kamar yadda kowa ya tafi yabarni?  Fauxa qawancenmu yace haka?. 

Ta xauna gefen Mimi tare da cewa qawata haquri xakiyi, kinsan nabar Aslam a gida gurin mama, kuma nasan yanxu yanacan yana kuka, indai har Baba ya dawo ya datta bananan nabarshi yana rigima fada xaimun.  Wlh dana taho dashi sai najira xuwan su Badaru inyaso sa maidani gida. 

Ta riqe hannun mimin sannan tace "qawata kiyi haquri komai yayi farko xaiyi qarshe, ikon Allah ne kawai bashi da farko bashi da qarshe,  Allah ya sa alkhairi acikin aurenki. Kimaida AL AMARINKI gurin ubangiji,  in shaa Allahu zakiyi alfahari da wannan aure, karki bari rashin son mijinki ya taba biyayyarki gareshi har irin tawa ta sameki (mutuwar aure),  bana fatan haka Mimi.  Ki tuna ba duk abunda kakeso kake samu ba. Kiyi biyayya, kiyi ibada,  abu na qarshe da xan fada miki shine kada ki sake ki zauna da yunwa ".  Na sanki Jan wuya ce ke wurin ibada,  to qira akai". 

Tana kaiwa nan ta juya ta tafi ita kuka Mimi kuka.  

Tun bayan tafiyar fauxa take xaune a tsorace, koya taji motsi sai ta firgita duk kuwa da cewa ita din ba gwanar tsoro bace,  amma yau sai tasami kanta cikin mugun jin tsoro,  ji take kamar ta tashi ta xura da gudu, kasancewar ba wuta a unguwar sai chaja aka kunna. 

Batasan iya lokacin data dauka a haka ba, sai ji tayi ana bude kofar gidan ta waje, alamar me gidanne. Shigowarsa parlon ya xowa Mimi da wata irin faduwar gaba matsananciya, gumi ya dunga karyo mata. 

Sam bazata iya tantance ko yayi sallama ko beyi ba,  domin ko yayi bataji ba balle ta amsa. Direct yayo kanta tare da cire mayafin data rufe kanta dashi yana huci kamar a fagen daga (filin yaqi) duk da a tsorace dake da abunda yayi hakan baisa ta motsa ba, ya qare mata kallo tare da hadiye wani mugun yawu duk da ramar da tayi hakan bai hana surarta bayyana ba,  ya dure kallon nasa akan fuskarta ya qura mata ido yana mata kallon qurullah,  abunda bai taba lura tana dashi ba kafin ya aureta yau ya ganshi wato tabon sallah take goshinta da danannen bakinta,  sannan kwantancen gashin dake gaban goshinta,  hakan yasa ya cire mata dan kwalin kanta,  kyakykyawan gashin kanta dashi sampoo yake tashin qamshin mega growth ya bayyana, " SUBHANALLAH " ya furta afili sannan a zuciyarsa yace dama anasamun macen bahaushe da irin wannan gashin?  Ya shafa gashin,  sannan ya tura hannunsa cikin wuyar rigarta ya cafko qirjinta, abunda yayi tsananin firgigita tai saurin yin baya ta maqure jikinta. 


Taso muyi sallah,  ya fada ransa a hade cikin sigar bada umarni,  sanin cewa batai sallar ishaba yasa ta tashi ta bishi inda yabi wato toilet tayi alwala suka fito, ya jasu Sallah sukayi isha,  sallar ma aurata ta biyo baya. Tasan akwai adduar da manxon tsira (s a w) ya umarci miji ya dafa kan matarsa yayi mata ita kam baiyi mata,  ya tashi yaje kitchen ya dakko cup ya tuttula L&Z Milk ya shanye sannan ya kuma cika kofin ya miqa mata a hankali ta girgiza kai alamar bata sha,  ya bude ledar kazarsa ya cirota sai tashin qamshi take ya dora kan plate " zo muci " abunda ya cemata kenan, bayan ya fara yagar kazarsa yana hadawa da madarar yana kurba, alamar an dade ba a hadu ba 🤣 (lol), ko kallonsa bataiba balle ya samu amsa. 

Bayan ya tashi da kaza guda da liter daya na gorar madarar l&z, ya ture ragowar   kayan da yaci gefe ya cire rigar shaddar jikinsa tulelen cikinsa ya bayyana alamar anyiwa cikin loding da yafi qarfinsa,  ko singlet babu ajikinsa. Babu batun yin brush domin tsaftace baki kafin kwanciyar bacci balle aje ga dan yin tattaki domin narka abinci daya loda kamar yadda addini ya hana kwanciya bayan cin abinci. 

Ya hayo gadon tare da janyo Mimi jikinsa ya saki ajiyar zuciya, cikin zaquwa ya fara cire mata kayan jikinta,  lamarin da yayi matuqar tsoratata domin Sam babu nitsuwa a tattare da abunda Badarun keyi,  lokacin da yazo cire mata riga ne ta riqe riga qam ta hanashi cirewa, yayi yunqure kwacewa ta qara riqewa gam,  hakan yasa yayi amfani da qarfinsa wajen rabata da rigar, tuni ta sakar masa ganin yana shirin yaga  atamfar super wax mallakar kamfanin Sheraton ( Sheraton super wax).

A haukace yake tsotsar qirjinta duk ya rude,  ya kuma rudata,  kuka take me hade da ihu 😭 , Jin yadda yake matsa mata nono ba tare da tausayi ba kamar ba jikin me rai yake latsawa ba. Ya cire hannunsa ya shinfideta a kan gadon sannan ya xare wandon jikinsa,  ita kam ya dade da rabata da nata kayan,  ya rankwafo kanta da nufin hada bakinsa da nata,  tai saurin kauda kanta, domin a tunaninta ai sai da soyayya akeyin kiss,  ita kuma batason Badaru kuma tayi alqawarin bazai taba shan bakinta na,  kuma bayan haka ma ai Badaru bashi da tsaftar da xata hada baki dashi,  ita kuma macece me tsaftar gaske,  yanxun hakama daya kifu a kanta qarnin gumi yake alamar tun rana rabon jikinsa da ganin ruwa (wanka). 


Sucking din nononta yake tun qarfinsa kamar me shirin xugo ruwa,  radadin da takeji ya zarce faduwa da baki.  Ana cikin hakan ne taji ya danna yatsansa a matancinta,  ta kwallah wani irin ihu tare da miqewa zaune a kan gadon ba tare da tasan tayi hakanba. Xuwa wannan lokaci shikam ya zaqu wajen San cimma burinsa,  ya kalleta cikin fita hayyaci yace "ke meye haka?  Dare na fa kike ihu maqota xasu iya jiwo ki,  hanya nake nema shiyasa,  in kuma kinsan gurin nunamun."  ya qara janyota ya kwantar tana ihu tana bashi haquri da cewa "Dan Allah Badaru kayi haquri na dena,  na tuba da xafi Dan darajar iyayenka."


Yayi murmushin mugunta yace "ba kince bakya sona na ba?  nima ance miki ina sonki ne?  Kinga wannan abun da nake miki shine dalilin aure na dake,  domin MARYAM tun randa na fara ganinki Allah ya jarrabeni da muguwar sha 'awarki,  wlh ko yarinyar da nakeso kamar raina bana sha'awarta kamar ke, tundaga ranar Kullum na kwanta sai nayi mafarkin ina saduwa dake,  komai na halittar jikinki yayimun, amma fa bawai Love ba,  no Just sha'awa ".  Yana kaiwa nan ya kuma danna hannunsa a gabanta tare da tambayarta nanne?  Gara fa in kinsan gurin ki nunamun dan karna shiga inda ba nanba,  Dan wlh saina sadu dake ayau ko mutuwa zaki ".


Shigewar da gaba daya ta ya tsan hannunsa tayi ya tabbar masa da nanne hanyar kuma a take ya fara qoqarin shigarta iya qarfinsa yana wani irin ihu da sambatun ambaton sunan Nafeesa tare da yiwa Nafeesan wasu alqawura na soyayya,  alamar dake nuna cewa itace a ransa.  Muryar Mimi ta katse masa sambatun da yake. 


Cikin kuka wurjanjan take furta "ka dubi Allah kayimun a hankali wlh ban taba yiba,  kayi haquri xata jimun ciwo 😭" . Kalamanta suka sanyaya masa jiki kwarai, ya shafi gefen fuskarta yace "maryam wlh nasan ke ba mazinaciya bace, domin kedin duk wanda ya kalleki zega alamar kamewa a tare da ke koda maqiyinki ne, sai dai mutum yaqi Allah ya yi miki sharri" 

Yana kaiwa nan yaci gaba da abunda yake,  amma ala tilas ya haqura bayan ya dan samu nutsuwa, saboda ya gane baxai taba iya kauda budurcin Mimi a dare daya ba, saboda tana cikin jerin mata masu qaramar halitta, sannan masu kwarin tantanin budurci.  


Bacci kona 1 minute Mimi bata samuba a daren saboda a tsorace take ga ciwon jiki,  ga muguwar yunwar take addabarta,  wacce ta haifar mata da tsananin ciwon kai.


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 1⃣8⃣

Dedicated to 
Maryam Baita


   Har garin Allah ya waye bata rintsaba saboda axabar ciwon kai,  ta kalli agogon dakin dai dai lokacin 7:45am. Amma ta kasa tashi tayi wanka tai sallah.

Shikam Badaru kiran farko ya miqe yaje ya tsarkake jikinsa yayi nafilfili tana kallonsa, har akai kiran assalatu yayi sallah yaci gaba da karatun qur ani,  da taga bashi da niyyar taimaka matane tace " Dan Allah taimakamun intashi lokacin sallah yana qurewa". 

Ya kalleta shagarai "wai nufinki dan wannan abun da ya faru shine ya hanaki tashi? 😏 lallai ke muguwar yar rainin hankalice,  sai ki tanadi ambulance ranar da mai gaba dayan zai kasance,  tashi kuma karki tashi ai da kindamu dayin sallah akan lokaci da baki tsaya langwai ba,  hakan ya nuna ko acan gidan iyayenki haka kike wasarere da harkar addini abunda kuma bazan dauka ba kenan,  dan ni natsani mutum din dabe damu da addini ba"


Ta runtse ido kalamansa sunfi abunda yayi mata daren jiya muni a gareta, domin ita mutum ce me tsananin kiyaye lokutan sallah,  yan gidansu har cewa suke mata "mayyar sallah" amma rayuwa yau ita ake qalubalanta akan sallah. 


Tana kaiwa nan a tunaninta ta qara kallon agogo a karo na biyu 8:03 agogon ya nuna,  tai wani irin nishi cike da qarfin hali ta yunqura ta miqe,  ta wuce ta gabansa tanajan qafa saboda axaba,  taje kitchen ta kunna gas ta tari ruwa famfon kitchen ta cika tukunya ta dora.


Tananan tsugune a qofar kitchen din ruwan ya fara shuuuu alamun ya kusa tafasa taje toilet ta dakko bokiti ta juye ta daga dakyar ta kai toilet,  naya kallonta dan rashin tausayi ko ajikinsa. 


Bayan tayi wankan zarki dana sabulu ta xuba ragowar ruwan zafin a baho tasa gishiri ta shiga ciki ta zauna dakyar.

Koda ta fito daga wanka ta sameshi xaune yana shan tea da bread din daya shigo dashi jiya,  kuma ga dukkan alamu iya cikinsa ya dafa ruwan tea din banda ita. 


Tuni Badaru ya fita,  ita kuwa tunda ta idar da sallah tana kan daddumar a zaune saboda kabaitar da ita da yunwa tayi ga wani mugun amai da yake taso mata.


Ta rarrafa da dakko wayarta dake kan bed side,  ta kira yaya Faty,  bugu daya ta dauka,  "bazaku zo bane yaya Faty"?  Shine maganar da Mimi ta fara fada bayan Faty ta daga wayar.

Ta danyi jum,  cikin dauri ta danne kukan dake shirin taso mata,  sannan tace "kinga Mimi na tashine da ciwon kai,  ko sallah ma a zaune nayi,  bazan samu xuwa ba sai kin dan kwana biyu,  ya mijin naki kun tashi lfy?. 


Duk da Mimi tasan cewa abunda ya Faty ta fada ba haka bane,  saboda ta fuskanci yaya Faty batasan xuwa gidan Sam dan jiya ma batazo kawota ba,  kuma tasan tausayinta da Faty keji shi ya haifar da haka. Ta daure tace "ayyah sannu sister Allah ya baki lfy,  agaida ya Ahmad. 

Bata qara gigin kiran wani ba,  duk da tasan a al adar gidansu washegarin biki sai sun hadu duk yan gidan anje gidan amarya,  amma ga dukkan alamu ita bata Sami hakan ba tunda gashi har goma tayi amma ko kare baixo wajenta ba. 


Tananan zaune cikin ciwon kai da yunwa wanda tun qarfi suke shirin tayar mata da ciwonta na sarqewar numfashi,  tunani take irin rayuwar auren tada ke shirin faruwa a kanta,  ita dai tasha ji a fili da kuma littattafan soyayya yacce namiji ke tattalin mace a daren farko da kuma washe garin ranar musamman inya sameta virgin,  amma ita sai yunqurin fyade da Badaru yayi mata (to fyade mana tunda bataso kuma bebi a hankali ba) duk da yasani kuma ya tabbatar da cewa ita din virgin dince. Sai kuma dan karen wulaqanci da tasha yau da safe ta hanayar yin halin ko in kula da ita.  Afili ta furta "ALLAH KAINE KA JARRABENI,  KUMA KASAN XAN IYA SHIYASA KA JARRABENI DAN KA GWADA IMANINA,  ALLAH KA BANI IKON CIN JARRABAWA,  KA BANI IKON BIYAYYA GA MIJINA."


Tananan zaune cikin yunwa da nauyin qirji, amma kuma sam batasan koda hadiyar ruwa balle abinci,  taji ana buga gidan. 

Ta tashi dakyar cikin jiri, ta fita ta bude. Little ta gani wato autar momy yar mama, sunanta na gaskiya MARYAM wato sunansu daya da Mimi, kasan cewar sunan hajja gareta babar su momy Lima itace auta a gidan momy shiyasa ake ce mata little (wato  qarama),  yarinyace da bazata gaza shekaru 13 ba,  doguwa fara sol siririya kamar ka harareta ta karye saboda siranta kyakykyawa irin kyan su yaya Faty tunda dama tafi kama da yayan momy.  


Little akwai kafirin iyayi da son nuna iyawa saboda rayuwar da ta taso ciki kasancewarta auta yasa aka sakar mata take sangarta son ranta ga kuma gatan yayye dana iyaye. 


Tsaye take a qofar gidan alamar itace da buga qofar sanye take cikin riga da skirt yan kanti (kamar yadda yake ga dabiarta bata cikasa natives ba indai ba biki ba) kanta ba dankwali sai siririn gyale datai yane kanta dashi, fuskar nan tasha make up ga kuma wani qaton glass data kwama wanda ya shafe rabin fuskarta. Daga can bayanta kuma Huxaifa ne (Dan gidan Baffa)  ke gyara parking din mota da alama shiya kawo Little din. 


Mimi farin ciki ya rufe ta daka tsalle ta rungume Little din kamar ta shekara bata ga na gida ba haka takeji,  tace "autar momy kece 😊" ku shigo ciki Huxaifa,  

Little tace " name sake kamar yadda take kiran Mimi ko kuma tace mata ya Mimi,  wlh mama ce ta tasoni,  wai duk wanda tace yaxo ta aiko shi sai ya zame, waisu tausayinki sukeji,  shine suka hadu ita da momy suka tattgoni " 


Ta kalli gidan ta yatsine fuska sannan ta dora da cewa " nima fa name sake da nasan haka zanxo in tadda gidannan bazanzo ba,  no wonder kowa yaqi xuwa, tai tsaki,  ta dora da cewa duk yanda ake fadar munin gidannan banxaci abun yakai haka ba,  gida sai kace xuciyar kafiri, gaskiya guy dinnan ya kwafsa mana " 


Dai dai nan Huxaifa ya shigo da kaya niqi niqi,  ya ajiye ya fita yace bari in jiraki a waje Little,  Mimi tayi tayi ya zauna yaqi ko saboda qanqantar parlon ne oho. 


Mimi ta fara fito da kayan daja ajiye tana gani, yawanci kayanta ne na amfanin yau da kullum, kamarsu system da chajar waya sai kuma pos 👛 dinta, wacce ke qunshe dasu ATM dinta da I D cards. 


Little ta matso tana bude ragowar kayan data shigo dasu yanxu tana cigaba da mita " ai wlh wannan anguwar kwata kwata batai ba duk ba Local champions ne a unguwar muna kawo kai naga ana kiwon shanu da raquma sai kace a ruga "

Mimi tai murmushi tare da cewa to ya za ai Little kowa da qaddararsa a rayuwa kuma mutum baya kaucewa qaddararsa ni tawa qadddarar kenan 😊.

Ta fito da leda da wani ruwa a ciki me sanyi tace wai gashi Maltina ce da madara mama ta hada miki tace ki shanye yanxu, Mimi tai tsai tana jinjina soyayyar uwa ga danta, wato tasan tana cikin yunwa sannan kuma dan tsabar soyayy sai data hada mata, sannan ta bayar a kawo mata lallai agaida uwa (Allah ya sakawa uwa da gidan aljannah).  


Atake kuwa ta bula ta shanye,  wani sanyi yana ratsata ta balli maganinta da aka hado mata dashi yanxu cikin kaya ta hadiya saboda nauyin da qirjin ke mata. Little taci gaba da nuna mata kayayyakin ta miqo mata miya cikin tukunya da taji naman kaji ta soyu tai shar sai qamshi take tace gashi inji momy,  sannan qanqara guru guru ta pure wata cikin leda tace wannan kuma inji mama ga kuma soyayyan naman shanu cikin bokitin roba inji yaya Faty. 


Haka dai abun alheri niqi niqi ta dunga kukan murna da jinjina soyayyar uwa da dangin uwa akan dá. 


Nan da nan kuwa taji kwarin jikinta ta tashi Little ta tayata suka gyara gidan ta bawa Huxaifa kudi acikin wanda mama ta kawo mata ta riqe a hannunta ya siyo mata ruwan pure wata leda daya da maltina rabin dozin ta xuba a cooler ta fasa qanqara akai,  sabida gidan fridge be samu shiga ba.  



Taga kayan abinci a kitchen sai dai kayan miyane babu   hakan yasa ta dafa farar taliya da nufin aci da miyar da momy ta kawo. 

Suka bade gidan da room freshners masu sanyin qamshi,  gidan yayi fes tayi wanka ta canja kaya harda make up dan qarfin hali. 


Koda Little ta tashi tafiya Mimi ta bude akwatin lefenta ta dakko mata atamfar súper collection me kyau da sabulu da mai,  domin taji dadin xuwansu sosai,  shi kuma Huxaifa ta bashi turare da sabulai,  sannan ta bawa little ragowar kajin da Badaru ya kawo guda biyu tace ta kaiwa mama.

Har mota ta rakasu tana ta godia tace da Little sai yaushe autarmu?  Ta daure fuska sannan tace " Allah name sake baxan kuma xuwa ba saboda daga gidan har me gidan basuyimun ba,  wlh kinfi qarfin auran wannan bagidajen kawai dai akwai abunda Allah yake nufi da hakan" 

Huxaifa ya jinjina kai cikin mamakin qarfin hali Iron na Little, sannan yayi saurin katseta da cewa "ya isa uwar iyayi in banda shirmenki mutum yana auran matar da ba tasa ba"?

Sukaja Mota suka tafi suna dagawa juna hannu. 





Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 1⃣9⃣

Dedicated to 
Maryam Baita


Tafiyarsu bada jimawa ba akai kiran sallar zuhr,  bayan tayi sallah tana zaune kan kujera so take tadan runtsa ko tasami saukin ciwon kai,  amma abun ya gagara sai tunani take. 

A irin hakan ta tunano rayuwarta acan baya.  Akwai wani lokaci da AL AMARINTA ya damu mama har ta dau shawarar wata qawarta yar gurin aikinsu wacce suke kira da Anty saude.

Anty saude ta dade tana fadawa mama ta nemi taimakon malamai akan LAMARIN Mimi amma maman tanayin burus da zancen, sai dai a lokacin da matsin lambar Baffa Yayi qamari akan Mimi dole tasa mama amsa gayyatar Anty saude. 

Anty saude ta tasa Mimi gaba babu san ranta ko kadan dandai mama ta dage ne,  sukaje gidan wani malami acan wajen kurna babban layi.

Duk da bayanin da Anty saude taiwa malamin akan matsalar Mimi sai da ya buqaci Mimi ta qara yi masa bayani da kanta,  wanda hakan yasa Mimi kuka domin batasan abunda zatace masa ba.  Cewa xatai ta kasa daukan qaddarar da Allah ya dora ko yaya?  Ko cewa xatai ya jawo mata mijin aure koda lokacinta beyi ba?. Sam ita batasan bin malamai. 


Ganin Mimi na kuka yasa ya haqura dajin lamarin daga bakinta sannan ya dora da yimata tambayoyi kamarsu : kina mafarki ana saduwa dake?  Tace gyada kai,  alamar eh.  Kina jin bacin rai haka kawai?  Tace eh. Kina tsanin ciwon mara lokacin al ada?  Tace eh. 

Ya kalli anty saude yace da alama baqin aljani ya auri yarinyar nan,  kuma indai ba a rabata dashiba to wlh ita da aure har abada.

Mimi ta tsorata dajin cewar wai itadin aljani ya aureta. 

Ya basu turaren hayaqi ya fada musu yanda xatai amfani dashi,  Anty saude ta bashi sadaka yace "a a dauki aimu sai buqata ta biya ake biyanmu."

Koda suka dawo ta mayarwa da mama yacce akai tabata turaren daya bata,  mama tasata gaba tayi saida tayi duk turaren. 


Kafin wa adin daya dibar musu na komawa gurinsa yayi,  cikin ikon Allah Mimi ta sami saukin mafarkan da take yawanyi har ta fadawa mama ta dunga murna da cewa " Allah ya sa qarshen baqin cikinmu kenan,  dama saude ta dade tanamun tayin neman taimako ina sharewa ashe akwai waraka aciki "

Ranar komawarsu gurin Anty saude bata samu xuwa ba saboda wani uxuri da yazo mata,  Mimi ita kadai taje gidan. 

Tai sa ar samunsa shi kadai acikin dakinsa da yake sallamar baqi, ta fada masa irin nasarar data samu akan maganin, yace yau ina maman taki?   Tace taje asibiti gurin me haihuwa. 

Yawwa dama nasarar aikin mukeso mu fara gani tunda yanxu anyi nasara akan wannan sai mutafi mataki na gaba.  Ya kalleta sannan ya dan rage murya "kinsan tunda aljanin ya ruga ya sadu dake dole sai anyi miki wani dan gajeren aiki,  wato sai an tsarkake gabanki saboda shafar da aljani yayi miki,  sanyi rubutu a gabana sai in dan shigeki  da nufin haramtawa aljanin qara kusantarki anan gaba." 

Yana kaiwa nan ya matso kusa da ita da nufin tabata tai wufff ta miqe tsaye ta nufi qofar fita yayi saurin riqota da cewa ke taimakonki xanyi,  inkuma bakiso shikenan ki biyani kudin aikin da nayi miki rannan.  Kafin ya qarasa tai masa wata muguwar kutufo wanda ita kanta batasan ta iyaba, sai yanxu da taga ana shirin keta mata haddi.  Nan take kuwa sai gashi a qasa wanwar.  Sannan ta dora da cewa "in abunda kai nufin yimun alkhairine Allah ya saka maka da alkhairi in kuma sharrine Allah ya kawo me kwatantashi akan yar cikinka" sannan ta bude jaka ta watsa masa kudi,  tace ga ladan aikinka nan, domin ni banacin haqqin mutum. 


A burkice ta shiga gida, saboda har yanxu tsoron abunda akai mata bai bartaba idonta jawur,  umma take tsakar gidan tace "lfy Mimi?  Naganki wata iri ko hatsari kikai " ko ta kanta batabi ba ta shige dakin mama. 

Har bedroom din maman ta isketa cikin kuka ta fara magana " mama meyasa bazaki dau qaddarar Allah akaina ba?  Shin na dameki da yawon bin mazane shiyasa kika damu nai aure?  Bakya ganin takurawarmu ga lamarina ba shishshigine ga Allah ba?  Indan Allah ya kyalemu da kanmu xamuji dadi?  Akwai wanda xai mana abu ba Allah ba? Wlh tun farko banso xuwa gurinnan ba Allah ya gani kece kika takura. Wlh!  Wlh!!  Wlh!!!  Da inbawa malamin tsibbu jikina da nufin zaimun aikin da zan samu miji gara nayi ta xama ba miji har abada , domin nasan Allah baya mantuwa kuma bai manta daniba "

Jikin mama na rawa,  cikin razana ta kamo mimin sannan ta zaunar da ita kusa da ita tace " meya faru mamana?  Kinsani a duhu waye yayi yunqurin keta miki mutunci? "

Ta mayarwa da mama yadda sukai da malamin,  mama ta tsorota da lalacewar zamani,  ta yadda malami zai nemi mace dan kawai taje neman taimako,  sannan ta godewa Allah daya bata nutsatstsiyar ya.  Tace yi haquri Mimi bansan haka lamarin yakeba wlh da bazan soma ba.  Da haka aka rufe chapter neman taimakon malamai akan LAMARIN MARYAM. 


Badaru bai dawo gidanba sai magariba,  gidan yayi baqiqirin saboda rashin wutar Nepa kuma duk fitilolin babu chaji.  Ga xafi kasancewar ana tsaka da xafi,  ya qudure dole ya samo injin generator koda qaramine saboda bayason zafi.


Yayi amfani da fitilar wayarsa wajen haska parlon ya ganta a xaune akan pray mat alamar sallah tayi. 

Tayi masa sannu da xuwa, ya amsa direct ya wuce kitchen ya xubo abinci a tray (ina ruwan khadimul ci,  bama a plate ba 🤣) taliyar da ya xubo xatai guda daya, lafto miyar kafin dama kajin, ya faraci ba tare da tambayar inda ta samu kayan miyan da tayi girkin ba ganin cewa baibata ko asi ba kuma bai kawo kayan miya ba. 

Tayi mamaki da taga ya cinye Raliya tas ya dora da gwangwanin maltina, kamar shi ya siya.  Yayi gyatsa. Sunanan zaune ita tana jan carbi shi kuma na danna waya aka kira isha ya tashi ya tafi masallaci. 

Bayan idar da shafa'i  da wuturi ta je kitchen ta debo red meat din da aka kawo mata dazu soyayye ta zauna taci tasha maltina,  sannan taje tayi wanka da brush ta gyara jikinta da turarurka masu sanyi ta sanya riga da wandon bacci cotton,  ta fito parlo ta xauna tana charting duk kuwa da cewa babu chaji a wayar,  jira kawai take abunda taci ya fada taje ta kwanta dan bacci takeji. 

Yau dai ansamu cigaba domin Badaru yayi wanka bayan dawowar daga masallaci, brush ne dai beyiba alamar be saba yiba. 


Beyi mata magana ba, kawai dai yazo yaja hannunta kamar tunkiya ya shiga da ita bedroom din ya cillata akan gado tare da cewa " gara mu fara da wuri mu gama don yau bacci nakeji" babu xancen wani romance a cikin tsarinsa kawai dai ya hau wasa da qirjinta da kuma tsotsa kamar tababbe,  tun tana daurewa har ta gaza ta fara yunqurin ture kansa daga jikin nipple dinta, lamarin da yasa ya gartsa mata cixo a nipple din,  ta kwalla qara.  Ya fara yunqurin cinma burinsa, amma sai dai yauma kamar jiya ya kasa duk iya nacinsa dole ya haqura domin shima ya fara jiwa kansa rauni.

Ya kwanta cike da baqin cikin kasa cimma burinsa,  sannan na kukan da Mimi ke masa,  a xuciyarsa yace kin kusa kiyi me dalili dan wlh gobe gurin Mekudi (abokinsa) xanje ya nemomin maganin qarfin maza. 


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣0⃣

Dedicated to 
Maryam Baita


Washegari bai samu kansaba sai wajen qarfe hudu na yamma,  saboda yaje kasuwa daga can kuma ya wuce ya sayi inji (generator) ya kai gida ya kira masu hadawa suka hada, sannan yayi sallah ya tafi majalisarsu dake unguwarsu unguwar da iyayensa suke.

Ya samu Maikudi yace yawwa wlh kai nake nema tun safe nake kiran wayarka a rufe,  Maikudi yace wlh babu chajine.  Sannan suka kebe daga can qarshen tabarmar dake gurin. Yan gurin sunata zolayarsa da ango meya fito da kai yanxu,  ba mun baka hutu ba. 


Mekudi abokin Badaru ne,  duk da cewa halinsu ba daya ba, domin mekudi irin mazannan mayun mata bashi da aikinyi sai yawan yaudarar yayan mutane duk da cewa yana da mata har yaya biyu,  gashi Dan duniya na qarshe.


Bayan Badaru ya gama fada masa abunda ke faruwa na kasa kauda budurcin Mimi (kuji rashin sanin ciwon kai 😒). Mekudi yace " to kodai tayi cushe cushe nan nasu na mata a wajen?  Kasan hakan nasa irin hakan" 


Badaru yace "banajin hakan,  domin yarinyar bata da rawar kai irinta yan matan yanxu,  bayan haka kuma bata sona banaji zatai wannan abun da nufin burgeni,  nafi dauka dai halittartace hakan.  Yarinya fa yar baiwa ce ya fada yana dariya,  sannan ya dora da cewa ta hadu dan kawai banasonta ne"


Yace to shikenan  yanxu inada wani ragowar magani yana Mota ka hadiya tunda naga amatse kake,  kafin in samo maka wani.  Yawwa mutumina cewar Badaru wlh na matsu inji ya lamarin yake 🙈.


 
Suna tsaye kofar gidan su Nafee,  hira suke,  awanni 3 kenan da shan maganin da Mekudi ya bashi, amma ga dukkan alamu maganin ya fara aiki a jikinsa,  dan ji yake kamar cafko Nafee.


Yace mata "ni bara in tafi Nafee"  ta marairaice tace kace baka santa amma tunda ka aureta inkazo Allah Allah kake ka koma gunta,  me hakan ke nufi? 


Yace "yi haquri yau kam banajin dadi ne,  amma gobe innazo xan dade kinji" yana kaiwa nan ya fice ko takanta be kuma bi ba.

Yana xuwa ya ganta a duhu ga zafi saboda qanqantar gidan,  wayarta babu chaji dan haka take zaune a duhu. 


Yaje ya tada inji, kunna fankar parlon . Ta saki ajiyar xuciya dan zafi ya dameta kuma zafi kan iya tayar da ciwonta. Yaje yayi wanka ya xuba abinci yaci. 


"Zo" yace da ita yana kashingide a jikin kujera, yanajin wani irin feelings.  

Ta marairaice cikin zubar da kwallah tace "Badaru kayi haquri wlh kaina ciwo yake tun renda aka kawoni gidannan" 

Yayi dariyar mugunta yace to aini ba kanki xan taba jikinki kawai nakeso,  saboda haka kixo kafin na tashi nayi miki abunda xakiyi nadama.  

Tai saurin qarasawa inda yake da rarrafe Jin abunda yace, "cire rigarki" ta zaro ido 😳. Haka dai saida yasata tai tik ta hanyar tsoratar da ita. 


Sannan ya buqaci ta tashi tayi tafiya a gabansa a hakan, lamarin da ita kuma taqi yarda duk kuwa da yadda yakai da naci dole ya haqura,  ganin tana bata masa lokaci kuma ga magani na aiki a jikinsa yasa ya huqara ya haye kanta anan kan centre carpet din parlon da kuma fitila akunne (Dan tsabar rashin sanin ciwon kai da rashin kunya). 


Ashe kuwa gaskiyar Badaru da yake cewa ta tanadi ambulance,  domin kuwa bata tabajin labarin daren farko me wahala irin nata ba. 


Tun tana yunqurin kwatar kanta harta gaza ta xuba ikon Allah ido,  ta gurxu iya gurxuwa cikin mugunta da wutar ciki ya kauda budurcinta.


Ya dunga kuka wiwi yana sambatun kiran sunanta ( dan rainin wayo ashe kasan sunanta🤔) tare da alqawarin riqeta iya rayuwarsa.


Wannan dare ma bata runtsaba saboda ji take kamar an tsagata da reza an mata tsarki da attaruhu.  Yayin da Badaru yake bacci harda munshari alamar cikar buri,  kuma munsharinsa ya temaka kwarai wajen hanata bacci.


Sai gab da asuba ta samu baccin shedan ya kwasheta (na shedan mana tunda zai hanaka sallar akan lokaci).


Sanyin ruwan daya shafa matane yasa ta farka,  "sannu maryam, kin hadu ni nasan bada banxa na gigice akanki ba,  gaskiya xan huta,  fatana ki koyi dauriya dan naga kedin raguwa ce" kalaman Badaru kenan. Kuma yana gama fadar hakan yasa kai ya fice,  ba tare da la akarin yayi mata tagargazar da xata buqaci temako ba.


Yauma kamar ranar itace ta gyara kanta tayi sallah, ta nade xanin gadon da ya baci da wani abu chakal .kamar jirwaye da kuma ruwan ciwo. Amma babu jini sam. Ta shinfida wani.


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣1⃣

Dedicated to 
Maryam Baita


A hankali rayuwa taci gaba da tafiya, lokuta na gudu tunda gashi Mimi ta samu kimanin wata daya da rabi a gidan miji. 

Ixuwa yanxu yan gidansu kaf babu wacce bataxo mata ba inka dauke Faty,  domin ta kasa xuwa gidan Mimi,  ko meye dalili oho.

Kuma duk wanda yaxo tanajin dadi sosai,  kusan ma ince duk takun saqar da suke da wasu daga cikin yan gidansu xuwansu gidanta ya goge mata komai aranta, duk da cewa in anxo sai anyi habaici da kushe gidanta da kuma jajanta mata irin mijin data samu. 

Fauxa kam xuwanta daya gidan duk kuwa da nacin da Mimi ke damunta dashi a waya na rashin xuwanta. Takance "Mimi ni bamai aure ba aga ina yawan xuwa gidanki sai ace naqi zaman aure inaso inkashe miki naki "

Dake ita din ba gwanar qawaye bace,  sannan kuma mafi yawan qawayen basusan tayi aure ba,  sai ya xamana babu wata qawa inka dauke fauxa da taxo gidanta.  Lamarin da yayiwa Badaru dadi,  domin shi a tunaninsa qawaye na iyasa Mimi tayi masa bore kan axabar da yake mata. 


A fannin kwanciyar aure dai Mimi ta kasa sabawa da salon Badaru,  domin ita dai ixuwa wannan lokaci Kullum abun sabo yake gareta.  Mekudi ya riga ya bata Badaru da shan maganin qarfin maza, kawai dan aganawa yar mutane azaba.


Saboda da haka Kullum Badaru cikin buqata yake,  baya duba cewa ita din abun Sam be qarbeta ba duba da yanda take jigata aduk sanda ya kusanceta,  wataran ma har rasa numfashi take na wucin gadi (ciwonta). 


 Yau laraba,  kuma tun 7:30  Badaru ya fita a cewarsa akwai wadanda zasuzo siyan kaya shagonsa a kasuwa zaije ya sallamesu.


Bai dawo gidan ba sai yanxu,  11:45 am, ya datta Mimi duke a qofar kitchen tana shirya kayan wanke2 da tayi. Tana cemasa sannu da xuwa bebi takanta ba,  kawai hannunta ya kama kiiiii yayi daki da ita.


Yana xuwa ya axata kan gado ya cire wandonsa,  yana me cewa "kinga abunda ya dawo dani,  wata nagani yanxu a kasuwa shedan ya qawatamun ita shine na dawo insamu nutsuwa"


Yana fadar haka ya farmata ya fara yunqurin shigarta,  babu batun romance a salon kwanciyar Badaru sam,  yanayin kwanciyarsa dai tafi kama da kwanciyar da manxon Allah (s w a)  ya siffata masu yinta da dabbobi,  wadan da suke farwa mace batare da tayar mata da tata sha'awar ba.


Sai da ya biyawa kansa buqata,  sannan ya lura da pink din janbakin data fente bakinta dashi,  ya bashi sha'awa kwarai,  dan haka ya nufi bakinta da nufin kissing dinta, tai saurin kauda kanta. 


Ya tsaya,  yana qare mata kallo da Jin haushin ta hanashi tsotsarta yace " wai ke kina nufin bazan sha bakinki ba?  Inafa lura dake duk sanda nazo shan bakinki sai ki kauda kanki,  sai kiyi tayi kinwa kanki,  tunda nasamu abunda yafi baki ajikinki kuma ina yanda naso dashi ai shikenan"


Bayan yayi shirin fita ya sameta akan gadon har yanxu bata gama wartsakewa ba da dirxar da yayi mata,  yace " ni xan fita inason inbiya gidane in duba Abba yau be fita kasuwa ba wai kansa ke ciwo"  tace to  Allah ya sawaqe,  kai mai sannu. 


Sannan tace " Dan Allah ka siyo wake so nake inyi wake da shinkafa" sai da yakai qofar fita sannan ya cillo mata 30 naira yace gashinan ki sayi waken,  yasa kai ya fice.


Tai tsam tana tunani,  naira talatin ai ko wake gwangwani daya baxata sai mata ba duba da yacce rayuwa tai tsada yanxu. 

Tunda aka kawota gidan Badaru bai taba daukan ko naira biyar ya bata ba,  da sunan kudin cefane ko kudin wani abun daban.  Duk da cewa baya kawo kayan miya ko nama,  tunda ya aciye abinci da maggi me star sai jarkar mai kings sai gishiri be kuma kawo komai ba. 


Tunda miyar da momy ta kawo mata ta qare,  bata qara sa kayan miya a idonta ba, sai da ta gaji dan kanta da cin abinci da mai da yaji (duk da cewa ada tana marmarin mai da yaji,  lokacin tana cikin gata) taga cewa kanta take cuta tundashi bai cika cin abincin rana a gidan ba,  na dare ma inyaga bai masa ba sai ya fita wajen mai shayi a hada masa da kwai,  ko ya siyo tsire iya cikinsa yaci a gabanta babu tayi,  duk da ko yayi mata tayinma baci take ba.


Da yake gidan amarya baya rabo da yara a hankali yaran unguwar suka fara shiga gidan,  ita kuma tasa hannu bibbiyu ta karbesu bata nuna musu kyama ba,  dan sune yan uwanta yanxu,  cikin shirinta na karbar rayuwa aduk inda tazo mata. 

Wadannan yara su take aika su siyo mata duk abunda take buqata acikin yan kudinta da mama ta bata, wanda little ta kawo mata. Wanda kuma tun daga su maman bata kuma aiko mata da kudiba saboda rashin dan aike.

Amma ta da wata yaxo qarshe akai salary ta saka mata kudi a acctn dinta, kamar yadda suka saba ita da yaya Faty duk wata in sukayi albashi sukan tura mata kudi ta acct dinta,  hakan yasa da wuya ta rasa kudi. Amma yanxu abu 2 yayi mata togaciya daga daukan kudin da suke tura mata. 

Na farko,  ATM dinta da yayi expire wanda dole sai taje ta gyara kafin ta samu hurumin fidda kudi. Na biyu kuma shine takunkumin da Badaru ya qaqaba mata,  domin tun sati 2 da xuwanta gidansa ta tambayi xuwa kitso yace mata baya cikin tsarinsa fitar matarsa daga gidan aure inbada lalura ba,  kuma koda xata fita ma yanaga sai ta shekara a gidansa.  Wannan shine dalilin da yasa ko daxu da yace zashi gida duba Abbansa batace xata bishi ba,  saboda yace wannan shine tsarinsa. 


Da yake ance me dá wawa, saboda jan yayansu da take ajiki yasa be kitson take xuwa har gida tai mata kitson da baya wuce kwana 5 ya tuje saboda Kullum cikin xubawa kai ruwa take da kuma yanayin halittar gashinta, domin kanta shampoo din da tayi da biki ya dade da fita,  kuma bata da wani man shammpoo din da take amfani dashi (mega growth) domin kaf cosmetics din lefenta ba irin wanda take amfani dasu bane,  kuma yawanci anrabar dasu ga dangi (kamar yadda akeyi a al adance).


Kudin hannunta sune kayan miya, siyan salak in buqatar cin salak din ta taso,  sune biyan kudin kitso da kuma siyan sabulun wanki. Domin akan idonta Badaru kan hada wankinsa ya bayar a wanko a gogo masa, amma bai taba hadawa da nata ba.  Gashi ita kuma bata iya wanki ba zata iya cewa tunda take bata taba wanke kayanta na sawa ba,  iyakacin wankinta undis suma a washing machine take watsasu ta wanke.


Duk da cewa Badaru yasan bai taba kawo kayan miya gidansa ba,  hakan baya hana in yaga anyi abinci da miya koma har da nama ya zauna ya take tumbinsa,  kusan ma bayacin abincin gidan sai yaga Cima da canja maana anyi me dadi,  Ko kunya bayaji ko kuma ya tambayi ina akasamu kayan girkin saboda tsabar San banxa (san banxa mesa gidan yari cika 🙄😄). 


Yau da gobe tafi qarfin wasa kuma xara bata barin dami dan haka kudin hannunta bai gaxa 800 ba, dan haka ta tambayeshi ya bada kudin wake (abunda bata taba yiba, wato tambayar Badaru abu koda kuwa haqqinsa ne yayi).  Acikin wannan 800 din data rage mata tanason siyan pad dan lokacinta ya kusa,  ga siyan sabulun wanki ga, ga kudin wankin,  sannan ga kanta ya dameta ya cika ya sarsarqe alamun yana buqatar shampoo, amma da yake hakan bata samuwa dole ta biya kudi a kitse matashi. Gashi tanason siyan wake ta hada a dahuwar shinkafa dan tagaji dacin fara da mai. 


Atake a gurin ta samowa kanta solution,  domin kudin bazasu isheta ba,  saboda haka ta yanke shawarar siyan always (pad) tunda ita dole ce,  kasancewarta mace me xubar da jini a lokacin al ada yasa sinqi daya bata isarta sai daya da rabi ko biyu.   Yanxu da rayuwa taxo mata a haka ta yanke shawarar hadawa da tsumma, ragowar kudin xata sai sabulun wanki tai wankin da kanta tunda ba kudin kai wankau, sannnan ta bada kudin kitso ai mata kitso ragowar kudin ta sai wake ta dafa a shinkafa. 


Rayuwa kenan abar tsoro wai yau maryam ce da wanki. Ahankali ta furta "rayuwa ce wataran sai lbr, dama aure a 2 ne ko kaci gaba ko kaci baya." 

Tana kaiwa nan a tunaninta ta miqe ta fara aiwatar da abunda ta shirya.


Badaru bayan ya isa gidansu ya duba jikin Abbansa,  yana zaune suna dan taba hira da Abban ummansu take gefe sai kallonsa take asace,  saboda kunya irin ta dan fari.  

Can dai ta kalleshi tace ina wajen su maryam din?  Yace ko lfy,  ai canake da ita xakuxo duba alh? 

Yayi saurin cewa tananan qalau tace ma a gaisheshi da jiki,  ni banason gantaline a tsarina banason matata ta fita. 


To sannu me mata hakan yayi dai dai mara kunya inji Umma.  Sannan ta dora da cewa " ai wannan yarinya Allah ya saka mata da alkhairi,  ta gyaraka kayi tas kayi jajur da kai har wata teba ka ajiye.  Wannan yarinya ta samu tarbiyyar Allah ya sakawa iyayenta da alkhairi" ta kalli abbansu Badarun sannan tace "wlh Alh tunda mukaje yarinyar nan take hidima damu ta kawo wannan ta kawo wancan,  sannan ta samu hijabi ta saka a jikinta har muka taho bata cire ba,  muna kan kujera tana qasa idanunta a qasa. Aini Alh banzaci acikin yaran yanxu masu xurfin karatun boko akwai irin maryam ba,  haka in su Aisha (yayanta mata) sukaje mata take hidima dasu da yayansu inzasu taho,  tabawa wannan mayafi wannan takalmi kai gashinan dai abun sai San barka"


Alh inuwa ya dubeta yayi murmushi sannan yace lallai kaltume wannan suruka taki tayi miki 😊 dan naga kullum in muka zauna sai kinyi bitar ahalayenta. 

Tai saurin cafewa da cewa wlh kam tayimun,  ai maryama ta haifu yarinyar yar halak ce,  ni da Xaiji shawara ma ai daya haqura da Nafeesan yayi xamansa da wannan dan ni kam maryam tafi kwantamun.


Badaru yaji maganar kamar saukar aradu ya dago a razane 😳, yace Umma in haqura fa kikace?  Shekara nawa Nafee na jirana?  Innaqi auranta na yaudareta,  Kuma bayan haka ma ina sonta baxan iya haqura da itaba. 


Umman ta watsa masa harara tare da cewa "ai tare aka hallicceku shiyasa bazaka iya haquri ba"


Abba yayi saurin katsesu kafin maganar tayi nisa yace "ya isa kaltume,  ki gyaleshi tunda yana sonta.  Maryam din ma da za a aurota ai saida kika nuna turjiya,  amma yanxu kinfi kowa yaban halinta.  Itama wannan kikasan nata kyawun halin?" 

Umma dai ta tabe baki tare da cewa Allah ya bada sa a 😏



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣2⃣

Dedicated to 
Maryam Baita


Watanta biyu dai-dai a gidan, xuwa wannan lokaci ta saba da wahala,  duk cewa ance ba'a sabo da wuya.


A bangare guda kuma tana cikin matsananciyar wahalar  auratayya da Badaru. Irin yanda duk wata amarya da takai budurcinta gidan miji ke fuskanta a farkon aure. Ta wahala iya wahala saboda kwanciyar aure da Badaru tafi komai jigatar da Mimi.


Ga wani irin ciwon qirji da yake yawan fyadeta,  saboda bacin rai da rashin cima mai dadi (mai da yaji). Tuni maganinta na numfashi ya qare,  kuma tun kafin maganin ya qare intasha baya yimata aiki.  Ga uwa uba zafi dakesa koda yaushe cikin daukewar numfashi take,  saboda Sam yanayin ciwonta bayason zafi. Badaru kuma baya tada inji saiya dawo kuma duk inda 11 tai zai kashe yayi baccinsa inda ita kuma xata kwana fiffita da hand fan dan kiyaye lfy ta.


Babban abunda yafi damunta kuma shine; duk wannan hali da take ciki baisa Badaru ya tausaya mata yace taje asibiti ba, ko ya kaita.  Hasali ma haka yake shafe tsawon lokaci yana auratayya da ita cikin shauqi da sambatu.  Baya gajiya da abu daya wani lokacin sai yaga bata numfashi sannan yake saurara mata.


Bacin rai,  yunwa,  zafi da rashin kwanciyar hankali ya hadu ya saukar mata da wani irin matsanancin ciwon qirji. Wanda ya kwantar da ita wanwar ko sallah sai dai tayi zaune,  aikin gida kuma in su abuwa (yaran maqota dake shigo mata) sunxo suke yimata,  babban abin takaicin shine bata da ko naira 5 din siyan ruwan pure water.  Wayarta ma kona plashing babu. 


Yau monday,  wanda ta kama kwananta 3 da kwanciya wanwar saboda nauyin qirji da daukewar numfashi.  Ya xamana ko kwanciyar ta gagara sai dai tai ruf da ciki ta danne qirjinta saboda ji take kamar inbata danne dinba zai tarwatse. Daga waje kuwa kana iya jiyo hakin da take.


A haka Badaru yazo cikin shirin fita, yana balle botiran rigarsa, ya kalleta a wulaqance tana kwance ruf da ciki a kan centre carpet din parlon yace 'bakisan wannan kwanciyar babu kyau ba a musulunce?' sannan ya dora "nifa banason langwai kin cika gida da gurnani sai kace tsohuwar kafura wai ke ciwo ko?  To wlh wannan ciwon da kike rashin dogaro da Allah ya kawo miki shi"  (kunji jahili 😒). Yana ida fadar haka ya sa kai ya fice dan tsabar rashin tausayi da tsaurin xuciya.


Ta share hawayenta, aranta tana ayyana ko maqiyinta bazata so Allah ya jarrabeshi da qaddarar abokin zama me taurin zuciya irin Badaru ba.  Kansa kawai ya sani gashi da manmaqo da masifar rowa.


Tananan kwance har yamma,  xuwa lokacin ta ida jigata.  Sai dai in lokacin sallah yayi takan samu sauqi a dabi ance,  saboda tasa sallar aranta.  


Bayan idar da sallah ta jawo wayarta cikin qarfin hali da jan numfashi dakyar. Tana tunanin wanda xata kira,  shin mama xata kira ta fada bata da lfy,  ta daga mata hankali?  Ko yaya Faty data watsar da ita ta nuna batayinta xata kira? (duk kuwa da cewa Faty na kiranta a waya itace bata dauka saboda ta gaji da jin uxurin Faty akan rashin xuwanta gidanta, kawai ta dauki Faty a matsayin wacce bata santa a yanxu)  dole dai mama da Faty sune dolenta (ranar naka sai naka) 


Yaya Ahmad mijin Faty yayi saurin fado mata ta jawo wayarta tai masa pls call me,  kafin ta aje wayar ya kirata. 


Ta dauka "assalamu alaikum ya Ahmad " ya amsa sallamar "mimina kina lfy?  Ya naji muryarki haka? " ya fada agigice.  "bani da lfy ne shine nace dan Allah ko zaka taimakamun kaiwa Badaru magana ya kaini asibiti" ta fada a wahale.  "subhanallah sannu Mimi bari muga ya za ai?   Sannu autarmu" da haka ya kashe wayar.  


Ya tashi ya shiga bedroom gurin Faty dake zaune (yau aikin safe tayi shiyasa take gida a wannan lokacin) ya kalleta tare da cewa "fadima meyasa bakyajin maganata ne?  Inashan fada miki kece babba karkiyi abunda zai bata xumuncinku da Mimi,  na fada miki mama har fushi tayi dake akan rashin zuwa kiga halin da Mimi ke ciki,  amma duk kinqi ji ko?  To yanxu Mimi ta kirani bata da lfy kuma ga dukkan alamu tanajin jiki,  babban abun takaicin shine: mijinta yaqi kaita asibiti,  daya takaicin shine;  ko zancenki batai ba a wayar, wanda hakan ke nuna cewa ta watsar dake kamar yadda kikai mata" yana kaiwa nan a maganarsa yasa kai ya fita. 



Tunda ya furta Mimi babu lfy  kuma ta kirashi a waya,  Faty take a fingice. Ta tashi tabi bayan Ahmad da gudu ta fada jikinsa ta baya ta rumgumeshi tare da sakin kuka "yaya kace Mimi bata tambayeni ba?  Kace Mimi bata da lfy?  Yaya wlh tausayin Mimi da halin da xan ganta ciki ya hanani xuwa gurinta, bawai bijerewa umarninka dana mama ba. Yaya banason mijin Mimi tunda Mimi bata sonsa" ya dagota ya juyo da ita yana share mata hawaye,  yace "my luv, bata wannan hanyar xaki nuna tausayin Mimi ba,  neman kusanci da ita da maganta mata matsalarta da kwantar mata da hankali shine hanyar tausayinki da soyayyarki gareta" tace naji kuma xanyi yadda kace "  duk a rude take wannan magana. 


Ta shiga daki ta dakko mayafinta da key din mota ta fito,  ya kalleta ina zaki?  "Gidan Mimi " ta bashi amsa direct.  Yace a a bari insa ta turo no mijin nata infara yi masa magana tukun.  Tai rau -rau  tace 'yaya Mimi babu lfy kace in tsaya injira ayiwa wannan wawan waya?  Mimita cefa ba lfy?  Ka bari inje xanyi duk abunda ya dace" yace "to my luv sai kin dawo kibi komai a hankali karki abunda xaki xubar da mutuncinki a gurinsa,  kuma matarsa ce ya fimu iko akanta"  ta gyada kai tare da ficewa. 



Lokacin da ta isa gidan Mimi yamma tayi sosai,  domin har Badaru ya dawo. Ta dunga kwada sallama Mimi na parlo a kwance tana jinta tai mata shiru,  yayin da Badaru dake cikin bedroom yaji sallmar kuma yaji Mimi bata amsa ba ya fito.  Lokacin Faty ta gaji da jiran a amsa mata sallama har ta shigo parlon,  Mimi kuwa tanajin ta shigo ta juya baya tabar kallon qofa,  ta fuskanci kujerar parlon.  Badaru yana tsaye yana ganin ikon Allah,  shidai yasan Faty yar uwar Mimi ce,  kuma a dan iya xamansu da Mimi bai taba ganin tayiwa wani haka ba koda kuwa batasanshi ba,  balle Faty yar uwarta. 


Faty bata kula da wanxuwar Badaru ba dake kofar bedroom riqe da cotton (labule) ba, saboda gigitar halin ko in kula da Faty tai akanta. 


Jikinta a sanyaye tasa gwiwarta kan centre carpet din dake parlon ta marairaice tace "Mimi na tuba,  karkiyimun hukunci irin wannan,  bazan iya jure rashinki gareni ba. 



Mimi ba tare da ta juyo ba,  tace "ai tunda kika iya jure 2 month baki ganni ba kuma baki damuba hakan na nuna kin yanke alaqa tsakaninmu,  shiyasa nima na cireki a raina kuma ban nemi taimakonki ba.  Duk mutumin daka rayu tsahon wata biyu babushi wannan sheda ce dake nuna cewa ko babushi xaka iya rayuwa"


Faty ta fashe da kuka "MARYAM karki bari shedan yayi tasiri a xuciyarki,  kinfi kowa sanin cewa duk halin da kike bazan gujeki ba.  Kuma duk tsahon lokacinnan wlh dake nake kwana nake tsahi,  Mimi kinsan dalilin da yasa banxo gurinki ba,  sai dai kiqi gasgata dalilin nawa.  Mimi wallahil azim ko yayan dana haifa banai musu soyayyar da nake miki, saboda duk duniya bani da yar uwa uwa daya uba daya saike" 


Mimi taji wani irin mugun tausayin Faty ya kamata amma ta danne saboda tanason hora Faty akan karta qara yimata haka anan gaba tace "yaya Faty ki tashi kije gidanki,  nasan dake na naimi yaya Ahmad ban nemeki ba kuma da nasan ke zai turo da ban nemi ya taimakamun ba" duk tana wannan maganar ne a juye (ta bawa Faty baya). 


Parlon yayi tsit na tsawon 5 minutes.  Mimi da taji shirun yayi yawa ta juyo a zatonta Faty tayi fushi ta tafi.  Amma me?   Sai tayi arba da Faty tana tsugune tana hawaye. 


Ta qura fatyn ido itama tana hawayen,  ita kuwa Faty ganin yadda Mimi ta lalace ta kade yasa ta qara sautin kukanta cike da nadamar rashin xuwa taga lfyr mimin. 


Cikin kuma Faty tace "#FATIMARYAM# bazasu taba rabuwa ba,  bazasuyi fushi da junansu ba,  matsalar Faty ta Maryam ce,  matsalar maryam ta Faty ce. Mimi wannan shine alwashin mama akanmu,  karki karya alqawarinnan tun yanxu 😪" 



Mimi najin haka ta taho da rarrafe domin babu qarfin tashi,  taje ta rungume Faty.  Faty ma qanqame Mimi tayi kamar xata maidata ciki.


Suka dunga a jiyar xuciya xuciya a tare,  Faty ta dunga sharewa Mimi hawayenta sannan ta kwantar da Mimi a qirjinta kamar yarinya tana shafa kanta alamar lallashi. 


Badaru yana tsaye,  yana kallon dramar su,  kamar masu shirin film.  Aransa yace dama akwai irin wannan soyayyar yan uwantaka?  Lallai yarannan suna san junansu. 


Ya juya da nufin komawa daki,  motsinsa ya sanar dasu wanxuwarsa a gurin,  yayi saurin cewa da Faty "haj Faty barka da xuwa,  ina wuni? " dan haka kawai yaji ta masa kwarjini duk da cewa xai girmeta da kadan ko kuma suyi sa anni. 


Ta kalleshi cikin tsana, sannan ta kalli yar uwarta dake kwance kan cinyarta.  Yayi tas yayi qiba yayin da Mimi ta tsummace da qare kamar me jinyar shekaru da yawa. Ta amsa gaisuwarsa sannan ta dora da cewa " ranka ya dade ya akai akabar Mimi ciwo yaci qarfinta haka?  Ciwon Mimi fa ciwone me hadarin gaske kuma yana da alaqa da xuciya,  duk sanda ciwonta ya tashi inbai samu kulawar gaggawa ba hakan kan iya jawowa arasa rai.  Kuma babbar abunda ke motsa lalurar Mimi bacin rai"


Yayi wuqi wuqi, yana kame kame da bawa Faty haquri.  Tace to gobe da sassafe xanxo in kaita asibiti dan naga abun yayi worst,  xansa ayi mata booking tun yanxu. 


Cikin kunya yace "to Allah ya kaimu,  Allah ya bata lfy kuma za a kiyaye in shaa Allahu"


Ganin magariba ta kawo kai yasa Faty tai nufin tafiya,  ta karanci matsalar Mimi harda yunwa aciki. Sannan ko zafin wannan gidan ya isa ya tashi ciwon Mimi. 


Mimi kamar tabi Faty takeji,  kuma ganin yar uwarta da daidaitawarsu yasa tasamu rangwamen ciwon. Faty ta lallabata da cewa tayi haquri gobe da asuba xataxo kuma,  tayi wanka ta shirya kafin taxo din. 



Fitar Faty befi da minti 15 ba wani yaro ya shigo da leda yace gashi inji wata mata fara a mota tace abawa maryam.  Ta karba ta bude taga freshyoo me sanyi qarara guda uku. 


Atake ta bude ta shanye daya,  sanyin ya ratsata ta kuma bude wani tasha rabi sannan taji ta qoshi.  Tayi hamdala tare da cewa "Allah sarki dan uwa rabin jiki"


Da xumudi ta kwana, saboda tana murna gobe xata fita bayan wata biyu a kulle a gida. 


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣3⃣

Dedicated to 
Maryam Baita

    Asubar fari Faty ta gama shirinta na tafiya, har breakfast ta hadawa Mimi. Taiwa Ahmad sallama ya kawo kudi ya bata da nufin taiwa Mimi amfani dasu a asibiti.


5:30 AM agidan Mimi tai mata,  ta samu Mimi tayi wanka amma tana zaune bakin gado bata shirya ba saboda jikin ya motsa mata.  Suka gaisa da Badaru ta shiga cikin daki.


Haka ta dunga bincika drawern Mimi da nufin dubo mata kayan da zata saka, domin duk kayan sun yamutse (anyi wanki babu guga). Gashi kayan sai qarnin sabulun wanki suke.  Dakyar ta samowa Mimi zani da dankwalin atamfar dutch wax (holland) da shirt (domin rigar atamfar tayi mata yawa saboda ramar da tayi) ta saka. Ta dakko humra ta zazzga ta murxa a jikinta (domin humrar kadai take dashi,  turarurrukanta tuni sun qare,  dan bata saka turare daya tafi gane ta hada kaloli da yawa.  Kuma da Badaru suka hadu suka qarar tunda shikam baya siyan turare ya saka  sai da yaga Mimi dashi ya tayata suka qarar anga banxa 🤣) ta dan gyara fuskarta, ta hade kitson kanta tasa ribbon. Ta yafa mayafi kumar suka fito. 

Suka tadda Badaru a parlour ya dakko 500 ya bawa Mimi tare da cewa "ga wannan ku riqe ko za'a buqaci wani abun" Faty tai saurin cewa "no bashshi babu abunda xai gagara da ixinin Allah" .


Bakwai a AKTH (Aminu kano teaching hospital) tai musu inda Faty ke aiki. koda likita yaxo ita ya fara gani saboda sanayya da kuma booking din da sukai.


Suka gaisa da Faty likitan mai barkwanci,  yana duban Mimi ya duba file dinta dake gabansa yace " fatima kina da wannan African queen din shine baki bani na aura ba? "  Faty tai murmushi tace "Dr babu rabone shiyasa baku taba haduwa ba, amma Mimi ai tana xuwa nan"


Ya duba record din ciwon Mimi,  yace "maryam meyasa kike sa damuwa a ranki?  Bakisan ciwonki bayason damuwa ba? ". Mimi dai shiru tai masa kanta na qasa.


Ya rubuta allura yace Faty taje ta karbo yanxu a pharmacy  ta kawo masa xai mata.  Allurar 9k ce saboda haka ya rubuta note,  dan acikin albashinsa xa a cire. Faty ta dunga yi masa godiyar karamcin da yayi mata,  yace bakomi ai zaman tare ne ya kawo.


Bayan fitarta, nasiha ya dunga yiwa Mimi cikin hikima. Duk cewa baisan matsalarta ba. Suna haka Faty ta dawo,  ya fasa allurar ya nemi jijiyar hannu yayi mata,  sannan ya buqaci ta zauna ta huta xuwa 10 minute saboda allurar nada qarfi.



Cikin qanqanin lokaci,  Mimi taji nauyin da qirjinta yayi ya sauka,  numfashinta ya koma fita normal.  Ta dago ta dubi likitan tace "nagode Allah ya biyaka da gidan aljannah naji dadi". Yayi murmushi yawwa maryam nagode da addu a Allah ya qara sauqi,  suka dauki takardar magunguna suka fita.


Suka tsaya cikin asibitin suka sai magunguna. Sannan Faty ta tsaya ATM ta ciri kudi suka tafi.  Ta miqawa Mimi travelling mug cike da tea murtuk dashi (hadin kauri inji Mal kabiru dadin kowa 😂) tace shanye.  Mimi ba musu ta shanye domin tana ganin shayin yawunta ya tsinke domin rabonta da shayi da madara tun madarar amarci. Bayan ta gama sha ta miqa mata food warmer cike da soyayyar doya da kwai da miyar qoda a gefe. Tace "kici ki qoshi dan ba gida xan 
kaiki ba". Taci doyar ta qoshi nak,  atake wata nutsuwa ta saukar mata.  Lallai ta yarda matsalarta harda yunwa a ciki. 


Direct zoo road ta tsaya inda Mimi keyin saloon,  ta ajeta tace a gyara gashinta a wanke mata qafa, sannan ta tafi tace xataje ta dawo.


Suka taya Mimi ta tsefe kan,  aka shamfe shi,  sannan aka dora da steaming. Akai mata gyaran fuska (cire gashin fuska)  ba abunda bai buqatar gyara,  nan da nan saiga Mimi tayi tar fuskar ta washe. 


Ana wanke mata qafa Faty ta dawo, ana gamawa ta biya kudin suka tafi. Direct shoprite suka nufa,  suka fara da gurin electronics Faty ta sayi reachargable fan (fankan da akewa chaji).  Sannan suka shiga gurin provision tace Mimi ta dau duk abunda take buqata,  dake Mimi tasan ko bata dauka ba Faty fada xatai mata shiyasa tadau duk abunda tasan tana da buqatarsu, kamarsu : mayan robobin madara da milo,  omo,  sugar, pads, toothpaste, cookies da sauran kayan amfanin gida. Faty ta qara mata da wasu kayan shayin irin na sachet da catoon din cake da caton din freshyo da su malt da exotic duk catons.  Ta kalli Faty cikin soyayyar yan uwantaka tace "ya Faty basu yawa ba kuwa?  Karba ki dorawa kanki wahala" ta kalleta tace "Mimi yanxu dan na miki abu ya xama wahala kenan? Yaushe muka fara haka dake? Ta dafa kafadarta tace,  Mimi ina qaunarki mu kadai mama ta haifa,  ina roqon Allah indai xai bani abunda bazan Mora miki ba kada ya bani shi ko menene" Mimi tai saurin fadawa jikin Faty suka qanqame juna. Kudi sosai ta biya na siyayyar da sukai,  sannan suka dau hanya. 


Lokacin da suka isa gidan Faty qarfe biyun rana, adaddafe tayi sallah sabida yunwa dake damunta.  Tana idar da sallah taje kan dining table,  ta cika plate da jellof din macaroni da hadin salad tayi tai qat ta dora da pepper soup.  Duk abunda take Faty na ankare da ita,  tabbas Badaru yana yiwa Mimi horon yunwa domin ada Mimi bata cikin jerin mata masu cin abinci, amma yanxu har mamakin cin da Mimi tayi take. 


Abincin yana fada mata ta nutse akan royal bed din Faty wanda yasha shinfidu tausasa na alfarma, sanyin AC na ratsata tayi bacci me dadin gaske.

Bata farka ba sai 5:16 pm tayi salati,  tare da miqa.  A gaggauce ta shiga bandaki ganin lokacin sallah ya qure.  Sai dai tana cire pant dinta da nufin yin wanka ta tarar period dinta yaxo,  duk kuwa da cewa lokacinta yayi har ya wuce batai ba.  Tai mamakin xuwan period din ba tare da ciwon mara ba,  ko hakan yana nasaba da allurar da akai mata oho? Ta dakko shaving cream (veet) ta shafa a jikinta ta qalqale gashin. Ta salla wankanta da mayukan wanka da subulai, ta dauki sabon pant a drawer ta manna pad ta saka.  Ta gyare jikinta da mayuka da perfumes masu sanyin qamshi, ta dauki doguwar rigar atamfa a kayan Faty ta saka.  Tai mata cif sakamakon ramar da tayi, ta danyi simple make up ta fito tas da ita. 


Ta iske Faty da Ahmad da yaran zaune a parlour suna kallon drama (madhubala) a mbcbollywood.  Tace "ya Faty har lokaci yaja haka baki tasheni ba? Tace "sry Mimi shigata biyu da nufin in tasheki saina tarar baccin ya muki dadi shiyasa na gyaleki.  Ta samu guri kusa da Faty ta zauna,  suka gaisa da Ahmad, ya jajanta mata jikin sannan ya zarce da yi mata nasiha.  Dan har ga Allah yanason Mimi ganinta yake kamar uwa daya uba daya suke, tunda shi bashi da yan uwa.  


Taje fridge ta dakko robar ice cream ta dawo ta xauna tanasha suna hira.  Ji take kamar karta tafi dan xaman yayi mata dadi.  Ahmad ya kalli Faty yace,  tashi ki kaita gida kada muyi rashin hankali.  Faty ta yunqura tare da miqawa Mimi wata leda tace kinga a siyayyar da mukai kin manta baki dauki masuka da turare ba shine na koma na siyo miki" Mimi ta leqa ledar taga muyakan da take amfani dasu ne cocoa butter (palmers)  Set dinsa har sabulunsa sai turaren da take amfani dashi da sure na feshi da sauran spray.  Ta dunga godia.


Sai da Ahmad ya bata 10k,  sannan ya jaddada mata duk sanda take buqatar taimako ta fada,  kada ta qara zama ciwo yaci jikinta haka.  Saida Ahmad ya temaka suka saka kayan a mota saboda kayan da yawa.  Har sun fara tafiya Faty ta tuna da fankar da tasa chaji,  ta dawo ta dauka. Suna tafiya suna hira cikin nishadi ta dauki jakar Mimi ta saka mata ledar magungunan da suka siya tare da kudi sannan ta qara da cewa gashinan ki kula,  ki rabu da namiji ki dainasa baqin cikinsa a ranki, lfy tafi komai kuma shi kansa inbaki da lfy bazai zauna dake ba,  so dat ki lallaba lfyarki.  


Suka tsaya yahuxa suya dake kabuga ta sai mata kaza da furar habib.  Kafin suje gida anyi sallar magruba saboda sun tarar da hold up.  


Suna gama shiga da kayan Faty ta juya gida.  Mimi da bata sallah xataiba da kimtsa kayan takai kowanne muhallin daya dace. Tana zaune tana lazimi aka kira sallar isha ta tashi tasa kayan bacci dan jikinta fes yake bata buqatar wanka.  Bata damu da dawowar Badaru ba domin ya kunna inji,  ta kunna fankarta wacce tai chaji full.  Iskar fankar na kada ta tana danna waya (chating)  a zuciyarta cewa take "Allah ya sakawa yaya Faty da alkhairi badan taimakonta ba da tuni ina zaune cikin zafi. 


Takwas nayi ta balli maganinta tasha dama tana timing. Ta janyo kazarta ta bude ta fara ci da bisimillah. Qarar injin da taji ya tabbatar mata da dawowar Badaru, ya shigo dakin yayi tozali da Mimi.  Idonsa fes akanta saboda hasken wutar lantarki,  tayi masa kyau ainun kamar sake masa ita akai. 


Yayi saurin qarasawa gabanta tare da cewa "maryam sauki ne ya samu haka da wuri? Sannu" ta danyi murmushi tare da gaisheshi.  Ya amsa idonsa na kan ledar gabanta wanda qamshin kazar ya cika dakin,  yace " harda hidima haka? " ta amsa da cewa "eh yaya Faty ce tasaimun da wannan fankar (ta nuna masa fankar) yace " to madallah haj Faty kenan bataso kudi su zauna lfy" (kuji banxa🤣)


Ba kunya ya tayata suka cinye kazar sukasha furar,  lamarin da yayiwa Mimi dadi.  Domin yaune rana ta farko da suka taba cin abinci kwano daya da Badaru. 


Yana ta kallon Mimi wai ta burgeshi qarshe,  ya kalli qafarta yar dundubus da ita har tafi jikinta haske yatsunta kansu abun kallone be taba lura Mimi takai haka ba sai yau (dama ya xa ai kasani?  Wahalar gidanka tasa tayi kaushi) ya ruqo hannunta yana murxawa cikin shauqi "maryam tashi muyi shirin kwanciya" ya fada yana mai qura mata ido.  Azuciyarta tai masa dariyar mugunta,  saboda tasan bata da tsarki. 


Ba musu ta miqe taje tai brush,  shima ganin tayi yaje yayi amma ba batun wanka duk kuwa da tsamin ranar da yake.  Ta feshe jikinta da turare ta kwanta hankalita kwance yau ba kawo farmaki 😜. 


Tayi mamaki kwarai da taji ya kashe inji,  ya shigo dakin yana me cewa tunda ga fanka ai sai man injin ya huta. Yana hawa gadon ya kamata ya rungume yana shafar gashin kanta yana cewa "maryam kinada shiga rai,  komai naki me kyau ne" tadan motsa bakinta cikin sigar murmushi har dimple dinta ya lotsa.  Lamarin da Badaru yaji ba abunda yake muradi illah ya hada bakinsa da nata.  Amma yasan bazata yadda ba shiyasa beyi yunqurun hakan ba,  domin yau hakanan yaji bayason batawa maryam rai. 


Ganin abun nasa yana nisa yasa tace masa bata da tsarki,  atake ya saki wani mugun tsaki tare da tureta daga Jikinsa,  ya koma gefe ya kwanta.  Dama hakan take jira dan haka ta gyara kwanciyarta ta maida fankar dai dai saitinta tai adduar kwanciya bacci.



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣4⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)


Tasamu canjin rayuwa saboda taimakon Faty,  ta rabu da matsalar zafi saboda fankar da Faty ta sai mata. Koda babu wuta takan bada fankar da 50 naira akai mata wani company dake bayan gidanta kadan mai gadin gurin ya karbi hamsin din yasamata caji,  saboda company ne basa rabo da wuta.  


Sai dai da yake rayuwa indai kai imani baka rasa jarrabawar ubangiji,  sai wata sabuwar matsalar da bullo mata.  Matsalar kuwa itace;  kawo abokai da Badaru ya tsiriyi cikin gidan saboda yaga cimar gidansa ta canja (ansamu mai dadi).


Ba kawo abokan nasa ne problem dinba ko kuma abunda zasuci,  cin mutunci da toxarcin da Badaru keyi mata agaban abokan nasa shine babbar matsalar. 


Sau tari zai cika gidan da abokansa duk kuwa da qanqantar gidan,  wanda hakan ke hanata sakewa sai dai ta takure kanta adaki.  In fita parlour ta kamata ko duba girki sai dai ta saka hijabi, har mamakin inda ilimin addininsa yake take domin babu addini sam acikin abunda yake, kodan ya takura mata yake hakan?  Sannan bayan tayi hidima dasu da jikinta da aljihunta (domin babu ko sisinsa aciki) sai kuma ya dunga zaburarta yana daka mata tsawa agabansu,  a qoqarinsa na nunawa abokansa cewa ita din bata isa komai ba. 


Yauma hakace ta kasance,  domin tare suka shigo da wani abokinsa sani around 5;30 pm.  Suka taddata zaune parlour ta tasa fanka agaba tana shan iska,  a xuciyarta bata gajiya da yiwa wacce ta sai mata fankar adduar alkhairi (ya Faty) 


Tai saurin miqewa ta shige daki da nufin suturta jikinta,  domin shimice kawai a jikin nata.  "kinaji ana sallama dan rainin hankali baxaki amsaba" cewar Badaru.  Sani abokinsa yayi saurin tareshi da cewa "bakaga hijabi zata dakko ba,  laifinane dana shigo kai tsaye ban tunanin halin da xan taddata ba" ta fito sanye da jihab me hannu tana cewa "sannunku da xuwa" ta gaishe da Sani, sannan ta nufi kitchen ta qara sanwar abinci dan ganin baqo,  ta debo musu ruwa da kwalin exotic ta dora akan tray ta glass cups ta kawo ta koma daki ta zauna. 


Tananan zaune tana yan danne dannen waya taji xuwan wasu abokan nasa har su 3 domin taji ya ambaci sunayensu.  A xuciyarta tace yau kuma anan xa ai mana zaman majalisar kenan. 


Ta tashi domin ta duba abincin data dora,  ta gaishesu ta wuce kitchen.  Ta gama komai ta maida miyar kan gas domin ta qara dumamata ta jiyo Badaru na kwala mata kira,  ta fito parlour ta dan durqusa gefensa "gani" ya dubeta yana wani daga hanci yace " ke wace irin mahaukaciyar mace ce mara tsari?  Bakiga nayi baqi bane?  Ko sai nace ki qaro wasu kofunan da lemon? Banason dabbanci."  Ba tare da tace komai ba ta miqe taje ta kawo  wani kwalin lemon da kofuna ta ajiye,  tana shirin juyawa yace " abincin ma sai nace ki kawo ko?  To karki kawo" tai saurin xuba abincin a warmers har tana qonewa saboda kar wani cin mutuncin ya biyo baya.  Domin tana jiwo shewar abokan nasa,  suna yaba masa yadda yake tafi da ita.  Har wani a cikinsu wanda bazata iya gane kowaye ba yana cewa "da kyau mutumina haka akeson mutum ya xama jan wuya a gidansa"



Ta hada musu komai na abincin a gabansu, sai da ta tabbatar ta hada komai sannan ta nufi daki.  Badaru yayi saurin katseta da cewa "waye bawan gidanku anan dazai zuba musu? " ta duqa a takure take saboda kallon da wasu acikinsu suke mata,  xata fara xubawa Sani yayi saurin katseta da cewa "a a jeki maryam mungode  kowa zai xuba nasa" dan ya lura a kunyace takeyin komai. 


Badaru yace "a a ta xubawa kowa umarnina ne,  ni naga damar haka.  Tana gama xubawa ta miqe ta shige daki.  Sani ya dubeshi ransa adan bace " ka daina haka Badaru,  wannan yarinyar kyautace Allah ya baka ka riqeta da amana ku zauna lfy.  Yawanci yaran yanxu basu cika bin miji haka ba,  bare ita da take da xurfin ilimi" Badaru ya daga murya,  domin yanaso Mimi ta jiyo abunda zaice "yo ni ina ruwana da ilimin mutum,  ko parpesa ce ita bai dameni ba domin miji ta rasa na taimaka mata na aureta,  inba dan nidinba da tuni tanacan a jabe gidan ubanta"  




Yayi sa a kuwa domin duk maganar da suke akan kunnen mimin sukayi saboda tana da ji sosai,  kuma dakin bashi da xurfi. Hawaye ya wanke mata fuska,  lallai yau wulaqancin na Badaru yafi na koyaushe.  Muryar daya daga cikinsu ta katse mata tunani inda yake cewa "au wai kana nufin tana da ilimi? " Badaru ya bashi amsa da cewa "degree      ne da ita akan fannin sharia" wanda yayi tambayar yace "Tab ai wlh gwanda daka riqe mata wuta daka sake mata rainaka zatayi musamman intasan tafika ilimi mata yan boko mugayen yan rainin wayo ne.  Kai kuma sani da kake wani xance ai mata xuma ne da wuta ake cinsu" Sani ya balla masa harara yace "inkasan ba shawarar arziqi zaka bayar ba ka daina xuga xugagge yana ciwa yar mutane mutunci"



Badaru yayi saurin tareshi cikin hargowa "kaga sani ya isa,  ni ba wani wanda yake zugani haka nayi niyyar tafi da gidana kuma haka nakeyi.  Intaga xata iya xama dani a haka ta zauna, in kuma bazata iya ba sai in mata saki daya taje gidan nasu ta dandana xama taji.  Ai tasan rufa mata asiri nayi,  kaf gidansu ita kadaice budurwar data rage. Sannan tace xata kawomun wani fi ili?  Bokon banxa bokon wofi  meyasa bokon nata be bata mijin aure ba.  Wlh ko shugabar qasa ce ita dole ta bini yadda nakeso intaqi ga hanya nan.  Nasan kina jina MARYAM in bazaki iyaba kixo ki tafi gidan ubanki."


Duk yanda taso danne xuciyarta abun ya gagara kuka take wurjanjan,  batasan yadda akaiba sai ganinta tayi a parlourn adai dai lokacin da yake cewa "ai kinsan yadda kika sha wuya kika zaunu kafin Allah ya kawo miki ni na aureki,  ki qoqari ki kashe auran kina budurwa ma kin rasa miji bare kina BAZAWARA."




Sai a lokacin ya ankara da wanxuwarta a parlourn,  ya kalli idonta da fuskarta gabansa yayi mugun faduwa  domin bai taba ganinta cikin wannan yanayin ba duk abunda yake mata.  



Sani yayi saurin shan gabanta ganin ta nufi qofar fita, a qoqarinsa na dai daitawa,  yace MARYAM Dan Allah dan darajar iyayenki kiyi haquri kar fita.  Ta tsaya cak! Badaru dake gefe ya saukewa boyayyar ajiyar xuciya ganin ta tsaya. 



Sani yace Badaru,  beye lefin yarinyar nan?  Saboda ni kayi haka? Daga gaya maka gaskiya xaka ci mata mutunci haka?  Lefin me tayi maka? 


Mimi ta matso kusa dashi ta kalleshi, yai saurin yin qasa da kansa.  Tace  cikin nutsuwa da qarfin zuciya " kayi haquri qaddarace ta hadamu, amma karka manta kai ka ganni kace kanaso ba talla aka kawo maka niba.  Kuma tabbas miji na rasa shiyasa na aureka,  inba dan haka ba ai babu wacce xataso xama da  namiji irinka.  Kuma da Allah ya hanani miji daga baya ai yabani kai?   To haka nake sakaran duk renda Allah ya sa ka rabu da ni Allah xai bani wani mijin.  Gari da yawa ai maye bayacin kansa Badaru. In shaa Allahu yadda Allah ya doramun jarrabawar xama da kai xai bani ikon cin jarrabawar, wlh nima ba Jin dadin xama dakai nake ba.  Allah ya na madakata yana jiranmu kuma zai mana sharia"



Simi simi daya bayan daya abokan nasa suka fice,  kodan kada aure ya mutu ace ta sillarsu ne.  Ya rage sai Sani kawai,  ya kalleshi yace "yanxu wannan abun da kayi me gari ya waya?  Burgewa kayi? Ka tauna asirin gidanka a idon duniya.   Allah ne kadai yasan inda wannan zancen zai tsaya,  kuma tunda da wata niyya kake kawo abokai gida daga yau babu abokin da xai kuma xuwa gidanka.  Ya juya ga Mimi yace MARYAM kiyi haquri,  anbata miki Allah ya baki haquri ya huci xuciyarki." ya juya ya fita. 




Tunda ta shiga daki bata qara fitowa ba sai da akai kiran magriba ta fito alwala,  ta taddashi zaune a yayi tagumi.  Daganan bata qara fitowa ba har wajen 9:03 taji ya tada inji tayi shirin kwanciya ko wanka bataiba bare cin abinci dan ranta har yanxu a bace yake.  


Tanajin lokacin da yaxo ya kwanta kusa da ita,  tai saurin rintse ido.  Dan jitayi wata irin tsanarsa ta taso mata.  Bata tabbatar da Badaru bashi da kunya ba sai da taji hannunsa a jikinta  yana lalubarta.  A tunaninta yau zai haqura tunda sunyi sabani,  amma ina mayen ya kasa haquri duk kuwa da ya gwada yin haqurin ya kasa.  Tai masa banza taqi bashi fuska,  take banxa ne sai ya fara qoqarin gwada mata qarfi zai shigeta,  a salonsa na kwanciyar awakai.  Ta qanqame jikinta ta hanashi yin hakan,  dole qanwar naqi yayi amfani da lallashi ta hanyar cewa "maryam dan daure ki barni nayi,  na kasa bacci kinsan na riga na saba" sama sama ya samu nutsuwa ba kamar yadda ya saba ba. 




Ya koma gefe ya kwanta yana tunanin da maryam din ta tafi dazu da ya zaiyi?  Dole ya sake taku,  kodan lalurarsa ya xama dole ya zauna da maryam dan bayajin xai iya haqura da buqatarsa koda ta kwana daya ne.  Dan yana sahun mabuqata ga kuma qarin magunguna da yake sha,  bayan haka kuma bai gama more kudinsa ajikin maryam dinba.  



Duk da bata taba turje masa a gurin kwanciya ba sai yau,  amma yana mamakin duk sanda ya batawa maryam rai to ranar baya samun yadda yakeso ajikinta.  Duk da kuwa ba hanashi takeyi ba,  amma duk qoqarinsa baya gamsuwa.  A fili yace dole in gyara lamura na da maryam kodan shimfidata. 


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣5⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Su 3 ne kawai zaune a majalisar,  Badaru,  Mekudi sai wani abokinsu da suke kira KB.  Hira suke yayin da KB ke daga gefensu kadan yana karatun news paper.  Badaru ya kalli Mekudi yace "ya babu lbr ne?  Na jika kwana biyu shiru? " Mekudi yayi wani shu'umin murmushi sannan yace "yo ni ana raba ni da lbr ne? Kamar ka shiga xuciyata ansamo wani be zafi,  amma fa a tube yake ita zaka matsa ka cusawa kafin ka shiga,  sauran bayani kuma xaka bani lbr da kanka.  Ya fada yana daga gira" 


Badaru ya washe baki tare da cewa "Allah mutumina 😄? Yana ina?  Bani " mekudi yadan muskuta tare da cewa " sai dai fa yana da illah,  yakan bata mahaifa ko hana haihuwa gaba daya,  saboda haka ka kula,  amma dadi kam xakaji dadi kamar ka mutu 😜"  Badaru ya miqa masa hannu suka tafa yace " yo ni ina ruwana,  ai dama bandamu in haihu da ita ba,  amfanin ta kashe qishirwata da ita".


KB da tunda suka fara maganar hankalinsa na kansu ya magantu "Badaru me kake shirin aikatawa?  Sirin shimfidarku kake budewa anan? Har kake shirin batawa yarinya mahaifa? to wlh karka soma.  Kai kuma mekudi kaji tsoron Allah ka tuna kana da yaya mata in akaiwa yarka haka xakaji dadi? "  sukai tsit suka sunkuyar da kai,  saboda suna respecting KB dan ya girme musu. 


Suna idar da sallar magriba Mekudi ya tashi tafiya Badaru ya miqe shima tare da cewa " Bari in koma gida nasan tana zaune a duhu ba wuta." 



Yayi saurin tadda mekudi a motar sa yana shirin tashin motar ya bude ya shiga,  ya miqa masa hannu "Bani maganin" mekudi ya sheqe da dariya yace "shege baka haqura ba" shima yayi dariyar tare da cewa "aimu bama wasa da kayan aiki". Ya miqa masa maganin a kwalinsa tare da cewa "ka kula". Badaru ya fito ya shiga tasa motar,  yayi gida yau ko gurin Nafee baya son xuwa tunda ya samu......... 



Mimi tayi mamakin barin jikin da Badaru keyi a kanta yau,  duk da ba sabon abu bane a gurinta sambatunsa a shimfidarsu.  Tana jin lokacin da ya cusa mata wani abu a gabanta.  Tai saurin yunqurawa xata tashi,  yasa hannu ya danneta.  Tace "meka sakamun a jikina?"  cikin rashin nuna kulawa ya bata amsa "xan cuceki ne? To vaseline na saka saboda kin matse da yawa na kasa shigarki" daren ranar ta gurxu a hannun Badaru,  ga wani irin ihu da sambatu da yake tana tsammanin maqota na kusa zasu iya jiyoshi. 



A dan wannan tsakanin Badaru ya xama wani irin qasurgumin jarababbe,  kullum cikin yin abu daya yake.  Ba dare ba rana,  domin da ranar Allah xai baro kasuwa yazo gida ya shafe awanni yana dirxarta.  Kuma in dare yayi ma babu hutu,  sai yayi aqallah sau 3. Ita har mamaki take sam baya gajiya,  zata iya cewa tunda aka kawota gidan Badaru yau kimanin wata hudu kenan (4 month)  bai taba fashin kwanciya da ita ba,  sai dai in period take. 


Lokaci guda ta qare ta lalace,  a xuciyarta take cewa ashe da ba wahala nakesha ba,  yanxu ne nake ainihin wahala.  Gashi dai bata nemi komai ta rasa ba (Faty ta tsaya mata)  amma jarabar Badaru tasa ta xama kamar tsumma.  A gefe guda kuma ga rashin mutuncinsa domin babu abunda ya fasa,  sai ma qaruwa da yayi.  


Sau tari takanyi tunanin matan da suke cewa aure da dadi,  sai ta rasa ta inda sukejin dadin auran, ta xaman takewar gida kota kwamciyar aure?  Domin ita dai tunda suke da Badaru ko na second daya bata tabajin dadin kwanciya ba,  hasali ma axaba takeci ba kadan ba.  Da farkon aurenta tana danganta hakan da rashin sabo,   amma yanxu data dan kwan biyu sai take ganin halittar tace haka.  Ita dai tasan in azabar da takeji ce jin dadin aure sai take ganin ba macen da xatace aure da dadi. 



A lokacin sai takejin babu abunda ta tsana a duk duniya irin sex life (kwanciyar aure).  Duk da gori da qalubale data fuskanta a rayuwarta ta yan matanci sai ta kwammace gara rayuwarta ta gida da wannan rayuwar da take yanxu. 



***    ***       ***     ***


Yau babban baqo garesu,  Badamasi qanin Badaru wanda tunda akai auren bai taba xuwa gidan ba.  Yauma yaxo ne bisa takurawar ummansu. 



Tunda yaxo Mimi keta hidima dashi dakko wannan,  kawo wannan.  Duk da batasan da xuwansa ba, tai masa tarba ta musamman da girkin alfarma.  Tana ta xarya tsakanin parlour da kitchen,  cikin tsawa da umarnin Badaru,  wanda duk fitowar da tayi sai ya nemi wani abun da zaice batai dai dai ba. 


Yanxu ma tafito ne dauke da qaramin tray wanda ta doro cups da lemon happy hour na kwali ta taho,  ya daka mata tsawa da cewa "wai ke komai sai anyi jiranki ne?  Kinsa wani hijabi na munafurci,  wazai kalleki anan?  Ni da babu abunda bansani ba a jikin ki, ko Badamasi dake dan uwana uwa daya uba daya? "   Badamasi ya runtse ido cikin takaicin abunda Badaru yakewa yarinya,  tana qoqarin kare masa mutunci ta hanyar suturta kanta yana kwaye mata baya.  A dan xaman da yayi yanxu ya fuskanci inda aurensu yasa gaba. Shiyasa yaga maryam din duk ta canja,  mace qayatacciya kyakykyawar gaske me fasali amma cikin lokaci kadan ji inda Badaru ya kwararrabata.  Ya gyara xaman wayarsa dake kan hannun kujera, wacce yake recording din duk abunda ke faruwa tun daxu,  da nufin in yakoma gida ya sakawa iyayensu suji yadda Badaru kewa yar mutane. 


Tunaninsa ya katse lokacin da yaji Mimi na ajiye lemon da ta kawo a kusa dashi.  Badaru ya tsai da ita, tare da daka mata wata muguwar tsawa "ke dauke Badamasi bayashan irin wannan lemon na kanti, sai zobo kije ki kawo masa zobo" (kunji fa kamar ya siya ya ajiye)  ta dauki tray din lemon tare da cewa "to bara na dafa zobon sai dai babu qanqara...... " maganar ta dauke lokacin da taga Badaru ya daga hannu da nufin kai mata mari.  Tai saurin saka tray din hannunta ta kare fuskarta,  hakan yasa dukan ya sauka kan farantin kayan ciki suka watse.  Badamasi yayi saurin miqewa tsaye cikin razana 😳. Badaru ya dora da cewa "Dan ubanki harni xan saki aiki kice babu qanqara?  Meyasa baki siya kin ajiye ba?"  idon Mimi qurrr akansa tana kallonsa cikin mamaki Dan yaune karon farko da yakai hannu jikinta da sunan duka,  kuma yaune karon farko da ya xagi ubanta dake qarqashin qasa. 



Cinkin dinbin mamaki da razana Badamasi yace "Badaru 😳dukan mace?  Kamar jahili,  metai maka?  Dama abunda nakiji na cewa kana tara abokai kaci mata mutunci gaskiya ne? Me tayi maka? " Badaru ya tare Badamasin cinkin hargowa kamar xai dakeshi,  "baka ga abunda tai ba?  Yar iska mara mutunci,  duk abunda xata xubarmun da mutunci ta iya, banxa jaka" 



Idanunta jajur suna digar hawaye take kallon Badaru ba komai yayi mata ciwo ba irin zagin ubanta.  Cikin qarfin zuciya tace" karka kuma zagarmun uba,  domin yana kabari akwance".  Yayi saurin cewa "an zageshi uban ubanki ma yaci ubansa,  kiyi abunda xakiyi"  ta mayar masa da martanin cewa "babu abinda xanyi domin xagi xagawa yake, kuma duk abunda kakemun Allah ya na jinka, yana ganinka kuma zaimun sakayya." 



Ya watsa mata wani kallo sannan ya funciko hannunta ya hankadata bakin qofa tare da cewa "fita ki tafi gidan ubanki shegiya mara tarbiyya gayyar tsiya." Badamasi ya daka tsalle tare da dakawa Badaru tsawa kamar shine gaba da Badarun yace "wlh Badaru ka kiyaye ni, na rantse da Allah xaka tarkowa kanka bala'i,  domin yanxu xanje na fada Abba abunda gidanka yake ciki"  yana kaiwa nan ya figi muqullin motar Badaru dake kan kujerar parlourn (domin shi baixo da mota ba) ya fita. Mimi ma tasa kai ta fita yayi saurin cewa " ban baki izinin fita ba" ko takansa bata biba tai waje ya bita da gudu ya jawo ta ya dawo da ita tare da furta "maryam akanki ake shirin hadani da iyayena,  kowa nawa sai ya rabu dani a kanki. Abokaina, yan uwana, yanxu kuma iyayena?  Meyasa haka?"


Acikin motar Badaru kuwa Badamasi ne a kifa kansa a sitiyari yana jin quna a ransa, wlh da yasan yacce xai tarar da Mimi kenan da bai zoba.  Bazai juri ganin Mimi cikin wannan halin ba,  yanxu meye abunyi?  Yayi dan gajeran tunani,  baxai fadawa iyayensu abunda gidan Badaru ke ciki ba yanxu.  Domin inyayi silar mutuwar auren Mimi sannan daga baya yazo yace yana sonta cewa xa ai ya kashe mata aure dan ya aureta.  Ya dakko wayarsa yayi saving recording din da yayi saboda wata rana. 



Hannunsa yakai kan aljihun motar ya jawoshi,  saiga kwalayen magani guda 4 duk iri daya (maganin da mekudi ya bawa Badaru,  yake ajiyarsa amota saboda kar Mimi ta gani) ya dakko ya duba kwalin hotunane ajiki na mace da namiji tsirara suna xxx kala kala hutunan abun ba kyan gani.  Ya duba rubutun jikin maganin,  yaga illar da yake,   a qa'idar maganin ma matan banxa masu blue films akewa amfani dashi dan su fita hayyacinsu, kuma suma din sai anyi aggrement.  Amma dan zalunci da son zuciya Badaru yakewa yar mutane amfani dashi, kuma bama kwali daya ba,  alamu sun nuna ya dade yana mata amfani dashi tunda ga kwalaye nan har guda 4. 


Ya share hawayensa ya dauke ragowar maganin a fili yace "MARYAM Allah ya saka miki,  Allah ya miki canjin alkhairi domin Badaru ba miji bane. 



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣6⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Cikin kwanakin da suka biyo baya tai wata irin ramewa kamar me ciwon SIDA (AIDS). Ta fita hayyacinta kwarai,  ga wani irin mugun qaiqaiyi dake addabarta a qasanta,  ga dukkan alamu ciwon sanyi infection yayi mata mugun kamu. Domin har gari gari take gani a gabanta a memakon danshi da akasan ya mace dashi, ga wani irin wari danma bata ramo da inserting almuski. 


Badaru tsakaninta dashi dangantaka tayi tsami kwarai da gaske,  domin sai suyi 3 dayz koma fiye da hakan bai mata magana ba, kuma inma tayi masa baya amsawa. Walau kuwa koda gaisuwa ce,  sai dai tagaji da tsuguno ta tashi.  Wanda hakan shiyasa kawo mugun koma baya a lfyarta,  sau da yawa sai dai ta ganta a kwance kamar gawa batasan abunda ya faru ba tunda babu kowa a kusa balle ya karanta ta mata abunda ya faru kafin ta tsinci kanta a hakan. 



Babban abun takaicin shine : duk wannan takun saqa da suke da shi,  hakan baya hana in dare yayi yazo ya mutsutstsuketa da sunan yazo neman haqqinsa na aure.  Sakamakon ciwon sanyi da yayi mata illah yasa ko yazo baya samun komai (babbar illar ciwon sanyi kenan,  wato qafar da ni'imar mace) wanda hakan ke jawowa ya fusata yayi ta xaginta da aibatata. 



Data kula sosai sai ta gano cewa ba ita kadai ciwon ke damu ba,  saboda Badaru ma Kullum cikin sosa al aurarsa yake,  alamu shima ciwon na addabarsa. 


Dan lfyar kanta da kuma maganin wulaqancin da Badaru kemata a shimfida (domin tana kyauta zaton rashin samun biyan buqatarsa na daga abunda ya sa wulaqancinsa ya kuma ta azzara) yasa ta tunkareshi da sunan ya barta taje asibiti domin ciwon sanyi ke damunta.  Da farko be kulata da maganar ba,  sai daga baya ya jiyo qanshin gaskiya a maganarta.  Domin ciwon da tai masa bayani yayi kama da wanda masu magani ke bayani a kasuwa.  Hakan yasa ya sameta har daki yace "kawai kinje kin kwaso ciwon sanyi kinxo kin gogamun,  wlh in hakan yayi sanadiyar raguwar qarfin mazantakata bazan yafe miki ba"(🤣🤣🤣).


Ta dago arazane jin abunda yace,  cikin sanyin murya tace "ni kuma Badaru?  Ni ina fita ne?  Canake tunda nazo gidannan fitata daya?  A ina xan kwaso ciwon?  Nafi zaton kaine ka dakko mana a kasuwa" yasan tana da gaskiya shiyasa bece komai ba ya kada kai yayi gaba. 


Da yamma kuwa sai gashi da ledar magani,  ya siyo a irin gurin masu saida maganin hausar nan na kasuwa.  Wadanda ke yawo da mota suna tallah a speaker.  Ya miqo mata wani qaramin qulli "wannan gashi ki juyeshi a madara yanxu ki shanye,  ya miqo dayan wannan kuma ki dunga turare dashi kina tsugunawa akai" (kunji fa!  Mtsew komai aka hada da jaki sai yaci kara) tace  "to" ta karba,  azuciyarta take tunanin shidai asibiti ne bayaso arayuwarsa.  Ta qudure bazatai amfani da wandannan magungunan da batasan ingancinsu ba haka kawai ita ba qoshin lfy suje su illatata.



Tofa! Abu fa ya kacame, komai ya xama chocolate 😂. Iskancin Badaru da wulaqancinsa kanta ya kazanta,  ko alabari bata taba jin inda ake cin mutuncin matar sunnah yadda Badaru kecin mutuncinta ba.  "Banxa jaka,  na tsaneki" sune kalaman da Badaru ke fada mata adun sanda suka hada shimfida dashi saboda baya samun biyan buqata Sam.  Gashi ita a kanta tanajin yadda tai wata irin budewa tai sako sako,  kamar matar data haihu bata gyara kanta ba. 


Bama sai sun hada shimfida ba,  a rana daya yakan ce mata "na tsaneki" yafi sau cikin carbi. Sunanta kuwa a gurinsa ya koma "jaka" dan sau tari zai sata aiki sai yace "ke jaka yimun abu kaza" yayin da agefe guda kuma ya dage da aikin ginin da yake,  domin ya auro Nafee wacce yanxu Kullum a gurinta yake kai 11 dare. 



Mimi,  yar kwalisa yanxu ta xama wata muguwar siriri mara fasali,  tayi fari fau kamar me amfani da mayunkan kwaile fata (bleaching) yar kewayayyar fuskarta ta koma tsuru sai manyan idanuwa 👁👁 da hancinta 👃🏾 wanda rama tasa yayi bodardar.  A taqaice dai ta xama mummunar qarfi da yaji. 



Babbar matsalar dake addabarta itace rashin ganin al adarta (period) rabonta dayi tun tana wata biyu a gidan, wato lokacin da taje asibiti ta biya gidan Faty.  Tayi tayi Badaru ya barta taje taga likita ko wata matsalar ce yaqi.  Data dameshi da xancen saboda ciwon marar dake addabarta  sai yace karta dameshi,  saboda ba akanta aka soma CIKI ba.   Tunda daganan itama bata qara xancen ba,  saboda itama data duba cikinta sai taga tafi kama da masu qaramin ciki. 



Kuma wani ikon Allah sai ta tsinci kanta cikin farinciki da cikin,  saboda kasancewarta meson yara tunda basu taso sunga kowa a dakin mama ba sai su biyu.  A fili tace " Baby ki rasa lokacin da xakixo sai lokacin da ake sa toka sa katsi?  Allah ka rabamu lfy,  Allah ya miki albarka yata😊" ta fada hannunta na dafe akan cikin. 



Badaru dake gefe yana sauraranta yayi saurin matsowa kusa da ita yace "au mace kikeso ki haifa?  To ai se ki roqi Allah kada ya baki me irin BAQIN JININKI,  domin in ta rasa miji wlh sadakarta xan bayar"  ta dago ta kalleshi tayi murmushi 😊 tace " Badaru in tayoka ai bazatai baqin jini ba, tunda ka ganni ka taimaka ka aureni itama sai Allah ya dubi kyakykyawan aikin da kayi a kaina ya kawo me auranta 😊"



Yasan magana ta fada masa dan haka yayi tsit. 

*******       ********    ******

Tun jiya cikin dare take murqususun ciwon mara,  har xuwa yanxu 9:43 na safe.  Tun tana iya yunquri har qarfinta ya qare ta kasa.  Badaru tun shekaran jiya yayi tafiya Lagos akan harkar kasuwancinsa, kuma gashi bata da lambarshi kamar yadda bashi da tata.


Badamasi da yau ya shigo kano yazo daga inda yake aiki (Dutse) tunkan ya qarasa gida hankalinsa yake akan maryam.  Tun rabuwar da sukai da Badaru akan ciwa maryam mutunci hankalinsa ya kasa kwanciya,  dan haka direct ya wuce unguwar su Badaru. 


Tun daga soro yake kwada sallama amma ba amsa,  ta bangaren Mimi ta dakko waya da nufin kiran Faty ta fada mata halin datake ciki sallamar ta rusketa.  Kuma tana amsawa amma dake muryar a shaqe take saboda wuyar ciwo shiyasa bayaji. Ya sako kai parlour tai miqe daga kwanciyar cikin qarfin hali tana haki tace "inata amsawa bakaji" ya dubeta a razane yace "maryam badai ba lfy ba? Ina mai gidan ya fita ya barki cikin wannan halin?" 


Tai murmushi tace "yayi tafiya tun Lagos,  bayan tafiyar ne ciwon ya riskeni shi......" bai qarasa jinta ba ya dakko waya a aljihu.  Sai ji tayi yana xancen rashin lfyrta kuma ga dukkan alamu da Badaru yake.  Can yaji yana cewa "babu batun ragonta,  dan mace na da ciki bazatai ciwo ba sai ace tacika ragonta?  Nidai yanxu xan kaita asibiti ya kashe wayar"



"Tashi ki shirya muje asibiti, " ya bawa maryam umarni.  Sannan ya zarce da mitar cewa kasan lalurar ciki ne?  Inda kai Allah ya dorawa wayasan kwakwazon da zakai?  Kaiwa yar mutane ciki ka tafi kabarta da wahala.   Itadai ta yunqura dakyar ta miqe tayi hanyar toilet tana godewa Allah da ya kawo me temakonta. 



Cikin qarfin xuciya tai brush da wanka suka tafi.  Ganin yadau hanyar yan kaba yasa tace "Aminu kano nake ganin likita ai" ya waiwayo ya dubeta yace " rana tayi shiyasa xan kaiki asibitin wani abokina da mukai karatu tare,  amma shi likitan mata ne"  tace ai a Aminu kano akwai yayata dake aiki acan,  inka kaini ko likitan yamma ne sai nagani" 



Yana kallon titi yace "sry bari na kaiki private din xaki fi samun kulawa inyaso har awo da haihuwa sai kije can. Yasan aikinsa sosai" ta sunkuyar da kai cikin kunya jin yayi maganar cikin jikinta.  Ya qura mata ido cikin burgewa dan yanason mace me kunya. Aransa yana aiyana rashin imanin Badaru dan kowa yaga maryam yasan ba a dadi take ba kuma ga ciki na wahalar da ita. 


Sun tadda layi kasancewar safiya ce. Badamasi yayi masa waya da kansa ya fito ya shiga dasu bayan ya nemi alfarmar na kan layi. 



Yana dubata suna dan taba hirar yaushe gamo da Badamasi,  ya kalleta yace maryam alamu sun nuna kina da qarancin jini a jikin ki,  shiyasa kika dashe kikai haske.  Badamasi yace " ba ciki bane ya kawo hasken?"  Dr yace "bazan iya cewa da ciki ba ko babu,  amma dai bari nayiwa sister sarah magana ta tafi da ita can nursing station tayi mata checking sosai akan hakan" 


Ya kirata a waya nan da nan sai gata yace "kuje da wannan yayi mata bayani" Mimi ta bita yayin da Badamasi ya koma reception dan bawa ragowar marasa lfyar damar ganin likita. 



Acan gurin nursing din sun dubata sosai taji wacce ta dubata na fadawa dayar cewa,  tana buqatar aimata wankin ciki. Lamarin da yasa Mimi tsorata, domin tasha ji ana fadar wahalar wankin ciki. Dan haka ko takan mayafinta da jakar bata biba ta ranta ana kare 🏃🏽‍♀.


Badamasi na zaune yaga fitowarta daga dakin a harkitse,  tana tafiya tana waiwayen bayanta taga ko nurse din ta biyo ta.  Ya taho gurinta da sauri cikin rashin sani suka gabxa karo. Tai qasa xata fadi yayi saurin tarota jikinsa,  jinta jikin mutum yasa ta qanqameshi tana cewa "Badaru kaji wai wankin ciki zasuyimun,  kuma da xafi sannan xasu wankemun Baby dan Allah karka bari suyimun." shidai Badamasi tunda yaji maryam ajikinsa ya tafi wata duniyar,  ya xaci irin mafarkan da yasa ba yine akanta dan haka ya rungumeta jikinsa tsam yana sauke ajiyar xuciya. Akayi sa a itama ta xaci mijintane ta kwanta lub.


Nurse din data biyo Mimi da jakarta da mayafi ce ta dawo dasu hayyacinsu.  "oga gashi ta gudo dakaji ance xa ai mata wankin ciki"  yai saurin rabata da jikinsa daya farga ba mafarki yake ba,  a xuciyarsa ya dunga cewa astagfirullah Badaru kai ka jawomun da ka kula da matarka da ban kawota asibiti ba balle harna rumgumeta.   Itama Mimi sai yanxu ta dawo hayyacinta,  ta dunga jero neman gafarar Allah.  



Suka koma office din Dr,  nurse din tayi masa bayanin matsalar Mimi da kuma qin yadda ai mata wankin cikin.  Ala dole ya rubuta mata maganin ciwon mara dana qarin jini. Badamasi ya tambayeshi akan cikin.  Yace "yanxu kam bazan iya cewa da ciki ba ko babu tunda akwai lalura da yawa a tare da ita, sai dai ko in kun kuma dawowa ayi scanning.  Ga maganin ta dage da cin abinci da shansu kuma basu da qarfi koda da cikin baxasu illatashi ba" sukai sallama suka tafi. 



A hanya suna tafiya tace masa "dan Allah karka maidani gidannan na kwana ni kadai jiya nasha wahala,  bansan abunda hali xaiyi ba yau." ya dubeta yace "to Maryam ai bani da ikon kaiki wani gurin bada ixinin mijinki ba,  amma bari in masa magana saboda akwai hatsari abari ki kwana ke kadai" ya dakko waya ya kirashi tanaji yana masa bayani,  can ya miqo mata wayar yana cewa gata.  Tai sallama be amsa ba bare ya saurari gaisuwar da take masa ya hau masifa " kince bazaki kwana gidanki ba ko?   Uwar langwai to kitafi duk inda xaki tunda kinsa anmun titsiye inna dawo kya dawo." yana kaiwa nan ya kashe wayar, itama ta kashe ta miqa masa tare da cewa kaini yahya gusau gidan yaya Faty.  



Koda suka isa gidan sun samu ya Ahmad na nan,  dan haka koda yaya Faty ta fito domin temakamata su shiga ciki yaga bata lokaci ne dan haka ya dauketa cak yakaita har cikin parlourn.  Badamasi ya dunga kallonsu cikin birgewa,  domin sai ka xata Ahmad ne dan uwan Mimi ba Faty ba. 


Badamasi ya dade a gidan suna hira, saboda family din sun burgeshi.  Faty ta dunga jerawa Mimi sannu ta duba magungunan da aka bata.  Tare sukayi dinner sannan tasha maganin kana Badamasi ya tafi. 


Yau dadi takeji xata kwana gidan yaya Faty,  har dare sunata hirarsu cikin nishadi sannan suka nemi makwanci,  yaya Faty ta dunga mitar ramar da Mimi tayi amma koda mimin ta fada mata ciki ke wahalar da ita sai mitar ta koma murna.  Suka raba dare suna hirarsu sannan sukai bacci. 



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣7⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Kwanaki uku da tayi gidan Faty yazo mata da wani irin canji,  har mamakin nishadin da take ciki takeyi. Sai take ganin rayuwarsu kamar lokacin da suke gida kafin suyi aure.  Suci abinci tare,  bacci tare,  sannan gashi ya Ahmad duk sanda xai shigo saiya shigo mata da abun kwadayi,  yakance me ciki ba a rabata da kwadayi, sai kace shi xa a haifawa dan.  Amma aduk sanda ta tuna xata koma gidan Badaru sai jikinta yayi mugun sanyi sannan gabanta yayi ta faduwa. 


Rana ta biyar a gidan Faty wanda ya kama da satin Badaru daya a Lagos,  da yammaci suna zaune ana hirar da aka saba anata dariya.  Mimi zaune a gefen Faty akan kujera 3 sitter tanacin guava,  yayin da ya Ahmad ke gefensu akan kujera 1 sitter yana basu lbr sai dariya suke. 



Badamasi yayi sallama ya shigo,  Mimi na ganinsa gabanta ya yanke ya fadi.  Nan take nishadin da take ya qare kuma duk wanda ke parlourn ya lura da wannan canjin na Mimi.  Ko Badamasi bai fada ba tasan Badaru ya dawo kuma xuwa yayi ya maida ita kamar yadda ya alqawaranta. 


Suna gama gaisawa ya fada musu labarin dawowar Badaru tun safe,  kuma yace yaxone ya maidata gidan.  Ya Ahmad ya katseshi da cewa "shi maiyasa bazaizo ya dauki matarsa ba?  Sati daya baka gari?  Inka dawo ai iyalinka ya dace ka nema kaji lfyarsu,  ko akuya ka bari da ciki sati daya inka dawo ai ka binciki lfyarta.  Wannan abunda yakeyi sam babu tsari a cikinsa,  na kuma gaji dab nake da indau mataki akai " ya qare maganar cikin bacin rai 😔. Badamasi ya bude baki da nufin kareshi ya Ahmad ya tsai dashi "karkace komai,  nasan halinsa kuma shirun da akai masa baya yana nufin Mimi bata da gata bane, kawai muna kau da kaine saboda iyayenmu" Faty na gefe na share hawaye .



Sha tara ta arxiqi suka hada mata,  kamar wacce xatai tafiyar shekara.  Har Badamasi ya dunga jinjina soyayyarsu ga Mimi. Faty bata fito rako Mimi ba saboda kuka da take bataso tasa mimin kuka itama,  sai ya Ahmad ne ya tsaya aka loda kayan a bayan motar sannan ya kawo kudi ya bawa Mimi,  har anrufe motar ta fito da gundu ta fada jikin ya Ahmad tasa kuka ya kamo fuskarta ya share mata hawaye yace "maryam kici gaba da haquri Allah ya na tare dake,  baxaki taba tabewa ba a rayuwarki" ya bude motar ya sakata suka tafi. 




*****       *****        ******

Bata canja xani ba rayuwar da suke a baya itace dai,  gashinan abun babu tsari kamar a jahiliyya period.  



Kimanin kwana 11 da dawowarsa daga Lagos kenan daren ranar suna kwance,  ya hauro kanta yasa qarfi ya danneta.  Kimanin sau uku kenan yana  yin hakan,  inya gama buqatarsa yaji bai gamsuba yayita zaginta yana ci mata mutunci. 



Yanxun ma hakace ta kasance,  ya shigeta da dukkan qarfin da Allah ya bashi.  Taji xafi kwarai harta kwallah qara,  yaja dogon tsaki yace "qarar me kikemun?  Wai nufinki xafi kikaji?  Abunda duk kin bude kin tale,  innaxo shigarki kawai ji nake na rufta babu wata madatsa 😳🙈 shine har xakice kinji xafi?" 


Tai qasa da murya"wlh Badaru tun lokacin da ciwon sanyin nan ya samemu inkanayi ji nake kamar kana xubamun yaji daurewa kawai nakeyi,  da kabari naje asibiti da tuni mun warke."  cikin hargowa da daga murya yace "ya sameki dai, dan ni tuni na warke,  ai nakawo miki magani kikaqi amfani dashi ke lallai sai na asibiti ko Baturiyya? To wlh baki isa ba dan mugunta kin hanani inji dadi dake?  Wlh wlh whl yau ko xanyi sau dari sai naji dadi xan kyakeki ya rage naki"



Yana kaiwa nan ya farmata kota ina juyata yake yayi,  tun tana jin xafi harta denaji.  Numfashinta ya fara gazawa. Batasan iya lokacin da ya shafe yana durxarta ba,  ita dai tasan yayi mugun dadewa yana abu daya.  Sannan ya sauka ya koma gefe ga dukkan alamu gajiya yayi bawai biyan buqatar ya samu ba. 



Kukansa ya dawo da ita hayyacinta,  inda cikin kukan takaici yake cewa "maryam kin cuceni, kin xalunceni,  ni zakiyiwa haka ko?  Ni zaki hana jin dadi dake ko?  Kimanin wata daya kenan Kullum cikin buqata nake kin kasa biyamun ita.  Kije Allah ya isa ban yafe miki ba,  in Allah ya yadda bazaki gama da duniya lfy ba. KE MARYAM ALLAH YA TSINE MIKI." 😳😳😳😳



Jin furucin Badaru na qarshe yasa tai xunbur ta miqe,  tare da cewa "Badaru me yayi zafi haka??? 😳" ya bata amsa da cewa "ubanki ne yayi zafi" yana fadar haka ya fita daga bedroom din. 



Wani irin yanayi ta shiga ita ba matacciya ba ita ba rayayya ba.  Kukan ma ta kasa,  tsinuwa daga mijin aurenta?  Akan abunda bata da iko akai? Tab akwai matsala.  Saboda da gajiyar dirxar da Badaru yayi mata batasan sanda bacci ya kwasheta ba.  Sai ana kiran sallatu ta farka,  qasanta wani irin xugi yake mata kamar ansa reza an ketata taje tai wanka tai sallah ta roqi Allah sauki da gaggawa kan halin da take ciki. 


Sukuku ta yini saboda tsinuwar da Badaru yayi mata ta taba xuciyarta sosai, ta qudure a ranta inya kunna inji da dare ta samu chajin waya xataiwa ya Faty maganar infection din ta kawo mata Magani, domin wulaqancin ya isheta haka gara ta naimi magani ya dunga samun biyan buqata axauna lfy domin ita batasan tashin hankali (Allah sarki rayuwar ya mace,  Kullum cikin sadaukarwa namiji take.) babu abunda ta iyaci ranar illa ruwan lipton da lemon tsami. 



Ta idar da sallar laasar,  tadan kwanta kan sallayar tana azkar,  ta qudure aranta yau laraba intasamu dan aike xata bashi kudi yayi mata sadaka domin yau yini tayi gabanta na faduwa. Bazai wuce hudu da rabi ba 4:30 lokacin da taji dawowar Badaru, tayi mamaki kwarai dan bai cika dawowa haka ba sai inda muhimmin abu da xaiyi. 



Ya wuce daki fuu sai gashi da tulin kayansa masu dauda. Ya fita tsakar gida,  sai gashi ya dawo ya danqi gashin kanta ya fita da ita,  ya nuna mata tulin kayan wankinsa yace "ga wanki nan kiyimun,  tunda baki iya biyamun buqata ba kimun wanki,  dan baxan dunga baki abinci a banxa ba" tai tsam sannan tace "to kayi haquri kaga nawa ma bayi nake amma in ya Faty ta aiko karbar nawa wankin in shaa Allah xan hada maka da naka." 



Ya danqi wuyanta ya hadata da bango, sannan cikin huci da tsabar tsanar yace "ke kin isa insaki aiki kice baki ba? Wlh baki isa ba,  na tsaneki wlh da inka kashe rai babu wani hukunci a kanka da kece mutum ta farko da xan fara kashewa,  maryam ban taba tsanar wata halitta a duniya kamar ki ba.  Saboda haka dole kimun wanki dan ubanki"  ta fusge wuyanta tayi gefe ganin yana shirin kaita lahira, tana maida numfashi tace "wanki bazanyi ba kisa kuma bisimillah ka kasheni." cikin bacin rai take furta wadannan maganganun domin ranta yakai matuqar baci da xagin da Badaru kewa ubanta.  



Kafin ta ankara ya tsinka mata mari ji kike kau! 😳 tayi baya cikin azama ya dora da cewa "lallai wuyanki ya isa yanka? Yauni kike maidawa magana?  To dan ubanki...... "ta tari numfashinsa kafin ya qarasa. "karka kuma xagin ubana domin nasan darajarsa,  kuma da yana raye wlh bazan auri wanda besan darajar iyaye kamar ka ba,  maraicine ya jawomun"


Ya kuma dauketa da wani gigitaccen mari,  "na xagi uban naki bayan xagima na dakeki dan haka kije ki haqoshi daga kabari yazo ya rama miki."  ta dago idonta jajur " ka mareni?  Wlh komai daren dadewa saina rama,  wannan alqawarine na yiwa kaina." 



Ya ja hannunta qiiiiii ya bude gidan ya turata waje ta fadi dabas.  Sannan yace "ai basai andade ba kije yanxu ki tasoshi daga kabari kuxo ke dashi ku hadu ku dakeni,  kije na sakeki kuma Allah ya isa tsakanina dake in shaa Allahu bazaki gama da duniya lfy ba." 



Ya maida gidansa ya rufe,  yabarta zaune babu takalmi babu mayafi. Kuma dai dai lokacin hankalin mutane ya fara dawowa kanta, aka zagayeta ana kallonta tai qasa da kanta taji duk ta muxanta. Ya qara bude gidan ya wullo mata hijabi da wayarta,  jehowar da yayi tasa wayar taci screen. Ta miqe tasa hijabin qafarta babu takalmi gashi bai bari ta dakko kudi ba dan shiga Mota. 




Har ta fara tafiya wata maqociyarta yar dattijuwa wacce yayanta ke shiga gidan Mimi ta biyota a baya ta tsai da ita,  tace "maryam yanxu akaje aka sanar dani abunda ke faruwa, kiyi haquri indai baki cuceshi ba Allah saiya saka miki AURAN BAYA SADAKIN NA GABA." ta cire takalmin qafarta ta bawa Mimi tace saka ki tafi Allah ya hada fuskokinmu da alkhairi,  ta juya ta tafi tana kuka dan tana qaunar Mimi.



Cikin wani irin yanayi take tafiya,  tafi kama da mahaukaciya sabon kamu sam ba kuka take ba, idonta da xuciyarta sun bushe qaraf.  Jinta take ita ba matacciya ba ita ba rayayya ba,  abun kamar almara aurenta ya mutu cikin wata biyar da kwana shida kacal da yin auren.  Batasan mutuwar aure sam koda akan maqiyinta bare a gida irin nasu wanda bata taba ganin ko yaji anyi a gidanba.  Ita kuma haka QADDARARTA take,  andade ba ai aure ba,  anyi ba a dade ba ya mutu.  Tasan qalubalene a rayuwarta qatoto,  wlh duk ixayar da take ciki gara ta haqura ta xauna da Badaru da ace aurenta ya mutu. Koda kuwa takata zai dungayi yana wucewa. Kuma da tasan zai dauki matakin saki akanta wlh da gara tayi masa wankin. 



Saboda tashin hankalin da take ciki yasa bataga nisan tafiyar gidan Badaru xuwa titi ba, kawai ta tsinci kanta a bakin titi.  Ta tare dan sahu tace kaini yahya gusau (gidan ya Faty) dan koda wasa tasan bazata iya tunkarar gidan Baffa ba (gidansu) 



Har bakin gate din gidan ya kaita kasancewar gidan a bakin titi yake.  Ta sauka tace bari in kawo maka kudin. 



Faty na zaune a parlour tanashan golden morn taga fadowar Mimi parlour kamar an jehota,  ta miqe a razane tace "lfy Mimi,  jikin naki ne ya tashi?" nabar dan sahu a waje ban bashi kudin ba" itace amsar da Mimi ta bawa Faty,  tana fadar haka ta shige bedroom din ya Faty. 



Bayan Faty ta sallami dan sahun,  ta riski Mimi a bedroom dinta kwance kan gadonta tace "Mimi ki fadamun abunda ke faruwa na ganki a hargitse haka" dakyar ta daga ido saboda tsabar ciwon da kanta ke mata,  a taqaice tace da Faty "ya sake ni" ko kalma daya bata qara akan haka ba ta koma ta kwanta kan Royal bed din Faty.  Sama sama ta dunga jiyo salati da sallallamin fatyn.  



Har akai sallar magriba ana gab dayin ta isha suna zaune a gurin da sukai sallah jugum jugum.  Suna idda sallar isha Mimi ta kuma hayewa gado ta qudundune mugun sanyi takeji saboda zazzbin da ya rufar mata. 



Duk yadda Faty tayi da Mimi taci abinci taqi ci,  domin batajin ko maqogaronta abinci zai wuce,  saboda wani irin malolo takeji a maqogaron shi beyi gaba ba shi beyi baya ba.  Kuma itama Faty da take maganar itama bataci abincinba. Ta hado tea ta miqawa Mimi tace "karbi kisha kodan abunda ke cikin ki" ba musu ta karba tasha. 



A haka Ahmad ya riskesu,  dawowarsa kenan.  Ya shiga har bedroom din yace "lfy Faty?  Mimi jikin ne ya kuma tashi?" duk sukai masa shiru, Mimi tacigaba da shan tea din ya kalli Mimi " Mimina lfy?  Ko muje asibiti?" nan ma shiru ya kuma kallon Faty yace " Faty na kiyi magana mana lfy?" a hankali Faty ta furta "sakinta Badaru yayi".



Ga mamakinsu sai sukaji Ahmad yace "ALHAMDULILLAH " nan take fuskarta ta nuna tsantsar farin ciki,  dukkansu suka saki baki suna kallonsa. 



Ya ajiye jakarsa ta office akan side bed, sannan ya haura kan gadon ya kwantar da kan Mimi a kafadarsa yace "maryam ki godewa Allah da ya rabaki da Badaru,  domin bai dace da samun salihar mace irinki ba,  MARYAM keep praying in shaa Allah sai kinsamu mijin da baki taba mafarkin samu ba haqurinki bazai tashi a baxan ba" 




Ita dai bin kowa take da ido ga alama ta samu kurumta ta wucin gadi.  Haka suka kwana gado daya da Faty,  inta fara bacci sai ta farka a furgice sai dai Faty ta tofa mata addua ta maida ita ta kwantar.  Ya Ahmad kuma kwana yayi yana nafila yana roqawa Mimi waraka gurin ubangiji,  in yai sallama ya shiga dakin da suke kwance,  yaga halin da suke ciki,  a duk sanda ya shiga Mimi kanyi xunbur ta miqe zaune alamun a firgice take sai dai ya maida ita ya kwantar ya tofa mata addua.  Da haka har suka wayi gari. 




HAPPY EIDIL FITR,  TAQABBALALLAHU MINNA WA MINKUM.  

Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣8⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)


A bangaren Badaru kuwa,  sai bayan ya saki maryam sannan fargabar abunda zai biyo ta bangaren Abbansa ya shige shi. Amma daya tuna yanda ya tsani maryam da yacce ya suqe da xama da ita sai yaga ai yanci bana rago bane.  gara kawai da ya saketa komai xai faru ma ya faru. 


Ana iddar da sallar isha, ya hada tea murtuk ya soya kwai 5, kamar shi ya siya.  Ya dake cikinsa sannan ya sheqa wanka ya xaba shadda,  ya samu turaren Mimi ya feshe jikinsa da shi.  Ko lura da cewa turaren mata ne bayi ba. Yaywa gidan su Nafee tsinke. 


Tare suka fito da dan aiken da yaje kiranta kamar jira take,  ko gaisawa bata bari sunyi ba ta fara qorafi "Badaru anya kuwa kana sona?  Anya kuwa xaka aure ni?  Nifa na fara yadda da maganar mutane da suke cewa yaudara kake"


Ya danyi dariya 😄 yace "Nafee ko gaisuwa babu za a fara da qorafi" tace da maganar na yini tana damuna.


Yace to "ki fara shirin bikin ki nan da wata biyu masu xuwa" ta waro ido tace "bayan sallah fa kenan" yace kwarai kuwa tace "wace sallah?  Yace wacce sallah ke gabanmu yanxu? "  tace in nayi lissafi dai dai qaramar sallah kake nufi domin yau kwana 8 ko 7 ya rage a fara axumi"


Yace yawwa yar gari,  kin gane kenan.  Ta daka tsalle tace "da gaske?" yace "wlh da gaske nake"  ya qara murmusawa yace "kuma daya albishir din da xan miki shine : ke kadai ce dani yanxu" tai far 🙄 tace "kamar yaya?" yace "mun rabu da maryam daxu" 



Wannan karon tanayin tsallen ta fada jikinsa (kuji rashin kamun kai) ta qanqameshi duk kuwa da cewa basu taba hakan ba.  Yayi saurin cireta a jikinsa jin yana shirin loosing control.  Wannan dare haka suka sha hirar soyayya cikin nishadi saboda matsalarsu ta tafi (maryam) tare da hirar yadda aurensu xai kasance. 

*****   ******    ******    *****


Karfe taran safe 9:00 am a gidan kakanninsu tayi musu bisa shawarar Ahmad da kuma rakiyarsa,  domin ita kanta bai yadda da nutsuwar Faty ba a lokacin shi yasa ya hanata driving.  Yasan tunkarar Baffa da lamarin mutuwar auren Mimi ba karamin balli zai tayar ba,  shiyasa yace abi abun takan surukan Baffa ko zai zo da sauki. 



Babba gidane me cike da kango a da,  amma yanxu da yayansa suka xama wasu sun bigeshi sun maidashi na tsamani da tsari.  A katafaren parlourn gidan sukai masauki hajja na kan kujera, yayinda mal manu kekan well chair ( saboda girma baya iya tafiya)



Tiryan tiryan Faty tai musu bayanin lamarin tun rashin lfyar maryam da kuma halin data tsinceta a gidan Badaru  har xuwa jiya da auren ya qare.  


Hajja tunda aka fara take share kwallah,  mal manu kuwa baice komai ba sai wayarsa daya dakko ya kirawo mama yace ta sameshi gida yanxu,  sannan ya kira Baffa ma ya fada masa. 



Tana gurin aiki kiran ya risketa,  dan haka ta kasa nutsuwa. Tasan ba qaramin abu bane zaisa Baba kiranta a wannan lokacin,  sai ta barwa kanta kawai Hajja ce ba lfy. Taje office din Principal din ta naimi excuse ganin bata taba hakan ba kuma da alama a rude take yasa ya barta. 



Kusan tare suka iso da Baffa,  domin shigarsa kenan taxo.  Ganin motarsa a kofar gida yasa ta qara rudewa.  Tana saka kai parlourn gabanta ya yanke ya fadi,  dan ganin Mimi ta tsummace rabonta da ita tun randa aka kaita gidan miji (halayyar uwa ta gari bata xuwa gidan yayanta sai da babban dalili) ta samu gefen centre carpet ta xauna. 


Faty ta kuma yi musu bitar abunda ya faru tas (dan ma Mimi bata fada musu waye haqiqanin Badaru ba da irin azabar da yayi mata). Baffa ya miqe ya watsawa Mimi kallon kinwa kanki,  dagani akwai magana a bakinsa kuma bai yarda da abunda Faty ta fada ba,  amma ganin idon surukansa yasa bece komai ba.  Yace "ni natafi kasuwa dan nakusa makara"



Mama ta kasa dauriya da abunda ya samu Mimi tasa kuka,  hajja da tun dazu take kukan itama ta qara volume  Faty itama tasaka nata kukan.  Mimi ganin mama da Faty na kuka (mutanen data fiso fiye da komai) itama ta saka nata kukan (tunda abun ya faru sai yanxu tayi kuka.


Kamar jiran nata kukan suke, kowa yayi shiru da nasa kukan parlourn yayi tsit  sai sautin kukanta.  Faty ta yunqura xata tashi taje gurinta mal manu yayi mata alama ta zauna.  Sai da tayi 43 minutes tana kuka baji ba gani,  sannan tayi shiru dan kanta.  


Mal manu ya garo kujerarsa yaxo kusa da ita ya dafa kanta "MARYAMU kiyi haquri kinji, wata rana sai lbr,  haqiqa mijinki ya cutar dake,  amma kiyi haquri wlh duk wanda ya toxarta aure saiya wulaqanta, sakayyar aure a duniya Allah ya ke yinta. Allah ya baki wanda ya fishi,  in shaa Allah wannan hawayen da kika xubar a dalilin baqin cikin aure sai Allah ya sa kin xubar da hawayen farin ciki fiye da wannan, Allah ya albarkaci rayuwarki" duk suka amsa da Aminnnnnnnn



Faty ta miqe xata tafi gurin aiki,  mama ma ta miqe.  Mimi tai saurin tashi tabi bayan mama. Hajja tace "maryam da kunyi xamanki anan kin dan murmure bakyaje wannan gidan naku  haka ba suyi ta kasaki a fefe ana tallanki.  


Mama tace "Hajja barni intafi da ita,  hankalina sai yafi kwanciya" Mal manu yana jinsu yayi musu shiru domin daga uwar (mama) har yar (Mimi) tausayi suke bashi. Sai yake ganin rayuwar Mimi kamar ta mama acan lokacin da ya wuce,  tabbas tarihi yana shirin maimaita kansa akan Mimi.  Yana fata itama nata qarshen labarin yayi kyau (Mimi) kamar inda na fadimarsa yayi kyau. Yanason yarinya fiye da duk jikokin da yake dasu, yana ganin wasu halayyar MARYAM (matarsa Hajja) a tare da Mimi kamar haquri da sanyin hali,  biyayya da kuma ibada. Kai hatta tafiya Mimi irin ta hajja take yi,  afuskane kawai basa kama (tafi kama da mahaifinta AL AMIN,  kamar photocopy dinsa ce) yana wannan tunanin har suka fita tsakar gida.  Ya kwalawa mama kira "Fadimatu" ta amsa "naam Baba"



Ta sameshi yace "duk sanda kikaga tana kuka karki hanata, kibarta tayi ya isheta,  baqin cikin zai ragu. Rashin kuka alokacin da abun kuka ya sameka kan illata lfyar kwakwalwa,  shiyasa daxu na barta tayi kukanta,  tashi kije Allah ya yi muku albarka ke da zuri ar ki" tace amin Baba Allah ya saka da khairan.


Umma kawai suka samu a tsakar gida tana yanka salak,  ta tashi ta bisu har daki tana cewa "maryam meya sameki haka duk kika tsummace?  Jiya nake cewa baffanku ya kamata aje a ganoki, tunda aka kaiki babu wanda yaje (kuji qarya)"  sukai mata shiru har ta gama surutunta.  Daga dakinsu gurin Anty ta nufa ta kai mata kanun labarai,  tun kafin a gama fada mata ta nufi dakin mama. 


Tana xuwa tace "maryam!😳 yanxu cikin ne yasa kika tarkato kika taho gida? Yara qannan bayanki suna gidan miji a zaune inma cikin ne sai dai mugansu dashi ya girma? Koda yake da alama cikin na wahalar dake duba da yadda duk kika qare,  yo uwarki ce har yanxu bata daina abun mutanen da ba,  wai ita kunya bata xuwa gidanku mu ba haka muke xarya gidan namu yayan ba" itama har ta gama haukanta basu tanka musu ba.  Mama ta tashi tana tunanin hali irin na matan gidan wai ai wata biyar ba a ga mutum ba, amma in anganshi ko irin nuna murna nan ta yaushe gamo. 



Mama ta dumamawa Mimi tuwon shinkafa miyar kuka tasa yajin daddawa ta isketa har bedroom kwance a saman gado ta kai mata "mimina tashi kici" ta girgixa kai alamar bataci mama ta hayo gadon ta dagata ta zaunar da ita tace "nasan mutuwar aure Mimi, nasan ciwon sakin aure.  Musamman saki irin naki na wulaqanci amma babu yadda zaki da hukuncin Allah,  barin kanki da yunwa bashine solution ba." ta karbi tuwon ta faraci,  mama ta qura mata ido tana kallonta,  tana son gano cikin da akace Mimi tana dashi.  Ita sam abun bai mata dadi ba,  dan dai babu yacce xatai da hukuncin Allah ne. 



Acan kasuwa kuwa Baffa yini yayi yana xirga xirgar neman Badaru, tun yana xuwa da kansa har ya gaji ya dunga aika yaransa.  Sai dai amsar dayace baixo kasuwa ba yau,  kuma abun kamar hadin baki shima abban Badaru yau be zoba. Kuma Badaru yaqi xuwa kasuwar ne saboda yasan sai Baffa ya nemeshi. 



Koda ya koma gida bai nemi mama ba duk kuwa da cewa ita keda girki,  ta karbi girki da yamma.  Wanda hakan ke nuna laifin Mimi ya shafeta,  itama ta fison haka.  Tasa yarta da jikanta (Dady dan Faty wanda ke xama a hannun Maman) agaba sukai kwanciyarsu. 


Sai dai yadda Mimi ta kwana jiya, haka ta kwana yau.  Ta dunga farkawa a firgice, kuma duk farkawar da tayi xataga mama xaune tana kalkonta. Farkawa ta qarshe da tayi tasamu mama tana sallah. Ita sai yanxu ta tuna in masifa ta sameka kana addua.  Dan haka ta miqe taje tayo alwala ta fara sallah kamar motsatstsiya,  duk sujjadar da tayi takance "ALLAH HUKUNCINKA NE WANNAN BANYI FUSHI BA,  ALLAH KA QARAMUN JURIYA"



Da sassafe Baffa ya yiwa gidan alh inuwa tsinke,  yana bacci xuwan kiran Baffa ya iskeshi. Sama sama suka gaisa Baffa ya karanta masa abunda Badaru yayiwa Mimi.  (saboda da abun ya tayar masa da hankali, abunka da wanda ba a taba sakarwa ya ba). Wata irin kunya kunya ta rufe alh inuwa,  ya tashi ya shiga gida yace da Baffa yana xuwa. 


Yasamu Umma a kitchen ya labarta mata abunda Badaru yayi,  gabanta ya yanke ya fadi ta xauna dabas a qasa tana sallallami tace "alh meye abunyi yanxu?  Har Badaru yayi saki ba tare da saninmu ba. Maxa kirawoshi yazo ya maida ita tunkan abu yayi nisa" ba musu ya dakko waya,  dan shima abunda yake shirin yi kenan.  


Dajin kiran ABBA da sigar da yayi masa magana, yasan lbrin sakin ya ruskesu.  Saboda haka ko wanka beyi ba ya tashi ya nufi gidansu yana qudurce cewa sai dai ayi duk wacce xa ai amma wlh ya gama xama da maryam. 



Dake Bahaushe yace baya bata da kadan,  be dade da fita ba mumy (Adda halima) yayar mama da Faty suka yiwa gidan tsinke.  Sukai sa a yabar muqullin a gurin wani me shagon kofar gidan,  suka shiga suka kwashe duk wata kayan sakawa na Mimi (suturu)  mumy taiwa wani me furniture waya yaxo ya kwashe kayan dakin ya siya kuma ya siya da daraja tunda sababbi ne kuma sun samu kulawar Mimi.  Kayan Badaru dake drawer mumy tasa Faty ta dau akwatin Mimi daya ta loda masa kayansa a ciki.  Kayan da tayi amfani da su kuwa kamarsu tukwane,  tea flask da food waemers, jugs cups plates duk tasa aka dunga rabawa maqota. Kayan abinci kuwa dana tea da lemuka duk tace a bar masa duk da kuwa Faty ta fada mata bashi ya siya ba, shinkafa kawai yake siya a gidan,  mumy tace duk hada ki bar masa Faty shine matsiyaci,  mukam ai bamu gaji tsiya ba. Ai mun auna arziqi tunda ya sakar mana yar. Dan ni dama gaba daya Badaru be mun ba a mijin Mimi.  


Maqota da aka basu kaya suka dunga shigowa godia,  suna yaba hallayar kirki irinta Mimi da alhinin rabuwa da ita,  wasu harda kuka sunai mata fatan alkhairi.  Wanda ya sayi Kayan yana gama fita dasu suma suka fito hannun Faty dauke da system (laptop) din Mimi da fos dinta suka qulla gidan suka bawa mai shagon muqullin,  drivern mumy ya loda kayan a mota dake seinna ce tas ta dauke suka shiga suka tafi. 



Badaru kuwa yana xuwa bai shiga gidansu ba,  saboda kar Umma ta takura masa ya mayar da maryam,  direct sitroom ya nufa gurin abbansa da Baffa ya gaishesu cikin daure fuska dan karsuce lallai ya maida Mimi.  Abbansa cikin fada ya fara yi masa jawabin abunda Baffa yazo dashi,  bayan ya gama ya bashi umarni da ya maida Mimi dakinta.  Badaru ya motsa ya qara daure fuska yace "gaskiya abba kayi haquri nagaji da xama da ita,  yarinyar Sam bata ganin girmana duk tsawon wannan lokacin haquri nake da ita" Baffa da yazo da nufin ciwa Badaru mutunci akan sakin Mimi yayi saurin sakkowa jin Badaru yace bazai maida Mimi ba. Cikin sanyin murya yace "haquri xakai Badaru duk matan haka suke duk wanda ka ganshi da matarsa sun dade haquri yake da ita" ya fada cikin qanqan dakai.


Badaru ya qarayin fuskar shanu yayi burus da lallashin da Baffa ke masa yace "Baffa tunda na auri maryam ban isa insata abu tayi ba,  Kullum cikin yimun gorin ilimi take wai ta fini ilimi.  Yanxu kuma akan bautar qasa ta tada balli wai sun kusa tafiya,  nace ta bari lokacin yayi inga yacce za ai sai kawai tahau xagina wai bansan darajar ilimi ba.  Dan haka ni na haqura da ita taje can ta auri wanda yasan darajar ilimi" hmmmmm (ni kuwa nace kuji qarya)  ya ciro takadda daga aljihunsa ya miqawa Baffa ga takaddarta nan,  dan Allah suyi gaggawar xuwa su kwashe kaya saboda xan saki gidan in karbe ragowar kudina. 




Baffa ya bishi da kallo har ya bar gurin, cikin yaba rashin kunyar Badaru.  Amma kuma baiga laifinsa ba tunda ya xayyano abunda Mimi tayi masa dole ya fusata.  Abbansa ya dubi Baffa "to alh kaji abunda maryam tayi masa, bata kyauta ba sam inai mata kallon mai hankali.  Inaga yanxu muyi haquri da batun kome tunda ya ruga ya fusata,  inda rabon xama gaba a sasanta."(kuji tsabar san kai)  Baffa bece komai ba sai gyada kai yayi ya tashi ya fita. 



Badaru na shiga gida,  ya tarar da ummansu a kofar sitroom din a tsaye idonta cike da kwallah.  Ga dukkan alamu taji duk abunda ya wakana.  Yana shiga ta fidda hannu ta tsinka masa mari,  wanda hakan yayi dai dai da shigowar abbansa. Ta kalkeshi tace " wlh tallahi nasan maryam bazata taba aikata abunda ya fada ba,  sharri yayi mata.  Ai suffar macen da xatayi hakan daban take.  Maryam ka saka ko Badaru?  Macen arziqi,  baka kyautawa kanka ba inajin kamar yar cikina aka saka,  inason maryam.  Kuma wlh sai kayi nadamar rabuwa da maryam. Kaje duniya ce" Abban ya daka mata tsawa "ke!  Karkiwa dana baki akan wata maryam, ko shi kadaine ya taba sakin aure?" itam ta daka masa tsawa cikin fusata tace anyi masa,  ko ka fini sansa ne.  Badaru sum sum ya fice ganin abun nasu zai zama fada. 


Ko daya koma gida yaga gidan fayau kuma yaga tulin kayan abincin da suka bar masa harda kyautar akwati sai duk jikinsa yayi sanyi,  amma daya tuna da Nafee da kuma soyayyarsu sai yaji wani kwarin gwiwa ya shigeshi. 

******** ********************



Baffa ya riga su mumy isa gida,  ya iske mama a gida bata fita aiki ba dan bata da kwarin gwiwar yin hakan.  Lokacin wajen 10:30 na safe,  yaran gidan duk sun tafi makaranta sai masu aikin gidan tsofaffi guda biyu wadan da ke wanke wanke da shara. Ya tsaya a tsakar gida ya kwallawa mama da Mimi kira, gabansu ya fadi a tare dan yanayin kiran kawai xai fada musu abunda kiran ya qunsa. Suka fito Mimi ta tsuguna mama ta tsaya daga gefensa,  matan gidan ma duk suka fito.  Ya kalli Mimi ya daka mata tsawa "keee!  Kinwa kanki daga gidan iyayen mijinki nake naje naji irin rashin mutuncin da kika shuka har ya sakeki,  kin cuce ni kin batamun tarihin gida,  ba a taba bazawara a gidana ba sai a kanki, wai har kece kike zagin mijinki na aure akan xaki tafi hidimar qasa.  Irin tarbiyar da nai miki kenan?  To tunda kinqi xaman gidan aure akan bautar qasa bazakije bautar qasar ba in anfara tafiya,  kuma tunda kika dawomun gida a matsayin bazawara bazaki huta ba.  Ya kalli shashin da yan aikin ke tsaye cirko cirko yace ku! Na hutar daku,  kuma xanci gaba da biyanku albashinku,  kubar mata aikin daga yau na maidashi doka tayi shara tayi wanke wanke kuma tayi girki, ya wulla mata takardar sakin a fuskarta yace ga certifacate dinki nan na xaman gida kitashi ki fara aikinki tun daga yanxu.  Ya kalli shashin da mama take yace kuma duk wanda ya sabamun doka akan aikin dana sakata Allah ya isa"



Kowa ya watse wasu cikin farin ciki wasu akasin haka,  Mimi ta nufi bakin famfo ta tara ruwa ta fara tulin wanke wanken,  sam idonta babu digon kwallah. 



Bai dade da fita ba,  su Faty suka shigo.  Drivern ne ya shigar musu da tulin a kwatinan Mimi,  sannan suka zauna ana gaisawa.  Faty tace "mama ina Mimi xan bata fos dinta" Maman tace tana waje tana wanke wanke,  mumy da Faty suka hada baki sukace "wanke wanke kuma 😳" Faty taci gaba da cewa waya sata wanke wanke ina masu aikin gidannan? " 


Baffanku ne ya sakata,  yanxu yazo yana fada yaje gidan su Badaru har sun bashi takaddar ta,  shine ya dora mata aikin gidannan gaba daya.  Faty najin haka ta dau jakar xata tafi,  mumy tace mata "Faty ki zauna ki huta mana"  ta kalli mummy idonta taf da hawaye tace " me xan xauna nayi mumy Baffa na shirin kashemun yar uwa.  Kuma wai mama tanaji tana gani baxatai magana ba" tasakai ta fice. 



Mumy ma ta miqe,  ta kalli mama kanta a sunkuye,  ta miqa mata tulin kudi "gashi kudin kayan dakin Mimi ne dana siyar ki ajiye mata" mama tace to akwai na sadakinta ma a hannu sai inhada mata. 


Mummy ta nisa ta fesar da iska cikin bacin rai tace "lokaci yayi da xan hada alh Buhari da human right akan abusing din maryam da yake yi (qungiyar kare haqqin Dan Adam)" mama ta xaro ido jin abunda da Adda halima tace.  Cikin sanyin jiki tace "Adda kiyi haquri ku gyaleshi yarsa ce yana da iko akanta" mummy ta daka mata tsawa " daallah yimun shiru shashasha ki zauna ya kashe miki yaya da bakin ciki sukenan kike dasu,  shi bashi da asara.  Wlh fadima inbaki tashi kin kwatarwa yayanki yanci ba wlh saina hadashi da human right" itama ta juya ta fice. 




Har inda maryam ke wanke wanke taje ta dafa bayanta,  ta dago ganin mumy yasata yin murmushi,  mumy tace "mamana kiyi haquri na ya qare akan lamarinki acikin gidannan na kusa in kwatar miki yanci kinji."  tace " to mumy ai ba komai ma wata rana bazan ba, wata rana ko ganina saiya gagara sai dai aje kabarina ayimun addua"  tace hakane Mamana Allah ya saka miki,  Allah ya albarkaci rayiwarki amma kafin ki mutu in shaa Allah sai kinji dadin rayuwa. 



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 2⃣9⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)


A hankali aikin da Baffa ya dora mata ya fara xamar mata jiki,  duk kuwa da farko tana ganin wahalar aikin.  Gidansu babban gidane wanda shararsa kawai aikine,  sannan ga uban wanke wanke saboda yini ake da fita da abinci daga gidan domin adadin mutanen dake karbar abinci a gidan suna da yawa. Ko dattijan da suke aiki a gidan (masu wanke wanke da shara) sau tari aikin yawa yake musu, sannan ga wanke toilets din dake tsakar gidan.  Batun girki kuwa dama da coal suke yinsa bisa manyan tukwanen tasa,  kuma me girki ita keyin girki sai dai masu aikin su tayata da wanke wannan yanka wancan.  To lokaci daya Baffa ya dorawa Mimi duk wannan aiki. ( qalubalenku iyaye, miji ya wulaqanta yarinya ko kuma ya korota ku iyaye memakon ku karbi qaddara ku kwantarwa da yarinya hankali,  a a sai a tsiri muzguna mata da sunan hukuncin ta naqin xaman aure. Wlh kuji tsoron Allah irin haka inba a samu me hangen nesa ba kome haquri sai ta gudu ta shiga duniya.  Haba ai abun yayi yawa gidan miji ba dadi gidan iyayema ba dadi) Da yake tana da qarfin zuciya duk sai aikin yaxo mata da sauki. Takan tashi tun asubar fari ta fara shara,  ana kira taje tai sallah da azkar sannan ta dora breakfast ta zauna wanke wanke.  Bakwai da rabi na safe ta gama breakfast sannan ta rabawa yan makaranta ta wanke bandakuna, taje gaida Baffa wanda intaje baya amsawa sai dai cin mutunci da gorin zawarci da yake biyo baya. Kafin taje gyara dakin mama takan tarar Maman ta gyara ta wanke toilet a qoqarinta na ragewa Mimi aiki.  


In mama ta tafi aiki takanji gidan yayi mata xafi bata samun sukuni sai 11 tayi lokacin da take dora abincin rana ko kuma in dady ya dawo daga skul ya zauna yayi tayi mata shirmen yara ko kuma tayi masa homework. 


Kafin kace meye wannan lbrin mutuwar aurenta yayi fitar dango,  ta hanyar Anty da Umma.  Karma Anty taji lbr domin gida gida take aiken mutuwar auren Mimi,  kamar me rabon katin biki.  Inda kuma baxata iya xuwa ba ta buga waya ta fada.  Har gara Umma takan boye farin cikinta akan mutuwar auren, amma Anty a fili take nuna murnarta.   


A irin hakan lbr ya riski fauxa  qawar Mimi wacce suke maqota na kusa,  da farko bata yarda ba a ganinta in hakane Mimi xata fada mata.  Dan haka taje gidan da kanta,  ta iske mugun lbr kuwa domin ganin da taiwa Mimi tana tulluqar aiki ya tabbatar mata da ingancin maganar. 


Can cikin dakin Mimi (dakinta na yan matanci) suka qule. Fauxa ta riqo hannunta Mimi ta bude baki xatayi magana fauxan ta tsaidata tace "basai kince komai ba qawata,  nasan halin da kike ciki ni da ke qadadarar da Allah ya dora mana kenan. Allah ya sa muci jarrabawa" ta fada tana share hawaye, Mimi ta goge mata hawaye tace "kiyi haquri fauxa,  bakiji daga bakina ba ganinayi kyakykyawan lbr ake fada" tace nagane Mimi kuma  banyi fushi ba,  Allah ya bamu haqurin jure halin da muke ciki" Mimi tana murmushi tace amin qawata. 


Tun daga ranar Kullum sai fauxa da shigo debewa Mimi kewa,  in ta dawo daga aiki (tana aiki a wata private skul). A duk sanda ta shigo Anty kan saki shewa tace " ayyuririri bazawara qawar bazawara 🤣 Allah ya sa a dade anayi zaurawan asali." babu wanda ya taba tanka mata.  Kuma daya abun takaicin shine : Baffa yasan tana haka amma bai taba hanata ba ko ya tsawatar mata,  wanda hakan yasa ta qara qaimi wajen cin fuskar Mimi.  Ga kwanuka da ake batawa da gangan da kuma bata gida duk dan a qara mata aiki. A duk sanda fauxa ta shigo taga Mimi na aiki takan Sabe mayafinta ta taya Mimi aiki. 



Bayan haka kuma,  Anty Kullum cikin gayyato mutane take dan suxo suga Mimi,  kuma takan yi musu jagora har dakin mama a cewarta wai suxo suga gyatumar da tai wata 5 a gidan miji auren ya mutu.  Ko kunyar idon mama bataji,  kuma abun sha awa daga mana har Mimi babu wanda ke tanka mata,  ko ya nuna damuwa kan abunda tayi.  Wanda hakan shike baqanta mata rai kwarai,  domin ta fiso su tanka mata. 


Abun na Anty sam babu shaawa,  kamar ba mace ko kuma bata da yaya mata.  Ko tayi alqawari da nata mijin bazai taba sakinta ba.  



Daya matsalar itace : muguwar rashin kunyar da Mimi ke fuskanta daga qananan yaran gidan yan mata,  dan sau tari sukan bangajeta su wuce sai dai ta kauda kanta tayi kamar bata ganiba.  Domin suna yine fisa umarnin iyayensu, wadanda ke zaman shirin ta tanka su cimata mutunci.  Dan tashaji Umma na cewa " mutum bazai kasa xaman gidan aure ba, sannan ya dawo gida ya takurawa qananan yayanmu."


Duk mai imani inyaga Mimi a wannan lokaci saiya tausaya mata,  domin ta qare ta mole tayi wani yagwal da ita.  Babu rashin ci babu rashin sha, amma duniya ta juya mata baya.  A wannan lokacin sai ta kwammace xaman gidan Badaru akan mazan gida.  Wai dama haka mutuwar aure take?  Tambayar da take yawan yiwa kanta kenan.  Kota ina babu sauqi, sai a gurin ubangiji.  Ta haqiqance babu mai santa yanxu sai mama da fauxa da kuma uwa uba ya Faty. 



Faty tun daga ranar da suka debo kayan Mimi bata kuma xuwa gidan ba,  domin sam batasan ganin Mimi cikin halin da Baffa ya sakata.


Mama ce ta lura da soshe soshen da Mimi takeyi,  ta turketa ta tambayeta babu kwana kwana ta fadawa mama infection ke damunta.  Dan haka mama ta bugawa Faty waya tace gobe tazo ta tafi da Mimi asibiti,  qaiqayin bandaki na damunta. 



Saboda tasan da xuwa asibitin tun qarfe hudun asuba ta tashi ta fara aikinta,  bakwai dai dai ta gama Faty taxo suka dau hanya.  


Likitan mata ta gani, ya basu kwaje kwaje,  saboda Faty ya sa basubi layi ba suka gama da wuri suka kai masa result din.  Ya duba yace "nikam banga ciki a jikin result dinta ba,  amma ta iya yiwuwa akwaishi,  matsalar magungunan da tayi ta amfani dasu suka cushe mata mahaifarta ya kuma haifar da rashin xuwan period dinta.  Ya kalli Mimi yace ko anan gaba ki kiyayi cusa abu a gabanki,  gurin yana da rauni kuma yana da saurin karbar kwayoyin cuta.  Kinga dalilin cushe cushen da kikayi yasa ciwon qaiqaiyin tsanani a jikin ki.  Amma yanxu ga magani nan  da allura inkikayi amfani dasu yadda ya dace duk qarfin ciwon sanyi zai rabu dake, kuma suna da qarfi sosai kici abinci sosai kafin kisha" sannan ya rubuta wani abu a takadda ya bawa Faty yace " wannan maganin kinsan yadda ake amfani dashi,  duk sanda jinin al adarta yaxo shedar ta warke daga ciwon kenan sai ki siya ki saka mata acan ciki ki tabbatar ya taba mahaifarta,  tunda kince sister dinki ce xaki iya yi mata a gida basai kun dawo ba" 



Suna kan hanyar xuwa gida daga asibitin Faty ta gallawa Mimi harara tace "Mimi har magani kike cusawa a jikin ki dan ki burge Badaru ko?  Mutumin da baisan mutuncinki ba?"  Mimi ta marairaice tace " wlh ya Faty ban taba shan komai ko cusa wani abu a jikina ba,  kinaga kazar da kuka yimun ma kafin a kaini ko dandanata banyi ba. Kawai dai lalura ce Allah ya doramun"  Faty ta sauke fushinta dajin abunda Mimi tace,  kuma tasan tabbas hakan ne domin kazar ma itace ta cinyeta bayan Mimi taqi ci.  Dan haka ta sauke murya tace "ko kuma Badaru ya debo ya goga miki ba."



Da xuwansu gida tayiwa Mimi alluran tasha maganin sannan Faty ta daura mata drip (qarin ruwa) domin a cewarta Mimi ta dashe da yawa jikinta na buqatar ruwa da gaggawa. 



Kwana 8 da sakin Mimi aka tashi da azumin watan ramadan. Kuma suka tashi ta baquncin Baba Saude (wata yar uwa a gurin Baffa, wacce ke xuwa daga can garinsu Gombe duk azumi da kuma sallah ta karbi kayan azumi ko kuma kayan sallah da Baffa ke bawa yan uwansa nacan taje ta raba)  Baba saude irin mutanenne masu fadar gaskiya,  dan haka take da baqin jini gurin matan Baffa (Umma da Anty) bayan haka kuma suna baqin cikin abunda take karba a gurin Baffa ta kaiwa yan uwansa na qauye. 


Mama dai babu ruwanta cikin wannan shaani,  tsakaninta da Baba saude kyakykyawar muamala ce.  Duk sanda tazo takan tsinci kwancen kayanta kona Mimi dana dady ta bayar akai qauye a rabar,  sannan kuma takan bata yan kudi ta qara akan na Mota.  Ko kunsan alheri kan saka qauna,  dan haka tafi sauran matan Baffa daraja a gurin Baba saude.


Wannan xuwa da tayi ta tarar da baqin lbrin mutuwar auren Mimi,  ta jimanta kwarai domin ta sauyawa halin da taga mimin aciki.  Basai anfada ba kasan xaman gidan baya mata dadi,  ga uwarta me haquri tasan duk cin kashin da xa aiwa Mimi mama bazatai magana ba.  



Ana haka Anty ta fito tana kumfar baki cewar Mimi bata dora abincin shan ruwa da wuri ba.  Baba saude ta cafe maganar da cewa "ke yanxu jamila dan yaya buhari ya dorawa maryam aiki sai ku sakar mata har abincin azumi?  Ai aikin azumi yafi qarfin hannu daya " 

Umma ta shiga cikin maganar da cewa " ai bamu muka sakata ba,  ubanta ne ya sakata kuma dole tayi, sannan bamu mukaje taje tai rashin mutunci a saketa ba"  Anty ta qara da cewa "kemadai Hajara kike bata bakinki,  ai abunda uwa tayi shi yar take maimaitawa,  inbaki manta ba ai haka uwar ta dunga yawan aure aure kafin Allah ya hadata da Aminu ta maqale masa sannan daga baya aka dawo kan mijinmu.  Waya sanima ko garin yawan asiri akan korarmu abun ya koma kan yarta?  Ai maryam gadan aure aure tayi da mugun abu a gurin uwarta,  Alhmdl Allah ya mayar mata da mugun abunta kanta kuma in shaa Allahu mutuwar aure yanxu kika fara,  da yardar Allah sai kin auri maza goma" 


Mimi najin haka ta fashe da kuka me cin rai,  mama ta fito daga daki taja hannun Mimi.  Baba saude ta harxuqa ta tofa Anty yawu tare da cewa " aniyarki ta biki,  kuma ki tuna kina da yaya mata,  fata nagari kuma lamiri.  Saboda haka wlh ki kiyayi Allah, harshenki zai jawo miki bala in da yafi qarfinki,  ba a yiwa Allah ixgili" Anty tace kema taki aniyar ta biki.  Baba saude tai saurin cewa "amin,  ai duk wanda kikaji ance aniyarsa ta bishi yaji haushi wlh aniyar ba me kyau bace.  Kuma indai ana gadon mugun abu ke hana zaman aure da naki yayan basu xauna ba."


Taci gaba da mita ita kadai a tsakar gida,  haka al amuran gidannan suka dame? Lallai yaya Buhari inbewa tufkar hanci ba tabbas jamila xata watsa masa gida.  Taja tsaki mtsewww.  Inbanda abunsa ma meye na damuwa da mutuwar auren maryam?  Sama da yaya goma suna gidan miji a xaune dan Allah ya dora masa qaddara akan daya ya kasa dauka.  Bare inda mutuwar aure ta zama gama gari,  aimu ko acan qauye ba a tsangwamar mace dan aurenta ya mutu. 


Umma ta leqo ta taga tace da Baba saude "karki kuma cewa yarsa ce,  domin shi duk nasa yayan na gidan miji a zaune basu taba zawarci ba saboda basu ga munayiba"  Baba saude ta katseta da cewa "to saiki zuqe jinin maryam daga jikin Buhari domin sharia ta riga ta bashi ya" Umma tace ai shi da kansa yace ba jininsa bace,  shi jininsa basa mutuwar aure.  Taje can ta nemi inda tayo gadan aure aure. 



Baba saude bata kuma cewa komai ba,  sai daga murya tayi yanda Mimi xata jiyota tace "ke maryamu kiyi shiru kinji,  Allah ya na tare dake,  shi dora miki kuma in shaa Allah xai baki mafita"


Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 3⃣0⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)


A haka ta fara axumi wanda ya qarasa ramarta ta qazanta,  domin sam abinci baya ciyuwa a gurinta. Ta dage da adduar neman sauki gurin ubangiji,  kuma duk wani masoyinta na tayata.  Kullum in ansha ruwa Mimi ke xuwa gidansu fauxa su tafi masallaci yin sallar tarawih domin gidansu fauxa yafi kusa da masallacin.  Sau tari a masallacin ma bata rasa masu yin zundenta da qusqus din mutuwar aurenta. 


A al adar gidan Baffa duk goma ga watan Ramadan yayansa kaf maza da mata, masu aure da marasa aure har na wani garin ana haduwa asha ruwa agida saboda sada xumunci.  Kuma uku ga kowacce sallah (sallah babba da sallah qarama) suna kuma taruwa shima aci abinci a sada xumunci ayi hotuna.


To wannan karon ba ai shan ruwan goma ga azumin ba kamar yadda aka saba,  saboda ya jafar bezo daga kaduna ba inda yake aiki.  Sai da azumi yayi rabi (15) sannan yaxo kuma a ranar aka fara shirin shan ruwan.  Yawanci duk yayan gidan mata sukanxo tun azahar a hadu ayi aikin abincin shan ruwa.  To yau dinma hakance ta kasance,  wadanda ke farin ciki da mutuwar auren Mimi da wuri sukazo sukaga dahir sannan suka dunga shewa suna sakin habaici. Masu hankalin ciki kuwa,  abun bai musu dadi ba saboda haka Anty Adawiyya ta jagorancesu sukaje dakin mama suka jajanta mata mutuwar auren sannan suka taushi Mimi tare da bata haquri akan abunda yan uwansu ke mata.  Mama taji dadin wannan karamci da sukayi mata ta dunga godia kamar sun bata wani abun.  



Azahar kowa ya hallara inka cire ya Faty da bata taso daga aiki ba,  duk suna baje a tsakar gidan suna aiki, masu gyara kaji nayi, masu hada zobo nayi masu gyara ayar kunun aya sunayi da masu gere dankali.  Baby tai sallama ta shigo jikinta sanye da uniform da alama daga skul take. Baby itace ya ta tara a dakin Anty,  shekarunta bazasu wuce 15 ba,  tana aji 1 a babbar sakandire (senior secondry).


Tana shigowa wani almajiri ya biyota,  "wai ana kiran wacce ta shigo yanxu" inji almajirin.  Baby ta murguda baki cikin tsabar fitsara da tashen balaga tace " wlh na tsani naci, tundaga makaranta yake bina maye."  


Anty tai saurin fitowa daga kitchen tace "je kace yarinya ce bata tsaiwa da samari" yaron ya fita fadar abunda aka aikeshi. 


Anty ta ruqe haba cikin sigar al ajabi tace "kai wadannan yara da farin jini suke,  babu dama su fita sai an biyosu.  Wlh bari Baffa ya dawo mu xauna ayi magana,  gara tanayin candy a aurar da ita inyaso jamiar tayi a gidan mijinta.  Aini nadau darasi da barin da ya dade a gabanka, qarshe kwantai yakeyi.  Wlh tana candy xan aurar da ita" (kunji fa kamar auren a hannunta yake,  mudai munsan koda miji a hannu aure sai Allah yayi tunda aure lokaci ne.)


Rashida ta kalli shashin da Baby take tsaye tana murmushi saboda jin abunda uwarta tace na cewar tana da farin jini,  tace "aike Baby ki godewa Allah tun yanxu anfara kawo miki hari,  alamar cewa ba zaki Bandaro ba.  Saboda wlh in mutum yayi kwantai ko yaje gidan mijin ba iya xama yake ba" ragowar yan jam iyar Rashida (masu qin Mimi) suka saki dariya tare da cewa "wlh kuwa 🤣🤣🤣"


Anty Adawiyya dake gefe ta cije lebe saboda duk wanda ke gurin ya fuskanci inda maganar Anty da Rashida ta nufa,  Anty Halima ta kalli Adawiyya cikin takaicin abunda uwarta da yar uwarta sukai (halima yar Anty ce) tace Anty wai haka zamu zuba ido abubuwannan suci gaba a gidannan,  infa akaci gaba da haka nan gaba kadan xumunci xai watse mune manya ya dace mu gyara abun.  Anty Adawiyya tace " Halima mexance?  Ai baka canja mutum kina ganin kwanaki da nai hukunci akan abunda Rashida kewa Mimi qarshe abun fada ya xama tsakanin Umma da Anty.  Saboda haka duk wanda aka fada masa yaqiji sai a kyaleshi duniya tai masa nata karatun"



Suna zaune akan qatuwar tabarma da aka malala a tsakar gidan,  kayan abinci ne jibgi a gabansu kowa na diban abunda yake so yana ci.  Duk zuriar gidan sun hallara tundaga kan Baffa, matansa, yayansa da surukarsa (matar yaya Ali) da kuma jikokinsa.  Anata hira ana jin abinci cikin raha,  ya jafar ya kalli Baby yace "ke jeki kice Mimi ta fito,  inna kuma aiko ta fito bata fito ba sai ranta ya baci." wannan shine karo na 3 da yake aikawa kiran Mimi amma taqi fitowa,  kuma ba wani abu ke hanata fitowar ba sai gudun abunda ka iya faruwa inta zauna a cikinsu.  


Umma tai tsaki ta dan harari jafar,  tace "to kai ina ruwanka da rashin fitowarta,  ai dan ta nuna muku mugun halinta ne yasa bata fito ba,  tayi abu yazo ya dameta ya hanata shiga cikin mutane." 



Wannan karon Mimi tare suka fito da Baby,  sanye take da hijab me hannu.  Faty bataso tilastawar da ya jafar yayi Mimi ta fito ba saboda tasan dole sai anyi abunda xa aci xarafin Mimi.  



Ganin babu guri a inda Baby ta xauna yasa Mimi tayi nufin tsallakewa can kusa da Anty safiyya (matar ya Ali) . Ganin da Rashida tayi Mimi na shirin tsallaketa yasa ta miqe qasa tare turo qatan cikinta,  Mimi ta daga qafa xata tsallaka a hankalce saboda kar ace tayi wani abun ko ta buge mai ciki Rashida tasa daya qafar ta tade Mimin. Ai kuwa ta yanke jiki ta fada kan Sumayya take zaune da jaririnta dan 4 month akan cinya, sannan ga kofin shayi sai tururi yake a gabanta.  Cikin axama Sumayya ta ture Mimi daga kan jaririnta ta tura mimin kan ruwan shayin tare da cewa "bakya ganine zaki kashemun da?" 

Zafin ruwan shayin bai gama ratsa Mimi ba taji saukar mari a kuncinta.  Tai dafe kunci tare da dagowa taga wanda ya mareta tai arba da Baffa sai huci yake yana kallonta cike da tsana yace "dan bakisan ciwon haihuwa ba shine xaki fado mata akan jariri?  Ke dan kin gaza xama a naki gidan ki haifi naki dan zakixo ki fado musu ka?  Ke wace irin muguwar yarinya ce". 


Umma tace ai dama tunda aka tilasa mata fitowa batai niyya ba nasan saitayi abunda xata sosa mana rai kuma shine muguntar taki xata qare akan jikana?  Rashida na gefe sai murmushin jin dadi take. 


Duk wanda ke gurin ya lura da abunda ya faru saboda hasken nefa tanyar a tsakar gidan.  Mimi abun yayi mata yawa ga zafin qonewa ga zafin maganganun Baffa,  ta fashe da kuka tace " Dan Allah kuyi haquri,  inwani laifin nai muku kuka tsaneni dan Allah ku fadamun in gyara" tana kaiwa nan ta shige daki.


Ya jafar da tausayin Mimi ya hanashi daurewa ya kalli Baffa yace "Baffa wannan wane irin hukunci ne?  Wlh ina kallon abunda ya faru, Rashida ce ta turota dan me xaka goyi bayansu qonata fa sukayi" Anty tai saurin kare Rashida da cewa karkai mata sharri, kawai dai ta shirya mugutar fadawa kan Rashida tasa ta naqudar dole ita kuma Allah ya bata sa a ta tureta.  Baffa ya hau borin kunya da "yimun shiru jafar, kaine ka haifeni?  Ko kai xakaimun hukunci a gidana"



Faty tabi bayan Mimi itama tana kuka. Jafar ya kalli shashin da mama ke zaune yaga tananan inda take ko motsawa batai ba sai dai ta kasa cin abincin sai juya tea take da spoon.  Anty Adawiyya ta dakko qaramin try ta xuba duk nau in abincin dake gurin ta bawa Anty safiyya tace "kaiwa su Faty daki"  Faty na zaune kan kujera tana kuka tana shafawa Mimi jelly a dantsen hannunta inda ruwan shayin ya xaba.  Anty safiyya ta bata abincin tace ki tabbatar Mimi taci. Kuyi haquri Allah baya zalunci kuma ya haramtashi garemu in shaa Allah xakuga sakamako. 



Faty ta dunga diban abincin da hannu tana bawa Mimi,  ita kuwa ba musu ta dunga karba tanaci.



Tun jiya da abun ya faru har ixuwa yanxu da gari ya waye tunani take. Wai shin meyasa indai aure ya mutu a Society dinmu laifin kan zama na ya mace ita kadai?  Wai yaushe YA MACE xata samu yanci a Society namu?  Wadannan sune tambayoyin da ta rasa me amsa mata. 


Kanta ke mugun ciwo,  wanda tasan tunani ne ya haddasa matashi.  Ga kuma yanxu mararta ta daure,  alamu kamar period pain.  Tananan kwance,  taji ciwon marar ya fara tsananta kuma taji danshi a qasanta.  A fili tace "babu ciki a jikina kenan kamar yadda Dr yace" gudun kar ciwon mara ya galabaitar da ita gashi mama ta tafi aiki yasa ta tashi taje parlour ta dakko gwangwanin maltina a fridge tazo ta balli maganin ciwon mara tasha.  Lokacin ko ganin gabanta bata iyayi saboda tsananin ciwon kai. 


Tana kwance tana murqususun ciwon mara da ciwon abunda Baffa Yayi mata,  itadai tun take da Baffa bata taba gani ya dora hannunsa akan wani da a gidan ba sai ita.  Koda yake itakam a gidan tana da banbanci da kowa,  domin Baffa ya mata abubuwa da yawa da bata taba gani yayiwa wani ba. 


Da farko bayan qin biya mata ko sisi a cikin hidimar karatunta,  yazo ya takura mata da sunan taqi aure,  yayi mata auren dole sannan auren babu dadi bai taba taka gidanta da sunan yaje ganinta ba,  duk kuwa da cewa dabiar sa ce xuwa gidan yayansa yaga halin da suke ciki kuma ya musu alheri.  Amma ita tunda aka kaita ko waya bai taba yimata ba.  Abu na qarshe shine: anyi mata sakin wulaqanci ta dawo gida ya kuma takura mata,  takurar da tafi ta farko,  ga kuma duka anfara jiya.  



A wannan gaba taga ya dace ta karbi shawarar da xuciyarta tasha bata a kwanakin baya,  dan haka ta miqe ta dauki kudi ta fita ta tsaya a soro ta aiki wani almajiri ya siyo mata abunda take buqata.  Tananan tsaye yaron yaje ya kawo mata aiken,  ta bar masa ragowar canjin. 



Da magriba ta gama duk wani aikinta ta shige daki tunda ba azumi tayi ba, tabar mama tana shan ruwa a parlour. 



Fauxa da tagaji da zaman jiran Mimi ta biyo mata zuwa sallar tarawih bata zoba ta tashi domin biyawa Mimi,  dan taji har an tayar. 


Ta sami mama a parlour suka gaisa Maman na shirin shiga bedroom tace "qawartaki na dakinta tun dazu kinga ma ko ruwa bata sha ba" tace to bari in dubata. 



Shigar Fauxa dakin tayi dai dai da lokacin da Mimi ta daga kwalbar FIYA FIYA (abunda aka siyo mata daxu) xata kai bakinta.  Fauxa ta kwala kiran "MIMI" a razane 😳 tare da doke hannun mimin.  Kwallah kiran da tayi ya janyo hankalin mama daga bedroom, taiwa dakin tsinke tana tambayar lfy?.  Fauxa batabi takan tambayar da mama keyi ba.  Ta qarasa ta riqe kafadun Mimi tana girgixata cikin kuka tana cewa "Mimi kashe kanki xakiyi akan mutuwar aure?  Shin in kashe kanki wanda ya sakeki yana da asara ne?  Mesa xakiyi haka?  Duk fa abunda xai faru ya riga ya faru.  Ansake ki,  an takura miki,  anyi gulmarki,  anmiki sharri.  Inbaki sani ba maganganu da yawa ke yawo akan mutuwar aurenki.  Akwai masu cewa cukumar mijinki kikayi kina zaginsa ya sakeki,  wasu kuma suce wai sata kikai masa ya sakeki,  ke harda masu cewa ya kamaki ne kina lesbian (neman mata) ya sakeki.  Amma duk wandannan maganganu da nakeji bana fada miki saboda kar in daga miki hankali. Amma shine yanxu xaki kashe kanki Mimi?  Why Mimi,  Why. Wlh indai akan baqin cikin namiji kike haka gara ki dena,  shin ni ba a sakeni ba?  Ni harda Da aka sakeni mutu nayi?  Ko takurar da aka yi miki ba ita akemun ba,  kafin Baba ya gane gaskiya ya sakarmun mara?"



Maganganun da Fauxa keyi yabawa mama amsar tambayar da take yi,  dan haka cikin kuka ta juya tabar dakin.  Mimi ta gigice ganin kukan mama dan tasan ba qaramin abu kesa mama kuka ba,  tai gargawar biyo bayan mama tana cewa "mama ki yafemun na tuba 😪"  


Fitowar mama tai dai dai da shigowar Faty parlourn, ya Ahmad na biye da ita.  Dan bata gamsu da yacce tabar Mimi a jiya ba shiyasa ta kuma xuwa ta taushi Mimi.  Ta iske wannan mugun lbr, fauxa ta fada mata tace "WHAT" kalmar data janyo hakalin matan gidan, nan da nan kuwa suka cika qofar dakin mama suna kallo.  Ya Ahmad kuwa gurin mama yaje ya tsuguna gefenta yana nemarwa Mimi yafiyar abunda tayi. 



Faty kallon Mimi take da wata irin fuska 😡 wacce babu wanda ya taba ganinta da ita.  Mimi tana rabe jikin bango,  cikin kuka take furta "am sry,  am so sry sister"  Faty batabi takan haqurin da Mimi ke bata ba,  ta kifawa Mimi mari,  ta kuma kifa mata wani,  ta qara mata.  Ataqaice dai sai da tayiwa Mimi mari guda 6 xafafa.  Mimi idanunta a runtse,  bata dauke kanta ba, ba kuma ta fasa furta "am sorry sister"  


Wadanda ke bakin kofa suna kallo abun yayi matuqar girgizasu,  domin ba qaramin abu zaisa Faty ta daki Mimi, bama su taba gani ko fada Faty taiwa Mimi ba bare duka.  Dan haka kansu ya qulle suka rasa lefin da Mimi ta aikata Faty ke mata wannan hukunci.  Kuma ta wani barin abun ya burgesu domin daga Anty har Umma babu wacce daya daga cikin yayanta na sama ya isa yayiwa na qasa hukunci haka,  ba ai gagarumin yaqi ba. Kuma daya abun burgewar har wanda akaiwa hukuncin yana bada haquri. 



Faty na gama marin Mimi itama ta fashe da kuka, ta janyo mimin ta rungumeta tsam suka xube qasa tana shafa kan Mimi tare da cewa "is Ok sister" Fauxa ma ta matso kusa tana lallashin Mimi cike da yabawa hukuncin da ya Faty tayi mata.  A xuciyarta tana aiyana duk renda Allah ya bata yaya mata xatayi iya yinta ta hada kansu kamar yadda mama ta hada kan Faty da Mimi. 



Yan kallo kuwa dole suka watse ganin film ya qare.  Ya Ahmad ya tafi ya bar Faty ta kwana,  saboda halin da mama ke ciki.  



Can tsakiyar dare suna kwance kan doguwar kujera,  mama dauke da Dady kan cinyarta,  sai Faty dake zaune tana bacci Mimi kuma ta tada kai da tata cinyar.  Tun faruwar abun Mimi ke bawa mama haquri amma mama tayi kunnan uwar shegu kamar batajin abunda Mimi ke fada,  yanxu ma sai kuka take tana qara neman gafarar mama.  Mama ta shafa fuskarta tace "na haqura Mimi, amma ko wane irin hali xaki shiga karki qara yunqurin halaka kanki,  kinga ku kadai nake daku in kintafi kinbar yar uwarki ni da ita ya xamuyi?  Bakisan rayuwarki nada matuqar mahimmacin a gurin mu ba?  Danme xaki kashe kanki akan wadanda mutuwarki sukafi so akan rayuwarki?  Mimi kiyimun alqawari daga yau zaki cire duk wata damuwa a ranki ki fuskanci abunda ke gabanki.  Da ace mutane suna riqe abunda ya riga ya wuce wlh da baqin cikin ya kashe rabin mutanen duniya.  Saboda haka past is gone forever, ki gyara present dinki,  future kuma ki barwa Allah shi yasan abunda future xata xo miki dashi." 



Mimi ta gyada kai cike da gamsuwa da kalaman mama, sannnan ta qudure yin aiki da abunda maman tace mata.  


Ta yunqura ta miqe xataje toilet domin canja pad din jikinta da ta jiqe,  mama tai saurin cewa ina xaki?  Tace " xan canja pad ne"  wani farin ciki ya xiyarci mama,  jin Mimi taga jini wanda hakan ke nuna babu ciki kenan.  Ta dunga godia ga Allah domin batason Mimi ta haihu da Badaru.  Tace da mimin muje in rakaki,  Mimi ta zaro ido 😳 tace "mama toilet din xaki rakani?" mama na tafiya tace "eh nasani ko ki kuma yunqurin halaka kanki"  Mimi ta marairaice tace " mama zargina kike wlh bazan kuma ba na baya ma da nayi kuskure ne."



Yan kwanakin da suka biyo baya ta dan samu sauki,  amma fa ba sauqin aikin gida ba saukin damuwar dake xuciyarta a bisa amfani da shawarar mama.  Ta kuma yardarwa kanta xatai karbi rayuwa a duk inda taxo mata. 



Mrs 😊
[9/30, 1:03 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 3⃣1⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Ranar da Mimi tayi wankan tsarki ranar Faty tazo gidan,  ta tasa Mimi a gaba harda yan kayanta set 2. Mimi tace "ya Faty Baffa inyaxo ya tadda banyi aiki ba xaimun fada." Faty ta fallara mata harara "xan dura miki xagi Mimi,  ana xancen lfyarki kina xancen fadan Baffa?  Ko kin manta abunda Dr yace in kinga jini insamiki wani magani?" Mimi ta marairaice tace "ya Faty ai na warke ko sati banyi ina amfani da maganin ba na daina qaiqaiyin, wlh kamar ban taba yiba." Faty ta kuma watsa mata harara tace " ke wlh sai kin bini in yaso in kin dawo Baffa ya kasheki bashi kikejin tsoro ba?" tace tuba nake sis muje 😊



Bayan sunsha ruwa sun huta,  Faty ta dakko maganin tasa safar hannu tace da mimin kwanta.  Mimi ta waro ido tace "ya Faty😳 yanxu wai saina bude jikina?"  Faty tace "a a karki bude insa miki magani, amma ai kin budewa Badaru ko? Mimi najin haka ta kwanta ta bude jiki,  Faty ta gama yi mata gwaje gwaje tasa mata magani.  Tanata tsaki tare da cewa " wannan mutumin ya cuceki Mimi dole sai anmuki stitches (dinki)" Mimi ta zaro ido cikin kidima 😳😳😳 tace "ya Faty na samu qari ne? Naga masu haihuwa akewa dinki" tayi tsaki tace "ba gara wacce ta haihu dake ba, ita tasan haihuwa tayi.  Kuma ba sai lallai masu haihuwa akewa dinki ba. Ba qari kika samuba amma ya miki barna a jikin ki ya nuna mugunta wajen kusantarki, gara ma da Allah yasa nagani amma wannan in kikayi aure ai sai kiji kunya, wata 5 a gidan miji amma wani mijin ya sameki sakwakwa haka ai sai yace qarya ake cutarsa akai."


Washegari kuwa tana dawowa daga aiki tace da Mimi ki shirya in ansha ruwa xamuyi aikin, na siyo kayan aikin masu kyau wanda in anyi basai an ware ba zaibi jikin ki. 


Kafin asha ruwa Mimi ta tsure,  mugun tsoron dinkin takeji kamar tace a fasa.  Haka dai ta haqura aka fara dinkin,  tunda aka fara ta runtse idonta tare da cije lebenta saboda azaba.  Har akayi stitches din aka gama ko tari bataiba,  Faty ta dunga yabawa dauriyar da Mimi tayi.  Mimi ta kalleta tace "ya Faty xai kai kwana nawa kafin ya warke?" Faty tace "kayan aikin da nayi miki amfani dasu masu kyau ne,  amma duk da haka ya danganta da irin jikin ki da kuma irin kulawar da kikayi dashi." ta bata magani ta hadiya saboda ya kashe xafin gurin, ta qara da cewa indai jikinki me kyaune gurin zai koma fresh kamar baayi dinki ba. 



Kwananta biyar a gidan Faty, ta samu nutsuwa da kuma sakewa ga kulawa da shiga ruwan dumi saboda stitches din. Nan da nan kuwa ya kame kamar bame dinki ba tafiyarta ta koma normal.  Kuma a ranar ne Baffa ya lura ko kuma aka kai masa gulmar Mimi bata gidan.  Shima daya lura sai yaga baya ganin kai kawonta a tsakar gida, kuma tsaftar gidanma ta ragu saboda masu aikin sun karbi aikinsu, lokacin da Mimi  na aiki gidan yafi tsafta.



Dan haka ya bugawa Mimi waya yace ta taho kafin ranta yayi mugun baci,  a cewarsa tunda batai zaman nata gidanba bazataje ta kashewa wata nata auren ba. 


Sai wajen goman dare ya Ahmad ya maidota gida.  Ta dunga lallaba jikinta saboda kar stitches din ya samu matsala,  duk abunda xatai tana kula sannan ko mama batasan da xancen dinkin ba.  



Azumi ya tasamma qarewa anata shirin sallah,  a wannan lokaci ita kanta tasan ta samu sauki.  Domin tana jin jikinta a matse kamar lokacin da tana 15 years, ita kanta tasan ta samu canji a jikinta.  Gashi ta dan murmure saboda kwanciyar hankali data samu.



Ranar 3 ga sallah gida ya cika kamar yadda suka saba zuwa, kowa cikin kwalliya ta burgewa da qoqarin nuna tattalin arziqin mijinsa. 😄



Mimi bata fita tsakar gidanba inda aketa photuna ake shewa, saboda tayi alqawarin dena shiga cikinsu duk rintsi.  Tana zaune parlour tana karatun wani novel da aka turo a grp,  Rashida da tawagarta suka shigo.  Rashida tace ina mama?  Xuwa nayi inyi kallo a dakinnan parlourn Umma yara sunyi yawa.  Ta xauna akan kujerar kusa da Mimi,  ragowar wadanda suka shigo tare ma duk suka nemi gurin xama.  Ta kunna kayan kallon sannan tasa fefen CD na film din ZAURAWA na AISHA DANKANO,  wanda takanas Rashida ta taho dashi daga gidanta dan kawai taci zarafin Mimi.  Ana kallon film din su Rashida na hira tare da aibata zaurawa da tsine musu,  wai a cewar Rashidan "duk wata bazawara karuwa ce,  suna fakewa da xawarci suna neman maxa. Kuma da mijinki ya auro miki bazawara gara ya auro miki visites domin bazawara saita nuna miki tasan namiji.  Ta kuma gyara xama tace,  ai duk macen da ta fara mutuwar aure to wlh haka take qare rayuwarta a aure aure yo dama mutum dakyar ya shiga bare yanxu." 


Mimi tayi banxa dasu tana danna waya, saboda ta kasa karatun novel din dan maganganun Rashida sun tabata.  A zuciyarta kuwa cewa take "rashin fita cikin nasu ma ban tsira ba tunda har dakin uwata anbiyo ni ana zagina" tana wannan tunanin har film din yazo dai dai inda Aisha Dankano ke cewa "ZAURAWA" nan take kuwa Rashida ta saita babban yatsanta saitin Mimi 👍🏼 tare da cewa "SUNE" ragowar suka saka dariya sukace Rashida baki da M. 



Anty safiyya dake dakin Mimi a kwance duk abunda suke tana jinsu,  kuma babu wanda yasan tana dakin.  Ta fara tunanin dalilin da yasa yan gidannan suke haka sai kace ba yan boko ba,  kawai dan aure ya mutu sai a takurawa yarinya. Itakam bataga laifin Mimi ba,  yarinyar tanada haquri da shiga rai.  Ta tashi ta fito ta riqe labulen dakin tace "tace meye haka nakeji Rashida?  Waike wace irin yarinyace mai neman fitina? Ki biyota har dakin uwarta kina insulting dinta?"  Rashida ta murguda baki cikin fitsara tace "babu ruwanki malama,  muna abunmu iya yan gida kinxo kinsa baki,  wannan aiba abunda ya shafeki bane" Anty safiyya ta nunota da yatsa tace "ke!  Kikiyayeni,  in kinsaba iskanci a kyaleki ni inkaimun Ali (mijinta) xansa ya casaki." Rashida najin haka tayi shiru dan tasan yaya Ali babu ruwansa ubanta zaici. 



********   ********      *******

Kwana goma dayin sallah ta kuma tsintar kanta cikin jini,  wanda ke maxaunin jini na biyu bayan sakinta. Kuma hakan ya nuna saura jini daya kenan ta tashi daga matar Badaru,  tunda munsan cewa iddah jini 3 ce.  Ba wata uku ba kamar yadda wasu ke fada,  sabida ba kowace mace ke jini duk wata ba.  Wata tanayin sati 3 wata kuma 25 dayz (kamar Mimi kenan). 



Haka al amura sukaci gaba da tafiya,  tasamu saukin rayuwa sosai saboda aikin da Baffa ya dora mata ya xamar mata jiki inbataiba batajin dadi.  Sai dai surutun mutane akan mutuwar aurenta har yanxu abun be sauki ba,  wannan kuma ta kance suyi su gama watan kwaram daya ne, na biyu sai gagara. Mutane kan bata mamaki,  inbakai aure ba a dameka inkayi balain gidan auren ya hanaka xama nanma asaka agaba. 


Duk magribar duniya fauxa kan shigo susha hira sai goman dare take tafiya.  Wanda hakan kan yiwa Mimi dadi,  kuma yakan debe mata kewa.  Dan ita Baffa ya hanata fita ko kofar gida.  A cewarsa kunya yakeji aganta ace yarsace kuma bazawara ce.  Dan haka suka qara shaquwa sosai da fauxa.  Duk wani abu da take buqata fauxa take bawa ta siyo mata. 



Sati hudu dayin qaramar sallah katin bikin Badaru yazo gidansu.  Kuma a lokacinne mate din Mimi suka fara registration din tafiya service domin an bude musu portal,  ta dunga kuka saboda Baffa ya hanata.  Sam bikin Badaru baya gabanta bata sansa balle tai kishinsa dan haka in mata 100 zai aura wlh baxata damu ba. 



Ranar asabar data kasance ranar yinin bikin Badaru matan gidansu Anty da Umma suka shirya suka tafi duk kuwa da cewa ba wani xumunci ke tsakaninsu da Umman su Badaru ba,  amma saboda a cuzgunawa Mimi suka tafi,  mama kuwa dama ba a gayyaceta ba. 



Ai kuwa suka dawo da lbrin irin gidan da Badaru ya qera domin sunje kai amarya,  da kuma irin bushashar da yayi a bikin.  Sukaita fadar magana wai ai yanxu yayi aurenso domin ya nunawa duniya yanason Nafee.



Ranar da aka kai masa Nafee a daren ya tumurmusheta, saboda yana yunwar abun. Amma ga mamakinsa a daren ya shigeta tsaf,  sabanin Mimi da sai da yayi kwana biyu dan ma tagomashin maganin kuzari.  Abun ya daure masa kai,  gadai Nafee danya shataf (mai qarancin shekaru) amma Mimi ta fita qaramar halitta.  Ashe abun ba shekaru bane.  Amma duk da haka ya yaba mata kwarai  tunda ya sameta cikakkiyar mace wacce ta kawo masa mutuncinta dan haka ta kuma samun gurbi sosai a zuciyar Badaru. 


Itama ta bangarenta tasha wuya sosai,  amma ta daure ne saboda soyayyar da takewa Badarun. 



Ranar da Mimi taga jini na uku (ranar cikar iddarta) har sadaka tayi saboda farin cikin sun rabu da Badaru har abada (abunda take fata). Mama kamar ta xuba ruwa a qasa tasha,  ta dunga sallar Nafila tana roqawa Mimi da duk wata ya mace samun miji nagari da ingantacciyar rayuwa. 



Daf ake da babbar sallah. Cikin wata guda da aurensu suka fara samun sabani da Badaru a dalilin yawan buqatarsa,  ita kuma tagaji da juriya.  Abunda kuwa ya faru shine: dake ance me hali baya fasa halinsa Badaru yaci gaba da bankar magungunan qara kuzari,  wanda ya qara yawan buqata akan tasa,  ita kuma Nafee taga sam bazata jura ba.  Duk kuwa da cewar Badaru baya ware mata qarfi kamar yadda yakewa Mimi.  Sabanin haka ita yakan yi romancing dinta ya lallabata kafin yakai gaci.  Kuma yanayin hakanne saboda soyayya da kuma duba qarancin shekarunta. 


A bangare guda kuma bata samun yacce takeso ta wajen cima, sabida ta gama sawa a ranta inta auri Badaru zaman jin dadi xatai saboda yana da kudi, ga kuma gida daya qera mata.  Shi kuma Badaru baisaba siyan komai a gidansa ba, amma duk da haka yasan xaman da yayi da Mimi babu macen da xata yadda da haka.  Dan haka yake sassauta wasu al amuran.  Yana siyan komai na cefanen gida dai dai gwargwado saboda har yanxu gushirin yana kan kaxa.  Sada nama da kayan shayi da bai taba saiwa Mimi ba yakan saiwa Nafee da sun qare,  sai dai kudi ne kwandala bata taba shiga tsakaninsu ba.  Wanda Nafee taga bazata lamunta ba.  



Abunda ya fara kawo musu sabani kuwa shine : tara qawayen da takeyi danta nuna musu itafa yanxu ta kere sa a ta auri mai kudi.  Wanda shi Badaru sam baya qaunar yaga anshiga gidansa,  kuma in sukaxo inyananan sai tace ya basu kudin mota inma bayanan saita ciwo bashi a maqota inya dawo ya biya.  Kuma duk wani nama da ya siya a gidan in qawayenta sukaxo sai sun cinyeshi.  A irin haka wata rana qawayenta sunxo dayar ta buqaci Nafee ta bata always ta canja,  Nafee da son gwaninta ta dakko ledar always ultra gaba daya ta bata.  Wacce dakyar Badaru ya siyo mata ita  domin cewa yayi bai taba siya ba,  kuma tai masa kudi da yawa harda cewa abar da za asa ayar har sai ansa 500 ansiya?  A taqaice dai sai da aka kai ruwa rana kafin ya siyo gashi Nafee ta bada ita lokaci daya. 



Yana dawowa kuwa ko sannu da xuwa batai masa ba ballantana ta bari yaci abinci tace "kaje ka siyomun always" ta fada cikin sigar rashin mutunci dan kar yace bazai siyo ba.  Ya kalleta a kaikaice yace "amma kyabari inci abinci ko"  ta qara tsuke fuska tace "ai babu abincin domin nayi baqi sun cinye kuma kafin na dora wani ka dawo"  ya jinjina kai cikin qosawa da halinta domin ba wannan ne karo na farko da tayi mai haka ba yace "ba shekaran jiya na siyo miki ba? Harta qare kenan?"  cike da isa tace "na bayar da ita daxu,  domin da kunya axo a ganni a wannan makeken gidan inkasa bada ledar always ai wlh kamata yayi ka dunga saimun sunqi guda saboda qawaye na"  yace "ok haka ya dace kiyi?  Kinyi dai dai"



Ala tilas yaje ya siyo mata always din,  domin da yaqi siyowa xama ta dunga yi ko ina tana batawa da jini daga qarshe ma da taga bai dauki abunda tayi da mahimmaci ba saita zauna akan cinyarsa ta batashi da Jinin (su Nafee yan iska🤣) dan haka ya yi saurin tashi yaje ya siyo tun kafin ta haram ta masa xama a gidan saboda qazantar jini,  domin shi Allah ya yi masa kyankyamin jini.  



Ranar alhamis suka tashi cikin tashin hankali, fada kacucur suke da Nafee yana fada tana mayar masa kamar ba sune masoyan da suka shafe shekaru suna soyayya ba.  Dalilin fadan kuwa shine: Nafee tace ya siyo mata kaza domin ta dade bataciba a fadarta rabonta dacin kaza tun ta daren amarci,  kuma wannan danqareren gidan kamata yayi ace Kullum da farfesun kaza ake breakfast 🤣. Shi kuma ya bata amsa da bazai siyo ba,  domin a gidansu ma ai ba kazar take ciba,  naman kasuwar ma da ta samu ta godewa Allah (abunki da wanda ya saba da fadar baqar magana) ai kuwa yana fadar haka Nafee ta taso masa kamar xata dakeshi tanayi masa warning din karya kuma sa gidansu acikin rashin mutuncinsa domin inya kuma xatayi babban rashin mutunci. 



Da haka ya tarkata ya fita saboda karya zauna zuciya ta xugashi ayi batacciya. A kasuwa tunani ya yini yi na mamakin halin Nafee. Shidai a iya zamansu baisan haka halinta yake ba ashe lambu lambu tai masa,  to kodai qawaye ke xugata?  Wata xuciyar tace ba wasu qawaye halintane hakan ta boye makane sai daka aureta.  Wannan shine ana zaton wuta a maqera ansameta a masaqa,  yana zaton a gurin ruqaqqun yan mata masu ilimi irinsu MARYAM ake samun fitsara da rashin kunya wa miji ashe abun ba haka yake ba,  sai gashi yar qaramar yarinya Nafee da ko secondry bata gama ba tanayi masa abunda bai taba tsammani ba.  Ada ya dauka xai juya Nafee yacce yakeso ya koya mata irin aqidunsa sai yaga labari yasha banban domin tun kafin aje ko ina Nafee na neman fin qarfinsa.  



Haka ya yini tunani a kasuwa, da dare ya dawo batai abinci ba. A cewarta wai ya bata mata rai saboda haka bazatai girki ba. Sai gurin me shayi yaje yaci indomie 😂.


Dake tsohon jarababbene,  a wajen kwanciya sai ya nemi haqqinsa.  Ai kuwa tace "kai ka isama?  Bakaban nama naci ba kazo ka mutstsukeni? Aikin banxa jarababbe kawai bakasan komai ba sai dare yayi ka danne mace" qiri qiri ta hanashi abunda yakeso kuma dole ya haqura. 



A daren ya gama yanke shawarar abunda zaiyi, domin ya gaji da rashin kunyar Nafee da iskancinta.  Kuma gashi ta fara hanashi haqqinsa shi kuma bashi da juriya a wannan fanni.  Dama kuma cikin yunwar abun yake domin sam baya samun gamsuwa da Nafee yacce yake samu da maryam,  ya saba da xagaye daya ya gamsu amma itakam Nafee sai yayi biyu xuwa uku yake samun biyan buqata lamarin da Nafeen taqi yarda dashi domin tace ita ba shinkafa bace dazaita sasuqarta. 



Dawo da MARYAM xaiyi domin ya fara gane kuskurensa na saurin rabuwa da ita.  Saboda haka xai dawo da ita ta zabe masa ruwan kashe shaawarsa a duk sanda ya buqata. Ita kuma Nafee yaci gaba da ajiyeta a matsayin matar so ya kuma ci gaba da haquri da halinta domin har yanxu yana sonta,  dan San tsakani da Allah ya ke mata itace dai ta rufeshi.  Dan haka ko gida daya bazai hadata da Nafee ba kartaga irin abunda Nafee take masa itama tace xatayi,  wani gidan zai kama mata haya anan kusa da Nafee.  



Yana kaiwa nan a tunaninsa wani farin ciki ya shigeshi, 😄 harya fara hangosu shi da MARYAM cikin yanayin auratayya.  Yasan xuwa yanxu ta nemi maganin ciwonta na sanyi, sannan kuma gata da qaramin ciki yasan xai shana kwarai dan MARYAM yar baiwa ce ko babu ciki bare da ciki. Sai yanxu yaji yana son cikin jikinta kuma yanason ganinta da cikin yasan cikin zaiyi mutuqar kyau ajikinta dan komai nata me kyau ne (Dan rainin sense 😏) da wannan tunani bacci ya daukeshi cike da mafarkin MARYAM wanda ya kaishi ga wanka.



Ganin kansa a jiqe yasa Nafee fallara masa harara, tace ina ruwan dan anace mafarki kai kenan?  Bai kulata ba saboda  bayason ta bata masa mood,  dan daga masallacin asuba gidansu zai tafi gurin Abbansa suje bikon MARYAM. 



Mrs 😊
[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 3⃣2⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Bakwai saura kwata (6:45 AM) a gidansu tai masa. Yasha shadda fara sol yar ciki da babbar riga, ya dankwafa hula kamar kansilan qauye.  🤣



Har cikin dakin Abbansu ya shiga, ya samu Umma tana hadawa Abban shayi. Ya tsuguna har qasa ya gaishesu, Abba ya gama shirinsa tsaf da alama fita xaiyi.  



Badaru ya qara sunkuyar dakai cikin sigar neman alfarma yace "Abba dama nazone dan Allah muje mu dawo da MARYAM,  Na janye sakin da nayi mata. Naga gara ta dawo mucigaba da xama ta haihu a dakinta, na huce da fushin da nake da ita."  Umma ta ware ido tace 😳 au dama MARYAM din ciki gareta amma ka saketa?  Kuma shine baka taba fada ba?  Wannan yaro ka jawo mana abun kunya wlh,  ai da munsan da ciki da mun dunga xuwa dubata."  yayi dan murmushin alamun samun nasara yace "Umma kuyi haquri lokacin rainane a bace shiyasa ban fada muku ba."  tace " eh ai yayi kyau hakan,  yaro yarone, yaro bakasan wuta ba saika taka.  Yanxu kuma da xaka dawo da ita ka manta da xagin naka da kace tanayi? Ka sheqa kaji babu kwaya kenan.Hmmm to wlh bakayi  
daya ba kaji dadi duk randa ka kuma sakin wata mace bama MARYAM ba daga ranar ka canja uwa domin ni bazan xama uwar mai auri saki ba"



Abba yayi gyaran murya yace "tunda dai yayi kuskure kuma ya gane kuskurensa shikenan,  kuma itama MARYAM din nasan yanxu tayi nadamar abubuwan da tayi masa. Yanxu xanje Dawaki daurin aure amma in shaa Allahu bazan kai sallar juma a acan ba.  Yanxu xanje insamu kawunka in fada masa,  inyaso ina dawowa daga masallaci sai mu wuce dashi muje gidansu MARYAM din."



Badaru ya dunga murmushin farin ciki, sai yakeji a ransa kamar ta dawo ta gama.  Dan haka yace "Abba inaga gobe kawai su dawo da ita,  yanxu xanje inga inda xata zauna acan gurin Nafee kafin in samar mata gida" Abban yace to hakan yayi, bari intashi kar inyi rana. 



Bayan komawarsa gida,  yana kashingide yana tunanin maryam har wani lumshe ido yake inya tuno sweet moment dinsu. Ya gama tsara cewa dakinsa da yake ciki zai bawa maryam din kafin ya samu gida ya sai mata, bazai qara sakinta ba zai zauna da ita saboda buqatarsa.  



Yana cikin tunanin ne Nafee tazo ta dangwarar masa da baqin shayi (lipton) da breadi.  Tace gashinan babu madarar.Bai ce mata komai ba, sai dariya da yake mata a xuciyarsa. Tanai masa kallon biri yana mata kallon ayaba,  domin bazai fada mata xai dawo da maryam ba sai dai taganta.  Ya qudure suna dawowa daga gidansu Maryam din zaije yayo mata shoping na komai da komai ita kadai, Nafee kuwa taji a salansa, dan yagaji da barnar da Nafee keyi masa. 



Kamar yadda Abban Badaru ya alqawaranta tare sukayi sallah da Baffa a masallacin jumaar gidan sarki,  kuma daganan yabi Baffa gida yace suje zasuyi magana me hamimmanci. Baffa dajin haka yasan maganar Komece farinciki ya cika zuciyarsa. Abba tare da qaninsa da Baffa sukaci abinci tare a gidan Baffa.  Kuma dama ga al adar Baffa ranar juma a daga sallar juma a gida yake tahowa baya komawa kasuwa. 



Suna gama cin abinci suka labartawa Baffa maqasudin xuwansu da kuma saqon Badaru na amaida maryam din gobe (kunji fa kamar wata yarsa) harda labarin cikin Mimi sai da suka fadawa Baffa. Babu wani nuna ja ko tauna tsakuwa dan aya taji tsoro ko kuma tsawatarwa dan kar Badaru ya kuma yin saki anan gaba Baffa ya yadda da komen maryam gidansa (dan Allah ku duba inda ake wulaqanta ya mace. Ba dole namiji yayiwa mace wulaqanci ba dan yasan inma ya saketa bazai sha estalar dawo da ita ba) suka sha hirarsu cikin nishadi ya basu tabbacin gobe ana magriba A dar uma yaxo ya dau maryam su tafi. 



Suna tafiya Baffa ya shiga gida,  a lokacin qarfe uku na yamma.  Tunda tsakar gida ya dunga kwallawa mama da Mimi kira,  har ya bude parlourn Sá ya shiga bai fasa kiransu ba.  Mama ta fito ta bishi dakinsa, yace jeki ki rawomun maryam yana fara a. Taje ta taso Mimi take bacci,  Umma da Anty jin kiran da Baffa kewa Mimi yasa suka fito suka shiga dakin Baffa kamar an gayyacesu. Dan Susan tunda ya kira Mimi watace ta taso dan inba haka ba sai yayi sati bai kirata ba.  Ya jafar ma yanxu ya shigo gidan xuwansa kenan daga kaduna yazo weekend kuma yana xuwane saboda Mimi, jin kiran da Baffa yake mata yasa ya tsaya daga gefen kitchen kusa da dakin Baffa dan yaji dalilin kiran, babu wanda ya lura da xuwansa. 



Baffa ya kallesu,  Umma, mama, Anty sai kuma Mimi dake gefe daya.  Ya fadada faraarsa tare da cewa "ALHAMDULILLAHI,  Allah ya sani tunda abunnan ya faru nake adduar Allah ya sa a daidaita, to Allah maji roqon bawa yanxu Alh Inuwa da qaninsa suka xomun da xancen mayar da auren maryam da Badaru.  Domin shi Badarun da kansa yau yace ya janye sakin ta koma dakinta. Dan haka maryam sai ki hada kayanki gobe zaizo da almuru ya daukeki, basai nace miki komai ba in aurenki ya kuma mutuwa karki dawomun gida"



Mimi ta kwalolo 👀, jin abunda Baffa yace wai Badaru ya maida ita.  Ta juya ta kalli da nufin mama tayi magana, domin ita bazata iya cewa da Baffa ta gama iddah ba.



Ai kuwa mama ta magantu "Alh wani irin kome kuma?  Ai aure ya qare, tunda yau kwanan Mimi 6 da gama iddar Badaru." 



Baffa ya dakawa mama tsawa tare da cewa "Faduma karki kawomun zancen banxa mana,  yarinya da akace tana da ciki itace xakice ta gama idda?"


Mama ta hade rai cikin shirin ko ta kwana😡. Umma tai saurin sa musu baki a maganar da cewa "a ciki kuwa akwaishi dan ko mu munsan dashi, sai dai in Faty ce ta jagoranci " maganar ta katse a dalilin hararar da mama ta watsa mata.  Abun ya bata mamaki domin ko da wasa mama bata taba harararta ba,  dan haka yau da taga fadiman na shirin canjawa taja bakinta ta tsuke saboda kar girmanta ya xube. 



Baffa shima ganin mama tayi fuskar shanu tana hararar Umma yasa ya bar maganar ciki. Yace "to shikenan ai duk da haka akwai mafita bara in kirawo Alh inuwan suxo da daddare a daura aure ya wuce da matarsa"



Mimi da mama suka kalli juna a razane. Mimi ta dago kanta cikin dakiya tace "Baffa karka kirawoshi,  nikam nagama auren Badaru in shaa Allah,  Allah ya hada kowa da rabonsa na alkhairi"



Baffa ya taso mata cikin hargowa yace "ke ki kiyayeni kuma aure dole ki koma,  kina zaton akwai wanda zai aureki inyaji abunda kika shukawa tsohon mijinki ya sakeki a wata 5? Kinsa ana zagina a gari kamar ni ace inada bazawara a gidana? Kin batamun record din gida.  Saboda haka dole ki koma gidansa ayau basai gobe ba"



Ba tare da wani shayi ba ko shakka, domin xuciyarta ta gama bushewa.  Ta dago kanta tace "Baffa bazan koma ba wlh,  saboda ni kadai nasan irin wahalar da nasha a gidansa"



Baffa ya dauketa da wasu irin maruka guda 2, tare da cewa "ni xance kiyi abu maryam kice baxakiyi ba? Lallai na yadda Badaru yayi haqurin zama dake.  Kuma wlh sai an mayar da aurenki ayau, inyaso ni dake aga wanda ya haifi wani"  



Idonta jajur saboda zafin marin da Baffa yayi mata, ta kuma dagowa ta kalleshi tace "wallhil azeem bazan koma gidan Badaru ba,  da inkoma aurensa gara inshiga duniya." 


Umma da Anty dake gefe suna kallo tun abun na burgesu har ya koma basu tsoro, suka kwalalo ido dan yau Mimi ta shayar dasu mamaki. 


Baffa kuwa baiyi wata wata ba ya tashi yasa hannu ya rufe mimin da duka kota ina. Nan take kuwa jini ya fara fita ta hancinta wato habo. Mama ganin jini na xuba a hancin Mimi ta runtse ido,  xuciyarta na tafasa tana kai kawo.  Mimi kuwa duk dukan da Baffa ke mata bata fasa fadar "wlh ko kasheni xa ai bazan koma gidansa ba" Baffa yaje ya ciro wayar receiver ya nufi Mimi da niyyar sake dukanta dan yagaji da dukanta da hannu, yana cewa "to ayau kuwa xaki barmun gidana bayan na gama fasa miki duk jikinki da duka dan ban haifi dan da zai fada in fada ba"


Mama tai saurin tashi tasha gabansa (ta shiga tsakaninsa da Mimi) tare da cewa Alh Buhari karka qara dukarmun ya, domin baka tayani naqudar kawota duniya ba.  Haka kawai kasa marainiyar Allah a gaba sai jibga kakeyi kamar kana dukan namiji dan uwanka. Ai ko musulunci bai baka dama kai mata auren dole ba a matsayinta na bazawara"



Umma da Anty dake gefe abun ya basu mamaki kwarai,  Anty ta kasa haquri ta miqe tare da cewa "amma kam kedai fadima baki da kunya baki da kara, yanxu sunan mijin naki kike ambata tare da yi masa tsawar ya daina dukar miki ya? Ai ab" kafin ta qarasa abunda tai niyyar fada mama ta dauketa da mari, tare da nunata "👉🏼 ke! Na kasa dake balle ki dauka?  Da wanda ya ajiyeki nakeyi" Anty da tasha mari ta dafe kunci tana kallon mama cikin kidima, Umma kuwa nan take ta kuma shiga taitaiyinta. 


Mama ta maida kallonta ga Baffa da ke tsaye nayi mata kallon mamakin abunda takeyi taci gaba da cewa "ni har a fadamun kara akan yayana?  Nagaji nagaji da abunda kake jagorantar matanka kukemun haqurina ya qare.  Kuma yau na tabbatar da AL AMIN baya duniya, domin da yana raye da ko cikin shege maryam tayi zai karba ya rufa mata asiri.  Duk cikin yayanka wa kayiwa auren dole?  Sai yata, saboda qasa ta rufe idanun ubanta ko?  Nagaji da abunda kakemun nagaji da wariya akan yayana,  ai koda ace ba yayan dan  uwanka bane kayimun kara.  A karatu ka fifita yayanka akan nawa,  a wajen tarbiya da nuna soyayya ka fifita naka akan nawa,  a wajen aurar da yayama salon auren yayanka daban da nawa,  sannan ka debi yayanka ka dunga kaisu saudia kabar nawa, to shin ubansu bashi da gado a dukiyar da kake facaka da itane ko kuma sudin shegu ne?  Duk abubuwan da kakeyi ina sane kuma ina ganewa domin ni ba mahaukaciya bace kamar yadda kuke xata.  Sannan akan wani banxa Badaru ka mayarmun da ya baiwa me aikin gidanka,  sannan kuma yanxu kana nema kasa yata ta shiga duniya saboda Badaru? Shin wai maryam yar dan uwanka ko Badaru?  To tunda kana qaunar Badaru ka dauki daya daga cikin yayanka ka aura masa. Tunda anyi ruwa qofar dakin kowa ta jiqe (ma ana kowa yana da yaya) duk cikin yayanka wacece take maka biyayyar da Mimi take maka? Amma duk da haka kafi tsanarta kafi wulaqantata bansan abunda ta tsare maka da kai da yayanka da matanka ba kun tsangwamarmun ya kun takurata, to wlh duk wanda ya qaramun abunda bai gamsheni ba akan yayana sai yaga tashin hankali. Ko kasan cewa akan takurar da kaiwa Mimi har yunqurin kashe kanta tayi? To wlh Buhari duk randa maryam ta kashe kanta saboda takurar da kake mata wlh sai nayi sharia da kai daga nan har kotun duniya. Kamar yadda kasha fada kuma kake nunawa a aikace cewa Mimi ba yarka bace to yau na tabbatar maka cewa FATIMARYAM ba yayanka bane yayan AL AMIN da FADIMA ne.  Saboda haka na yanta yayana daga barin yi maka bauta. Abu na qarshe dazan fada maka shine : kamar yadda kace Mimi tabar gidanka xata bari,  amma ni da ita xamu barmaka gidan tare domin saboda su nake zaune a gidannan inkuma ankore su banga xaman da xanyi ba." 


Ta juya ta kama hannun Mimi tare da cewa "taho maryamu daga yau na yanta ki" Baffa yayi sakato kamar an dasashi jikinsa yayi mugun sanyi  wata irin kunya wacce bai taba zato akwaita ba yakeji. Ashe duk abunda yakewa fadima tana sane? Lallai ya dade yana zaluntar wannan baiwar Allah da yayanta, yau ta fada masa abunda bai taba tunani ba kuma shi kansa baisan hujjarsa ta nuna banbanci tsakanin yayansa da yayan dan uwansa Al amin ba.  Lallai mai haquri bai iya fushi ba yau fadima ta zame musu horo, yasan tabbas abunda ta fada gaskiyace tsantsan duk yayansa babu mai masa biyayyar da Mimi keyi masa kuma babu wacce yayiwa auren wulaqanci irinta. Kuma wlh baisan abunda yasa yakewa Mimi haka ba, kuma yasan da Anty ko Umma yakewa yayansu abunda yakewa Mimi wlh da sai anyi yaqin duniya na uku. Muryarsa a tausashe yace da mama dake shirin fita daga parlourn "ban baki izinin fita daga gidannan ba daga ke har maryam" Umma da Anty suka kalleshi jin abunda yace suka jinjina kai.  Domin sun dauka zai saki fadima ne nan take, da daya daga cikinsu ce da tuni ya sender ta gida.



Mama na fitowa daga dakin Baffa ta tsugunar da Mimi a bakin fanfo da nufin wanke mata jinin daya bata jikinta.  Jafar da ya gamajin abunda ke wakana yayi saurin xuwa kitchen ya dakko mata ruwa a freezer ya miqa mata, ta karba ta wankewa Mimi fuska dashi.  Nan take habon ya tsaya, taja hannun Mimi suka shige dakinta. 


Jafar ya furta "jarumar uwa" ta jure abubuwa da yawa akan yayanta sannan lokaci daya ta kwatarwa Mimi yancinta.  Ya dunga farin cikin jin Mimi ta gama iddah yace "in shaa Allah maryam matata ce"



Har magruba tayi mama bata fito ta dora girkin dare ba duk kuwa da cewa ita ke da girkin. Anty ta samu Baffa har daki yayi tagumi tanayi masa mitar cewa,  mama bata dora girki ba mai zasu bawa yara suci?  Ya dago ya kalleta yace "ku masu yaya bakuje kun girka kun basu ba sai ita me ya guda daya? Saboda haka karku dameni" Anty ta ruqe haba cikin ranta na jinjina soyayyar fadima a gurin Baffa,  wato duk abunda tayi batai laifi ba kenan? Har marin da tayi mata 🤣. Ala tilas taje ta dora jellof din taliya dan lokaci ya qure kuma itace me qananan yaya. 


Bayan ta gama ta hana kowa sai Baffa kawai ta xubawa ta kaima masa daki,  shi kuma ya tambayeta da cewa kin kaiwa fadima? Ta harzuqa tace "aini bata shanye ni ba kamar yadda ta shanyeka ba, saboda haka ban kai mata ba dan ba xamanta nake ba.  Ana cikin hakan Umma ta shigo tana tambayar Anty ina nata abincin?  Tace nima dafawa nayi ni da yayana kema kije ki dafa dan ba baiwarku bace ni.  Umma tace dakata karkiyimun fitsara inba haka ba yanxu in wanka miki mari dan naga sai anmareki kike samun nutsuwa 😂. Anty da jin haka ta harzuqo suka fara cacar baki ita da Umma.  Baffa ya katsesu da cewa ko suyi shiru su bashi guri ko kuma kowacce ta tafi gidansu.  Anty ta cije lebe da cewa ai dole kace mu tafi gida,  ita wacce  ta qare maka zagi daxu ai ta kwana lfy saboda ta iya bun malamai. 


Daya fita sallar isha ya biya ya siyowa mama da Mimi qatuwar kaza da fura roba biyu, jin cewa ba a basu abinci ba. (lallai mama ta motsa kwanji 😄) ya shigo Anty na alwala a tsakar gida kuma taga ledar daya shiga da ita dakin mama.  Har ta miqe xata bishi sai ta tuna marin da tasha daxu dan haka ta koma ta xauna.


Yasameta xauna akan kujera ita da Dady suna kallon mbc 3 Mimi kuma tana kujera zaman mutum daya da digital casbaha a hannunta tana dannawa.  Baice musu komaiba sai ajiye ledar da yayi kan qafar mama ya fita.  


Dimin da taji shiya tabbatar mata abinci ya kawo musu,  kuma dama shiri take ta tashi ta samar musu abunda xasuci.  Dan yau jin ranta take sawai,  abunda yake ranta shekara da shekaru yau ta amayar dashi.  Dan haka ta dakko musu faranti da cups sukaci kazar suka sha fura suka qulle dakinsu suka kwanta,  daga ita har Mimi basu garka ba sai asuba sun sami bacci me nauyi. (dole tunda anraba xuciya da damuwa)


Mrs
[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 3⃣3⃣

Dedicated to 
Sahura Musa Mohd (ina cigiyarki)



Baffa kwana yayi yana tunani,  haqiqa yayi kuskure yayiwa fadima abubuwa da yawa kuma babu wanda ya taba fada masa yayi ba daidaiba.  Tabbas yaci amanar Al amin,  yayansa kwaya biyu yakasa hadawa cikin nasa yayan ya rike.  Kuma dole su Faty sunada gado a dukiyarsa domin tunda Al amin ya mutu ya tattara abunda yabari ya riqe,  ko mama bai sallama ya bata tumunin takaba.  Su bai basu dukiyarsu sun mora ba su baiyi masa da tasa ba.  Dole zaisan abunyi akan dukiyarsu,  ko bebawa su Faty tasu ba dole zai sallami mama da tumuninta.



Ta bangaren Mimi kuwa,  baisan dalilin tsanar da yayi mata ba.  Amma yasan akwai tagomashin matansa wadanda Kullum cikin kawo masa sukar Mimi suke.  In yayi kallo xuwa hallayyar yarinya sai yaga yarinyace sassanya wacce ko acikin gida ake hira da wahala kaji harshenta, sai dai in anyi abun dariya tayi.  Gata da kirki da qarfin xuciya,  duk da bata cika lfy ba Kullum xaka sameta cikin aiki ko a tsakar gida ko a dakin uwarta.  Bata da qashin cewar bazatai aiki ba saboda akwai yan aiki a gidan kamar yacce yayansa keyi.  In kuma yanason ai masa abu misalin gyaran daki ko wani aiki to Mimi yake sakawa domin tana tsayawa ta yishi babu hainci wanda ko matansa basu iya yimasa shi tsaf kamar nata.  


Dan haka ya fuskanci xuga ce jigon tsanar da yakewa Mimi,  sai kuma issue din rashin aurenta da wuri wanda ya dauki hakan iya shege.  Dole ya kawo canji domin yanason fadima kuma bazai iya rabuwa da itaba,  yanxu gashi tana shirin rabuwa dashi saboda Mimi. Nan take yaji rabin tsanar da yakewa Mimi ta tafi. Afili ya furta Fadima nagode da kika karantar dani kuskurena da wuri tunkan in mutu Allah ya kamani da haqqin xumunta dana marayu.  Kuma daga yau xan sakarwa yarki mara tayi irin rayuwar da take so. 


Lokacin da yafito domin tafiya masallacin asuba ya kirawo masu aikin gidan  yace su karbi aikinsu yau sannan ya fita. 


Mimi kuwa bayan ta iddar da sallar asuba ta gaida mama,  mama tace mata kije kiyi registration din tafiya service din yau.  Mimi tayi rau rau tace " mama ai anrufe sun kusama tafiya camp domin har call up dinsu ta fito" mama tace to kiyi haquri haka Allah ya shirya kaje wata shekarar"
Anan kitchen din cikin parlour suka hada break fast sukaci,  domin mama ta quduri aniyar kwatar yanci. Tunda ya hanata tafiya ai sai tayi yajin a dakinta.


Badaru yadda suka kwana da Nafee jiya yauma haka suka kwana,  domin shima ya bar mata abunta yace ta jiqa tasha.  Aransa kuwa cewa yake ni da xan kwana da maryam yau dan anhanani wannan ruwan daurayar ai ba wani abu bane.  



Wajen qarfe goman safe yaje gidansu,  dake asabar ce kuma basa fita kasuwa weekend da wuri duk ya samesu a parlour.  Har Badamasi da yazo weekend. 


Ya zauna ya kwashi gaisuwa gurin iyayensa,  ya juya suka gaisa da Badamasi sama sama domin Badamasin yanxu yake samun lbrin saki da kuma maida maryam da Badaru yayi sannan da zancen auran da yayi.  Dan haka yaji yayi mugun tsanar Badaru sabida maryam. 


Badaru ya kalli Abbansu yace "Abba inaga da yamma xanje in dauko maryam din,  saboda inason inkaita store tayi shoping din kayan abincinta da kanta inyaso sai mu wuce gida daga can" 


Abban yace to babu laifi,  bari na fadawa Alh Buharin saboda karkaje bata kimtsa ba" Umma dake gefe tana murmushi aranta taji dadi ga dukkan alamu Badaru ya gane mahimmancin maryam, dan haka tace "Alh ai da ya kira maryam din da kansa yace ta shirya da wuri zaizo da yamma" 


Badaru ya sunkuyar da kai cikin kunyar abunda xai fada yace "ai bani da lambarta" babu wanda yace masa komai sai Badamasi dake watsa masa harara kamar ya tashi ya dakeshi. 


Abba ya ciro wayarsa yace bari na fada masa da kaina. Lokacin da kiran Abba ya shigo Baffa na xaune yana karyawa Umma na gefensa ga dukkan alamu itace tayi girkin tunda mama tayi bore. 


Ya daga suka gaisa,  har yanxu jikin Baffa a sanyaye yake.  Abba ya fada masa buqatar Badaru.  Baffa yace "ai Alh inaga sai dai mu haqura domin yarinyar har ta gama iddah, kaga babu maganar kome kenan?"


Abba dajin abunda Baffa ke fada yasa wayar a hands free domin Badaru yaji abunda Baffa yace.  Abba ya maimaita abunda Baffa yace "ta gama idda?" Baffa yace "eh"


Badaru ya dafe qirji yace "to cikin jikinta fa?  Xubarwa tai?" Baffa da yaji abunda Badaru yace saboda hands free din da aka saka yace "ita dai tace babu ciki kuma iddarta ta cuka tun kwana 6 baya" 


Abba yayi saurin cewa "to ai abun bai baci ba har yanxu,  tunda yayi nufin maidata sai mu kawo sadaki in anjima a maida auren" Badaru yayi saurin gyada kai cikin gamsuwa da abunda Abba yace"


Sai dai muryar Baffa ta katse masa hanxari inda yake cewa "Alh sai dai muyi haquri inaga iyakacin xaman da Allah ya rubuta musu kenan, domin nima na kawo batun maida auren maryam ta nuna bata da raayin kuma xama dashi dana takura sai anmaida auren adalilin hakan nima xaman lfyar gidana ya tabu,  domin uwarta tace baza a kuma yiwa yarta auren dole ba har tana barazanar dauke yarta su barmun gidana.  Ni kuma inason matata kaga garin gyara kuskuren Badaru aurena zai mutu,  gara kawai a haqura." 



Abba ya kashe wayar cike da jin haushin Baffa, yana mitar kamar Buhari ya zauna mace na juya shi?  To kada Allah ya sa maryam din ta dawo,  metafi Badarun ai Badaru ba illah ce dashi ba babu inda xaije neman aure ba a bashi ba (kuji san kai?)  


Badaru tunda ya gama jin abunda Baffa ya fada gabansa ya yake ya fadi,  qirjinsa ya dunga bugawa sai yanxu ya tabbatar ya tafka kuskure.  Tabbas yasan maryam bata sansa,  wlh da yasan haka xata kasance da bai saketa ba.  Ta xubar masa da cikin da yake ganin shine tsanin da xai dunga hadasu. Umma kuwa hawaye takeyi jin maryam ta bar xuriar ta, tasan Badaru yayi rashi.  


Badamasi kuwa dake gefe fuskarsa a washe sai murmushi yake.  Ya dunga godewa Allah a xuciyarsa,  yace lokacin aurena yayi, maryam ta dawo.  Jin fadan abba yaqi qarewa kuma Abban baya blaming kowa sai Mimi,  shiyasa ya matsa gaban Abban,  baice komai ba sai wayarsa da ya ciro ya kunna recording din da ya tabayi wanda Badaru ke tsagin Mimi da korarta daga gidansa.  Yace Abba ku saurari wannan"



Sukayi tsit har Badaru suna sauraran recording din harya qare sannan Badamasi ya dora musu da sauran abunda yagani na zamantakewar auren da kai Mimi asibiti da yayi da kuma abunda yakeji lbr gurin abokan Badaru. 



Jikinsu yayi mugun sanyi, Umma kuwa kuka take tana kallon Badaru a razane.  Ta kalli Abba cikin kuka tace "Alh kaji abunda nake fada maka ko? Kake goyon bayansa,  wlh nasan sharri yayiwa yarinyar nan,  ai dole tace baxata xauna dashi ba saboda ya azabtar da ita,  inma cikin ne ai baqin cikinka ma ya isa ya xubar da cikin.  Kuma wlh indai nadama ce baka fara ba,  ka cuceni ina qaunar yarinyar nan ka rabani da ita"  ta qara fashewa da kuka.  Abba ma ya kalleshi yace "baka cuci maryam ba,  ba kuma ka cuceni ba kanka ka cuta.  Na yarda da kai kasa ina jin haushin yar mutane ashe kaine babban dan iska,  sabida haka kajira sakamako wlh sai Allah ya saka mata"



Badamasi ya matsa kusa da qafar Umma ya riqo hannunta yace "Umma share wahayenki,  baki rabu da maryam ba,  maryam xata dawo cikin xuriar ki kuma a matsayin surukarki,  domin xan auro maryam.  Idon kowa a gurin ya dawo kansa.  Yaci gaba da cewa tun farko ni naga maryam, ni na fara sonta,  ni nafara yi mata magana.  Ina shirin inje innemi soyayyarta Badaru yazowa Abba da maganar aurenta ganin haka yasa na haqura,  amma wlh da nasan Badaru haka zai maltreating maryam wlh bazan haqura in bar masa ba.  Saboda haka Umma ban taba neman abu a wajenku ba yanxu nazo da alfarmar neman goyon bayanku akan neman auren maryam,  ba haram bane dan Allah ku kauda kai a magoar mutane ku goyamun baya." 


Umma ta share wahayen farin ciki,  ta shafa fuskar Badamasi tace "na baka goyon baya 100%, nasan bazaka wulaqanta maryam yanda Badaru yayiba Allah ya sa rabonka ce"  ya juya gurin Abba yace "Abbana inkace in haqura xan haqura"  Abba ya kalli Badamasi a nutse yace " na baka goyon baya likita,  indai har kun daidaita kanku da kaina xanje gurin Alh Buhari a karo na biyu in nai mar maka aurenta" ya dunga godia yana dariya ji yake indai Mimi ta amince nan da 2 wks xa ayi komai a gama.  Yau yana da daurin auren abokinsa a Danbatta amma gobe in shaa Allah zaije su gana. 



Badaru da tunda Badamasi ya fara magana yake kallonshi har ya gama,  ya tashi idanunsa jajur da tsabar kishi ya tari gaban Badamasi cikin sigar rigima yace "oh dama ashe san maryam kake?  Shiyasa ka hure mata kunne ta ciremun ciki ta gujemun sannan ka nado sirrinmu ka kawo ko?  To wlh baka isa ka auri maryam ba indai ina numfashi,  kai ko kunya bakaji ka auri tsohuwar matata? Ban taba neman abu na rasa ba, na auri maryam da farko kuma yanxu ma xan kuma aurenta domin wlh saina kasa ka,  ka rubuta ka ajiye,  inkuma ban aureta wlh sai dai ayi biyu babu kowa ya rasa."


Badamasi yaja da baya ya kalleshi yana dariya yace "ka saba yiwa kanka kirarin duk abunda ka nema kana samu,  amma inkasamu baka iya alkinta abun,  kaga kodan haka Allah xai iya jarrabarka,  saboda haka maryam dai yanxu rabonace in shaa Allah gara kaje ka lallaba kucakar matarka ku zauna lfy.  Kuma ni bazan fada da kai ba domin yau cikin farin ciki nake dan haka kaje ka nemi irinka looser  kuyi " 


Badaru yakai masa duka Badamasi ya tare tare da cewa kasan in dambe xamuyi wlh karyaka xanyi ka wani tara teba sai kace me ciki.  Abba ya daka musu tsawa tare da ja musu warning.  Kowanne ya fita yana hararar dan uwansa.  Umma tace "Alh baraka fa xata bullo idan bamu tashi tsaye ba"


Abba yayi shirin fita kasuwa ya leqa dakin Badamasi yace "Bani wayarka ka saitamun gurin maganar nan, gara insami Alh Buhari in wanke yarinyarnan a gurinsa." Badamasi ya bashi wayar tare da bude masa recording din,  yana xuwa play kawai xai danna. 



Baffa naganin Alh Inuwa a shagonsa ya hade fuska,  don a xatonsa xuwa yayi ya qara neman alfarmar mayar da Mimi.  Amma sabanin haka sai yaji yana bashi haquri tare da neman itama Mimi abata haqurin, kana ya budewa Baffa recording din ya saurara.  


Baffa yayi matuqar tsorata da lamarin Badaru,  ya kalli Alh inuwa yace " kace dan iska ka kawomun cikin manyan kaya ni kuma banyi bincike ba na dauki salihar mace na bashi" Alh inuwa yace "wlh Alh bansan abunda Badaru ya aikata ba kenan, shiyasa na kawo maka abunda yayi kaji.  Amma dan Allah kayi haquri  kuma ka bawa maryama haquri babu hannuna a abunda aka aikata mata kuma wlh da nasan haka zaiyi da ban nema mishi auranta ba"  Baffa yace " shikenan nagode da sanar dani da kayi shi kuma ya je dan kansa ya cuci marainiyar Allah"


Baffa yayi sakato yana tunani,  lallai ya tafka kuskure a baya.  Ya dauki ya yabawa dan iska yana zaginta da goranta mata,  amma kuma duk abunda Badaru yayi bashi da laifi, shine babban mai lefi da bai riqe su da daraja ba kuma ya nuna maryam din ba wata bace.  


Tausayin Mimi da soyayyarta ta dirar masa nan take,  dole Mimi tace bazata koma gidan Badaru ba saboda ya zalunceta sannan ya biyota da sharri shi kuma ba bincike yahau ya xauna.  Jin soyayyar Mimi yake har cikin bargonsa kuma yaji yana kunyar hada ido da ita da uwarta. 



Badaru na zuwa gida ya samu Nafee a parlour tana kallo, ya kalli parlour komai kaca kaca ya kalleta da yake a kusa yake neman masifa yake sai yace "ke haka ya dace kibar guri ki xauna kina kallo dake ke jaka ce?"


 Ta kalleshi sheqeqe tayi dariya tace " jakai dai,  ni da kai in ban gyara ba kai baka da hannun gyarawa?"  kafin ta ida fada ya kifa mata mari.  



Batai wata wata ba ta dakko plate din da ta gama cin indomie yanxu ta jefa masa tana huci, sannan ta dora da cewa "ga dukkan alamu ka saba ganin tsohonka na jibgar gyatumarka shine kazo xaga gwada a kaina,  to wlh duk randa ka qara dukana wlh saina sake maka kaciya 😳"



Ya tsorata da mutuqa da maganar Nafee,  bece uffan ba ya shige bedroom dinsa,  ya rasa abunda yake masa dadi.  Shi yanxu yasan duk wanda ya fadawa abunda Nafee ke masa dariya zaiyi saboda yacce ya daukaki Nafee.  Ya dunga juyi akan gado ya kasa bacci,  har akai sallar laasar bai fito ba ga yunwa na addabarsa kuma yasan Nafee yau bazata bashi abinci ba.  Ya tashi yayi wanka yayi sallah,  ya zabo kayansa na qure adaka yasa.  Gurin maryam xaije ya bata haquri ya nemi yafiyarta,  yasanta da sauqin kai xata haqura su koma aurensu. 


Ya samu Nafee zaune ta cokala dauri ture kaga tsiya tana sanaar (kallo), ya tsaya domin yayi mata magana,  ta dauki remote ta qure volume alama batason jin abunda xaice, dan haka ya fice. 



Ya dade a qofar gidan Baffa babu dan aike kuma bashi da no Mimi. Mimi ta fito domin zuwa gurin fauxa,  tana sawo kai waje idonta cikin na Badaru gabanta ya yanke ya fadi ta diririce,  ta juya da nufin komawa gida yayi wuf ya damqe hannunta yajata cikin sit room din dake soron farko. 



Cikani, baka da hankaline xaka riqe mani hannu? "ta fada cikin fita hayyaci.  Ya sassauta riqon da yayi mata, amma still yana riqe da ita karta gudu ya fara magana murya a kwance " maryam dan Allah kiyi haquri nasan na bata miki naci zarafinki na hadaki da iyayenki na tauye haqqinki na kuma toxarta ki. Amma wlh nagane kuskurena abaya na aureki ne dan shaawa amma xaman da mukai da ke nagane kyawawan halayenki da son addininki hakan ya jawo miki soyayya a gurina." Mimi tayi sakato tana kallonsa wai dama Badaru ya iya magana a hankali?  Kuma dama yasan duk abunda yake ba dai dai yake ba? Tambayar da takewa kanta kenan. 


A bangare guda kuma Baffa dake azumi (azumin kaffarar rantsuwar da yayi ta Mimi saita koma gidan Badaru, ya fara yau) ya dawo gida da wuri domin ya kawo salad din da yakeso a kwada masa yayi buda baki dashi.  Yana xuwa soro aci burki dan jin maganganun dake fitowa daga sitroom.  Da farko bai gane mai maganar ba,  amma jin an ambaci sunan maryam ya gane me maganar da inda maganar ta dosa.  A fili yace lallai wannan yaron bashi da kunya bari inje inyi masa tsakani da yata. 



Sai dai muryar Badaru ta katse masa hanxari inda yaci gaba da cewa "maryam ki tunano rayuwar auratayyarmu me dadi 🙈, ke bakya tunawa? Wlh kullum cikin kewarki nake da mafarkinki,  ki dawo muje mu zauna duk abunda kikeso zan miki   duk yan uwanki na gidan miji ke kadaice kika rage,  kin wuce xaman gida ki dawo dakinki shine rufin asirinki"




Ta katseshi da cewa "xaman gidanmu yafiyemun zaman gidanka,  kuma lokacin da sakeni ka wurgoni kofar gida baka duba cewa na wuce xaman gida ba sai yanxu? Rayuwar auratayya kuma da kake fada kaika santa har take maka dadi,  abunda kawai zan iya dorarwa aciki shine: fyaden da kakemun duk daren duniya.  Abubuwan kuma da kayimun a duk xamanmu na barka da mahaliccinka shi zaimun sakayya." tana kaiwa nan ta fusge hannunta ta kifawa Badaru mari,  kafin ya gama mamaki ta kifa masa wani 😳. 



Ta dora da cewa " yau alqawari ya cika, lokacin daka mareni a gidanka na fada maka cewa wlh saina rama gashi kuma na rama din.  Zagin ubana kuma da kayi kace inje in haqoshi a kabari,  bazan rama ba,  domin nasan darajar iyayena sannan nasan duk daren dadewa naka uban xaije inda nawa yaje.  Gida kuma basai nace karka kuma xuwa ba,  saboda bata dalilina ka fara xuwa gidanba."



Baffa dake sauraransu yayi murmushi cikin jin dadin abunda Mimi tayi yace "yar halak kenan, tayi alqawari ta kuma cika maryam jinin Al amin ce domin ga halinsa nan a jikinta. 

Ta fito ta koma gida memakon gidansu fauxa da tayi niyyar xuwa,  shiyasa bata kula da Baffa ba dake tsaye a qofar fita.  Badaru ya gama mamaki ya jawo qafafuwansa jiki babu kwari yayi hanyar waje,  yaci karo da Baffa. Baffa ya nunashi da yatsa yace "karka kuma xuwarmun gida,  in kuma ka kuma xuwa xan hadaka da hukuma" yana fadar haka ya shige gida.  



Washe gari lahadi da yammaci aka aiko kiran Mimi,  har taqi fita mama tace taje in Badaru ne taxo ta fada mata.  Sai dai me tana fita taga Badamasi a tsaye. Tana ganin mutuncinsa dan haka tai masa iso sit room. 


Ya xauna suka gaisa a mutunce ta tambayeshi mutan gida da gurin aikinsa. Yayi farin ciki ganin maryam din ta fara dawowa hayyacinta ba kamar lokacin da tana gidan Badaru ba, ya dunga hasketa da murmushi yana kuma jinta a xuciyarsa.   Yayi mata jajan mutuwar aurenta,  tace ba komai iyakacin xaman da Allah ya nufa kenan. 


Ya karanto mata abunda ke cikin xuciyarsa,  ta dunga kallonsa a kidime ba tace komai ba ta miqe da nufi fita.  Yayi saurin shan gabanta yace "maryam wlh babu inda xaki sai kin fadamun matsayina a xuciyarki,  inbaki manta ba nina fara sonki Badaru furtawa ya rigani indai ba so kike inyi hauka a kanki ba ki amshi soyayyta" itadai babu baka sai kunne,  domin kanta ya daure da yawa. 


Da yaga taqi magana saiya kamota ya sata a bango yayi mata rumfa da qirjinsa yasa hannu ya katangeta ta inda duk motsin da tayi saita taba jikinsa.  Yakai fuskarsa dab da tata ya fara magana "Mimi ki laluba xuciyarki bazaki rasa soyayyata aciki ba,  ba halinmu daya da Badaru ba soyayyar da nake miki bazata bari in cutar dake ba,  xan kula dake xan baki yancinki,  xakiyi duk abunda kikeso, bazan tauyeki ba irin rayuwar da kike mafarki xakiyi. Maryam fargabar me kikeyi?  Bazan akiyeki kusa ba balle a dunga yi miki surutu,  can gurin aikina xan tafi dake sai dai kixo da yawo." 


Ganin cewa kamar baya cikin hayyacinsa yasa tayi niyyar yimasa dabara.  Dan haka tadan dauke kanta daga fuskarsa,  yayi saurin dawo da fuskarta kusa da tasa har tanajin numfashinsa,  yace "yimun magana a haka in san cewa mafarkina ya kusa xama gsskiya."  tayi qasa da murya tace "kadan bani lokaci inyi tunani inkuma yi istikhara" 


Tunda ta fara magana, ya lumshe ido yana shaqar hucin bakinta.  Sai data gama sannan yace "to shikenan,  xanso hakan nima kuma nima zanje inyi sallatul istikhara.  Saboda haka wani satin xan dawo saboda gobe xan koma Dutse" ya dakko kudin da ya ware zai bata 10k ya lalubi hannunta ya manna mata.


Ta kalli kudin ta kalleshi tace "ai basai ka bani kudi zan soka ba."  ya kalleta hankalinsa ya kuma kwanciya da ita yace nasani maryam amma ai kyauta ce.  Tace "nasani amma ka riqe wata rana ka bani"  yayi murmushin cin nasara yace "to my soul"

Ya nemi ta bashi no dinta tace wayar na gida kuma bata ruqe no dinba,  dan haka ya bata tasa xata kirashi.  Dake ya makance a soyayya be gane cewa wayo taimasa ba,  ba musu ya dakko katinsa na gurin aiki ya bata. 


Mama tayi matuqar kaduwa dajin wai Badamsi keson Mimi,  tace "duk da ba haramun bane ai ana barin halak dan kunya,  kuma naji dadi shine gari.  In shaa Allah ko wanda sunansa ya fara daga BA bazaki auraba. Yazaki qara fita yayi haukansa ya gama"



Ranar litinin ranar Baffa ya dau azuminsa na qarshe,  kuma yau ya shirya tunkarar mama akan fushin da take dashi. 


Da yamma ya shiga har dakinta,  ya sameta xaune a kan kujera Mimi tana kwance tayi pilo da cinyarta tanacin chocolate.  Tana ganinsa ta miqe daga kwanciyar,  mama tace mata Mimi shiga ciki.  Ba musu ta shige bedroom din. 



Baffa ya xauna ya fara da bata haquri akan dukkan abunda ya dade yana yimata da kuma godia akan tunasar dashi da tayi, kana ya dora mata da abunda baban Badaru ya kawo masa yaji a waya da kuma abunda yaji da kunnensa Badaru na fadawa Mimi.  Yace yagane kuskurensa kuma ya canja daga yanxu,  kuma Dan Allah ko anan gaba taga yana nufin kauce hanya a wani abun tayi gaggawar tunasar dashi, domin yagane itadin macen arxiqice.  Sannan yayi mata xancen tumunin takabarta yasa an fitar mata a kotu tasamu gidaje biyu da wajen miliyan biyu (saboda andade ana juya kudaden) ya karbi acct no ta da nufin tura mata kudaden ya kuma danqamata takaddun gidajenta.  


Ya kwallah Mimi kira,  ta fito ta tsuguna. Rayuwa kenan duk wanda yayi haquri zaiga haske domin wai yau Baffa ke neman yafiyar Mimi da kuma bata haquri akan abunda duk ya faru a baya.  


Mimi tana hawaye tace "komai ya wuce Baffa,  kai ubanane duk duniya bani da wanda ya fika,  nima ka yafemun abunda nayi maka rannan saboda bani da xabi sai hakan shiyasa nayi" yace baki komai ba MARYAMU  Allah ya miki albarka ya baki abokin xama nagari sakamon biyayyar da kikaimun. 


Mama na gefe na share hawayen farin ciki,  ta dunga godewa Allah.  Tace da Baffa nagode da kulamana da dukiya da kayi.  Amma inaganin wadannan ka karba ka riqemun."


Yace "riqe abunki Haj Fadima,  nadai riqe na yayana Faty da maryam kuma suma na rubuta da shedu saboda halin rayuwa, gidajen dai xantsaya a xuba yan haya."  tace to duk yadda kayi nagode.  



Yace " to ai bazan yadda kin huce ba sai kin karbi girki,  ga cefane can nakawo inaso aimun special girki dan azumin nake kuma nadade banci delicious dinki ba."



Mama ta miqe tabi bayanshi tana dariya tace " yau kuwa xakici domin xan tabbatar maka na huce." Umma da Anty da tunda ya shiga dakin mama suke tsaye suna jiran suga abunda xa ai suka qiqim qiqim ganin mama da Baffa tare suna dariya.  Mimi ma ta biyo bayansu da nufin taya mama girki itama tana tata dariyar. 


Mrs 😊
[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼
AL AMARIN MARYAM 
🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼


📝FANTASTIC STARS WRITERS 
 {F S W }
 
Writing & story by 
Rahma Muhammad {hajia} 

Editing by
Mmn khairat 😍

 
   Page 1⃣4⃣


     Cike da farin ciki Baffa ya shiga gidan,  gami da kwalawa mama kira tunda daga tsakar gida,  ta fito a gigice saboda Jin kiran farautar da yake mata ta iskeshi daki gami da yimasa sannu da xuwa.  Ya amsa yana washe baki kamar bebe yaga wawan zama (Lol) sannan ya dora da cewa wani abun farinciki ne ya samemu fadima shiyasa ki ganni gida yanxu,  wato yaronnan dan wajen Alh Inuwa shine yaga Maryamu yace yanaso, kuma ga dukkan alamu akusa sukesan auren dan Alh inuwa da kansa yayimun maganar ni kuma nayi dattako nace kawai in sun shirya su kawo kayan aure kawai ayi.  Mama ta kalleshi shagarai tare da daure fuska tace,  Alh wannan wane irin neman aure ne sai kace auren yar tsana?   Daga yaro yaga Mimi yace yanaso sai ace ya fito anbashi?  Ita mimin baza aji raayinta ba?  Kuma banaji ma Mimi tasan maganar domin da tasani xata fadamun, sannan shin kayi bincike akan yaron?  Ko kuma dan ansan mahaifinsa shikenan?  Aure fa in anaso a zauna lfy sai anyi da yardar maauratan,  kuma naga ai bakai da Alh inuwa ne zakuyi xaman auren ba,  yaran ne masu xama  saboda haka inaga ku basu dama su fahimci juna inyaso daga baya insun dai daita kwa shiga lamarin. Baffa dake kallon mama tun da ta fara magana a dage tare da fallara mata harara wacce ita sam bata kula ba,  ya magantu da cewa sai yanxu nasan ke babbar mahaukaciya ce fadima.  Ta miqe tsaye tare da qara daure fuska tamau tace hauka kuma?  Yau kuma nice mahaukaciyar?  Nan da nan kuwa ya dai daita nutsuwar domin ya farga da kasassabar da yayi (ya tuna da fadima yake magana wacce Sam bata daukar irin cin mutuncin da yakewa ragowar matansa, ta nuna masa tasan ciwan kanta dan haka ko fada xai mata yakan tausasa kalamansa)  dan haka yanxu ma sai yayi saurin yin kwana da cewa ai kece naji kina qoqarin yiwa Allah butulci,  shekarar maryam din nawa ana neman miji?  Ba a taba budurwa mai shekarunta ba kaf danginki da nawa,  sai yanxu Allah ya kawo kice ga xance ga magana.  Ta kalkeshi tace ni ba butulu bace kuma ba butulcewa nai ba inaso ne dai a gina auren akan fahimtar juna da soyayya,  amma tunda haka kace shikenan Mimi yarka ce kana da ikon xaba mata miji, Allah ya sanya alkhairi yasa tsohuwar gida ce.  Yawwa yanxu kikayi magana fadima da tun farko abunda kikace kenan ai da ba a tsaya sa insa ba, amin Allah ya yi miki albarka cewar Baffa. 

       Maryam kwance saman gadonta acan hostel na law skul rubda ciki take tana danna system,  qarar Waya ya katseta daga typing din da take a system din, ta tsurawa screen din wayar ido gabanta na dukan 3 3 , tun tana qanqanuwarta ta tashi da tsananin tsoron Baffa da kuma dison qiyayyarsa acan qasan zuciyarta saboda halin ko inkula da yake da al amarinsu, duk da cewa mahaifiyarsu awancan lokacin tana boye musu lamarin baffan garesu kafun su girma su gane,  sai kuma alokacin mama take yawan cemusu halin Baffa garesu ajixanci ne irin na Dan Adam.  Amma AL AMARIN MARYAM na jinkirin aure da kuma takura gami da gorin Baffa akanta yasa dison qiyayyar Baffa ta samu girma a zuciyar maryam wanda takai tayi yado ta zama tamkar bishiya mai rassa,  domin ji takeyi kamar ta raba auren Baffa da mahaifiyarta domin auren Baffa ba abunda ya qari mama dashi sai muzgunawa da gori daga gurin matansa daga gareshi kuma xa a iya kiran abun da yaudara domin kulawar da take kwadayin yayanta su samu inta aureshi basu sameta ba.  Wayar ta sakeyin qara akaro na wajen 4 wanda hakan ya yankewa maryam tunaninta,  tai shahada ta daga wayar.  Ta gaisheshi cike da tsoro da firgici,  ya amsa farai farai tare da tambayar karatunta da kuma lokacin kammalawa,  lamarin daya daure kan maryam tamau,  acikin ranta ta farta Baffa da tambayar karatuna? 😳 first in history.  

         Bayan hakanne kuma ya zayyano mata dalilin kiranta a waya akan maganar Badaru,  sai da ta nutsu kwarai sannan ta gane wadanda yake nufi domin ita tamanta da haduwarsu,  amma kuma tayi mamaki dajin cewa wai har ana zancen qarbar kudi ba tare da sun zanta da wanda ya nuna raayin a kanta ba, (domin ita a zatonta wanda yayi mata magana shike sonta wato Badamasi) amma da yake mama batai musu tarbiyyar ja da maganar Baffa ba sai kawai tace masa to Baffa Allah ya xaba mana abunda yafi alkhairi, yaji dadin furucinta kwarai ya dunga samata albarka.  Koda ta kashe wayar tunani ya cikata to meyasa yaya Faty da mama babu wanda ya mata maganar ko dai suma basu sani ba? Sannan ta shiga wassafa siffar guy din da azatonta shine Badarun,  ta dan tabe baki 😏 tare da furtawa a fili "yayi babu laifi he is handsome " amma ba irin mijin da nake mafarkin samu bane  duk da bashi da muni amma bashi da tsahon da nakeso daga da namiji " 🙈 ta rufe idonta cike da kunya kamar wani yana ganin.  Wannan dare dai haka ta qareshi cikin tunanin irin nata salon neman auren cikin gaggawa wato haka Allah ya shirya mata kuma dama fauxa (wata qawarta yar unguwarsu)  tasha fada mata in Allah ya tashi bata miji in shaa Allah gaba daya zai fito jinkiri zai kawo mata alkhairi,   ta miqe cike da farin ciki da kwarin gwiwa ta dauro alwala ta tada sallah aranta tana cewa ashe nima zanga ranar aurena,  ashe ankusa a daina yimun gorin aure 😊. 
  
        Ranar jumaar data kasance aranar aka karbi kudin auren Mimi da kuma lefe,  da misalin qarfe 2:30 pm Faty ta shiga dakin babarta afujajan, daga gurin aiki take.  Yau dinnan zancen kawo kayan lefen ya isketa daga bakin Ahmad mijinta. Tai sallama danta na fari dady (AL Amin)  wanda yaci sunan babanta yazo da gudu ya rungume qafafunta da yake a gurin mama yake tun daga yaye,  na biyun kuma wato Muhsin dan kimanin shekara 2 tun safe suke gurin mama dashi dame rainonsa.  Ta sunkuya ta sumbaci dady tare da cewa sannu babana,  muhsin ma ya gangaro ta daukeshi tana shafa kansa.  Ta zauna akan kujera gefen mama tare da bawa laure (mai rainon muhsin)  umarnin ta dakko mata maltina a fridge,  da kyar ta ida bari suka gaisa da mama saboda xance na cinta, suka qule uwar daki.  Ta kalli mama da alamar tambaya tace mama wanene mijin Mimi?  Wane irin neaman aure ne wannan bamuji neman aure ba banusan mijin ba sai kawo lefe mukaji da sa rana? 😒 . Mama ta gyara xama cikin hikimar uwa ta gari da sigar lallashi ta kwashe zancen tas ta fadawa Faty sannan ta dora da cewa kuma shima Baffa besan har lefe zasu kawo ba,  shi kudi sukace masa kawai sai gasu da kayan lefe.  Kuma banaso ki dau dumi a lamarinnan tunda baffanku yace yayiwa Mimi maganar ta bada goyon baya kinga hakan ya nuna tanason yaron,  kuma kodan mutan gidannan inaso ku karbi lamarinnan haka Allah ya tsara muyi mata addua da fatan alkhairi.  Tace to mama ai tunda kince mimin tanaso shikenan 😊 dama ni banaso a danne haqqinta ne,  yanxu ina kayan lefen?  Suna can dakin ummanku.  Ta miqe ta nufi dakin Umman, tanasa qafa a falon ta fara cin karo da cosmetic din kayan lefen alamar angani duk an watsar ba a gyara ba. Umman na ganin Faty ta dan saki fuska da yake makira ce tare da cewa a a Faty har kin qaraso?  Tace eh suka gaisa tare da yiwa juna murna akan auren na Mimi, ana cikin hakan ne anty ta shigo baqin cikinta sam be boyuba akan fuskarta,  ta kalli Faty tare da cewa sai kuma kikaji abu babu zato?  Ai bana dai yan kwantai sai aure suke,  Faty da maganar ta bata ranta tayi murmushi da cewa aishi aure lamarine na Allah in lokaci yayi sai kikaga duk hassadar mutum sai anyi kuma sai kiga duk dadewarka babu aure abun ya zama tarihi.  Ta fada tana duba kayan Anty da taga Faty ta dagota sai tai saurin sakin zancen tare da kama wani gadai lefenan akwati 4  da kit ne kaya kala 30, takalma qafa 5, jaka guda 3, 
 Sai mayafai 6. Kodan gold qaramin Set babu,  babbar atamfa a cikin lefen itace cote d voire,  leshi bafi tsada acikin kayan kwanaki  Safna (yar antyn ce)  ta saimun irinsa a gurin aikinsu biya 2 8k  kinga a kasuwa baifi 6k  kenan? Ai wlh a tarihin gidannan ba a taba matsiyacin lefe irin wannan ba, wai lefen mai kwalin degree a hannu kenan ta qarasa fada tare da sheqewa da dariyar mugunta 🤣, sannan ta dora da cewa ana cewa jinkiri na kawo alkhairi ni dai banga alamun alkhairi ga wannan auren ba nashaji ana cewa in guga ya dade a rijiya yana jawo ruwa tsullum amma shikam gugan gidannan yayi shekaru aru aru a ruwa ya dago fayau.  Faty ta dago tai qayataccen murmushi cikin qoshi da ilimi da wayewa tace "mashaallah kaya kam sunyi mu sun ishemu haka duba da babu irin tufar da Mimi bata saba indai a duniya take kuma da kudi ake siyanta, to kinga kuwa indai ka saba saka sutura me tsada ai ta lefe baxata dameka ba,  kuma ai lefe bashine xaman aure ba mu alkhairin abun muke nema,  kuma bamusan arxiqin da Allah ya yiwa Mimi ba anan gaba kinga kuwa be dace mu sare tundaga kan lefe ba.  Tana gama fadar haka ta tattara kayan ta maida komai muhallinsa ta dubi umma wacce ke kan kujera tana kada qafa ga dukkan alamu xancen Anty akan Mimi yayi mata dadi domin ga fuskarta nan ta nuna alamar hakan.  Tace Umma Allah ya sanya alkhairi ya kuma kaimu lokacin sannan ta fice . Haka sukaci gaba da shirin biki wanda xa ayishi da zarar Mimi ta gama law skul da sati daya. 



Mrs Muhammad 😊
[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼
AL AMARIN MARYAM
🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼 


📝FANTASTIC STARS WRITERS 
{F S W }        

Page 1⃣5⃣


NA RAHMATULLAH (Hajia) 




       Kammaluwar karatun Mimi da kawo IV din bikinta abune da ya kasance a tare,  kuma aranar data dawo ne Badaru yaxo domin suga juna tare da tattauna al amuran biki ( kuji fa kamar auran qauye), da taimakon yaya Faty wacce kullum sai tazo gidan saboda shirin biki  ta shirya kanta cikin atamfar súper wax ja ta yafa mayafi kalar atamfar da dan takalminta shima ja plat, fuskarta tasha make up wanda ya fito da idanunta sukai tar saboda eye liner da mascara da akai amfani dasu wajan qayata idanunta.   Jikinta na tashin qamshin turarurukan companyn Al rehab, domin ita a raayinta tafison Arabian perfume .

           Zaune ta iskoshi a sitroom din gidan,  qamshinta ya fara sanar masa ta iso, ya dago ya qura mata ido tare da hadiye wani irin abu da ya tsirga masa maqogaro ya saki murmushi aransa yana qisima bai taba ganin macen da ta birkita masa hankali ba, idan aka dauki lokaci bai samu maryam a matsayin mata ba tabbas zai iya sabawa ubangijinsa akanta,  duk wani abu da ake buqata ajikin mace maryam tana dashi , wata irin muguwar sha awa yakeji akanta, feelings din dabe taba sanin yana dashi ba akan mace maryam tasa yana jinsa , shiyasa ya yanke shawarar auranta duk da baya sonta kuma baya raayin mace me shekaru da wayewarta,  zai ajeta amatsayin wacce zai dunga kashe qishirwar shaawarsa akanta,  sannan gefe kuma ga burin ransa wato Nafeesa a matsayin matar so.  A bangaren Mimi kuwa tana hada ido da Badaru gabanta ya yanke ya fadi a fili ta furta "innalillahi wa innah ilaihi raju un " saboda tsananin firgici data shiga na ganin Badaru amatsayin mijin auranta nan da yan kwanaki,  ashe wanda take zato ba shi bane?  Ashe ita duk hauka take?  Ashe Badamasin ma da take ganin be cika irin sharadin mijin da takeso ba , ba shine mijinta ba?  Ashe kasan Badamasin ne? Shin meyasa ta dauri kanta ta cewa Baffa ta yarda da mijin da ya bata tunkan taga kalar mijin?  Yanxu fisabillah ina ita ina wannan dan tsamurmurin bafillacen wanda tasan tafi tsaho nesa ba kusa ba???  Tambayoyi burjik ta dunga yiwa kanta a xuci a fili kuma tana hawaye,  wata irin muguwar tsanar Badaru ta shiga xuciyarta nan take.  Badaru da tun daxu yake kallon Mimi cikin mamaki, ya magantu " yanaji da ganina kin furta adduar da sai anga masifa ko abin qi ake yinta? " cikin baqin ciki da bacin rai idanunta jazur ta kalleshi tare da cewa meyasa kaimun haka?  Dan me baka nemi yardata ba ko Jin raayina akanka kakai maganar gurin Baba na?  Wane irin neman aure ne haka?  Ya bata amsa da cewa irin neman auren da addini ya tsara,  batare da tunanin komai ba tace to kasani ni Banasonka wlh 😪  shima cikin nasa sigar bacin ran da tsantsar rashin mutunci yace to nima anfada miki ina sonki ne?  Kawai dai xan aureki ne saboda bani da xabin da ya wuce auran naki,  xancen rashin neman yarsarki kuma sai kije ki tuhumi babanki wanda daga ganin sarkin power yasa miya tai zaqi,  dagaji ance ina sonki yace in fito wanda hakan ya nuna baki da wani sai ni din danake shirin rufa miki asiri shine xakimun iskanci,  wlh maryam bani da auran mace me shekaru kamarki kawai qaddara Allah ya doramun akanki.  Ance inxo ne in mutsara lamarin biki to ni kisani bani da raayin wasu bidi 'o'i saboda haka sisina baxan bayarba nayi abunda yake wajibi wato sadaqi.  Yana fadar haka yasa kai ya fice. 

       Jage jage fuska duk ta dame saboda make up daya hade da hawaye ta shiga dakin mama,  Faty ce kawai ta kula da shigowarta dakin ta sauri tashi ta tareta ta fada jikin Faty tare da qara fashewa da kuka,  yaya Faty dama irin mijin da Baffa ya zabamun kenan?  Sam be dace dani ba wlh banasonsa na tsaneshi bana raayin auren mutum irin wannan.  Faty ta dago kanta cikin rashin fahimta tace Mimi yimun bayani yanda xan gane,  ba ance kun taba haduwa ba?   Tace ba shi bane sister wanda nake zato ba shi bane 😭😭 wannan mugune wanda baya qaunata kuma ya furtamun da bakinsa,  bazan aureshi ba sai dai in duk abunda za ayi ayi.  Mama ta iso kansu ta tsaya cike da al ajabin abunda mimin ke fada,  ta durqusa a gabansu tace Mimi babu abunda za ai wanda ya wuce ki yarda da qaddara kinsan wlh auren nan babu mai hana faruwarsa sai Allah tunda baffa ya tsaya akai,  kuma turjiyarki ga wannan lamari yana nufin tashin hankalina acikin gidannan.  Ta share kwalla tare da cewa mama yanxu auren dole kike nuna goyon baya ayimun?  Tai saurin tareta da cewa a a wlh Mimi ko maqiyina bazanso auren dole akansa tunda anyimun banji dadi ba,  bare ke yar cikina, amma inaso kiyi haquri ki dauki wannan aure a matsayin qaddara mutum baya taba gujewa qaddararsa wlh tun kan nasan waye mijin da Baffa ya xaba miki naji Sam lamarin bai munba, MARYAM indai ni na haifeki bazaki kaucewa umarnina ba,  umarnina kuma gareki ki karbi wannan aure,  in shaa Allah bazaki danasani ba.  Ta dafa mimin tare da cewa kin yarda xakibi umarnina MARYAM?  Tai saurin kwada kai tare da cewa yar halak ce ni mama bazan taba kaucewa umarninki ba,  naji nagani na yarda.  Kukan da take yasa dady dan yaya Faty shima yasa kuka tare da xuwa ya rungume Mimi yana share mata hawaye da cewa Anty yi shiru ki dena kuka Anty,  ta kalli yaron soyayya ce me qarfi tsakaninta da dady ko uwarsa be shaqu da ita ba yadda ya shaqu da Mimi saboda a hannunsu ya tashi,  tayi dariyar yaqe cike da qaunar dady tace nayi shiru Baba na ta rungumeshi suka kwanta akan cinyar yaya Faty.

      Badaru tsaye qofar gidan su Nafee,  yafi 30 minutes a wajen yana dakon fitowar ta amma shiru,  har ya fidda rai ya juya zai tafi sai kuma gata ta fito tana yatsina wacce take nuna dab take da tayi rashin mutunci. 

 Ya dan matsa kusa da ita tare da cewa ranki ya dade yana washe baki 😁. Tai far da ido 🙄 sannan tace meya kawo ka?  Ai canake kanacan gurin masoyiyarka?  
 
Yayi saurin tareta da cewa ai bani da wata masoyiya da ta wuce ki,  ai ban zaci ma zaki fito ba kusan fa sati 2 ina xuwa bakya fitowa.  Ta fallara masa harara sannan tace ai dole ce tasa na fito,  tunda naga rashin fitowar tawa be hanaka abunda kake niyya ba wato auren Maryam. Ta fada tare da 
fashewa da kuka 😪.

 Tausayin Nafeesa da sonta ya qara qamari a xuciyarsa cikin sigar lallashi yace yi haquri Nafee wlh auren maryam qaddarace a guri..... Dakatamun ✋🏽 ta tsai dashi a hassale,  Kullum abunda kake fada kenan a matsayin abunda xaka kare kanka a wajena kuma nagaji dajin hakan,  ai wlh Badaru ka cuceni, ingama jiranka inbar karatuna sabida kai amma yanxu kaimun haka.  Yanxu bani da ikon fita sai aita nunani ana zundena,  wasu har cewa suke ka fasa aurena. 

 Nafee kiyi haquri wlh babu abunda xai hanani aurenki sai mutuwa,  kuma duk masu yi miki dariya a sannu zasusha mamaki domin aurenmu na barshi daganan xuwa bayan sallah in shaa Allah. 

 Amma dai kasan bazan zauna da ita ba ko?  Saboda haka ka nemar mun gurin zama tun wuri saboda na tabbatar bazan iya hada kishi da wata ba a kanka. 

Nasani Nafee shiyasa ma na nemar mata gurin xama shi kuma wancan gidan dama nakine ke kadai keda yayan da zamu haifa. 

 Nafeesa ta dan sakko jin wannan furuci na badaru kuma ta tabbar har yanxu yana sonta,  tace wai muga photon ta kyau ta finine naga kanata rawar kai a kanta?   Yayi murmushin cin nasara yace wlh bani da photon ta amma wlh ko kama qafarki batai ba Nafeesa. Wai shin kinsan ma dalilin auranta?       Nan ya kwashe abunda ke ransa game da Mimi ya fadawa Nafeesa ba tare da tunanin illar da hakan kan iya haifarwa ba nan gaba. 

Lamarin da yayiwa Nafeesa dadi kwarai da gaske,  domin tasan halin Badaru baya qarya hasali ma ya tsani maqaryacin mutum,  kuma tasan abunda ya fada mata harga Allah hakane a xuciyarsa.  Shiyasa ta saki jiki sukaci gaba da hirarsu ta soyayya kamar ba abunda ya faru. 

Mrs Muhammad 😊
[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼
AL AMARIN MARYAM 
 🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼🙆🏼          

📝FANTASTIC STARS WRITERS 
                  {F, S, W}

Written by 
RAHMTULLAH (Hajia) 


Dedicated to 
MARYAM BAITA 


Page 1⃣6⃣

   Kwanaki kadan bayan hakan Mimi tai wata irin muguwar rama ta fita hayyacinta,  kallo daya xakai mata kasan akwai abunda ke cinta a xuci. Duk da ba fita tayi rabon i v ba,  acewarta a turawa kowa ta waya inda hali ma a haqura da shagali a bikin a daura aure a kaita.

Abubuwa da yawa sun taru sun cudewa mama da yaya Faty da duk ma wani masoyinsu,  ta bangaren mama dai abu da yawa na damunta,  babban abunda yafi damunta kuwa shine damuwar halin da Mimi take ciki,  na biyu kuma abunda Baffa Yayi mata.  Abunda ya faru dai shine : abunda yayi a bikin Faty shi ya maimaita akan Mimi koma ince har gara Faty akan Mimi domin kuwa tunda ya sai set din kayan gado guda 1 da saitin kujeru yaja bakin aljihunsa ya tsuke daga haka ko tsinke be kuma siya ba,  abunda yayi mugun baqanta ran mama da duk yan uwanta,  domin a xaton mama Baffa xai saki jiki yayiwa Mimi kayan daki kamar yadda yake yiwa yayansa kodan albarkacin biyayyar da tai masa akan mijin da ya bata.  Ita tunaninta abunda yasa yayiwa Faty haka a lokacin aurenta dan bayasan auren da Ahmad ne,  amma sai taga sabanin haka domin har gara kayan Faty akan na Mimi, kenan Baffa ya na nuna mata yayan Al amin daban da nasa tunda ga banbancinnan yana nunawa qiriri,  amma duk cikin lamarin Baffa wannan yafi bata mata rai fiye da rashin kai yayanta sauke farali kamar yadda yakewa yayansa domin a cewarta xuwa maka lokacinsu ne bayi ba. Ta kuma qudure a ranta cewa lokaci yayi da xata takawa Baffa burki akan yayanta. 

Ita kanta Faty da bata cika daukan abu da xafi ba wannan karon taji zafin Baffa kwarai akan abunda yayi. 

Da yake dangin mama ba matsiyata bane da ita kanta maman da Faty suka fidda kudi naqudai Adda halima da yaya Faty sukaje suka lafto siyayya daga kan kayan kicin da kayan qayata falo komai acan acan,  sukaxo suka lafce kayan a tsakar gidan Baffa,  duk girman tsakar gidan sai da kayan sukai ragowa aka dora wasu kan wasu.  Cikin falon mama kuma danginta ne cike taf tunda da kan Adda halima (momy)  har xuwa kan matan yayyensu da kuma yayansu, bakajin komai sai tashin hira da shewa cike da nishadi.

A dai dai wannan lokacin kuma matan gidan na cikin dakunansu cike da baqin ciki. Umma dai anata bangaren tun lokacin da aka kawo lefen Mimi har xuwa kayan auren da Baffa yayi mata tana cikin farin ciki,  domin ita macece wadda bataso taga anfi yayanta,  to ganin komai na Mimi tsiya tsiya yasa hankalinta mugun kwanciya, domin taga Mimi batafi yayanta ba, amma ganin wannan uban Kaya da dangin uwar Mimi suka kawo yasa murnarta komawa ciki. 


Bangaren Anty kuwa kusan tafi Umma shiga tashin hankali akan wannan kaya,  domin ita Sam batason cigaban wani koda kuwa dan uwanta uwa daya uba daya,  bare kuma Mimi yar kishiyarta wacce tafi tsana a duniya.

Ana cikin hakanne saiga Baffa ya dawo diban wani katin daurin aure domin wanda ya fita dashi ya qare, ya tsaya turus ganin kaya sun cika gida ya kwallawa Umma kira suka fito tare da Anty (kamar ita aka kira),  yace mata wannan kayan fa?  Momy wacce ta fito daga dakin mama tace sannu Baffa ya juya tare da cewa haj halima ashe Kina ciki? Suka gaisa tai masa Murnar qaratowar biki sannan ta dora da cewa, dama kayane ta fada tare nuna kayan,  muka kawo tamu gudumnawar babu yawa.  Wata irin kunya ta rufe Baffa wacce tunda yake bai taba jiba, nan take ya fara nadamar abunda yakewa fadima akan yayanta,  har yake tambayar kansa shin meyasa yayi haka kuma meye ribar nuna bambamcin da yake tsakanin yayansa da yayan dan uwansa guda daya da ya mutu yabar masa,  gashinan dai abunda beyi ba danginta sunyi mata kamar yadda sukai a bikin Faty,  yasan acikin matansa duk wacce za aiwa yarta aure ko cokali bata siya,  amma fadima abikin Faty dana Mimi ta nunka abunda ya kashe wajan sau 3, baiji ragowar abunda momy take fada ba saboda tunanin da yake,  sai dai kawai ya tsinci kansa da yi mata godiyar kayan da suka kawo. 

Ba yanda yaya Faty batai da Mimi ba taje wankin kai da qunshi amma taqi,  da kyar fauxa qawar mimin maqociyarsu ta lallami mimin suka tafi saloon akayi mata shampoo aka gyara gashin, qunshi kuwa qiri qiri taqi zuwa dole sai yaya Faty ce tasa me kunshin tazo har gida tayi mata.  Duk da cewa Badaru be bada kudin event din yan mata ba, yan uwanta sun kama gidan dan hausa inda xa ayi luncheon kawai,  domin ko sun qara wani event din Mimi bazataje ba,  dan luncheon dinma cewa tai ba inda xata. 

Ana gobe kamune akaje kafi (jere) gidan amarya ko 2 hours masu jeren basuyiba suka dawo jiki a sanyaye,  domin kuwa wata yar qaramar gida Badaru ya kama haya a wani Geto area da nufin nanne gidan Mimi.  Gidan dai yafi kama da gidan student wanda suke kamawa inbabu guri a hostel,  domin dan qaramin tsakar gida ne sai qofa daya wacce inka shiga xaka tadda falon da ko Set din kujeru baxai ci ba sai bedroom daya da toilet aciki sai dan kicin dan qarami daga hagun falon,  irin kitchen da in kin shiga bazaki iya tsgunawa ba saboda qanqantarsa. 

Wannan gida ya faranta ran maqiyan Mimi na gida (irinsu Umma da Anty da kuma wasu daga cikin yayansu) da na waje. Anty ta dunga murna tana cewa yarinya dai ko FARHAN kitchen aka sai mata a banxa tunda babu gurin xubawa,  domin kuwa ala dole aka juyo da kayan Mimi gida dan abunda ya samu shiga cikin gidan ba wani yawane dashi ba,  don ko fridge da cooker gas basu samu shiga ba sai dan qaramin gas aka siya mata irin na yan hostel.  Direct aka wuce da kayan gidan kakakannin Mimi (gidan mal SULAIMAN)  aka jibge. 

Matar babban yayan su mama (Umma)  da momy suka dunga masifa akan wulaqancin da gidan su badaru sukaiwa Mimi akan gida kuma haka suka samu Baffa da xancen, shima da yake bayason harkar qaranta a take ya nemi mahaifin Badaru da zancen,  har yana barazanar inbasu da wuri ajiye maryam a fasa auren dan ransa ya baci shima,  alh inuwa ya dunga bawa Baffa haquri da cewa wlh suma sai a qurarren lokaci Badaru ya nuna musu inda zai saka maryam kuma basu so hakan ba, amma su kwantar da hankalinsu ya kusa gama gininsa.  Wannan ne yadan kwantar da hankalin masoyan Mimi, amma duk da haka qananan maganganu sunyi ta kai kawo a tsakanin mutane akan auren.

Ranar alhamis itace ranar da aka fara bikin ko ince ranar luncheon,  duk yanda aka kai da lallaba Mimi ta tashi tai shirin tafiya Gidan Dan hausa gurin luncheon Sam taqi anyi fadan anyi nasihar anyi waazin duk taqi ga dukkan alamu halinta na kafiya ya motsa,  ala dole aka kyaleta ganin ciwonta na daukewar numfashi na alamun tashi domin qirjinta sai bugawa yake wanda shine alamun ciwonta yana gab da tashi,  duk ta yankwane tayi wata irin migues rama duk wannan cikar jikin ta xube a 10 dayz,  sai idanuwa xuru xuru da qasusun wuya. 

Haka dai aka dade aka barta a gida daga ita sai kakarta (hajja maryam)  wacce taci sunanta kenan sai kuma mama da tace ina xata yarta babu lfy?  Hajja ce ketaiwa Mimi nasiha da falalar yadda da qaddara mama na gefe tana shafawa hajja mai a qafarta saboda wankan da tayi,  nasihar ta shigi Mimi sosai saboda kwatancen da hajja tai mata da mama mahaifiyarta da kuma irin quncin da ta shiga a dalilin damuwarta,  a fili hajja ke nuna San Mimi fiye da duk wasu jikokinta tanason yarinya fiye da tinanin me karatu.

Mama kuwa ko kallon Mimi batason yi saboda kwantsamewar da Mimin tayi, kuma sau tari in ta kalli Mimi sai taga kamar tana kallon hoton rayuwarta ne ta baya, domin itama haka ce ta kasance gareta lokacin aurenta na fari.  Ta maida hankalinta kacokan kan kula da hajja ( mamanta)  wacce tazo bikin Mimi da nufin sai angama xata tafi. 

Bayan magriba yan bikin da babu amarya suka dawo,  atsakar gida suka jiwo muryar anty na cewa wannan wane irin biki ne kamar na bagudajiyar qauye?  Biki lami kuma dan abun kunya event daya? Neman kudi anan dai beyi rana ba wlh,  shiyasa amaryar taqi xuwa ta qirqiri ciwon qarya 😄. Ai wlh ba a taba abun kunya a gidannan irin wannan ba domin ko taron suna ake a gidannan anayin shagalin da yaci uban wannan kai andaiji kunya wlh,  lallai kwantai beyi ba, 😂 dama haka bikin yan kwantai yake komai tsiya 2 ? Allah ka cigaba da bawa yayanmu miji da wuri tun suna da quruciyarsu.  Babu wanda ya kulata a dangin mama da suka cika gidan domin hajja ta hana a tanka mata a cewarta wanda ya tara jama a baya fushi ko fada in yayi fushi to ya bata taronsa. 


Washegari juma a aka daura auren MARYAM AL AMIN da BADARU MOHD INUWA akan sadaki 50k,  kuma a take Baffa ya kirata ya bata sadakinta kamar yadda addini ya tanada,  tana shiga daki ta wullar da kudin sadakin ta sa kuka,  sai mama ce ta dauke kudin.  Washegari akai yini anan gidan  babu wani armashi qarfe biyar aka tafi kai amarya kasancewar unguwar da xa a kaita da nisa sosai da kyar aka fito da ita daga gidan domin ta qanqame mama tana kuka da kyar momy ta banbareta daga jikin Maman tai waje da ita tasata a mota, momy da wata yar uwar su Baffa (qanwace a gurinsu baffan)  mama saude suka shiga aka tafi kaita. 


Mrs😊[9/30, 1:04 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 5⃣5⃣




Yayi mamaki kwarai daya tadda Mimi gidansu dake NNDC,  ta gyara gidan qal komai need da taimakon sabuwar yar aikin da mumy ta samo mata.  Kamar ta shiga xuciyarsa dama wanka yakeson yi yaje gidan mama ya dakkota sai gashi ya sameta gida,  afili yace kai mace mai hankali da tunani tayi a arayuwa. 




Ranar tasha aiki don gaba daya maxan wato qannansa da ishaq anan gidanta suka sha ruwa.  Ta fuskanci a dabi ance Bature meson nasa yaxo kusa dashi ne don duk sanda yan uwansa sukaxo gidansa yakan rasa inda xai sakashi. 



Ana gobe sallah aiki yai mata yawa sosai ita da Aisha sunan sabuwar me aikin ta kenan.  Ansanar da ganin wata tun tuni,  ta kwaba funkaso kana adaren tai miyar agushi ta soya naman kaxa da yawa tayi zobo tasa a fridge.  




Tun hudu ta tashi ranar sallah ta dora tuwo,  ta dafa shayi wanda yaji kayan qamshi sosai.   Ta koma ta taya ya Bature shirin tafiya idi,  7:30Am ya gama ya fito cikin falon inda tagowar yan uwansa ke jiransa don tafiya idi.  Fuskarsa ta nuna tsantsatsar farin cikin da yake ciki ganinsu kowanne da cup din tea din da Mimi ta dafa yana kurba,  suka dinga gaisheshi yana amsa tare da yimusu barka da sallah.  Ishaq kuma ya miqa masa hannu suka gaisa.  Mimi ta miqa masa cup din nasa shayin,  yana kurba da sauri don sunso yin late.  Yana ajiye cup din ta matso ta dora masa hularsa ta gyara masa ita sosai kana suka tafi. 




Kafin su dawo wadda ta bawa aikin waina (masa)  da sinasir da kawo don ita aikin ya mata yawa shiyasa ta bada aikin ita kuma tai miyar.  




Ta shimfida musu ledar cin abinci babba akan centre carpet ta jera musu duk nauin abincin da tayi akai sannan ta kawo ruwa da drinks na kwali ta hado da xobo da kunun ayar da tayi yanxu duk ta ajiye da isassun plates.  Matansu suka dunga kawo nasu abincin sallar duk wacce ta kawo Mimi anan take ajiyewa.  Farida ce ta karshen kawo nata girkin. Ita kuma yasmin uwar malalata snacks tayi da pepe chiken.  



Ta xuba na na gidan mumy ta bawa Aisha kudin napep ta tafi kaiwa,  na gidansu kuma mama tace ta turo huxaifa ya karba don bata da dan aike.  Tanata sauri don tanason kafin suxo tai wanka. Faty ma dan aikenta ta bawa nata abincin ya juya mata dashi.




Ta koma daki ta gyarashi, dama shi kadai ya rage bata gyara ba.  Tai wanka      kwalliya sosai tayi don ta dade batai kwalliya ba sannan kuma koba komai ai tayi kwalliyar sallah.  Ta danyi rama bamai muni ba sabida azumin wata daya ba wasa bane,  acikin kayanta wanda ta dinka na biki ta dakko wani lace ta saka har yanxu bata gama sakawa ba don tafi saka qananan kaya. Ghana Weaving ne akanta shiku yayi tsam,  ta kafa dauri mai steps ta fito da gaban goshinta inda aka dau kitson.  Tasa turaren wuta a bunner na jiki ta turare jikinta kana ta saka na daki ta dunga bi dashi kusufa kusufa na gidan tana turareshi ta dire a kitchen. 




Suna shigowa falon qamshin turare dana abinci ya musu maraba,  komai tsaf gwanin shaawa.  Suka zazzauna suna sabe riguna xaa kwashi girki shi kuma ya nufi kitchen don wanko hannu.  Ya samu gumbiyar tasa a tsaye tana cire wayar bunner daga jikin socket din wuta.  Ta bayanta ya lallaba ya zagaye hannusa a qugunta ya kwanto kansa akan wuyanta yana shaqar qamshinta.  Kitchen din qal dashi kamar ba aciki akai aikin abincin sallah ba,  sai qamshin turaren wuta yake.  




Ta juyo tana kallonsa,  tace "har kun dawo?" bai bata amsa ba sai kallonta da yake ya furta sunanta "MARYAM" ta amsa naam "ya Bature"  ya zarce da fadar "Allah yayi miki albarka ya biya miki buqatunki na alkhairi ya bamu zuria ta gari,  Allah yasa kedin ki xama uwar gidana a Aljannah" idonta cike da kwallah jin dadin adduar da yayi mata tace "ya Bature amin, amma me nayi akaimun wannan kyakykyawar addua?" ya kamo fuskarta dab da tasa yace "a cikin abunda baifi wata hudu ba da auren mu kin cikamun burikana da yawa,  burina wanda kika cika yau shine hada mana abincin sallah da kikai ni da yan uwana da qannena, haqiqa na dade da wannan buri inga na hada taron sallah irin wannan sai gashi ba tare dana fada miki ba kinyi hakan.  Gashi kinyi mun kwalliya kin gyaramun gida kinsani farin ciki maryam Allah ya biyaki da aljanna" ta amsa da amin.  Ya kamota ya rungume tai saurin tureshi ya kalleta dason qarin bayani tace "xaka kwancemun daurin danayi da kyar"  ya kamata ya cire dankwalin yana cewa "ai dama ban gama ganin wannan kyakykyawan kitson ba,  saina saka anjiqashi xanji dadi" tana dariya tace ."ka makaro yaro babu way"    shima dariyar yayi yace "ni xakiyawa wayo ai nasan qalau kike lokacinki beyi ba,  haba Mimi luv nayi qoqari fa tun kan axumi a matsayi na na ango" ta kwashe da dariyar shaqiyanci tace "ango ko angogu?"  ya kamota yace "xakiga angogu don ke xan goge in anjima" ya manna mata rafar yan hamsin sabbi yace "wannan ki sallami yara kana ya bata ta yan 200 ita sababbi yace wannan kuma nakine barka da sallah" ta sunkuya har qasa tana masa godiya yai saurin riqota yace 'adana godiyar ki in anjima kyamun a gado' ya wanke hannunsa ya fita cin abinci gurinsu ishaq falo. 




Itadai tea kawai ta iya sha taje ta kwanta don gajiya,  shi kuma suna gamawa ya fita shi dasu audu gaisuwar sallah gidajen yan uwa.   




Baccinta baiyi tsaho ba tanayi ana tashinta sabida sai baqi take yan yawon sallah da masu kawo abinci.  Qarshe ma sai falo ta dawo ta kwanta, sabida Aisha nata zaryar tashinta.   Da azahar ta tashi dole tai sallah, ta fara yan ciye ciyen fruit da tasan xasu kawo mata niima ajiki har gumba ta dama da madara ta shanye.  Wajen uku matan suka shigo su yasmin, Farida da sauran matan yan uwansu da suke layi daya suka cika falon anata hira cikin nishadi Mimi ta dakko musu kajin data soya da kunun aya suna ci ana maida yacce akai.  Basu tafi ba sai magrib kowacce ta koma gidan mijinta don suma maxan sun dawo har sun wuce masallaci.  





Wanka ta farayi kana tai sallah ta jira isha itama tayi,  sannan tayi kwalliyarta cikin fitted gown ta atamfa mai dogon hannu budadde daga qasansa.  Bata daura dankwali ba ta saki jelolin kitson.  





Yana shigo falon da ita yayi arba a kame a falo,  idonsa cikin nata yace "kai Mimi badai gayu ba, bari nai wanka naxo naga wannan wankan" ya shige ciki.  





Tana nan zaune ya fito,  ya xauna kusa da ita ya jawota ya dorata kan cinyarsa yana binta da ido.  Tadanji kunyar kallon da yake mata tace "bari in kawo maka abinci" ya katseta "barshi ban tare da yunwa ai" tace "fruit salad fa? " yace "dakko musha" ta miqe tana takawa a hankali yabi tafiyarta da kallo yana murmushi.  Ta dakko ta dawo ta xuba masa ya karba ya kuma maidata maxauninta akan cinyarsa yanasha yana bata yana kuma yan tabe tabensa. Hirar batayi wani nisa ba  yace suje su kwanta. 





Sosai yake nuna yana buqatarta tadan janye tace "ya Bature ka bari sai gobe mana nagaji"  yace "haba mana Mimi luv kar muyi haka kinsan yadda nakeji kuwa?  Kuma ai bamu tabayi a wannan garin ba ki bari mubar tarihi mana" dama itama jin baki ne don tanaso dan haka ta bada kai bori ya hau.  Sambatu ya dunga yi mata sosai,  lallai abun in anayi a marmarce yafi dadi kuma anfi riritaka 😜  tunanin Mimi kenan ganin yadda duk ya rude kamar yau farko.  




Xamansu mai dadi ya dore a cikin kwanakin sallar, sai kace yau sukai auren bata da kewa ko kadan Kullum cikin baqi take ko yan uwanta ko nasa ko matan abokai.  Duk wanda yaxo bata rasa abunda xata bashi. 




Har sun fara azumin sittash shawwal,  lokacin  CDS dinsu yaxo tana kano ta shirya cikin kaki xata tafi ya kalleta yace "corper weeee" tana dariya tace "waaa" taje ta dawo har clearance ta samu. Sai sallah da kwana goma sukai shirin komawa.  Su hudu suka tafi a mota ishaq da Bature agaba ita da Farida abaya.  Farida da dai an harbu don kusan a cinyar Mimi taje Abuja duk kuwa da maganar da Bature ke mata na ta danne masa mata. 




Tarayyarsa da Hanifa tananan a yadda take,  har yanxu bata saduda ta daina bautawa na tsugune ba Kullum kudinta suna can. (ni kuwa nace dama kin tashi kin shaidawa mai duka gwanin hukunci da wannan yawon da kike ke a kode xaninki a kode ga asarar dukiya)




Basu jima da dawowa ba hutun sallah suka sami baquncin Anty mami taxo 9ja Abuja yin wani aiki kuma a gidan su Mimi ta sauka,  Mimi na ganinta gabanta ya yanke ya fadi amma duk da haka ta danne taje ta taro ta ta karbar mata akwatin hannunta tana cewa "sannu da xuwa Anty mami" tana wani yatsina da basarwa ta banbare Mimi daga rungumar da tai mata,  ta samu guri a falon ta harde.  Mimi da hadiman gidan suka dunga xarya dan samar mata abun buqata, sai da suka cika centre table din gabanta da nau ikan abinci da kayan motsa baki sannan Mimi taje ta gyara mata daya daga cikin bedroom din dake part din duk da a gyara yake tasa sabon bedsheet da maganin sauro na feshi ta turaren wuta kana ta kai mata jakarta da akwati dakin ta dawo falo gurinta don su gaisa.  





Ta durqusa har qasa daga gefenta tana gaidata. Ta juyo tana hararta tace "amma dai kya bari in ci abinci in huta kafin ki isheni da gaisuwarki ta fi'ili"  duk da Mimi taji haushin maganar saita danne a fuskarta bata nuna komai ba tace "to" ta tashi ta xuba mata abincin ta shiyaya mata ruwa da lemo ta tura mata gabanta sannan ta koma gefe ta rakuye.  





Dake isowar yamma tayi tana cikin cin abincin ya Bature ya dawo,  ya nuna farin cikin ganinta sosai ya matsa kusa da ita kamar xai shige jikinta suka gaisa tana fada masa aiki taxo na company dinsu kuma xatai 2 wks ne.  Mimi ganin ta amsa gaisuwar Bature duk da tana cin abincin itama ta matsa ta kuma gaisheta.  Bature ya kalleta yace "Mimi sai yanxu xaki gaisheta?"  kafin tai magana Anty mami ta rigata da cewa "eh ai wai ita isashshiya yanxun ma ganinka yasa ta gaisheni inaka da bakaxo ba baxan samu arxiqin gaisuwar ba,  nafi awa daya a gidannan amma ko kallon inda nake batai ba sai yan aiki take ba order a kawon abinci ga mayunwaciya"  ya juya yanawa Mimi kallon tuhumar abunda tayi.  "ta danne duk wani mamakinta na qaryar Anty mami ita cikin qasqantar da kai tace "yi haquri Anty gani nayi kinacin abinci shiyasa na bari ki gama ki nutsu saimu gaisa,  bakyayo doguwar tafiya tun daga wata qasa in tareki da gaisuwa ba"  cikin gamsuwa Bature ya jijjiga kai yana duban mami yace "Allah sarki Mimi badai hankali ba, Anty Kinji nata uxurin shiyasa baku gaisa ba" ta  bata rai jin baiga lefin matarsa ba.  Mimi kuma ta matso ta gaida ita,  ganin idon Bature yasa ta amsa da dan sakin fuska.  Mimi aranta mamaki take ada duk dangi sun shaida bayan yan uwan Anty mami babu wanda takeso kamar Mimi ko xuwa tai tsarabar Mimi ta dabance amma yanxu gashi duk wannan soyayyar da take mata ta koma tsana a dalilin ta auri qaninta.  To me xa a kira wannan abun?  Son Baturen take har abun ya xama kishi ko kuma Mimi ce bataso ta auri dan uwanta?  Bata da amsar wannan tambayar shiyasa ta miqe ta shiga ciki ta barsu suna hira da yar uwarsa.




Da dare gurin cin dinner ma harta zauna cikinsu don cin abinci Bature yanata jan Anty mami da hira, ita kuma tana bashi amsa da e ko um.  Can dai tagaji ta dubi inda Mimi take tace mata "wai ke bazaki barmu muyi hirar xumunci bane komai sai kinji?" Mimi ta dubi shahin da Bature yake,  fuskarsa bata nuna komai ba sai cin abincinsa yake ganin haka ta miqe da plate din abincinta ta nufi gefen falon inda Coffee table yake ta xauna tanaci.  Abincin ya fita daga ranta amma intaqici kamar tayi fushine bataso kuma Anty mami ta gane taji haushin abunda take mata.  



Tana gamawa taje tai shirin bacci bata jirashi ba,  don taga abun nasu nayi ne. 



Acan kuma bayan sun gama cin abinci shi da Anty mami hirar tasu daki ta koma wato inda aka sauketa.  Tana zaune kan gadon dakin shi kuma ya dora kansa akan cinyarta suna hira.  Anty mami tanason Bature fiye da kowa cikin qannenta, shima kuma biyayya yake mata kamar ita ta haifeshi.  Batason yafison matarsa kanta Kardai Mimi wacce take ganin bata dace da Dan uwan nata ba.  




Tana shafa sumar kansa ta sako masa xancen dake cin ranta "sulaimanu ya dace fa ka ganemi wata macen ka qara aure,  zamanka da wannan ita kadai baxai yiwu ba tana illolin da ba a iya xama da ita kawai ba a matsayin matar aure.  Kaga na farko ita din bazawara ka aureta,  sannan kuma nasan ba santa kake ba akwai dai dalilin da yasa ka aureta wanda har yanxu na kasa gano menene,  dalili na uku kuma bafi girma shine ba haihuwa xatai ba don duk da nema dakai a rufemun case dinta da tsohon mijinta sai da naji xancen,  kaga kuwa ina kai ina xama da macen da bata haihuwa?"  



Ya qurawa Anty mami ido yana tsananin mamakin inda taji xancen matsalar Mimi da Badaru ya haddasa mata,  a iya saninsa sai da mumy ta hadasu duka ta kwabesu akan kar a fada mata to waye kenan ya bujurewa maganar mumy ya fada?  




Tunaninsa ya koma kan batun da tayi na qarin aure,  ya hada maganarta da nacin Hanifa na ya aureta,  to kenan inma qarin auren ne Hanifa zai aura? Dake lokacin giyar asirin Hanifa ya dan sakeshi sai yayi saurin kauda wannan tunanin a xuciyarsa.  Hanifa ba irin matar da yakeson aure bace tundaga kan halittarta har xuwa halayyarta in case of xai qara auren kenan.  



Hujjarsa kuwa itace yar soyayyar da suka fara da Hanifa ya gane wacece ita,  don sosai take kwada masa suyi soyayyar banxa wato ta tabe tabe,  dataga yaqi ganewa sai ta fito fili ta fada masa wai shidin bai iya soyayya ba don in namiji nason mace Allah Allah yake yakai hannu jikinta. Ya nuna mata shi sam wannan baya gabansa Last xuwansa gidansu wanda bai qara marmarin komawa ba fada sukai sosai akan ta xauna akan cinyarsa cikin bacin rai ya nuna mata bayason hakan suka rabu baram baram.  




Tun daganan bai qara xuwa gidansu ba, kuma itadin kanta ta fice mai arai.  A raayinsa bayason macen da xata nuna tanason ya tabata ko tanason kyansa har gara wacce xata nuna kudinsa takeso anasa raayin. 



Ya dubi mami cikin kulawa yace "Anty mami Dan Allah waya fada miki maganar Mimi da ex dinta?  A iya sanina mumy tace kar a fada miki amma acikin yayan gidanmu har xa a samu wanda mumy xata hana abu amma yayi?" cikin kulawa itama ta dubeshi tace "ba wannan na tambayeka ba kawai ka amsamun maganar auren don shine burin danasa gaba a yanxu" cikin rashin bawa waccen maganar mahimmanci yace "tabbas nasan little ce ta fadi maki kuma sai nawa mumy waya na fada mata" 




Anty mami tace "karka janyowa little fadan mumy dan wlh ba ita ta fadan ba,  maijidda ce ta fadamun"  yayi shiru yana tunani lallai xaiyi takakkiya har kano yaje yaci uban Maijidda in bata fita daga harkarsa ba,  ina ruwanta da matsalar Mimi dahar xata dunga yaya tawa a dangi.  (in baku manta ba Maijidda yar wan su mumy ce wacce taqi aure sabida tana jiran ai masu hadin gida da Bature) yace da mami "lallai xanci uban yarinyar nan,  don ubanta taqi aure tana yawan karatun boko shine ni xataxo ta tasamun mata a gaba?"  Anty mami ta yatsine fuska tace "can itaku ni dai bani amsar tambayata"  ita kanta Anty mami Maijidda batai mata ba kuma ta dade da sanin Maijidda nason Bature don har da ita ta kama qafa taga babu hanya ta haqura.  Don Maijidda wankin idonta da wayewarta tayi yawa intana abu kamar karuwa ko shigarta irinta jaruman Hollywood take.  





Cikin kulawa ya dubi gefe daya ya fara magana "Anty mami ana aure ne kan abubuwa da yawa,  babba daga ciki kuma jigo shine yin aure don ibada da kuma kare kai daga zinace zinace sannan samun zuria.  To ni kam duk nasamu wannan abubuwa,  inkuma na qara wata matar bayan Mimi wlh Allah zai kamani da rashin adalci a tsakaninsu. Inkuma dan rashin haihuwa ne Allah ba yacce bai iyaba Kullum ina addua kuma ina kyauta xaton xai bamu" 


Cikin bacin rai tace "ni duk ba wannan nake dubawa ba kuma basu nake nufi ba, just naqasu ne ace handsome kamarka kuma mai kudi kana zaune da Mimi kadai a matsayin mace."   shima ya kuma gyarawa yace "Anty bara inmiki gwari gwari,  indai don jin dadi ake aure ko shaawa to wlh Mimi anan bangaren ta xarce tunanina don har sawa take inrasa hankalina na wucin......  Kafin ya qarasa Anty mami ta durka masa dundu tare da runtse ido tace "ya isa basai ka qarasa ba mara kunya, ni ba wannan na tambayeka ba" Bature ya kwashe da dariya ganin yadda ta runtse ido kamar taga wani abun qi.  Jin yana mata dariya ta dauki filo ta fara jifansa dashi yayi waje da gudu,  anan hirar taxo qarshe ya nufi daki yayi shirin bacci ya duba agogo wajen 11 na dare.  Ya samu Mimi tana baccinta ta bashi tausayi sosai don abunda Anty mami tai mata daxu baiji dadi ba just ya danne ne.




Washegari ya fita aiki, Anty mami kuma ba yau xasu fara aikin ba sai gobe don haka har ya fita bata tashi bacci ba. 




Wajen 11 Farida ta shigo gidan kamar yadda ta saba a gidan Mimi take yini in ishaq ya fita don cikinta mai laulayine kuma ga kwadayi inta shigo Mimi ke dawainiyar dafa mata duk abunda takeso itace dan malele, dan wake, wainar fulawa.  





Batasan da xuwan Anty mami ba,  suka xube a falo suna hira kuma hirarsu ce ta tashi Anty mami.  Ta jisu inda take cewa "yau kam besty Babyn ki wake da shinkafa yakeso,  jiya har mafarki nayi inaci da manja da yaji"  Mimi cikin dariya tace "ya kwantar da hankalinsa dama muna da jan wake yau kam sai adafa wake da shinkafa gaba daya gidan har salak da tumatur yau Baby na yayi kwadayi mai kyau don nima inason ci"  




Anty mami ta fito da taqama taga wacece wannan har take fadar abunda xa a dafa a gidan.  Jikinta yai sanyi ganin Farida kuma nan take ta gane ciki ne da Farida.  Farida tace "au Anty mami, saukar yaushe" tana dariya tace "jiya da yamma" tace "mashaallah amarya har an harbu kenan?  Ai gara haka haihuwa itace ribar aure" Farida dariya take cikin kunya don bata xaci habaici taiwa Mimi ba don ita tunaninta bai taba bata mami xataqi Mimi ba.  Mimi kuwa duk da ta fahimci saqon mami sai tayi murmushi ta sunkuya tana gaidata.  Ta amsa tare da cewa Mimi "kije ki gyaran daki a wanke toilet"  Farida tace "masu aikin gidan basa nan ne?"  cikin isa mami tace "No Just ita nakeso tayi"  Farida tadan fara fahimtar abunda ke going Mimi kuma ta wuce gyara daki. 




Ta gama gyara dakin tana wankin toilet safna iso,  xuwanta gidan kenan na farko tun xuwan Mimi tana shigowa tace "Anty mami  memakon ki sauka gidana kya sauka gidan amare?"  Anty mami ta bata amsa da cewa "ga gidan Dan uwana wanda nake da iko akan komai xan taho gidanki ina rabe rabe muna hada hanya da mijinki?"  sai a lokacin idon safna yakai kan Mimi dake wankin toilet.  Cikin mamaki tace "Mimi kece ke wankin toilet kodai shaawa kikai?" "ni nasakata" Anty mami ta bata amsa. 




Mimi ta fito bayan ta gama tana cewa "Anty safna nayi fushi fa sai yau kika leqoni? Kuma nasan yanxun ma xuwan Anty mami ne ya kawo ki ba gurina kikaxo ba" kafin safna ta bata amsa mami tace "to inba gurina tazo ba gurinki taxo?  Ai tasan dake din da bata shigo ba sai yanxu da naxo don ta nuna miki wata kusan tafi wata"  safna ta saurinta tace "a a ni ba haka nake nufi ba,  yi haquri matar yaya guri na baku ku gama amarci don innafara xuwa saina gundureku"  Mimi cikin jin dadin kalaman safna tace "Allah ya kawoki bazamu taba gundura dake ba, mutum ai baya gundura da nasa"  tai waje  don kawowa Anty mami breakfast. 




Tana bada baya safna ta kalli Anty mami ta fara magana "gaskiya baki kyauta ba,  ya daga xuwa gida xaki fara sata aiki wannan abun fa da kike sam be dace ba kuma karkiga mijinta baya damuwa wlh kawai gara yake muki amma kinkacigaba da haka wlh mutunciki zai zube a gurinsu" Anty mami cikin hargowa tace "aishi ba tanbadadde bane irin Audu kuma yana sona yanamun biyayya akan wata banxa Mimi bazai juyamun baya ba" safna ta kuma dorawa da cewa "ai kuwa inkaci gaba da nuna haka akan matarsa wlh zai taka miki burki,  dama mumy tanajin ance anan kika sauka tai hasashen matsala xaki zame musu.  Hasashenta kuma ya xama gaskiya daga xuwanki kin fara bautar masa da mata"  cikin tsananin fushin nuna son Mimi da suke tace "to ai saiki buga ki fada mata abunda ke faruwa taxo ta koreni inkoma hotel tunda kunfison Mimi akaina"  safna ta bata amsa da cewa 'ko bakice in fada mata ba nima innaga abun naki ya wuce makadi da rawa zan fada mata don banga dalilin qiyayyarki ga matan qannenki ba don xubar da girma irin haka ta janyo miki raini gurin yasmin" 







Mimi ta hado abincin kari a qaton try ta kawo ta tsuguna ta hadawa Anty mami tea kana ta hadawa safna ma duk da ta qoshi amma sai data qarba don karta gwale Mimi.  Ta cika musu plate da chips da platain soyayyu tasa musu wainar kwai a gefe da saka musu fork akai ta tura musu,  kana ta kuma xuba musu farfeso na kayan ciki tana shirin tura musu ne Anty mami tace "wannan duk abincin ina xamu kaishi? Ko ance miki kowa cikin zani gareshi irinki?"  batace komai ba ta fita ta samu Farida kwance gadonta suka fara hira kan gidan abincin Farida da aka bude na Abuja yan kwanakin da suka wuce.  Suna cikin hirar ne Farida ta sanyo Anty mami ciki da tambayar abunda tagani dazu.  Mimi bata boye mata komai ba ta fada mata tsakaninta da ita a da da kuma yanxu data xama matar qaninta.  




Farida masifa ta dunga yiwa Mimi akan wannan sanyin da kwantar da kai baxai kaita ba gara ta horoncewa Anty mami irin yacce yasmin tayi.  A fadar faridan in itace wlh saita casa Anty mami da qafarta xatabar gidan.  Mimi ta bata tabbacin baxata iya ba sabida xumunci da kuma mumy, xatai haquri da Anty mami darajar wadannan abubuwa.  Farida ta watsa mata harara tace "ai saiki xauna kita hadiyar baqin cikinta"  Mimi tana dariyar daukan dumi irin na Farida tace "xo muje kitchen din mu dora girkin kar kuku ya rigani"   suka nufi kitchen Farida ta xauna kan stool Mimi ta hadata da yankan salad ita kuma ta dora wake. 




Acan daki kuma Mimi na fita safna tahau Anty mami da fada tana nuna mata kuskuren takura Mimi da taxo tanayi har gidan mijinta duk kuwa da biyayyar da Mimi ke mata.  Anty mami ma tahau sai cacar baki suke kamar saanni daga qarshe dole safna ta bar mata tunda ita din ba gwanar masifa bace.    Daga qarshe Anty mami ta share safna ta dakko system tana dannawa wai ita a dole tana fushi safna tai mata rashin kunya akan Mimi.  Ta gaji da xaman jugum jugum ta nufi kitchen maida kayan da suka karya anan ta tarar da su,  tasa hannu jin rice nd beans ake suka ida  sukaje sallah sannan suka xuba a try su ukun yaji manja da yaji salak da tumatur da gurji da dafaffen kwai suka baje a falo sukaci sukai qat suka dora da coke.  Ita kuwa wacce ta sawa kanta kunci tana qunshe a daki.





Sai dawowar mai gidan suka tafi,  yace da Mimi yunwa yakeji bata gama abincin dare ba hakan yasa ta dakko masa guntun wake da shinkafar da yayi ragowa ta xubo masa hadin salad akai. Ya xauna yaci yana santi har yana tambayarta ta aikawa ishaq?  Tace "eh Farida ta diba masa"  Anty mami ta fito daga daki yana dariya yayi mata barka da gida.  Bata amsa ba ta xarce da qorafin Mimi tasan tananan amma tayi wake da shinkafa, ita kuma bataso. Ya dubi Mimi dake xaune gefensa yace "Mimi luv ya akai abincin da Anty mami bataso"  cikin kwantar da kai tace "yi haquri ranka ya dade, bansan bataso ba Farida ce take shaawa shine nayi a gidan gabadaya"  ya juya gurin da Anty mami ke tsaye "to Kinji uxurinta Anty mami amma kiyi haquri"  cikin fusata ta fara magana don ta farajin haushin tufkar da take Mimi na warwara duk yacce  taso haddasa rigima tsakaninsu sunki bata hadin kai "to saiki fadamun da Farida da ni wayafi matsayi da iko a gidan?"   Bature yayi saurin tareta da cewa "a a Anty duk abun bai kai haka ba,  yanxu ya kikeso ayi?"  cikin izzah tace "ta dafamun abunda xanyi don yunwa nakeji,  don zalunci tasani yini da yunwa ni da gidan Dan uwana"  ya kalli Mimi yace "Mimi luv dan daure ki samawa Anty mami abunda xataci me sauki" ta haskeshi da murmushi tace "to yaya luv" ta miqe ta nufi kitchen.  Anty mami taja dogon tsaki kodai xatabi shawarar safna ta fita harkarsu?  Amma kishin Mimi take sosai akan Bature. 



Ta dora mata farin couscous wanda ta yanka koran tattasai ta xuba mai a dahuwar sai green beans. Gefe kuma tana duba girkinta na dare data dora (tuwon shinkafa da miyan kuka) babu jimawa ta gama ta dumama mata stew din da take da ita a fridge ta hada mata ta kai mata har daki.  




Ta kalli couscous din bayan fitar Mimi,   batacin couscous don haka ta dibi wake da shinkafar da aka ajiye mata tun rana taci ta barbaza kamar bata diba ba don dama tanaso don san haddasa fitini tace bataci.





Da daddare  gurin dinner Mimi bata xauna cikinsu ba sabida abunda ya faru jiya.  Anty mami bataiwa kanta ba wannan karon sakin jiki tayi ta kwashi tuwon shinkafa miyar kuka don ko tayi akai mata bata qin ci, tanason wannan cimar kwarai kuma sabida ita Mimi ta dafa,  duk sai taji kunyar abunda tayi dazu.   Ragowar tuwon tace Mimi ta ajiye mata xataci dumame. Yauma can ta barsu suna hira a falo taje baccinta. 




Ranakun da suka biyo baya ta dan samu saukin takurar Anty mami sabida ta fara halartar aikin da ya kawota,  sukan yini da Farida a gidanta ko ita taje gurin Faridan.  Sai dare Anty mami ke dawowa,  inta dawo kuma a gajiye take amma dan  kishin kar Bature ya bawa Mimi lokacinsa haka xata tareshi da hira yana hamma tana hamma har sai lokaci yaja wanda takega koya koma gurin Mimi bacci kawai xaiyi.  




Akwana na hudu da xuwan Anty mami gidan da yamma Bature ya dawo ya sami Anty mami gida, yau ta dawo da wuri.  Mimi tamai barka da dawowa ta cire masa jacket din saman suit dinshi tada fara jiqewa saboda ruwan saman da ya sauka babu jimawa ta shige cikin daki don ajiyewa ta barsu shi da Anty mami suna hira.  Shiru shiru yana jiran Mimi ta fito daki ta kawo masa abun sha kamar yadda ta saba inya dawo amma bata fito ba.  Yace da Anty mami yana xuwa ya tashi yabi Mimi daki. 




Ya sameta xaune kan kujerar gaban madubi riqe da rigarsa data cire masa tana hawaye,  dakin da dan duhu kadan sabida hadarin daya lullube sararin sama kuma bata kunna haske sosai ba. Jin takun mutum yasa tayi saurin qudundune rigar ta boye a jikinta, sai dai ta makara don ya riga yaga abunda tayi yana xuwa yasa hannu ya ciro rigar ya qurawa rigar ido da nufin gano abunda yasata kuka ajikin rigar.  Sai da yayi amfani da fitilar jikin wayarsa sannan yaga shatin lebunan mace da jan janbaki (💋)radau a jikin light ash din suit dinshi. Jikinsa yayi sanyi qalau don yasan ba Mimi bace don ita da wuya tasa jan jambaki indai ba period take ba ko kuma tasa kayan da suka dace da kalar ja,  tafi saka pink ko dark purple.  




Tunani take a xuciyarta tun sanda ta shigo dakin ajiye rigarsa ta dagata tana yarfe ruwan jiki da nufin ta dan shanya idonta yakai kan 💋 wannan,  wato kenan Bature yawan bin mata yake shiyasa kwanaki yake yawan fitar bayan isha sai wajen 10 ya dawo? Shiyasa Kullum yake cikin yin waya babu dare ko rana kuma intana gurin baya amsawa? Lallai ita din banxa ce tun a lokacin ya kamata ta gane ba sai yanxu da abun ya girma ba har ya fara nuna mata shedar yana bibiyar mata.  In kuwa ya Bature neman mata yake tabbas ya cuceta cuta ta har abada kuma wlh xata iya haqura dashi duk soyayyar da take masa don ita batason fasiqi tun farko abunda tai gudu kenan ya Faty ta kakkareshi kyakykyawan namiji kamarsa ba a rabashi da yan mata bare shi bayan kyau ga kudi.  Wannan dalilin shi yasa ta riqe rigarsa tana kuka har yaxo ya sameta. 




Shi kuma anasa bangaren tunanin yadda akai wannan janbakin yaxo jikinsa yake,  inyaje office yakan cire jacket dinsa a rataye wasu lokutan baya sakawa sai antashi ya mai da abarsa jikinsa.  Babu shakka Hanifa tayi amfani da wannan dama xata haddasa masa fitina da xargi tsakaninsa da iyalinsa tabbas sai ya dau mataki akan hakan.  




Tunaninsa ya katse lokacin da yaga Mimi na shirin fita ta bar masa dakin,  yayi saurin isa inda take ya riqo hannunta yana bata haquri.  Bata da niyyar sauraranshi don sai kici kicin kwace hannunta take,  ganin haka ya kai gwiwoyinsa qasa ya tsuguna gabanta ya riqo hannayenta.  Jikinta yayi sanyi ganin mijinta a haka tace "ya Bature me haka?  Ka tashi don Allah" ya katseta da cewa "MARYAM wallahil azeem ban taba aikata abunda kike zargina akai ba,  kuma ni kaina bansan yadda akai jambaki yaxo rigata ba,  amma na miki alqawari indai ni SULAIMAN aurene ya haifeni baxaki qara ganin haka ba"  idonta cikin nasa tana xubar da kwallah tace "ya Bature basai kayi wannan rantsuwar ba,  na yadda da kai da kuma abunda ka fada don Allah ka tashi" bai tashinba sai matsowa yayi kansa dai dai mararta ya kwantar da kan nasa a cikinta, ita kuma tasa hannu tana shafa masa.  Yace "indai kin huce kiyimun dariya" ta washe masa fararen haqoranta kana ya miqe ya rungumeta suka fito saqale da juna.




Da daddare be zauna hira da Anty mami ba kamar yadda suka saba,  yayi mata qaryar kansa na ciwo ya nufi gurin Mimi.  Yana hawa gadon ya amshe wayarta da take chating ya ajiyeta gefen gado,  ya fara balle mata botiran  gaban shirt din jikinta. Shauqin son Mimi din ne yau yake damunsa kuma dama anjima ba a hadu ba,  ya fara binta da hot romance dinsa kamar yadda ya saba,  sosai yakeson wankewa Mimi zuciya saboda bacin ran da tayi dazu. 




Taga abun nasa na neman zarcewa ta riqo fuskarsa ta qura masa ido ya fara futa hayyacinsa,  taji tausayinsa  tace "ya Bature bani da tsarki fa"  bai kulata ba sai maida fuskarsa da yayi yana lasar wuyanta kana yace "haba Mimi ni xaki yiwa wayo?"   ganin da gaske be yadda ba taci laya "ya Bature wlh da gaske nake"  ya dago ya bar abunda yake jin ta rantse yace "yaushe hakan ta faru bansani ba?" tace "yau da asuba na tashi dashi, nima nayi mamaki don banji ciwo ba ko kadan sai ganinsa nayi"  ya danne abunda yake taso masa yace "to Allah yasa ciwon ya rabu dake kenan"  ta amsa adduar da yayi.  Ya matseta tsam a qirjinsa tana shafa kansa har ya samu relief. 





Allah Allah yake ya isa office ya samu Hanifa yaji dalilin abunda tayi masa a jikin rigarsa jiya, yace da driver ya qara sauri don yaso makara tunda sai da suka kai Anty mami.    




Hanifa ta shigo gaisheshi kamar yadda ta saba,  bai amsa ba sai tambaya yayi mata cikin daure fuska "mesa kikasa min lips dinki jikin rigata jiya?"  tayi tsit kanta a qasa,  ya kuma maimaita tambayar yana waro mata idanu.  Cikin firgita da yanayinsa tace "Sir,  ba ba ba nice ba" ta fada tana qiqina.  Ya buga table din gabansa cikin tsawa yace "to uban waye inbake ba?  Nine kenan?  Tunda daga ni sai ke a office din"  tai tsuru tsuru a tsorace take dashi sosai don fada yake kamar ya daketa.  Ya qarashe fadansa da cewa "to inma kinyi donki haddasa fitina tsakanina da Mimi ne to kinyiwa kanki don bakison darajar aure bane shiyasa kikai haka,  kuma fitinar da kikai niyya ba ayiba don muna da fahimtar juna da matata.  Wlh Hanifa kika kuma yin abunda kikai sai kin bar office din don canjaki xansa ayi,  da bacin ran Mimi gara in rabu dake har abada"  ya qara watsa mata kallo "get out of my sight"  




Ta fita wajen office din tana hawayen baqin cikin cewar da yayi da bacin ran Mimi gara rabuwa da ita.  Ta ciro waya ta kira gwaggoriya ta fada abunda tasa tayi tayi amma ba a dace ba don hakan ya janyo mata cin mutunci.  Gwaggoriya ta bata haquri da cewa karta kuma hakan tunda zai dau matakin korarta a office  dinsa,  ta kwantar mata da hankali da cewa indai da malamai a duniya bazasu watsar da makamansu ba sai ta auri sulaiman. 



******* ******** ********


Tun daga ranar Anty mami ta tsiri indai taje office ta dawo da daddare sai ta bawa Mimi aikin lecture din da sukai ta shigar mata a system,  Mimi kan shafe tsahon dare har xuwa 2 na dare tana typing kuma ko xata kwana a xaune Anty mami baxata tausaya mata tace taje ta kwanta ba har sai ta gama,  wanda a lokacin mami takai wajen kai 10 na baccinta.  Kuma tayi hakanne don ta hana Bature da Mimi damar kebewa suyi soyayyarsu  tunda Baturen ya fara bijirewa hirarta ta dare yana mata qaryar ciwo.  





Ranar data farasa Mimi wannan aiki Mimi sauri ta dungayi don ta gama ta tafi gurin mijinta wanda tasan baya bacci sai a jikinta.  Tana gamawa tai wa Anty mami dake gyangyadi sallama, anty mami ta wartsake jin Mimi har ta gama shigarda uban aikin data bata a syatem.    Tace cikin mamaki "kai amma kinyi sauri kina da saurin typing, bari inbaki ragowar ki shigarmun" Mimi cikin kunya tace "Anty mami bari inje in kashewa ya Bature fitila in dawo,  nasan yayi bacci da fitila a kunne"   Anty mami ta daure fuska tamau tace "Dallah zauna kimun aiki,  jarababbiyar banxa inda shi ya damu dake yadda kika damu dashi ai da tuni ya biyo sahunki"   ta xauna jiki sanyaye ta fara aikin data bata. 



Acan bangaren kuma Bature yagaji da jiran Mimi ya kasa bacci sai juyi yake,  ya dubi agogo 12:48 AM,  ya miqe ya nufi dakin Anty mami.  




Ya tarar da Anty mami na bacci Mimi na gefen gado tana mata aiki kamar tare zasu raba kudin,  shigarsa yasa mami ta tashi.  Abun dariya wai saita dubeshi tace "lfy?"  yadanyi dariyar jin abunda yace "Mimi na biyo taxo muje mu kwanta naga daya saura"  ta basar dashi ta koma xata kwanta,  Mimi ganin haka tace " Anty mami in bishi?"  jin furucin Mimi ta miqe tace da Bature "fita kaban guri,  inta gama xata dawo ai basai ka biyota ba ko so kake ka nuna mun ban isa da ita ba"  ya fita waje jin abunda tace.  Ta juya gurin Mimi tace "ke kuma aikin nawa xaki bari ki tafi gurin miji ko?  Ke ko tsoronsa bakyaji?  Dubeshi qatoto dashi kita binsa yana daddanneki"  Mimi dai sunkuyar da kai tayi tacigaba da aikin.  Bata gama ba sai 1:26  ta miqe a gajiye tabar dakin donkar Anty mami ta kuma sakata wani aikin.  




Ta sameshi ya jera fululluka a gabansa ya rumgumesu abun tausayi ta shige jikinsa,  jinta jikinsa yasashi tashi xaune.  Ya jawota yace "Mimi kiyi haquri nasan duk Anty abunda Anty mami ke miki inajin babu dadi kawai ina haquri da itane" idonta yadan kawo ruwa,  tace "ya Bature ada Anty mami tana sona amma tundaga bayyanar maganar aurenmu ta tsaneni ta kuma canjamun." yana share mata hawaye yace "bakece Anty mami bataso ba,  nine bataso na aurin qayatacciyar mace irinki ba.  Ta fiso ta aura miki dattijo irin Dr. Mijinyawa yadda xaki xama sillar samun kudinta a koda yaushe ta buqaci hakan.  Shiyasa ta ke miki hakan"  ya canja salon maganarsa xuwa wasa da xolaya don ya cire mata damuwa yace "kuma abunda bata saniba shine;  inda kike jarababbiyar nan data aura miki wancan tsohon ai da baxai iya miki ba,  nidin dai nike iyawa jarabarki"😆     jin haka ta juyo ta dau filo tana masa dukan wasa da cewa "nice jarababbiyar ko?"  shima ya dauka yana dukanta suna dariya. 





Cikin sati biyun da Anty mami tayi a gidan Mimi taci gwagwa a hannunta ta hanyar sata duk wasu ayyukata na office ga kuma hantara da gyara koda agaban yan aikin gidan bata lura hakan kan iya ragewa Mimi daraja a gurinsu.  Inkuwa weekend ne tana gida komai Mimi tayi bata iya ba,  gashi Kullum dare bata barin Mimi sai kusan qarfe biyun dare take komawa gurin mijinta tun be saba da hakan ba har ya haqura ya saba.   





Mimi sai yanxu tagane abunda ke hada Anty mami da yasmin fada,  babu shakka irin wannan abun da take mata yanxu ta nemi yiwa yasmin ita kuma ta bijire. 




Shikansa Bature duk ya fara gundura da xamanta duk kuwa da irin qaunar da yake mata sabida yadda ta takurawa matarsa da kuma hanashi sakewa da ita.  





Ranar monday ta tafi wanda yayi daidai da kwananta 15 a gidan,  harda kukanta duk yadda Mimi tagaji da wahalar Anty mami saita tsinci kanta da kewarta,  lallai ranar naka sai naka dadin xama kuma sai bare. 



Ranar da wuri suka kwanta ita da mijinta abunda suka dade basuyi ba,  duk jikin rawa yake akanta kamar bai taba saninta ba.  Ta katseshi da nuna masa batason abunda yake shirinyi.  Ya marairaice mata sosai da magiya kuma dama shidin yakan dade bai buqaci mace ba,  amma duk randa buqatar taxo masa baya iya haquri ko kadan.  Ita kuma yau sam she is not in d mood. 



Ya fara mata dadin baki "haba Mimi ninefa in wasa kike don Allah ki dena kinsan bana iya haquri innakai haka"  yayi mamakin ganin ta bijirewa duk wani sweet mouth dinshi.  Ya riqe kafadunta yana kallon kwayar idonta "Mimi tunda na aureki yauce rana ta farko ta kika bijirewa shinfidata,  nasan laifi nai miki shiyasa xakimin wannan hukuncin amma Dan Allah kiyi haquri bazan iya juraba kinga bani da wata matar sai ke ki bari insami nutsuwa sai ki fadamun laifina kinji Mimi na a yafemun"  ta cire hannunta daga nasa ta sauka akan gadon ta koma kan sofa ta kwanta,  ta lura duk yadda xatai masa bayani idonsa ya rufe baxai fahimta ba gara ta canja makwanci inyaso ya haqura dole don yau gani take ko mutuwa xaiyi baxata bashi jikinta ba don sam bata raayin abun kuma ita kanta batasan dalilin hakan ba.  





Baki sake kamar sabon shashasha yake kallon Mimi da sabon salon raba musu makwanci yau.   Ya tashi ya nufita halin da yake ciki yasa har tsigar jikinsa na tashi. Ya riqe dantsen hannunta yace "Mimi wani abun kika koyo na guduna a shimfida?"  ta fusge hannunta a xuciye itama tace "tunda nace banaso ka rabu dani mana ko dole ne?"   ya tsuguna gabanta jiki a sanyaye ganin Mimi yau ta canja masa yace "maryam kodai abunda Anty mami tai miki ne kike daukar fansa a kaina?  Naga ai na baki haquri ko kuma nima ba a sona take miki hakan ba"  jin abunda yace itama nata jikin ya danyi sanyi tace " ba wannan bane xan iya cemaka na manta da abunda tayimun kuma Anty mami ai yar uwata ce dole nai haquri da ita tunda inason qaninta.  Kawai dai abun ne banaso Don Allah ka haqura"   



Ya miqe yaje ya kwanta akan gado ruf da ciki yana runtse ido.  Ita kuma ta kwanta kan sofa.   Kusan awa daya da kwanciyarsa ya kasa bacci sai juye juye yake,  yayin da ita tuni ta sami bacci.  Yaga alama indai yanason ya runtsa a daren nan to saiya fitar da abunda ke cikinsa,   ganin bashi da xabi ya tashi ya nufi Mimi. 





Cikin baccinta ta jishi ya turmusheta iya qarfinsa,  ta bude ido ta fara kai masa duka da hannunta a qirjinsa iya qarfinta tana kuka tana cewa "banaso,  nace maka banaso inkayi mutuwa xanyi ka rabu dani" ya hada hannunta ya riqe tsam ya fara shigarta a hankali don bata bashi hadinkan yi mata romance ba. Tana jinshi jikinta tayi shiru tsit tabar kukan,  matar da tace bataso sai gata tana nunfarfashi.  Sun dau tsawon lokaci suna abu daya sannan ya gyaleta ya dauketa ya mayar kan gadon suka kwanta.  





Sai dai a wannan daren basu rintsa ba don kwana tayi bata da lfy,  xaxxabi take me zafin gaske harda rawar sanyi.  Ya kashe AC ya kulle Windows ya rufeta da jibgegen blanket amma bata daina jin sanyin ba.  Gashi kusan duk minti biyar saiya rakata bandaki fitsari,  haka suka kwana har ya fara zargin kansa da haddasa mata ciwo,  wane haukane ya kaishi yin sex da mace bataso kamar wani bagidaje? Ga abunda ya jawo nan. 



Haka suka kwana da asuba ma a gida yayi sallah,  ita kuma a xaune.   Tana idarwa ta fara bacci,  shikam ko falo bai fita ba bare wani office yananan bakin gado yana  gadinta tana bacci shi kuma ya na gyangyadi.  Yayiwa mr Alex waya yadau excuse ya fada masa madam ce babu lfy. 




Sai 11 safe ta farka ras da ita kamar batai ciwoba jiya cikin dare ya hada mata ruwa tayi wanka,  suka fita cin abinci a dining itace ma kedan kunyar abunda tai mai jiya,  ya nuna mata babu komai ajixanci ne irin na Dan Adam shima ya bata haqurin hakke mata da yayi ya fada mata ba halinsa bane jiyanma ya rasa abunda yasa haqurinsa ya gaxa.   Bayan sun gama ta shiga gidan Farida,  shi kuma bacci ya koma. 



Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 5⃣6⃣



Babu jimawa babbar sallah taxo,  hutun babu yawa kwana hudu ne kawai. Ranar arfa suka isa da safe kuma a ranar suka kewaye yan uwa da daddare bayan sunsha ruwan axumin arfa da akai.  Kamar yadda suka saba ko ina maraba ake dasu,  mama harda bawa Mimi kayan qamshi irunsu kanumfari da citta wanda xatai aikin naman sallah. Mumy kuwa da sukaje cewa tai da Mimi karta bawa kanta wahalar aiki irin na wancan sallar ta samo mata yar tayin aiki kuma ga Aisha nan yar aikinta ta yarda da ita sosai ta bawa Mimi.  A gidan hajja kam sun shafe kusan 11 dare suna hira da kakanninsu cikin nishadi,  Mal manu adduoi yadunga bawa Mimi kamar yadda ya saba yana cewa ta dunga yiwa kanta da Bayahuden mijinta.  Su Faty har sun rufe gida suka buga musu,  ganin sune har sun kwanta Ahmad ya taso Faty wacce cikinta yayi wani irin mugun girma don har ya wuce watanninsa na haihuwa ta kumbura suntum.  Ta tausaya mata sosai lallai mata suna wahala da ciki,  Faty tana dan dariya tace da Mimi "karki damu  an tabbatar da lfy lau muke ni da Baby kawai lokacin da Allah ya dibar masa na xuwa duniya ne beba" haka dai suka rabu cikin kewar juna tana fadawa Faty tana haihuwa ta fara fada mata ranar xata taho kano ya Ahmad yace "to unguwar xoma"  





Washegari idil adhha,  suna sakkowa idi yayi layya sa da rago ya yanka, kuma nan take ya rabar da naman san gaba daya ga maqota da danginsa akaita kaiwa.  Kayan ciki kawai ya bari da naman rago, maaikatan da mumy ta samo mata su sukai gyara naman (kayan ciki) jikin ragon kuma aka ratayeshi.   Ta tsaya ta kula da suyar akai mai kyau da tsafta.  Rana ta biyu da sallah da daddare sukaje gidansu Farida gaishesu,  Mimi ta dibarwa ummansu soyayyan nama.  Acan suka tarar da Farida sai shagwaba take xubawa.  Umma taji dadi ta bawa Mimi danbum nama ita da Farida cikin bokitai da kilishi,  washegari uku ga sallah suka koma Abuja kamar yadda sukaxo su 4 sabida washegari talata xa a koma aiki hutun da federal ta bayar ya qare.  



(Eid Adha Mubarakh, Taballallahu minna wa minkum)  

******* ***** ******* ****


Sati biyu kenan da yin sallah,  suna kwance bayan sallar asuba wata irin yunwa ta tasheta.  Ta tashi zaune baya kan gadon,  ta nufi dakin motsa jiki dake can qarshen falon.  Acan ta taddashi kan gym yanata motsa jiki sai zuffa yake.  Ta kalleshi "yaushe ka tashi bansani ba?"  ya bata amsa "aini ban kwanta ba ina ganin kinyi bacci na fito tunda naga yanxu ke bakyason motsa jikin kin xama malalaciya" ta yamutsa fuska "wlh ya Bature ni kaina bansan abunda ke damuna ba these dayz in nayi haki nake nafi gane inta bacci"  yace "inaga gajiyan tafiyane har yanxu bai barki ba"  batace komai ba ta nufi kitchen samawa kanta abunda xataci.  




Dafadunkan shinkafa ta dora,  ta samu barkono ta dakashi ta afa kana ta yanka albasa ta xuba manja.  Girkin dai gwanin ban haushi kamar girkin yar koyo, amma ya xatayi haka takeson ci.   Ai kuwa tana tafasowa yaji ya cika kitchen din,  sai tari take ahaka ta gama girkin ta xubo a plate kana ganin abincin kasan zaiyi yaji don ga yayan barkono nan burjik akai sai kuma manja kamar yayi magana.  Gidan gabadaya ya kaure da qaurin girkin wanda shiya fito da Bature daga daki yaxo yaga ko wani abun aka dora aka manta.  Yayi turus lokacin daya hangi Mimi da plate din shinkafa agaba da wannan farar safiyar sai loma take ga bottle water a gabanta robarsa sai diga take sabida sanyinsa. 




Cikin mamaki yace "Mimi?  Kece ke cin wannan abun me qauri haka da safe?  Lfyar ki kuwa?"  ta kalleshi na second 2 tacigaba da lomar shinkafarta karta huce, ya qaraso gabanta ya riqo hannun data dibi abinci xatakai baki yace "ke meke damunki haka?"   tace "ya Bature don Allah ka kyaleni inci yunwa nakeji kuma wannan nake shaawarci"  ya saketa ya koma kujerar dake fuskantarta ya xauna tana naxarinta,  sai data cinye shinkafar nan tas ta kwankwade ruwa roba daya me axabar sanyi.  



Tundaga ranar yake kula da duk wani takunta,  gaba daya ta canja Kullum cikin cin abinci ta manja take safiyar duniya sai tayi wannan dafadukan tata me qauri taci in kuma ba itaba ta kwada garin kwaki tasa manja da yaji tai taci kwadayi dai kamar me,  kuma duk abunda take shaawa sai taci ta qoshi take samun nutsuwa.  



Ranar da abun ya isheshi cewa tai masa "ya Bature a ina xan samu magarya?"  ya kalleta cikin rashin fahimta yace "meye magarya?" ai tanajin haka ta saka kukan shagwaba wai ya raina mata hankali ita magarya xata sha. Lokacin dawowarsa kenan daga aiki,  dayaga abun nata da gaske ne sai ya ciro waya yaiwa ishaq text don bayason taji abunda xai fada.  Ya kalleta yace "yi shiru ba magarya xaki sha ba? Tashi muje gurin ishaq sai ya fadamun inda xaa samo muje in siya miki" tanajin haka ta miqe ta saka hijab dinta na sallah ya tasata gaba suka shiga gidan ishaq.




Suka tararsu a falo,  ishaq ya saka safar hannu ya matso kusa da Mimi take zaune yace "maryam muga hannunki" ta kalleshi kana ta maida idonta kan Bature dake gefenta tace "nifa lfy ta qalau"  ishaq yace "munsani ai ba cewa akai baki da lfy ba just wani gwaji xa ai miki" jiki a sanyaye ta miqa masa hannun,  ya qurawa tafin hannunta ido sannan yacigaba da jujjuya hannunta,  ya gwale idonta yana dubawa sannan yace ta fito da harshenta.  Bayan ya gama dube dubensa ya fara yimata yan tambayoyi,  tambayar qarshe itace yace yaushe rabon da taga period.  Ta fada cikin tunani don ita har ta manta da wani abu period don rabonta da yi tun Anty mami na nan,  kardai ace ciki gareta?  Anya kuwa hakane?  In gaskiyane ya kamata ita ta fara sani, amma sabida ta riga ta sawa kanta baxata haihu ba shiyasa bata kawo ciki gareta ba. 




Maganar ishaq ta katseta,  inda yace da Farida taje da Mimi toilet tayi fitsari ya bata kwalba.  Sukaje tai fitsarin,  bayan fitowarsu ya shiga toilet din kamar 10 minutes ya fito da tsinken gwajin ciki a hannunsa yana cire safar hannunsa ya kalli Bature daya miqe tsaye yana jiran cewar ishaq din.  Ya bugi kafadar Bature yace "sai yanxu na yarda kai din namiji ne ba mace ba kamar yadda nake fada maka abaya,  na yadda tunda ga Mimi nan dauke da cikinka"   



Bature ya tsurawa ishaq ido yana kallonsa,  can jimawa idonsa ya kawo kwallah.  Tabbas tunaninsa ya xama gaskiya Last period din Mimi itace wacce tayi Anty mami na nan,  sannan kuma a xatonsa randa ya kasa bacci Mimi taqi yadda dashi har yayi mata dole a ranar ta dau ciki.  Ashe shiyasa ya kasa haquri,  rabone yasa yayi mata haka.  Allah azeem. 



Mimi kuwa kamar an dasata akan kujera haka tayi,  da gaske itace keda ciki kodai mafarki take?  Lallai Allah maji roqon bawa.  Farida ta taba ta tana murmushin farin ciki tace "ba kuka xakiba besty godia xaki ga Allah da kuma adduar Allah ya saukemu lfy.  Dama can ni ban yarda cewa baxaki haihuwa ba kawai dai abune na lokaci,  gashi kuma Allah ya kawo mu"  




Bature ya tsuguna a gaban Mimi,  yace "maryam burina ya cika xan samu zuri a dake, ya fara share mata hawaye  meye na kuka kuma?" tana dariya hade da kuka tace "kaima ai kukan kake"  yace "aini kukan farin ciki nake" tace "nima haka"  suka saka dariya a tare.   Ishaq da Farida na tsaye na kallonsu.  Yaja hannun Mimi sukayi musu sallama suka wuce gidansu.  Har sun fita suka dawo yace da ishaq "Dan Allah broz banaso kowa yasani,  nafiso inya bayyana kowa yagani"  ishaq yace "baka da matsala"





Ranar taga gata gurin Bature sai wani riritata yake,  kamar kwai a cokali. 



Can dare ta tashi ta dunga addua da godia ga Allah daya nuna mata wannan rana,  bayan ta idar gaban mudubi ta tsaya ta daga rigar baccinta tana kallon shafaffen cikinta wanda akacemata wai da Da aciki. Bataji tashin ba sai ganinsa tayi ta cikin mirrow yaxo ta bayanta ya xiro hannunsa yana shafa mararta a hankali sannan yana kallonta ta cikin madubin.  Cikin kunya ya ta juya ta rungumeshi,  ya dauketa cak ya mayar kan gadon.  




Ya fara magana "Mimi ki fadi duk abunda kikeso inbaki ko in miki sabida kinmun abunda yasani farinciki wanda bantaba yiba"  ta matso jikinsa ta kama hannunsa tace "ya Bature kome nace kaimun xaka iya?"  ya riqo fuskarta yace "in shaa Allah indai inada iko dashi xanyi miki"  ta xama serious tace "so nake kaimun alqawari baxakaimun kishiya ba iya rayuwarmu"  yayi gaggawar sakin fuskarta dake tafin hannunsa ya kauda kai gefe yace "maryam meya kaiki irin wannan maganar?"  tasa hannu ta juyo dashi tace "azatona basai na nemi wannan alqawarin ba xakaimun shi, amma sai gashi bayan na karya billena na nema har turjemun kake. Ca nake sabida bani da damar haihuwa a koda yaushe kana iyayin aure amma yau da muka tabbatar da mun sami Dá ai ya kamata in san matsayina ko?"   ya juyo yana kallonta,  ranta a bace yake don ta daure fuska tamau ya kwantar da kanta akan cinyarsa ya fara magana "maryam bakya gani inna dauri kaina nai miki alqawari Allah yakan iya jarrabata da qarin auren? Wanda yin hakan xaisa mutuncina ya xube a idonki ki dunga kallona a matsayin maqaryaci?" ta katseshi "dakata,  nagane inda ka dosa ada naxaci sabida rashin haihuwa kana iya qara aure,  amma yanxu nagane sabida baka aureni budurwa ka sami budurci a tare dani ba shiyasa xaka buqaci aure anan gaba"  ya riqota don ta fara qure haqurinsa cikin bacin rai yace "karki kuma hada shirmenki da cewa bansameki budurwa ba,  ai nasan da hakan na aureki kuma haka nayi raayi.  Yadan sassauta murya,  maryam bani da raayin xama da mace sama da guda daya amma bansan ko nan gaba ba sannan duk yan uwana da iyayena kinga wanda yake da mace sama da daya? Mu abun kamar a jininmu ne da mata daya muke rayuwa amma fa ban miki alqawari ba wannan maganar babu ita"  ta fusge daga riqon da yayi mata ta juya masa baya ta kwanta batace komai ba. 




Ya bita da kallo saroro, me kenan?  Fushi tayi?  Ya matsa kusa da ita cikin kwantar da kai yace "Mimi nayi lefi amma kiyi haquri kinji karkiyi fushi" tai kamar bacci take,  yasa hannun ya dagota ya fara mata susar qadangare a bayanta.  Ta fara dariya babu shiri tana tureshi ya riqeta gam har saida suka shirya,  yace "da kina nema ki bata mana wannan kyakykyawan yanayin da wani shirmen tunaninki ki fara fushi dani bakisan fushin me ciki bata sauka da wuri ba?" 




Ma masallacin asuba bayan idar da sallah ya fadawa limamin asakashi a addua matarsa nada ciki yana barar adunga sata a addua Allah ya rabasu lfy.  Ya kawo kudi ya bayar. 




A office ma yau sai walwala yakeyi yana faran faran da kowa aciki kuwa harda Hanifa da suke yar tsama kwana biyu baya amma yau sabida yana cikin farinciki sun shirya.  Biyar nayi ya nufi gida. 




Mimi kuwa tashi tayi ta tarar ya fita don yanxu ita da bacci sun daura abota,  tana shirin dora abunda takeson ci Farida ta shigo taxo musu da taliyar hausa dafaffiya da manja da yaji suka zauna suka dunga ci sai da suka tashi da ita tas kana masu aiki suka gyara gurin su kuma suna gefe suna hira. 




Sai da aka kira laasar Farida ta tafi xataje tasa hannu a girkin dare,  Mimi kuwa tana sallah wanka tayi tasa wani blue din wandon Jeans da yellow din shirt.  Fes yaxo ya sameta,  yana xuwa ya buqaci baqo ya tattaro masa duk wani maaikaci na gidan.  




Suka hadu a falo suna mamakin wannan kira,  ya dubesu bayan sun amsa gaisuwarsa.  Yace "inason kowa ya maida hankali akan aikinsa sosai duk da kuna qoqari amma a qara musamman wadan da ke kula da part din madam. Banaso ko tsinke inga tana daukewa sabida tana da lalura irinta ciki a halin yanxu". Mimi take gefensa kunya ta kamata ta sunkuyar da kai sabida harda yan tsaffin dake aiki a gidan a gurin da matar me gadi.  Suka rude da yimasa murna dafatan Allah ya inganta. Ya amsa ya dubi moses wato kukun gidan yace "daga yau na hanata shiga cikin aikinka ka kiyaye duk abunda takeso xata fada maka ka dafa ko kuma ta koya maka yadda akeyi" ya amsa yes sir"




Yakai dubansa ga grace da kuma dayar wato Ester yace?"kune masu tsaftace shashinta sabida haka a kula da kyau kar abar guri da danshi ta zame in hakan ta faru Allah ya kiyaye daureku xanyi"  suka amsa da girmamawa sannan ya juya ga Aisha sabuwar me aikin da suka taho da ita daga wacce mumy ta samo musu yace "Aisha daga yau kece me kula da cikin dakin Mimi da tsaftace toilet dinta da duk wani motsinta wanda ya danganci nan kema ki kiyaye" ta amsa da "to" ya dubi Mimi yace "madam hakan yayi miki?" ta gyada kai kana tace "amma ni banji ka fadan aikina ba kuma kasan xama haka baxai yiwu ba motsin yanada amfani" ya dubeta yace "ki dunga gyara gado kina shiryamun drawer ta sai Aisha tayi ragowar"  tayi dariya tace "ina neman alfarma abarmun gyaran dakinmu da toilet,  innaji baxan iyaba na nemi taimako" ya kasheta da murmushi yace "anmiki"  




Ya dubi matan wato maaikata mata yace "Don Allah kar a ringa barinta ita kadai,  indai anganta ita kadai ko kuma in mutum ya gama aikinsa yaxo ya debe mata kewa don batason kadaici qofa a bude take ga kowacce mace a cikinku." ya dubi yan tsaffin guda biyu yace "Don Allah Baba duk abunda takeso ko yake da hadari ga masu lalura irin tata sai a fada mata" suka amsa suma kana ya sallamesu.   Yakai dubansa ga Bako yace "Bako sai a kula sosai a tabbatar kowa yana aikin dana dorashi akai,  ita kuma maryam duk abunda takeso in sun fada maka koda bana kusa ayi qoqarin samar mata"  ya amsa cikin girmamawa sannan yayiwa Mimi fatan sauka lfy. 




Bayan isha ya dawo masallaci ya shiga wanka,  ita kuma tana dakin tanata xarya daure da towel so take ta shiga bathroom din suyi wanka tare kamar yadda ya dade yana buri amma ta kasa.  Can ta runtse ido ta shiga,  ya bita da kallon mamaki yana xaune cikin qaton bahon wanka wanda ya cika ruwan dumi da sabulan ruwa sai kumfa ke tashi da qamshi.  Mamakinsa ya qaru lokacin da yaga ta cire towel din ta nufeshi, ya qurawa jikinta ido komai ya qara girma daga bobs dinta har hips wanda ada bai kula ba sai yanxu jikin ya kuma haske tas. Ta shiga cikin bahon,  ya janyota tsakiyar qafafunsa yasa soso yana wanketa ya fara yi mata magana a kunne "Mimi luv amma dai inkin haihu jikinki baxaiyi wannan abun ba ko?" tace "wanne kenan?" yace "wannan murmurdrewar ciki ya yakutse stregcht mark (nankarwa) ko kuma kiyi tumbi wannan plat tummy din naki ya baci" cikin dariya tace "inyayi hakan dena sona xakai?" da sauri yace "Allah ya sawaqe just banaso ne amma ni koya kika xama ina son abata a haka" tace "to ai duk akwai maganinsu inba nayi,  amma dai ba lallai bane jiki jiki ne wasu basai sun haihu ba in sukai qiba sukeyi, wasu kuma koda qibar da haihuwar basayi is defense da irin kyan jikin mutum.  Amma dai manya na cewa ba a gane kyan mace saita haihu sabida lokacin in jikinta bashi da kyau duk sai tai ragaf jikinta ya baci in kuma me kyauce wato jikinta xakaga kamar bata haihu ba saima tsam da jikinta xaiyi tayi kyau sabida sabon jini yaxo mata." yace "to in shaa Allah kina cikin masu kyan jikin" 




Yaci gaba da juyata son ransa wai yana mata wanka, yace "Mimi amma dai yanxu na tashi daga rago ko tunda na miki ciki?"  ta hade rai tace "gaskiya ni ya Bature banason irin wannan zancen sai kace wasu yan iska😞"  yana dariyar zolaya yace "ai kuwa kowa ya ganki yaga yar iska tunda ga shedar iskancin nan a jikin ki.  Haka kika dunga bina kinamun wayo  kika amshemun samartaka har saida kika maidani Dan iskan nima 🤣"  ta fara kukan shagwaba tana bugunsa,  ya sassauta dariya yace "sry na janye Mimi luv nine dan iskan tunda na hanaki sukuni saida nai miki ciki"  haka suka dunga wasa acikin ruwa har kusan taran dare,  kana suka shirya suka fito yin dinner.  





Ta xage tayi white rice da stew din da akai sosai,  yana kallonta asace alama cikin nata mai sauki ne don duk abunda ta samu ci take tayi nak sai dai in kwadayin ya motsa. 





Washegari ma kafin ta tashi bacci ya fita,  ta dunga takaicin halin da wannan ciki ya sakata taita baccin asara har mijinta ya fita tana kwance.   Ta lalubi wayarta ta kira baqo tace masa in akwai inda xa a sami wainar gero da quli a nemo mata ita takeson ci.  





Ya fita nema babu dadewa ya dawo ya samota awani gidan abinci anqawatata da kabeji,  ta karba tanaci Farida ta shigo suka faraci tare amma Sam wainar babu dadi wadda ake a Local area tafi dadi.  Farida tace mata taxo su fita xata supervising gidan abincinta daga nan su biya shagonsu suga yadda ake tafi da cinikin.  




Ta kirashi a waya ta fada masa inda xasu,  yace adawo lfy amma su kula sosai sabida abunda yake tare dasu.   



Farida ke tuqin suka isa gurin. Mashaallah komai tas da tsafta anata shige da fice,  masu kula da gurin kamar suyi musu sujjada Mimi tace akwai tradicional food?  Cikin girmamawa sukace wanne xa a kawo musu a ciki?  Tace " tuwon dawa da miyar kuka" suka kawo ta wanke hannu taci Farida sai yamutsa fuska take ita bai mata ba.  Daganan can boutique dinsu sukaje, Mimi a xuciyarta tace kudi shegu ganin yadda ake wani basu girma duk da sun girmi duk yaran shagon.   Suka duba komai har sabuwar order din da akayo da kuma record na ciniki komai babu matsala kana suka tafi. 




Baqo ne ya siyo  tandar wainaganin Mimi yanxu bata da abun so kamar wainar gero da yar tsala kuma wacce ake siyowa bata mata yadda takeso,  yace matarsa ta dunga yi mata duk sanda takeso.  Matar me gadi tace akawo ita tadau nauyin wannan,  hakan yasa Kullum da safe Mimi ke samun abun breakfast irin wanda takeso.  Bature yaji dadin wannan abu da sukayi sun tayashi son abunda yakeso.





Cikin yan kwanaki kadan tai wani irin kyau ta dashe tayi tas ta xama fara sol sabida ciki,  kulawa kuwa har kunya takeji wani sa in duk wata halitta ta gidan hankalinta nakan Mimi.  Bature ya dauke mata komai na hidimarsa,  sau tari kafin ta tashi ya fita aikinta a gidan kawai ta gyara gadon dakinsu ita dashi ta wanke toilet ta kuma gyara kayansu na sawa sai wankin undis a washing machine. In kuma yana gida yana gefenta ko ruwa xatasha saiya dauko mata robar in xama xatai saiya kyara mata gurin  xama. 




In kuma baya gida sukan cika falon kowa yana qoqarin sata farin ciki,  wani lokacin sai tasa a kawo mata yayan Bako taita hira suna mata shirmensu tana dariya ko kuma su fice da mazajensu da daddare suna yawan xuwa shan  ice cream.  



Sosai Aisha ke mata biyayya ta kwadata sosai taga bata da matsala kamar yadda mumy tace,  xata iya cewa bata tabajin dadin xaman aure  irin wannan lokacin ba.   Ishaq yaso taje can asibiti ayi mata scanning aga kan cikin amma taqi tace lokacin beyi ba suka haqura tunda sunsan cikin befi wata daya ba da yan kwanaki.




Ana cikin haka Faty ta haihu, ranar ta kira Mimi ta sanar mata amma namiji ta haifa a maimakon macen da take qulafaci.  Mimi murna kamar me,  tun a ranar ta soma shirin tafiya amma har akai kwana 5 da haihuwa bai barta ta tafi ba don cewa yayi baxai bari taje da wuri taita aiki ba ta jawo masa asarar abunda ya sha wahala kan ya samu.   




Tayi fushinta har ta sakko don kanta ta koma lallashi,  ana gobe suna da safe tana ta hada jaka xata tafi.  Sai lodar Kaya take nata da wanda ta saiwa Faty da baby.  Ya dubeta yace "kiyi sauri mu ajiyeki a airport din karkiyi late"  tace "to,  ai kaqi fadamun kwana nawa xanyi"  yana gaban madubi ya bata amsa "karki damu kiyi tafiyarki in lokacin dawowar ki yayi xan kiraki ki taho" cikin munna tace "to yayana, ai nasan tunda baka barni tafiya da wuri ba xaka bari in dade, Allah ya sa ka barni in wata daya inxaga dangi sosai har garko xanje da gombe" yana dariya yace "karki damu shekara ma xakiyi, fatana Allah yasa karsu gane abunda ke qunshe a mararki don kunya nakeji kowa yasan abunda mukai kan hakan ta samu" cikin damuwa tace "wlh kamar ka shiga xuciyata nima banaso a sani amma dai xan daure baxan nuna inason komai ba.  Inkuma sunce nayi fari da yawa ince mai na canja"  ya yaba da  dabarar data kawo yace "yawwa gud idea" suka sauketa a airport ya juya office.





A gidan Faty ta sauka,  ta tarar sunata aikin suya shinkafar da za a yi amfani da ita gurin fried rice gobe ba tare data suta ba tasa hannu suka dinga aiki sai da suka gama cikin dare kana suka nutse daki da ya Faty suka gaisa ta dauki jariri,  ta bata kayan data lafto duk yan waje suna zaune ya Ahmad ya dawo.  Ya zauna cikinsu aka fara hira har kusan dayan dare kana ya basu guri suka kwanta.



Washegari suna yaro yaci sunan baban ya Ahmad,   suka fara aiki tun asuba har wajen 11 gida ya fara cika komai ya kammala sai kayan cikin rago da suke wuta basu qarasa soyuwa ba.  Taje tai wanka tasa Kaya ba tare da tayi kwalliya ba,   yan gidansu duk sunxo batasan mumy taxo ba sai data fito falo ta tarar da ita a xaune. 




Ta matsa jikinta tana gaisheta,  mumy tana shafar kan Mimi dake qasa tace "lfy lau Mimi ya mijin naki?"  ta amsa mata kana ta gaida matar qanin Dady dake kusa da mumy.  Lubna take xaune kan kujerar dining danta na kuka tace "Dan Allah Anty Mimi goyashi tunda fita xaki inna goyashi baxai bari in xauna ba.   Mimi tace to ta karbeshi ta sabashi abaya tai waje. Aranta tanajin dadin girmamawar da su lubna ke mata a matsayin matar wansu duk da sun girmeme mata amma tundaga kan audu har xuwa auta little babu mai fadar sunanta kai tsaye sai dai suce Anty Mimi ko matar yaya. 




Tana ta aikin juya kayan cikin ragon suna daya kusa soyuwa har yaran yayi bacci,  ta koma ciki ta saukeshi a bedroom ta fito falo.  Habib dan wata cousin dinsu na kuka ta karbeshi shima ta goyashi ta fita da sauri sabida kallon da mumy take binta dashi duk inda tayi.  



Mumy ta juya kallonta xuwa gurin Haj Hawwa faccalarta tace "Hawwa sai nake ganin yarinyar nan cikine da ita ko?"  da rashin fahimta a fuskarta tace "wacce kenan Anty halima?"  tai qasa da murya tace "maryam mana matar Bature" tace "bari ta shigo ingani aini ban kula ba amma mu ciki sati daya ma muna iya ganeshi jikin mace"   



Mimi ta shigo ta kwance Habib da yayi bacci ta miqawa uwarsa shi tace "karbeshi baccinsa beyi nisa ba sabida hayaqi na dawo dashi ciki"  ta karbeshi tace "yawwa na huta rigimarsa"    




Haj hawwa ta tsirawa Mimi ido harta fita ta dawo da kallonta ga mumy tace "tabbas ciki gareta,  bakiga duk ta dashe ba tayi fari fau haba Anty halima ai ko ya kamata ki gane maryam qaramin ciki gareta"  mumy bakinta yaqi rufuwa, nan take ta dakko waya ta turawa mama wacce bataxo ba text na abun farincikin daya samesu. Mama na ganin text din ta kira mumy tana wani irin farinciki.  




Tana gama suyar hancin ta xubo a plate ta wuce dakin ya Faty ta badeshi da yajin daddawa, yawunta sai tsinkewa yake sam ta manta da wani zancen kar agane cikine da ita.  Taxo falo cikin su Lubna ta faraci, wannan abun da tayi shiya tabbatarwa dasu mumy abunda suke zargi. 





Tana gamawa ta miqe zata fita,  anty Zainab din gidansu tace "Mimi dan goyamun mamana tunda fita xaki bacci takeji" Mimi ta miqa hannu xata karbeta Haj Hawwa tace "kai jama a, itama dai kwa kyaleta nata Dan yayi kwari a mararta kun jibge guri daya ita da bata da son jiki sai aiki take tana muku rainon yaya"  Mimi najin haka ta fasa karbar yarinyar tayi bedroom da sauri. 




Lubna ta kalli su mumy tace "Dan Allah Umma Mimi cikine da ita?" Haj Hawwa tace "wlh da gaske gashi nan sai kwadayi take" yasmin tace "haba gaskiya mana naga tayi wani mugun haske"  falon ya dauki sowar murna cikin Mimi kamar itace mace ta farko da xata haihu a zuriar gidan. 




Ana cikin haka saiga almajirin ya Faty ya dawo da aiken da Mimi tai masa na siyan goba (guava) Anty yasmin ta karba tai cikin daki inda ragowar suke da Mimi.  Tana xuwa tace "me ciki ga saqonki yaran da kika aika ya dawo"  Mimi ta qunshe kai a tsakiyar cinyoyinta cikin kunyar duk yadda takai ga kaf kaf dinta saida suka gano cikin jikinta. 




Duk wadan da ke dakin suka xuba mata ido aciki kuwa harda me jego Faty,  yasmin ta tabbatar musu da gaskiyar xancen ta hanyar fada musu abunda ya faru a falo yanxu. Suka dunga murna suma Anty Adawiyya harda guda. Faty kuwa tsurawa Mimi ido tayi tanason gano cikin da akace Mimi nadashi.  







Yasmin ta matsa jikin Mimi ta miqa mata ledar gobar sannan tace "congrat maryam,  indai macece a cikin ki inawa Adil riqo tun yanxu don dake da ya Bature in colour dinku suka tashi haihuwa fure suke haifa wanda kan xama abunso ga kowa."  Faty ta katseta da cewa "gaskiya Anty yasmin Dady ya rigaki,  shima tunkan cikin ya samu yake riqo"  aka kwashe da dariya gabadaya dakin Anty Adawiyya tace "ke kunji mata ko wacce tanawa danta na fari campaing babu ko kunya,  to ai nice uwar yar don haka sai wanda naga dama xan bawa kudai kawai ku fara toshi tundaga yanxu" aka kuma saka dariya Anty Zainab data shigo yanxu tace "wai da alama wannan Baby xatai farinjini daga fadar akwai cikinta har ta samu samari biyu?"  haka dai sukasa Mimi tsakiya suna zolaya tun tana kunya harta ware.





Tacinye gobar tas ta miqe a gado tai kwanciyarta ta fara sanaar datafi karbarta wato bacci.  Lokaci xuwa lokaci Mumy kan leqo dakin taga lafiyar Mimi,  abun ya bawa mutane da yawa mamaki.  Haj hawwa tace "wannan suruka taki Anty halima yar gatace,  bantaba ganin inda ake son suruka haka ba."  bata tashi ba sai qarfe uku,  tai sallah da wanka tayi kwalliya da kayan datai musu iri daya ita da Faty.   Gida ya cika sai hidima ake mumy ta hana Mimi yawan zirga zirgar da take ta datseta saidata tabbatar Mimi taci abinci sannan tace ta zauna duk abunda takeso su Lubna su miqo mata. 



Sai magrib mumy suka tafi,  kafin ta tafi ta tabbatarwa da Faty ta kula da Mimi sosai karta bari taita wannan zaryar sabida qaramin ciki bai juri wahala ba.  Daga qarshe ma sai mumy tace "gobe Mimi ta taho gidanta in sun gama aikin nama don tasan inta zauna anan dole xataita aiki" Faty tana dariya tace to mumy in shaa Allah xan turota da wuri.  





Sai da dare yayi sosai qafa ta dauke Faty ta tambayi Mimi akan cikin "Mimi dashen akai miki ko kuma Allah ne ya kawo?" Mimi ta kwanta a kafadar Faty tace "ya Faty babu wani dashe,  Allah maji roqon bawa shiya dubi rauninmu ya bamu"  Faty tace "Alhamdulillah,  inaji ke xaki haifi macen dana dade ina qulafaci Allah ya inganta ya rabaku lfy ssurukar Dady 😄"  ta miqe tai dakin Ahmad don fada masa labarin cikin Mimi. Mimi tasa jaririn agaba tana kallo tana ayyana lokacin daya rage  ta samu nata dan.  Da haka bacci ya kwasheta. 





A wannan dare wadanda suka san labarin cikin Mimi Allah yayi yawa dasu aciki harda Dady wanda mumy ta fada masa, mama ta fadawa Baffa,  Faty kuma ya Ahmad sai yasmin data fadawa Audu.  Abun dai kamar hadin baki duk wacce ta koma gida daga gidan suna saita fadawa mijinta labarin cikin Mimi.  Sai dai abunda mumy bata sani ba shine shin Bature yasan da labarin cikin ko bai sani ba?  Tasanshi sarai da shiririta tanaso ta fada masa ya kula da Mimi sosai amma kunyar yimasa maganar cikin take.  




Da wuri suka fara aikin naman don haka suka gama akan kari suka gyara gidan tas,  Mimi tai wanka ta shirya Faty ta dibar mata nama sunan da yawa ta sa mata wani a kakidi ta bata yaji shima kamar itace ta haihu ita kuma tayi hakan ne don taga cikin Mimi alama yanason naman suna.  Ta bawa mumy nata naman,  sukai sallama ta hada kayanta kaf tai gidan mumy wacce tun daxu take wayar cewa Mimi ta taho.  




Kusan qarfe uku ta isa gidan mumy tana xuwa dakin mumy taje tai kwanciyarta bayan sun gaisa da mumy din.  Bata tashi ba sai kusan biyar,  tai sallah ta fita falo suka kuma gaisawa da mumy sannan tão kitchen tasa hannu a girkin dare duk da hanata da mumy takeyi taqi hanuwa,  saida ta xuba shinkafar tuwo a ruwan kan gas sannan ta koma daki tai wanka tasa doguwar rigar atamfa sakakkiya taci kwalliyarta ta fito ta dora miyar agushi.  




Tana ta aikinta tsakanin falo da kitchen suna taba hira da mumy abun shaawa kamar ba surukai ba.  Little batanan tana gidan yayar Dady hutu. 




Dady ya dawo suka hadu a falon gaba daya,  shima kamar mumy bai dauki Mimi a matsayin suruka ba.  Yana zaune bayan sun gaisa da Mimi ya fara karatun jarida, mumy kuma ta maida hankali tana kallon tashar MBC action.  Mimi ta fito kitchen ta kawowa dady fura a glass cup,  ya karba yasha kana ta tsiyayar masa ruwa ta miqa masa.  Ya karba yana cewa "Allah yayi albarka uwata"  ta tattara kayan ta mayar kitchen, shi kuma ya maida glass dinsa yana karatun jarida.  




Baifi saura 20 minutes ai kiran sallar magrib ba, Mimi ta gama tuwon danyar shinkafa fara sol yayi ligif yayi laushi ta sassakashi a leda ta kawo dinning tana shiryawa kafin miyar ta qarasa.  Gidan ya cika da qamshin miyar agushi wacce taji kifi.  





Tana tsaye wajen dinning din kamar a mafarki ta hangi Bature a qofar falon,  ta ware ido don ta tabbatar shidinne ko gixo yake mata.  Kiran sunanta da yayi shiya bata tabbacin shidinne.  Su mumy da basu kula dashiba sai yanxu suka xuba masa ido,  shidinma yakai 5 minutes tsaye a gurin kafin Mimi ta ankara da xiwansa don tun lokacin data kawo food warmer yake gurin yana kallonta ita da yan bokon surukanta dake zaune a falon.  



Dady ya katseshi da cewa "sulaimanu shigo mana" baice komai ba sai kallon Mimi yayi dake tsaye alamar ita yake so tazo taryarsa. Ganin haka Dady yacigaba da karatun jaridarsa,  Mimi ta dubi mijinta dake tsaye ya marairaice yana kallonta alamar taxo.  Takai kallonta kan mumy da Dady kowanne  yana abunda ke gabansa kamar basusan da Bature da Mimi ba a gurin (shegu yan boko 😄) 




Tana ganin haka ta nufeshi,  ta karbi jakarsa dake goye bayanshi wacce take dauke da kaya set biyu,  yadan rabata a jikinsa tai saurin kaucewa yakai hannu mararta yace "ya Baby na?" wannan magana daya fada karaf a kunnen mumy.  Tayi hamdala a xuci ya tabbata Mimi tana ciki kuma daga Mimi har Bature sunsan da cikin, ita kam sai yanxu ta yadda danta namiji ne ada ta dauka sulaimanun aljana ta aureshi ko kuma bashi da lfy irinta maxa kuma a xatonta xaman kai da qafa suke shi da Mimi amma yanxu wannan tunanin ya kau tunda ga Mimi nan dauke da cikinsa.  





Mimi tai saurin ture hannunsa ta nufi cikin falon da jakarsa,  dakinsa ta nufa na da ta ajiye masa ta fito.  Ta sameshi xaune akan kujerar dake tsakiyar su mumy, mumy ta kalli qafarsa tace "Baba ya kashigomun falo da takalmi har kake takamun centre carpet?" ya marairaice yana duban Mimi dake tsaye can nesa yace "mumy Mimi ce kemun wannan hidimar kuma yau ganinku ya hanata yimun"   Dady ya kalli Mimi yace "maryam  xoki hidimtawa mijinki mu babu ruwanmu daku"  




Ta matso a kunyace  ta taimaka masa ya cire jacket dinsa,  ta tsuguna ta cire masa sau cikin qafarsa ta zare  masa sucks tai daki.  Ta fito ta kawo masa try dauke da cup din fura da ruwan roba,  ya karba yasha ruwan yabar furar yace "Mimi ba a gama abinci bane yunwa nakeji nayi missing delicious dinki." tace "na kusa qarasawa kasha furar kafin na ida" yace "No barshi innasha fura yanxu kashemun jiki xatai,  inkin gama naci" ana kira suka nufi masallaci shid Dady. 




Basu dawoba sai bayan isha,  suna xuwa dinning suka nufa.  Mimi ta xubawa kowa abinci kana ta xauna,  sukaci abincin sosai don  girkin yayi dadi sosai.  





Har kusan tara tana falo xaune yayin da tundazu yayi wanka acan daki yake jiranta,  mumy ce tagaji da xamanta ta koreta gurinsa.  





Tana bude qofar ya taso ya dauketa gaba daya ta fara wuntsula qafa ya direta kan gado ya kifa kanta,  ta hararreshi tace "ai bakacemun  xakaxo ba kawai saina ganka"  yace "nakasa xamane shiyasa na biyoki my luv"  tace "yaushe xaka koma? "  yace "cewa xaki yaushe xamu koma?" ta marairaice "haba ya Bature banfa je gidan mama ba"  yace "tashi muje yanxu" tana hararsa tace "yanxu inmunje minti nawa xamuyi dare fa yay" yace "to shikenan gobe sai mu maida tafiyar da yamma sai in kaiki da safe wajen uku ki dawo ana laasar saimu tafi" ta zunburo baki cikin shagwaba tace "nifa gaskiya ba yini xanyi ba kwana nakeson yi" fuskarsa dauke da takaicinta yace "Allah inbaki maida bakin da kika zunburomun ba bazakije ba sassafe xan tasaki muyi gaba" 





Maimakon tayi abunda yace sai ta miqe ta kwanta,  ya leqa fuskarta yace "fushi kikai?" taimai banxa ya burkitoto ya fara kissing dinta yace "sry Mimi luv kinga aiki na baro na taho sabida na kasa haqura ki dawo,  kinga kuma bai dace naqara kwana ba saboda gurin aiki dama mr Alex yace tunda na aureki na fara shiririta da aiki" haka ya dunga lallabata harta sakko. 



Kamar yadda yayi alqawari da sassafe ya kaita gidan mama,  suka gaisa ya tafi yace zai dawo daukarta bayan azahar don su tafi da wuri.  Daganan gidan Faty ya nufa yaga Baby,  Ahmad ya dunga yimasa tsiyar angon qarni shidai kunya yake ace matarsa nada ciki kowa yasan abunda sukai wai shin ya akaima suka gane. Yayi musu shiru sukayi suka gama.  



Acan gida kuwa Baffa da mama kamar su goya Mimi,  Baffa daxai fita kudi yabawa Mimi wai ta riqe ta dunga siyan duk abunda takeso.   Matan gidan sun san abunda yake faruwa don alamun ciki sun bayyana jikinta.   




Mama tasa Mimi agaba akan ta fada mata abunda takeso wanda babu acan tasa anemo mata.  Mimi tace magarya sai yajin barkono Faty ta bata na daddawa.  



Daya daga cikin masu aikin gidan mama ta aika kasuwar rimi suka siyo kurna, magarya, goruba bararriya, tsamiyar biri da dai dangin irin wadannan kayan har aya danya.  Ta hadawa Mimi su kusan buhu guda  ta daka mata yaji me dadi cikin bokitin roba.  Matan gidan suka tsaya suna kallo wato ashe su duk ba son yaya suke ba yau sukaga yadda akeson yaya.  



Mimi na kwance akan doguwar kujera tunda ta idar da sallah tayi filo da cinyar mama, mama tanata shafa kan Mimi dake bacci cikin tsanin son diyar tata lokaci xuwa lokaci takan sumbaci kuncin Mimi.  Ahaka Bature ya shigo ya samesu,  mama tadanji kunyar yadda yaga tana shafa kan Mimi.  Yadan bugi qafar Mimi yace "maryam tashi qatuwarki dake kin kwanta a cinya" mama tana dan murmushi tace "auta ce fa Babana" yadan sosa. kai yace "au hakane fa"  ta miqe ta shiryo dama tayi wanka,  mama tahau sawa afita da kaya ana sakawa a motar Bature yayi mamakin wadannan kaya duk dasu xasu tafi kamar masu gudun hijira.  



Ta rakasu har qofar gida tana jaddada musu su kula sosai,  ta budewa Mimi qofar mota ta shiga ta rufe tace "autata a kula sosai kinji yanayin yanxu ba kamar da bane sai a hankali" Mimi tai rau rau xatai kuka tana kallon mama, ganin haka mama ta koma ba tare data qara magana ba itama tana share tata kwallar.  Bature jikinsa yayi sanyi, banda aure waya isa ya raba da da mahaifi?  Sai dai ko mutuwa.




Acan ma gidan mumy  ta hadawa Mimi kayan gwadayi da yawa hardasu aya me suga da kantu.  Ana idar da sallar laasar yaso su tafi amma   mumy ta tsaidasu da abu mara dalili don kawai bataso su tafi su barta.  Dady cikin qosawa yace "Halima Dan Allah kibar yaran nan sutafi kar suyi dare a hanya"  tayi shiru can tace " nikam Bature ka haqura ka tafi mana kabar yarinyar nan a gurinmu xatafi samun kulawa"  ya zaro ido yace "mumy 😳 tab inbar Mimi anan inxauna acan ni daya?  Gidan ai yaxama kango inba maryam.  Gaskiya mumy baxan iyaba nafiku buqatarta kusa dani kuma ina kulawa da ita ko Mimi?"  mumy badan tasoba tace " to ai shikenan amma nikam hankalina baxai kwanta ba"  yasa Mimi agaba lokacin biyar harta kusa suka shiga mota mumy tace "Dan Allah babana ka kulamun da ita gatanan amana a hannunka" yace "mumy  ina kulawa da ita  amma xan qara akai in shaa Allah xan kula da ita"  suka tafi suna dagawa juna hannu.  



Mumy tace "Allah yasa dai wannan rawar kan da yake ba takurawa yarinyar nan yake ba don namiji bashi da haquri sam akan mace mai ciki" Dady dake bayanta yace "ji yada girma to koma meyayi ba matarsa bace"  tai shiru ta koma ciki. 





Su Bature kuwa sunata sharara gudu akan titi don yanason su isa da wuri,  Mimi ta fito da yajin ta na daddawa dake qulle a leda acikin jakarta ta dunga dangwala tana lasa Bature ya dunga kallonta aransa yana mamakin kwadayi irin na me ciki.  Yace "yarinya keda kano kuma sai kin haihu"  tace "haba kai ka soma?" yace "wlh da gaske nake duk abunda xaisa kixo angamashi sai dai inwani abun ne ya taso" tace "tab  aikuwa dana kira mumy na mata kuka"  yace "ai sai dai in xuwa xatai ta tafi dake amma ni ko tace in kaiki baxan iyaba"  suna cikin hirar yaji shiru ya leqa yaga tayi bacci ya dora kanta kan kafadarsa suna tafiya suka tadda check point.  Sojan ya buqaci Bature ya tada Mimi,  yace masa matata ce bacci take  yace "katashe dai in tabbatar" yadan bugi kuncin ta tashi tana kallonsa ya nuna mata sojan dake tambayarta tace "eh mijinta ne" yace "Allah ya baku xaman lfy"  ta koma baccinta. 




Bayan isha suka isa,  sunayin ramuwar sallolinsu suka kwanta.  Washegari da Farida suka kwance tsaraba ai kuwa suka hau kai suka dunga ci.  Abun ya xame musu abinci Kullum suna fama da kayan kwadayi. 





Sunje asibiti anyiwa Mimi scanning cikinta wata biyu babu sati daya. Yayin dana Farida yaje kusan 4 months babu yan kwanaki,  Bature ya dunga kallon Dan tayinsa dake cikin Mimi ta cikin computer din. Ya shafa cikinta yana murna. 

 


Xamansu suke me dadi yana bata kulawa duk wani motsi datayi tayi kyau tayi yar qiba irin ta ciki fatar nan kamar ansaka mata leda akai. Bata da kewa inyanan yana manne da ita inkuma bayanan hadimanta suna kewaye da ita suna mata fadanci da girmamawa kamar suyi mata numfashi. Da kayan kwadayinsu ya qare mama takanas ta loda musu wasu ta aika ta tasha Bako yaje tasha ya karbo musu,  mumy ma Kullum cikin waya da vedio call tana ganin Mimi.  Hajja ba a barta baya ba itama saqonta yana iske Mimi kota kirata.  Safna kan shigo duk bayan kwana biyu tana duba amanar mumy da ya Bature.  Ya Taheer ma bai taba shigowa gidan ba tunda aka kawo Mimi amma wannan karon hardashi amasu sintirin duba Mimi bisa umarnin hajja da mumy. 





Bature kuwa Sam bashi da sukuni akan Mimi sonta yake kamar wani mahaukaci,  baya gajiya da kusantarta sabida wani abu dayakeni yanxu dangane da ita bashi da sukuni inbai jishi jikinta ba.  Abun burgewar itama bata nuna masa ta gaji koda yaushe tana maraba dashi.  



Fauxa ta haihu su Mimi da Farida sukaje Lagos suka kwana uku bayan suna suka dawo Baby girl ta samu duk da dai 7 month ta haifi cikin (bakwaini)  sunga gata gurin sunusi yarinya taci sunan Mimi (maryam) sunji dadin wannan kara da fauxa da mijinta sukai.  





Suka koma Abuja cike da kewar juna, sukacigaba da rainan cikinsu.


Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by rahman Mohammed (hajia)

Editing by mmn khairat 
📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 5⃣7⃣



Wata litinin da yammaci suna zaune suna hira ita da yan aikin gidan hadi da kallon wani film a tashar Max, tana sanye cikin atamfa riga da skirt dai dai jinkinta ta cokala dauri.  Tana xaune kan centre carpet ta miqe kafa tana hambadar garin quliqulin dake gabanta yayin da su kuma wasu suna kan kujera wasu kuma suna zaune kusa da ita.  



Wajen hudu da rabi Bature yayi sallama ya shigo,  suka amsa suna gaisheshi ita kuma Mimi kallonsa take ganin ya dawo da wuri.  Suka watse suka barsu a falon,  ya matso kusa da ita yana cewa "Mimi da iyalanta kunajin dadinku"  ta riqo hannunsa ta dora akan cikinta tace "ya Bature ai mutum rahama ne xaman kadaici ba koda yaushe yake da dadi ba,  duk da akwai lokacin da mutum ke buqatar yaji ya kadaice" ta miqe ta kawo masa ruwa da kunun ayar da bata rabo dashi.  



Ta rage masa kayan jikinsa takai daki ta dawo ta haye cinyarsa suna hirarsu,  wajen qarfe shida yasmin tai sallama bayanta me aikinta ce dauke da Adil sai Bako daya dakko mata qatuwar trolley dinta.  



Mimi ta taso da saurinta kamar xataci da baka ta nufi yasmin ta rungumeta tana cewa "Anty yasmin wannan ziyara taki da dadi take" yasmin dinma dariya take tana "Anty Mimi karki kadani ki yiwa Babynmu illah"  ta karbi akwatin yasmin a hannun Bako xata shiga daki saiga little itama tana kici kici da tata akwatin.  Mimi da gudu suka rungume juna da little tana cewa "yau gida yayi albarka" little tana dariya tace "name sake dama munso baki surprise ne shiyasa bamu fadamiki xuwanmu ba" ta karbi kayansu ta fara shiga dasu daki,  little ta nufi Bature dake xaune yana kallonsu ta shige jikinsa yana shafar kanta yace "autar mumy yau kune a garin namu?" yasmin kuma matsawa tai tana gasheshi.  




Mimi ta dunga xarya tsakanin falo da kitchen ita da masu aiki,  sai da suka musu gabansu da duk abun buqata kana ta zauna suka gaisa.  Tace "kuci abinci kuyi wanka ku huta"  yasmin tace "bamu tare da yunwa ko gajiya don a jirgi muke"  basuci abincin ba sukace saiko jimawa sunsha dai kunun ayar da dambun nama sannan aka zarce da hira anan takejin wai bikin qanwar yasmin sukaxo wanda za a fara jibi laraba kuma ita yasmin din anan suka sauka gidan Mimi sabida batason can don cikowa da sharing toilet.  



Anayin kira Bature ya tashi ya shige ciki yayi shirin masallaci ya fita,  su kuma sukai sallah. Yana dawowa isha ya taddasu cikin shirin fita Mimi na jiransa xasuje gidansu yasmin din don susan isowarta.  Yace a dawo lfy suka dau hanya. 



Acan gidansu yasmin hannu bibbiyu suka karbi Mimi duk da bata taba xuwa ba amma yawanci sun santa  don sunje bikinta.  Lallai ta samu karbuwa sosai a gidan don kamar su goyata manya da yara sai haba haba ake da ita,  suna mata mitar bata taba xuwa ba itadai murmushi take a xuciyarta cewa tai masu kudinnan sai kana baya baya dasu inba haka sai suga kamar don abun duniya kake tare dasu.  Aka shiga hirar bikin harda amaryar ta dakko anko ta bawa Mimi kyauta duk kuwa da cewar da yasmin tayi tayiwa Mimi amma tace itadai tayi niyya.  Mimi ta karba tana xuba godia,  har kusan 11 suna gidan Mimi taji dadi don yadda suka karbeta duk da kudin da suke dashi da kuma shedar kafirin girman kai da ake musu ita dai basuyu mata ba. 




Ta ayyana a ranta ba qaramin soyayya yasmin kewa Audu ba don inba haka ba da bazatabar wannan daular duniyar gidan nasu ta auri Audu ba.  Duk kuwa da cewa shima ya tara manyan kudade amma ko kusa baxa ahada kudinsa da ex gwamna ba kuma sanate a yanxu.  




Suka fito suka shiga mota ita da little suna jiran yasmin da bata fito ba.  Little kewa Mimi gulma "gaskiya ya Mimi ba qaramin so yan gidannan suke muki ba,  jiba daga xuwa kamar su riqeki gaba daya.  Wlh mugayen yan rainin wayone suna kallon mutum a dage inkaxo kafin ai maka dariya sai anji waye Dad dinka amma kinga ke daga xuwa kurtun farin jini ya fashe miki a gidan, muma fa don sunga babu abunda suka fimune duk da ubansu politician ne shiyasa suka sake damu"  Mimi ta dunga dariyar maganar little tace"haka ake yawan fada ko yasmin dake qaunata mutane da yawa mamaki suke ana ganin aurena da ya Bature zaisa ta fara kishi dani, amma kinga babu matsala ko kadan" little tace "wlh kuwa har mumy mamaki take kuma tanasan kusancinku wai ko yasmin xatai koyi da wani halinki" Mimi tace "to Allah yasa amma Anty yasmin sai a slow wani lokacin kamar yar gwaya"  haka sukaita hira ko ince gulma harta fito suka tafi. 




Qiri qiri Mimi ta guji dakin mijinta ta koma cikin su suka kwana hira sai dab da asuba sukai bacci.



Cikin kwanakin bikin sunsha zarya  don yasmin akwai qafar yawo, tajasu can ta jasu nan amma dai sunyi shar sunsha qunshi da kitson gashin kanti ita kuma Mimi dake akwai gashi da nata akai mata.  Farida ma ba abarta a baya ba da ita aketa wannan zirga zirgar,  sau tari sai Bature da ishaq su dawo gida matansu basanan.  Bature yakance yasmin akwai shedanin yarinya,  Mimi tun tana tambaya tace xasu fita ta waya harta dena tambayata.



Ranar juma a za ai dinner kuma itace ta qarshe a tsarin bikin sai wacce za ai asabar bayan ankai amarya da safe Audu ya iso,  da daddare sukaje dinner din suka dawo harda Farida wacce Mimi ta bata ankon da amaryar ta bata kyauta.  




Sun sami Bature shi kadai a falo yana xaune yana aiki a system,  suka xube falon lokacin wajen 12 na dare Farida ta shige gidanta.   Audu ya cire hular kansa,  yace "ya Bature bakai bacci ba?" yace ina naga ta bacci kun barmin gadin gida?" duk sukai dariya,  yasmin ta xauna kan kujerar da Audu ke kai ta dora qafarta kan cinyarsa bayan ta cire hills din qafartata tace "Dan dannamin qafata darling nagaji"  ya gyara xaman qafarta akan cinyar ya fara ja mata yatsu yana matsa kafar.  




Little kuma kusa da Bature taje ta dora kanta a kafadarsa,  yayinda Mimi ke daya gefen nasa xaune batare data jingina dashi ba don ita kunyar su Audu take.  Kamar an musu dole suka fara watching horror movie din da ake a MBC action,  sunyi tsit Audu yana dann waya yayin da Bature ke aikinsa.   Little ta qara shigewa jikin Bature cikin tsoro,  Mimi ma dake gefe batasan lokacin data matsa jikinsa ba ta qanqameshi,  ita da little sun hanashi aikinsa ta hanyar kankameshi sun hanashi motsi.  




Wayar little tayi qara yasmin dake jikin Audu itama a tsorace qarar wayar tasa ta callara qara,  suka dubeta a lokaci daya suma a razane suka fuskanci tsoro yasakata yin qarar kana suka kwashe da dariya har maxan.  





Little ta dauki wayar tasa a handfree don Dady ke kiranta,  a shagwabe tace "Dady ka tsoratamu wlh" yace "kiran nawa ya razanaki autata?" tace 'just muna watching horror film ka kira' yace "Ok" suka gaisa har Bature, Dady yana cewa ta dawo sunday lallai don monday xa a koma makaranta.  Ya tambayi Mimi  ta miqa mata wayar  tace "Dady ina wuni?"  ya amsa 'lfy mamana , ya jikin naki' tace "Lfy lau Dady" yace "to a dunga kula kinji,  mumyn ki tananan Kullum tana xancenki"  tace "to Dady agaida mumy,  bata kusa?  Yace "eh taje birthday din friend dinta"  ya tambayi yasmin aka miqa mata wayar,  itama hira sukai sosai kuma har tafi Mimi sakewa da Dady.  Mimi kuwa tunani take shidai dan boko babu ruwansa,  da ace yasmin ce yar uwarsu da sakewar da xatayi sai tafi ta Mimi don Dady yadda yakeson yayansa haka yakeson surukansa. 



Hira ta balle bayan ajiye wayar Dady,  har Audu ya fara hamma yace "ya Bature nidai bari inje in kwanta" yace "Ok nima baccin nakeji amma maryam da maryam (little da Mimi) sun sakani tsakiya ko motsi sun hanani yi don ma gobe weekend"   Audu yayi dariya yace "tsofaffi ba kunsan kuna tsoron kuka fara kallah" 



Yasmin tace "Tab lallai ma, kan uban can"  duk suka juyo suna kallonta.  Mimi tace "Anty yasmin lfy "  tana haki kamar wacce tayi tsere tace "wani labari akeyi a grp dinmu na skul yanxu a watsap wata friend dinmu xa aiwa kishiya" ta fada tana nuna wayar hannunta fuskarta cike da tashin sense kace ita xa aiwa kishiyar.  





Mimi ta dan maida numfashi tace "kai amma har kin bani tsoro wlh na dauka wani abun tashin hankalinne ya faru"  tana kallon Mimi tace "akwai tashin hankalin daya wuce kishiya Mimi? Ai wlh da aimun kishiya gara in mutu" duk suka xaro ido suna kallonta cikin mamaki banda Audu don yasaba jin haka.  




Mimi tace "lallai Anty yasmin kice randa ya Audu xai qara aure akwai world war 3"  ta kalleshi hankalinta kwance sannann ta dubi Mimi da alama maganar da xatai har xuciyarta ba tare da la'akari da yayan mijinta dake xaune ba tace "ai wlh Mimi duk randa Audu  yanemi qara mata kasheta xanyi, inkasheshi sannan inkashe kaina"  Mimi cikin tsanin kidima tace "duk soyayyar da kike masa?" tace "yes gara in kasheshi da inyi sharing dinsa da wata"  




Suka tsit babu me motsi kamar ta danna musu pause 😄. Bature cikin ransa cewa yake lallai yasmin saiti be isheta ba, koda yake yawancin mata haka suke akan kishi,  ashe shi tasa matar data tsaya akan yayi mata alqawari kawai musulmin kishi gareta koda yake komai na Mimi unique ne.  




Audu ya katse masa tunani inda yayi dariya ya kalli yasmin don sam be damu da wannan maganar da tayi ba da alamu ya saba ji, yace "kwantar da hankalinki Baby baxaki kashe kowa ba don ke kadaice xaki xama matata a gidan duniya in shaa Allah.  Amma fa kinsan baki isa ki hana abani hurul ayni ba a aljannah 😅" duk sukai dariya jin shaqiyancin sa.  Yaja hannun futsararriyar matar sa (inji hajja 😄) sukai daki.  Suma duk suka watse Mimi tabi nata mijin yayin da akabar little ita kadai a dakin baqi. 


Bature dariya ya dunga yiwa Mimi wai tabar mijinta sabida yasmin, yanxu yasmin da mijinta yaxo ta gujeta. Kai madallah da aikin yar duniya yasmin. 



Ranar lahadi sukai shirin tafiya, duk taji babu dadi don tana da sabo. Little tace "ya Mimi don Allah Baby girl xaki haifo mana me irin gashinki"  yasmin tace "harda ma skin colour dinta" Mimi taji kunyar maganar cikinta da sukai a gaban Audu tace "kaji Anty yasmin ni bani da komai ke mukesa ran ki haifa mana twins"    ta zaro ido tace "ni da haihuwa kuma ai sainan da 10 yrs kema don bakisan yadda take ba shiyasa kikemun fatan in kuma,  amma nasan inkikai kikaji yadda akeji baxaki kuma bari kiyita kwana kusa ba"  Bature yana jinsu Audu kuma cewa "eh dake ance miki kowacce mace raguwace irinki ba"  suka tafi suna marmarin juna Mimi tace da little "don Allah my little kina gama junior waec Ki taho nan muyi xamanmu kinji,  xan fadawa Dady ma" little tace "to in law xanxo muyi ta yawo muna kashe selfie ina sawa social media ina cewa nayi hadu da Sasha Obama"  yasmin tace "wlh kuwa yadda xa ai bare yanxu data kuma haske kamarsu tafi fitowa"  



Bayan tafiyarsu Mimi ta xauna jugum,  duk batajin dadi da suka tafi. Itadai Allah ya dora mata son yan uwanta duk kuwa nisan dangartakarta da nata tana sonshi. 




Ya kalleta yasan matsalarta,  duk son mutanensa Mimi ta fishi.  Besan akwai ragowar matan dake qaunar dangin mijiba sai akanta,  koda yake ita Mimi ba dangin miji kawai ba kowa ma so take koda kuwa masu yimata hidima Kullum tana cikinsu ko gani tai mutum baya walwala xata tambayeshi akwai problem ne?  In tana da hanyar da xata temaka tana gaggawar kawo qarshen rashin walwalarsa.  Wannan shiya siya mata mutunci da soyayya a wurinsu. Yasha ji tana fada musu sudin ba kasassu bane don suna aiki qarqashinta kawai haka Allah ya tsara musu. 





Ya qarasa gurinta ya lallabata har yana mata macilili da qafafunsa tana dariya.


***** ****** ****** ******


Wani daren lahadi, lokacin cikin Mimi yakai wata uku daf yake da cika hudu ya fito yayi das a jikinta wanda kana ganinta xaka ankara she is pregnant. 


Goman dare ta gama karatun novel din da aka turo a grp dinsu mai suna ZAKISAN KONI WAYE na Ummu maryam.  Ta miqe ta kashe kaf kayan wutar dake falo ta nufi bedroom. 



Ta tsaya bakin kofar kofar tana kallonsa sanye yake cikin kayan bacci blue me haske yana xaune kan gado ya jingina jikinsa da allon gadon yayinda qafafunsa ke miqe sanbal ya dora system akan qafar yana aiki as usual,  fuskarsa sanye da glass wanda yake amfani dashi inyana kallon system don rage hasken, kuma ta hasken system dinne take kallon fuskarsa don dakin babu haske sai na fitilar gefen gado. 



Ta taka a hankali ta isa gabansa ta kira ssunansa cike da shagwaba "ya Bature" yana jin yanayin yadda ta kirashi yasan halin ya motsa (shagwaba da kuma rigimar da take masa tunda tasamu ciki) yayi serving aikin da yakeyi kana yayi shutting down din computer ya ajiye kan bedside ya riqota ya xaunar akan jikinsa yace "ya akai Babyn yayanta?" 




Ta narke ajikinsa tana shafa sajen fuskarsa da gashin daya kewaye qasan hancinsa zuwa habarsa tace "inason yin bacci ne, kuma kasan bana iya kwanciya ba ajinkinka ba kai kuma naga aiki kake" ya zare glass din fuskarsa ya ajiye yace "ai na ajiye aikin ranki ya dade, kinfi komai mahimmanci a gurina kedai kawai yi baccinki zuciya da jikina duk nakine"  ta kalleshi cikin ido takai bakinta daf da nasa har hancinsu na haduwa tace "are u sure?" ya qara hada fuskarsu yace "i m sure soul"  ta lumshe ido tana shaqar numfashinsa da yake sauka kan nata hancin tace "Duk duniya babu inda nake xama naji dadi sai kan qafarka,  babu inda nake kwanciya naji dadi nai bacci gamsashshe sai qirjinka" ya kamota ya kwantar da kanta a saitin zuciyarsa yace "MARYAM AL' AMIN daka yau na mayar miki da wadannan wurare da kika ambata wajen xamanki da kwanciyarki har abada, duk sanda kike buqatar hakan kixo ki kwanciyarki" tai luf tanajin bugun zuciyarsa.



 Washegari monday a wurin aiki mr Alex ya buqaci yaje supervising wani aiki da sukeyi da wata company.  Ya fito cikin shirinsa na fita lokacin wani wurin 10:34 AM,  Hanifa dake wajen office din ta miqe da sauri tace "sir xakaje wajen aikin ne?" yace "eh"  a takaice,  ta danyi qasa da murya cikin sigar lallashi tace "to inmaka rakiya mana?" yayi jim yana nazari kamar baxai amsa ba, can yace "Ok taho muje kya rubutamun report "  ta dauki jakarta cikin rawar jiki tabi bayansa. 





Wani irin farinciki take ciki lokacin da suke zaune bayan motar ita dashi driver na jansu,  ta dunga hangosu a matsayin ma'aurata ita dashi, inama hakan azahiri ne da matsawa xatai jikinsa ta kwanta kan dantsensa tana wannan mafarkin har suka isa wurin. 




Sun jima a wurin sosai don an dan samu mushkila,  yatsa ya dudduba wurin da ake buqatar gyara yayi musu gyara, yayin da Hanifa ke gefe ke rubuta duk abunda ake. 



A gajiye suka fito lokacin ankusa sallar azahar,  garin yadau xafi sosai irin zafin damuna ga hadari ga kuma rana ta kwallare,  suka shige bayan mota ya bawa driver umarnin ya qure AC shi kuma ya rage rigar jikinsa ya bar shirt ya sassauta tie din wuyansa. 




Ya jingina bayansa a jikin motar kansa yanadan sara masa ya gaji sosai,  kwatsam ya tsinci muryar Hanifa tana cewa "sir tunda mungaji mudan biya gidanka musha ruwa muyi lunch mana sai mu koma" yayi shiru yana tunani kafin yace "to shikenan muje"  ya bawa driver umarnin ya wuce dasu gida"  Hanifa kamar ta xuba ruwa qasa tasha don dama bata taba xuwa gidan ba,  lallai asirinta yana tasiri akansa inba dan haka ba aiko kafin yayi aure bai taba kaita gidansa ba balle yanxu da yayi aure.





Suka shiga cikin gidan ya jagoranceta har main falo,  ta xauna kan doguwar kujera kusa dashi. A kaikaice take kallon maka makan pics din Dake falon wato window size,  Bature ne da Mimi a pics din wanda yafi jan hankalinta shine wanda suka dauka ita Mimi sanye da weeding gown wacce ta matseta tsam ta saqala hannyenta a wuyansa tayi qasa da kanta tana dariya, shi kuma sa hannayensa ya zarge qugunta ya hadata da jikinsa yana kallonta cikin soyayya,  daganin pic din anyishine ranar dinner dinsu ta aure don kayan da suka saka ranar ne hanye jikinta. Sai wanda suka dauka tana sanye da baqaqen kaya riga da skirt ta riqe jar flower a hannunta shima baqin suit ne a jikinsa sun zarge hannun juna suna tafiya akai pic din wato walking picture suna kallon juna suna dariya.  Ta hadiye wani abu wanda xa a iya kira baqin ciki da kishi tace a xuciyarta, Allah ka nuna min ranar da sulaiman zaimun irin wannan daqumar. Ya dauki wayar landline ya kira kitchen ya sanar yana da baquwa,  kuku yayi saurin kawo ruwa da lemo sai snack ya fadamasa bai gama abinci ba amma ya kusa qarasawa yana mai bashi haquri da cewa besan xai dawo  da wuri ba.  Ya daga masa hannu  alamar yaje,  babu bata lokaci ya bar wurin. 




Hanifa ta  dauki fork ta faracin fruit din dake kan try, ta ciro pawpaw ta nufi bakinsa da ita,  ga mamakinta saiya bude bakin ta saka masa. Ta qura masa ido yana taunawa, yayi dan murmushi yace "wannan kallonfa kamar baki sanni ba?"  




Direct ta fara magana "sulaiman inasonka,  ni kaina bansan irin wannan so da nake maka ba. Ya dace ace na rabu dakai tun lokacin dakai rejecting dina kayi aure, amma natacciyar zuciyata taqi bani hadin kai,  Kullum da axabar sonka nake kwana nake tashi da ace nasan yadda xanyi in cirewa kaina wlh da nayi, amma dake Allah ne ya jarabceni dashi bani da mafita.  Sulaiman bani da burin daya wuce in wayi gari ingannin a matarka dubeni sulaiman Kullum girma nake babu aure sabida soyayyarka" ya qurawa Hanifa ido tana kuka wurjanjan, kuma alamu ya nuna maganar da take babu qarya ciki don irin maganar nance wadda ke fitowa daga zuciya.  




Tausayinta ya kamashi tabbas yasan tana sonshi amma bai zaci abun yakai haka ba.  Ya fara magana cikin kwantar da halshe da lallashi "Hanifa kiyi haquri karki daukeni a mayaudari, mara tausayi ko wanda besan darajar soyayya ba.   Baxan iya cemuki komai ba tsakanina da Mimi,  abunda kawai nasani in na hada soyayya Mimi da wata xan xalunci dayar kuma baxan iya adalci ba"  




Ta katseshi ta hanyar kwanciya a qirjinsa tasa hannu ta balle botiran rigarsa guda biyu ta zira hannunta tana wasa da gashin qirjinsa tana shafa nipple dinsa. Har yanxu hawaye ke tsiyaya a idonta. Ganin halin da take ciki yasa be hanata ba, saima hannu da yasa ya shafar bayanta a hankali jikinsa yana amsar saqon data ke aika masa.




Bata taba samun irin wannan damar akansa ba, wai yau itace bisa qirjin Bature har tana wasa kuma yana lallabata cikin kissa ta fara magana "Bandamu da rashin adalcinka ba sulaiman,  ni dai burina in ganni a matarka koda kuwa a matsayin sadaka   (kwarkwara) in hakan ta faru na rantse da Allah xan maka biyayya kuma xan yiwa matarka biyayya." cikin tausaya mata yace "Hanifa baza ai haka ba kidena ma fada,  darajarki ta zarta ta sadaka kuma nidin ma ba sanki ne banayi ba just ina tsoron azabar ubangiji in na kasa adalci amma ki bari.........., " 



SULAIMAN!  Ya tsinci muryar Mimi ta kirashi wanda shiyayi dalilin katse masa maganarsa.  Yakai idonsa kanta tana tsaye jikin bene wanda ke nuna alamar sakkowatta kenen hannunta riqe da qarfen benen na silver,  idonta waje kamar xai fado xai iya cewa bai tabajin Mimi ta kira sunansa ba kai tsaye sai yau. Don haka yayi gaggawar janye Hanifa daga jikinsa, amma yana xaune ya kasa motsi kamar an dasashi a gurin.




A nata bangaren Mimi bata dade da barin falon ba taje sama tayi wanka saboda azabar zafin da ake  tayi sallar azahar ta sakko kenan ta tarar da wannan aikin mijinta rungume da wata mace acikin gidansu na aure wannan al amari yayi matukar kidimata.




Ta qaraso kusa da inda suke xaune cikin bacin rai idonta rufe ta fara nunashi tana magana "sulaiman?  Abunda kake kenan?  Yau Allah ya tauna maka asiri don wulaqanci duk abunda kuke a office bai isheku ba sai kun biyo ni har cikin gidan aurena"  yayi saurin tashi ya riqeta  ganin ta horonce musu,  ta fusgeta daga riqon ya kuma kamata nan take suka fara kokawa tana cewa karya tabata da hannunsa me dattin zina.  





Dakyar ya kama qugunta ya riqe tsam dole ta dakata da kokawar,  yace cikin rudewa "maryam me mukeyi a offfice din?  Kardai zargina kike?" ta tareshi cikin masifa da hayagaga tace "zina kukeyi mana, kukayi acikin gidana ma bare a office wanda babu mai ganinku sai Allah" ta fincike jikinta daga nasa cikin tsabar masifa,  ganin inbai cikata ba zaiwa Dan cikinta illah yasa ya cikata,  ta nufi kusa da Hanifa dake tsaye tana kallon yadda Mimi ke casa sulaiman ta fara magana. 



"ke kuma karya qazama taxi no garage sabida tsabar rashin class karuwancin naki har gida kikebin maza a memakon ki bari yaje kungi,  banxa jaka barauniyar miji"  wannan zagi yayiwa Hanifa ciwo kwarai wai yau ita ake kira da karuwa.  Takai ido kan cikin jikin Mimi tabbas badon karta daki Mimi ta ballowa kanta tashin hankalu ba da wlh rufeta xatai da duka sai dai duk abunda xa ai ayi amma tasan yanxu inta daketa xata iya janyo mata bari, Itama cikin tata masifar ta tasowa Mimi "ke ni kike kira karuwa do.......," 





Bature yayi saurin tareta "ke ya isa haka da Allah kar kicemun komai inba haka ba in saba miki wlh"  ya juya ga Mimi dake huci kamar ta rufesu da duka shi da Hanifa haqiqa hankalinsa ya tashi don baisan haka Mimi take ba.  Ya qara riqota yana cewa "maryam don Allah kiyi haquri karki....... " bai kai qarshe ba ta fusge tace "kai sulaiman karka kuskura ka qara kai hannunka jikina don ni ba qazama bace irinka kuma ka s..... " ya hade bakinsa da nata   ba tare data qarasa ba,  tsotsarta yake kamar xai maidata cikinsa sai da ya tabbatar ta gama xuwa hannu kana ya cire bakinsa ta koma jikinsa yabar ta kwanta yana ganin haka ya dagata cancakas  yayi saman bene da ita. 




Hanifa tai mutuwar xaune ganin wannan abun, anci mata mutunci xata rama an hanata sannan kuma ya qalailayeta da soyayya sunyi sama lallai wannan yarinya jikinta  da zaqi yake inba haka ba irin wannan rawar jiki da sulaiman yake akanta tayi over.   Ta miqe cikin sanda ta bisu sama don taga qarshen film din. 





Ta samu qofar dakin a bude kamar yadda ta xata don shauqi ya hanasu rufewa bayan haka kuma shi ke dauke da ita a hannunsa don haka bashi da damar rufewa. Dake gadon saitin qofa yake kallo acan ta hangosu   kwance yana kwada mata wata irin soyayya, ta runtse ido da sauri ta nufi qasa tana dana sanin wannan gani da tayi musu. 




Ta dauki jakarta ta fice gidan da sauri tana kuka kala biyu,  na farkô Kukan cin mutuncin da Mimi tai mata na biyu kuma kukan ganin da tai musu a halin auratayya wato Mimi bayan cin mutuncin da tai mata aka hanata ramawa har saka mata yayi da tsadaddiyar soyayya? 



Su kuma a nasu bangaren sai bayan angama kashe arna sannan Mimi ta fara masa bore da kuka hadi da bugunsa wai ya cuceta ya shafa mata dirty.  Ya samu ya riqeta jikinsa yace "maryam na rantse da wanda raina yake hannunsa ban taba zina ba,  akanki na fara sanin ya mace, tabbas bani da mafita tunda kin ganni da Hanifa cikin wani hali amma wlh yaune farko kuma shima din lallashinta nake wlh ba abunda kike nufi bane ki bari inyi wanka in dauko miki qur ani in rantse" ta toshe masa baki tace "na yarda ya Bature basai ka rantse da littafin Allah ba, amma dan Allah kar ka kuma kawomin ita gidana"  ya tsuguna gabanta yace "in shaa Allah shine farko kuma qarshe"  



Yayi saurin canja topic don Mimi yau ta bashi tsoro yace "amma in anjima xamu kuma yi ko?" ta hade rai tace "fatana Allah yasa wannan jaraba taka karta xubar da cikin" ya matsota yace "waya fada miki?  Kefa sokuwa ce ai kwari zai kuma yi kuma sannan baxaki sha wahalar labour ba in kinxo haihuwa" tsakaninta da Allah ta yadda tace masa "haba?" yace "yes my luv, kedai kawai kita bani ina rage miki aiki" tace "to ya Bature kamar kuwa kasan ana fadar wahalar haihuwa" ya gyada kai a ransa yace yaro  dai yarone, yaro man 🐓.Ya
 dagata suka shiga toilet.



A daren Hanifa kusan kwana tayi tana kuka don abun sosai ya taba zuciyarta.  Koda gari ya waye batai niyyar xuwa aiki ba don mugun haushin sulaiman takeji ga kishin ganinsa a shinfida da Mimi. 



Can tsakiyar rana xaman kadaici ya isheta ta fito falo,  tayi breakfast ta tambayi yan aikin gidan ummanta,  sukace ta fice tun safe.   A daddafe tai wanka ta tsira doguwar riga idonta yayi luhu luhu kanta kuwa kamar ya fashe sabida kukan data sha.



Gidan gwaggoriya ta nufa,  tana xuwa ta samu gidan cike kamar koyaushe anata shelele,  batare da tace komai ba ta shige bedroom din gwaggoriya ta kwanta kan gado,  ganin Hanifa burkice yasa gwaggoriya ta sallami abokan shashancinta ta shiga dakin. 



Ta yiwa Hanifa tambaya takai sau shida amma Hanifa ko kallonta bataiba tana kwance idonta kan rufin dakin,  dole data gaji tai shiru tana kallon Hanifa da tunanin meya sameta haka?    



Dan kanta ta tashi zaune bayan wani lokaci ta riqo hannun gwaggoriya tace "inada wata matsala ne a rayuwata bayan sulaiman?" sai hawaye wani na korar wani.  Gwaggoriya ta qura mata ido cikin tausayi ganin yadda take kuka harda shashsheqa ita dai tanason Hanifa kuma batason take sawa kanta son sulaiman over don sunsha yawo a kansa da kashe kudi gurin bokaye.  



Tace cikin tausayi "ya isa fadamun meya faru" Hanifa ta koro mata duk yacce akai jiya a gidan sulaiman din.  Gwaggoriya tace "lallai wannan yarinya ta cimiki mutunci kuma wlh sai tayi danasani don lokacin dena kukanki yayi Hanifa, ki share hawayenki don dama ko bakixo ba xanje gurinki. Wata malama muka samu aikinta kamar yankan wuqa" cak Hanifa ta tsaya da kukanta tace "malama ko malami?" "malama macece" gwaggoriya ta amsa mata, Hanifa ta yatsina fuska tace "abunda maxa suka kasa shine xanje gurin mace? Allah ya kiyaye" gwaggoriya tace "kefa banxa ne Hani,  wlh ta iya aiki kusan 2wks kenan da naje gurinta taimun aiki akan wata matar qusan gwamnati da nakeson a hadamu,  tana bajemun aiki saiga matar har gidannan taxo nemana. Abunda yasa ban fada miki lbrinta ba bari nayi taimun aiki inga kalar bajintarta don banaso kiyi ta kashe kudin ki abanxa, amma tunda naga buqatata ta biye kece wacce na fara ayyana xan kai mata"  Hanifa badan ta gamsu ba tace "to yaushe xamuje?"  tace "yanxu xan watsa ruwa muje ai ba a bori da sanyin jiki"  gwaggoriya ta tashi ta shirya a gurguje tace da Hanifa "akwai kudi a gurinki?" Hanifan tace "ko babu sai incire a ATM"  suka fita suka hau motar Hanifa suka tafi. 





Suna tafiya Hanifa ta kasa haquri tace "anya kuwa gwaggoriya ba fasawa xanyi ba?  Jikina yana ban kawai yar 419 ce ba malama ba" gwaggoriya tai saurin bige mata baki da cewa "yimun shiru, indai kasa shakku akan aikinta ba yaci." 




Suka isa unguwar can bayan gari babu mutane sosai,  kuma gidane dan matsakaici maana ba kyau babu muni.  Basu tarar da kowa ba sai wata a tsakar gida alamar maid ce,  ta gaishesu tace "tana ciki uwar gidan" suka shiga. 



Hanifa tai mamaki, sabanin malaman tsibbu data saba gani wannan fes take ga falo da kayan alatu dai dai irin namu na talaka,  tana xaune kan kujera da wani murtukeken carbi tana taunar cingam. 




Ta washe baki tana musu maraba alamar tasan gwaggoriya,  suka gaisheta,  kallo daya xakai mata kasan yar duniya ce ajin qarshe don alamu sun nuna ada can antaba bariki.   



Gwaggoriya ta gabatar da Hanifa a matsayin qawarta sannan tai mata bayaninta tun farko har xuwa jiya akan sulaiman.  Matar ta saita madubinta na tsafi saitin Hanifa,  ta fara kallon cikin mudubin.  Ita kuma Hanifa gabanta kamar xai fado duk da ba yau ta fara ziyartar irin wannan wurin ba amma yau ta rasa dalili duk a tsorace take.   




Tafi minti 5 tana canjawa madubin gurin xama tare da kallon cikinsa kuma duk inda ta juyashi saita sashi saitin Hanifa.   Ta gama naxarinta ta dago ta dubesu ta fara magana "kinsha wahalar bin malamai akansa amma haqarki bata cimma ruwa ba,  duk wadanda kike bi suna iya qoqarinsu suyi miki aiki amma sai dai kash! Basa duba taurarin da suka dace da aikin"  Hanifa da gwaggoriya suka dubi juna a tare,  tacigaba da cewa "Duk da matarsa na yawan bata miki shiri da addua amma da anbi aikin bisa tsarin taurarinsa da tuni ankai gaci"  Hanifa tai saurin tarar da cewa "yanxu meye abunyi ki taimakeni don Allah" ta dagawa Hanifa hannu alamar ta dakata sannan tace "ba a katseni in ina jawabi don nima fadomun ake ina fada" Hanifa ta qunshe bakinta tayi gum. 





Uwar gida taci gaba "inbaki kawar da matarsa ba baxaki taba nasara a kansa ba don ko kinyi aiki xata bata miki, kuma shidin ma ai akwai aikinki a jikinsa don yana da raayi a kanki amma baxai tasiri ba sai kin kauda ita. Gashi kinyi dace akwai abunda ya dauke mata hankali daga yawan addua yanxu ,bayan haka ma baxamu wahala sosai ba wajen aiki akanta don acikin makusantanta akwai wanda ke aikin rabasu ita da shi."  tai shiru alamar ta gama magana,  Hanifa cikin imani da abunda akace tace "to yanxu ya kike ganin xa ai?" gwaggoriya kuma cewa tai "kawai a kasheta sannan ayi masa aiki ki shiga gidan kamar yadda tayi masa"  





Uwargida ta kuma haska Hanifa da mudubinta wacce duk lokacin da akayi hakan Hanifa sai gabanta ya fadi. Tace "Sam ba  asiri tai masa ya aureta ba kuma bata asiri,  kawai hadine na soyayya." ta dubi Hanifa tace "kina da zabi guda biyu, na farko kodai a nakasata ta hanyar illata wata gaba jikinta,  ko kuma a haukatata.  Wannan sone kawai abunda xa a iya yi mata bayan haka babu damar raba aurensu ko kuma rabata da duniya"  Hanifa ta kalli gwaggoriya cikin neman shawarar abunda ya kamata ayi.  


Uwargida ta kuma kallon Hanifa tace "tana da ciki ko?" Hanifa taimata kallon mamaki, lallai aikin matarnan data raina xaici tunda harta gano cikin dake jikin Mimi. Uwargida ta katse mata tunani da cewa "inkina tunin akwai ko babu fa aiki baxai ba, don dole sai ansan matsayinta xa ai aikin" cikin imani da matar Hanifa tace "tabbas tana da ciki amma qarami ne" 
Uwargida ta miqe ta fita waje ba tare da magana ba.  Hanifa da gwaggoriya suka rikice da sambatun ingancin aikinta, Hanifa cewa take "wlh ji nake kamar na auri sulaiman, maryam kuwa in shaa Allah saita xama abar bawa sadaka akan titi wai ni ta kira da karuwa hmmm" tai kwafa.  




Dawowar uwargida tasa sukai tsit,  ta shigo dauke da wata mage qatuwa baqa wuluk ta akwantar da ita a gabanta.  Ta kallesu tace "ki qaddara wannan maryam ce a xuciyar ki, sannan wannan mage tana dauke da ciki a jikinta kamar yadda maryam ke dauke dashi.  Yanxu ki qaddara gaki ga maryam kuma kidau fansar abunda tai miki  amma fa banda kisa"  ta miqawa Hanifa wani qaton dutsen wuta,  tace wannan dashi xaki amfani ki daki duk inda kikeson ya nakasa jikin ta.  


Hanifa cikin tsananin farin cikin son daukar fansar cin mutuncin da Mimi tai mata da kuma baqaqen maganganun da har yanxu takejin sautinsu a kunnenta ta daga dutsen wutar ta bugawa magen dake kwance a gabanta a qafarta.  Magen ta saki kukanta da qarfi "miyau"  ta kuma dagawa xata kwada mata a daya qafar gwaggoriya ta tsaidata,  "Hanifa me kikeyi haka kenan?" cikin farinciki Hanifa tace "gurguntata xanyi shegiya naga da qafar da xata dunga tafiya tana kada wannan qugun kinga kona aureshi ta gurgunce nice keda gida ko?" 





Cikin takaici gwaggoriya tace "Dan bura ubanki ke wace irin jaka ce? duk wannan wahalar da mukasha a iya gurguntata xaki tsaya?  Dagawa xaki ki daketa aka ta haukace ta shiga duniya ta haife cikin acan, kina aurensa gida ya xama naki keda yayan da xaki haifa ita kuma bai ganta ba balle abunda ta haifa suqare ita da Dan akan titi cikin hauka"  




Uwargida ta kalli gwaggoriya cikin jinjinawa da baqar xuciyarta tace "gaskiya Hajiya kin iya mugunta 😂"  Hanifa cikin sauri tabi shawarar gwaggoriya ta daga qaton dutsen iya qarfinta ta bugawa magen akanta  cikin rashin tausayi da imani, dakin ya gauraye da kukan magen cikin azabar da akai mata.  Tanata birgima a gurin kunenta na zubar da jini,  kimanin 17 minutes tana abu daya kwanin tausayi kana ta tashi dakyar tana dingisa qafa tana janta tai waje da gudu tana ihu.  





Bayan fitar magen matar ta dubesu tana dariyar mugunta tace "aiki ya cika yadda wannan magen tayi haka xataita ciwo kafin daga baya ta shiga duniya a matsayin mahaukaciya me dauke da ciki.  Kowane lokaci daga yanxu labarin haukacrwarta xai iya xo muku" 





Hanifa ta kalli gwaggoriya bakinta yaqi rufuwa "qawata nagode da wannan shawara kinga ai duk san da yake mata ai baxai xauna da mahaukaciya ba ko?"  gwaggoriya tace "inma xai xauna da ita ina xai ganta tashiga duniya?"  sukai dariya cikin farinciki harda tafawa.  


Hanifa ta maida kallonta kan uwargida tace "shi kuma me xa ai masa hankalinsa ya dawo kaina?"  uwargida tace "babu komai, ai na fada miki da aikinki har yanxu a jikinsa itace ta hana aikin tasiri sabida taurarinta da nasa in sun hadu aikin asiri baxai tasiri ba, amma tunda kin kauda ita yanxu komai xai tafi dai dai.  Maryam dai anshiga duniya sai dai uwarta ta haifi wata"  




Kudi sosai ta cajesu akan aikin,  babu wani jimami Hanifa ta biya suka tafi suna mata godia ita ma tanai musu.   Suka hau mota suna hirar haukan Mimi suna dariya harda tafawa.  Hanifa tana cewa xataso ganin Mimi a halin hauka ta fada mata cewa itace tai mata aiken a matsayin ramakon biki.  Gwaggoriya tana tuqi tace "shegiya illah biyu kikai mata kin gurguntata kin haukatata" suka kwashe da dariya suka tafa.  Kamar bazasu mútuba anbasu tabbacin zasuyi jiran duniya.  Ta kai gwaggoriya har gida sukai sallama ta koma gida ta fara ramuwar baccin da batayi ba jiya.  




Allah ya kiyashemu tabewa (amiiiinnn)  



Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)


📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 5⃣8⃣



Kwana uku a tsakani, tana zaune da yammaci ita kadai sai yan aikin gidan wadanda suka kammala aikinsu suke tayata hira kamar yadda suka saba. Amma yau abun babu armashi domin uwar dakin nasu yau bata da walwala ko kadan,  duk da ba hade rai tayi ba amma abun nasu babu armashi don basu saba ganin haka a gurinta ba.  Sun maida hankalinsu kan kallon TV,  yayin da ita kuma ta xuba tagumi tana tunani.



A haka ya dawo ya taddasu, suka dunga yimasa sannu da xuwa suna fita. Ya xauna kusa da ita,  ga mamakinsa bata kulashi ba ko nuna tasan yana gurin a tunaninsa bata lura da xuwansa ba saboda zurfin tunani. Ya kira sunanta "Mimi"  ta tago ta kalleshi na yan seconds kana ta maida taguminta,  babu sannu da xuwa,  babu drinks din data saba kawo masa inya dawo,  babu rage masa kayan jikinsa balle aje ga hada masa ruwan wanka. 



Ya tashi ya nufi kitchen,  aransa yana tunani.  Ada can yasha ji ana cewa Mimi miskilace ta gaske amma bai dau abun da  wani mahimmanci ba balle da suka xauna yaga kyawawan halayenta,  amma yanxu kam yaga illar wannan muskilancin.  Yau kwana uku kenan tana masa halin ko in kula ko kuma yace tana gaba dashi, domin bata tanka masa kuma inyayi mata magana iyakacin amsarta eh ko a a duk da cewa na yau yafi tsanani.  




Ya dakko ruwa yasha kana ya dakko lemo ya xuba a cup ya nufo falo,  yasha rabi kana ya rage mata kamar yadda ya saba duk sanda yasha ruwa ko wani abun saiya bata ragowarsa tasha.  Ya nufi bakinta da cup din,  ta bude tashanye lemon tas ya ajiye cup din.  Xaman jugum jugum ya biyo baya,  ya gaji ya tashi da jakarsa ya nufi bedroom.  A fili yace "Sam baxan yadda da wannan hali ba maryam, ai wannan ya zarce muskilanci ya koma mugun hali" bai fito ba sai magrib yayi wanka da shirin masallaci,  ya wuceta a falo tana zaune inda ya barta. 




Sai bayan isha ya dawo, yayi mugun mamaki daya sameta  inda ya barta ko xama bata gyara ba.  Cikin tsoronta yake a halin yanxu da hanxari ya taho gunta baice komaiba ya dagata yayi ciki da ita,  ya cire rigar jikinsa yaje bathroom ya hada mata ruwan zafi ya dauketa yaje yana mata wanka, kallonta yake cikin mamakin halin data tsiro dashi.  Ya gama yayi mata brush da alwala kana suka fito.  Lotion  ya shafa mata iya hannye da qafa,  ya dakko mata doguwar shadda light yellow me laushi ta saka. Yasa mata dadduma da hijab ta kawo sallar magrib da isha tana idarwa ta miqe ta cire  hijab din babu addu'a balle shaf'i wal wutir.  Idonsa akanta, gashin kanta butsu butsu  atsefe yake kuma tayi kusan kwana uku bata kwanceshi ta tajeba, ribbon din duk ya sakwarkwace.  




Ya tako inda take tsaye ya kama hannayenta ya riqe yana kallon fuskarta, ta sunkuyar da kanta yajata sukai falo kan dinning ya xuba musu abinci a plate daya yace mata "maxa muci maryam" ta fara juya spoon ba tare data kai abincin bakinta ba. Ya qura mata ido cikin tausayin halin data saka kanta aciki,  duk da babu kwalliya ko dis a fuskar amma ta masa kyau gashinta ya barbaxo gaban fuskarta ta rame kadan sabida damuwar data saka kanta ciki.  Ya matso kusa da ita har kafadarsu na gugar juna ya dafa dan qaramin cikinta daya fito das ta cikin rigar yace "maryam daure kici abinci ko dan danmu dake cikin ki" ta dibi kadan ta kai bakinta daganan bata kuma ci ba.   Shima ya dakata dacin nasa ya riqo hannunta duk biyun cikin nasa yana murxawa yace "maryam Dan Allah menayi miki kike irin wannan fushi haka babu ji babu gani?"  tai shiru babu amsa  yagaji da jiran cewarta ya kuma cewa "Dan Allah in akan Hanifa ne kiyi haquri,  na tuba Mimi na, na baki haquri kuma tun a lokacin kin nuna kin haqura amma yanxu kin tsiro da fushi muna cikin xamanmu me dadi.  Maryam kiyi haquri mu xauna lfy yan watanni muke da aure be dace ace haka ta fara bullowa tsakaninmu ba"  har yanxu shiru batai magana  ba,  ya dakkota ya dorata kan cinyarsa yana shafa cikinta yana cewa "Baby na ka tayani bawa mamanka haquri,  nayi missing dinku sosai. Mimi tunda kika tsiro da wannan hali naki duk gidan babu dadi har maids dinki basa walwala Mimi duk sun damu da halin da kike ciki,  fadamun duk abunda kikeso inyi miki ki daina wannan fushin my luv"   tai rau rau cikin muryar kuka tace "ni gidan ya Taheer nakeso naje" ya shafa kanta yana murmushi yace "wannan shiyafi komai sauqi my luv tashi muje"  ya dakko mata siririn gyale ta rufe kanta suka tafi.  




A qafa suke tafiyar tunda kusa suke tsiran maifi gidaje 5 ba,   yana riqe da hannunta har cikin babban falo.  Sun taddasu zaune kan dinning da kidz dinsu suna dinner,   har gurin suka isa aka gaggaisa kana suka hadu gaba daya suna cin abinci.  Mimi dai bata saki jikinta ba kamar yadda yake xato kuma batacin tuwon shinkafar dake gabanta,  yadan dubeta yace "maryam ci abinci mana"  Anty Rabi ta dora da fada mata ta dunga cin abinci sosai sabida abunda ke cikinta don xata iya jigata kuma ta jigatashi in batacin abinci sosai.  Ganin sunyi mata caaa yasa taci loma uku dakyar duk kuwa da son tuwo da take da kuma uwar yinwar dake sakadarta. Ya Taheer baice komaiba amma yana kallonta cikin nazari. 




Har goman dare suna gidan suna hira, ita kuma hakimar tana kan kujera a lafe bata samusu baki a cikin hirar amma fuskarta ta dan saki ba kamar daxu ba da suka shigo.  Bature ya gaji kwarai so yake yaje ya kwanta sannan ya lallashi miminsa da kalaman soyayya su shirya don yagaji da wannan quncin nata.  





Ya fara gyangyadi da hammar qarya duk don ya Taheer yace su tafi dare yayi,  amma yaji yayi shiru sai zaqulo wata hirar yake.  Ya qara wata hammar yace "Mimi taso mu tafi nagaji so nake in kwanta"  tanajin haka ta koma kan kujerar da ya Taheer yake ta riqeshi tana kuka tace "ni baxan koma ba, nidai kabarni anan babu inda xanje" yayi sototo yana  kallonta cikin tsananin mamaki ya yabawa makircin mace kwarai da gaske wato Mimi wayo tai masa ta shinfida masa gadar xare ta yaudareshi ya kawota gidan ya Taheer sannan ta nuna musu cutarta yake wato dai a fakaice qararsa ta kawo kenan?  Ya danne duk wani bacin ran data haddasa masa ya kuma cewa "haba mana Mimi luv kefa kikace inkawo ki kuma nabi umarninki na kawoki sai kuma kiqi komawa?  Daure ki taso mu tafi da safe xan dawo dake in xanje aiki."  



Ta kuma shigewa jikin Taheer tace "wlh bazan bika ba, ka tafi kabarni, banason wannan gidan baxan koma ba."




Ya Taheer ya dago daka kallon Mimi dake jikinsa ya maida kallonsa ga Bature dake tsaye. Ya fara harar Bature, ya dafa kan Mimi yana kallon Bature yace "sulaiman yanxu wannan yarinyar kake cuta? Wannan salihar baiwar kake zalunta?  Tun daga shigowarku naga yanayinta nasan akwai abunda ke damunta,  amma ka bani kunya,  ban zaci haka daga gareka ba.  Aurenku da yan kwanaki har ka sako matsala cikin xamanku?  Dama ka auretane don raba zumuncin iyayenku mata?  Kasan matsala acikin aurenku na nufin matsala ga family dinmu gaba daya?" 




Anty Rabi ta dubi Bature dake tsaye yana sauraran fadan Taheer kana ta maida kallonta ga Mimi wacce ke kwance kafadar Taheer din tana kuka wurjanjan.  Ta matso kusa da ya Taheer tace "Abban sayyeed kabar fadan haka,  lamarin aure ba a bawa mutum daya laifi,  ka bawa Bature dama ya kare kansa mana" ya tareta da cewa "sulaiman shine babba sabida haka dole yayi haquri da maryam, kuma tunda kikaji ta dau matakin qin komawa gidansa abun babba ne."  




Bature ya hadiye yawu dakyar yace "ya Taheer kayi haquri na karbi lefina  in shaa Allah baxan kuma ba" jin haka jikin Taheer yayi sanyi ya dan yimusu nasiha da yin haquri a xaman aure kana yace "maryam tashi ku tafi Kinji ki dunga haquri da mijinki"  duk da bata da taurin kai sunyi mamaki lokacin data noqe wuya, alamar baxata bishi ba.  




Anty Rabi tajata daki don tambayarta meyayi mata haka wanda ya hanata komawa,  amma juyin duniya Mimi taqi magana qarshe ma tasa kuka.  Ganin haka ta fito falon ta samesu Taheer na qara yimasa fada. Mimi ta nemi guri ta kuma xama,  Taheer ya matso gabanta cikin lallashi yace "maryam yi haquri ku tafi, gobe in nadawo aiki xanxo har gida ki fadamun abunda yayi miki, amma kafin nan ina nemar masa afuwa ki tashi ku koma"  





Ta dubi ya Taheer bata da niyyar tashi ta saka kuka.  Bature xuwa yanxu ransa ya gama baci da rainin hankalinta ya matsa kusa da ita ya riqo kafadarta ya fara magana .





"maryam karki raina mana hankali kinji,  waye sa'anki anan?  Ki fada mana abunda nayi miki kinqi, maryam sai yanxu xaki tsiro iskancin baxaki xauna dani ba?  Sai da kikaga baxan iya rayuwa me dadi ba inbabu ke?  Sai da kikaga farin cikin mahaifanmu ya ta'allaqa akan Dan dake cikinki?  Meyasa kikeson duk saka wadannan mutane cikin baqin ciki?  To wallahil azim in bacci kike ki farka, baxan sakeki ba koda bakya sona dole ki xauna dani, aurenmu mutu ka raba." 




Kalamansa suka sakata saka sabon kuka,  shima hawaye yake.  Ya Taheer da Anty Rabi kuma tuni suka koma bayansu suna kallon wannan almara.



Bature ya miqar da ita tsaye ya fara jan hannunta yana cewa "taho mu tafi ko in sabeki in maidake dan dole,  muguwa wacce batasan soyayyar gaskiya ba sai yaudara, wacce  batasan farin cikin kowa ba sai nata" 



Yayi gaba yana janye da hannunta ita kuma tana turjewa, taku daya, biyu,  ana uku ta yanke jiki ta fadi wanwar.  Sukayo  kanta da gudu suna jijjigata da fadar sunanta,  shi kuwa Bature na tsaye yana kallonta yasan Mimi pretending tayi don karta bishi.  




Suna aikin jijjigata a gigice tana kwance sanbal shi kuma ya na tsaye hannu a aljihu yana kallonsu.  A zuciyarsa ya raya bari yayi maganinta,  yanufi kitchen ya bude freezer ya dakko ruwa me sanyi har ya fara qanqara ya nufi falon.  Yasan dai ko suman gaske tayi ya xuba mata wannan ruwan zata farko balle pretending. 




Yana xuwa ya bude ruwan daga tsaye ya fara tsiyaya matashi a fuska,   sai dai har ya kusa juye mata goran ruwan Faro ko yatsanta be motsa ba.  Ya Taheer ya daka masa tsawa da cewa "sulaiman!  Kai mahaukacine da xaka dunga xuba mata wannan ruwan me sanyi? Baka ganin halin da take ciki ne?" yayi saurin yarda gorar ruwan don ya fara tsorata. 




Ya fara kuka yana jijjigata da fadar sunanta yana cewa "maryam ki taimakeni ki tashi,  maryam karki mutu ki barni,  ki tashi maryam xan barki anan gidan tunda nan kikeson xama baxan qara tilasa miki xaman gidana ba.  Ki tashi Mimi luv ya Baturenki baxai jure rashinki ba" jijjigata yake iya qarfinsa, amma ko gixau bata motsa ba tana yadda take.  




Ya miqe ya dauketa a hanzarce ya fita da gudu ko takalmk be tsaya sakawa ba,  su ya Taheer suma suka rufa masa baya. 




Gidan ishaq ya nufa da ita,  suna xaune shi da Farida wacce ta fara bacci akan cinyarsa suka ga Bature a kansu dauke da Mimi, baice komai ba ya shimfideta a gabansu kamar gawa,  su ya Taheer suka shigo suma a gigice.  




Maganar Bature ta katseshi inda yake cewa "ishaq,  maryam ce,  ka temakamun ishaq xan rasa maryam ka temakamun"  ishaq a gigice ya fara duba tsintsiyar hannun Mimi,  kana ya kai kunnansa saitin xuciyarta yaji tabbas tana bugawa amma ba yacce ya kamata ba.  Ya dubi Farida wacce maganar Bature ta tasheta daga baccin data fara yace "dakko mun jakata ta aiki a ciki" da sauri ta nufi dakin. 




Ya karba ya fara duba Mimi cikin kwarewa,  yasa hannu ya dunga danna qirjinta da qarfi har xuwa wani lokaci kana ya dakko drip yayi wata allura aciki ya jona mata ruwan.  Ya dago ya kallesu a tsaye cirko cirko duk sunyi zuffa kamar yacce shima ya hada gumi sharkaf kamar babu sanyin AC.  Yace "shikenan doguwar suma tayi, wanda firgici ya haddasa mata amma yanxu mun shawo kan abun.  Yanxu haka bacci take na mata allurar bacci ruwan kuma sabida jikinta babu abinci yayi weak shiyasa na saka mata." 




Bature ya matsa kusa da Mimi dake kan doguwar kujera kwance, shi bai yadda bacci take ba gani yake ta mutu.  Ya kara hannunsa a qasan hancinta yaji fitar numfashinta sannan ya yarda da maganar ishaq ya saki ajiyar xuciya.  




Su ya Taheer suka matso suka dubata suma kana suka tafi, lokacin har har sha biyu tayi. Ya matsa ya daga kanta ya dora akan cinyarsa yana shafa gashinta don babu dankwali akanta.  




Farida kuma ta shige jikin ishaq ita kuma kukan halin da Mimi ke ciki take, yayin da ishaq yake lallabata da cewa mimin bacci take sabida allurar da yayi mata amma ba a sume take ba kamar yadda Faridan ke zato. 




Bature yana hurawa Mimi iskar bakinsa a fuskarta ya labarta musu abunda ya faruwa, sunyi mamaki kwarai sunanan zaune jigum jigum har ruwan ya qare.




Bature yayi niyyar komawa da Mimi gida amma sai ya tuna cewa maganar komawarta gidan yasata suma karya dauketa ya kaita ta farka tayi masa bore gashi babu mataumaki kusa,  ya kalli Ishaq yace "inaga xan barta anan xuwa safe don karta farka tayi rigima"  ishaq yace "hakan yafi don karma ta farko da wata matsalar kuma bana kusa" yace da shi "dakkota ku shiga daki Kaima ka kwanta don duk ka jigata"  



Farida ta shiga bedroom din dake kusa da nasu ta shimfida musu sabon bed sheet ta kunna AC.  Shi kuma ya dakko Mimi ya shigo da ita ya kwantar,  ishaq ya qara dubata yaga babu matsala bacci dai take sannan sukai sallama suka fita.  Yaje ya dauro alwala yayi musu addua ya tofesu shi da ita yajata jikinsa ya rungumeta a hankali bacci yayi gaba dashi, amma yanayi yana farkawa yanaganin halin da take ciki.




Kiran sallar farko ta farka kamar yadda ta saba, ta ganshi  kwance a kusa da ita,  ta miqe ta kunna wutar dakin lamarin da yasa ya tashi yayi saurin xuwa inda take ya kamota jikinsa yana tambayarta ya jikin nata. 





Ta tureshi daga jikinta tace "nace banason gidan nan amma ka dawo dani ko?  Na tsani gidan kaima na tsaneka" ya toshe mata baki yace "Mimi tsakiyar dare ne yanxu kiyi magana a hankali,  kuma wlh ba gidan na maidake ba gidan su ishaq ne nan" ta cire hannunsa daga bakinta direct tace "karya kake nan gidanka ne,  don me xakaimun haka?  Don me xaka kaini inda banaso?"  





Jikinsa yayi mugun sanyi wai yau Mimi kecewa yana karya ido cikin ido kuma tace ta tsaneshi.  Ya dakko pic din Farida da ishaq dake kan bed side ya nuna mata tare da cewa "kinga pic dinsu ma,  wlh gidan farida kike"  suna wannan daru Farida da ishaq wadanda hargagin Mimi ya tashesu suka shigo dakin. Ganinsu yasa ta yadda cewa ba gidanta takeba sannan ta haqura ta dena masifar.




Ya temaka mata tayi alwala kafin a kira assalatu sukai raka atanil fajr,  ya barta da Farida suka wuce masallacin asuba shida ishaq.   Tayi sallar asuba babu batun azkar ta miqe ta kwanta Farida na kallonta tana hawaye,  wai Mimi ce ta xama haka daga jiya xuwa yau. A iya saninta da ita inta idar da sallar asuba takan xarce da azkar kana ta dora karatun qur'ani bata komawa bacci sai bakwai da rabi xuwa takwas na safe,  amma dake Dan adam ba bakin komai yake ba yau Mimi ce ke sallah kamar wata farin shigar shiga addini.  A cikin sujjadar qarshe ta sallah tana kuka tana roqon Allah ya yayewa maryam wannan baqon lamari daya tunkarota.  





Bature daga masallacin asuba gidansa ya zarce yaje yayi wanka yayi shirinsa na fita kayane kawai bai saka ba, ya saka wando 3 qt da t shirt ya dibarwa Mimi kayanta set biyu da brush da undis kana ya daukar mata wayarta da sosan wanka da mayunkanta da turare  ya xuba a qaramar trolley don yaga abun nata nayi ne baisan ranar qarewar wannan hijira tata ba.




Shigarsa gidan ishaq ya sameta  tana baccinta sosai,  lokacin har 7:00 AM tayi.  Ya matsa kusa da ita ya shafa fuskarta cike da soyayyarta da kuma tausayi,  yakai bakinsa ya sumbaci kuncinta da lebenta.  Ta bude ido tana kallonsa,  ya mata murmushi ya tadata zaune ta jingina da allon gadon yace "morning my luv" ta qura masa ido ba tare data amsa ba,  ganin xai makara a office yace "tashi muje in muki wanka" ta miqe ya ciro towel ya miqa mata,  ta kalleshi da alamar batasan abunda xatai dashi ba.  A hankali yace mata "cire kayanki ki daura"  ta cire kayan ta daura kamar yace ta daura suka shiga bathroom. 




Brush ma daya miqa mata sai da ya fada mata ta wanke baki sannan ta fara wankewa,  don ya kwadata yace mata "to yi wankan mana maryam"  tayi shiru tana kallon kwamin wankan daya cika da ruwan dumi da sabulai can ta kalleshi tace "ya akeyi?" gabansa ya yanke ya fadi,  me wannan abun ke nufi wai?  Mimi loosing memory tayi ko me?  



Ya dauketa ya sakata cikin bahon wanka ya fara yimata,  a xuciyarsa tunani yake wannan wace irin lalura ce ta samu Mimi haka siddan anya abun bai shafi brain dinta ba.  




Tas ya sullube abarsa ya nadota a towel ya dakkota xuwa cikin daki,  suna tafe tana kallon fuskarsa kamar yadda ta saba inyayi mata irin wannan daukar.   Ya ajiyeta akan gado ya tsane ruwan jikinta ya shafa mata mai,  yasa mata undis da body spray, ya saka mata doguwar riga don riga da zani baxai saku a gurinta ba yanxu tunda komai sai anmata.   Yasa dankwalin rigar ya daure mata kanta yasa mata powder harda jan baki.  Ya kalleta tayi kyau sosai don kwana biyunnnan bata kwalliya,  ya kama kafadunta yana nuna mata kwalliyar da yayi mata cikin mirrow,  ta danyi murmushi har dimple dinta ya motsa.  Farin ciki ya rufeshi don ya kwan biyu bega hakan ba,  ya ayyana maryam a matsayin farincikinsa don dan murmushin da tayi yanxu kawai ya samu raguwar abunda ke damunsa a xuciyarsa. 





Cikin kwarin gwiwa ya riqe hannunta suka fita falo,  ishaq da Farida na dinning tana hada masa breakfast yanaci yayi shirin fita.  Sukai joining dinsu,  farida ta gaisheta da tambayarta jiki, ishaq ma haka.  Farida ce ta hadawa Bature tea ta xuba masa farfeson kan sa ta tura masa kana ta hadawa Mimi itama.  Yaci abincin sosai don yunwa yakeji, ya kalli Mimi dake gefe batako taba abincin ba,  ya dakko ragowar tea dinsa ya bata a baki ta shaye ya kuma qara mata da nata.  Farfesun ma yanaci yana bata da cokali,  a xuciyarsa yana tunanin kardai Mimi abinci ma sai an nuna mata yadda xataci ko anbata?.  Yace mata "dauki ruwa kisha magani" ya fada yana xuba mata maganin da ishaq ya bashi yanxu a tafin hannunta,   babu musu tasha maganin.  






Ya saki ajiyar xuciya tare da godewa Allah don abun nata da sauki tunda duk abunda akace tayi tanayi babu musu,   ya riqo hannunta yasaka mata wayarta yace "Mimi xan tafi office Kinji" ta daga kai ba tare da magana ba.  





Ya kalli Farida yace "Farida kiyi haquri xan bar Mimi anan muga xuwa wani lokaci ko xata dawo dai dai,  Dan Allah ki kula da ita karta xauna da yunwa in lokacin sallah yayi a nuna mata yadda xatai kuma abata abinci."  Farida tace "haba sulaiman ka kwantar da hankalinka, Mimi kamar a gida take ko shekara xanyi ina kula da ita in shaa Allah baxan gaji ba xan kula da Mimi kamar yadda xan kula da kaina don nasan da ni wannan lalurar ta samu sai yadda qarfinta ya qare"  yaji dadin kalamanta yayi mata godiya yace bari yaje ya taho da Aisha ta dunga temaka mata ganin itama faridan ga ciki jikinta.  Tace "daka barta ma ai ma aikatan gidannan ma sun isa kuma nidin bana aikin komai sai muyi xaman ko Mimi?" ta fada tana dafa kafadar Mimi.   





Yace "to bari inje in dawo"  acan gidan ya tara ma aikatan kaf yayi musu bayanin madam babu lfy kuma tana gidan ishaq qarqashin kulawarsa ya buqaci Aisha ta shirya ta koma can ta taya Farida hidimar Mimi.  Nan take wasu suka fara kuka,  gaskiya mana kwana biyu take musu fiskar shanu,  ya kallesu cikin soyayya don sun burgeshi a dalilin son me kyautata musu,  yace "ba kuka xakuyi ba just kuyi mata addau ita tafi buqata"  suka rude dayi mata adduar samun lfy, yana amsawa. Grace tana kuka tace "intaje church ran sunday xatayiwa madam special prayer" yayi mata godiya.  




A gaggauce yasa kayansa na fita sannan ya fito da jakarsa a hannu yana gyara tie din wuyansa,  ya tarar da Aisha ta shirya suka fita xuwa gidan ishaq.  




Ya kai Aisha sannan yayiwa Mimi sallama yace "Mimi luv na tafi office"  ya sunkuya dai dai fuskarta ya sumbaci lips dinta ya fita.




A office ya kasa nutsuwa kusan duk after 1 hour saiya kira Farida ya tambayi jikin Mimi ta kuma bashi tabbacin tana lfy.  





Suma a gidan yini sukayi suna debe mata kewa,  sunata hira amma banda ita, sai dai in anyi abun dariya takanyi murmushi.  In lokacin sallah yayi sukan nuna mata yadda xatai alwala, in sukace tai sallah tana tambayarsu guda nawa xatayi lamarin dake saka Farida xubar da hawaye.  
Abinci ma taci sosai sabida Farida hada musu tayi. 



Lokacin tashi yanayi yayo gida,  yayi farin cikin yadda ya sameta ta sake sosai suna kallo a falo tayi wanka ta sake Kaya. Ya qarasa yanawa Farida hannu da gida da kuma gajiyar kula da Mimi.  Mimi tana ta kallonsa batare da magana ba,  ya jata jikinsa yana tambayarta yata yini?  Batai magana ba amma ta lafe a jikinsa. 




Da magrib suka fita masallaci da ishaq suna hirar ciwon Mimi,  ishaq na fada cewa xafin zazzafi kansa irin wannan matsalar amma a barta takwan biyu aga yadda jikin xaiyi.  Bayan idar da sallah ya fadawa imam din masallacin cewar matarsa babu lfy asata a addua.  




A gurin dinner ma yanaci yana bata a baki har sukaci suka qoshi. Yauma kamar jiya anan gidan suka kwana kuma yau sunyi bacci sosai da taimakon addua da maganin baccin da ishaq ya bata.  




****** ******* ****** ****

Kwananta 3 a gidan ta sake sosai,  duk da bata walwala bata kuma magana saiya xama dole amma dai abun da sauqi.  Bature ya gane matsalar Mimi dai gidansane kawai bataso,  duk da yaso kaita asibiti sabida taga likitan kwalkwalwa amma ishaq yana yawan fada masa cewa koda ya kaita babu abunda xasuyi mata a halin yanxu saboda ciki. Aisha na yawan tofa mata addu'o'i a ruwa da kuma ayatushshifa dake Aisha yarinyace nutsatstsiya me ilimin addini xafin talaucine ya korota yawan aikatau.  Wanda adduoin Aisha su suka kawo Mimi wannan sauqin. 




A ranar dai data cika kwana ukun a gidan da yamma ya dawo office ya shigo gidan kamar yadda ya saba,  ya samu ishaq a gida sabida yau fitar dare zaiyi a aiki wato "call up duty" suna zaune shida Farida kan kujera daya, yayin da Mimi da Aisha ke kan carpet Aisha na matsa mata qafarta suna kallo.  Yana shigowa ta taso da hanzari da nufoshi,  ya dakata da tafiyar da yake yana kallonta tana sanye da atamfa dinkin riga da skirt sunyi caras jikinta fuskarta tayi tas saboda kitson da Farida tasa yar aikinta hanne tai mata daxu ganin jikinta da sauqi. 





Tana xuwa ta shige jikinsa tare da cewa "ya Bature na" ya yar da jakarsa ta aiki ya dagata ya rungumeta kamar yadda yake in zai rungumeta sabida ya fita tsaho.  Lamarin daya bawa su Farida mamaki,  sun dade a tsaye rungume da juna kafin ya ajiyeta yana kallonta. 



A gurin suka zube ta qura masa ido cikin shauqi tace "ya Bature i miss u" ya amsa yana qara shigewa jikinta yace "i miss u too Mimi luv"  ta qara kallonsa tace "tashi mu tafi gida ya Bature" ya kalli sashin dasu Farida ke xaune suna kallonsu yace "na fada muku ishaq, Mimi bata cikin hayyacinta a wancan lokacin shiyasa ta furta bata sona batason gidana amma yanxu data dawo dai dai gashi da kanta ta buqaci mu koma" ya daga hannu yana cewa "Alhamdulillah,  Allah nagode maka daka kawo mana qarshen wannan abu Allah kada ka maimaita mana" 




Ya juyo ya hada bakinsa da nata ya fará kissing dinta ko kunyar su ishaq da Aisha dake gurin bayaji. Dakyar ta banbareshi a jikinta,  ya kalleta cikin burgewa yace "maryam taso mu koma gidanmu mucigaba da soyayyarmu mai dadi,  taso Mimi luv mutafi ni da gidana munyi missing dinki da kulawarki."  




Ta miqe tana rumgume gefen jikinsa ta juya tanawa su Farida waving suka fice.  Sai Aisha ce ta tsaya ta dakko mata wayarta da kayanta na gidan.  





Farida ta kalli ishaq tana jinjina wannan lamari tace SULAIMAN da MARYAM tsakaninsu sai Allah. Allah ka kare wadannan bayi naka daga sharrin maqiya don suna qaunar junansu. 




Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)


📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 5⃣9⃣



Tana sa qafarta a cikin gidan taji duk duniya tai mata zafi amma ta cije sabida taga yana cikin farin ciki bataso ta bata masa mood dinsa.  Akan kujera ya xaunarta ya shige ciki ya rage kayan jikinsa ya fito kitchen,  dakko wannan dakko wancan haka ya dunga hidima da ita kamar wata baquwa, ita kuma tana binsa da murmushin yaqe. 




Yan aikin suka dunga shigowa suna gaisheta dayi mata hannu da jiki, yana murmushi yana amsa adduoin su har aka kira magrib ya fita. 




Sai bayan isha ya dawo, yaji dadi kwarai daya sameta akan pray mat tayi sallah. Ya wuce bathroom ya hada musu ruwan wanka yazo ya kwasheta sukayi tare,  suka shirya cikin kayan bacci iri daya masu sauqin nauyi.  Har cikin daki ya kawo musu abinci yanaci yana bata don taqi saka hannu,  suka gama ya kwashe kayan suka koma bandaki suka kurkure baki da lestirine suka dan zauna har xuwa 9:30pm suna kallo a TV din dake bedroom din.  



Mimi dai ba kallon take ba,  hankalinta a mugun tashe yake don inuwar dodon photo kawai take gani cikin TV din,  bayan haka kuma sai gilmawar mutane take gani ta saitin window din dakin. 


 
Anasa bangaren shima yanajin bacci,  amma ya dan dakata ne abincin da sukaci ya narke kafin su kwanta. 



Dataga abun bana qare bane saita ce masa "ya Bature nikam xan kwanta"  ya dubeta yana naxartar da take ciki yace "to Mimi luv" ya tashi don rakata  bandaki amma ita ta kasa miqewa,  ya lura yace "ya dai Mimi?" ta cije baki tace "qafatace ta dan riqe na kasa miqewa" ya dagata ya kaita, tayi fitsari yace tayi alwala, ta danso tirjewa amma ya tilasa mata tayi.  Kana yazo ya kwantar da ita.



Ya kwashe kayan kallon,  ya kimtsa komai shima ya dauro alwalar kana yaxo ya kwanta gefenta yana karanto azkar din kwanciya bacci ya tofesu shi da ita ya jata jikinsa yana mata wasanni. 




Tayi luf kamar mai bacci, amma bashi take ba runtse ido tayi sabida gane ganen da take.  Ta fara samun saqonsa na soyayya,  tun tana daurewa har ta kasa ta fara yunqurin kwatar jikinta.  Tace "ya Bature ka ajiye wannan rayuwar a gefe don Allah,  nidin banason gidannan yanxu daurewa nake kuma ni kadai nasan abunda nake gani, kuma nakeji a jikina,  kaga inkace xaka tsiro da wannan abun xafin xaimun yawa xaka xalunceni." 



Jikinsa yayi sanyi da kalamanta amma shima yanayin da yake ciki ya qazanta da zai iya haqurin da yayi sabida haka yace "maryam ni kuma haqqina xaki shiga wlh,  da ace xan iya haqura dana haqura amma na miki alqawari baxan dadeba ina samun nutsuwa xan kyaleki." 




Badan ranta yaso ba abun yacigaba,  yanayi tana tureshi kamar yau ya fara kusantarta,  haka dai badan yaje inda yakeson xuwa ba koya samu nutsuwar ya haqura dan taqi barinsa yayi yadda yakeso dondaima jarabace irin ta namiji da haqurin yafi. 




Ya tashi yaje yayi wanka don baya kwana da janaba,  tana kallonsa yaxo ya dauketa itama ya mata.  A halin yanxu abunda take gani ya qazanta har mace take gani tana yafitota da hannu. Ta runtse idonta daga kallon matar, ga qafarta ta isheta da xugi kuma abun takaici ta kasa furta kalmar tsari ko guda daya.  



Ya jawota qirjinsa yana shafa bayanta har yayi bacci,  itakam tafi 2 hours bata samu bacci ba sai daga baya wani bacci cike da qaxaman mafarkai ya kwasheta.





Yau ya rigata tashi sabanin da da ita ke tadashi,  ya janyeta jikinsa ya kwantar da ita akan filo yayi toilet don dauro alwala.  Gabansa yayi wata irin muguwar faduwa lokacin daya hangi jini face face a gaban rigarsa ta bacci.   Ya koma dakin da gudu ya murgino Mimi daga kwanciyar da take ya fara  cajeta yana neman daga inda jinin ya fito jikinta don yasan shidai ba ajikinsa ya fito ba itace kwance akan qirjinsa. 




Hasken bed side lamp yayi masa kadan, ya kunna wutar dakin haske tanyar abunda ya tashi Mimi kenan.  Yana duba duk jikinta ita kuma tana kallonsa a firgice don ta rasa dalilin hakan. Can ta hangi jini malele a gaban rigarsa takai hannu ta taba,  da danshi a gurin lamarin dake nuna jinin bai dade da xuba ba. Ta gigice sosai tace "ya Bature jinin meye wannan jikinka, ciwo kaji?"  yace "maryam ba daga jikina jinin yake ba a jikinki ne tayani dubawa" sunata duba jikinta ya hango bushashshan jini gefen kunnanta.  Ya kamata ya riqe yana tambayarta kunenta na ciwo ne?  Tace "babu abunda kemin ciwo sai qafata"  da kyar ya tafi masallaci ya barta ita da Aisha.  Ana idar da sallah ko adduar da akeyi bai tsaya ba yayo gida,  a gaggauce ya shiryata suka tafi asibiti. 





Dake ishaq ya kwana akan aiki basu sha wahala ba aka hadasu da sashin kunne,  sukai iya dube dubensu babu komai suka bata magani kana sukaje bangaren yan qashi sabida qafar dakyar take takata tana dingishi,  suma nan xray akai take aka cire photon consultant yazo wajen qarfe tara ya rubuta report babu komai a qashin qafar sunfi xaton ciwon qafar masu cikine ta fara tun yanxu,  suka rubuta mata man ciwon qashi me zafi "volini"  aka sallamesu sukayo gida. 




Sai wajen goman safe ya tafi aiki bayan ya kai Mimi gurin Farida kuma ishaq yana gida ko wani abun zai taso.




Safna daga gurin aiki gidan Farida ta wuto dan sai yau tasamu labarin Mimi babu lfy ta bakin mijinta abokin Baturen. Suka hadu suna hira tare da sako Mimi aciki amma batasa baki sai dai tai murmushi.  Safna ta karbi maganin ciwon qafar ta mulkawa Mimi shi tun daga cinya xuwa tafin qafar.  Anty Rabi ma nan ta taho suka hadu har bayan laasar suna tare lokacin kuma Bature ya shigo gidan, yaji dadin yadda ya samesu sun sata tsakiya sunata lallabata. Suka gaisa sannan safna ta buqaci ganinsa suka kebe. 




Tace "ya Bature anya wannan ciwo na Mimi baxa a sanar dasu mumy ba?  Yadda na ganta da kuma kukan ciwon qafar da bayanin Anty Rabi abun ya tsoratani kuma fa bata magana anya ba ciwon iska bane"  ya watsawa safna daquwa hade da harara yace "to bakinki qanin qafarki, innaji xancen nan yaje kano sai nayi mugun saba miki,  matsalace qarama kuma munje asibiti akanta anbata magani an tabbatar babu komai sannan kuma ai mun isa kulawa da ita basai anje kano ba kinsan mumy tanaji xatace a dawo da ita gida kuma ni gaskiya ina buqatar matata kusa dani,  kuma karki kuma cewa ciwon aljanu ni matata mata da iska. Kedai kawai abunda nakeso dake ki dunga shigowa inkin dawo aiki kina ganin jikinta aimun isa kula da ita, gaki ga ya Taheer gasu ishaq" safna ta jinjina kai dan taga idon ya Bature ya rufe da tsananin son maryam, shi kawai burinsa xamanta kusa dashi kar a rabasu amma inba haka ba kowa yaga maryam yasan ciwonta na iskane.  Tace "to shikenan xan dunga shigowa in shaa Allah amma dai ya Bature a hada da addua kuma xansa ayi mata sauka" yace "yawwa safna karki bari mumy taji ko Faty" tace "to"




Yasaka Mimi agaba suka koma gidansu. Kamar jira ake ta shiga qafar ta rikice da wani irin azabar ciwo, ta xube a dai dai kofar shiga falo don tsaiwa ma ta gagara.  Ta dubeshi tace "ya Bature xan mutu qafata" ya sunkuya ya shafa qafar kana ya ciccibeta yana cewa "sry Mimi luv xata dena tunda ansaka magani. 




A kan gado direta ya shiga wanka,  ta runtse ido ta rasa abunda yake mata dadi tayi mugun tsanar gidan ga wata faduwar gaba dake addabarta.  Ta dunga jiyo wata murya tana kwallah mata kira a gigice,  tun tana sharewa har kiran ya fara yawa ta miqe dakyar tana dingishi ga gumi tanayi sabida azabar ciwon qafa ta nufi kofa don ganin me kiranta,  Allah ya saka dai dai lokacin ya fito wankan.









Ya isa gurinta da sauri yana cewa "maryam ina xaki haka?" ta cije lebenta na qasa cikin azabar ciwo tace"kirana ake tun daxu bakaji ba?"  ta fada tana nuna masa saitin qofa.  Ya kalli gurin data nuna yace "ni banji komai ba Mimi, kunnenki ne kawaia" tasa kuka tana cewa "wlh kirana ake kuma mamace ke kirana don muryarta naji"  a tsorace ya dubeta yace "mama kuma? Mexai kawo mama nan da yammanan?"  dakyar da sudin goshi yajata suka koma suka xauna.  Ya dorata cinyarsa yana qara shafa mata maganin hadi da lallashinta yace "maryam kiyi haquri nasan ni na haddasa miki ciwonnnan,  sai da kikace bakyaso na kusanceki amma nabi son xuciyata. Nasan dana haqura da kinanan qalau dake,  ya marairaice  ya riqe hannunta yana furta i m sry Mimi luv,  plz forgive me na biyu kenan in shaa Allah baxanyi na uku ba "binsa take da ido bata fuskantar maganarsa ita kawai burinta ya saketa taje kiran da ake mata don har yanxu kiranta ake kuma da muryar mama.  





Da yaga bata hayyacinta sai yaqi fita masallaci a gida yayi sallar sukai jam i tare,  sukaci abinci ya bata magungunanta tasha xuwa taran dare suka kwanta. Yauma dai kamar jiya gane gane ta dungayi kafin bacci ya dauketa mara dadi da munanan mafarkai,  kuma ya tashi da jini fiye dana jiya a jikinsa wanda yau yaga inda jinin ke diga ta kunnen Mimi data kwanta donyin bacci.  Wajen 2"30 AM ya tashi yaga tana birgima a qasa tana hawaye,  a razane ya taho gurinta yana tambayarta lfy?  Ta nuna masa qafarta yakai hannu zai taba tasaki wata gigitacciyar qara da sauri ya janye hannunsa.  Ya taba jikinta xafi rau.  



Ya dauki towel da ruwan sanyi ya dunga goge mata jikin ya shafa mata maganin ciwon qafa kana ya bata paracetamol tasha ta kwanta,  yayi sa azazzabin ya sauka kuma ta samu bacci.  Amma shi kam idonsa kyam a kanta tana sharar bacci akan cinyarsa.  




Ya xubawa jinin dake diga daga kunnenta ido,  diga yake babu tsayawa yayin da Mimi ke bacci. Wani irin tausayin yarinyar yarufeshi yana hawaye yana tunani wannan wane irin ciwone?  Ai sai jininta ya qare wace irin lalurace ta samu Mimi haka ga ciki a jikinta? Kodai laulayin ciki ne yaxo mata da haka?  Yana kallonta gami da kuka da tunani har garin Allah ya waye tangararau bai sallah ba.  Danma yau saturday babu office saida Mimi ta tashi daga baccin kana ya shima ya tashi donyin sallah.  Xuwa wannan lokacin jinin daya xuba jikinta bashi da iyaka,  dan wandon jikinsa ya jiqe sosai har bed sheet ya baci.  




Ya dunga tambayarta ya jikinta ina ke mata ciwo kanta na ciwo?  Ta bashi tabbacin babu inda ke mata ciwo sai qafarta wadda yanxu bata iya yakawa sai dai ya dauketa duk inda xataje. 

*******   ******* ********


Yan kwanakin da suka biyo baya AL' AMARIN MARYAM ya qazanta sosai,  kamar jira ake ta dawo gidan matsaloli sukai chaaaa.  Xubar jini daga kunne har sun saba da hakan tunda yanxu hartakai inxasu kwanta sai ansaka zani sabida zubar jinin. Abunda suka fuskanta duk sanda Mimi ta kwanta danyin bacci xubar jinin xatace salamu alaikum domin baya dena xuba saita tashi, duk da cewa baccin ba me dadi take ba. 



Qafarta ta kunbura tayi suntum har kyalli take kamar a tabata ta fashe,  Mimi dai yanxu bata tafiya sai dai a turata a well chair.   




Ciwo yayi tsanani bata um bata um um sai dai komai ayi mata. Kuma duk abunda akace tayi yi take babu musu, babban tashin hankalinsa batacin abinci saiya takura mata ko kuma asaka mata drip.  





Shi da ishaq Kullum suna yawan asibiti ana aunata amma antabbatar lfyarta lau daga qafar har kunne babu problem.  Sai dai Kullum ana bata maganin qarin jini sabida xubar jinin da kuma maganin bacci.  



Kwana take kukan ciwon qafa da kuma ita ya barta taje kiran mama,  wai ita a lallai mama ke kiranta.  Ta fige ta lalace sosai. 



Yasha fadawa ishaq cewa indai cikine yasa Mimi wannan abun to shikam a cire cikin domin xai iya xama da Mimi ko bata haihuwa ba. Ishaq na yawan kwantar masa da hankali cewa, babu ruwan ciki lalura ce kawai Allah ya saukar mata, amma cikinta lfy qalau yake.  Abun dai gwanin tausayi dan sun daina ta cikin balle a aunashi ko bashi kulawa,  kawai ta lfyar Mimi suke. 




Xuwa yanxu yan aikin gidan sun gama fuskantar matsalar madam din tasu,  suna xuwa dubata kuma kowa yana mata adduar data dace da addininsa.  Baqo ya sami Bature da xancen ciwon Mimi bana asibiti bane yana ganin aljanu ke shafarta.  Bature ya balbale Baqo da fada kamar ya dakeshi yana cewa "karya qara kirawa matarsa aljanu,  shi matarsa bata da aljanu laulayin ciki take in kuma ya kuma cewa tana da iska to a bakin aikinsa." ya sunkuyar da kai yana bashi haquri,  a xuciyarsa kuma yayi masa uxuri domin shi kansa Baturen ya xama kamar wani zararre. 



Baba me gadinsu yaxo har daki duba Mimi wani yamma daya jiwo ihunta akan ciwon qafar,  ya dunga kallonta cikin tausayawa.  Ya kwantar da halshe da hikima irinta manya yace da Bature "Alhaji inaga yarinyar nan kamar akwai sammu acikin lamarinta, dan da ace ciwon asibitine xuwa wannan lokaci da ko bata samu lfy gaba daya ba yaci ace ta samu saukin wani abun."  Bature ya dubeshi yayi shiru,  Baba mai gadi ya dora da cewa "duk wanda yayiwa wannan yarinyar mugun abu yacika marar imani,  wannan yarinya meta sani in banda kyauta tawa wadanda suke tare?   Lallai duniya taxo qarshe indai har xa a Jefe irinsu haj maryam" Bature ya tsaidashi cikin gaxa sauraran maganganunsa,  darajar furfurarsa ya gyaleshi donshi ya tsani ace ciwon Mimi bana asibiti bane.  Yace "Baba addua kawai xakai mata Allah ya yaye mata"  Baba yace "xan temaka alh dan shine hanyar da xan nunawa madam alherin da tayi mana kenan,  xan dunga bada tofi ana kawo mata Kullum tasha a shafa mata a qafar" Bature yace "to angode Baba"  ya fita daga falon,  shi kuma ya sauke ajiyar xuciya dan dama ya matsu yabar gurin dan ya shafawa Mimi maganinta na ciwon qafar.  Ya matsa kusa da Wll chair din ya taba kafadarta,  ta dago idonta da suka kuma fitowa sabida ramar da tayi tana kallonsa.  Yace "sannu maryam, Allah ya yaye miki ya mayar kaffara ya tashi kafadarki" tace "ya Bature na gurgunce ko?" ya sumbaci bakinta yace "maryam ko da qafa ko babu qafa ina sonki a haka,  ki daina maganar gurguncewa kinji" tace "to,  amma yaushe mama xataxo?  Banaso in mutu ban nemi yafiyarta ba" yace "maryam baxaki mutu yanxu ba in shaa Allah, sai kin haife wannan cikin na jikinki kin shayarmun da Dana nononki yayi koyi da kyawawan halayenki"  tai shiru tana kallonsa kawai,  yaci gaba da yimata hira me dadi tana murmushi. 





Haka rayuwa tacigaba, Mimi ciwo shi kuma damuwa,  sau tari a office sai yayi aiki ya tura gaba sai a dawo masa dashi ace da gyara duk kuwa da kwarewa irin tasa.  Sai ya xauna ya gyara ko mr Alex yasa a gyara,  sarai yasan abunda ke damun sulaiman matsalar ciwon matarsa ne,  yana tausayinsa kuma yana yawan kwantar masa da hankali cewa xata warke da xarar ta haihu.  Kuma yaje har gida duba Mimi shi da family dinsa.   Anata bangaren Hanifa tasan matsalar sulaiman sarai don sunsan Mimi babu lfy ta hanyar wacce suke bawa kudi take musu bincike akan Mimi din.  Ta damu kwarai da damuwar da sulaiman ke ciki don duk ya bushe ya xama wani soko danma dan gayu ne me tsafta.   Tana labewa tai kukanta ta share hawaye don tasan ciwon Mimi ne silar wannan hali da yake ciki kuma ita tana kukane don sulaiman amma badan halin da suka jefa Mimi ciki ba.  Yanxu ta tabbatar sulaiman ba qaramin so yakewa Mimi ba tunda har ya shiga wannan yanayin a dalilin cutarta kawai ina ga tashiga duniya da sunan hauka?  Anya shima baxai haukace ba kuwa?  Bataso ciwon Mimi ya tsaya anan ba don tasan uwargida cewa tai musu hauka xatai kamar yadda magennan tayi amma kash ya akai abun ya tsaya iya ciwon qafa kawai?  Lallai Mimi nada qarfin jini,  amma baxatai gajen haquri ba Kullum tana kasa kunne taji yar rahotanta taxo mata da labarin haukacewar Mimi tasan a lokacin dole inyayi haukansa na wucin gadi ya haqura sannan hankalinsa ya dawo kanta,  a lokacin xasu faracin duniyarsu da tsinke. 

   wannan shine tunanin Hanifa a Kullum.



Ya Taheer ya samu Bature da xancen kodai xa a fadawa iyayensu halin da Mimi ke ciki. Sulaiman ya futttuke ya dunga fada shifa a kyale masa matarsa ciwonta ba wani seroius bane just laulayin ciki ne,  kuma suna addua suna xuwa asibiti kuma ya saka ana mata sauka Kullum a masallaci.  Ya Taheer ya dunga kallon yadda sulaiman ke masa masifa kamar ada can ba girmamawa ce tsakaninsu ba,  lallai ciwon maryam dab yake da saka SULAIMAN hauka.  Ala dole ya haqura domin bayan ya gama fadan sai kuma ya dawo lallashi da roqon Taheer din karya bari mutan kano suji, a cewarsa in sukaji xasu karbe maryam shikuma bazai iya rabuwa da itaba a halin yanxu don in yarabu da ita yaci amanar soyayyar da sukewa juna,  bayan haka kuma besan son Mimi ya masa mummunan kamu ba sai yanxu da take cikin lalura.  Ya Taheer ya haqura, haqiqa suna cikin jarraba yana mugun tausayawa yan qannan nasa sulaiman da maryam. 



Mai gadi ya fara kawo ruwan tofi kamar yadda yayi alqawari, amma Aisha yake bawa domin ya lura ogan nasu bayason irin wadannan abubuwan.  Inya bata ita kuma takan saka pure xuma ta bawa Mimi tasha kuma ta shafe mata qafar dashi. Abun yaxo mata da sauqi don Mimi duk abunda akace tayi yi take babu musu domin brain dinta kamar ta yara ta koma, yaro dan shekara 3 na iya juyata.  




Ayoyin qur anine na karya sihiri da ayyatushshifa yake mata safe da yamma, kuma Aisha kansata agaba taita karanta mata qur ani da ayoyin korar aljanu.  Yarinyar nason Mimi sosai,  ita ke kula da ita da duk wani shaaninta, da ita din barauniyace da tayi arxiqi a wannan tsakanin don itake gyara kayan Mimi haka xataita cin karo da kudi tana bawa Bature.  Amma abunda Mimi tai mata na alkhairi baxai barta ta saka mata da sharri ba. Domin Mimi ce ta biyawa mahaifiyarta kudin aikin ido wanda ta shekara 8 tana fama dashi sabida rashin gata,  sannan ta biyawa Dan uwanta kudin makaranta wanda shima rashin gata yasa ya dena duk kuwa da brain din karatun da Allah ya bashi.  Kana ta kwato mata takardar saki gurin mijinta daya saketa shekaru uku amma yaqi bada takadda sai ta tashi aure yace bai saketa ba, in ta kafe ya saketa yace ina sheda?.  Abun ya dade yana damunta, amma daga haduwarsu da Mimi ta fada mata duk wannan matsalar daya bayan daya ta dunga yi mata maganinsu.  A qarshe ta kai mijin kotu aka rubuta sammaci aka kai masa, dake Dan iskan qaryane yana ganin sammaci ya bada takaddar dan aiken kotu ya dawo da ita.  Abu na qarshe wanda Mimi tai mata kwanaki kadan kafin ta fara ciwo shine : kwato mata yaranta guda 2 mata daga hannun ubansu ta danqawa uwar aishan kana ta bata 50k tace tai jari ta kula da kanta da jikokinta. 





Wannan abu yayi mutuqar farantawa Aisha rai, kunsan uwa da Da sai Allah kuma dama yayan a wuyanta suke,  sannan duk wannan alheri da Mimi tayi batajin ko sulaiman mijinta ya sani ita da aishan kawai suke sirrinsu.  Ita kuwa ya xataiwa wannan baiwar Allah wacce tai matá wannan dinbin alheri butulci?  Wlh tasan inbata sakawa Mimi ba sai Allah ya tambayeta.  Gatan kowa Allah amma Aisha tana kallon Mimi a matsayin itace gatanta kuma babban jigo a rayuwarta,  tanawa Mimi duk hidima a matsayin tanawa yayarta uwa daya uba daya. 



 Farida da su safna,  anty Rabi kusan Kullum nan suke wuni kuma suna yabawa da kulawar Aisha ga Mimi.  




Dake Qur'ani warakane sai gashi a hankali Mimi ta fara samun sauqi,  ta dena digar da jini ta kunne kuma qafar kumburin ya Sabe sosai kadan ya rage sai dai bata takawa.  Rashin maganar nan dai shine matsalar da kuma shirmen cewar mama na kiranta.  




Bature yafi kowa murnar samun wannan sauki, ya kuma dagewa da kaita asibitin a zatonsa maganin asibitine yasa hakan.  Kudi kuwa baisan abunda ya kashe ba Kullum cikin sadaka yake da sakawa ayi sauka Allah ya kawo sauqi.  Kuma a hankali sauqin yana samuwa shima kuma ya fara maida hankali kan aikinsa.  




Ya Taheer Kullum da safe saiya shigo duba Mimi kafin ya fita aiki, kuma ya yaba da saukin da ake cewa ta samu har yaga gaskiyar Bature daya hanasu fadar bata da lfy wa yan kano,  ashe da sun fada da sunyi gaggawa tunda gashi sauqi Kullum samuwa yake.  




Su Farida da safna sun dan rage shigowa kowacce ta samu xama a gidan mijinta a dalilin ganin sauqi ya samu.  Farida sai a lokacin ta fara awon ciki don da bata faraba tunda babu nutsuwa. 




Yammacin asabar liqis tana falo tana kallo da Aisha shi kuma yana cikin dakin batasan me yake ciki ba amma dai ya dade.  Ta miqe tsaye tace da Aisha bara in gwada inga xan iya tafiya?



Aisha tace "a a madam bari inxo in riqeki karki fadi" tayi dan murmushi tace 'barni dai in gwada Aisha komai saida gwaji"  ta fara takawa a hankali Aisha na binta a baya karta fadi,  har qofar shiga bedroom din kana Aisha ta dawo tunda tasan yana ciki. 




Ta shiga ciki a hankali take takawa tana dingishi,  yana cikin bathroom yaji shigowar mutum yace "waye?" tunda yasan bamai shigowa ciki sai Aisha, a iya saninsa kuma Mimi bata tafiya sai an turata a kujera.  Yacigaba da kiran waye?  Amma shiru.  



Kamar a mafarki yaga Mimi a bakin bathroom din yana cewa "maryam kece ko mafarki nake?" ya tsame hannunsa daga cikin kumfar da yake mata wankin undis dinta (pants da bra) ya dauraye ya matso jikinta yace "maryam ke kadai kika shigo?  Lallai sauqi ya samu godia ta tabbata ga Allah." ya kamota ta xauna kan kujerar daya ajiye mata suna dan hira yana wankinsa. 





Ta kalleshi xuciyarta cike da tausayinsa da sonsa tace "ya Bature kai kakemun wankin undis?" ta fada tana kwallah.  Yace "common meye aciki Mimi luv dan nayi miki?  Ada aike kikemun ko?  Yanxu Allah ya kawomu lokaci nima ina miki aiba wani abu bane" ta share hawayenta, yana aikin suna jifan juna da murmushin luv har yagama sukai alwalar magrib suka fito.  




Sosai  sauki ya samu, kowa ya saki jiki don abunda ya rage kawai dawowar walwalarta. 



Ranar monday da wuri ya fita aiki sabida suna da meeting, kuma Mimi tayo masa rakiya har bakin mota da dingishinta sai dayaga ta koma sannan ya shiga suka tafi. 




Batare data xaunaba ta shiga bedroom ta koma bacci,  Aisha tanata aikinta hadi da leqawa taga ko Mimi ta tashi ta kawo mata abinci amma taga bacci take.  Har tagama komai Mimi na bacci,  ta fitowa da mimin kayan da zata saka dan a tsarinta tana tashi take wanka kana ta yi break fast.   Doguwar rigar atamfa mai laushi ta dakko mata,  bataga Dan kwalin rigar ba so saita dakko mata kashka medium irin wanda ake dorawa saman doguwar rigar ta hada mata da atamfar ta ajiye a kusa da Mimi gefen gado.  Kana ta fita gurin kitchen gurin moses inda suke haduwa gaba daya da ragowar ma'aikatan suna ganin yadda yake girki suna hira. 



Dake hausawa sunce baya bata da kadan, Mimi cikin baccinta taji ya Bature na tashinta,  ta farka a firgice ta kalleshi tace "harka dawo?" yace mata "eh" kawai ya zarce dayi mata wasannin soyayya.  Ta xare jikinta don batason wannan harkar sam a halin yanxu tace masa bari nai wanka, ta dingisa ta wuce bathroom.  Tana wanka tana tunanin meya dawo da ya Bature gida yanxu shi da yace mata yau meeting garesu?  Da wannan tunani ta fito wankan, abun mamakin sai ta samu dakin wayam babu kowa,  da sauke ajiyar xuciya a fili tace "dama nasan bazai dawo yanxu ba, May be mafarki nayi"





Ta shafa mai tana saka riga ta hangeshi kwance ta cikin madubi tsirara akan gado, gabanta yayi wata irin faduwa.  Ta juyo taga gurin wayam,  ta kuma kallon madubin ta hangoshi kwance.  Hankalinta yayi wani irin tashi tayi yunqurin ihu amma ta kasa don bakinta ya sarqe. 






Tana cikin wannan haline taga ya dunfarota, ta runtse ido tana so tayi ihu ko addua amma bakin ya rufe gam,  dalilin ihunta kuwa ganin wannan mutumin mai nufota tsirara da nufin sex da ita al'aurarsa har qasa take wato takai gwiwarsa kuma wai sex xeyi da ita.  A fuskarsa dai kamannin mijinta sak, amma tasan mijinta bashi da wannan mummunar Al aurar. Allah ya temaketa ta yunqura ta miqe tare da xarar mayafinta tai waje da gudu.  Tafiya take tana waige amma ga mamakinta binta yake tsirara yana dariya. 




Ta nufi gate dake brain din irinta yarace wai saita nufi office din su Bature a nufinta taje taga shine wanda ke binta koba shi bane.  Me gadi ya bude mata gate yana cewa 'sannu madam jiki yayi kyau, gidan alh ishaq xaki leqa kenan?" ta fita ba tare data tankashiba sabida hankalinta yayi gaba. 




Ta tari napep a layin ta fada masa yakaita Company din NNPC. Ya fara tafiya da sauri don yaga alamar sauri take don suna tafiya tana waige.  Ita kuma anata bangaren ya Bature take gani har yanxu yana binta kuma tsirara yana dariya ga mamakinta kuma sauri yake har yana wuce ababen hawan dake gudu kan titin. 




Yana ajiyeta ta shige cikin ma aikatar da gudu, yana cewa hajia kudin bata saurareshi ba ita kawai burinta ta gujewa wannan dake binta kuma taje office din ya Bature taga shine koba shiba. 





Sai dai abunda yayi mata cikas bata San office din nasa ba tunda bata taba xuwa ba,  dan haka ta nufi babbbab hall din da suke meeeting inda ta hango jamian tsaro jibge gurin suna gadi.  




Ta nemi shiga suka hanata tare da tambayar wacece ita,  ta dunga nuna musu mutumin dake binta tare da ce musu gurin mijinta xata.  Sukace ta tafi tabasu guri su basuga kowa ba,  daya daga ciki yace "su kyaleta da alamar mahaukaciya ce"  




Suna ta dauki ba dadi tsakaninsu da ita, su sun hanata shiga, ita kuma ta kafe saita shiga sabida wanine ke binta. 





Daga cikin dakin meeting din suka farajin hayaniya tayi yawa,  mr Alex ya tura Hanifa taje taga meke faruwa.  Ta miqe dan cika umarninsa 





Duk da tanada masaniyar abunda ke going amma sai datayi mamakin ganin Mimi anan tana fada da sojojin.  Direct tace "ku barta ta wuce matar Eng SULAIMAN A AZEEZ ce,  tana da tabin hankali"  ta bawa Mimi hanya ta wuce tana wani shu'umin murmushi na cikar buri.  





Tana shiga gurin ta fara cewa "ya Bature!  Ya Bature!!  Kana ina?  Kaxo xai kasheni, ko kaine ka turoshi ya tsoratani?"  Bature kansa sunkuye yana rubutu ya tsinci muryar Mimi tana fadar haka. 






Ya tashi da sauri ya nufeta,  tuni ta fita hayyacinta sai maganganu take wanda rudi yasa baya gane abunda take fada.   Duk gurin yayi shiru ita kawai ake sauraro,  Hanifa na tsaye jikin qofa tana murnar Mimi fa lokaci yayi domin da alama hauka ya kankama. 



Yaje ya riqeta yana girgixata da cewa "Mimi ki dawo cikin hankalinki plz,  waye xai kaaheki?  Meya kawoki nan?" ta dubeshi ta kuma dubi me kama dashi wanda har yanxu take ganinsa yana mata dariya tare da kiranta da "taho Mimi luv nine ya Baturenki" ta dunga kallonsu a tare, ta rasa waye na gaskiyar, take anan kwakwalwarta ta juye ta kwallah qara ta xube qasa sumammiya. 





Wadanda ke gurin suka taso xasu tayashi daukarta, ya tsaidasu da cewa xai iya.  Ya ciccibeta cikin rashin sa a mayafin dake rufe kanta ya xame ya fadi qasa,  tsautsayi yasa ya takashi bai saniba aikuwa satsin tiles dana mayafin ya kwasheshi yayi qasa ya fadi Mimi dake hannunsa kuma ta fadi gefe wanwar kan cikinta.  





Qarar faduwarta da kiran sunanta da yayi a tare suka fito,  beyi ta nasa faduwanba ya nufeta a gigice yana girgixata da fadin "maryam ki tashi, maryam ki taimakeni ki bude ido" duk wanda ke gurin sai da ya tausaya masa ciki kuwa harda Hanifa da itace silar faruwar komai.  





Akayo kansu gaba daya ana masa sannnu cikin sauri ya dakko wayarsa ya kira ya Taheer da ishaq a taqaice ya fada musu abunda ke faruwa. 





Suna tsaye cirko cirko yayin da Bature ke tsugune gaban Mimi da bata motsi yana kuka haiqan ya Taheer ya iso.  Ya dudduba Mimi shima take ya fara hawaye don gani yake Mimi ta mutu.  Isowar ishaq yasa suka tsagaita da kukan,  ya tsuguna ya dinga chaje Mimi, ya dago yace musu tana da rai tabbas.  Ya Taheer cikin hanxari yace "to sulaiman inaga a sada yarinyar nan da iyayenta tunda har abun yakai haka ta fara fitowa." ishaq yace hakane yafi dacewa.  





Bature badan yaso ba ya yadda,  Taheer yace bari yaje ya samo tiket.  Ishaq kuma ya fara bata taimakon gaggawa don numfashinta ya dawo.  





Mr Alex ya matso cikin tausayawa yace "ya bada jet dinsa akaita" Bature yaji dadi sosai sukai godia, nan take ya kira pilot din yazo da jet din,  Aka dora Mimi kan gadon marasa lfy ishaq ya juna mata drip da oxygen Taheer da Bature suka shiga jet din ya daga xuwa kano. 





Meeting din daba a qarasa ba kenan,  akaita jimamin halin da matar Eng sulaiman ke ciki.  




Ishaq be koma asibiti ba gida ya nufa. 



Hanifa kuma gwaggoriya ta kira ta fada mata abunda ya faru cikin farinciki amma bataji dadin tafiya da Mimi kano da akaiba.  Gwaggoriya ta kwantar mata da hankali cewa ai a kano sai tafi nesa da sulaiman don tasan yana kaita zai juyo ya dawo Abuja sabida aikinsa ita kuma acan xata sulale ta gudu ta shiga dawa.  Hankalin Hanifa ya kwanta da jawabin gwaggoriya ta bar damuwa data fita har sadaka tayi murnar aikinta yaci, kuji kwaba yan uwa wai layya da kare. 





Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)


📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 6⃣0⃣




Ishaq yana isa gida ya samu Farida har bed room tana shirin wanka daure da towel.  Babu sallama ya balbaleta da masifar cewa tana ina har Mimi ta fita taje office din sulaiman sabida tsabar shashanci da sakaci irin nata?   



Farida ta tambayeshi cikin rudewa da neman maimaita mata abunda yace Mimi tayi.  Cikin masifa kamar xai daketa ya fada mata duk yadda akai.  



Ya dakata da fadan da yake dai dai lokacin da yaga Farida tayi xaman yan bori tana ihun kukan kiran sunan Mimi dan Allah a temaketa a dawo da mata da Mimi. 



Ai tuni ya dena fadan ya dawo lallashin Farida da fada mata Mimi yanxu an wuce da ita kano kuma xata samu sauqi in shaa Allah.  Shima dai a ranar aiki ya sameshi don farida taqici taqi sha sai kuka da kiran sunan Mimi da kuma cewa lallai saiya kaita kano itama dan gani take Mimi mutuwa tai suke boyewa.  Haka ya yini lallashinta har bayan sallar asr. 




Ya yiwa Baqo waya yace ya tattaro masa duk masu aikin gidan su sameshi anasa gidan. 



Cikin qanqanin lokaci sukaxo suka sameshi,  ya dunga binsu da kallo yana kada qafa, mugun haushinsu yakeji kamar ya tashi ya rufesu da duka.   




Ya fara magana cikin qunar rai "abun takaici ne ace duk yawanku a cikin gida har maryam ta sulale ta fice baku sani ba,  bayan kudin kunsan tana da lalura ba a rufe muku ba" suka rude da jimami da kalaman kare kansu na basusan fitar madam ba. 




Ya daka musu tsawa da cewa suyi masa shiru, sukai tsit suna sauraransa yace "sakamakon abunda sakacinsu ya haifar antafi da maryam kano, dalilin haka ni kuma na koreku aiki gaba dayanku." falon ya cika da koke kokensu,  farida tana zaune tana jinsu batasa baki ba idonta yayi jajur sabida kukan data yini yi. 




Ya daka musu tsawar cewa su bace mai da gani,  suka tashi jiki a sanyaye suka dunga fita Aisha ce kadai ta rage.  Ishaq ya kalleta yace "ke xaman me kike?" ta matso kusa da qafafunsa cikin kuka tace "Dan Allah Alh kayi haquri, wlh lokacin dana bar madam bacci takeyi, sai yanxu da kaxo da lbrin abunda ya faru.  Nidai kasani motar kano yanxu in bita can in tayasu jinyarta badon a bani kudi ba, sai don rama dinbin alkhairin da tayi yimun" ishaq yayi dan jim, Farida ta dafashi "ya ishaq ka kyaleta ita,  amanace sosai tsakaninsu da Mimi"  yace "to shikenan kije xuwa da safe sai inkaiki tasha ki tafi kano dan yanxu dare yayi." 





KANO 

Isarsu direct Aminu kano teaching hospital (AKTH) suka sauka.  Dake abun na manya ne  da gaggawa aka amshesu aka wuce da ita  A&E. Likitocin emergency suka rufu kanta a qoqarin neman numfashinta.  




Ya Taheer shi yayi waya ya sanar da gidajensu halin da ake ciki dan Bature bashi da nutsuwar haka,  duk nacin likitocin da ya fita ya basu gurin suyi aikinsu amma dole suka kyaleshi domin yaqi fita qememe.  





Faty wacce ta zama metro a halin yanxu ta riga kowa isowa don tana cikin asibiti wayar mama ta sameta tana kuka ta fada mata ankawo Mimi yanxu bata da lfy. 




Ta tsaya akan Mimi tana taya likitocin aikinsu,  suma sun qara bawa Mimi kulawa da suka gane sis din metro Faty ce.  Aka bawa Bature takaddar biyan kudin gado da sauran charges din yaje ya biya.  Amma qememe yaqi fita sai ya Taheer ne yaje ya biya aka bata gado. 




Likitocin suka fito dan ansamu komai ya dawo normal amma tana bacci. Lokacin mumy, mama Dady da Baffa sun iso hankalinsu tashe.  Faty ke musu bayanin Mimi ta samu bacci yanxu. 




Suka dunguma dakin hankalinsu tashe yake har yanxu, mumy keta tambayar Taheer wane ciwone wannan farat daya Mimi tai wannan uwar rama kuma har aka kawota gida? 




Sun sami Bature a dakin yana zaune gefen gadon hannunsa riqe hannun Mimi.  Sai da suka xauna suka nutsu kana ya Taheer ya bude musu komai tun farkon ciwon har kawo yau.  




Sukai jugum jugum suna sauraransa,  mumy ta kalli ya Taheer tace "amma Taheer kaci amanarmu a matsayinka na babba a tsakaninsu,  don sulaiman bashi da hankalu kaima baka dashi kenan?  Marainiyar Allah bata da lfy kusan 3wks ku hada baki ku rufe mana?  Nagode kwarai Taheer wlh in maryam ta mutu saina daureku kaida sulaiman" 




Taheer ya gigice yana bawa mumy haquri, bai zaci xata dau abun da zafi haka ba.  




Ta dunga watsawa Bature harara cike da tsanarsa tace "nagode sulaiman kamar nasan abunda xai faru naji hankalina bai kwanta ka tafi da ita ba" ta daka masa tsawa "tashi ka bacemun a gurin"   Bature dai bayajin abunda suke cewa balle yaji tsawar mumy, yacigaba da riqon hannun matarsa.  




Mumy a ganinta rainin hankaline yana jinta, ta tunkareshi Faty tai saurin tsaida ita tana kuka tace "mumy yanxu duk ba wannan ne abunyi ba lfyar Mimi itace agaba,  abunda xai faru ya riga ya faru" dole mumy ta tsaya.  




Mama dai babu baki sai ido takebinsu dashi tana share hawaye. Dady kuma yanata kiran consultants daya sani a asibitin ta cikin wayarsa, yayin da Baffa ke kallon Mimi cikin jimamin jin wai maryam din yanxu ko tafiya batayi. 






Xaman jigum jigum ya biyo baya har xuwa yamma,  Mimi bata farko ba gadai oxgyen an saka mata da wasu manyan ingina.  Sabida alfarmar Dady da Faty manyan likitoci keta zarya akan Mimi,  tuni suka nemi asibitin Abuja aka turo musu duk record din ciwon on-line. 




An turata xuwa dakin xray akai mata brain CT scan (photon kwakwalwa)  photon da yakanyi 1wk kafin ya fito ita sabida gata a cikin 1 hour ya fito consultant a bangaren ya duba yace brain dinta normal take babu komai akanta. 



Adai cikin wunin aka kaita physiotheraphy (bangaren likitan qashi) suma xray din sukai aka tabbatar babu matsala kamar yadda result din ya nuna a Abuja.  



Duk wannan abun da ake Mimi bata sani ba don bata farko ba,  a qarshe aka maidata  Female medical ward, aka bata aminity (wato daki ita kadai)  aka qara mata wasu inginan akanta da hanci sai qafar da suka daddaura wasu manyan qarafuna sukayi hanging din qafar da qarfen saman gadon. 



Dukkansu sun rame a wuni guda kawai,  anyi anyi Bature yaje gida yaci abinci yayi wanka tunda ance Mimi bacci take amma yaqi.  Dady ne ke faman dashi mumy kam babu abunda tace masa tsakaninsu harara in sun hada ido dan mugun haushinsa takeji. 




Magrib tanayi bayan idar da sallah Audu yazo,  shidin ma dawowarsa aiki kenan lbr ya sameshi a gurguje ya kimtsa yaci abinci ya taho.  Ya samu Baffa da Dady sun tafi gida, mumy da mamane kawai a gurin sai Faty daketa zirga zirga. 



Suna gaisawa ya Bature ya dawo daga sallah,  yayi fici fici dashi.  Ya tashi yaje gurinsa suka gaisa yana masa yame jiki bejiba ya koma mazauninsa wato kan gadon Mimi ya riqe hannunta. 





Mama ke masa bayanin tun safe yake haka riqe da ita, anyi anyi dashi yaje gida ya yi wanka yaqi. Yace "mama ke da mumy kuxo muje gida ku kintsa sai ku dawo tunda gani ga ya Bature ga Faty, in yaso inkun dawo saimu koma ku kuma ku kwana da ita.  Suka yarda da shawararsa dan suma din tun safe suke tsaye yakamata suyi wanka suci abinci.  



Ya debesu ya fara kai mama sannan ya kawo mumy gida ya wuce gidansa, yasmin na tambayarsa jikin Mimi yace da sauki kawai.  Ya debi kayansa qanana Set 2 ya fice.  Sai daje eatry yayi siyayyar snack dasu ice cream kana ya sayi fura.  Ya koma store ya sayi soso dasu brush da kayan tea kana ya koma asibitin. 




Yasamu ya Bature yadda ya bashshi Faty kuma ta fita.  Ya rufe dakin  yaje toilet ya hada masa ruwan wanka yakai masa komai sannan ya fito yace "ya Bature dan shiga ka watsa ruwa" baiyi gardama ba Don shima yana buqatar hakan.  





Ya jima a toilet din,  yayi komai har brush, ya fito ya shafa mai da perfumes ya saka kayan da Audu ya kawo masa.  Yaji dadin jikinsa sosai, sai alokacin yaji gajiya  bacci da yunwa sun rufeshi.  Audu ne ya bashi tarkacen kayan da ya siyo, yana hillatarsa da hira yaci sosai ya kuma shanye furar tas.   Faty ta shigo tana musu sannu,  itama sai a lokacin ta samu xama taci abunda Audu ya siyo.  Ta karbi Babynta a hannun me raino wanda yayi kuka har ya gaji ta bashi nono.  Sunata hira ko ince jimami har 10:17 lokacin mumy da mama suka dawo,  mumy dauke da tea flask mama kuma food warmer.  





Suka qara jimantawa juna,  mumy tace Faty ta tafi ita da Audu da Bature su kuma su kwana da Mimi.  Bature qiri qiri yace "nifa babu inda xanje wlh"  mumy ta haushi da xagi tana cewa "Dan ubanka kasan kana santa ka bari ciwo ya ragargajeta haka?" mama ta shiga tsakaninsu  don ita Bature tausayi yake bata.   




Likita da Faty suka kuma shigowa  ya qara duba Mimi yace "bacci take kuma xata iya farkowa koda yaushe,  sannan sunyi magana da wani likitan qashi a Dala zaizo gobe ya dubata shi da wani likitan kwakwalwa inma da yiwuwar a canja mata asibiti xuwa na Dala xa a canja" sukai godia ya fita.   Audu ya dau Faty suka tafi ya kaita gida shima ya wuce nasa gidan. 




Bature kuma ya miqe kan doguwar kujerar dakin ya fara bacci, yayin da mama da mumy sai lokacin suka zauna kan centre carpet din da sukaxo dashi suna cin abinci tare da jimanta ciwon Mimi.  Mama kecewa "nikam Adda da anhaqura da surkudawa Mimi allurai mun koma gida anyi na musulunci don yadda Taheer yayi bayanin ciwonta kamar dasa hannu aciki" mumy tace "nayi wannan tunani fadima amma a bari xuwa goben muga farkowarta"  Bature dake kwance yana sauraransu gabansa yayi wata irin faduwa,  wannan shine abunda yake gudu ace xa aiwa Mimi maganin gida su riqe mai mata da sunan magani.  Wlh kuwa baxai yadda ba ko sama da qasa xata hade, qafarsa qafar Mimi.  Dan haka ya fara motsa kwanjinsa tun yanxu da cewa "mama maryam fa laulayin ciki ne ke damunta kawai,  kuma tun a can munyi magani ta warke yaune abun ya dawo,  munyi magana da wani abokinmu likita acan Germany ishaq na nema mana Visa ana samu xan wuce da ita can ayi duk abunda ya dace inta haihu ma dawo ki..... " mumy ta katseshi da cewa "Dan ubanka munsa da kai cikin maganarmu? Inka kuma saka mana baki saina zabga maka mari,  karka nayi shiru akan abunda kayi kaxaci na haqura ka cuci banxa wlh saina maka hukunci, maryam kuma mu da kai naga wanda yafi iko da ita.  Taqamarka daya dai matarkace ko?  To ni kuma nina haifa na aura maka kuma innaga dama ina iya tsinka igiyar auren in aura mata wani tunda bakai kadai na haifa ba"  jin haka yayi tsit, mama kuma haquri take bata. 





Sun kwanta suna baccin suna farkawa sabida ko Mimi xata tashi.  Qarfe uku dare nayi mama ta tashi ta shiga toilet ta dauro alwala da duqufa kan abun sallah tana nemarwa diyarta sauqi gurin Allah.  Har akai kiran sallar farko shima Bature ya miqe yayo tasa alwalar ya fara nafilfili.  A lokacin ne kuma Mimi ta tashi,  tanata jijjiga gadon abunda ya farkar da mumy ta isa gurinta tana kiranta.  Bature yayi gaggawar sallame sallar a xuciyarsa yace tabbas abunda mutum ya sabayi ko mutuwa xaiyi yana mutuwa akansa, tashin qarfe hudun dare yabi jikin Mimi ko a halin ciwo saita tashi. 





Ya isa gurin Mimi wacce take kiran sunansa bakinta tar tana cewa "ya Bature xai kamani ka ceceni" abun dariya mumy ta hanashi qarasa kusa da Mimi ta shiga tsakaninsu tana cewa "kinga maryam bude idonki ki ganni mumyn ki ce a gida kike cikin kulawarmu babu wanda xai kamaki"  itadai Mimi tunda ta hangi ya Bature ta bayan mumy take miqa masa hannu yaxo gurinta.  Mama dake watching komai ta taso ta kamashi takaishi kusa da Mimi kana mimin tayi shiru tana qara damqe hannunsa kamar bata lura da wanxuwar su mumy a gurinba ko bata ganesu ba. 




Yana shafa kanta dayi mata magana a hankali aka samu ta koma bacci.  




Qarfe bakwai da rabi na safe ta kuma farkawa, lokacin dakin ya cika da yan dubiya kuma hayaniyarsu ce ta tasheta.   Ta kwallah  qarar kiran ya Bature,  hankalinsu ya dawo kanta.  Baffa da Dady suka matsa suna mata sannu,  bata amsa ba ta fara sambatun a cire mata qafarta ta isheta da ciwo.  Ta fincike qarafan da suka saka mata a qafar tana ihu, Faty tai saurin matsawa tana riqeta tare zare mata drip din karta jiwa kanta ciwo. Shigowar Bature tare da Dr yasa tai shiru.




Ya qaraso ya riqeta ya tadata zaune tanata sambatun ciwo,  likitan ya fara aune aunensa tana dukansa da cewa ita ya kyaleta ya Bature ya cire mata qafar tunda yace ko babu qafa zai zauna da ita.  Dr. Yace yana ganin afara kiran likitan kwakwalwa don matsalar brain dinta tafi tsamari yanxu don wannan abun da take shine matakin hauka na farko.  





Kukan mama ya katse musu maganar da suke, inda take kuka tana cewa "wanene haka yayimun wannan aiki?  Wanene ya jefemun yar da ciki a jikinta?  Me maryam ta aikatawa wanda yayi mata wannan abu so ake ta shiga duniya da ciki kome?" Baffa ya taso ya riqeta yana bata haquri,  Mimi sai lokacin ta lura da mama.  




Tace "mama ki yafemun mutuwa xanyi, qafata da kaina ciwo sukemun.  In na haihu a hayyacina koba a hayyacina ba na bar miki abunda na haifa duniya da lahira nasan xaki soshi ki masa tarbiyya yadda kikaimun"  mumy da Faty suka saka kuka a tare.  Likitan yace da Dady a ragu a dakin xaiwa Mimi allurar bacci.  Amma Mimi tace "kar wanda ya fita akyaleta tai sallama da yan uwanta ta nemi yafiyarsu."  lamarin daya saka kowa kuka a dakin. 




Ta kama hannun Bature da Faty ta riqe gam tana hawaye,  Faty ma kukan take, shi kuma Bature idonsa jajur.  Mama ta matso tanawa Mimi adduoi tana tofa mata.  Nan take Mimi ta rikice tana ihu ita batason wannan tofin tana qoqarin dukan mama.  Bature ya tashi ya kama mama yakaita bakin kofa yana cewa "Dan Allah ku kyaleta tunda bataso, ya yarinya bata da lfy xa a xo a kama yimata tofi aka?" su mumy kallonsa suke sororo da alamu ya manta matsayin mama a gurinsa.  Mumy cikin lallashi tace "Bature wannan ya nuna cewa ciwon Mimi iskace tunda batason a tofa mata ayar qur ani" ta kalli Dady tace "inaga Dady mu nemi sallama aje ayi na gida kawai"  Baffa yace "haka ne dai dai Halima"  take anan Bature ya hausu da fada cikin fita hayyaci yace shi babu inda xa akai masa maryam dan visarsu ta kusa fitowa zasuje Germany.  




Dady daya lura dansa baya cikin hayyacinsa sai ya fara lallabashi da cewar ba rabashi xa a yi da Mimi ba just xa a riqetane na wani lokaci tanajin sauki xa a dawo masa da ita. 




Ya fincike hannunsa daga riqon Dady yace "baxan baku itaba, meyasa kuke hakane? Kai rabaka da kai da taka matar? Sama da shekaru arba in kuna tare, sai ni dan mugunta xaku rabamu"  ganin abun nasa ya wuce hankali mumy taxo ta zabga masa mari,  Mimi ta saki wata ajiyar xuciya me kamada shaquwa.  Mumy ta qara kifa masa mari,  a wannan lokacin Mimi watsi tayi da duk wata na urar dake jikinta ta taso ta nufo mumy da nufin hanata dukan Bature.  Sai dai kafin ta qaraso ta fadi qasa.  



Ya riga kowa isa inda take ya dagata ya maidata kan gadon ya kwantar,  tana kuka yana kuka tana shafa kuncinsa inda hannun mumy ya fito rada rada. 




Tana kuka tana cewa "ya Bature karka tafi ka barni gurinsu,  zasu dunga yimun wannan tofin ni banaso xan bika ka kaini asibiti."  



Be daddara ba ya kuma komawa gurin Dady yace "Dady na tuba karku rabani da Mimi yanxu,  she is my wife nd my best friend, nafi kowa iko da ita ku bani abata kota warke ko bata warkeba ina sonta a haka kuma xan kula da ita." 



Dady yana hawayen tausayinsu yace "SULAIMAN haqurin dai xakai, gata ake muku kaida ita." yana jin haka ya juya ya nufi qofar fita.  Ganin haka Mimi ta fara ihu na fitar hankali tana kiran "ya Bature karka tafi ka barni, ya Bature ina sonka  Don Allah karkaimun haka,  bazan iya rayuwa babu kaiba"  tana yunqurun tashi Faty da Audu na riqeta.   Shima Bature yana kuka sharban kamar mace ya bar dakin ko juyowa baiba.  



Babu wanda be xubar musu da hawaye ba,  da kyar Audu ya danneta Faty tai mata allurar bacci.





Cikin minti bakwai bacci ya fara daukarta, suka cikata Faty ta gyara mata kwanciya.  Ta qaraso gurinsu mama tace "mumy anya bamuyi kuskuren raba ya Bature da Mimi ba a wannan gaba? Shi ya tafi yana  kuka kamar mace,  ita kuma tana ihun kiransa cikin fita hayyaci."  




Mumy ta share kwallar idonta tace "Faty inbamuyi hakan ba ya xamuyi?  Bature da Mimi basusan komai ba sai soyayyar junansu, kuma indai ba haka mukai masa ba baxai bari ayi mata magani ba" Faty tace "to Allah ya bata lfy. "




Abun mamaki Mimi ko rabin awa bataiba tana bacci ta kuma farkawa cikin ihu,  duk kuwa da qarfin allurar da akai mata.  Kiran sunan mijinta take tana cewa yazo ya dauketa. 




Mumy da Faty suka matso suna mata magana,  mama kuwa tana gefe tana kuka.  Ta kalli Faty tace "ya Faty kiramun ya Bature indai kina qaunata" mumy tace "maryam yi haquri yaje ya karbo maganin da aka rubuta miki." ta kau dakai daga barin da mumy take tace "ya Faty nace ki kiramun ya Bature inban ganshi ba mutuwa xanyi"  Faty tace "Mimi mumy na miki magana"  tace "ba ruwana da ita, baxan qara kulata ba tunda ta daki ya Bature" tana fada tana kuka.  




Faty tai murmushi tace "mumy kinji lefinki shiyasa akaqi kulaki" mumy jiki a sanyaye tace "yi haquri maryam, bansan xakiji haushiba da ban dakar miki shiba"  





Suna haka har yamma tayi, qarfe shida lokacin yan dubiya ya wuce.  Likita yaxo Dady ya nemi sallama,  babu dogon bincike ya sallamesu dalili kuwa shine suma likitocin yau sha biyun dare dai dai xasu shiga yajin aiki.  





Aka dorata kan kujera sukai gida da ita,  a lokacin magrib tayi Mimi har tagaji da ihun a kira mata ya Bature ta haqura.  Amma tayi jigum babu ci, babu sha babu magana. 




Bature kuwa yana fita asibiti anan tashar gyadi gyadi yaji ana ambaton motar Abuja,  ya shiga ya zauna take qaramace tana cika suka tafi.  





Xuwa laasar yana Abuja cikin gidansa har yayi wanka,  bai fitaba har bayan isha ko sallah a daki yake.  




Ishaq ya shigo har bedroom din ya sameshi,  shima Baqo ne ya kaimasa tsegumin sulaiman ya dawo ya qulle kansa a daki.  Ya dafa sulaiman din yana tambayarsa jikin Mimi,  bai bashi amsa ba sai kuka ya saka masa kana ya dora da cewa "sun kwaceta ishaq,  sun kwacemun maryam kuma mumy ce ta jagoranci kwacemun ita,  abunda nake nufi shiya faru wai maganin gida xasuyi mata.  Abunda ya gagari likita shi xa a xauna ace xa ayi a gida?" ishaq ya jinjina wannan lamari, kuma shima yana bayan sulaiman don be yarda wai iska ke damun Mimi ba,  shi yafi ganin malária ce ta haddasa mata wannan ciwon.  




Ya danne nasa damuwan ya lallabi sulaiman din da cewar ya bari a kwana biyu suje suyiwa Dady bayani da nuna masa takaddun asibitin sai su taho da maryam din.  Dakyar ishaq yasashi yaci abinci ya bashi maganin bacci yasha ya kwanta. 





Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)


📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 6⃣1⃣



Saqon masoya na iso mani ta hanyoyi daban daban, ina godia sosai. 



Matan Baffa suka fito suna kallon maryam dake zaune kan kujera babu magana,  aka shigar da ita har dakin mama.  Baffa ya nemi ganinsu gaba daya suka hallara dakin mama harda Rashida wacce ke zaune a gida yanxu.   



Baffa yayi musu bayanin lalurar dake damun Mimi kuma ya nemi hadin kansu akan hakan karo na farko a rayuwarta.  Duk iskancinsu wannan karon basu nuna ba suka dunga jimantawa suna mata sannu da fatan samun sauqi.  Ya gabatar da Aisha a matsayin yar aikin Mimi wacce taxo xama da nufin temakawa Mimi.  




Bayan fitarsu mama ta fadawa Baffa Mimi fa babu abunda taci tunda aka kawota kano,  ada ana saka mata drip yanxu kuma da suka baro asibiti babu wannan maganar.  Yace to tabari yaje sallar isha ya dawo zaisan abunyi.  




Ya maza jikin kujerar Mimi yace "maryamu me kikeson ci?" tai masa shiru.  Mama tace ai haka take tunda ta fuskanci mijinta baya kusa da koma kurmar qarfi da yaji.  




Faty xata iya cewa taji dadin wannan yajin aikin domin ta samu damar jinyar Mimi,  daga asibiti gida ta biyosu ya Ahmad ya biyota da akwatinta da ragowar kaya. Shima babu yadda beyi da Mimi ba tai magana taki, Faty tai mata alwala akai akai tai sallah taqi.  




Baffa daga masallaci ya taho da wani malamin islamiyya maqocinsu, ya nuna masa Mimi.  Yace suyi mata alwala, sukace da alwalarta.  Ya fara karanto mata ayoyin korar shedanu amma shiru kakeji,  sai da aka fara karanta ayoyin sihiri sannan ta fara ihu da kuka.  





Yace a samo garwashi da sauri Rashida taje maqota ta samo, ya xuba turare aciki.  Mimi da bata iya miqewa sai gata a tsaye tana neman hanyar gujewa wannan turaren hayaqin.  Baffa da Huxaifa suka riqeta dakyar don abun ya girmi mata. 




Xan iya cewa aranar babu wanda ya runtsa a gidan sabida ihunta,  ko ince har maqota na kusa.  Tun malamin nayin abu shi kadai har abun ya gagareshi aka kira wasu malaman.  Sunkai 3:00 AM suna abu daya, sun jigata sosai sun gaji itama ta gaji duk jikinta yayi laushi ga ihu ga yunwa.  Sai dab da asuba ta samu bacci aka huta.  




Duk tajiwa kanta ciwo da wadanda ke riqe da ita.  Malamin kewa su Baffa bayani cewa Mimi fa asiri akai mata wanda aka hadashi da aljanu marasa imani kuma haukatata akasoyi don haka wannan aiki sai annemi taimakon wasu malaman wadanda suka fishi sani don abun yafi qarfin mutum daya ko biyu. 




Mama dajin haka ta dunga kuka tana cewa ita ba Mimi take tausayiba illah abunda ke cikinta shi da bashi da haqqqin kowa,  hankalinta a tashe yake akan haka ganin yadda ake dambe da Mimi take burgima tana murje cikin. 





Sassafe saiga mumy taxo da Dady harda wani malami, shima yaxo duba matsalar Mimi,  lokacin bata tashi ba.  Faty ta lallaba ta tasheta,  cikin hukuncin Allah kuma ta tashi qalau sai dai babu magana. 




Faty ta taimaka mata tai wanka,  ta shirya ta kalleta tace "ya Faty nayi sallah?" tace "a a maryam ana binki salloli da yawa"  Faty ta dunga gaya mata sallolin da xatayi da kuma adadin raka oin tanayi harta idar.  




Aka kaita dakin Baffa gurinsu Dady,  ta dunga kallonsu ba tare da magana ba,  sai sune sukai mata sannu da jiki, shima bata amsa ba sai murmushi tayi.



Malamin yana kallonta yace "maryamu meke damunki?" tai shiru,  ya kuma maimaitawa har karo 3 amma tai shiru.  Ya guntsi ruwan dake hannunsa wanda yaxo dashi ya fesa mata.  Ta yunqura da gudu tayo waje tana ihu,  duk suka biyota ya bada umarnin a riqeta.  Baffa ya riqeta tamau, shi kuma yacigaba da guntsar ruwan yana fesa mata tana tsala ihu kamar ta tsaga gidan.  





Dake Dan Adam dai sunansa Dan Adam saiga Anty ta fito tana mitar cewa "wannan wane irin bala i ne?  Jiya kin hanamu bacci yanxu kuma munsa haqarqarinmu xamu kwanta kin kuma tada iskancin ihu, ai wlh ko alhakinmu ya hanaki warkewa"  wannan magana da Anty keyi karaf a kunnen Hajja wadda ke shigowa yanxu.  




Ta qaraso tsakar gidan tana duban Anty fuskarta murtuk tace "jamila anya kuwa ke macece?  Shin yarinyarnan itace ta dorawa kanta ciwonnan?  Babu tausayi babu kyakykyawar kalma?  Babu komai kiyi duniyace babu wanda ya wuce irin wannan lalura kuma inkasan farkonka bakasan qarshenka ba" 




Mama tana kuka tace "Hajja ya isa,  yanxu ba lokacin maida martani bane,  kalli diyata Hajja so ake a haukatamun maryam.  Allah karka kashemun yayan nan sukenan kabani guda biyu, Allah ka duba raunina ka rayamun su"





Kalamanta sun bawa kowa a gurin tausayi,  malamin yacigaba da xubawa Mimi ruwan addua tana kuka harya qare.  Yace zaije ya dawo sai an sake shiri kuma a cire mata duk rings din dake jikinta a barta ta azurfa kawai kana ya bada wani turare yace a shafa mata gaban goshinta.  




Suka tafi shida Dady, Baffa ma ya fita kasuwa yana qara jaddadawa mama abawa Mimi wani abun taci.  Mumy, mama, hajja dasu Faty duk suka koma dakin mama.





Hajja ta kwance ledar data zo da ita ta fito da qullin rubutu,  ta juye a kofi ta bawa Mimi, duk da Mimi a lafiyayyarta batashan rubutu sai dai tofi amma yanxu dai babu musu tasha. Ta samu ragowar ta shafe mata jikinta,  kana ta fara cirewa Mimi zubunan hannunta tana mitar cewa "bandaku yaran yanxu aiko wannan ya isa ya kawo muku shedanu, dan masifa zobe hannu da qafa" ta zaresu tas harna qafa ta miqawa mama.  





Mumy ta juya kunun gyadan dataxo dashi a kofi tace "Mimi xokisha kinji" tayi shiru, ta kuma cewa "uwata taso kinji kisha"  Mimi tsam ta miqe ta koma dokin qofa ta kwanta tana birgima da kuka.   




Sukai sukai ta tashi taqi ga gida babu kowa duk maxan sun fice.  Dakyar Faty ta lallabata tace mata "Mimi na menene? Me kikeso?  Kinga ke kadai nake da ita fadamun duk abunda kikeso in miki kinji"  tana sharbe hawaye tace "ni kusamun xobena ya Bature ne ya sakamun"  





Hajja tace "baxa asaka miki dan qaniyarki,  wannan dagajin maganar ba maryamu bace aljanace ke magana a makwafinta" Mimi ta qara xandara ihu tana turje turje,  Faty dataga abun na qoqarin fin qarfinsu taje ta debo rings din gaba daya ta mayar mata hardana qafar kana aka zauna lfy.  



Dakyar tasha kunun gyada rabin kofi aka saka mata turaren ta kwanta.  




Ranar haka aka yini ana xuwa dubiya,  da masu xuwa dan Allah da kuma masu xuwa ganin kalar haukan Mimi.  Umman fauxa da hajiyan su Farida anan sukayini ana jimami,  ciwon Mimi kuwa ya tashi yafi sau a qirga.  Babban abunda ke daga hankali shine yunqurin fita take in abun ya tashi kuma taqi shan koda ruwa tun kunun da tasha da safe. 





Haka suka yini qofa a rufe,  Aisha da Faty na riqeta. Anty kuwa sai mita andamesu take, itadai Umma babu yabo babu fallasa bata nuna ta damuba kuma batai murna ba da ciwon.  



Hajja sai azahar suka tafi tare da mumy,  Hajja tace "xa a dunga kawo rubutu Kullum ana shafa mata kuma tana sha Mal manu ne yasa ake mata sauka."




Sai dare Baffa ya dawo  tare da malamin,  aka kuma xaman ruqiuya  suka zagayeta ko wanne yanayi, tana ta ihu sun dade suna abu daya har wajen taran dare kana aka kyaleta.  




Aka bada ruwan magani da man xaitun habbatus sauda malamin yace ai mata wanka da ruwan maganin sannan a mayar mata da wadannan mayukan sune na shafawarta koda yaushe. 





Mama ta jata taje tai mata wankan maganin sannan tai mata alwala tace tai sallah tace "mama guda nawa xanyi?" mama ta fada mata tayi magrib da isha.  Ta tashi tayi, Faty ta shafa mata maganin har gashin kanta.  




Mama ta fita kaiwa Baffa abinci,  yace taje ta kira masa Mimi.  Mama tasata agaba ta kaita,  ta xauna gaban Baffa mama na gefe tana cemasa "Baffa Mimi fa har yanxu bataci komai ba tun safe" yace "to ba komai" ya kalli Mimi yace "maryamu saka hannu muci" ta xuba masa ido ba tare da tayi magana ba.  Ya fara gutsuro tuwon yana saka mata a baki,  babu musu ta fara karba.  Yanaci yana bata har suka cinye.  Mama ta miqa masa jug din fura bayan ya wanke hannu,  furar ma yana kurba yana bata harta suka shanye sannan ya bata ruwan saukar da akayo mata tasha.  Aisha ta samo garwashi akayi mata turare ta kwanta.  



Wannan daren dai da sauqi sun sami bacci don tunda ta kwanta bata qara tashi ba.  Mama da Faty qarfe 4 suka tashi suka fara sallolin nafila har xuwa ketowar alfijir. 



 
Kwana uku da xuwanta xa a iya cewa abun da sauki,  an durfafi addua kota ina duk inda malamai masu korar aljanu suke xuwa ake,  wani akai Mimi wani kuma yaxo har gida. 



Babban abun tashin hankalin ciwonta shine yunqurun fita waje a duk sanda ciwon ya tashi. Wani maganin in anyi ciwon ya lafa wani kuma ya tadashi.  Kudi kota ina kashesu ake,  Dady yayi Baffa yayi sannan Audu ma yi yake kamar shine mijin.  




Anty Kullum cikin mita take a cewarta wai Mimi taje Abuja xatai musu iyayi da nuna iyawa irin wacce ta saba su kuwa yan matan Abuja suka korota tare da haukatata, mijin kuma dayaga ta haukace ya kawota gida ya ajiye yaje yana holewarsa da yan mata.  




Abun takaici kuma a gaban Mimi take furta irin wadannan kalaman,  intana fada Mimi kan xura ido taitai kallonta.  




Rashida kuwa har kusan tsine mata Anty tayi a cewarta wai Rashidan taqi sharar masallaci tanayin ta kasuwa, ko kuma tace "Rashida haka kikaga yafi miki ko?  Kinqi xaman gidanki kinxo kina jinyar mahaukaciya.  





Rashida kuwa duniya ce tai mata atishawar tsaki, domin mijinta irin maxan nanne masoyan mata ganin yana da kudi haihuwarta daya yayo mata kishiya.  Ta tada hankalinta sosai ta fara yimata mugun hali da tsangwama kamar yadda tayiwa Mimi a baya, yarinyar mai wankakken ido ta ware bajewa Rashida makirci wanda takai har saída mijin ya korota gida da saki daya.  




Rashida da Anty hankalinsu ba qaramin tashi yayiba, sunso rufe maganar sakin kar kowa yaji sannan ya maidata dakinta.  Amma mijin yayiwa Baffa aike cewar azo a kwashe kayan Rashida xai amfani dakin. Baffa yazo ya rufe Anty da fada kuma ya fasa maganar sakin a tsakar gida,  babu kunya Umma ta dunga sheqa dariya tana cewa Anty uwar bazawara tare da tutiyar ita ba a taba sakin yaranta ba.  Da gorin Umma ya ishi Anty sai tasa Rashida a gaba sukaje har gidanta suka bawa mijin haquri tare da roqonsa ya maidata.  Dake lokacin giyar amarci na kwasarsa suka hadu shida amaryarsa suka ciwa Umma da Anty mutunci.  




Labari ya iske Baffa shima ya kuma ciwa Anty mutunci kuma yace su yayansa ba a abun wulaqantawa bane tun daga kan Mimi ya dawo daga rakiyar a sakar maka ya ka dunga roqon a maidata domin bakasan bala in daya hanata xama ba gidan mijin.  



Da Anty taga babu nasara a wannan bangaren saita tsiri takurawa Rashida da gori a nata dabbacin tana ganin hakan zaisa Rashida ta gaji ta koma gidan mijin ta xauna qarqashin wulaqancin miji dana kishiya.  A bangare guda kuma ga Umma Kullum tana gorantawa baxawara da uwarta (dama ance abunda kai shi ake maka,  abaya ai da ita da Umma babu abunda basuyiwa Mimi da mama ba)  




Da bala'in Anty ya ishi Rashida saita koma dakin mama gaba daya take xaune dakin Mimi. Domin maman dai da suka raina suka kuma dauka maqiyarsu ita kadai ke tausayawa Rashida da kwantar mata da hankali.  Rashida gaba daya tayi sanyi, har yanxu tana kunyar mama da Mimi bisa abunda ta dunga yimusu a baya gashi yanxu sun saka mata da alkhairi. 





Tun Faty da mama na dari dari akan Rashida karta cuci Mimi har suka saki jiki don sunsha gwadata su barta ita da Mimi su kadai a daki amma sukan samu komai lfy koda ciwon ya tashi Rashida bata bari Mimi taiwa kanta lahani sai dai suyi ta kokawa da Rashidan wani sa in harta jimata ciwo.  



Dakin mama cike yake, gata, ga Mimi,  Rashida,  Aisha,  Faty da yan jikokinta.  Safe xuwa dare kuwa ba a raba gidan da baquncin mumy Umman fauxa hajian Farida sai yasmin. 




Duk da Umma ta sararawa Mimi qiyayya tun lokacin bikin jafar amma yanxu abun yana neman dawowa, dalili kuwa kulawar da Baffa yakewa Mimi don yanxu babu mai kwana a cikinsu Baffa kan shafe dare yana xarya tsakanin dakinsa dana mama yana ganin lfyar Mimi.  Mama kuma bata da shamaki a dakin yanxu koda wane lokaci shiga take, wannan dalili yasa Baffa yace babu xancen raban kwana sai bayan warkewar Mimi don sau tari Mimi da mama a dakin baffa suke kwana in ciwon ya tashi.  




Wannan dalili ya sabun tawa Umma qiyayyar Mimi wacce ta kwanta a dalilin kyautatawar Mimi ga yayanta.  Tana ganin Baffa yanawa Mimi soyayyar da ko yayan cikinsa bayayiwa.  





Anasa bangaren Baffa tausayin Mimi yake sosai da santa fiye da kowa cikin yayansa domin yarinyar taga iftila 'in rayuwa kala kala. 



****** ******* *********



Yau satin Mimi daya a kano,  malamai sun sami kudi ba kadan ba a jikin su Dady,  kowanne yana kwada tasa baiwar.  




Jiki kam Alhamdulillah ana ganin sauqi sai dai babu magana sai dai tai jugum tana tunani.  Magani kuwa sunkai buhu uku a dakin mama dana sha dana wanka sai kace yar mai ganye.   





Ranar dai data cika sati ta kama monday,  Rashida ta tafi aiki.  Faty da Aisha sun fita Aisha taje raka Faty banki gida ya rage sai mama,  a lokacin ne ciwon Mimi ya tashi,  ta dunga ihun kuka tana burgima kamar yadda ta saba, mama ta dunga yunqurin riqe Mimi amma abun yafi qarfinta don tuni Mimi ta wullar da mama gefe guda tai hanyar waje, mama ta taso da gudu ta kuma riqe mimin.  Mimi ta kuma angijeta tana cewa kirana ake yanxu xanje in dawo. 




Duk wannan abunda ake Umma da Anty na ganinsu amma babu wacce tai yunqurin taimakawa, sai Umma ce ta miqe ta rufo qofar tsakar gida ta koma ta rabe wai tsoron Mimi take karta daketa.  Anty kuwa tana xaune tana sakace tace "yo kaje a illataka ? tunda haukan ya motsa  da akwai igiya kusa dana leqa ankira maxa an daureta."  




Temakon Allah baya yankewa ana cikin haka saiga mumy da Audu ya kawota,  mumy da Audu ne suka hadu aka riqe Mimi aka maidata daki dakyar. Aka kunna saudi qur an.  




Mumy taiwa Anty tas da cewa "wanda yayi da kyauma yaya ya qare jamila bare ke da Kullum cikin aibata yayan mutane kike, da kina da hankali da kin gane mugun bakinki ga Mimi ya jawo mutuwar auren Rashida amma dake kedin jakace har yanxu baki karatun ta nutsu ba.  Kuma Mimi batai gadon hauka ba dan haka ciwonta bana hauka bane." Anty tayi qus domin ta tsani a goranta mata mutuwar auren Rashida wannan abu shine weak point dinta yanxu. 




A cikin satin jafar yaxo daga KD. Hankalinsa yayi  mugun tashi lokacin da Anty ta sakashi a gaba ta fada masa karya da gaskiya akan ciwon Mimi.  Kamar yadda take fadawa duk wanda ya shigo gidan cewa Mimi hauka take muraran kuma ta fita tsirara sai qarti ke shigowa da ita. Shi kuma Bature tunda yaga ta haukace ya sakota mota ita da me aikinta ya korosu kano har yanxu be kuma xuwa ba.  A fadarta. 



Ya tausayawa Mimi sosai, ya dunga xagin Bature a xuciyarsa ashe duk soyayyar da yake nunawa maryam yaudarace tunda har ya gujeta a halin lalura. Yasa ransa cewa lokacin da xai auri maryam yayi, koda Umma xata tsine masa saiya aureta, abunda kawai zai hanashi aurenta yanxu a halin lalura shine cikin jikinta inbayanshi da ahaka zaisa Baffa ya aura masa ita don ya nunawa duniya yana sonta. 




Amma xai jira ta haihu, ya aureta ya riqe mata danta kamar shine ubansa, tunda ko bai aureta ba ai dan maryam dansa ne.  



Shida yaxo da nufin yagaidasu ya koma a ranar saiya bige da kwana. Yaje gidansa xuwa yamma ya dawo,  ya tarar Baffa da Mimi xaune akan tabarmar tsakar gida.  Mimi na gefen Baffa yana bare mata dafaffiyar gyada yana xuba mata a hannunta taci.  




Ya qaraso ya tsuguna yana cewa "Baffa ashe kana cikin gida, ai na axa baka dawo ba"  Umma tai karaf tace "ai dole ka ganshi gida yanxu yar gwal babu lfy, yine yake jinyarta"  yayi shiru babu wanda ya tanka mata. Jafar ya qurawa Mimi, ta rame sosai tayi duhu sai dan ciki kadan daya bayyana jikinta. Yayiwa Baffa jajen jikin Mimi,  Baffa ya fada masa cigaban da aka samu.  Anan suka xauna har magrib sukai jam'i daganan aka kawo musu abinci, kamar yadda suka saba Baffa naci yana bata tanaci har suka gama. 



Mimi dai sauqi ya samu sosai, sai dai babu magana sai dai tai tabin mutane da kallo.  Babban abunda ke damunta maganganun Anty na cewa Bature yaga ta haukace ya kawota gida ya ajiye,  tun Mimi bata ganewa harta gane ta fara fuskantar maganar Anty fa gaskiyace tunda gashi  tunda ya kawota kano ya ajiye ko awaya be kuma nemanta ba.  



Taso qullatarsa bisa wannan abun da yayi mata, amma xiciyarta taqi bata hadin kai musamman inta duba farkon ciwonta acan baya irin yadda ya dunga jinyarta yana kulawa da ita. Sonsa take kewarsa ta dameta ainun, ciwonta kanyi kwanaki bai tashi ba amma babu magana. 




***** ***** ******* ******




Acan Abuja kuwa Bature wata irin rayuwa yake me cike da loneliness.  Baya kula kowa baya shiga shirgin kowa, yakanje aiki ya yini yana aiki babu hutu, wani sa in har dare yake kaiwa acan.  So yake ya manta da Mimi da duk wasu mutane dake kano sabida abunda sukai masa.  Amma hakan ta gagara don Mimi batai masa lefin komai ba, hasalima sun rabu tana ihun cewa baxata iya rayuwa babu shiba ba.  Ya fige ya lalace ya tara gashi cunkus kansa da fuskarsa.  Ishaq sai ya gaji da rashin ganinsa yake xuwa gidan,  yayi fadan, yayi lalllashin, yayi nasihar , amma duk a banxa domin Bature ya xama kamar wani motsatstse.  A office mr Alex yana tausaya masa yana masa nasiha,   amma duk a banxa ya haukace asan Mimi. 




Hanifa ke xaman jiran Bature ya furta yana sonta amma taji shiru,  gwaggoriya ce tai mata famfo cewa taje tai masa tuni tunda uwargida tace da aikinsu a jikinsa.  Ta yarda da wannan shawarar kawai tana jiran sulaiman din ya fita daga damuwarsane. 





Ana cikin haka Anty mami taxo 9ja, wacce mutuwar uban mijinta ya kawosu ita da mijin.  Acan katsina suka sauka wato family house din su mijin.  Lubna ke fada mata Mimi babu lfy amma bata fada mata ainihin abunda ke faruwa ba.  




A gidan mumy ta sauka data iso kano, ita da mumy sukaxo gidan mama.  Anty mami tayi matuqar kaduwa da ganin Mimi da kuma jin asalin ciwo.  





Hausawa sunce "ranar naka sai naka, dadin xama kuma sai bare." a takenan Anty mami ta manta duk wata qiyayyar Mimi, kuma dama can ita tanason Mimi aurenta da Bature ne bata soba. Ta dunga kallon Mimi tana kuka tace "Mimi me kikeso in sai miki? Fadamun kinji Mimi duk abunda kikeso  kinga ni yar uwarkice bayan haka kuma Dan uwana kike aure." tai shiru kamar yadda ta saba tanabin Anty mami da kallo.  Ta kwanto Mimi jikinta tanacewa "Mimi ko kinaso intafi dake can Canada insaki makarantar rainon ciki kiyi xamanki kedasu Raudah?" wannan karonma shiru Mimi tayi.  Babu yadda Anty mami batai ba taji muryar Mimi amma abun ya gagara.  Ta dunga kuka duk kuwa da taurin xuciya irintata,  tayi nadamar abunda tayiwa Mimi last xuwanta kano, yanxu gashi tana nema Mimi tace wani abun amma babu baki.  




Da Anty mami ta matsa sai Mimi ta fadi abunda takeso taga Mimi ta kasa magana sai tasa kuka, itama mimin tasa kuka.  Ta rungume Mimi jikinta tana lallashinta.  Mumy taji dadin wannan daidaito da aka samu tsakaninsu.  Da xata tafi kudi ta bayar masu yawa wai a siya mata duk abunda takeso. 



Daga kano Abuja ta nufa,  ta furgita lokacin dataga Bature ya dawo office wajen taran dare.  Ta kalleshi tasa kuka,  gaba daya ya canja.  Suka samu xama a daren ta dunga kwantar masa da hankali cewar maryam ta samu lfy maganace kawai batayi.  Ta godewa Allah da batai sillar rabuwarsu da matarsa ba,  yanxu kawai rabasu akai nadan lokaci ya xama haka inaga an rabasu gaba daya,  anan ta saduda kuma tayi niyyar fita a rayuwar aurensu.  




Washegari ta rakashi aski aka cire masa sumar kansa akai masa gyaran fuska, sai ramarsa ta kuma fitowa.  Suka dawo gida ta yanke masa farce tasashi yayi wanka ta bashi abinci a baki.  Ta gyara bedroom din da ya cika da kayan wanki.  



A ranar ta tara ma'aikatan gidan,  ta dunga yimusu bala'i da hausa in hausar ta kakare ta koma turanci, inta fiskanci basa gane turancin da koma hausa.  Ita zarginsu take sunada hannu a abunda ya samu Mimi, a cewarta inbata hanyarsu babu yadda xa ai Mimi ta samu wannan matsala, kuma xatai bincike indai ta tabbatar da hannun wani a ciki tofa hukuncinsa life in prison.  Sun tsorata da ita don ita din gwanar masifa ce.  Baqo a xuciyarsa yace "wannan mata da masifa take kamar ba jinin mumy da Dady ba" 




Ta dakko masu aiki aka saka matakan tsaro a gidan dake aikine na kudi, wasu shegun qofofine wanda sai sun tantance mutum kafin ya shiga ga cameras kota ita kamar xaka shiga fadar gwamnati.  




Ta shiga gidan ishaq don taji yana ina Bature ya xama haka?  Amma ganin da tayiwa ishaq da Farida ya hanata masifar da tayi niyya domin suma duk sun qare Farida sai uban ciki a gaba wanda yakai 7 months. 



Jiki sanyaye ta xauna kan kujera tace "ishaq baku da lfy ne naga duk kunyi wani iri?" yayi qasa da murya yace "Anty mami rashin lfyar Mimi da kuma halin da sulaiman ke ciki ya maidamu haka.  Mimi ta tafi da farin cikin mutane da yawa" ita da ta shigayin masifa sai ta bige da nasiha.  




Kwananta uku a Abuja ta koma kano, ranar anyiwa Mimi sauka a take ta bada kudin rago tace a siyo a yanka a sadakar.  



Ta samu mama da mumy a killace ta xana musu halin da sulaiman ke ciki ta roqesu da indai baso suke ai biyu babu ba tofa su bashi matarsa.  Uwa da Da sai Allah, mumy jikinta yayi sanyi tana kuka tace 'Duk wanda yayiwa maryam mugun abunnan wlh baxan yafe masa ba don ya watsa mana rayuwar yaya"  suna cika sati daya ta juya Canada ita da mijinta, bayan ta kuma bawa Mimi maqudan kudi, ta tafi da burin son jin muryar Mimi amma har tatafi Allah baisa Mimi tayi magana ba. 




Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)


📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 6⃣2⃣



Assalamu alaikum.  Masoyan Mimi ina neman afuwa,  anatamun maganan cewa "Hajia ya dace ace Mimi ta huta da wahalar rayuwa haka" wasu ma har waya sukemun ana roqon Anty Rahmatullah ta saurarawa Mimi 😊. To naji kuma duk nagode soyayya ce ta kawo har akemun haka kuma nagode sosai.  Amma ina qara baku haquri, abunda nakeson fans dina su sani shine; 50% na labarin AL'AMARIN MARYAM true life story ne (wato ya faru a gaske) ragowar kuma na qarane sabida nishadantarwa. Sabida haka sai anyi haquri komai ya kusa xuwa qarshe.  Tanxz nd luv u all 😊❤


Hanifa ta shiga cikin office dinsa lokacin break, kamar yadda tayi tsammani aiki yake a maimakon break din.  Sai data zauna ya lura da xuwanta, takai hannu ta dau frame din dake kan table din wanda ke dauke da pic din Mimi da Bature ranar daurin aurensu, sanye da fararen kaya sun qurawa juna ido. Ta ajiye frame din da cewa "Allah sarki maryam ya jikinta kuwa?" 




Ta sosa masa inda ke masa qai qai yadan bata attention yace "da sauki nagode da kulawa" ta qara gyara xama cikin siyasa tace "Sir, dama inason muyi wata magana, so inata jiran inga kasamu nutsuwa daga halin da kake ciki" ya runtse idonsa yace "baki da damuwa da halin da nake ciki kiyi maganarki, i m all ears" 




"Dama naga maryam babu lfy kuma ko baka fada ba kowa yasan kana neman kulawar mace a yanxu shine nace maixai hana ayi maganar auren mu yanxu?  Nayi alqawarin kula maka da maryam" 




Kallonta yake cikin tsabar mamaki da son xuciya irin nata, saida ta ida yace "bansan ke akuya bace sai yanxu, kin dauka kowa daqiqi ne irinki?  Matar tawa babu lfy kikemun maganar in aureki?  Wato ga mahaukaci irinki ko?  To bari kiji ko ada bani da raayin aurenki balle yanxu, bana buqatar kulawarki akan maryam kuma ko tana da lfy ko bata da ita inason abata a haka. Na haramtawa kaina  kowace mace, sulaiman mijin maryam ne ita kadai"




Ta katseshi cikin bacin rai "dakata sulaiman, so fa ba hauka bane, akan inasonka saika kirani akuya? Akan mahaukaciya kake cimun mutunci to w.... " marin dataji bisa kuncinta biyu shiya hanata ida maganarta.  Ta bude ido razane tana kallonsa, ya xago ya damqo hannunta ya jata kiiiiii ya fita da ita daga office din. 




Tana ihu tana turjewa tare da cewa "sulaiman ka tsaya, ina xaka kaini don Allah kayi haquri" bai kulata ba, yacigaba da janta mutane na kallonsu ana yan surutai, wasu ma binsu suke suga inda xai kaita. Kuma dama shidin tseguminsa ake da cewa duk wannan haduwar tasa matarsa mahaukaciya ce. Bai direto ko inaba sai office din mr Alex, ya wurgata ciki. 



Mr Alex ya miqe tsaye yana kallonsu, sulaiman na huci. Hanifa na kuka, kafin ya tamvayi abunda akai Bature yace "karabani da wannan masifar, ka rabani da wannan anobar, nagaji da xama da ita. Hanifa tayi silar bacin ran maryam da dama kafin yau ta kirata da mahaukaciya." 



Mr Alex ya jinjina lamarin, Hanifa tayi wauta yadda sulaiman ke qaunar matarsa ai kisama zai iya a kanta ba rabuwa da mutum ba.  Hanifa ta rarrafa ta riqe qafarsa tace "na tuba sulaiman na janye kalamaina akan maryam, ka yafemun Allah ma muna masa laifi ya yafe bare yan Adam. Sulaiman har kauce hanya nayi sabida soyayyarka" ya cillata gefe guda, yace "ai kinsaba kauce hanya,  da nabiye taki da tuni kin maidani hamshaqin maxinaci" a xaton Bature abunda take nufi kenan. Ya kalli mr Alex yace "a canjamun sect, kuma namiji nakeso ba mace ba. Wlh indai ba a janxa wannan anobarba xan aje aiki" 





Dajin haka Hanifa tayi dif ta qura masa ido, lallai kwabarta tayi ruwa. Ta kuma tunkararsa yayi saurin kaucewa yace "karki tabani, ko a hanya kika nuna kin sanni saina saka an sassaba miki kammani" yakai dubansa gurin mr Alex yace "a tura wani ya kwaso mata karikicanta a office dina wlh inta kuma saka qafa ciki ni nabar aiki" ya juya ya fita.  




Xuciyarta ta bushe ta kasa kukan, tabi bayansa da kallo Allah ya dora mata masifar son sulaiman akansa ta kauce hanya, yaci ace ta haqura dashi sabida wulanqancin da yayi mata tun akan auren maryam, amma xuciyarta taqi sarara mata soyayyarsa, taso ace ya biye mata sun watse wataqil inta maida kwadayinta a kansa ta samu sauqin soyayyarsa amma sai akai rashin dace duk wayewarsa baya cikin maxinata. Yanxu gashi ya rabu da ita gaba daya, meyasa asirinta baya kamashine?  Me gari ya waya yanxu?  Ta bata lokacinta, ta bata kudinta, ta sabi ubangijinta,  ta shiga haqqin baiwar Allah wadda batai mata laifin komai ba,  a qarshe agaban dubban mutane ya cimata mutunci kuma ya rabu da ita.  Nan take nadama ta saukar mata taji ta tsani kanta,  wai itace yau tai silar haukacewar mutum?  Meya jawo mata? (son zuciya da xugar gwaggoriya) lallai manxon Allah yayi gaskiya da yace "mafi qin abun bautawa a akan qasa son xuciya" ita yanxu gashi ya kaita ya barota.  Tayi asarar lokacu, dukiya, mutunci kuma duk babu riba. Inta mutu yanxu mezatace da Allah?  A fili tace "maryam ki yafemun na xalunceki ba tare da kinyimun laifin komaiba.  Allah kaimun hukuncin daya dace da tsinanniya muguwa irina" ta fashe da kuka meban tausayi. 



Mr Alex yana kallonta cikin tausayawa, tsammaninsa kukan rabuwa da sulaiman take donshi bai gane abunda take fada ba. 



Te tashi ta fita office din da gudu tana kuka tana maganganun Mimi ki yafemun Allah kaimun hukunci a duniya" ta yanki burtali a qafa bata tsaya daukan mota ba,  mutane anata kallonta kamar motsatstsiya.





Ta samu mahaifiyarta a gida wacce suke kira Hajia, yau anyi sa'a bata fita yawan gantalin ba. 



Ta riqe Hanifa tana tambayarta a firgice "Hanifa accident kikai?"  tayi wannan tambayar ne  sabida taga idanunta sunyi luhu luhu ga fuskarta jajur sabida marukan da sulaiman yayi mata. Ta dubi yan aikin dake tsaye a kansu, alamar baxata fadi maganarba a gabansu.  Hajia tace "ku bamu guri" 




Suna kaucewa Hajia ta kuma tambayarta,  Hanifa xuciyarta cunkushe take neman wanda xata fadawa damuwarta take.  Ta kwancewa Hajia komai tundaga farkon ganinta da sulaiman har xuwa yau da kuma abunda sukai ita da gwaggoriya.  Ta qarashe da cewa "Hajia ina neman kiban ixini inje infadawa sulaiman nice silar haukacewar maryam"




Hajia ta xabga mata mari  tare da cewa "da ixinina kika nema lokacin da xaki haukata masa matar?  Gwaggoriya ko?  Itace uwarki?  Dama ni can hankalina be kwanta da ita ba"  ta qara rufe Hanifa da duka kota ina tana takata da qafa tana cewa "kin cuci kanki Hanifa, kin taba gani ina asiri?  Wannan ba Hanifar dana shayar nona bace, gwaggoriya ta canjamun yata. Kin taba ganin nayiwa wani asiri?  Tun yaushe duniya ta waye ko wadanda basu da ilimin boko sun dena asiri bare ke da kika qoshi da ilimi" Hanifa bata gujewa dukan Hajia ba sai data gaji dan kanta ta kyaleta.




Ta kwanta jikin Hajia tana kuka tace "Hajia ke kika haifeni kinfi kowa sanin ciwona,  ki temakeni ki rufamun asiri ki fadamun hanyar da xanbi in gyara kuskurena kar inyi biyu babu na rasa duniya tunda na rasa sulaiman, banaso in rasa lahirata sabida hakkin maryam." 



Hajia tana kallon Hanifa cikin tausayawa tace "kin kyauta da baki fadawa sulaiman ke kika haukata matarsa ba, domin da kin fada da yanxu rayuwarki na cikin hatsari." ta qurawa Hajia ido, Hajia ta kalleta tace "hanya daya ta rage mana wacce xaki gyara kuskurenki itace muje mu warware asirin da kikayiwa maryam" Hanifa ta kalleta a firgice tace "Hajia hakan xai yiwu kuwa?" ta bawa Hanifa amsa da "dole mubi duk hayyar da hakan xai yiwu. Ki tashi muyi sallah ki rakani gidan matsafiyar taku"




Sun dau hanya bayan idar da sallah,  dakyar suka gane gurin don sai da suka hada da tambaya.  




Uwargida ta watsa musu kallon wulaqanci bayan sun gama koro mata buqatarsu. Tace da Hanifa "aimu bama amai mu lashe, da kinsan baki shirya bata ba kika fito  yawan asiri?  Ku tashi ko bacemun ko kuma mu haukataku yanxu"  



Hajia ta kalli uwargida, wai wannan matarce xata bude mata ido.  Ta dakko wayarta ta kirawo danta soja wanda yake yayan Hanifa ta bude speaker din wayar. Ya dauka tare da cewa "Hajia ya akai akwai damuwa ne?" tace "akwai, soji nakeso a hadamun mota guda akwai wata yar matsala su xama ready in naga babu daidaito xanyo waya su taho" yace "to angama Hajia"




Ta kalli uwargida bayan gama wayar tace "xakiyi abunda nace ko sai nasa an markadeki an markade gidan?" uwargida ta miqe tsam ta fita ba tare da tace komai. Jim kadan ta dawo da kayanta na tsibbu himili guda, ta xauna ta dunga surutai tana jefasu a gabanta wuta na tashi.  Ta dau tsawon lokaci tanayi, kana ta dubesu tace "xaku iya tafiya nagama" Hajia ta watsa mata kallon kyamata tace "inma karya kikai mana baki karya ba xan kuma dawowa in miki hukunci,  tsibbu kuma baxan hanaki ba kije kiyi tayi wata rana qaiqayi xai koma kan masheqiya." suka tashi suka fice suna hararar juna. 




A daren Hanifa taiwa munnir waya wani tsohon saurayinta kuma cousin dinta wanda ya shafe shekaru yana sonta amma taqishi har yayi aure da yayansa biyu.  Yayi mamakin jin abunda Hanifa ke fada masa cewar in dai yana sonta har yanxu ya turo ayi magana.  Ya gigice bakinsa na rawa ya tambayeta da gaske take mai?  Ta tabbatar masa da gaske take, ya dunga godia yace xatajishi bada jimawa ba.  





Kwana biyu tsakani aka kawo kudin auren Hanifa harda sa rana wata uku kacal.  Munnir santa yake  kamar ya cinyeta, ya dunga bata tausayi. (dama hakane dai dai, kuskurene ga wanda ke sonki kije ki mannewa wanda bai damu dake ba don salan kwantai.😜) gwaggoriya labarin engage din Hanifa ya sameta, ta dunga kiran Hanifa a waya taqi dauka. Ta nufi gidan afujajan, a xatonta sulaiman Hanifa xata aura.  Tana xuwa Umma da yayyun Hanifa suka hadu sukai mata caaa, suka tsageta tas tare da fada mata anraba qawancensu da Hanifa  don Hanifa yanxu aure xatai. Wanta soja yace inya kuma ganinta ko a hanyar gidansu saiya kaita barikin soji.  Da wannan aka raba gwaggoriya da Hanifa.  Hanifa ta rubuta takaddar barin aiki ta tura NNPC da nufin ta samu wani aikin bayan bikinta don baxata iya xama inuwa daya da sulaiman ba don har yanxu babu abunda ya ragu na soyayyarsa a xuciyarta kawai dai ta haqura ne kuma bataso ta dunga ganinsa a matsayinta na matar wani tunda tuban gaskiya tayi. 



******** ******** *******


A cikin satin Mimi na uku a kano sauqi ya samu sosai, hankula sun kwanta. Faty harta koma gidanta, Aisha kuma taje ganin gida garinsu.  Dakin ya rage daga Mimi, mama, Rashida sai Dady. 




Duk da sauqi ya samu sosai babu abunda aka fasa na magani,  sabida malamin dake mata aikin yace irin wannan lalura tana da kwan gaba kwan baya kana kuma kota warke sai anmata dafa'i sabida gaba. 



Rashin maganarta dai na nan, saita kwana biyu batace da kowa komai ba amma duk abunda aka sakata xatayi. Duk da akwai burbushin lalurar a tare da ita amma damuwa itace silar wannan shirun nata. Mimi tasa damuwar mijinta a ranta sosai, abun kan bata mamaki wai ya Bature ko a wayar mama ya gaxa kira ya tambayi halin da take ciki.  Ita ba a ta tata domin daga ita sai kayan jikinta aka kawota kano babu xancen waya don ko kayan sakawa maternity gown din ya Faty wacce mama ke dinka mata ta kwaso ta kawowa Mimi take sakawa, sai kuma wanda mama ta kuma dinka mata.  Wannan damuwa ita ke kawo koma baya a lfyarta.  




Ta rame sosai tayi duhu sabida mayunkan da ake shafa mata na magani, ciki kuma ya koma dan qarami kai kace baifi wata biyu ba, bayan ya cika wata biyar har yana shirin shiga na shida.  Batacin abinci sai dole ko in sunci da Baffa, Faty na yawan fada mata in bata cire damuwa ba dan cikinta xai samu matsala tunda yanxu ma ana xargin cikin ya koma baya, ma 'ana saiya mai maita watanninsa. 





Yammacin laraba suna xaune ita da mama, TV kunne suna sauraran saudi Qur'an wacce ita ake kallo koda yaushe a dakin.  Ta kalli mama, a qoqarinta na kawar da tunanin Bature tace "mama bani lbrin Baba" mama ta kalleta cikin rashin fahimta, Mimi ta qara mata bayani da cewa "Baba yana sona?" mama ta shafa kanta tace "sosai kuwa Al amin yake sonki maryam. Kullum kina sabe a kafadarsa yana yawo dake ganin likita sabida Allah ya halicceki mai lalura." Baffa daya shigo tun daxu domin kawowa Mimi guava da ta bashi sallahu da xai fita ya kallesu uwar da yar gaba daya tausayi suke bashi.  Ya matsa gabansu yace "tabbas maganar fadima gaskiya ce maryam, da ace Al amin yananan yaga kin sami lafiya da ilimin da yake buri kuyi da bansan iyakacin farin cikin da xaiyi ba.  Don shidin yasha fadamun cewa yanason ki gajeshi ki xama lauya ita kuma Faty Malanje jinya,  duk da baya raye Allah ya hadaku da jarumar uwa ta tsaya tsayin daka ta cika qudurin daya mutu dashi." Mimi ta kalli Baffa cikin hawaye tace "in shaa Allah saina gina masallaci da makarantar islamiyya da nufin Allah ya kaiwa Abba ladan kabarinsa.  Baffa da mama suka amsa "Allah yasa."





Ranar laraba bashi da aiki a office sai dare,  da sanyin asuba ya tashi ya shirya daga masallaci ya wuce ko Farida bai fadawa ba balle yayi mata sallama. Ba a xancen Bature don basa magana dashi da ishaq din a dalilin Mimi, sabida ishaq din yayi yayi Bature yaje kano ko sato Mimi ne yayi suxo su kaita abroad a duba matsalarta yaqi a dalilin haka ya dena kula Baturen gaba daya, shima ya dena kulashi tunda a halin da yake ciki yafison kadaici sai suyi kwana 3 basu hadu ba sai a masallaci shima ko sahun sallah basa hadawa. Ishaq ne kuma kano ya nufa. 



A tsaya a hanya ya lodi fruit sosai hardasu coconut. Daf da shiga kano ya tsaya wata babbar store ya kuma siyan kayan masarufi dangin kayan tea da lemuka da biscuits wanda basu da illah ga lfy ko ga mace me ciki. 





Sanda ya isa kano ko taran safiya batai ba, kai kace anan ya kwana.  Gidansu Farida ya wuce suka gaisa yayi breakfast ya huta a sit room din gidan  ya sake sosai, suka dade suna hira da iyayen Farida ya kawo tsarabar da yayo musu ya basu.  Abbanta na tambayar yar lelensa, ishaq yace "wlh abba ban fada mata xanxo ba,  don cewa xatai saita biyoni, kuma  ga yanayin jikin nata ni kuma yanxu xan koma Mimi naxo. dubawa" abba yace "hakane kam" suka xarce da hirar ciwon Mimi Umma na fada masa cigaban da aka samu. Sai wajen 11:00 AM sukai sallama ya bar gidan 





Mimi yau dai antashi da miskilancin ko jikin ne ya motsa oho.  Silar kuwa shine; fauxa da taxo dubata takanas daga Lagos ta kwana biyu anan gidansu Mimin.  Mimi taji dadin xuwan fauxa kowa ya shaida haka don ko maganar da batayi xuwan fauxa yasa tanayi jifa jifa. Babyn fauxa kuwa wato maryam wacce fauxan ke kira "Mimi" tunda sukaxo Mimi ta amshe yar kuma yarinyar bata da rigima takan wuni a jikinta sai xatasha nono Mimi ke bawa fauxa ita.  Itama fauxan kuka take sosai da xata koma tace da Mimi in sunusi zai dawo qarshen wata xata biyoshi ta kuma ganin jikin. Tayi hidima sosai ta kudi data gaba,  don tunda taxo mama ta huta wankin undis din Mimi da hada mata ruwan wanka da sata alwala da bata magani.  Mama batasan Mimi nada masoya haka ba sai yanxu. Domin mutane ta ko ina barkowa suke dubiya wasu ta ganesu wasu kuma bata ganesu sai dai suce tare sukai skul da ita ko kuma dalibanta na legal.  Abun shaawa har qungiyarsu ta CDS sunxo kuma harda kudi suka hada ta hanyar platoon officer dinsu suka bada aimata magani. Ta samu alheri ba kadanba, wasu kudi, wasu kayan dubiya, wasu kuma magani ko tofi kuma duk wanda ya kawo tana karba ta bawa Mimi da kyakykyawar niyya tunda shi magani dace ne.





Tun bayan tafiyar fauxa Mimi ta burkice tayi kukanta da yan rigimarta Rashida da mama suka lallabata tayi shiru, ana cikin haka ishaq yaxo. 




Daga dakin Baffa bayan sun gaisa dakin mama ya shiga  suka xauna a falo aka taso masa Mimi wacce ta fara bacci. 




Tana ganinsa tasa kuka sabida tuna ya Bature da tayi,  shima nan take ya karanci dalilin kukanta. Da kyar ya lallasheta suka gaisa,  ya dunga yimata nasiha, bai mata xancen sulaiman ba itama bata tambayeshi shi dinba duk da azalzalarta da xuciyarta keyi nason jin halin da yake ciki.  Ta tabbatar Anty gaskiya take fada tunda gashi har ishaq yaxo kano dubata amma babu ko saqon gaisuwa daga sulaiman din.  Ta tambayeshi Farida,  yace tana lfy tana gaisheta batasan xaixo ba. 




Baffa ya leqo zai fita kasuwa  kamar yadda ya saba yakan leqo yayiwa Mimi sallama da kuma tambayarta abunda takeso ya siyo mata.  Yace "maryamu xan tafi me xan taho miki dashi?" tayi dan jum tana tunani, can kuma tace "alawar madara da kwan zabi dafaffe"yayi murmushi yace "yau baxa aci gobar ba kenan?"  kafin tai magana mama ta fito daga daki tace "Mimi banda abinki ina xaiga alawar madara?  Baffa ka bari xan bayar a siyo mata anan" yace "a a  xansa a nemo a kasuwa, kwan kuma xanyi waya akawo daga gidan gona saiki dafa mata" tace "to a dawo lfy" Mimi ma tai masa adawo lfy. 



Ishaq ya dawo da kallonsa kan Mimi, ya yaba kwarai da kulawar da ake bawa Mimi da gatan da take samu amma abun mamaki meke ramar da ita haka kamar me hadiyar allura?tunanin mijinta wata xuciyar ta bashi amsa.  Tabbas Bature bai kyauta ba da yaqi waiwayo AL 'AMARIN MARYAM  kuma dole inya koma ya bude masa wuta akan hakan koda xasu bata har abada. 



Ya fita waje yasa yara suka dunga shigo da kayan daya lodowa Mimi aka cika falon dasu sannan ya dawo ya xauna. Mama ta fito tana masa godiyar dawainyar daya sha, ya tambayi  mama "mama anya maryam nacin abinci kuwa? Dubi yadda ta qare ta lalace ya kamata a dunga kulawa kodan abunda ke cikinta" mama idonta ya cika da kwallar tausayi abunda ke cikin Mimi tace "wane abunda ke ciki kuma ishaq?  Ai muna tsammanin Dan cikinta bashi da rai, dubi yadda ciki ya qanqance wanda a lissafinmu yakai wata 5 amma Kullum baya yake. Dan dai kawai yanxu batashi akeba ta lfyarta ake"  




Ishaq ya dubi Mimi yana nazarinta da kallon qaramin cikinta yace da mama "banxo da kayan aiki ba dana duba nagani."  Mama tace "bari in dakko maka na Faty wanda take mata dasu" taje daki ta dakko masa. 





Ya karba Mimi ta kwanta kan duguwar kujera, ya auna cikin ya kuma yi checking dinta sosai. Ya cire abunda ke kunnensa yace da mama "komai lfy, kuma abunda yake cikinta da ransa, sai dai yana fuskantar baraxanar fita a mahaifa sabida yunwa da damuwar da take ciki" mama tace "to Alhamdulillah amma Faty tace zai iya maimaita watanninsa" yace "wannan ba lallai bane indai ta dage dacin abinci" ya dakko  jotter a aljihunsa ya rubuta wasu magunguna. Yace da mama "ko xa a samu wanda xai siyo wadannan magungunnan yanxu?" tace "eh bari in kira huxaifa" 





Taje dakin Huxaifa dake baccin asara ta tasoshi ishaq ya cire kudi a aljihunsa ya bashi yace yaje babban chemist don ba a samu a qaramin guri manyan magungunane. 




Babu dadewa ya dawo dake a machine yake ishaq ya karba ya rubuta mata yadda xata sha kana ya kwantarwa da mama hankali da cewa "wannan magungunan in tanasha ko batacin abinci baxata wahala ba kuma akwai nasa cin abinci dana qarin jini" 




Ishaq dai bai tafiba sai qarfe biyun rana don saida mama ta tsaidashi yaci abinci yayi sallah kana ya tafi, Mimi na hawaye tana cewa yagaida Farida. 




Bai isa gida ba sai bayan magrib, yana shiga Farida ta tashi ta rungumeshi tana cewa "ya ishaq ina kaje? Kasa na yini cikin jimami tun asuba sai yanxu?" ya sunkuya ya sumbaci cikinta yace "kano naje duba Mimi" tace "Allah? 😳" sai kuma tai rau rau tace "amma bakaje dani ba?" ya lallabata da cewa Mimi tana lfy kuma ta kusa dawowa.  Haka suka shafe daren ana hirar Mimi wanda ishaq ya lura tana kawowa Farida farinciki. 




Washegari da daddare har gida ya bi Bature wanda tun a harabar masallacin sallar isha yake masa magana amma Baturen ya shareshi kamar baiji ba.  A dai dai falo ishaq yasha gabansa yace "sulaiman dakata, ya xa ai dan rainin hankali tun dazu ina binka ina maka magana ka shareni?" Bature ya riqe kansa dake Sara masa yace "Bani da lokacin batawa, kawai fadan abunda yake tafe dakai" 





Ishaq ya danne bacin ran wulaqancin da Bature yayi masa yace "naje kano jiya, ga dukkan alamu maryam ta samu lfy sai dai tunanin wufintar da ita da kayi yana kawo koma baya a lfyarta. Yakamata kai wani abu akai, indai har soyayyar da kake mata gaskiyace ba iya bakinka ta tsaya ba" Bature ya taso da masifa yace "ni banxaci harda kai a masu cewa bason gaskiya nakewa Mimi ba,  Kalli yadda na koma sabida rashinta, inba soyayya ba mai zaisa inxama haka don bata kusa dani?" 




Ishaq shima cikin masifa ya balbaleshi da fada yana cewa "dole a xargeka a kan maryam duk duniya kallon mayaudari take maka, kayiwa yar mutane ciki a dalilin cikinka ta samu lalura ka kaita gida ka ajiye"  Bature ya fusata kwarai ya kaiwa ishaq naushi ya kauce ya riqe hannunsa.  Baqo daya shigo kashe wutar falon yaga suna shirin dambacewa ya shiga tsakaninsu ya nemi taimakon Baba me gadi wanda ya shigo dakyar ya rabasu suka fita da ishaq.  Bature ya kwanta a gurin yasa kuka, wai shi ake zargi da yaudarar maryam da wufintar da ita, matarsa, aminiyarsa, qanwarsa, kuma uwar dansa dake maqale cikinta to shi kuwa wane irin butulu ne shi daxai wulaqanta matar dake da wannan ranks din a gurinsa? Baqo yaxo dakyar ya dagashi ya maidashi bedroom yana bashi haquri don yaga sulaiman ya koma wani irin masifaffe tun bayan barin maryam gidan.




Acan kano kuma Audu ne ya samu labarin wani malami wanda ya kware sosai wajen maganin jinnu, an tabbatar masa da ingancin maganin mutumin.  Yaje sukai magana ya yaba da magungunansa don yaga duk abune irin na ahlissunnah, amma yace baya xuwa gida aje axo da Mimi.  




Ya kawowa su mama lbr, kuma a washegari suka shirya xuwa. Duk da anga sauqi kuma ciwonta baya tashi yanxu mama tace gara aje sabida wannan rashin magana ta Mimi yana damunta.  




Ranar da mama Baffa sai Audu dake jan mota akaje.  Sheshin malamin ya tambayi Baffa shin in ciwon ya tashi tana dariya ne?" Baffa ya bashi amsa "a a, kuka take in ciwon ya tashi.  Kuma in dai ta dawo hayyacinta abunda take fara tambaya shine ; tayi sallah?" yace "mashaallah,  anso haukatata ta hanyar sihiri, amma anyi dace tana addini sai abun ya tsaya a haka" Ansaka maryam gaba anyi ruqiuya ta kusan awa daya shiru, malamin ya miqowa Baffa wani turare a kwalba yace ya shaqawa Mimi a hanci.  Sai dai ga mamakinsu taqi bari a shaqa mata saida akasha dambe da ita sannan aka saka matashi a hanci.  




Ta burkice tanata ihu suka rufu ana mata karatu,  sai da suka kuma shafe awa sannan ya bada wata xuma a kwalba yace a bata cokali uku.  Aka bata tasha,  ya kuma miqo turaren yace a shaqa mata. Wannan karon babu musu ta shaqa tace "wash kaina" ya dubeta yace "me kikaji?" tace "jin turaren nayi har cikin kaina kuma kan kamar zai fashe" yayi murmushi yace "to Alhamdulillah"



Ya dubi su Baffa yace "to anrabu in shaa Allah" suka hau godia sunaiwa juna barka.  Ya hada magunguna da xuma wacce xata dungasha Kullum da safe kantaci komai da kuma dare kafin ta kwanta.  A cewarsa magungunan tsarin jiki ya bata wanda in an kiyaye yadda yace ita da ciwon iska in shaa Allah har abada. 





Ya fadi kudin Audu ya biya suka tafi.  A mota suna tafiya Mimi a baya ita da mama yayin da Audu ke driving Baffa na gefe.  Tace "ya Audu" yace "naam Anty Mimi" ta kuma cewa "ya Audu ciwon hauka nayi ko?" yayi shiru bai bata amsa ba sai kallonta da yake ta madubi.  Ta juya gurin Baffa tace "Baffa na haukace ko?" shima shiru yayi mata.  




Tace "ai ko baku bani amsa ba nasan ciwon hauka nayi dan Anty ta fadamun kuma shiyasa ya Bature ya kawoni gida ya ajiyeni yayi tafiyarsa" Audu cikin tsanar Anty da tausayin Mimi yace "Anty maryam ba ciwon hauka kikai ba, kuma ya Bature badan dan uwana bane wlh ba sabida lalurarki ya dawo dake gida ba.  Kawai dai akwai dalilinsa nayin hakan kuma nafi kyauta xaton fushi yayi sabida su mumy sun hanashi fita dake qasar waje" tai shiru tana tunani babu wanda ya qara magana, itama din daga haka tai bacci a cinyar mama. 




Tabbas kamar yadda malamin ya fada an rabu, don Mimi ta warke sosai. Tayi ragal sai damuwar rashin mijinta da kuma rashin cin abinci wanda har mama tayi fadan tagaji.  




Yau lahadi Baffa ya je daurin auren yar abokinsa ya dawo, mama ta tafi kaimasa breakfast dake bai karya ba ya fita.  Mimi da Dady ne kawai a falon Rashida na cikin daki tana bacci. 




Mimi nakan centre carpet kwance cikinta ya dameta da motsi, ta kalli Dady dake homework tace "Dady na xo kaji" ya matso kusa yace "gani maman Abuja" tace "tokaremun cikina irin yadda kake yimun dinnan, ya dameni da motsi" yace "to, sannu mama" ya xauna yasa qafarsa duk biyun ya danne mata cikin sosai cikin ya takure guri daya ya kasa motsi kamar yadda takesa Dady yayi mata Kullum. 



Suna cikin wannan hali mama ta shigo, ta dubesu a razane tasa salati wanda ya janyo hankalin Baffa dake daki ya taho da sauri ya dauka ciwonnne ya tashi.  





Ganin Mimi a xaune yasa yace "menene fadima?" ta nuna masa Mimi dake jikin kujera Dady ya take cikin tace "Baffa kaga wannan aiki da suke" ta kaiwa dady duka tace "daga mata ciki dan ubanka" 




Mimi tace "mama nifa nasashi, wlh damuna yake da motsi babu dadi shiyasa...... " Baffa yace "qaniyarki 🖐🏻 dan gidanku ba dole ya dameki da motsi ba bakyacin abinci." mama dai har yanxu kallonta take cikin mamakin wauta da danyen kai irin nata tace "inanan bansani ba xakiyi kisan kai, motsin ai shine lfy, da yana ciki xaki hanashi sukuni?  To wlh ki kiyayeni karkiga ina lallabaki Allah akan dannan sai nayi miki duka"  ta juya ga Dady tace "kai kuma dan banxa Kullum xancenka mama xata haifar maka mata ashe kaine me tayata kukashe matar taka" ya xaro ido yace "na daina mama, ni banason matata ta mutu" abun ya bawa su Baffa dariya suka dara a tare. 




******** ******* ********


Acan Abuja kuwa yau kusan kwana goma da fadan sulaiman da ishaq kuma tun daga ranar basu qara ganin juna ba, abunda basu tabayi ba a tarihin rayuwarsu ace suna gari daya amma sun kwana goma ko a waya basu tuntubi juna ba. 




Bature yasha wahalar da bai taba shaba a ratuwarsa cikin wannan kwanaki,  babu ishaq babu Mimi, ya tsani kowa ya tsani komai duniya ta masa xafi ya rasa inda xaisa kansa yaji sanyi. Ya   qara tara suma a fuskarsa da kansa.  Ya rame sosai kamar ba cikakken babarbare ba. 
Abinci inyakai bakinsa daci yakeji ga azabar ciwon kai daya sarqeshi. 





Ranar alhamis da abun yayi masa yawa saiya tura takaddar neman hutu xuwa ga DG.  Ko 30 minutes ba aiba aka kirashi ta landline din office din ya tashi yaje kiran mr Alex. 




Kallon sulaiman yake cikin tausayawa yace "baka fadi adadin hutun da kakeso ba cikin takaddarka?" yace "bansan kwana nawa tafiyar xata daukeni ba, inason xuwa ganin jikin madam ne, in da sauqi baxan dade ba." yace "to kaje duk sanda ka dawo saika dawo aiki, Allah ya bata lfy"  ya amsa yayi godia ya fita.  Mr Alex kallonsa yake cikin tausayawa, shi gani yake kamar sulaiman din ya tabu,  tabbas inyahana sulaiman hutu yasan yana iya ajiye aiki akan matarsa wanda baya fatan hakan don ma aikatarsu tana buqatar mutane irinsu sulaiman sabida gaskiyarsu adalilin matsalar zirarewar kudin rarar man fetur da ake samu Kullum acikin qasar nan wanda wasu masu fada aji suke wawushewa. 




A dai ranar wajen 9:32 pm ya shiga gidan ishaq,  ya samesu falo suna hira Farida na kwance jikinsa.  Ganinsa yasa ta tashi, shi kuwa ishaq fuskar shanu yayi yacigaba da kwanciyarsa tare da qure volume din TV.  Abun ya bawa Farida mamaki dan batasan sunyi fada ba. Kallon Bature take inda ya kuma ramewa yayi busu busu dashi tabbas ya mace itace gatan namiji yanxu da Mimi tananan da ya za ai tabar mijinta haka? 




Ya kalli ishaq yace "inason gobe inje kano xan dakko Mimi ko sun yarda ko basu yarda ba kota warke ko bata warke xan iya xama da ita haka" ishaq tunda Bature ya fara magana ya kashe TV din gaba daya, sai da ya gama yace "yes!  Kayi dai dai,  ko wayone kai musu ka satota xamu tayaka kulawa da ita ko Farida" tace "eh mun baka goyan baya 100% ka dawo da ita ko anan gidan saimu xauna tare"  daga haka hira ta balle suka xauna akaita plan din yadda xa a taho da Mimi gobe da dabarun da xaiyi ya satota.  Sun dinke kamar basuyi fada ba, sukaci abinci da ishaq ya bashi maganin ciwon kai ya dauki mota suka fita ya kaishi aski aka gyara masa fuska aka wanke masa qafa tare da yanke masa farce.  Ishaq ya kalleshi yace "harka fito kayi kyau  amma da kayi wani dugujunjun ai inkaje haka saika furgita mimin"  sai 12; 00 AM suka dawo, sukai sallama don yace da asuba zai wuce.  



A daren bacci yayi sosai sabida kawai yasan gobe xaije yaga Mimi kuma su dawo tare.



Qarfe hudu ya tashi yayi wanka ya hade cikin designers suit ya baza perfumes masu azabar qamshi kamar xashi neman aure, yasa jakarsa a mota yasha Coffee daga masallacin asuba ya wuce kano yana tuqi cikin nishadi yanajin fefen karatun qur ani. 




Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)


📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 6⃣3⃣

Dedicated to 
ANTY SIS 


Cikin daren juma'a suna kwance ita da mama akan gado, ta juyo ta fuskanci mama dake bacci ta qura mata ido tana kallon kamanin Faty da ya Bature a fuskar mama. Mama ta farka taga Mimi na kallonta babu ko qiftawa tace "meya faru? Ko jikin ne?" Mimi ta matsa jikinta tana cigaba da kallonta tace "mama" tace "naam autata" babu kunyar data sabaji a yau tace "yaushe xan koma Abuja?" mama ta kalli Mimi cikin mamaki ashe Faty tayi gaskiya da tace Mimi tunanin mijintane ya hanata watstsakewa. Ta katse tunaninta tace "sai kin haihu xaki koma" Mimi dajin haka ta tashi a raxane ta xauna tana kallon mama tace "nan da wata hudu zuwa biyar fa kenan?" mama tace mata "kwarai kuwa" tace "tab, wlh ni tafiya xanyi."  mama ta dubeta tace "au Mimi kin gaji da xama danine?" tace "a a mama ba gajiya nayi da xama dake ba, gani nai dai na warke kuma ya Bature ma ancan yana kula dani. Gara in tafi kema ki koma aiki" mama tace "to babu inda xaki dan gidanku, daga ke har Baturen ai ba hankali gareku ba, sai kin haihu xaki tafi inyaso ko randa kika haihu ne ki diremun dan kujecan ku qarata ke dashi"  




Tasa kuka tana cewa "ni wlh saina tafi Allah baxan xauna ba" mama najinta tai mata shiru har tagaji tai bacci sannan ta gyara mata kwanciya tai mata addua tace "rigimammiya ta xama sai kace yarinya abu kadan tasa kukan shagwaba tana bori,  in anmaidaki abunjan haka xaman rainonki xaiyi ko aikinsa?"





Da safe ta tashi fuska daure ita a dole fushi take ance baxata koma Abuja ba.  Sassafe akai sadakar wainar da Mimi keyi duk juma a tun kan tai aure, bayan an watse Baba lami daya daga cikin masu aikin gidan ta leqo dakin mama tace "mama ansauke ruwan wankan Mimi" mama tace "to sannu Baba lami" tasa Mimi agaba ta shiga bathroom din cikin daki tai wankan sabulu kana ta rakata waje tashiga bandakin tsakar gida ta kai mata ruwan maganin da Baba lami ta dafa tace "shiga maxa kiyi ina jiranki" Mimi ta shiga mama kuma ta koma daki ta matso mata maclean a jikin brush dinta.  (Haka Kullum ake mata bayan tayi wankan sabulu xatai na magani a bandakin dake tsakar gida, abunda yasa batayi a na cikin daki sabida baci tiles din keyi da maganin. Bandakin waje kuma siminti ne)




Tana fitowa mama ta bata brush tayi mama ta koma daki,  ta gama brush din ta daura alwala lokacin qarfe tara saura na safe.  



Sabida gudun da yake shararawa ya iso da wuri,  jikinsa rawa yake wanda baisan dalilin hakan  ba.  Faduwar gaban ta qaru dai dai lokacin da yayi parking kofar gidan, jikinsa a sanyaye ya fito ya rufe mota ya shiga gidan da sanda. 




A xaune ya tarar da ita akan kujera a bakin famfo ta idar da alwala tana xaune kawai, daure take da qaton towel wanda ya saukar mata har qasa da kuma qarami  akan kafadarta. 




Ya qura mata ido yana kallon bayanta, duk da bega fuskarta ba amma ya hango qanqancewar da tayi da kuma duhun da tayi. A jikinta taji ana kallonta,  ta dago takai dubanta bakin qofar.  Kamar a mafarki ta hangoshi tsaye hannayensa xube a aljihunsa,  ya rame sosai yayi fayau kana ya qara haske,  sai taga ramar tayi masa kyau. Kamar yasan ta kwan dashi a ranta, kodai gixo yake matane? 




Ta miqe ta nufeshi bayan sun dau tsahon 3 minutes suna kallon juna. Ta tsaya a gabansa tace "ya Bature" yace "Baby Mimi" tayi tsalle ta daneshi ya qara dagata dai dai tsahonsa ya mannata a qirjinsa, suka dunga sakin ajiyar xuciya a tare.  Sun dade a haka,  kafin Mimi ta tuna barinta da yayi ko waiyaye beyi ba bare kiranta a waya,  kai amma ta bada kanta, babu jan aji balle nuna masa ranta ya baci. Ta sauka daga jikinsa ta daure fuska ta fara kai masa duka tana cewa cikin kuka "shine ka tafi ka barni, nayi ta shan wahala ni kadai sabida na xama mahaukaciya ko?" ya toshe mata baki ya marairaice ya riqe kunnansa yace "na tuba maryam, wlh kina raina dake nake kwana nake tashi,  babu yadda banyi ba su mumy su bani ke sukaqi, dubi kikaga yadda na koma ba rayuwar jin dadi nake ba acan kewarki ta hanani sakat ishaq da Farida shedane akan hakan."  basusan da mutane a gurin ba sai da sukaji Anty tace "amma kedai anyi marar wayo. Sai da kika warke sannan ya dakko qafa zai miki dadin baki irin na maxa,  dacan mexoba sai yanxu?"  Mimi ta juya tana kallonta, ashe hardasu Baffa da mama da Umma a gurin.  Kunya ta kamata, wato a gabansu suke wannan rungume junan?




Baffa ne ya tsawatarwa Anty da cewa "ke meyasa duk kalamanki babu na alheri kona dattijantaka aciki?  Ina ruwanki dasu? Mtsew Allah ya shiryeki jamila" ya shige daki.  Mama tace "lale da Babana yanxu kake tafe? Shigo ciki mana" ya sosa qeya dan shima yaji kunya yace "wlh kuwa mama" yayi gaba Mimi na binsa suka shige dakin. 





Mimi tana gefen qafarsa kan centre carpet,  mama ta shigo ya sauka qasa suka gaisa. Sun dade suna hira yana tambayar jikin Mimi tana fada masa duk yadda akai bayan tafiyarsa.  Ya tausayawa Mimi dan tasha wuya ba kadan ba, ya dunga godiyar dawainiyar da mama sukasha da ita, mama tace suje su gaisa da Baffa fita xaiyi.  




Can ma dakin Baffa sun dade da shi suna hira akan ciwon Mimi,  sannan Baffa ya fita kasuwa.  Ya dawo dakin mama ya tarar da Mimi yadda ya batta sai flask din kunun tsamiya da ke gabanta, amma ta kasa sha gani take kamar baxai dawo ba.  Dawowarsa yasa ta saki ajiyar xuciya,  ta tsiyaya masa kunun a kofi ta miqa masa ya karba ya ajiye.  Mama tana shigo masa da kayan breakfast,  ta kawo kayan tea sannan ta xubo masa wainar shinkafa (masa) da stew ta ajiye,  ta koma ta xuba masa dumamen tuwon shinkafa miyar zogale.  Sai data cika centre table din tab da kayan abinci yanata yimata sannu, kana ta fita ta basu guri ta tafi dakin masu aikin gidan suna hira. 



Yana ganin fitar mama ya tashi ya xuge labulen falon ya koma kujera ya xauna ya janyo Mimi jikinsa,  ta kalleshi tace "nayi missing dinka" ya hada goshinsu yace "to nunamun a aikace my luv" ta hada bakinsu ta fara kissing dinshi tana romancing dinsa.  Ya saki jiki ya bar mata fagen, yau ta shayar dashi mamaki sosai daman ta iya irin wannan amma bata taba nuna masa ba?  Ganin yana neman fara sambatu ta rabu dashi don ya fara nishi.  Ya kalleta idonsa jajur yace "kinyi naki Mimi luv ni kuma bari in nuna miki kewar da nayi" ya sunce towel din jikinta ya dunga lasarta yana wasa da qirjinta dakyar ta tsaidashi ta hanyar nuna masa a gida fa suke cikin dakin mama.  



Rashida tana dakin Mimi tana baccin safe taji maganganu qasa qasa ta tashi ta dan leqo ta labule ta hangesu Mimi xaune dirshan akan cinyarsa shi kuma yasa bisa wuyanta yanata lasheta. Ta koma da sauri dafe da qirji tace "Mimi kinyi saar miji, kinsha wuya ada amma yanxu dadi yaxo Allah ya samu danshinki"



Ta kwaci kanta ta koma kan centre carpet din tana maida numfashi,  shi kuma lashe lips dinsa yake.  Ta qara miqa masa kunun data xuba masa, ya karba yana kurba yana bata itama tana sha, ya gama yaci masa ita kuma bata shaawar cin komai.  



Suna nan xaune mama ta shigo da sallama ta miqo mata waya Faty ce ke kiranta.  Ta dauka suka gaisa Faty tace "Mimi fate fate nai miki na tsaki amma babu dan aiken da xai kawo miki" Mimi cikin zumudi tace "Allah ya Faty? Har kinsa yawuna ya tsinke  ya Bature yaxo yanxu xai kawoni sai inci anan" Faty tace "to sai kinxo, ki sauri karya huce" 




Bayan kashe wayar ta kalli mama tace "mama dan Allah muje?" mama tace 'ni na isa in hana? Adawo lfy" ta tashi ta shiga cikin dakinsu ita da Rashida don shiryawa.




Ta qara dauraye jikinta a toilet, ta fito ta shafa mai ta ciro wata gown zata saka. Rashida ta tsaidata ta miqo mata wata atamfarta holland irin igbo wrapper dinnan (kalar ibo) dark blue ce sosai me adon orange atamfar tayi kyau sosai,  ta dinkata bata taba sakawa ba.  Mimi ta kalli atamfar tace "Rashida kya bani atamfarki me tsada in saka bayan baki taba sakawa ba?"  tace "Anty mimi ai kinfi atamfar a gurina, kuma kyauta na baki, ki karba ki saka kiyi kwalliya tunda da Bature xaku fita." Mimi tasa hannu biyu ta karba tace "nagode Allah ya baki dubunta Allah ya qara xumunci" Rashida taji dadin adduar Mimi tasan Mimi tafi qarfin suturar 100k ma, amma sabida karamci tana ta godia don anbata tufar da bata kai 30k ba. 



Ta daura zanin rigar fitted ce me dogon hannu, dake ta rame sai ta shigeta ta dan matseta kadan. Cikin ya fito dan kurcici, wuyan rigar wagege qirjinta ya fito ta sama. Ta daura dankwalin ta shafa farar powder tasa farin man lebe ta dan maqala barima, sai taga tayi kyau kodan ta kwan biyu bataga madubi bane? 





Ta fito falo ta wuce dakin mama yana binta da kallo,  ta fito da mayafin mama orange da takalmi shima plat orange ta yafa mayafin a kafada tace "ya Bature taho mu tafi" ya miqe yadan yaye mayafin data rufe qirkinta dashi ya qurawa qirjinta daya qara cika dam ido.  Kunya ta kamata tayi gaba tana cewa "saika taho"  



Suka tarar dasu mama a tsakar gida dukkansu,  sai a lokacin Bature ya gaida su Umma.  Mimi tana gyara mayafinta cikin xumudi ta riqe hannun Bature tace "mama xamu tafi"  mama kallon ikon Allah take, yau Mimi watanta daya da kwana uku cif tana xaune cikin qunci da rashin walwala amma cikin awa daya da xuwan mijinta mama taga farin cikin da rabonta da ganinsa a fuskar Mimi tun xuwanta sunan Faty. 




Bature ya katsewa mama tunaninta yace "mama xamu dade fa har gidan mumy xamu dan banjeba nan na sauka" tace "to adawo lfy, Allah ya kiyaye"  sukace amin suna riqe da hannun juna suka fita. 




Ta baje a kan centre carpet din falon,  Faty ta miqo mata farantin faten tsaki wanda yasha yakuwa, shiwaka da busashshen kifi ta cire dan kwali ta fara sha tana santi.  Bature ya dubi Faty yace "dan Allah tsefe mata gashin nan,  inaga rabonta da kitso tun wanda Farida tasa akai mata acan,  kan duk ya cude ko tsagar ba a gani" Faty tace "to gaskiya kam ai bata gyaran gashi akeba a lokacin shiyasa bamu kula kanba" ta dakko kibiya tahau saman kujera tanawa Mimi tsifa qura na tashi akan, tace "tab, ga yanda qura ke tashi kuma ni sainaga gashin ya kuma haukata da yawa, kodake ance gashi bashi da xuciya in ba a gyarashi yafi fitowa."   sunata hirarsu Bature na gefe yanawa Mimi sub awayarta wacce yaxo mata da ita yanxu ya kunna yasaka kudi. Mimi nata aikin shan faten. 





Ahmad yayi sallama ya shigo, idonsa Mimi ya fara gani yace "kai lallai maryam jikin yayi sauqi har an fito?" sai a lokacin yaga Bature ya qara cewa "au ashe tare kuke yaushe a gari?  Daga xuwa har kun mayarmun da mata baiwa kunsata tsifar kai" 





Kukan Mimi ya katsesu, suka dubeta a tare da tambayarta menene?  Ta kwabe baki cikin tsabar shagwaba da rigimar data koya tun bayan fara ciwo tace "Ba ya Ahmad bane ya dena sona"  suka kalli juna suna qunshe dariya, Ahmad ya matso kusa da ita yace "Mimi wayace miki bana sonki"  ta qara narkewa tace "da kana sona kana ji dani kana cemun mimina ko kacemun autarmu, amma yanxu duk ka dena"  yadan dara kadan yace "haba Mimi,  ba dena sonki nayi ba. Gano nayi gatan yayi miki yawa,  ga mama da Baffa, ga ya Faty da ya Bature, sannan ga mumy da Dady.  Shiyasa nace toni bari in xama Faty ita kadai tunda ita duk anbarta an tare a gurinki"  ta xunbura baki tace "to nidai kaci gaba da sona kawai" yace "to angama ranki ya dade autarmu" suka dunga dariya a ciki karta gani ta kuma rigima. Dake kitson ya tsufa babu dadewa suka gama tsifar suka tafi. 




Saloon ya kaita, suka wanke mata kan akai steaming, basu da irin mayukan da take retouching dasu shiyasa ba aiba.  Yana zaune akai mata aka wanke qafa sukai mata gyaran fuska.  Ta fito ras, gashin ya kuma cika da tsaho ta bakin Faty. 




Sha biyu da rabi sukabar gurin, gidansu wato NNDC ya wuce da ita.  Suka shiga falon komai yayi qura, da takalmansu suka taka har master bed room din.  Yayi qura sosai har rumfar gadon.  Yaye bed sheet din ya dage rumfar gadon,  ya janyota suka fada kan gadon da babu shimfida.  





Ya qura mata ido can kuma ya fara romancing dinta sosai,  itama ta tsinci kanta dason kasancewa dashi ta fara mayar masa da martani har takai ga balle masa botiran shirt dinsa.  Sun maqale sunata yamutsa juna. Ya dakata tsam daya tuna last kwanciyarsu data nuna bataso yayi forcing dinta a qarshe ta tashi da ciwo,  wannan dalili yasashi fasa abunda yayi niyya ya hadiye xalamarsa a tunaninsa insunyi ciwonta xai iya tashi kuma dole xa a gane dalili tunda saitayi wanka.  Ya yunqura da nufin tashi,  Mimi ta riqeshi ta marairaice tace "ya Bature ina xaka? Meya tsaidaka?" yadan fara qinqina "Mimi Baki da lfy ne" ta qara shigewa jikinsa tace "nifa na warke dan Allah karka barni haka kaxo muyi soyayyarmu" baice komai ba ya xameta ya kwantar ya shiga toilet.  Tabishi da kallon mamaki,  meyasa maxa ke hakane?  Da itace bataso shi yakeso da koxata mutu sai yayi amma take shine bashi da raayi yanxu ya gujeta.  Tace "nima maganina kenan rashin jan aji ya jawomun amma xakasan kayi da yar halak saina rama" 




Ya fito da alwalarsa, yayi shirin masallacin juma a. Bata nuna masa bacin raiba ko a fuska, yace "taso in kaiki gidan Audu inje masallaci in dawo sai muje gidan mumy" ta miqe ta bishi ya rufe gidan suka fita.  




Ya kaiwa yasmin ita yace ga ajiya nan ya kawo, tace "to ya Bature"  dake masallacin sharada yaje bai jima ba ya dawo itama tayi sallar suka tafi.  




Sun tarar mumy a Ita kadai Dady bai dawo masallaci ba,  ta rasa inda xata sakasu.  Ta hada musu abinci sukaci tana daga xuwa kaje ka tattagota?  Yace "mumy saloon na kaita kanta duk ya cude" bayan sun gama cin abinci suka dawo kan carpet suna hira. Dady ya shigo daga sallah,  Mimi tayi saurin jan mayafi ta rufa a kanta tana gaisheshi. Bature yana harararta ya riqe kafadunta ya xaunarta yace "Dady ya yafe tsugunan gaisuwarki, ki daina takura kanki"  mumy ta dakko kayan kitso tace da Mimi "matso in kitse miki kannan, babu dadi xama da tsifaffen kai" Mimi dai tana kunyar Dady ta cire dan kwali aka fara yimata zanen hannu.  Bature kusa da Dady sunata hira, little ta shigo daga skul take dauke da jakar makaranta.  Ta kalli mumy dakewa Mimi kitso tace "kai mumy babu nacin da banyi ba kiyimun kitso kinqi sai gashi yanxu kinawa Anty Mimi, wlh nima sai kinmun" Dady ya jawota ya xaunarta gefensa yace "sai haquri uwata, kinga fa ita Mimi yanxu ta fiku matsayi gurin mumy,  na farko  itadin yarta ce, matar danta datafiso,sannan kuma uwar jikanta nan gaba kadan" mumy tace "kai  Dady wayace maka shi nafiso?  Ga autata nan me sunan mamana" little tai karaf tace "to tunda kinfisona nima kimun kitso" tace "xan miki Kinji uwata" Dady ya tashi ya shiga dakinsa ya fito da wata jaka, yaxo ya xauna yana xuge jakar yana cewa "mami ce tayo aike tun last week aka kawo na manta sai yanxu dana ganku na tuna" Suka bude jakar, kayan jarirai ne unisex da yawa amma overall sunfi yawa masu kyau da suck da takalman jarirai.  Suka dunga dagawa Dady yace "Mimi tace a bawa afara ajiyewa xata dunga aikowa dasu" suka dunga daga kayan ana yaba kyansu, Mimi dai kunya ta hana ko kallon kayan tayi bare ta taba.  Bature ya daga wata safa yace "wannan yar safa kamarta yar tsana cewa akai mata doll Mimi xata haifa?"  little tace "ya Bature ai safar hannuce" yace "Ok" tace "now tell me Baby girl kakeso ko Baby boy" yace "bani da zabi little duk wanda Allah ya bani inaso" tace "to Allah ya baku kamar ni kuma Baby girl" yace "haba little ya xakiyimun fatan haifar kamar ke ai kafin ta girma munsha wahala, kuma wannan kafirin iyayin naki mukaishi ina in muka haifi irinki" Mimi ta dunga yimusu dariya. 



Dady yaja Bature daurin auren dan abokinsa,  Mimi kuma mumy ta jata bed room dinta tana shirya drawer Mimi na kwance kan gado suna hira,  babu yadda Mimi bataiba mumy ta bari ta shirya mata kayan amma taqi tace tai hutawarta ita data tashi daga ciwo. 



Sunanan har akai sallar la asar, mumy na mitar ina suka tafi suka dade haka, ya bar Mimi bai maidata gida ba har sai lokacin shan maganinta ya wuce.  Suna haka Lubna taxo,  ta xauna kusa da Mimi da cewa "a a yar tsanar ya Bature, yau nayi farin xuwa na tadda ki gidan ya jikin?" Mimi bata fuskanceta ba tace "wacece yar tsanar?" Lubna tace "ke mana"  tace "yaushe kika sakamun wannan sunan?" Lubna tai far da ido tace "tun washegarin kaiki da naga yadda yake daukanki kamar yar tsana na saka miki" Mimi tahau qifta mata ido wai tayi qasa qasa kar mumy tajisu.  Lubna ta matsa tai qasa da murya tace "ikon Allah wai Mimi dauke da cikin ya Bature, to ya akai kukai cikin? Cewa yake kixo kuyi ko ke kike kai kanki?" Mimi ta galla mata harara tace "ki xama quda ki shiga dakin ki gani mara kunya"  Lubna ta kuma kecewa da dariyar shaqiyanci ta juya ta kalli mumy taga hankalinta baya kansu ta kuma cewa "ana ganinku simi simi kamar mutanen kirki, amma wai kun iya lalube juna" Mimi ta yunqura xata kaiwa Lubna duka ta kufce tai waje tana dariya, Mimi ta bita a dai dai kofa sukai karo da Bature daya shigo.  Ya riqeta ya tambayarta menene?  Tace "Lubna ce ta tsokaneni xan bita in rama" yace "yi haquri kyaleta xan rama miki yanxu ba daya kukeba karki fadi garin binta." taqi haqura ita kuma lubna sai gwalo take mata, sai da mumy tasa baki ta haqura. 




Basu bar gidan ba sai bayan isha shima saida mumy ta matsa masa sannan yaje ya siyo mata kayan ciye ciye ya maidata.




Washegari ma yaxo ya dauketa suka dunga xaga gidajen yan uwa har gidan hajja, sunji dadin ganinsu ta dakko musu maganin data karbo musu na tsari ta basu da bayanin yadda xasuyi amfani dashi ta kuma maimaita Bature yayi amfani dashi ko ransa ya baci don takakkiya tayi har garko ta karbo musu tana cewa "inbanda iyayen yanxu sa turaku Abuja babu tsari ai dole a jefeku bare anga sai daukaka kuke samu" bata barsu haka ba sai da tayiwa mumy waya tace ta kula su tabbar Bature yayi amfani da maganin.  Ai kuwa mumy ta hanashi sauka a gidansa anan gidanta ya xauna kuma ta tsaye sai da yayi amfani da maganin. 




Acikin weekend din ya dunga yawo da ita gidajen family nd friends har garko sunje dangin iyayensu mata nan madai magungunan tsari aka hado musu, kuma ya shige mata yayi mata famfo ta taho su koma gidansu xai kula da ita akai sa a  itama so take ta bishi  ta hau ta xauna tace "nimafa ya Bature so nake bika, baxan xauna ba qafata qafarka." yace "yawwa Mimi luv" yana dariya a fili yace "na shiryawa su mumy tsiya kenan akwai daru"  





Babu wanda ya nunawa yaxo tafiya da Mimi ne kuma bai nuna musu ga ranar da xai koma ba har sai ran monday da safe,  ya shirya ya hado kayansa kaf sukai sallama dasu Dady da mumy yace xai koma. Mumy har da cewa "amma dai jirgi xakabi ko?  Naga yau da aiki kaso kayi latti" yace "a a mota xan tafi, sai gobe xanje aikin. Yanxu xan biya muyi sallama dasu Mimi" tace "to madallah Allah ya kiyaye hanya ai gara ka barta nan inta haihu ta koma" a xuciyarsa yace "tab ashe kan lokacin kewar Mimi ta xautani" mumy har bakin mota ta rakoshi tana maimaita masa ya kula taji dadi sosai dabeyi xancen tafiya da Mimi ba.  Shi kuma dariya yake mata a ransa.



Acan gidansu Mimi taci kwalliya kamar yadda ta saba tana jiransa,  amma yau taga yayi lattin xuwa tunda sassafe yake xuwa. Kuma ko ita bai fada mata yau xai tafi ba. 




Ta kalli a gogon wayarta, takwas harda kwata, shi da ya saba xuwa bakwai da rabi, to meya tsaidashi yau?  Mama ta kawo mata awarar data saka aka soya mata da kwai tace "Mimi har yanxu bakici awarar nan ba sai ta huce?" ta kalli mama duk dauriyarta ta qare tace "mama kinga ya Bature shiru har yanxu baixo ba anya kuwa lfy?"   mama tace "Mimi meyasa baki da dauriya kan sulaiman ne?  Tunda kikaga bai xoba ai wani uxurin ya tsaidashi,  nidai kici awarar karkisa inyi wahalar banxa."  ta kalli awarar takai hannu ta faraci, sai dai sam batajin dadinta duk kuwa da itace tasa mama tai mata tun jiya.  



8:33 AM yayi sallama ya shigo,  suka gaisa da mama dake tsakar gida kana ya shiga dakin Baffa suka gaisa yayi musu sallama da cewa xai wuce yanxu.  Mama dai sai da gabanta ya fadi, don tasan da wuya aiki be dawo baya ba, Mimi da tunkan ta ganshi take cewa xata tafi Abuja bare yaxo ya kwan biyu? 




Yana shiga dakin mama Mimi ta taso ta rungumshi tana ajiyar xuciya,  ya shafa kanta yana murmushi tabbas ta fada tarkonsa, game din kuma xai fara daga yanxu.



Ya jata suka xauna kan kujera yana murmushin Luv yace "Mimi nifa nayi harama wucewa xanyi"  ta kuma shigewa jikinsa tace "cewa xakai wucewa xamuyi  ai daka fadamun tun jiya na hada kayana"  yace cikin jimami "ai banajin su mumy xasu bari muje tare, sunce sai kin haihu." ya zareta jikinsa yace "bari inje karnayi latti inason isa da wuri sai anjima my luv ki kula da kanki" ya saka takalminsa sau ciki yayi waje. 




Tabishi da kallon mamaki,  mekenan hakan?  Ya fasa tafiya da ita kamar yadda ya fada mata jiya ko kuma dai mumy ce tayi masa fada shiyasa ta ganshi a sanyaye?  A fili tace "tab wlh baxata sabuba, wai bindiga a ruwa"  ta miqe da gudu tayi tsakar gida,  har yakai bakin qofar da xata kaishi soro, mama kuma natayi masa fatan isa lfy dan hankalinta ya kwanta da taga ya fito kuma bataji wani raddi daga Mimi ba. 





Ta rungumeshi ta baya tsam tace "ya Bature xan bika" ya juyo ya gyara mata kwanciya kan qirjinsa kana ya kai dubansa ga mama yana dan sosa kai yace "Mimi nima inason tafiya dake, amma su mumy sunfison ki xauna nan" tace "babu ruwansu damu, ai kafisu iko akaina muyi tafiyarmu mu kyalesu ni na warke" mama tayi mata daquwa tace "🖐🏻gidanku uwar marasa ta ido, wato babu ruwanmu ko?"  Baffa ya fito xai fita, matan gidanma duk suka fito jin kulle kofar Baffa xasuyi masa a dawo lfy.  Ya tambayi abunda ke faruwa,  kafin mama tayi magana Mimi take jikin ya Bature tace "ni Baffa ya Bature nakeson bi, kuma su mama wai saina haihu." Baffa ya kallesu duk su ukun yace "to ni narasa bayan wanda xanbi cikin ku,  in nabi bayanta(mama) kisamu gaba da rigima, ke kuma maryam innabi taki uwarki tahau fushi dani tace na barki kin tafi tunda bata da juriya a kanki"  Anty tace "eh gaskiya ne sabida angama da kai ba, am maidaka namijin hotiho" Bature dai yana riqe da Mimi data fara kuka, yaga abun yaqi qarewa ya dakko waya yayi text wa Faty. 




Mama tace "gaskiya Baffa kawai  ka hanata tafiya" Mimi ta fara kuka da qarfi tace "mama ni gaskiya baxan xauna ba saina bishi"  Baffa yayo mata daquwa yace "qaniyarki 🖐🏻 saidata gama wahala dake tun bakisan wanda ke kanki ba shine yanxu xaki gujeta"  Rashida ta fito xata tafi aiki,  ta kalli drama din da ake Mimi jikin Bature rungume ko kunyar su Baffa bataji tace a hankali "da gaskiyar ki Mimi, koni na samu irin wannan tsalelen mijin banga abunda xai xaunarni gida ba koda kuwa baya sona, bare ke abun burgewa bayan kyansa ga kudi uwa uba kuma son da yake miki"



Sunanan jugum jugum, Baffa sai lallaba Mimi yake ta haqura in ankwan biyu ya kuma xuwa tabishi, amma taqi yarda saima kuka da take Bature na lallabata.  





Faty tai sallama ta shigo gidan,  ko gaishesu batai ba ta kai kallonta kan Bature da Mimi dake riqe da juna. Ta miqowa Bature kujerar roba ya xauna, Mimi ta dane cinyarsa ta kuma qanqameshi.  Faty ta matso kusa da Mimi,  mimin ta runtse ido tace "ya Faty karki dakeni, ni ya Bature nakeson bi"  ta shafa fuskarta tace "ba dukanki xanyi ba maryam duk abunda kikeso shi nakeso" kana ta shige daki.   



Anty tace "to uwar iyawa da kwainane taxo yanxu kuma sai yadda mukagani" Bature abun ya bashi dariya amma ya gimtse, su wadannan matan kwata kwata basa girma.




Faty ta loda kayan Mimi a qatuwar jaka ta jawota ta fito da ita,  ta koma ta fara fito da magungunan Mimi,  suna kallonta.  Tace "Mimi badai mijinki kikeson bi ba?" tace "eh" tace "toh maxa ga kayanki nan,  Allah ya kiyaye hanya ya qara baki lfy" mama ta dubeta xatai magana. 





Faty ta rigata da cewa "mama indai har na isa da maryam ki barta tabi mijinta,  ku kalli Mimi da ya Bature kowa yana musu shedar sunada kunya, amma yau da kuke qoqarin rabasu kalli yadda suke xaune gabanku"  mama jiki a sanyaye dan ta hango gaskiyar maganar Faty tace "kin isa da maryam fatyma, tunda kinyi hukunci suje Allah ya kiyaye hanya" 




Umma baqinciki ya turnuqeta, dan ita bataqi ace auren Mimi ya mutu ba a yanxu kuma ta auri jafar ta xauna a qarqashin ikonta,  dan tasan jafar baiko kama qafar Bature a dukiya ba balle Mimi taji dadi har tafi sauran yayanta. Kuma dama nufinta in auren ya mutu ko jafar bai nemi auran Mimi ba xatace yaje ya nema yadda xata gasa Mimi a matsayin surukarta ta cikin ruwan sanyi.  Amma da alama burinta baxai cika ba ganin wannan sa-toka -sa -katsi da ake yanxu.  




Cikin lumana da nuna soyayyar bogi tace "anya fadima kya daka ta Faty ku tura yarinyar nan Abuja bata gama watstsekawa ba?  Kalli fa yadda muke fama da ita anan in ciwon ya tashi dukkanmu bare acan ita da miji kawai.  Mama tace "to ya xanyi Umma?  Kar inje in hanata binsa inya tafi ta tayarmun da rigima ta hanamu xaman lfy daga haka ciwo ya dawo" Umma cikin fusata da amsar mama tace "aikin banxa,  ai duk laifinku ne. Kunbi kun shagwaba yarinya duk ta sangarce saikace yar shekara uku intana abu." ta juya ta shige daki cikin qunan rai.  Suka bita da kallon mamaki, Anty ta saki shewa tace "toh?  Ke kuma meye naki ciki khadimul shishshigi?"





Baffa ma ya wuce kasuwa, Mimi kuma ta dakko wata kujerar ta xauna gefensa Faty tana cigaba da fito da duk abunda tasan mallakar Mimi ne tana ajiyewa a waje. 




Mumy ta shigo gidan baxata,  takai kallonta ga Bature da Mimi dake tsakar gidan akan kujerun roba suna facing juna hannuwansu sarqe.  Tai saurin dauke kanta, mama jin sallamar mumy ta fito tana cewa "Addah kece yanxu?  Kodai kinada masaniyar tafiyar tasu ne?" mumy tace "jikina ne yabani anan ana daru da Mimi, har naje gurin aiki na kasa xama na taho"  mama tace "ai kuwa dai taqi xama fafur gashinan an hada musu kayan tafiya"  




Mumy ta harari Bature ta nufi dakin mama tana cewa "Mimi xo kiji kinji uwata"  suka shige ita da mama, Mimi ta tashi xata bisu amsa kiran mumy Bature ya riqo hannunta yace "duk dadin bakin da mumy xatai miki karyi yadda,  ki tubure ni zaki bi,  in taqi kisaka ihu." Mimi tace "to ya Bature xanyi duk yadda kace" yace "dat is gud ma luv" ta shige ciki.  Shi kuma ya qara miqewa kan kujera ya dora qafa daya kan daya yana dariyar mugunta,  yasan ya dora Mimi ta hau tayi derere da wuya ta yadda da romon bakan su mumy.  




Ya tashi ya shiga falon ya xauna su kuma suna uwar daki,  kamar yadda ya xata mumy tasa Mimi a gaba tana mata dadin baki na ta haqura ta haihu sabida lfyarta da abunda ke cikinta, babu kalar lallashin da mumy batai mata ba.  Ya kwashe da dariya harda kyakyatawa lokacin da yaji Mimi tace "mumy ai shima ya Bature yana kulawa dani, ni nafison mu tafi tare" mumy cikin quluwa tace "kenan kinfison shi akanmu?"  ya saki dariyarsa a fili da yaji Mimi tace "eh nafison xama  dashi donshi....." kafin ta qarasa mumy ta duma mata dundu, ta miqe tayo falo da gudu tana fitowa ya tare abarsa ya rungumeta yace "well done my dear" suka xauna suna qus qus dinsu ita da mama. Shi kuma ya raka Mimi kitchen ta dumama musu awarar da mama tai mata a microwave ta tsiyayo musu kunu a cups suka fito falo suna ci cikin nishadi. 




Mumy ce ta fara fitowa ta gansu,  taso su hada ido da Bature tai masa harara amma yaqi yadda su hada idon yayi qasa da kansa,  ta matso kusa tace "ai dama nasan kaine ka hure mata kunne shiyasa taqi xama" mama tana fitowa tace "itama da halinta Adda, tunkan yaxo take cemun xataje Abuja gurinsa"  





Mumy tace "to tunda kun nace sai kun tafi tare saiku bari xuwa gobe nayi waya garko Yadukko taxo kuje tare kuma nayiwa Aisha waya ta dawo ku tafi tare. (yadukko yar uwace ta kusa ga hajja kakarsu Mimi, takanxo lokaci xuwa lokaci kano gurin hajja ta kwan biyu ta koma don mijinta ya mutu kuma tagama aurar da yayanta kaf) yace "to mumy muna godia" sai alokacin ta samu damar fallara masa harara tace "ka dena murna, don rahoto xan tura yadukko yimun, tana fadamun abunda baimun ba xanxo in taho da ita" yayi shiru yana sosa kai. 



Yinin ranar suna maqale da juna cikin dakin mama, yayin da maman keta faman hadawa Mimi kayan da duk take ganin xasuyi mata amfani intaje can.  A daren yadukko taxo Aisha ma ta dawo,  tanaji mama na cewa yadukko dan Allah ta kula da duk lokatan shan maganin Mimi da kuma turare karta bari Bature ya hana aiwa Mimi turaren.  Yadukko dake over acting ce tace "shidin banxa ya hana? Dako naci qaniyarsa." mama tana dariya tace "yawwa yadukko" tasan bata da wasa shiyasa suka yanke shawarar dakkota ita da mumy. 




Washegari da safe mumy taxo,  taxo da kaya niqiqi tabawa Mimi tayi tsaraba.   Aka hada da kayan da mama itama ta siyo mata aka cika highlander dinsa taf da kaya har sai da motar tai qasa.  Mimi tasha kwalliyarta cikin sabon lace din da Faty ta kawo mata jikinta har rawa yake xasu tafi, bakinta kuma yaqi rufuwa.  




Mama jikinta yayi sanyi da wannan rawar kan Mimi, sai take ganin kamar ajali ke kiranta in banda haka ai Mimi mai tsananin kunya ce.  Mumy ma tunaninta kenan, itadai kam wannan tafiya bata kwanta mata ba dandai babu yacce xatai ne. 



Wajen qarfe tara suka gama shiri tsaf su yadukko da Aisha har sun fita sun shiga mota, su Mimi ake jira da suke sallama da iyayensu.  Jikin mama ya kuma sanyi lokacin da Mimi hartakai qofar fita ta dawo ta riqe hannun mama tace "mama ki yafemun" mama tace "bakimun komai ba maryam" tayi murmushi tace "ni dai kawai ki yafemun" tace "na yafe miki maryam Allah ya hada fuskokinmu da alkhairi"  ta juya ta riqe hannun Bature dake tsaye bata qara waiwayowa ba suka fita.  Mama ta faki idon mutanen dake tsakar gidan ta share kwallah.  Mumy kuwa kasa daurewa tayi ta bisu waje. 




Ta samesu suna shirin shiga mota ta kalli Bature taci serious tace "sulaiman ga maryam nan, amana, duk sanda ka dubeta ka tuna cewa ita din marainiya ce." ya xago ya dafa kafadar mumy yace "na karbi amanar ki,  in shaa Allah baxan baki kunya ba" ta rungumeshi shi da Mimi ta juya ta koma ciki. 




Sun daura sit belt ta dubeshi ta dafa hannunsa tana murmushi tace "SULAIMAN meka tanadarmun a gidanka?" ya kafeta da ido yace "MARYAM soyayya, qauna,  kwanciyar hankali da kuma kulawa wacce baki taba ji ko gani ba. Sune abunda na tanadar miki in shaa Allah"  ta murmusa suka sarqe hannyensu tace "Allahu yasha'u" 



 Su yadukko dake bayan mota sukace "amin" yayi Addu'a ya tada mota suka hau titi. 




Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)


📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 6⃣4⃣


Dedicated to 
ANTY SIS


Sun isa lfy, sukayiwa kano waya suka sanar, sai a lokacin mama ta samu kwanciyar hankali tacigaba da harkokinta. 



Mimi tayiwa Farida waya ta fada mata sun dawo, babu jimawa suka shigo da ishaq. Mimi da Farida suka rungume juna suka sa kuka kana suka furta sunan juna a tare.  



Bature ya fada musu yadda ya dakko Mimi,  ishaq yana dariya yace "shege sulaiman kasan takan tsiya" yayi dariya yace "ai mumy bata barni haka ba, sai data hadoni da wata kakarmu yar tijara muka taho tare" haka suka xauna sunata hira,  ya tashi yayi wanka ya shirya suka fita da ishaq yace da Mimi xaije ganin wani gidan mai da yakeso ya siya.  Yayiwa safna waya, tana gurin aiki yace inta dawo ta biyo gida gurin Mimi ta tayata gyara bedroom dinsu.  




Safna tana dawowa ta shigo suka hadu ita da Aisha, suna gyara dakin Mimi na xaune sun hanata komai sunce ta huta. 



Suka gyara dakin tsaf safna ta ware kayan wanki ta hada wadanda suke buqatar sirri ta xuba a washing machine ta wanke ta shanya suka fesa turaruka masu qamshi.  Sai yamma suka tafi. 




Bai dawo gidanba sai goman dare, lokacin harta gaji da jiransa.  Ya shiga wanka, ta bishi bathroom din, ta sameshi a bayan labule cikin shower ta rufe masai ta xauna akai tace "ya Bature har yanxu baka gama ba?" yace "eh Mimi luv,  kinsan yau ango nake dole in cuccuda sosai" tace "hmmmm" kawai,  ta gaji da jiransa tayi brush dinta ta fita taje tai shirin bacci ta kwanta. 



Tajishi jikinta yana lasarta, ta watstsake ta kunna bed side lamp ta dubeshi. Ya sakar mata murmushi yace "Mimi luv ya kika tashi?" ta tureshi, ya qara shige mata yana romancing dinta tace "Stop it" yace "haba Mimi luv yaushe rabon da mu kasance haka" yacigaba da abunda yake,  tace "fyade xakaimun ya Bature?" 




Jim kalmar fyade data ambata ya tsaida abunda yake yana dubanta.  Ta qara da cewa "lokacin da nake buqatarka ranar a kano ai qi kayi,  amma yanxu dake kaine kake buqata kana qoqarin forcing dina" jikinsa sanyi qalau yace "wlh Mimi bana qi biya miki buqatarki bane wancan lokacin don toxarci  ni kaina a lokacin ina da buqatar data fi taki. Amma na tuna cewar wancan lokacin kinqi na tilasa kika samu lalura shiyasa na haqura karnayi ciwonki ya tashi." ya janyota ya rungumeta  yace "Mimi tun a wancan lokacin nayi alqawari baxan kuma ba,  nayi na farko kinyi ciki,  na biyu kinsamu lalura in shaa Allah baxan na uku ba dan bansan abunda xai faru ba" ya kashe masu fitila suka kwanta,  sai taji tausansa.  Tayi bacci ta barshi  shikam sai da yayi da gaske ya runtsa.




Washegari bayan sunyi karatunsu na al qur'ani ya motsa jiki yaxo ya kwanta,  ta dubeshi tace "yau baxaka fita aiki bane?" yace "nayi dauki hutun 1 wk" Yadukko tayi knocking tace "maryam fito kiyi wankan an sauke ruwan." tace "to" ta fita sukayi wankan harda turare ta dawo, ya dakko xumarta ya bata tasha suka koma bacci.  Sai 10:00 AM suka tashi sukayi wanka da breakfast ya fita gurin cinikin gidan man.  Kafin ya fita saida ta tabbatar Anty Rabi da Farida suka shigo. 




Ranar ma cikin mutane ta yini dan safna ma ta kuma shigowa, sukayi ta riritata, ya Taheer ma ya shigo daya taso aiki. Safna har tausa tai mata, Mimi tana cewa "haba Anty safna ki bari mana Aisha taimun" tace "barni nayi miki matar yaya dan da bakyanan munga banu horonce mana yayi gara mu lallaba masa ke"  yauma sai magrib ya dawo,  tayi kwalliya tayi kyau.  Sukaci dinner ya dunga lallabata duk sai taji ya bata tausayi,  a take gurin taiwa kanta fada. Shin meke damunta har ta hana mijinta haqqinsa jiya?  Bai cancanci haka ba a gurinta, mutumin dake sonta tare da tattalin farin cikinta, ta manta lokacin da Badaru yake kwanciyar wulaqanci da ita kuma daga baya yacimata mutunci.  Tayi kuskure, ina laifin me sonka?  Jiya ta kwana cikin tsinuwar mala'iku sabida gujewa shinfidar mijinta. Ta dunga neman gafarar ubangiji,  ta juya ta dubeshi yana xaune kusa da ita yana matsa mata qafafunta dake kan cinyarsa.  Ta gyara xamanta, ta dakko qafarsa ta dora bisa cinyarta itama tana matsa masa.  Ya janye yace "barshi Mimi, keda baki da lfy?" ta kuma dawo da qafar kan cinyarta ta qurawa tafin qafarsa ido, jajur yake kamar qafar jariri yayin da qafar take fara sol kamar jikinsa gata doguwa mai dauke da yatsu dogaye,  takai lips dinta tsakiyar tafin qafar ta sumbata.  Ya lumshe ido, ya budesu ya kalleta tace "ya Bature ina sonka,  kayi haquri abunda nai maka jiya ka yafemun na mata mummunar fahimta" ya jawota kan cinyarsa ya xaunar, yace "na yafe miki maryam tun a jiyan. Kuma wannan dalilin yasa nake kuma macewa akan sanki, sabida duk sanda kikayi kuskure kina saurin ganewa Kuma ki nemi afuwa" ta kwanta kan jikinsa tace "inka shirya nima na shirya amsa kiranka" ya miqe ya sabeta sukai bedroom.  



Ba tare sun canja kaya ba suka fada gado, tunaninsa ya qare akanta, mace mai ciki sai bakai da gaske ba saita zautar dakai, an gurji juna  ranar. Ya haqura badan ya gaji ba sai dan karya wahalar da Mimi luv,  suka koma hira mai cike da soyayya kamar ba dare ba. Ya dakko wasu takaddu a drawer ya dawo ya kwanta yana fuskantarta. Ya miqa mata ta farko, ta karba taga takardar gidace a kano wanda yake unguwar Kuntau.  Sai ta biyun ita kuma takardar gidan gonace itama dai a kano kuma duk malakarsa ce dan sunansa ne jiki.  Ta dubeshi dason qarin bayani, yace "xabi daya acikinsu, inason mallaka miki" ta kafeshi da ido,  kamar yadda ya saba yayi qasa da kansa, indai ta ware masa wadannan dangerous eyes nata sai yayi qasa da kansa dan baya iya jurewa kallonsu fitina suke haddasa masa. Tace "ni kuma ya Bature?  Sabida me?" yace "sabida nayi niyya tun da dadewa, ginin gidanne ba a gama ba sai yanxu" tace "to, ka xabarmun wanda yafi dacewa dani ka bani,  kasan bani da wani xabi sai naka" ya matsota yana murmushi yace "nasani Mimi luv,  nima bani da mashawarcin daya wuceki. Ni a ganina ki xabi gidan,  na gama komai anxuba kayayyki, part 6 a ciki kowanne sama da qasa, yan haya kawai xaki xuba kuma kayan sakawa kawai xasuje dashi, sabida kar a samu matsala ma bank na bawa gidan akan 500k kowanne part a shekara,  su kuma xasu dora nasu su xuba yan hayar. Kinga kawai babu ruwanki da matsalar yan haya lokaci nayi xakiji alert. Inaga gidan xaifi kawo miki kudi akan gidan gonar. Ta shige qirjinsa tana hawaye tace "ya Bature nagode Allah ya qara budi ya rabaka da iyaye da duniya lfy ya baka xuria mai albarka. Allah ya sa kayi kyakykyawan qarshe." yayi mata wata irin runguma kamar xai ballata,  yaji dadin adduarta sosai. Ya nuna mata vedio din gidan, ta dunga santin kyan gidan da tsarinsa lallai dole ace haya 500k wannan gida kamar hotel,  tace "ya Bature gidan yayi kyau dama mu koma. Yaja hancinta yace "sai dai inkinaso in munje kano mu sauka ciki mu kwan biyu kafin asa yan haya." Ya dago fuskarta daga jikinsa yace "amin Mimi luv,  amma ki nunamun godiar a aikece mana" ta gane nufinsa.  Ta baje kwanyarta ta ajiye kunya guri daya ta fara masa wata salon soyayya,  ya xauce mata tunkan aje ko ina ya fara surutai.  Sai data tabbatar ta cire masa duk wani kwadayi akanta sannan ta kyaleshi.  




Ya dubeta cikin burgewa yace "kai! mimi luv kin hadu fa qarshe, shiyasa akemun yanga ko?" taja karan hancinsa tace "hmm, ni mamakinka nake.  To lokacin da bananan ya kakeyi" yace "Mimi ai sai da kwanciyar hankali sha'awar ke xuwa. Wlh lokacin ko kadan bana tuna wani abu wai sex, ke nifa lokacin inaga mace na xama" ta sheqe masa da dariya, ya dauketa suka tafi wanka suna fitowa suka fara nafilfili dan shima yanxu baya baccin dare inbai sallar ba bayajin dadin bacci Mimi ta tarbiyanceshi akan hakan. 



 Washegari yana gida, ita kuma Farida ta shigo suka hauka hau hira.  Farida ta fara fada mata kasuwancinsu, bayan kwanciyarta ciwo kaya sun qare a shago ansamu riba sosai amma ancire albashin yaran dake jiran shagon ragowar kuma ishaq ya hada a uwar kudin aka kuma sayo Kaya.  Mimi tace "to hakan yayi Allah ya saka da alkhairi" Farida ta kuma dakko jakar leda ta dunga fidda kudi kowanne tasa sunan wanda ya kawo da kuma adadin daya kawo ajiki.  Tace "gashi kudin kayanki ne aka dunga kawowa, wasu anbawa Bature ragowar kuma gasu. Duk kayan sun qare kuma ana nema, tunda kin samu lfy sai a saro kayan kar business ya raunana" Mimi ta karbi kudin ta ajiye a gefe tace "to nagode Allah ya barmu tare" Farida ta dubeta tace "naga kin ajiye baki qirga ba" Mimi tayi murmushi tace "dan kin bani abu harsaina qirga Farida? Ban yadda dakeba kenan?  Allah ya sawaqe abun duniya ya hadamu" Farida tace "hakane besty,  Allah ya qara hada kanmu" Mimi ta dakko mata takaddun gidan da akai mata kyauta jiya ta nuna mata. 



Farida ta dunga godia da murna kamar ita aka bawa ta riqe hannun Mimi tace "maryam kinji dadinki, Allah ya daukaki sakamakon haquri da juriya da kuma miqa lamura gareshi. Haqiqa rayuwarki darasi ne ga wanda suka sanki kuma suka san tarihin rayuwarki.  Muma gashi da muka rabeki muka kuma koyi  wasu halayenki munacin albarkacinki Allah ya saka da alkhairi ya barku tare da sulaiman."  tace "amin Farida"




 Rayuwa me dadi cike da soyayya suke kamar yadda yayi mata alqawari ga wata kulawa ta mussaman.  Yadukko tsaye take kam akan maganin Mimi, kuma Bature yayi musu baxata dan be hana aiwa Mimi komai ba wani sa'inma shike dafa maganin wanka kuma yayi mata.  Basa xuwa awo daga ita har farida gida ishaq ke turo wata nurse tai musu har makarantar rainan ciki ishaq ya sakasu wadda suke xuwa weekend kuma kowacce dole saida mijinta take xuwa yana ganin yadda suke exercise din masu ciki kuma har yadda ake kwanciya da mace me ciki ake nunawa maxan.  Abunda yake musu dadi be wuce ganin yadda cikin Mimi ya tashi ba yayi girma kamar jira yake a dawo gidan babansa cikin qanqanin lokaci da dawowarta. Duk sanda akayi maganar cikin ya girma indai ba a gaban wadanda yake tsananin kunya bane yakance "ai allura nake masa safe da dare shiyasa yake girma" Mimi inya fadi haka kunya tana kamata.  Amma fa da gaskiyarsa domin ta sakar masa jikinta suna gurxar amarcinsu  jaraba yake sosai ita kuma bata iya hanashi sabida son da take masa. 



Yadaukko ta fuskanci Mimi sosai, sai yanxu ta gane sirrin soyayyar  da mumy ke mata. Wato Mimi wata irin yarinya ce me dattako da kirki kuma da wuya ka xauna da ita bata shiga ranka ba domin irin mutananne masu tsananin kirki, da kirki na yawa da saitace yayiwa Mimi yawa.  Da wuya tai maka abunda xai sosa maka rai,  inkuma tayi bisa ajixanci irin na dan Adam takan gaugauta baka haquri da neman yafiya.  Xaman da take dasu Kullum cikin tambaya take "yadukko me kikeso?  Me xa ai miki? Me xan miki? Ko inmiki tausa?" yadukko kanji kunya duk sanda Mimi take mata haka, takance "maryam keda aka turoni kula dake saiki bige da bautamun?" ta fuskanci abunta bai rufe mata ido ba, hannunta sake yake komai yadukko waja waja ake mata,  kai maryam bata tsaya nan ba ko ma'aikatan gidanta mai kirkice da sakewa dasu kuma ba yadda zasu rainata ba.  Yadukko dai tace taga gurin xama, xata xamanta anan yaranta duk wanda ke buqatar gaaninta yaxo ya ganta.  Inda ake ganin mutuncinka ake kulawa da kai a nanne gurin xama. Kuma akai dace yadukko tana jan girmanta sosai, bata shiga sabgarsu inka ganta falo Mimi taxo bawa magani ko dubata ko sun hadu ana hirar weekend, tafi gane taje can baya gurin tsaffin gidan masu aiki susha hira irin tasu ko tana daki tana kallo. 




Me gadin gidansu wanda Kullum xaka ganshi da qur'ani yana karatu kuma yana aikinsa na gadi yana tofa abunda yake karantawa a ruwa Kullum ya aikowa da Mimi shi, ita kuma babu kyamata takesha. 




Kwanansu goma sha biyar da tafiya, mumy tana can hankalinta duk yakasa kwanciya duk da Kullum cikin waya suke da vedio Call. Daren alhamis taiwa mama waya da umartarta ta shirya gobe in sun dawo aiki an sakko juma a xasu tafi Abuja da ita da mumy din ganin jikin Mimi,  mama tace "Adda indai kinje ai shikenan," mumy tace "aiko sai kinje kin gano diyarki itama ta ganki taji dadi, bayan haka ma ai baki taba zuwa gidanta ba yanxu kam kyaje dubiya da ganin daki.  Kuma ban yarda ki fadawa Bature ko Mimi xamuje ba,  so nake muyi musu baxata muga yanayin xaman nasu."  tace "to Adda Allah ya kaimu, bari inje in fadawa Baffa" 





Tana fadawa Baffa ya amince,  harda cewa "gobe da safe ki dunamun insa akawo kwan zabi a gidan gona, ni kuma inna fita xan aiko da danyar goba ai mata tsaraba. Ai gara kuje nima jikin nata yana raina da akusa ne da duk kwana biyu saina leqa" mama taji dadi tace "to shikenan Baffa angode" 





A ranar andata mama zaune tsaye,  ta dunga aike kasuwa ana siyowa Mimi duk abunda takeso,  ta daka mata yaji barkono da daddawa, tai mata alawar madara, kantu,  ta siyo mata manja a sabon gari me kya, kana hada mata garin dan wake. Tana aikinta cikin nishadi tana ayyana gobe inyanxu xataga miminta,  kai! Allah ya sakawa Dan uwa da alkhairi wato Adda halima kamar ta shiga xuciyarta taga da tunanin Mimi take kwana take tashi kawai dauriya take.  Taiwa Faty waya ta fada mata gobe xasu Abuja ta turo a dau Dady sabida makaranta.  Faty ma tace  xata aiko driver da kaya akaiwa Mimi sai atafi da Dady.  



Driver yaxo, Faty ta bada tsakin masara akaiwa Mimi, da busashshiyar rama,  bushashen kifi,  kafikaxa cikin bokiti sai nama soyayye cikin samira wanda ta lura Mimi tanaso kamar me ta xuba mata kakidi akai.  Mama ta dunga yiwa Faty godia a waya tana roqon Allah ya qara hada kansu. Ta debowa Mimi kayan data dinka mata, maternity gown wanda take shiga kasuwa da kanta ta siyo cotton materials masu kyau da laushi wadanda basu da damu ajikin me ciki sabida zafi taxo ta xauna ta tsantsara masu dinkin dogwar riga me kyan gaske wacce xata sake aciki kuma zatai kyan kwalliya, wanda duk gayun mutum inga rigar xaiyi shaawarta.  In Faty nada ciki take siyowa tai mata,  tun Mimi bata da lfy ta siyo bata dinka ba har suka tafi babu shiri.  Yanxu ma ba duka ta dinka ba, guda 7 kawai ta samu dinkawa da tasan da tafiyar da tayi qoqari ta dinka mata duka.  Ta gogesu tsaf ta hada a kayanta. 



Ranar juma a ana sakkowa masallaci mumy ta iso da ita da drivern da xai kaisu.  Itama kayane niqi niqi,  dambun nama tasa akai da uban kilishi an nadeshi a qatuwar takadda kamar sutura da gireba bokiti guda.  A cewarta kwana daya zasuyi, in sunga lfyarsu gobe xasu juyo gida.  



Umma ta kalli uban himilin kayan da ake futa dasu da sunan xa a kaiwa Mimi kawai, a xuciyarta tace "wannan yarinya da gata take, ita halima ko irin kishinnan da surukai batayi.



Suka dau hanya,  drivern mumy babu wasa ya dunga sharara gudu dasu.  Basu isa ba sai dab da magrib rana na gab da faduwa.  




Basu tadda su Mimi gida ba,  aka dunga shiga da kayan da suka xo dasu cikin babban falo.  Baqo ya rasa ina xai saka mumy,  ya dunga zarya tsakanin kitchen da falo sai da yaga ancika musu gabansu da kayan taryar baqi.  Yaxo kusa da mumy kamar xai mata sujjada yace "mumy  sannunku da xuwa, yanxu kuke tafe ya hanya?" ta amsa masa suka gaisa da mama. Yace "oga sun fita da madam babu jimawa, amma nasan duk inda suke suna hanya tunda ankusa kira. Bari in kirashi a waya" ta tsaidashi tace "kyalesu muna son musu surprise ne" yan aikin gidan suka dunka xuwa gaida mama da mumy suna cewa "ga babar madam da oga." 



Mama kallon aljannar duniyar da Mimi ke ciki take,  tana godia ga Allah ya xuciyarta.  Ashe duk yadda ake fadamata kyan gidan Mimi ya wuce faduwa a baki. Ta dunga kallon hotunan su Mimi da Bature dake falon,  ta kuma kallon pics dinsu ita da Faty da Mimi ranar yinin auren Mimi wanda sukasa kaya iri daya. 



Yadukko ta shigo suka kuma kacamewa da murna ana gaggaisawa,  mumy kallon yadda yadukko ta canja take acikin kwanaki 15, tace a xuciyarta wannan yarinya Allah ya saka mata da alkhairi, kalli yadda yadukko ta janxa a cikin qanqanin lokaci. 



Suna kiran sallar magrib suna shigowa, basu lura da mutanen dake falon ba. Sun shigo suna yar rige rige ita dashi,  ya rigata  tace ita bata yarda ba suka kuma komawa baya, dai dai qofar shigowa falon.  Ya kuma rigata  tasa kukan shagwaba wai ita wlh wayo yake mata. Su mumy na kallonsu cikin mamaki. Little tace "ya Mimi, kece baki ganeba dan yafiki tsaho ne sosai shiyasa ya fiki sauri, duk takunsa daya a matsayin naki uku yake" ta dago ta qurawa little ido kamar a mafarki take ganin su mumy yau a gidanta.  Bature kuwa baiyi mamakin xuwansu ba don yasan dole mumy xata biyo sahun Mimi. 



Mumy tai qasa da murya tace da mama "fadima kinga yayan xamani,  yarinya munacan muna tattalinta dan ganin ta dawo hayyacinta abu ya gagara amma dubi cikin yan kwanaki mijinta ya gyarata" mama tace "hm Adda nima tunanin da nake kenan, yaran yanxu sai su baka kunya, yadda Mimi ta nuna tanason biyoshi ai ko bamu yarda ba sai ta saci hanya ta gudu" 


Ta tafi da gudu, mumy tana cewa "hankali, yi a hankali maryama" bata kula ba, taxo ta hadasu duk ta rungume tana cewa "mumy na, mamana,  my little u'r highly welcome"  suma suka rungumeta.  Shidai alwala yayi ya tafi masallaci.  Suma Mimi ta jasu dakin kusa da nasu ta kai musu kayansu  sai dataga sun tada sallah kana ta fito, a gurguje tai wanka tayi sallah  ta fito kitchen.  Taji dadi da taga Baqo yasa an qara abinci sannan an kuma wasu abubuwan sabida xuwan baqi. Suka dunga xarya saida ta suka cika qatuwar ledar cin abincin data shimfida a falo sannan ta koma daki tai sallar isha. 



Yana shigowa tasashi wanka tana axalxalarsa yayi suka shiga dakin su mumy suka dattasu gaba daya akan gado suna hira.  Suka rankaya falo.  Akai gaishe gaishe,  Mama kalan diyarta take yadda tayi shar kamaninta nada sun dawo kamar ba mimin datasha jinya ba.  Mumy ma ta yaba da yadda ta samu su Mimi, sai yanxu hankalinta ya kwanta.  Cikin da suke qorafin baya girma ya tashi yayi kurcici ya turo gaba sosai.  Mimi ta xuba musu abinci suka faraci,  wani irin farin ciki take yau gata ga mama a gidanta, ga kuma mumy uwarta kuma surukarta. 




Bature ya kalli mumy yace "mumy kinxo supervising kenan?" ta watsa masa harara tace "eh shi naxo mara kunya,  Bature ka kiyaye ni, na fuskanci tunda na wanke Mimi na baka raini ya shiga tsakaninmu" yana dariya yace "nidin banxa mumy? Tuba nake"




Mama ta kalli yadukko tace "yadukko dama kiyi xamanki anan cikinsu" Bature yace "ai dama taxo kenan mama, nan xata xauna ta samu miji in aurar da ita" suka sheqe da dariya.  Yadukko tace "qaniyarka,  bakaine mijin ba, ko inada wani bayan kai" 





Sunsha hira, suka fito da tsaraba, Mimi ranar tayi ciye ciye, in ta fara cin wannan aka fito da wancan saita koma kai. Suka koma daki akai shirin bacci. Suka dawo aka kuma xama dakin su mumy aka kafa wata hirar,  yadukko tana fada musu irin xaman da suke da kulawarsa ga Mimi. Mama tace "aiko baki fada ba yadukko,  ga yarinya nan tayi shar daga dawowa" 





Har wajen sha daya basu tashi ba, mumy tace "ku tashi ku tafi dakinku, muma mungaji kwanciya xamuyi"  Mimi tace "mumy babu inda xanje wlh,  kuxo intafi in barku?  Ta miqe ta dakko manyan barguna ta shimfida musu ita da little a qasa yayin da su mumy ke kan gado. Shima Bature ya saka filo akan sofa yace "nima baza a wareni ba, gara ayi dafaduka." babu yadda mumy batayi ba su fita sukaqi dole ta kyalesu. Ya ciro wayarsa ya kira Anty mami vedio Call.  Suka hadu gaba daya ana hira da ita.  Ta dunga murnar ganin jikin Mimi yayi kyau tace "kai nayi farin cikin ganinku haka inama ina kusa.  Tace da Mimi.  "Mimi cikin na motsi?" kunya ta hana Mimi bata amsa, sai Bature ne ya bata da cewa "eh sosai ma kuwa" tace "kuje a duba Baby girl ne ko boy,  inason yo siyayya gaba daya dan nagama siyan unisex." yace "to anty mami" bakinsa yaqi rufuwa sabida kulawar da yaga Anty mami na bawa Mimi  




Su mumy da sukaxo da nufin tafiya washegari dole suka haqura da tafiya,  sabida ko goman safe batai ba gida ya cika.  Safna ta shigo, ishaq da Farida,  ya Taheer da sauran yan uwa na kusa.  Suka xauna akayi break fast tare cikin jin dadi. Farida da Mimi dai sun baje tsarabar su mumy sunaci babu ji babu gani,  ishaq yanata warning dinsu da kar abunda sukeci ya bata musu ciki amma a banxa dan saida sukayi qat kana aka tashi daga falon masu aiki suka hau gyara.  Haka aka yini a gidan cikin farin ciki,  sai lokacin sallah maxan suke fita in sun idar su dawo. Mimi xata iya cewa tunda take a rayuwarta bata taba lokaci mai dadin wannan ba, gata ga iyayenta da yan uwanta kuma acikin gidan aurenta da mijinta.  Itadai tana qaunar mutane kusa da ita,  kuma akai dace mijinta ma yana da son mutane suka hadu suka gina gidansu da soyayyar yan uwantaka. Suma su mumy basu wani damu da qara kwanan ba, dan ganin farin ciki a fuskar yayansu ya kori komai. 



Sai yamma liqis aka watse daga majalisar kowa ya nufi gidansa. Mama da Mimi suka samu kebewa a dakin su mimin,  ta rungume mama tsam tace "mama ina sonki, kinga muhallinmu ko?" mama ta rungume diyarta tsam tace "maryam nima inasonki,  naga gida,  Allah yasa albarka ya qara hada kanku ya baku xaman lfy.  Ki kula da ibada, karkiga Allah ya kawoki wannan matsayi ki  ki wulaqanta wani kowa naki ne kuma ki riqe ibada,  ki tarbiyanci danki tun aciki duk abunda kikasan bakyason danki yayi tun daga yanxu xaki gujeshi shi Dá tun a ciki ake tarbiyarsa." tana kwance kafadarta tace "To mamana duk abunda kikace xanyi.  Kuma in shaa Allah baxan wulaqanta kowa ba kome na xama a duniya,  ai nasha nononki na xuqi kyakykyawan dabi'a" tace "mashaallah uwata banxaci xan ganki haka ba" tana dariya tace "mama ai ya Bature dan halak ne, yana kula dani sosai,  adduarku kawai ita xakucigaba dayi mana" haka sukaita hira irinta ya da uwa. 



Sukai sallah har isha kana suka shirya suka fita a mota.  Mama, mumy da little a baya sai Bature dake gefe Mimi na driving.  Sukaje store ya dunga yimusu siyayyar tsaraba kamar hauka.  Suna fitowa Mimi tace "mumy bari na kaiku boutique dinmu ku gani" tace "to Mimi" suka nufi shagon, haske tanyar kamar rana anata shige da fice.  Yaran gurin na ganin Mimi suka fara sunkuyawa suna gaidata.  Aka sama musu guri suka xauna,  mumy sun kewaya gurin sun yaba sosai da tsarin gurin.  Mimi tace sudau duk abunda sukeso,  suka qi, ta daukar musu arabian gown, little kuma Mimi tace ta debi Kaya ta saki jiki ta lodi english wears sosai. 



Yauma guri daya suka kwana, washegari suka kuma kaiwa har azahar kafin suyi haramar tafiya.  Mimi ta bawa mama da mumy wani hadadden lace iri daya sak sai banbancin kala,  da hada musu da shoe nd bag cikin kayan data yo order ko kwancesu ba ayiba. Ta rasa mexata basu,  ta dakko wannan ta dakko wancan wani abun ma baxai masu amfani ba kawai ta rasa mexata basu ne,  duk abunda hannunta yakai kansa dakkowa take,  harta fara bawa mumy tausayi. Tunani take mimi wace irin halitta ce ita?  Ansha kawo mata suka cewa Mimi xata rabata da Bature inta yadda ya aureta, ko kuma su tattare arziqinsa daga ita sai uwarta da yar uwarta, amma ita kam ta qaryata domin sai yanxu ma take morar Bature da arziqinsa fiye da da,  dan maryam ta koya masa sakin hannu da xuciya akan kowa nasa.  Gidaje ya raba musu ita da ragowar yan uwansa kwanakin baya, mumy tace lallai itama maryam ya bata nata shine ya mallaka mata bayan warkewarta.  Haqiqa irinsu Mimi a duniya dai daiku ne  duk wanda ya xauna da ita saiya yabi halinta.  Little kuma ta bata mayafai da 20k tace tasa katin waya.  Drivern mumy ma bata barshi ba saida ta bashi tsaffin kayan Bature da 10k ya dunga godia dafatan Allah ya sauketa lfy. Yadda sukaxo da kaya niqiqi haka suka koma dasu.  Dan kowa nuna musu Jin dadin xuwansu yake ta hanyar tsaraba.  Suka rakosu har bakin mota Mimi ta riqe hannun mumy tace "mumy dama karku tafi kuyi xamanku nan"  mumy tace "wato sai mu xauna gotai -gotai damu cikinku sabida a garin gaba -gaba ake?"  haka dai aka rabu a marmarce Mimi harda hawayenta.


****** ******* ******* ***

Yaxo mata da labarin ansamu yan hayar da xa a saka a gidan ya kawo mata kudin da bank suka kawo miliyan 3 cis.  Tai tai ya diba yaqi daga qarshe ma sai saka mata dariya.  Tace kudin ka ajiye a gurinka so nake ka saimun motaci guda biyu iri daya. Yace "wa xaki bawa?" tace "mama da ya Faty" yace "to akwai yaran dake kawomun mota, a gunsa nake siyan mota xan masa magana ya kawo miki masu kyau" 




Ko 2 wks su mama basuyi da tafiya ba,  wani  yammaci tana kwance bayan idar da sallar asr dan bacci ya kwasheta duk da tasan babu kyau baccin bayan laasar amma wannan ya shamceta. 




Acan gate din gidan kuma jafar ne yaxo shi da matarsa.  Saukarsu kenan Abuja ya taho gidan Mimi yabi kwatancen da Faty tai masa, kuma Baffa ne ya dunga jaddada masa inyaje ya tabbatar ya leqa gidanta ya qara duba jikinta.  Semina ce ta kawoshi wanda aka turoshi daga gurin aiki ta kwana uku,  ya yanke shawarar ya fara xuwa su gaisa da Mimi kana su xarce hotel suyi masauki dan inya fara aiki bexama lallai ya sami sukunin xuwa ba. 




Dakyar me gadi ya bari ya shiga da motarsa cikin gidan domin saida yasha tambayoyi iri iri harda tambayar alaqarsu da Mimi din.  Jafar ya qulu sosai, ga gajiyar da suka kwaso ga iskancin me gadi, shi inbadan Baffa ya tilasa masa ba mexai kawoshi gidan Bature?  Dan tunda ya koma yaga ya dauke mimi yaji ya tsaneshi wato ya kawota da lalura ya ajiye sai data warke ya koma ya dauketa.  Kamar yadda Anty ta fada masa.  Shi kuma me gadi yana kan aikinsa ne dan har yanxu bai manta masifar Anty mami ba.



Ransa ya qara baci sosai da yaga sunfi rabin awa securities din gidan na musu tambayoyi kafin a barsu su shiga falon baqi. Gashi sai kiran Mimi yake a waya bata dauka ba, wato itama ganin ta samu duniya canja hali ko? Ya raya a xuciyarsa.  Matarsa maryam sai mita take "kaima kaxo mu tafi, mun debo gajiya munxo sai titsiyemu ake da tambayoyi kamar xamuga shugaban qasa ita kuma yar rainin hankali taqi daga waya" ya sauke fushinsa a kanta yace "kimun shiru ko ranki ya baci,  ina ruwanki, ba yar uwata bace?" ta murguda baki tace "tsohuwar baxawararka dai" 




Tsuguno bata qareba, saiga Baqo yaxo yana ce musu me sukaxoyi gurin madam kuma ya suke da ita? Indai tasan da xuwansu suyi mata waya ta bada umarnin a kaisu falonta.  Jafar yacigaba da kiran Mimi amma bata dauka.  Ya kalli Baqo cikin bacin rai yace "in kana iya xuwa inda take kaje kace mata jafar Buhari ne yaxo" ya fita jim kadan ya dawo yace "bacci take, kuma in madam na bacci ba a tashinta" dan takaici bece komai ba.  Aka kawo musu ruwa da lemo sunanan xaune duk motsin da sukai idon securities akansu kamar masu gadin barayi.  


Can Baqo ya kuma komawa yace da Aisha taje taga ko Mimi ta tashi dan yaga alamun baqin daga nesa suke.  Taje tace masa ta tashi wanka take ma.  10 minutes a tsakani ta fito ta zauna a falo tayi kwalliya me burgewa cikin doguwar rigar material wanda mama ta kawo mata. Ta kashe dauri da dankwalin kamar ba mai ciki ba tana tauna cingam.  Baqo ya koma yace da jafar ta fito wa kace sunanka?"  ya maimaita masa sunansa.  




Babu jimawa saiga Baqo sun taho da Mimi dan bata yarda cewa jafar kunnanta yaji Baqo yace ba.  Suka hada ido, taje da sauri ta tsuguna gabansa kamar xata shige jikinsa tace "ya jafar da gaske kaine?" ya fada mata yadda sukasha wuya kafin su ganta,  ta kira securities din tana musu fadan a daina yiwa wadanda sukaxo gurinta walaqanci.  Suka dunga neman afuwarta.  



Ta jasu falonta,  daga jafar har maryam matarsa sai da suka tsaya qauyancin ganin wannan aljannar duniya maryam a xuciyarta tace "a dole kiyi wulaqanci yarinya, ai koni nasamu wannan daular sai abunda yafi haka" ta xauna suka gaisa aka cika gabansu da kayan taryar baqi,  suka fara hira ya fada mata abunda sukaxo yi.  Yace "na kiraki a waya baki daga ba ai" sai yanxu ta tuna tasa wayar Silent tace "wlh na Sata silent na kwanta i m sry" yace"babu damuwa" ta kira landline tace a kawo mata wayarta, Aisha ta shigo ta miqo mata wayar.  Maryam a xuciyarta tace "Tab yarinya Allah ya baki duniya kina daga zaune komai ai miki."



Sunanan xaune suna hirarsu Bature ya dawo aiki,  kamar yadda ya saba ya shigo yana waqa, Sam bai lura da mutanen dake gurinba idonsa Mimi kawai ya hango masa.  Ya taho gurinta yana waqa, yayin da su jafar suke daga bayansa, wato Mimi saitin qofa ta kallah shiyasa yana xuwa ita ya fara gani ya bude hannusa yana cewa "hlo my african queen" ya tsuguna gabanta tana kan kujera ya dafa gwiwarta, ta danji kunya tace "bakai sallama ba" ya lakace mata hanci yace "nayi kene bakiji ba, bakixo kin taroni ba kin rungumeni" ta dunga qifta ido tanason nuna masa da baqi fa a dakin amma ina bai ganeba saima cewa yayi "ki dainamun wannan farin nan,  kixo muje ciki kimun in biyaki. Ya sumbaci goshinta,lips, dinta sannan ya sumbaci cikinta daga baya ya rungumeta. Su jafar na zaune a daskare suna kallon luv. 




Tana tureshi daga jikinta ta rada masa "akwai fa mutane a falon" ya dago yakai dubansa bayansa, suka hada ido dasu jafar.  Kunya ta kamashi ya dan sosa kai yace "jafar kune a garin namu yau?" jafar ya danyi yaqe yace "wlh kuwa aiki ne yadan kawomu Abuja na kwana uku shine na biyo duba maryam, yanxu xamu wuce masauki"  yace "kai amma kun kyauta" yaje sukayi musabiha aka kuma gaisawa sosai da tuntubar juna.  Bature yace "ai nanne masaukinku,  ina xakuje bayan ga nan din.  Duk girman gidannan ace kun fita hotel" jafar yace "a a wlh ai kuwa dai baxan sauka gidan qanwata ba da girmana" Bature ya dubeshi yace "au maryam kake kallo a matsayin yar uwarka? Ni bareni a cikinku?  Hakan yayi, nagode sosai" jikin jafar yayi sanyi, yace "kayi haquri sulaiman ba nufina kenan ba."  haka ya dunga bashi haquri Mimi tasa baki. Yace "is Ok,  taso muje mu dakko kayanku" dole jafar ya tashi sukaje mota ya bude aka fito da kwatinsu.  Bature da kansa ya dakko ya shigo da ita. Maryam din jafar kuwa kwanciya tayi bisa kujera, hakan yayi mata dadi xataso kwana a wannan aljannar duniyar dan tasan mijinta bashi da kudin da xai kama hotel din da xai kama koda kafar wannan gidan. 



Suka sake xaman hira anan falon,  ya tashi yaje kitchen yayi blending fruit ya xubo a cup.  Sai da yasha ya rage ya miqawa Mimi ragowar ta shanye.  Kiran sallah ya data su,  maxan sukai masallaci Mimi ta ja maryam dakinta sukai sallah. Ta dunga kallon makeken bed room din, yayi girman wani gidan wai duk bed room ne,  tab Mimi ta samu duniya.   Bayan idarwa Mimi da kanta taje ta gyara musu daya dakin tasa sabon bed sheet ta fesa maganin saura ta kai musu duk abun buqata irinsu masubulun wanka, maclean da sauransu. Ta ja maryam suka koma bedroom din ta sake wanka,  maryam kallonta take,  yanxu bayan wannan wankan har wani aka sake?  Tab ita wanka daya take.  Taga Mimi ta kuma chada kwalliya cikin bubu din atamfa.  Bayan dawowarsu masallaci kowanne ya shige dakin matarsa.  Jafar yayi wanka ganin haka itama maryam tayi dan kar ace mata qazama. 



Har daki Mimi taje ta kirasu xasuyi dinner.  Suka hadu jafar idonsa akan Bature da Mimi yana ganin wata irin salon soyayya me ban mamaki da shaawa.  Ya raya cewa da tuni shi Mimi kewa wannan kulawar.  Bature ya tashi ya xuba musu abinci da kowa a plate dinsa kana ya xauna, ya dauki plate din Mimi yaci cokali daya sannan ya tura mata gabanta yace "Bisimillah Mimi luv" tace "to ya Bature"  suna cin abinci cikin nishadi ana hira jefi jefi.  Mimi ta janyo kwanan da aka gasa nama ta bude,  yayi saurin karbarta ya tashi ya sakawa kowa a gabansa.  Maryam din ya jafar a ranta tace "tabdi bata girki kuma xubawar ma sai anyi mata?  Inama nice"  cikin san nuna ita watace ta kalli naman da Bature ya ajiye mata gabanta,  azatonta kaza ce ta yatsuna fiska tace "ni banacin naman kaxa" jafar kunya ta kamashi dan yasan qarya take.  Mimi kuma ta yarda da abunda tace, dan tasan mutum iri iri ne kowa da yadda Allah ya halicceshi,  tace "ayya sry Anty maryam ko in gasa miki red meat?  Wannan ma ba kaxa bace,  ba a cin naman kaxa a gidannan. Talo -talo ne." Bature yace "a a Mimi luv,  cewa xakiyi tunda kikai ciki kika daina cin kaxa sai talo talo." dajin ance talo talo ne tahau yaga tanaci dan tasha ji ana cewa wanda ya saba cin naman talo talo baya iya cin kaxa sabida dadinsa. 




A daren Mimi ta kwaba funkaso dan tasan shine favourite din jafar,  ta hada miyar taushe  ta dafa fari Sol din naman kan Sá ta rufe.  




Da sassafe yana kan gym ita kuma tana kitchen tana suyar funkaso, harya gama motsa jikin yaxo ya tayata aikin.  Sai wajen tara suka gama komai ta bar Aisha ta shirya table ita kuma taje tai wanka. Goma sun gama komai har maxan sun fita aiki,  ita da Anty maryam kuma kamar yadda take kiranta sunata hira tana janta duk gurin da xata a gidan tana nuna mata.  Itama maryam ta saki jiki da Mimi suna hira duk da rabin hirar tata qaryace dan a tunaninta gara ta hada da qarya kar Mimi ta rainata,  batasan ita ba haka take ba. 



Yauma kamar jiya, sun hadu falo da yamma bayan dawowarsu office. Jafar yana ganin wata extra ordinary caring  da Bature kewa Mimi,  inxata xauna saiya miqe ta zauna sannan shima ya zauna kamar wani yaranta,  in abinci xataci saiya  faraci kamar mai tsoron kartaci guba kuma in ruwa xatasha saiya tsiyayo mata,  duk maganarsa daya sai yace "Mimi luv"  


Yauma suna zaune kan dinning Mimi da kanta tayi jellof rice wacce tasha baqin kifi busashshe tayi shar sun cinye abinci tas dan yayi dadi sosai.  



Wajen 8:23 pm Farida ta shigo gidan tasha kwalliya sosai, da ritsetsen cikinta.  Ta dubi Mimi tada taso ta dosota kana takai kallonta kan maryam matar jafar.  Taci kwalliya da tufa me tsadar gaske ta xuba golds hannu da wuya a wannan daren kamar mai zuwa competition.  Amma kash!  Kwalliyar daban ita daban dan Sam bata iya kwalkiyar ba dagani bata da wayewa.  Farida tai qasa da murya tace "money miss road" Mimi ta tsunkuleta ta nuna mata jafar da ido tace "matarsa ce"  sai a lokacin taga jafar suka gaisa. Ta kalli Mimi tace "besty ya baki shirya ba?  Cinema fa xamuje kallon wannan film din" Mimi ta dafa goshi tace "kash namanta bari in sake kaya"  ta wuce daki Farida ta xauna kan kujera tana kallon maryam din jafar a sace tana dariya.  Anata bangaren maryam tayi wannan kwalliyar ne dan nunawa Mimi itama fa tana da kayan qarya dan bata taba xuwa Abuja ba, daji ance xa a je ta kwaso kayan qasan akwati da nufin axo Abuja ai fafa dasu,  sai akai sa a kayanta ya tsinke bakin kaba taxo gidan yan gayu dan haka ta fito da tanadi ta fara bawa Mimi mamaki a ganinta🤣


 
Ishaq ya shigo yace da Farida "dabaki tsayani ba gashi duk saurinki na taddaki" tace "wlh kuwa ya ishaq Mimi wai ta manta" Bature ya kalli jafar yace "koxo muje cinema kallon wani nollywood film kuma da jaruman film din shiyasa su Farida ke rawar kan zuwa sunason ganin jaruma jackie appiea" jafar yace a ransa lallai Bature ka cika shedani anbaka yarinya me tarbiyya amma har Cinema ka koya mata xuwa" a fili kuma yace "ba damuwa maryam tashi muje"  Farida kamar tace da wannan shigar xaki cinema din,  sai kuma tai shiru. 


Mimi ta fito cikin shiga english gown me taushi amrless ta dora boy friend jacket akai ta samu qaramin gyale tayi vieling fuskarta babu kwalliya sai powder da man lebe tayi kyau sosai.  Suka kama hanya. 




Daga wajen cinema suka tsaya suka sayi pop corn,  Mimi taje gurin kayan sanyi ta dauki qaton roban ice cream tace da Farida kawo kudi ban fito da jaka ba,  farida tace nima haka, amma ina zuwa.  Taje gurin su ishaq dake tsaye ta xare masa willet dinsa be sani ba, sukaje suka biya kudin,  sai gasu kowacce na tura ciki da robar ice cream.  Farida ta miqawa ishaq willet dinsa. Yace "yaushe kika dauka bansani ba?" Bature ya dubi Mimi ta robar ice cream din yawunta har ya soma tsinkewa so take su shiga kawai tasha yace "wa ya sai muku?  Ban hanaku shan sanyi ba?"  ishaq yace "kyalesu shammatata sukai suka xaremun willet. 



Sun nutsu a kallon film din kuma yayi kyau sosai,  Mimi dai tunda ta cika cikinta da ice cream tai bacci a kafadarsa, koda aka tashi sai dakkota yayi yasata a mota da sukaje gidama haka ya dau barsa har dakinsu. Jafar kallonsu yake cike da burgewa.



A yan kwanakin da sukayi da su ya fuskanci qaryane ace Bature baisan Mimi,  domin wannan kulawar da sukewa juna ta wuce misali.  Farko ya dauka ganinsune yasa Bature yiwa Mimi irin haka amma daga baya saiya lura haka suka gina rayuwar aurensu,  sonta yake tattalinta yake kamar ya maidata ciki ga kuma girmamata da yakeyi.  Wani dare sun zauna zasuci abinci Mimi ta miqe tsam ta koma bisa carpet ta fara kukan shagwaba, ya miqe yace dasu, kuci abincinku ni yau Mimi rigimar ta motsa,  ai kuwa abinciin da baiciba kenan ta dunga kuka tana burgima tsakanin qafarsa wai cikin yana mata motsi ya danne mata.  Ya dunga lallabata har tai bacci ya kaita daki.  



Har kwanakin aikinsu ya qare amma suka hanasu tafiya, wai sai week end ya koyi abubuwa da yawa a xamansu, wanda inka riqesu xaka xauna da matarka lfy duk tsaurinta.  Kuma yayi aniyar gyara rayuwar aurensa in shaa Allah.  Anata bangaren Mimi taja maryam ajiki ta dan koya mata tsaftar jiki wacce ta fuskanci tana da rauninta. Randa zasu tafi Mimi ta bata lace da mayafi sai fashion din yari da sarqa, shi kuma ya jafar ta dakko masa wani filtek a cikin kayan Bature wanda bai dinka ba,  koda taje dauka tace in dauki wannan ya Bature?  Yace dauki maryam dan nasan kyautarwa xaki Allah ya hadamu a ladan. Tace nagode yace "nima nagode da koyar dani da kikayi cewa mutum koda mawadacine in ammasa ihsani yana jin dadi" sun rabu cikin kewar juna. Jafar ya yadda soyayya ce me qarfi tsakaninsu babu xancen yaudara. 



Passing out dinsu na gama service lokaci yayi ana gobe xa ai suka tafi kano a motocin data saiwa su mama,  ita da Bature a guda daya driver ya Biyosu da dayar suka tafi tare.  



Washegari da safe sukaje state sect P O P din, yana xaune yana jiranta suka gama ta amshi cert dinta na NYSC sukayi pics din tarihi da qawayenta aka rabu.  Tana shigowa motar yace "BARRISTER MARYAM AL AMIN congrat" ta farareshi tace "kawai dai kace kanason fadar sunan Babana amma inba haka ba kace congrat din mana kawai" ya sheqe da dariya yana mamakin daru irin nata yace "sry ranki ya dade, na gyara congrat Maryam"  



Basuje ko inaba tunda jiya sukaxo,  da yamma suka shirya suka dau motacin iri daya sak ita daya shi daya.  Gidan Faty suka fara xuwa,  bayan murna da kewar juna da mamakin girman cikin Mimi da Faty tayi suka rabu ta rako su gate. Mimi ta shiga Mota ta debo takaddun motar ta ciro key din ta bawa Faty tace "gashi takice na saya miki" Faty ta daskare ta kasa magana sai bin Mimi take da ido har suka tafi batace komai ba. 



A gidan mama ma bayan murna aka gaisa, mama tace "sakko daga tudunnan in matsa miki qafar ta fara kumbura.  Mimi tace "kafin nan xo muje kiga" sukaje qofar gida ta dakko takaddu da key ta bawa mama tace gashi mama asa albarka mota na sai miki.  Mama sai hawayen farin ciki,  suna tsaye saiga Faty a tata motar taxo nunawa mama dan abun baxai fadu a waya ba.  Ta tarar da wata mamakin. Suka hadu suka dunga kuka sunawa Mimi adduar alheri, sulaiman na gefe na dubansu yana mamakinsu kamar su cinye juna.  Baffa ya fito yaga motocin yace "tofa aiki game qareka,  fadima haihuwa ta miki rana Allah ya sa albarka yasa a kashe lfy" matan gidan kuwa kamar wadanda  suka gamo haka suka burkice basu wani boye baqin cikinsu ba.  Mimi ta nuna musu cert dinta na NYSC tace "mama i m now a Barrister maryam, na cika burinki ko?" mama ta rungumesu duk tace "kun cika burin mahaifinku da ace yana raye da bansan irin farin cikin da xaiyi ba"  Bature sun burgeshi har vedio yayi musu.  



Washegari suka koma Abuja sabida aikinsa 



Farida ta haihu, yayin da Mimi cikinta ke 7 months daga asibitin aka wuce da ita gidansu dake Abuja, wanda Umman ta taxo ta xauna da ita. 


Mimi ta sameta gidansu ita da Bature,  bayan gaisawa da yiwa juna barka Umma ta basu guri,  Mimi kallon Farida take a tsorace ganin yadda ta rame a lokaci daya duk idonta ya xurma.  Ta karbi Baby girl ce ta miqawa Bature ta koma ta xauna tace da Farida "Farida haihuwa da wahala ko?  Naga duk kin rame" Farida tace "Tab, ai wahalar ma baxata fadu ba,  nifa inaga mutuwa nayi na dawo.  Wai a hakanma dan ya ishaq ya temaka mun dan yana tsaye kaina harna haihu. Kuma wlh ina dawowa hayyacina ke na tuna" Mimi ta dafe qirji tace "na shiga uku" ishaq ya harari Farida yace "ke ya isa haka, Mimi wasa take miki kowa da irin tasa haihuwar wani baya wahala"  


Tundaga ranar Mimi can take yini,  Kullum inxai tafi office yake kaita in ya dawo ya biya su taho tare.  Ishaq ma can ya tare kwanciyar bacci ke dawo dashi nasa gidan. Ranar suna yarinya taci sunan Umman ishaq Hawwa amma suna ce mata Jidda.


Mrs Hajia 😊
[9/30, 1:05 PM] ‪+234 706 296 6299‬: 🙆🏼🙆🏼🙆🏼AL 'AMARIN MARYAM 🙆🏼🙆🏼🙆🏼
            

Writing & story by Rahmatullah Muhammad (hajia)


📝FANTASTIC STARS WRITERS {F S W }

Page 6⃣5⃣


Dedicated to 
ANTY SIS,
MARYAM BAITA &
NAJA'ATU NAFI'U (yar malam 

LAST PAGE 


Farida nayin 40 dayz Umma ta tarkatota ta dawo da ita dan tace tagaji da xaryar ishaq,  itama ta tafi kano nata gidan. 



Mimi ancigaba da rainon ciki,  tafi duhu sosai irin na masu ciki wuyanta yayi baqiqirin ta kumbura kamar xata fashe.  Mijin Kullum cikin lallaminta yake dan ta tsorata da haihuwa tunda farida ta bata lbri.  


Ta fito daga wanka ta xauna gefen gado, yana kwance akan gadon, ta dan bigi qafarsa tace "ya Bature aramun t shirt dinka insaka da zani banasan saka gown xafi nakeji." ya tashi ya bude drawer ya dakko mata wata qatuwar t shirt dinsa yana cewa "sannu Mimi luv kin kusa in shaa Allah" ta saka rigar taxo mata har gwiwa.  Tace "shikenan ma na huta daura xani"  ta bashi dariya, amma baiyi a fili ba sai a ciki,  baisan ta jishi ta hade rai tace "ai dole kaimun dariya tunda na gama yimaka amfani ka maidani haka" yayi rau rau, baiji dadin maganar ba, ya rasa abunda yasa Mimi ta xama haka abun kadan sai fada,  yace "haba maryam,  nasan ba haka na aureki ba nine silar komawarki haka kuma in shaa Allah kin kusa haihuwa kiyi haquri my luv" ta dan samu sauqi jin kalamansa.  Ganin tana gumi ya qure AC amma duk da haka zuffa take.  Yaje ya kira yadukko taxo taga yadda Mimi ke nishi da gumi.  Tana xuwa tace "sulaiman wannan yarinyar naquda take ku tafi asibiti." tace "maryam kina jin ciwo?" tace "eh  tun jiya amma ba sosai ba.  Mamace tace in dunga daurewa" yaje ya dakko akwatin da suka dade da hadawa ya tattagi Mimi suka tafi.  Sun sami ishaq yasa aka dubata nurse din tace tabbas labour take amma yanxu tana 1 stage da ragowa sosai. Haka aka kwana tun ciwo na qarami har ta fara jigata sosai.  



Da sha biyun rana tayi washegari wanda Mimi tayi 24 kenan tana abu daya ya Taheer ya buga ya sanar da mumy dan tun akan rashin lfyar Mimi yayiwa kansa alqawari baxai qara dakata Bature ba a boye AL 'AMARIN MARYAM. 



Bature kam baya cikin hayyacinsa kai kace shi yake labour din, sai shige da fice yake a dakin xuwa office din ishaq.  



Dab da magrib saiga su mumy ita da mama da ya Faty,  sukaxo da rubutu tsibi tsibi wanda aka karbowa Mimi a gurin malamai daban daban na naquda.  Lokacin Mimi ta gama fita hayyacinta, aka dunga durawa Mimi rubutun. Bature kawai aka bari ya shiga dakin,  su kuma suna tsaye a qofar cirko cirko daga ciki suna jiyo nishin Mimi. Ya fito yanawa su mumy bayanin har yanxu da ragowa amma xuwa 8 din dare inbata haihu ba xa ai mata CS.  Nurse ta leqo tace yaxo,  ya tafi Faty tabi bayansa amma ta hanata shiga, ta ciro ID card dinta na aiki ta nuna mata, ta barta ta wuce.  Tasa safar hannu ta fara duba Mimi, tabbas da ragowa dan naqudar inta taho gadan gadan saita koma.  Ta kalli Mimi cikin tausayawa duk tayi laushi ta hada xuffa kamar ruwa ya daketa tace "Mimi ki daure kiyi nishi Kinji" bata amsa ba.  Bature yaje saitin fuskarta yace "maryam kiyi nishi ko kadan ne,  daure kiyi danmu xaki kawo mana duniya" ta bude jajayen idanunta tace "baxan iyaba, numfashina iya qirji yake tsayamun baya kaiwa ciki kasan ina sonka da xan iya ya Bature da nayi"  ya share kwallah aransa yace dama haka mata ke wahala wajen haihuwa.? amma wasu matan suyi ta haihuwa kamar mahaukata ko ciwon jikinsu basaji?  A fili kuma yace "nasan kina sona Mimi,  tunda kina wannan halin ma baki manta soyayya ta ba kuma kina wannan wahala ne don ki haifar mana sanyin idaniyarmu." ya miqe ya fita ya koma office din ishaq. 




Ya daure fuska yace "ishaq na rasa dalilin da yasa kake haka, na rasa me Maryam tai maka kake mata wannan hukuncin.  Kai lokacin da aka kawo matarka ai tsayawa kai ta haihu cikin sauqi, saini xaka azabtar da tawa,  tun jiya take abu daya gashi tana neman kuma kwana duk qarfinta ya qare" ishaq ya dan diririce  dan tunda aka kawo Mimi yaqi shiga dakin da take sai nurse da likitoci mata yake turawa su dubata.  Shi anasa ganin xuwa kan Mimi a halin labour kamar keta alfarmar aminin nasa ne.  Tun safe Bature ke fama dashi yaje yaga meya hana Mimi haihuwa a matsayinsa na babban likitan mata,  amma sai sun tafi rimi rimi sun kusa xuwa dakin sai ya xame yace ya manta be dakko wani abun ba. 



Ya kalli Bature yace "kayi haquri, na tura Dr Salma yanxu ta dubata inda matsala xata fada ko banjeba" Bature ya fusata ya buga table din gabansa yace "ishaq wlh in Mimi ta rasa ranta bisa wani dalili naka marar ma'ana Allah baxan duba tsakaninmu da kai ba makaka xanyi a kotu" ishaq yace "to Allah ya baka haquri muje in ganta" ya miqe ya fara duba lokar jikin table din kaman yana neman wani Abu.  A zuciyarsa kuwa addua yake Allah ya kawo masa mafita dan bayaso ya keta alfarmar Bature ya duba masa mata.  Dr Salma ta turo kofa tashigo,  yayi hamdala a xuciyarsa tace "Dr. Na dubata, da naxaci fitsari ya hanata haihuwa amma na xuqe mata har yanxu shiru qarfinta ya ida qarewa inaga CS ya kamata atafi da gaggawa kan wani abu ya faru." Bature ya runtse ido,  ishaq ya miqe ya dakko takadda ya tura masa yace kasa hannu xamu shiga CS da ita.  Dr Salma ta fita bayan ishaq yace taje ta shirya Mimi xuwa dakin  operation.  Shima  ya miqe ya fara saka kayan aiki,  Salma ta dawo da sauri tace "Dr yanxu muka hadu da sister zubaida a hanya, maryam din ta haihu yanxu." ai kafin ta gama fada Bature tuni yayi waje yana hamdala.  Yaje shiga dakin ya ganta a kulle an rufe ta ciki,  ya juya ya kalli su mama suma fuskarsu na nuna alamun murna yace "suna ciki ne?" tace "eh su ukune ciki har Faty ta hudu" sunata xaman jira har ya gaji yaje yayo sallar da ake binsa beyi ba ya dawo amma basu bude ba.  




Sai da suka kusa 2 hours ciki suka bude lokacin harya fidda tsammanin lfy kuwa?  Suna budewa suka duru dakin,  angyara komai qal dakin sai qamshin dettol yake.  Anwa Baby wanka, Mimi ma anmata tana sanye da kayan asibitin dark blue kamar yadda dokar take me jinya bayasa kowane kaya se nasu.  Tana kwance sunata daukar Baby ita kuma tana kallonsu tana murmushi,  ta kafe mama da ido wani masifar san mama take a yanxu data xama uwa,  ashe haka iyaye mata kansha baqar wuya kafin suga dansu?  Gaskiyar farida da tace mutuwa tayi ta dawo.  Duk Dan dabebi uwarsa ba ya shiga uku.   



 Mumy ta dubeta tace "sannu maryam, kin samu diya mace" batace komai ba sai lumshe ido da tayi,  tayi baccinta sabida allurar da akai mata.  Sama sama taji shigowar ishaq ana xuxuta kyan Baby. 




Tayi bacci me yawa ta tashi batasan ko qarfe nawa ba lokacin, Faty ta rakata bandaki tayi brush ta canja pad kana ta dawo ta fada mata tea a qaton cup ta shanyeshi tas.  Mama xaune da jaririya a hannunta tace a xuciyarta "wai yau nice riqe da dan Mimi?  I kon Allah kenan, mimin da akasha fama akan neman mijin aure yau gashi abu ya wuce lallai komai yayi farko xaiyi qarshe, kuma komai lokaci ne"




Aka miqa mata yar, ta karba a kunyace tana kallonta,  babu inda tabar mumy,  kamarsu daya sak,  sumar kantace kawai irinta Mimi dan gatanan a cike.  Mumy tace "bata nono tasha tun daxu take tande baki da Bature ya bata dabino" Mimi tace "mumy ai babu ruwa" tace "bata haka ta kama xata xuqo" Mimi ta fara yarfe hannu tace "mumy wlh da xafi abata madara kawai"  abu dai ya xama babba tun suna ganin abun wasa har ya xama gaske dan Mimi ta hana Baby nono.  Suka fita xuwa office din likita dan tambayo wace madara ya dace a bawa new born Baby.  



Bature ya taso bayan fitarsu ya kwanta kan gadon suka saka yar a tsakiyarsu, yace "dan bata nono Mimi luv,  kinga inkika bata yanxu shine first anaso Baby ta fara shan nonon uwa dan ya wasar mata da kwalkwalwa, inkika bata shikenan sai acigaba da bata madara"  tace "to" ya miqo mata yar ta xauna ta fara bata,  tana cije baki dan da xafi,  yana bata baki harta haqura ta saki jiki.  Ya matso yana mannata a jikinsa ko anan aka tsaya burinsa ya cika, Mimi ta haihu dashi tana kuma shayar da diyarsu nono.  Yace "Mimi kiyi haquri,  naso ace yadda kika wahala sunanki na sakawa Baby, amma sai dai na riga nayi alqawarin saka sunan mumy tun sanda scanning ya nuna mace xaki haifa" tace "babu komai ya Bature nima nafison taci sunan mumy dan da mumy take kama kamar ita ta haifeta." yace "to nagode Mimi amma naji mumy tana cewa wai kamarmu daya ina jariri" 



Faty ta shigo ta gansu ta koma da baya  ta tarar dasu mumy riqe da  takaddar madarar da likita ya rubuta tace "mumy ina xaku?" mama tace "sunan madarar xamu kaiwa Bature yaje ya siyo abata" Faty tace "to ku koma, Mimi dai da mukasha fama da ita ta bawa Baby nono taqi, gatacan mijinta ya lallabata tana shayar da diyarsu." mama da mumy suka kalli juna. 




Sun shiga daki sun taddasu kamar yadda Faty ta fada musu,  yana ganinsu ya sanfe yace "mumy takwararki aka samu HALIMATU" suka hada baki da mama sukace "mashallah Allah ya rayata" murnar sunan mumy da aka ya mantar dasu abunda ya faru. 




Washegari aka sallameta suka wuce kano akabar Bature  da kewar family dinsa.



A can kano gidan Baffa kuwa tun bayan sewa mama mota kowacce a cikinsu ta tasa yayanta gaba da takurar lallai suma sai sun saya musu motoci dan ba daya suke buqata, in sukai daya ai sunyi kunnen doki da mama.  Yayan gaba daya sunyi karatun ta nutsu suka hada kai sukace basu da kudin siyan musu mota su bari komai lokaci ne,  kuma ai akwai motar gida wacce Baffa ya siya ake kaisu duk inda zasu,  bayan haka kuma sunsan mama a nata bangaren baxata daga musu kaiba sabida tana da Mota basu da ita.  



Rashida kuma mijinta ya dawo tun bayan dashi da amarya kanwa takar tsami kwarnafi ya kwanta,  ita kuma ta qeqashe qasa tace ai sun rabu kenan.  Bai haqura ba yanata naci ita kuma tana yangwanashi. 



Mimi jego ta samu irin na mutanen da,  mama macece me kula da Dá ko ruwan sha sai ta tafasa take bawa Mimi tasha.  Tsakaninta da Baby kuwa sai dai in bata nono xatai,  Kullum tana bayan mama.  Mutane kota ina barkowa suke,  fauxa taxo daga Lagos kuma ta kawowa Mimi wani yoruba lace irin wanda suke sawa a event dinsu 15 yards,  kana ganin lace din kasan tsayi masifar tsada kuma duk wanda ya badashi a matsayin kyauta tabbas hannunsa ya cudi baya.  Daga ninta kasan ta fara kama qasa harda motarta taxo wacce sunusi ya siya mata.  Mimi ta dunga murna,  mama ta karbi lace din takai shagonta na dinki wanda ta bude ta xuba yara maxa.  Suka dinkawa Mimi buba da xani Bature kuma sukai mai irin dinkin yarbawa.  Alheri kota ina barkowa yake. Bature ko tsinke bai saiwa Baby ba, Anty mami ce tayi komai har kwanan da Baby xata fara cin abinci in aka yayeta sai data aiko dashi.  Ranar suna Audu ya kawo Sá da rago aka yankawa HALIMATU  wacce little ta fara kiranta da MIMA.  Ranar suna da yamma ya iso,  Mimi ta bashi lace din fauxa ta fada masa fauxace ta kawo musu ya karba ya saka sanin matsayin fauxa gurin Mimi,  itama ta saka aka dunga hotuna yana riqe da Mima.  Fauxa taji dadin saka kayanta da sukayi. 




Ta cigaba da rainon mima ita da mama,  kuma a xamanta da Rashida ta dunga bata shawarar ta yadda ta koma ta haqura kodan Dan dake tsakaninsu.  Taji shawarar Mimi,  ta tatseshi kudi sosai kafin ta yadda a qara daura aure ta tare.  Amaryarta dole ta kwantar da kai aka xauna lfy domin yanxu ita yakewa wulaqanci akan Rashida.  Dama hausawa sunce bulalar da aka daki uwar gida da ita tananan tana jiran amarya dan haka ki dena murna dan mijinki na wulaqanta kishiyarki akanki dan wata rana ke xai wulaqanta.


Mimi tayi tas tayi kyau dake ansamu jego original,  tayi shar kamar bata haihuba, tana yin arbain yaxo ya kwana suka koma tare. Mama ta dunga cewa su kular mata da mima, dan kowa yasan yadda mama ta dorawa mima son duniya fiye da komai a yanxu. 




Tanata fargabar haduwarsu, kamar ya sani ya kyaleta sai data kwana 4 da dawowa lokacin ta saki jikinta sannan ya far mata.  Ai kuwa ta dunga ihu suna kokawa, har ta tashi Mimi dake kan gadonta a gefe dole ya haqura karta tara masa yan aikin gidan a wannan daren.  Kwana biyu ana abu daya ya gaji ya tambayi ishaq "ishaq wai in mace ta haihu qara matsewa take ne?" ishaq bai bashi amsa ba sai dariya da yunduga kyakyatawa, ya fuskanci matssalar Bature dan shima sunyi haka da Farida.  Sai da ya gama dariyar ya bashi amsa "in mai kyan jiki ce tana kuma kamewa tayi tsam,  musamman in  suka samu kulawar jego.  Kawai abunda xakai,  kabi a hankali kamar daren farko da haka har ku saba"  yabi shawarar ishaq, akuwa aka wuce gurin.  A Kullum yakan godewa Allah da kuma fadawa Mimi cewa, shifa gani yake kamar ba daga jikinta mima ta fito ba kuma ko cikinta bai nuna alamar wata halitta ta kwanta ba,  a taqaice dai Mimi tana cikin mata masu kyan jiki wannan flat tummy din da yake masifar so tananan ana masa gayu da ita. 



Sukaci gaba da rainon mima,duk sanda ka duba dp din Bature mima ce a jiki,  anty mami koda yaushe cikin aiken kayan mima take.  Suna tsoron karta kuma samun ciki,  hankalinsu ya kwanta da suka gane Mimi tana cikin irin matannan masu tsaftar shayarwa.  Má'ana wadanda basa period in suna shayarwa dan haka suka sake suna gurxar amarcinsu.  




Mima kyakykyawar gaske kamanninta da mumy sai qara fitowa suke, amma yar siririya ce sosai kamar little kamar yadda little tai musu fatan ta haifi irinta. Tana da sumar kai sosai kamar ta Mimi,  ta taso cikin farin jinin mutane kowa sonta yake Mimi dai tana tsananin kau da kai akan mima kamar ba diyarta ba kowa ya sheda hakan.



Tana shekara daya Anty mami ta aiko da kudi da kaya akai mata birthday acan kano gidansu na sharada kuma kowa ya hallata an kashe kudi sosai.  Mumy tunda aka haifi mima duk wanda xaiyi dinki acikin yayanta saita karbi ragowar kayan ta ajiyewa mima,  kafin ta shekara antara mata natives sunfi akwati daya.  Zuwansu kano birthday mumy ta bawa  mama kayan ita kuma ta auna mima aka tsantsara mata dogayen riguna Kamar yan kanti masu jeluna, ta ajiye a gurinta dan tayi shirin dauke mima ne sabida son diyar take fiye da duk yayanta da jikoikinta (abun cikin kwai yafi kwan dadi)




Wannan karan kudin hayar gidanta yana xuwa gaba daya ta dauka ko shi mijin bai sani ba ta biya musu umra kusan su 6.  Ita da Faty,  mama da mumy,  little da Bature. Kana ta biya wasu kudin aka hada harda yayan Faty da mima dan Mimi yanxu kudi take samu kota ina business dinta ya fadada kuma har yanxu bata daina yiwa mom adduar fatan alkhairi ba dan itace tushen komai.




Ranar da Bature yaji abunda Mimi tayi yayi mata godia da alqawuran soyayya sunfi cikin 80 leaves. 



Mumy kuwa ta kasa boye farin cikinta kamar bata taba keta haxo ba,  duk inda taje ko akazo mata kaji tana cewa "umra xamu ni da little da fadima.  Maryam matar Bature ce ta biya mana dukkanmu" wannan karan ma matan Baffa suka kuma haukacewa, amma babu yadda suka iya dole mama ta dauki jikanta suka wuce. 



Anyi umra lfy, Mimi tasha adduar fatan gamawa lfy a gurin duk wadanda ta biyawa umra din.  



Basu jima da dawowa ba tayi shirin yaye mima kuma ta fadawa mama.  Ana gobe xata yayeta mama taxo Abuja huxaifa ya kawota a motarta.  Suka kwana, washegari juma a ta dauki mima xasu tafi,  Bature kamar xaiyi kuka yace "Allah sarki mima yanxu na daina ganinki sai takalmanki da kekenki?" mama tace "to mara kunya baka isa dai ka hanani tafiya da ita ba,  dan wannan yar tun tana ciki akaimun kyautarta dama jira nake a cire a gora intafi da abata" Mimi tana kallonsu tace "mama  kamar yadda nayi alqawari a baya ba,  na baki ita duniya da lahira, nasan xaki mata kulawar da koni baxan mata ba"  tace "hakane uwata MARYAM" aka kwashe kayan mima tas har kekenta aka xuba a mota, dakyar aka banbareta daga jikin Bature tana kuka yanayi suka shiga mota suka tafi.  Daga uban har yar sun bawa mama tausayi,  ta dura mata freso ta bata rubutun yaye da akai mata ta jijjigata tai bacci.  Mimi da Bature haka suka wuni wani iri, batasan tana son mima ba sai yanxu,  gwarancin mima har gixo yake mata.  Xuwa yamma zazzabi ya rufeta sosai ga ciwon nono.  Yaje gurin ishaq ya karbo mata wani maganin ciwon nono wanda ya siyo musu ita da Farida a singapore dan ba a samunsa a qasar nan,  tanasha ta watstsake xuwa dare kuma tayi mamakin ganin nononta bai fadi ba yananan dam dashi kamar bata haihuba maganin nada kyau shiyasa ba ko ina ake samunsa ba. 



Acan kano mima ta saki ranta sabida maganin dangana da aka bata,  tayi qiba sabida samun kulawa ta musamman,  tuni ta shiga harkokinta ga yara a gidan ga kuma dady wanda duk abunda yaci saiya bawa mima.  Kuma kulawa yake bata sosai ko shurin mima kayi cikin rashin sani saiya rama mata. 



Mumy duk weekend saita turo an dauki mima ankai mata ita ta kwan biyu acan.  Kuma Kullum little tana bisa hanya mumy tana cewa taje tagano mata mima kar mama tana wannan haqurin nata matan Baffa su dunga yiwa mima mugun hali yadda dukaiwa Mimi.  Duk sanda little taxo tana komawa mumy da saqon qalau taga mima, kuma tana ganin mama baxata bari a taba mima ba balle ai mata mugun abu dan bata de haquri akan mima ko kadan. 




Mima yar gatan iyaye da kakanni duk sanda taje gidan mumy saita dakko make up kit din Anty little kamar yadda take kiranta,  ta xauna ta dame fuskarta kamar yadda taga little nayi.  In little ta farga da barnar mima saita duddumeta intai kuka kuma taxo tana lallashinta. 




Mimi da Bature kuwa soyayya aka balle kamar farkon aurensu,  suna planning na calendar ko withdrawal method,  dan Bature yaqi yadda suyi allura ko saka roba yace duk suna da illah kamar yadda ishaq ya fada masa. 


****** ******* ******** **



Tafe take cikin motarta sanyin AC na bugata, tagaji liqis yau sunyi mahawara mai zafi a court amma Alhamdulillah sunyi nasara. BARRISTER MARYAM AL 'AMIN ce,  wacce ta fara aiki shekara uku da suka wuce a matsayin lauyan mai xaman kanta wacce ta fito daga chamber din AL 'AMIN MEMORIAL CHAMBER.  Itace ta qirqiri chamber din ta xuba lauyoyi irinta kwararru a qoqarinta na tunawa da babanta.  Kowa yasanta akan aikinta sunanta yayi fice ne sabida tsayawarta wajen kwatowa yaran da akaiwa fyade haqqinsu da kuma matan da maxa kan saki su barsu da wahalar yaya, wanda ta haqiqance wayan sakin aure shike maida yara marayin tilas daga nan kuma yasa yara kwarara kota ina suna nemanrwa kansu abinci hakan kuma ke kawo yawaitar fyade.  Duk wanda yasan maryam yasanta da sanyin hali da nutsuwa, amma in irin wannan case din yaxo gabanta babu mutunci Sam tsayawa take ta fafata tayi ragargaxa harsai anwa wanda aka kama sukunci.  Barrister Mimi kenan, lauyan kare yara da mata kuma lauyan mijnta SULAIMAN A AZEEZ,  domin a komai nasa na dukiya itace take tsaya masa. 




Ta shigo falon a gajiye,  ta cire rigarsu ta lauya,  sanye take da suit riga da skirt ta dora Baby hijab a wuyanta.  Ta rage kayan jikinta ya rage daga ita sai shirt da skirt.  Ta nufeshi yana xaune akan carpet yana latsa system as usual.  Yana ganinta ya dauke system din kan cinyarsa dan bawa Mimi maxauninta ta hau ta dare shi,  yana cewa "hannu da xuwa my luv, ya shariar taku?  Nasan kinyi nasara kamar yadda kika saba" ta zare glass din idonsa tana shafa gashin bakinsa da yatsanta kana ta kwanta akan qirjinsa ta kewaye hannunta a qirjinsa shima ya kewaye qugunta yana shafa gashinta tace "ya Bature munyi nasara kam, amma nasha wuya fa lauyan da gayen ya dauka yana da wayo amma qarshe Allah ya dorani kansa" yace "mashallah tashi muje wanka dama kenake jira" ta miqe ya dauketa suna dariya suka shiga bed room. 




Sai da mima ta shekara biyar sannan Mimi ta samu ciki,  watan haihuwarta na tsaya ya dau hutu itama ta dauka,  Germany yakeson kaita ta haihu dan yace baxata qara haihuwa a 9ja ba tunda ta sha wahala a wancan karon. EDD dinta ya nuna saura 9 dayz ta haihu su kuma saura 7 dayz su tafi kamar yadda yake a visarsu. Suka wuce kano dan tanan zasu tashi. 





Tunda sukaxo Kullum da daddare yan uwansa da matansu na kusa kan shigo bayan isha a hadu duka a babban falo aita hira sai goman dare suke watsewa. 




Yauma sun hadu dukkansu, anata hira kamar yadda aka saba,  Mimi na gefe guda ta baje ta tasa robar pop corn dinta agaba tanaci,  wanda ya xama shine abincinta yanxu Kullum sai anje kwari an siyomata shi me madara. Cikinta yayi wani irin mugun girma wanda ake ganin kamar yan biyu ne. Tun jiya take jin ciwo amma tana sharewa dan tasan wasa farin girki haihuwar mima da haka ta fara amma sai data kwan ta wuni sannan ta haihu. Yanxu ma wani azabar ciwon kwankwaso takeji ko sauraran hirarsu batayi. Farida ta dubeta tace "besty yaya?  Ko jikin ne?" ta kalleta itama da nata cikin dan kusan tare suka samu tace "a a ummu jidda (haka take kiranta yanxu) babu komai inason xuwa toilet  ne" Bature ya miqe da sauri yaje ya dagata,  dan inta xauna bata iya tashi saiya dagata,  in kwanciya tayi bata iya juyawa saiya juyata sabida girman cikin. Xai rakata tace ya barshi yanxu xata fito fitsari xatai. 



Ta wuce bedroom ta tsuguna akan gwiwarta tayi gofo dan baxata iya tsugonon fitsari ba. Wani masifaffen fitsari takeji amma ta kasayi sai nishi take.

Acan falo sukaji shirun yayi yawa yasmin ta tashi ta bita. Ta dawo da gudu tace da mutanan falon "wlh haihu xatai" Bature yayi wuf ya shige dakin,  Audu kuma ya kira Faty a waya yace tai maza tazo mimi na labour. 





Lokacin daya shiga kan Baby ya fito,  ya gigice ya rasa yadda xaiyi tace "ya Bature ka zaremun Babyn" yace "to ya akeyi maryam?" tace "kunnansa biyun xaka dafe ka zaro" yayi yadda tace ai kuwa saiga qaton da namiji akan tiles din bandaki.  Sunanan ahaka mahaifa bata fado ba,  ita kuma sai ajiyar xuciya take yana mata hannu duk sun dame cikin jinin haihuwa,  Faty ta iso,  ta shiga ciki tasa safa ta taimaka mahaifa ta gado,  baby ya cika gida da ihu. Faty tace "ya Bature dan fita ka bamu guri in gyarasu" ya watso mata harara yace "da Allah uwar iyayi kiyi mata abunda xakiyi mata kawai,  ni dana karbi haihuwar?" tanajin haka tace "to riqeta in kwarfe mata jini" ya riqeta ta kwarfe jinin, Mimi ta kalleta tace "ya Faty sai anmun dinki ko?" tace "a a Mimi baki qaru ba,  Allah ya baki da sauki." 


Mama da mumy sukaxo a tare Audu ya kirasu ya fada musu,  mama ta karbi gyara Mimi,  mumy kuma ta yiwa Baby wanka.  Cikin qanqanin lokaci sukai fes gida ya dau turaren wuta,  aka fito da Baby su yasmin anata dauka da sauran mutane farida kuma cewa take yadda besty batasha wuya ba nima baxan sha ba ko ya ishaq?  Sai yace mata eh maman jidda. Sai sha biyun dare suka watse,  ya shigo bedroom din dauke da Mima a hannunsa tana tamai surutu. Su mama duk suna ciki,  ya nemi gefen gadon ya xauna inda Mimi keshan tea.  



Mima ta dane cinyarsa tace "ABBA wai kaine Dady na,  Maman Abuja kuma mamana?" ya sumbaceta yace "eh mana ai shiyasa nake ce miki my lovely mumy,  amma waya fada miki?" tace "yaya Dady ne" Bature yace "kinga wannan Babyn kuma qaninki ne" tace "to Dady na" ya dakko Baby yana kallonsa,  kamarsu daya dashi sak,  duk da yaron jaririne kamarsu da Bature bata buya ba.  Ya miqe ya kwanta akan gadon yasa Mima da Babyn a tsakaninsu da Mimi sukai baccinsu, mama da mumy suka fita suka bar musu dakin. 



A taqaice dai Germany din daba ajeba kenan,  tunda abunda xai kaisu Allah ya kawoshi cikin sauqi. Ranar suna yaro yaci sunan "AL AMIN" Mimi tayi murna da sunan da babanta da yasa tana kiransa ABBA. 


******* ****** *********



Rayuwa ta tafi, Mimi ta xama attajira sosai,  ko aikinta ya isa ya riqeta balle business dinta wanda ya zama gagarumi ita kanta batasan adadin dukiyarta ba.   Duk sanda ta fidda xakkah asibiti take xuwa ta gaida marasa lfy a fito mata da wadanda suke da lalura babu kudin magani kona aiki ta biya musu kuma dama ta dade da wannan buri tun tana qaramarta,  sai kaga mutum ya rasa ransa ko ya nakasa akan kudin da basu taka kara sun karya ba, shiyasa take xuwa can takai zakkah. 




Gidan Baffa kuwa tuni Al amura sun dai daita,  abunda kuwa yasa hakan shine;  anty tayi wani zazzabi mai zafin gaske wanda yasata sanqarau daga baya kuma tayi jijjiga tasha wuya sosai kamar baxata tashi ba,  Allah yayi da ragowar shan ruwanta a gaba.  Ana ganin abun ya warke amma ina dan saidata shekara biyu cis tana jinya komai sai anmata.  Ansha wahala tun yayanta nayi har abun yayi tsaho suka dakko mace matashiya tana kula da ita dan babu manya duk sunyi aure sai qanana guda biyu. Mimi itace kan gaba wajen nemawa Anty magani da yawon asibitoci manya na kudi duk da yayanta sunayi amma ita tafisu hidimar kudi.  A qarshe dai ta warke ragal, abun dadi kuma sai Anty ta shiryu ta wannan hanya,  ta nemi gafarar mama da Mimi da duk wanda taiwa mugun abu.  Ta kwantar da kai sosai dan yanxu ko magana bata dameta ba saita wuni batace komai ba, sai dai ka ganta da casbaha.  Umma ganin abokiyar burminta abunda Allah ya aiko mata, itama tayi saurin watsar da makamanta ta nemi yafiyar kowa aka xauna lfy.  Girman da Baffa yaso taja a matsayinta na uwargida taqi ada yanxu ta dakkoshi ta dorawa kanta.  Ta riqe gida sosai tsakaninta da kowa girmamawace.  Mama itace qaramarsu kuma duk tafisu sauqin kai ta basu hadin kai gida yayi dadi Yayi kyau xaman lfy ya samu xama daram. 



Mimi itace attajira a gidan, kowa yasan haka babu wanda ya kai ko rabin dukiyarta, in biki ya tashi takansa aje shagonta na sai da furnitures a debowa amarya kaya iya girman gidanta.  Ta daukewa Baffa wannan nauyin, in kkuma namiji ne xata hado lefe na kece raini ta kawo.  Tuni ta qara gyara gidan ta saka AC taiwa su mama kayan daki iri daya sak.  Ta dakko masu girki wanda itace ke biyansu in sun gama wacce take da girki aikinta kawai rabo.  


Baffa kuma aikin hajji ta biya masa yaje, ranar har kuka yayi yace "abunda na gaxa yi miki yau kinmun Maryam Allah ya jiqan mahaifinku Aminu"  mama ta kama qasa sosai itama har private skul Mimi da Faty suka bude mata anan Hotoro bayan layinsu bayan tayi retire a aiki. 



Baffa ya kance "fadima haihuwar yaya mata tai miki amfani, yayan da ake miki gori akan baki haifi namiji ba gashi sun cika miki daki da jikoki maxa (Faty yayanta 4 duk maxa) wannan shi ake kira da "Goran duma me yado" kai madallah da haihuwar ya mace" duk sanda ya fadi haka sai jikin su Umma yayi sanyi dan sunsan da su yake.  Mamace tace Dan Allah ya dena tuna musu tunda sunyi nadama. 



Wannan karon shekarar Abba 3 Mimi tai wani cikin dan Bature cewa yayi gara suyi su gama karsu jera dasu mima. A cewarsa aure xai mata tana qare secondry skul zai aurawa Dady,  jidda kuma yar ishaq xai aurawa Adil dan Audu.  Ya hadasu ya kaisu jamiar Madina suyi xamansu can suna karatu da aurensu. 



Cikinta yana 7 months sukaje yawon bude ido qasashe daban daban ita dashi da mima da Abba. Dubaice ta qarshe daganan xasuyo gida.  




A Dubai sun fito xasu wata shago sanye take cikin doguwar riga baqa me duwatsu farare hannu da gaban rigar ta nade kanta da mayafin rigar tayi kyau sosai ta qara haske sabida jin dadi tana riqe da hannun abba shi kuma Bature yana dauke da mima yar 9 years wacce tai bacci a kafadarsa  suna tafiya suka hadu da Badaru. 




Suka tsaya aka gaisa, yayi qiba sosai ya dunqule,  Mimi tai mamakin ganinsa nan dan tasan a singa yake kasuwanci to meya kawoshi Dubai sarin Kaya kamar yadda yace.  Shima a nasa bangaren dubanta yake,  har abada bazai daina danasanin sakin maryam ba.  Tace "ka koma saida kayan mata kenan?" yace "eh tun da dadewa amma wancan kasuwancin ma ban barshiba ina tabawa" ya shafa kan ABBA yace "mashallah wato Maryam tsautsayi da kuma rabon wadannan kyawawan yaran da xaki haifa ya rabamu" tayi murmushi ta kauda xancen da tambayar yayansa nawa.  Yace "guda bankwai ne" tace "bakwai?" cikin mamaki. Yace "eh ai bayan Nafee na auri wata yar abokin abba, to ita tana da biyu Nafee tana da 5" tace "Allah ya rayasu" yace "amin" mama ta tashi daga bacci ta juyo tana kallonsa yace "yan mata ya sunanki?" kamar ankunna radio ta fara xuba "ni sunana HALIMA SULAIMAN AZEEZ. Mumy ma sunanta Halima sulaiman,  mutane na kirana MIMA. Amma Anty little da friends dina a skul suna cemun preety , ABBA kuma yana cemun ya mima, Dadyna kuma yana cemun my lovely mumy" Mimi tai mata tsawa tace "stop it Mimi, u talk too much"  Abba kafin a tambayeshi sunansa yace "ni kuma sunana AL AMIN SULAIMAN, ana cemun Abba mamana tana cemun abbana ya mima na cemun broda. Mama tace nima innasami qani zai dunga cemun ya Abba" ya fada yana taba cikin Mimi.  Kunya ta kamata ta ture hannunshi.  Badaru yace "mashaallah Allah ya rayaku ya baku ilimi mai amfani yasa kuyi koyi da kyakykyawan halin mahaifiyarku" Bature yaja hannun Mimi sukai gaba yace da Badaru "amin amma kyakykyawan hali sukam sun tsotsa a nono, so ko bakai musu addu a ba suna dashi." Badaru ya bisu da kallon shaawa yaran ko yace family din sun burgeshi. 


Mimi sunayin gaba ta kalli Bature tace "meye hakan da kayi kenan?" yace "Mimi luv ban taba ganin mutumin da yayimun abu na kasa mantawa dashi ba irin Badaru,  ina jin tsanarsa innna tuna shiya fara saninku diya mace sannan kuma ya azabtar dake shiyasa na kasa yafe masa" ta fuskanci kishi ke damunsa, ta sanyaya murya tace "amma ai kai kuma kaina fara so a rayuwata" ya juyo yana kallonta ya hadata da yayansa ya rungume yana jin qaunarsu. 



***** ************* ******


Xaune suke kaf dinsu cikin qaton falon gidan mumy,  birthday din Dady ake yau na cikar shekarunsa 75 a duniya wanda Mimi da yasmin suka shirya kuma suka dau nauyi.  



Cikin yayan mumy babu wanda babu har Anty mami dake nesa taxo.  Mimi tana kusa da mama da mumy a xaune tana fama da qaton cikinta suna aikin hada kayan rabo a qatuwar jakar takadda me dauke da photon Dady wacce xa a raba in anjima da yamma. Abba kwance akan cinyarta, Mima ta tsallako taxo itama ta kwanta akan cinyarta.  Abba ya hau ture kanta wai saita tasan mai a cinyar mamansa.  Mimi ta daga mima a jikinta da cewa "ke tasar mai a cinyar babarsa, haka kawai ki hanamun babana sakewa" Anty mami tace "mima taho kinji mamana,  kema in banda nuna qoqon usuli meye na xuwa jikinta ki kwanta keda kike da iyaye da yawa,  dan tsabar gata ma ke kakanninki iyayenki ne"  mama ta dubi Mimi tace "Mimi anya baxaki dena runquma dannan a cinya ba kina fama da qaton ciki" tana shafa kan abba tace "haba mama!  Babana ne fa,  kuma duk kunfison mima shi bamai yimun kara akansa shiyasa nake lelen abina" tace "ai shikenan" 



Audu ya shigo ya kallesu Cikin shaqiyanci yace "mumy, gaskiya ke kyakykyawa ce, abu daya yayi miki cikas, kedin gajeriya ce. Da ace duguwa ce wlh sai dai shugaban qasa ya aureki" tayo masa daquwa tace "Dan ubanka haka ubanka ya ganni da gajartar ya aureni kuma na haifi dogo kamarka"  aka kwashe da dariya,  ya kalli yasmin yace "honey babu magana?" ta harareshi kawai dan haushinsa takeji dan yayi mata wayo taje ta cire robar planing yayi mata ciki wanda ita bata shirya masa ba. Rabonta da haihuwa tun Adil.  Ya kada kai ya fita, mumy ta riqe haba tace "oh ni halimatu, tun kana haifar danka saika haifi jikanka.  Audu ya maidani kamar kakarsa" aka kuma kwashewa da dariya, Faty tace "wlh mumy ya Audu da Lubna halinsu daya, sun iya shaqiyanci." 




Bature ya shigo shima ya kallesu duka ya xauna kusa da mumy ya dafata yace "my lovely mumy, ina alfahari dake" tayi murmushi tana shafa kansa.  Ya dubi Mimi yace "Mimi luv" ta bashi amsa "yaya luv" akaci gaba da hira  can ya kuma kallonta yace "Barrister MARYAM" ta kuma bashi amsa "ENG SULAIMAN"  ya tashi xai fita har yakai qofa ya juyo yace da Mimi "Haj mairo"  a karo na uku ta kuma bashi amsa da cewa "Mal manu" ya xaro ido yace "lallai ma yarinyar nan ni kike cewa Mal manu😳" tayi far da ido tace "nima yaya meyasa kacemun mairo 🙄?"  aka kwashe da dariya ana kallonsu cikin burgewa, mumy tayo musu daquwa tace "🖐🏻 kunga yara muna zaune xai fadar sunan iyayenmu suke"  Anty mami tace "yi haquri mumy Romeo da juliet ne suke soyewa a gabanku" aka kuma dariya gaba daya. 



Anty mami ta bisu da kallo,  suna burgeta.  Bata yadda true luv yana existing saita dubi BATURE da MIMI.



Kamar yadda mumy tai hasashe adalilin kusancin yasmin da Mimi, yasmin ta koyi wasu halayen Mimi.  Kuma Mimi tasan yadda tayi ta shirya Anty mami da yasmin suka dawo kamar da aka koma xaman lfy.  Lamarin yayiwa Audu da mumy dadi tunda kowa nasu ne cikin yasmin da Anty mami. 



Ina miqa godia ta musamman ga 

Maman Khairat 
Maman shukra 
Anty sis 
Sadnaf 
Maryam Baita usman 
Hudallah (mrs JH)
Huraira Yabo 


(wanda da taimakonsu ne da kuma qarfafa gwiwa na ida rubuta wannan novel)


Ban manta da kuma ba 
Maryam (besty na)
Wasila (saqonki ya isoni)
Maryam sani mani 
Diyar khatibi 
Da  duk wata maryam(my maryams) 


Godiya ta musamman ga daukacin yan grp din 


Hudallah and Rahmatullah novels 
Fahimta novels 
Hausa novels 
S A AZEEZ Novels (maman khairee)&
FANTASTIC START WRITERS (F S W)👍🏼

Ina godia ga daukacin masoya fans din AL 'AMARIN MARYAM, wanda na samu damar ambata da wadanda lokaci bai barni na fada ba.  Masu bugomun waya da masu yimun text harda masu biyoni in box.  Dafatan ni da ku gaba daya xamuyi koyi da kyakykyawan halin "MIMI LUV"😊 


Tammat bihamdulillah. 

Sai munhadu a sabon novel dina in Allah ya kaimu 2018.



Ms Hajia 😊

No comments