Abraham Complete Hausa Novel
🍇🍇ABRAHAM 🍓🍓
*First edition*
#NoorEemaan
*WATTPAD*
@NoorEemaan
Am back again🚴♀️ it has been a while now....
All characters and lifestyle in this story are all drawn from my imagination, any resemblance of story should be considered as a coincidence!
⚠Caution ⚠️
Wanna liittafin Hakkin mallakan NoorEemaan ne! Ban yarda a juya min novel ta kowacce siga ba, idan kunne yaji...
The writer of
Rayuwar faheemah
Mijin ammina ne sila
Kyautar koda
Papi ne and now 👇
ABRAHAM...
*Wanna book din na so yin shi a matsayin paid book, amma saboda yanda masoyana suke ta tambayar :Noor yaushe zaki fara mana sabon novel ya sanya zan sakar muku shi a free domin Jin dadinku my fans, comment dinku kadai nake bukata, sannan wattpad fans dina kada ku manta da following dina sannan voting nagode...
*( bari na Baku wani takaitaccen labari game da book din ABRAHAM dazan fara in sha Allah...*
*Few days back ina cikin keke napep zuwa gidan mu, kwatsam naji labarin yazo brain dina, it's funny RIGHT? Yeah it's! Ni kadaina murmushi na saki domin abin yazo min a bazata, buh trust me guys zaku ji dadin shi fiye da zaton ku, ku dai ku rikitani da comments dinku kana kuyi following dina a wattpad.)*
_In sha Allah daga yanzu har zuwa lokacin dazan ajiye alkalamina wanna emojis din grapes da strawberry (🍇🍓) zan dinga amfani dashi a dukkanin novel dina kamar yadda kuka gani a sama, Dan haka masoya matukar kuka gan wanna emojis din 🍇🍓 toh tambarin novel dina ne_
*Note*
_Wanna shine second to the last novel dina Dana Yi, so ina ƙara reposting ne, ba sabo bane_
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
In the name of Allah, most gracious most merciful
Chapter 1-2
IMO OWEERI STATE NIGERIA
_WORDBANK ESTATE_
Unguwar wordbank na daya daga cikin unguwanin masu hannu da shuni a jihar imo. Wani Had'add'en gidane mai sassa daban-daban na hango, Ana wa gidan lakabi da ABRAHAM MANSION, sannan shine gida mafi kyau, haduwa, hadi da girma a Unguwar wordbank din gabadaya, cikin wani sashe na gidan na nufa....
Wata farar matashiya ce tallafe da katon cikin ta wanda yayi girma sosai, fridge ta nufa domin dauko Eva table water sakamakon kishirwan da take ji, balle murfin ruwan tayi ta fara sha, lumshe ido tayi kewar Mijin ta na nukurkusanta, Sosai take bukatar ya dawo, sai da ta shanye duka ruwan kana ta cilla Goran cikin dustbin, hanyar part din su ta nufa domin dauko wayar ta saboda ta yi Kiran mijinta, mutum mafi soyuwa a duniyar ta gabadaya baya ga iyayen ta, miskilancin sa kadai da ta tuno ya sata sakin murmurshi, she loves everything about him...
Har ta gifta sitting room ta dawo da baya sakamakon muryar mummy(madam Gloria) dake tashi, wani mugun murdawa dan cikinta yayi sakamakon abinda kunnuwanta suka jiyo mata...
"Sarah (babbar aminiyar madam Gloria) bazan taba bari wanna damar ta wuce ni ba, dole ne na salwantar da Nonye da Abinda ke cikinta, wanna aikin kuma zamu yi shi cikin daren yau kafin dan taurin ran ya dawo, domin matukar ya dawo komai ya lalace min , kin san cewa yana da wayo sosai basai na gayamiki ba, Dan haka ki shirya karfen biyun dare zamu aikata lahira, sannan na fasa ihun kukan mutuwar ta da safe, bayan na gama da ita, sannan a hankali zan aika Abraham lahira shi ma, daga nan dukiyar ABRAHAM ya dawo mallakina kaf, abinda na dade ina buri Kenan" madam Gloria ta fada da yaran igbo tana sakin dariyar zallan mugunta.
Nonye dake tsaye a bakin kofa ta saka dukkanin hannayenta ta rufe bakinta, sakamakon kukan dake k'ok'arin kufce mata, sosai zallan al'ajabi ya kamata, da mutum ne ya gayamata cewa madam Gloria nada irin wanna mugun halin sai inda karfin ta ya kare, amma gashi da kunnuwanta taji, azahiri ba wai a duniyar mafarki ba...
Kokarin barin bakin kofar take domin wani mugun duhu ke kokarin ratsa idanun ta, burinta ta isa dakinta domin Kiran Abraham ko da ita da Dan cikin ta basu rayu ba, amma zata so Abraham ya san da wacce yake zama, sai dai tana daga kafa daya tayi luuuuu zata fadi, sak'amak'on haka kofar ta girgiza, a kuma daidai lokacin ne madam Gloria da aminiyar ta Sarah suka kai idanun sa ga kofar a firgice, domin basa son kowa ya San da nufin su har su aiwatar dashi
Ta bangaren Nonye kuwa zaro fararren madaidaitan idanun ta tayi cikin tsananin tsoro da rudewa, domin Sam bata so su san cewa tana labe, hakan yasa ta aro jarumtar ta tsaya kan kafafunta, maimakon ta nufi dakinta sai tayi hanyar waje domin yafi mata sauki bacewa ganinsu...
tana fita waje su madam Gloria na bud'e kofar sai dai wayam basu ga alamun mutum ba...
Kallon juna suka yi, kana suka sake janye idanun su, cikin rashin yarda madam Gloria tace" kawata Sarah anya babu wanda ya mana labe kuwa“ ta tambayi Sarah da yaran igbo.
"abinda nake hasashe Kenan" Sarah ta amsawa madam Gloria
"tabbas akwai wanda ya mana labe, masu aiki basa shigowa nan sai idan za su yi aiki ko shirya dining table, shiyasa na zabi mu yi maganar a nan, amma zo muje in gani ..." madam Gloria ta fada tana nufar part dinsu Nonye....
Sai dai sama da kasa ta duba babu Nonye babu alamar ta, sosai hankalinta ya tashi kana zarginta ya tabatta.
A haukace ta nufi compound din gidan ta tambayi mai gadi ya sanar da ita cewa babu jimawa yaga ta fita...
Ai bata jira mai gadi ya karasa jawabin sa ba ta koma ciki ta dauko key din mota ta fito, kana ita da Anty Sarah suka fada ciki ta bawa motar wuta suka bar gidan a guje, shi dai mai gadi da kallo ya bisu kana ya tabe baki ya koma bakin aikin sa....
Bayan sun fito babban titi ta latsa wani number, bayan seconds biyar kacal aka daga... "hello Emma mu hadu a junction yanzu"
Daga dayan bangaren saurayin da aka kira da Emma ya amsa hadi da kashe wayar, wanda kallo daya mutum zai masa ya fahimci cewa shi din tantiri ne...
mintuna goma kadai suka kawo Emma Junction din, kasancewar ya San motar ta hakan yasa kai tsaye ya shige gidan Baya motar, yace "madam Gloria meye labari ne"? Ya tambaya cike da nuna shi din Jan wuya ne"
"babu labari mai dadi Emma, sanin kanka ne cewa duk sanda na kira ka aiki za ka min, ba kuma yau ka fara min aiki ba, in fact babu lokacin bayani" ta karasa tana fisgar motar da gudu, tayi driving mai nisa kana ta hango wata kamar Nonye tana sauri tamkar ba mai ciki ba, gudu ta kara har ta cimmata...
Nonye dake a rude ta waigo Jin karan mota a bayanta saidai wadanda ta hango ya sanya hantar ta kadawa, hakan kuma yasa Dan cikin ta wani tsalle
"get in the car" madam Gloria ta fada a kausashe hakan kuma shine karon farko data fara bayyana wa Nonye asalin kalar ta da tarin tsanar da take mata, domin dukkanin abinda ya shafi ABRAHAM tana adawa dashi
Sosai hankalin Nonye ya tashi, gashi shida na yamma ta kusa, ba tare da ta tsaya wani tunani ba ta fada dajin dake gefenta ta fara hudu, tana fatan ta tsira daga kaid'in madam Gloria.
Da gudu Emma da madam Gloria suka rufa mata yayinda anty Sarah ta shige motar, hakan nan take Jin wani yanayi a tare da ita mai kama da tausayi...
Sosai Nonye ke gudu tana kuka, yayinda su madam Gloria ke bin ta a baya a kokarin su na kamota, sun yi gudu mai nisan gaske har karfin Nonye ya fara karewa hakan yasa ta fadi ruf da ciki yayinda ta buge kafar ta a katon dutsen dake gefen ta, zafin daya ishe ta ne ya sanya ta saki karan azaba, kokarin mikewa take amma ta kasa sakamakon nauyin da cikin ta yayi, gashi ya dunkule waje daya, tana cikin wanna halin ne su madam Gloria suka cimmata...
Cikin kuka mai matuk'ar ban tausayi tace "please don't kill me" (na roke ku Karku kashe ni)
Daf da fuskar ta madam Gloria ta karasa kana cikin tsantsar mugunta tace "don't worry Nonye darling bazan kashe ki a nan, saboda haka relax ok" ta karasa tana shafa gefen fuskar ta cikin mugunta kana ta fashe da dariya, can ta dinke fuskar ta ta kalli Emma tace "daukota mu bar nan kafin duhun ya kara yawa" tamkar kayan wanki haka Emma ya sabe ta a kafada ko tausayi babu, Nonye kuwa shiru tayi sai hawayen dake zuba a fuskar ta, karfin ta ya Kare gabadaya, a halin yanzu tafi tausayin dan cikinta....
Bayan sun fito titi Emma ya wurga ta a bayan mota , madam Gloria kuwa ta mika mishi bandir din yan dubu daya ya tafi cike da mata kirari....
*2:00am*
Ko ina da haske a gidan tamkar rana,
tsaye madam Gloria take a kan Nonye, macece mai matsakaicin tsaho hadi da kiba, fara ce irin farin inyamurai nan (igbo). Ta sha kitson twisting kananu, tana sanye da short skirt hadi da farar singlet Wanda hakan ya taimaka kwarai wurin bayyana katon tumbin ta. Ido ta Kurawa Nonye da a shekaru bazata wuce shekara ashirin da shida zuwa da bakwai ba, sosai Nonye ke cikin mayuwancin hali da katon cikinta dan wata Tara da kwana biyar, juyi take tana zub da kwalla masu zafin gaske saboda azaban da take fama dashi, magana takeson yi amma ta kasa furta ko da kalma daya ce, sai bakin ta dake motsi, ga cikin sai wani motsi hadi da juyi yake sosai, wanda hakan ke nuni da cewa dan cikin ya galabaita yana bukatar shakar iskar duniyar mu.
Murmushin mugunta madam Gloria ta saki, ganin hakkan ta yana daf da cimma ruwa, Anty sarah dake gefenta ta share kwallar tausayin Nonye, ta sani cewa duk muguntar ta, bazata iya kallon mace mai tsahon ciki a halin nakuda ba tare da ta taimaka ko sausauta mata ba, kusan awa goma Kenan da Nonye ta soma nakuda saboda tsananin tsoron da firgici, Sannan bata isa ta hana madam Gloria aikata komai ba, duk da kasancewar Anty Sarah kawa ga Madam Gloria, amma a gidan take zama permanent, tana kuma a matsayin kukun su ce, wanda madam Gloria ta tsara hakan ne gudun kada ABRAHAM ya fahimci wani Abu a tsakaninsu, sosai Anty Sarah ke Rayuwa a gidan tamkar a gidan su. sannan ta San cewa idan ta nuna wani yanayi na tausayi ga Nonye dake kwance, ba shakka madam Gloria xata iya mata komai, domin tasan cewa anty Sarah ta gama sanin dukkanin sirrin ta....
Da murnushi mugunta kan fuskar madam Gloria ta juyo ga anty Sarah, k'ank'ance ido tayi, kana cikin son gasgata abinda take karantowa a fuskar anty Sarah tace " SARAH! ba dai tausayi nake gani shimfud'e a fuskaar ki ba, yau she kika fara Tausayi? Domin tun zamanin yarintar mu ke din ba mai Tausayi bace"(ta tambayeta da yaran igbo)
Saurin sanja fuska Anty Sarah tayi, wanda da a ce madam Gloria ta lura da ta gano abinda takeson gani din. "ko daya bana tausaya mata, ranar da muka dade muna jira ce fa tazo, haba kawata sai kace baki sanin ba " Anty sarah ta fada tana sauke boyayyen ajiyar zuciya, tana fatan kada madam gloria ta gano ta...
Murmushin jin dadin madam gloria ta saki, mayar da kallon ta tayi ga Nonye, ta kara galabaita sosai gwanin tausayi ga cikin daya tsananta motsin da yake, gashi tana son magana amma ta kasa...
Babu zato, babu tsammani madam gloria ta dauki pillow ta shiga dannawa a fuskar Nonye da dukkanin karfin ta, shure_shure Nonye ta dinga yi da kafafun ta saboda sosai madam gloria ke cigaba da danna pillow a kokarinta na kashe Nonye, Anty sarah ta dauke fuskarta, karon farko da ta ji wani mugun tausayin Nonye, sannan tayi nadaman biyewa kawarta...
A yau taji tana tsanar halayenta, domin har da gurbataciyyar shawarar ta a kisan da madam gloria ke kokarin yi wa Nonye
miye laifin nonye? yarinya mai kirki da faram faram da jama'a....
Sai da Nonye ta daina motsi kana madam Gloria ta d'auke pillow'n daga fuskar ta, sai dai me duk da cewa Nonye ta mutu, numfashi ya bar gangan jikin ta, amma sosai dan cikinta ke motsi....
Salon na daban ne,
Comment dinku kadai zai sa na cigaba da ABRAHAM...
Noor Eemaan🦋
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
But
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
Sunday 19 December
8:46pm
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 3-4
(Not Edited)
Sosai tsoro ya bayyana a fuskar madam Gloria, domin abu ne wanda bata taba gani ko ji ba, ta yaya dan cikin Nonye ke motsi bayan ta mutu? Sosai murnan cikar burinta ya ragu
Mai da kallon ta tayi ga Anty Sarah data yi mutuwar tsaye, sosai nadama da tsoron Allah ya rufe ta, domin abinda ke faruwa yanzu ikon Allah ne mai yin yanda yaso.
"Sarah kina ganin abinda nake gani kuwa ko mafarki nake yi?" madam Gloria ta fada a rude, tana jijiga anty Sarah
"ba mafarki kike yi ba kawata, da gaske ne, amma ga shawara daya" ta fada tana satar kallon madam Gloria, fatan ta ta amince da tunanin daya zo zuciyar ta yanzu, domin ta hakan ne kadai zata samu sasaucin tsantsar mugunta da suka yiwa Nonye.
"meye shawarar ki Sarah fadi ina jinki" madam Gloria ta fada a kage.
"mezai hana mu fita da ita ta kofar baya inda ba security sai ki kira Emma ya hayo mota daga nan mu kai ta asibiti ayi operation kana a ciro dan cikin kafin gari ya waye mun dawo, idan ba haka ba matukar mutane suka Lura da dan cikin Nonye na motsi za a samu matsala domin abinda bakya so ne zai faru, ma'ana Dan Abraham zai rayu" anty Sarah ta fada tana fatan kawarta ta amince.
Jinjina kai madam Gloria ke yi cikin gamsuwa domin ta yarda da shawaran Kawarta dari bisa dari, babu bata lokaci ta kira Emma ta sanar dashi abinda take bukata, mintuna ashirin kacal ya kawo Emma unguwar wordbank, Kiran madam Gloria yayi yace ya iso, ta fada masa cewa ta Bude kofar baya ya shigo domin su biyu baza su iya daukar Nonye ba
Bayan su ukun sun fita da Nonye cikin sanda suka saka ta a mota Emma na mata kirarin har ta cika aiki ta masa banza domin yanzu damuwarta a cire dan cikin dake ta motsi, har Emma zai ta da mota anty Sarah ta fita tace ta manta Abu, cikin Sauri ta koma ta shiga dakin Nonye da Abraham wasu abubuwa wanda Allah kadai yasan me ta dauka, cikin wani Jakarta ta saka kana ta fito ta fada mota, ta tarar madam Gloria na mitar basu da lokaci fa, me taje dauko wa ne? Hakuri kadai ta bata domin bazata so ta San abinda ta dauko ba....
Bayan sun isa wani karamin asibiti inda da
farko likitan yace sai anyi bincike, hankalin madam Gloria ya tashi abinda tayi gudu Kenan shiyasa basu je babban asibiti ba, take ta siye likitan da makud'an kud'ad'e inda ya amince, aka shigar da ita aiki bayan sunyi gwaji ya tabbatar musu da Nonye ta mutu
Cikin awa daya aka ciro lafiyayyun kyawawan y'ay'an cikin Nonye maza biyu , dayan sak ubansa tamkar yayi kaki, dayan kuma sak Nonye.
Masu iya magana sun ce zakaran da Allah ya nufa da chara ko ana muzuru Ana shawo sai yayi...
Sun kansu likitocin Sun Jinjina ikon Allah, domin abu ne wanda bai taba faruwa a asibitin su ba, a cire rayayye daga matacce, gasu kuma yan biyu...
Su madam Gloria sun kansu sun girgiza da abinda ya fito a cikin Nonye, yayinda hankalin ta ya kara tashi, fatan ta kadai a fito da yaran ta shake su har lahira, yayinda anty Sarah ke tunanin hanyar tsiratar dasu....
Likitoci suka fara aikin dinka Nonye yayinda
Nurses suka yanka cibiyar su hadi da goge jikinsu da olive oil aka nade su a wani babban towel domin babu kayan saka musu, bayan komai ya kammala, anty Sarah ta saci jiki ta je wajen babban likitan tana kuka tace ya mata Alfarman tseratar da Rayuwar yayan, domin madam Gloria bazata bari su rayu ba, da fari likitan bai amince ba, amma ganin yadda take kuka bilhakki da gaske ya sanya shi amincewa, kana yace zai ajiye record din komai daya faru a yau din saboda ko da bincike ya taso watarana, take anty Sarah ta amince
Y'ay'an aka bata, likita yasa nurse ta bi da ita ta wata kofar inda ma'aikatan asibitin kadai ke bi har ya sadata da bakin gate, direct tasha ta nufa inda ta ji conductor's suna Kiran garuruwa masu yawa, ta rasa wanne zata shiga daga karshe taji anje GOMBE sauran mutum d'aya
Babu bata lokaci ta fada ciki, duk da bata San ko ina a arewancin Nigeria ba, amma ta San cewa yaran zasu yi nesa sosai da madam Gloria ta inda bazata taba kawowa ranta cewa suna arewa ba, duk da bata San abinda likitan zai fada mata game da yaran ba, bata kuma damu ba tunda burinta ya cika ta tseratar da Rayuwar yaran.....
Likita ke tsaye gaban madam Gloria yana sanar da ita cewa yaran sun mutu sakamakon ruwan haihuwa daya shiga kansu inda basu Lura da wuri ba, sosai murmurshi ya bayyana a fuskar madam Gloria wanda bata San cewa ya subuce mata ba, take Likita ya gasgata maganar anty Sarah ya kuma godewa Allah daya bata yaran ta tafi dasu, ganin duk ma'aikatan na kallon ta ya sanya ta ankara da abinda tayi, sai tayi saurin sanja fuskar ta zuwa ta zallan damuwa inda ta Riga ta makaro, tabbas madam Gloria ta cika shu'uma.
"Likita Allah ya jikan su, amma bazan iya kallon yaran ba, da wanne zan ji da mutuwar Nonye ko da rasa Y'ay'an dana saka ran zasu maye mun gurbin Nonye" sai ta saka kuka kana ta cigaba "a binne su kawai a makabartan asibitin nan, amma bazan juri ganin gawar su ba" ta karasa tana sakin sheshekan kuka...
Biyar saura na asuba aka basu gawar Nonye suka saka a mota, sai a lokacin madam Gloria ta Lura babu anty Sarah amma bata tsaya neman ta ba, domin bata so gari ya waye basu koma gida ba, a cewar ta Sarah zata zo gidan tunda ba bakuwar ta bane....
Wanna karan da kyar Emma da madam Gloria suka shigar da Nonye, suna yi suna hutawa har suka kaita dakin ta, hadi da rufe ta da bargo, falo suka fito ta sallami Emma ya tafi, kana ta koma dakin ta, tana fatan gari ya waye sosai domin yanzu karfe Biyar da mintuna ashirin ne.
*WASHEGARI*
Kamar yadda madam Gloria ta fada karfe shidan safiya ta gwala ihun mutuwar Nonye
sosai take kuka tana birgima a kasa tamkar gaske, hakan yasa ma'aikatan gidan suka shigo part din halin tashi, suma kuka suka saka sakamakon Jin abinda madam Gloria take fada, "ewooooo Nonye yata kin tafi kin barmu, tayaya zamu kasance cikin farinciki bayan babu ke, kin tafi kin barmu da son(ABRAHAM) ya zamu yi da rashin ki, bayan kece cikon farincikin mu, mutuwa kin min yankan kauna " sosai take maganganu cikin fitar hayyaci kai ka rantse da gaske take
Kowa na gidan yaji mutuwar Nonye matuka, domin macece mai son kowa, bata raina mutum komin kaskancin sa, haka zalika tana da son mutane sosai...
Kamar yadda yake a al'adar inyamurai idan mutum ya mutu basa binne shi a take, mortuary ake kai shi zuwa wasu lokuta kafin ayi bikin binne shi, hakan yasa madam Gloria da ta sanja shiga zuwa bakake tare da wasu yan'uwan su.
Haka al'adar su take idan anyi musu mutuwa komai na jikinsu yana kasancewa baki ne har izuwa wasu kwanaki.
*GOMBE STATE*
Bayan anty Sarah ta sauka a garin GOMBE ta shiga raba Idanu domin babu inda ta sani, ga yaran Allah ya basu wani mugun hakuri domin har yanzu basu yi kuka ba, daga karshe ta yanke hukuncin fara tafiya, tayi tafiya mai dan nisa kana ta shiga wani layi, gida na hudu idonta ya sauka a kai, haka kawai taji gidan ya kwanta mata a rai, shiga gidan tayi inda ta tarar da wata k'yakyawar yarinya fara sol hadi da iyayenta dake zaune a gefen ta suna hira cikin annushuwa
Da kallo duk suka bi anty Sarah ganin ta shigo musu babu sallama, "lafiya baiwar Allah" uban yarinyar ya tambaya a tausashe.
Jim anty Sarah tayi domin bata ji ko kalma daya daga abinda yace ba, dan haka tace "please can I use your toilet? Am really pressed"
Duk shiru suka yi domin babu mai Jin turanci cikinsu gwara-gwara baffa ya fahimci kalmar toilet din cikin abinda tace Dan haka yace "shalelen baffa zuba mata ruwa a buta"
Take yarinyar ta yi yanda yace kana ta kalli anty Sarah tace "gashi"
Amsar butar tayi, duk da a yawan lokuta idan fitsari zasu yi basu fiye amfani da ruwa ba, shiga bandaki tayi da jariran inda babu wanda ya lura cikin su Baffa cewar yarane sabuwar haihuwa a hannunta
Ta kai mintuna biyar a ciki kana ta leko ta kofar langa-langan inda ya huje ta ga baffa da Inna(matar baffa) sun shige daki, ya rage saura k'yakyawar bafulatanar yarinyar nan mai suna Aysha, ita ma daga karshe mikewa tayi zuwa nata dakin, duk anty Sarah na kallon su...
Ganin babu kowa a tsakar gidan ya Sanya ta ajiye jakar hannunta hadi da jariran a kasa cikin bandakin, kana a hankalin ta Bud'e kofar cikin sanda ta fito, sai da ta je soron gidan ta fara sauri-sauri gudu-gudu domin barin Layin.....
Ga wacce take bukatar ayi adding dinta a group chat this num👇
07082281566
NoorEemaan 🦋
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
WATTPAD
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da facebook su yi join ta wanna link din.
Chapter 5-6
Sai da anty Sarah ta fito babban titi kana hankalin ta ya kwanta, ba tare da ta bata lokaci ba ta nufi tasha domin hawa mota da zai sadata da asalin kauyan su, Sam bata damu yamma tayi ba, haka zalika bata damu ko jin tsoron tafiyar dare ba, duk da yanda ta kai ga tsanar zaman kauye amma shine waje da zai sa hankalinta ya kwanta, domin bata son abinda zai sake hada ta da madam Gloria, ta kuma sani cewa har abada zasu da sauran kwannciyar hankali, domin kashe rai ba abun wasa bane.
Fatan ta daya mutanen nan su rike yaran amana, kuma in sha Allah zata yi kokarin sada Abraham da y'ay'ansa a lokacin daya dace matuk'ar tana raye, hawayen nadama ne ya saukar mata tuno cewa sune silan mutuwar Nonye, yanzu meye ribar su?
*GOMBE*
Baffa ne ya fito daga daki inna na biye dashi, "indo! Indon Baffa!!" baffan ya kira ta yana lekan Dan karamin dakin ta
"na'am baffana" ta fada cikin murya kasa-kasa wanda ke nuni da bacci ke shirin daukar ta.
Fitowar ta yayi daidai da dariyar da Baffa ya saki, kana cikin tarin kaunar tilon 'yarsa yace" shalelena ba dai bacci kike shirin yi ba ga magriba ta gabato"
"wallahi baffana bacci nake ji sosai" tafada a shagwabe tana dago lumsasun fararren idanunta da ya dan rine kadan sak'amak'on baccin da take ji.
"kinga ki danyi hakuri kiyi sallah idan yaso sai ki kwanta, zo mu zauna a tabarma kafin ayi kiran"
"toh Baffa bari nayi fitsari Ina zuwa" tafada tana daukar buta domin shiga bandakin.
Inna dake garken dabobbi tana tasar nonon shanu ta saki murmushi hadi da girgiza kai, domin sosai indo da Baffa ke kaunar juna wani zubin 'yar kallo take zama...
Kafar hagu indo ta saka a bandakin bakinta dauke da addu'ar shiga bandaki, sai dai addu'ar makalewa yayi sak'amak'on abinda tayi tozali dashi a kasan bandakin, shin mafarki take ko gaske? Ko ko shin aljanu ke kokarin bud'e mata ido?
Sanin cewa bata da mai bata amsa ya sanya ta kwala ihu daya yi matukar gigita su Baffa, hankali tashe suke nufi bandakin dan ganin abinda ke faruwa, ya kuma saka Indon su ihu...
*IMO STATE *
Zaune madam Gloria take sanye da bakaken kaya kamar yadda yake al'adarsu idan anyi musu rasuwa, idanunta sunyi luhu² sakamakon kukan karyan da take yi ba dare ba rana matukar a idon jama'a ne, sosai mutane ke tausaya mata, domin har tafi iyayen Nonye nuna mutuwar ta girgiza ta...
Wata yar'uwar su ce ta kalli madam Gloria hadi da cewa "Gloria kiyi hakuri hakan nan, sannan ya kamata zuwa yanzu ki kira ABRAHAM domin ya sani, saboda babu amfanin cigaba da boye masa"
Wani kuka madam Gloria ta saki har da majina tace "tayaya zanyi in sanar da dana wanna mummunan labarin? Banason hankalin shi ya tashi" ta karasa cikin kuka tana bubbuga kafafunta a kasa, riketa duk sukayi suna bata hakuri hadi da karfafa mata guiwan ta kira shi kan cewa ya dawo gida amma kada ta sanar dashi mutuwar Nonye sai idan ya dawo kasar.
Tana Jan majina ta fara dialing number'n shi kana ta daidaita muryar ta...
*KOREA*
Kwance yake gefen beach a wani had'add'en kujera sanye da boxer, sai sunglass dake manne a idanun sa, haka zalika sauran mazan sanye suke da boxer musamman masu shiga ruwan yayinda matan ke sanye da bikini wanda daga kirjinsu sai al'auransu ya rufe. Kyakyawane, chocolate color mai haske, yana da kirar nan da akewa lakabi da *giant* sai had'add'en six-packs dinsa idaunsa bai fiye girma ba, amma suna da matukar jan hankali, hancinsa dogo ne mai dan kauri, yana madaidaicin lips daya kara fuskar tasa kyau ainun, akwai wani karamin dankunne a kunnensa yayinda ya rataya cross + a wuyansa wanda hakan ke nuni da cewa shi din mabiyin addinin chirista(Christian) ne.
Burinsa yanzu ya gama abinda ya kawo shi kasar nan ya tafi domin yayi kewar gida sosai, kasancewar agajiye yake dawowa ko damar Kiran nonye da mummy baya yi, dan karamin tsaki yaja wanda sautinsa bai fito ba sai labb'an bakin sa ne suka motsa.
Haka kawai yake jin ranshi ba dadi, latsa wayarsa yake kokarin yi Kiran madam Gloria ya shigo, yaji dadi sai dai Sam babu alamar hakan a fuskar sa, domin shi mutum ne miskili da zurfin ciki wanda kai tsaye mutum bazai iya karantar abinda ke fuskar sa ba.
Latsa kore yayi hadi da kara wayar a kunnensa "good evening mummy, I was trying to call you guys now" ya fada da turanci.
Daga bangaren madam Gloria kuwa sosai ta daidaita muryar ta kana tace " yes son! Ya kamata ka zo kawo gida hakan gobe, idan yaso ka koma daga baya" ta fada masa da yaren igbo
"mummy is everything alright? How's Nonye and my baby doing?" kit madam Gloria ta kashe wayar ta, domin batasan sauran amsar bashi ba.
Haka nan yake Jin cewa there's something wrong Dan haka babu bata lokaci ya shirya kana yayi booking flight Inda yaci sa a samun jirgin da zai je Nigeria, amma sai karfen taran dare.
Dan haka gida ya dawo ya shirya cikin wasu had'add'un kaya da ganinsu kadai zai tabbatar maka da tsadar su, wayoyin sa hadi da system dinsa kadai ya dauka kana ya tura sakon Gmail ga company daya zo takanas domin su cewa akwai dalili mai karfi daya sanyashi komawa kasar sa, amma zai dawo as soon as possible, daga nan filin jirgi ya koma domin zuwa lokacin takwas ta wuce, ba kuma yaso yayi missing flight.
*NIGERIA*
IMO STATE
Bayan ya sauka a airport ya kira lambar driver gidan hadi da sanar dashi yana Airport, babu Jimawa yazo amma wanna karon driver'n bai yi masa surutunsa irin yanda ya saba ba, hakan ya dan bawa Abraham mamaki domin yasan driver akwai surutu sosai, amma Sam bai nuna ba
Tafiyar mintuna ashirin ya sada su da Abraham mansion, sauka yayi, bai jira driver ya Bude masa ba, direct ya shige general parlour sai dai abinda ya gani ya sanya gabansa fad'uwa sosai domin a iya saninsa a kuma al'adar su ta igbo sai idan mutum ya mutu ake sanya bakakken kaya irin haka, toh me yasa duk suka sanya bakin kaya? Waye ya mutu? Yayi duka tambayar a ransa yana bin fuskar kowa da kallo
Da sauri madam Gloria ta taso, ta isa gareshi kana ta fashe da kuka sosai tace....
_A GASKIYA COMMENT DINKU YANA KADAN HAKAN KE SANI RASA KARFIN GUIWAN TYPING DAN ALLAH IDAN KUN KARA YAWAN COMMENT ZAN DINGA YI MUKU KODA BAYAN KWANA DAYA NE, IF POSSIBLE KULLUM, DOMIN INA DA AIKI SOSAI NAKE DAUREWA NAYI MUKU DAN HAKA KUMA KU FARANTA MIN DA COMMENT DINKU_
Noor🦋
26/12/2021
9:41am
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
_note wanna ba sabon typing bane, reposting nake, so duk mai so ya fara bi yanzu ba sai nayi nisa ace daga farko ba_
Chapter 7-8
Yana shirin yin magana Kenan yaji muryar madam Gloria na fadin
"son munyi rashi, munyi rashi babba, Nonye ta tafi ta barmu, tafiya ta har abada, Nonye is gone for ever son" ta karasa tana fadawa jikinsa hadi da rungumeshi, yayinda sautin kukan ta ya karade gabadayan falon.
Tamkar wanda aka watsawa barkono haka ya runtse idanunsa, ji yayi gabadaya dakin na juya masa, sosai gabansa ke faduwa tamkar zata Faso kirjin sa ta fito
Nonyen sa ta mutu, ta tafi, tafiya ta har abada? abinda madam Gloria ta fada ya Shiga dawowa kunnuwansa , a karo na biyu madam Gloria ta kara cewa "ta haifi yan biyu wanda suma a take suka mutu, wayyo ni Gloria ya zanyi da raina" wanna karon k'wak'walwar Abraham ce ta daina gane komai sak'amak'on abinda madam Gloria ta kara fada, wanda ya sanya guiwowin sa yin Sanyi har ya gaza daukar gangar jikinsa, tilas ya sulale kasa, gabadaya jikinsa ya dauki rawa tamkar wanda yake cikin kankara, sabanin hakan gumi ne ke keto masa, na zallan tashin hankali, ga gashin kansa sun mimmike, duk da cewa babu ko digon hawaye a jajayen idanunsa, amma dole dukkanin wani mai tausayi da imani ya tausayawa halin da Abraham yake ciki a yanzu.
Rikeshi madam Gloria tayi tana kuka hadi da bashi hakuri, ko kala ya gaza furtawa domin nauyi da labb'ansa suka yi, hannu biyu ya sa ya rike kanshi dake barazanar fashewa, haka ya kasance cikin wanna halin fiye da awa uku kuma ko motsi bai yi ba, banda zuciyarsa dake bugawa da sauri² mutum zai yi tunanin matacce ne....
*GOMBE STATE*
Ba tare da su baffa sun lura da jariran dake kasa ba suka riketa hadi da cewa "aysha lafiya meya same ki, yi magana meya same ki aysha? " suka fada a tare suka duba jikinta...
Idanunta ta runtsa, sakamakon hakan hawaye ya zubo kan kyakyawar fuskar ta, hannu ta mika ta yiwa su baffa nuni izuwa ga kasan bandakin inda babies din ke kwance wanda zuwa yanzu sun fara mutsu² sak'amak'on sanyin ruwan bandakin daya fara ratsa ta cikin towel din zuwa fatar jikinsu, a tare suka zaro idanun su ganin abin al'ajabi, da ba dan kada su kara firgita tilon diyar su ba, da ihun suma zasu zunduma, a take kuma k'wak'walwarsu ya tariyo musu sanda anty Sarah ta shigo da farin towel din nan, amma basu taba tunanin cewa abu mai rai ne a ciki ba, a tunanin su ko wani kayan ta ne bata son ajiyewa a waje shiyasa ta shigar dashi bandakin.
Sosai mamaki da al'ajabi ya rufe su, babban tambayar su anan shine menene dalilin ajiye yaran da anty Sarah tayi? Domin basu ga alamun tabin hankali ga anty Sarah ba, bare su ce rashin cikakken hankali ne ya sanya ta manta yaranta a Bandakin, shakka babu wanna babban al'amari ne ya shigo cikin Rayuwar su...
Baffa da tausayin yaran ya gama rufe shi ya tsunkuya, amma gabansa na faduwa, amma ya dake, domin abu ne wanda bai taba ji ko gani ba ne ya ratsa gidan sa, sosai ya dake gudun kada ya kara firgita su Inna, addu'a dauke a bakinsa ya hade yaran a jikinsa, kana ya kalli su Inna yace "ki dauko jakar nan ku fito daga bandakin hakan nan" ya fada yana barin bandakin, sai a lokacin indo ta Bude idanunta dake ziraro da hawayen zallan tsoro, cikin tsoro Inna ta sanya hannu ta dauki jakar hadi da riko hannun indo suka fito daga bandakin....
Direct dakinsa baffa ya nufa da yaran, hakan yasa cikin muryar tsoro indo ta ce "wayyo baffa nah! kada ka shigar dasu dakin ka, Kar su cutar da mu, kila ba mutane bane, ni gaskiya bazan iya kwana a gidan nan ba, Dan Allah baffa ka fitar dasu daga gidan nan, muje mu nemi matar mu bata yaran ta " ta karasa cikin zallan tsoro mai hade da kuruciya hadi da sakalci....
Itama Inna irin tunanin Indo ne a ranta na cewa
Yaran ba mutane bane, amma bata furta ba, sai sai tsaf baffan ya karance ta, hakan ya sanya shi sakin murmushi, ya kuma girgiza kansa, tabbas duk shekarun mace da kaifin tunanin ta namiji ya fita koda bai kai ta yawan shekaru ba, ba tare da kuma yayi magana ba ya ida shigewa dan karamin dakin sa, ya kuma san cewa zasu biyo bayan sa domin basu taba ketare umarnin sa...
Wata jibgegiyyar kodaddiyyar malum-malum baffa ya janyo cikin kayansa ya saka yaran a ciki ya lullube su kana ya kwantar dasu kan gado irin dai na kauyen nan, towel din ya fitar waje ya saka cikin roban wanki ya saka kilin da ruwa ya jika shi, kana ya saka kilin ya wanke hannunsa sosai sannan ya koma dakin....
Gyaran murya yayi hadi da mai da duban sa ga Aysha Indo yace "shalelen baffa ina so kwantar da hankalin ki, ta ina kike tsamanin zamu ga matar? Wacce hanya tabi? Ba mu sani ba, Allahu masani.
Sannan ba fa manta yaran tayi ba, ko mai tabin hankali ta san kaunar abinda ta haifa, Allah ka dai yasan dalilin daya sa ta ajiye mana yaran, wadannan yaran mutane ne kamar mu, ki cire tsoro a ranki kinji, Allah kadai yasan dalilin daya sanya wadannan bayin Allah shigowa cikin Rayuwar mu, ko nace kaddarar mu" ya fada yana nuna yaran kana ya cigaba "domin akwai gidaje bila adadin a unguwar nan, amma nan gidan yaran suka fado, Dan haka nayi alkawarin kula da yaran nan har sanda zan daina numfashi, ina fatan zan samu goyan baya daga gareku"
Jinjina kai inna ta yi, wanda tsoron ya dan ragu sak'amak'on maganganun da baffan yayi, zai kara magana yaji an kwala Kiran sallar magriba a wani masallaci hakan ya sanya shi barin dakin da sauri yana gayawa su inna suma su hanzarta yin alwala kada su rasa jam'i domin su kan bi jam'i domin masallacin yana kusa da gidan su, wanda baffa shine Limamun masallacin....
Bayan an iddar da sallah da kamar mintuna talatin baffa ya shigo hannun sa dauke da bakar leda, kallon inna dake kokarin yin tarke/talke yayi, Cikin sauri yace "da kin fara yi wa yaran wanka da ruwan zafin nan, idan yaso sai a sake dora na tuwon" ba musu ta ajiye kayan tuwon, wani tsaftataccen bokiti ta dauko ta juye ruwan, kana ta zuba wani, hadi da gyara wutan, dakin baffa ta nufa da bokitin, kana ta fito ta nufi dakin ta domin dauko roban wanka wanda tun na indo ne amma yana nan da sauran kyansa da sabunta(kun San fulani akwai iya ajiya🤩)
Sai da ta wanke roban wankan kana ta dan sirka ruwan zafin kadan, kan gado baffa ya zauna, jariran na hannunsa yayinda indo ke gefe tana raba idanu wanda zai tabbatar wa mutum cewa har yanzu tsoron bai barta ba.
Ledar da baffa ya kawo inna ta zazzage, kayan jarirai da na Sanyi, sabulun yara da so so, man shafawar su, mataji(comb) hadi da hular Sanyi. Ba laifi siyayyar tayi daidai talaka...
Sosai inna ta wanke yaran ta kuma gasa musu jiki sosai, sai a lokacin jariran suka canyara kuka tun lokacin da suka shaki iskar duniya....
A kuma daidai lokacin ne Indo taji wani mugu_mugun tausayin yaran ya ratsa jikinta, wani Sanyi ya fara ratsa ko wani huda na gashin jikin ta, sak'amak'on hakan tsikar jikinta ya fara tashi, haka nan ta ke Jin wani yanayin na mussaman kan yaran Wanda bakinta bazai iya furtawa ba...
Ajiyar zuciya ta sauke, kana ta mai da duban ta ga yaran Inda zuwa Yanzu Inna ta shirya su cikin kayan da baffa ya kawo, sunyi kyau sosai gwanin sha'awa, karon farko da Indo taji tana son daukan yaran ta rungume su, hakan yasa ta fara takawa domin isa garesu....
*yanzu Abraham ya soma, yawan comment dinku shi zai bani kwarin guiwar cigaba da typing, idan ba comment nima bazan yi update ba*
*Sannan mai son nayi adding dinta a group ta yi chatting dina up ta lambar nan*👇
NoorEemaan🦋
07082281566
Share fisabilillah
Comment
Vote
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 9-10
Daidai ta gefen baffa ta dire gwiwowinta, kura wa yan biyun ido tayi, hakan nan taji gabanta ya bada ras! Amma sai tayi saurin aro jarumta domin so take wanna tsoron da bata san na menene ba ya barta, sosai yaran suke da kyau mai shiga rai, hannu tasa a nutse ta karbi daya, dayan kuma ta riko dan mitsilan hannunshi, kallon baffa tayi tace "baffana ina son su sosai , daga yau na dauke su y'ay'ana bama kanne ba, sannan kai da inna sun zama jikokin ku" ta fada Cikin iyakar gaskiyar ta kamar ba aysha indo mai kananun shekaru ba, domin duka shekarun ta bai wuce sha biyar ba.
Murmurshin farinciki ne ya bayyana a fuskar baffa, yasan cewa dama haka zata faru, tsoro ne dama ya sanya bata zo garesu ba, domin Indo na da son yara sosai, Allah ne ya nufa bazata samu kanne ba, domin baya mantawa Indai sunyi baki masu kananun yara ta dinga murna Kenan, amma da zaran sun zo tafiya zata fara kuka.
"toh Indon baffale Allah ya tayaki riko" dariya tayi har ya bayyana jerarrun fararren hakoranta, kana ta sanya hannu ta karbi dayan ta hada dukkansu ta rungume....
Ta dauki mintuna biyar a haka, yaran na manne da jikinta tana shakar d'adadd'an k'amshin jikinsu irin na jarirai...
Inna dake kallon su da murmushi a saman fuskar ta ta Mike domin zubar da ruwan da ta yi musu wanka hadi da wanke towel din da baffa ya jika, Bayan ta gama komai ta dawo dakin, baffa ya kalle ta yace "ina ga nonon shanu ya za a tasa a fara bawa yaran kafin mu ga yanda Allah zai yi, domin ragowar kudina nayi musu siyayyar nan dashi, naso dai siya musu madaran yaran"
"toh malam, bari na tasar musu, in sha Allah ma zasu karba, karka damu" ta fadi hakan domin kwantar wa da baffan hankali.
"Allah yasa" ya fada yana maida kallonsa da indo hadi da tsokanar ta, ganin yadda ta rike yan biyu gam bata da alamar kwantar dasu....
Bayan Inna ta kawo madarar shanun da ta dumama, ta wanke feeder ta zuba a ciki, cikin sauri indo ta karba ta fara sawa daya a baki, wani ikon Allah kuma ya karba ya fara tsotsa wanda hakan ya faranta ran baffa, yana fatan dayan ma ya karba.
Bayan dayan ya koshi, ta fara bawa dayan, shima ba laifi ya sha amma bai kai na farko ba, Bayan ya gama sha Inna tace indo ta kwantar da yaran hakan nan, basu da kwarin da za a yi ta daukar su sosai....
Ai fa nan indo tace bata San zance ba, ita haka zata rike su har gari ya waye, dariya su Inna suka saka mata kana da kyar aka lallaba ta kan cewa tare dasu za ta kwana, ganin lokacin isha ya karato ya sanya baffa ficewa zuwa masallaci, inda bayan sun iddar da sallar ne ya yi sanarwa abinda ya faru a yau na ajiye jariran da anty Sarah tayi, bai boye komai ba, ya kuma bayyana din ne saboda sanin halin jama'a, ya kuma yi hakan ne ko dan nan gaba, domin wasu zasu iya tunani, ko yin sharri ga tilon yarsa...
Nan fa mutane suka fara fadin albarkacin bakinsu, wasu ma har cewa suke sun ga shigowar anty Sarah Layin a firgice da farin towel , wasu kuma sun ce sun ga fitar ta cikin rashin gaskiya amma basu kawo komai a ransu ba, maganganu dai kala² kowa na fadin albarkacin bakinsa.
*IMO STATE*
Kwance yake flat kan had'add'en kuma yalwataccen gadon sa, azahiri idan mutum ganshi a yanda yake zai yi tunanin kallon pop'n daya k'awata saman dakin yake, sai dai sam ba haka bane, domin sosai ya zurfafa a tunani, Nonyen sa ta mutu? Abin ya yi matuk'ar tabashi fiye da zaton mutum, ganin abun yake kamar a mafarki, ji yake kamar yanzu zata shigo dauke da cikin sa ta zo gareshi, yanzu ta tabbata bashi da kowa sai mummy(madam Gloria) daddynsa ya mutu, mummy'nsa ma haka, tun daga lokacin daya rasa su ya rasa dukkanin farinciki kana walwalar sa ta ragu, shigowar Nonye cikin Rayuwar sa ba tare da ya shirya ba ya rage masa wasu abubuwan, duk da a lokacin babu soyaaya a gaban sa, ya kuma ki sauraran ko wacce mace, amma haka Nonye ta d'aure ta jure duk Wata shariya da yayi mata, ta kuma cire kunya ta furta tarin kaunar da take masa a matsayin ta na 'ya mace...
Hak'ik'a bai taba kawo wa ransa cewa zai rasa ta yanzu ba, ya kuma kasa yafe wa kansa kan me yasa bai nuna mata zallan soyaaya ko da rabin wanda take masa ba, gashi yanzu ta tafi tafiya ta har abada, ya tabbata bashi da kowa sai step mummy'nsa(kishiyar mahaifiyarsa wato madam Gloria)
Kasa rike kukan daya taho masa yayi, sosai ya saki kukan da sautinsa ke fidda zallan kunci, maraici, hadi da kewar da yake ciki, dole Abraham ya bawa mutum tausayi, domin cikakken namiji kamar sa na kuka tamkar karamin yaro.
Ya jima sosai yana kuka kana ya yi shiru yana sauk'e tagwayen ajiyar zuciya, k'amk'ame jikin sa yayi hadi da takurewa kan gadon yayi, duk da Sanyin da yake ji, amma ya kasa tashi ya kashe Ac ko kuma ya rufe jikinsa...
*Bayan Kwana Biyu*
Garin enugu a kauyen Nusukka anty Sarah ce ke zaune a asalin jahar ta, dakin karami ne ginin Jan kasa, duk da Rayuwar kauyen na matuk'ar bata wahala, domin ta jima rabonta da kauye, Rayuwar birni yagama ratsa ta, amma duk da haka ta fi Jin kwanciyar hankalin zaman nan din, Abu na karshe take son aiwatar wa kafin ta yanke duk Wata alaka dake tsakaninta da madam Gloria, hakan yasa ta fara latsa wayar ta, ta saka magic voice muryar namiji kana ta kara wayar a kunne ta mai dauke da barima guda shida....
Bangaren Madam Gloria kuwa zaune take a gadon ta da plate din kaza tana ci, key ta saka wa kofar domin bata so kowa yasan tana cin abinci, domin nuna wa take a gaban mutane cewa bata iya cin komai saboda tsananin damuwa da alhinin mutuwar Nonye, sosai take yagar kazar ta tana korawa da sanyayyar juice, Kiran daya shigo wayar ta ya sanya ta ajiye juice din hannunta, daukar wayar tayi, dam taji gabanta ya buga, ita kam har ta manta da anty Sarah, saboda yawan jama'a dake zuwa kullum yasa ta sha'afa.....
Latsa kore tayi ta kara a kunne ta, "Sarah ina...." kasa karasa maganar tayi a dalilin muryar namiji data ji, kara kallon number'n tayi taga dai number anty Sarah ce, tana cikin wanna tunanin taji muryar ta ce da yaren igbo "ba Sarah bace, Sarah ta mutu, ni yayan ta ne, Ina ta Kiran lambobin wayar ta ne ina sanar musu, hatsari tayi, Sarah ta tafi ta barmu, jiya aka yi burial din ta" muryar anty Sarah da ta rikide ta dawo ta katon gardi sakamakon magic voice din da ta saita a wayar ta.
"wayyo kawata Sarah! Sarah ta tafi itama? Ya zanyi da raina" madam Gloria ta fada tana fasa kuka, itama shesheka Anty Sarah ta fara kana ta katse Kiran tana dauke ajiyar zuciya, cire magic voice din tayi hadi da Layin da madam Gloria ta santa da ita, murmushi mai ciwo ta saki, domin tasan cewa ba lallai kukan da madam Gloria ke yi ya kasance har zuciyar ta ba, ta kuma god'ewa Allah da plan dinta ya tafi a daidai domin madam Gloria na da Wayo sosai.
Bangaren madam Gloria kuwa dariya ta tunsire dashi bayan Kiran ya katse, Abin mamaki kuma ga hawaye na zuba a idanunta, a fili ta furta "tabbas mutuwar ki ta shige ni Sarah aminiyata amma naji dadi ta wani fanni, domin kece kadai kike San sirrina na shekaru masu yawa, Dan haka hankalina ya kwana yanzu bana da matsala ta Bangaren ki, Abu daya ne ya rage ta yanda zan ga bayan Abraham, sanda na more dukiyar shi ni kadai " ta karasa tana sakin murmushin nasara...
*GOMBE*
A cikin kwanakin biyun nan mutane unguwa, abokan arziki, hadi da yan'uwa sai tururuwar zuwa ganin 'yan biyu suke, domin baffa Sam bai boye wa kowa ba, gudun abinda ka je ya dawo...
Kamar yau duk suna zaune da misalin karfe sha daya na safe, suna hirar su amma banda Indo da take ta faman yiwa yaran wasa, duk da suna bacci amma bata hakura ba.
"Baffa nah kasa wa yan biyu na suna, na dinga Kiran su kaji"
Kallonta duk sukayi suna mamakin tsananin soyaayar da take musu, murmushi dauke a fuskar Baffa yace "toh shalelen Baffa maganar da muke yi Kenan da Innar ki, na saka musu suna Abdul-jalal da Abdul-jabbar ya fada yana karban yaran hadi da yi musu huduba da sunan, lumshe ido Idon tayi, sosai sunan ya mata dadi....
" amma Baffa ni Anwar da Ammar zan dinga Kiran su kaji" kasancewar tana son sunan sosai, domin sunan wasu kyawawan yara ne a islamiyar su.
Babu musu Baffa ya amince domin yasan ma'anar sunan. Inna dai 'yar kallo ce, banda murmushi babu abinda take yi, dama macece mara son magana, amma idan ranta ya baci Abin ba dadi shiyasa Indo ke Tsoron bacin ranta.
Ranar da Ammar da Anwar suka cika sati daya baffa ya yanka musu ragon sunan daga Cikin dabobbin sa, Bayan an gyara an soya aka rabawa yan'uwa da abokan arziki....
_Har yanzu bamu shigo Cikin labarin ba, yawan comment yawan typing_
Share &
Comment
Noor ✍️🦋
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM 🍓🍓
*WATTPAD*
@NoorEemaan
_masu following account dina a Wattpad, Ina godiya, i love You guys_🫶🥰
https://facebook.com/groups/943534712916776/masu amfani da facebook su yi join ta wanna link din.
Chapter 11-12
(not edited)
Sosai jama'ar unguwa suka yabawa baffa da namijin kokarin da yayi, domin tabbas ya cika Muslumin kwarai mai yarda kaddara mai kyau ko akasin hakan, duk da baza a rasa masu tsegumi ba.
Yan biyu kullum suna tare da indo ko nauyin daukar su ma bata ji, ko aiken ta aka yi sai ta tafi dasu, ta goya daya ta rike daya, idan ma Inna tace kada ta tafi dasu sai ta fara kukan rigima, hakan yasa Inna ke kyale ta ta tafi dasu...
*IMO STATE*
Kamar yadda muka sani gawar Nonye na nan har yanzu, a kuma yau za a binne ta, kowa ka gani sanye yake da bak'ak'en kaya, wasu har da glasses baki, ciki har da Abraham wanda ya boye k'wayar idanunsa saboda jaa hadi da kumburin da suka yi, ko ina ya cika makil da jama'a ba masaka sinke, an shirya Nonye kana aka sakata a wani tsad'add'en akwati wanda kudin wanna akwatin ba kananun kud'ad'e bane, haka kowa ya shishiga mota ake tafi makabarta, inda suka tarar an hak'a rami da za a sa ta a ciki, gaban ramin aka ajiye akwatin, su pastor's, sister's hadi da wasu members na church din da Nonye ke zuwa a lokacin da take raye sun taru gaban akwatin domin yi mata addu'a, dama sun jima da zuwa makabartan isowar gawar suke jira.
Sosai su pastors din suka yi preaching (wa'azi) hadi da addu'o'i iri na addinin kirista (Christian) bayan sun gama wasu daga cikin mazan masu dakakiyar zuciya suka daga akwatin hadi da saka wa cikin ramin kana suka shiga watsa kasa a kai, cikin sassarfa Abraham ya koma cikin mota yayinda wasu hot tears suka biyo kuncinsa, wani mugun son matar sa ta shiga ratsa shi, har yanzu bai daina jin haushin kansa ba, a dalilin rashin mallaka mata zuciyar sa dabe yi ba a lokacin da ta fi bukata , tabbas a da ko digon sonta babu a ransa, amma ta jure ta cigaba da zama da shi hadi da bashi dukkanin Wata kulawa da soyaaya ba tare da gajiyawa ba, ina ma ana dawo da abinda ya wuce da ya nuna mata soyaaya ko da rabin wanda ta yi masa ne, wani tagwayen ajiyar zuciya ya sauke tamkar yaron goye kana ya saka hankici(handkerchief) ya shiga goge hawayen fuskar sa...
madam Gloria kuwa ganin an fara zubawa akwatin da Nonye ke ciki kasa ya sanya ta ruga da gudu gaban kabarin ta shiga kuka hadi da birgima, mutanen wajen kuwa sunyi matuk'ar tausaya mata, da kyar wasu yan'uwan Nonye suka janye ta daga kabarin suna kuka suna bata hakuri, hak'ik'a madam Gloria ta Shahara a fagen makirci, domin abinda take aikatawa a gaban mutane ba shi bane a ranta...
Bayan sun dawo gida, da karfe hudu na yamma aka yi weak-keeping inda aka cika har yafi na safe, an yanka shanaye guda uku, an yi girke-girke sosai tamkar gidan biki, ga palm wine, barasa, hadi da sauran abubuwan sha da yawa, ga waka dake tashi cikin yaran igbo, a takaice dai an yi bikin weak-keeping, an ci an sha sosai tamkar bikin farinciki ake, inda ba sabon abu bane a garesu domin al'adar su ce haka.
ABRAHAM da tun bayan dawowar su daga makabarta ya shige dakinsa ya danna key, domin a halin da yake ciki bayason hayaniya sam, Ji yake komai ya daina yi masa dadi bashi da sauran farinciki yana kuma ganin ya rasa dukkanin farincikin rayuwa, mutum daya yake gani yaji dadi a yanzu itace madam Gloria domin a tunanin sa ta dauke shi tamkar dan cikin ta, ga hayaniyar bikin weak-keeping din dake kara dagula masa lissafi, sam ko hayaniya d'aya baya bukatar ji, garin imo ma ya fita a ransa gabadaya l, duk da kasancewar sa garin sa na asali.
Tsaye madam gloria take a kofar da zai sadata da dakin Abraham rike da tray mai dauke da abinci different varieties, sai da ta bata tsawon mintuna biyar tana k'ak'alo hawayen karya kana ta shiga knocking kofar, Abraham daya ji knocking din har tsakar kansa ya runtse idanunsa da karfi hadi da cije pink lips dinsa masu dan duhu, " son! Open the door" madam Gloria ta fada cikin muryan kuka da ta san zai gigita masa lissafi kasancewar abinda ya tsana yaji Kenan kuka, kukan ma na mace, macen ma ita da take taka rawar uwa a gareshi, ba shiri ya mike ya bude kofa kana ya dawo da baya ya zauna kan gado hadi da rike kansa dake Sara masa, wanda hakan yasa jijiyoyin kansa suka fito suka yi rudu².
Ajiye tray din tayi kan wani had'add'en sofa peach color daya kara kawata dakin, kana ta zauna dab dashi ta dora hannun ta a bayan sa, cikin sanyin murya tace "son! You have to bear it, Nonye is gone forever and will never be back, ka cire damuwa a ranka, sannan kayi Mata addu'a, kalli yanda kayi loosing a lot of weight, you no more talk to anyone nor eat food, I no it's painful, amma ka jure, Nonye will remain in our hearts forever, But please be patient OK? I brought your favorite food for you" ta karasa ta nufar sofan domin dauko Abincin.
Tun da ta fara magana ko motsi bai yi ba, haka zalika bai amsa mata ba, "oya open up" ta fada bayan ta debo had'add'en jollof rice daya ji kayan lambu hadi da namomi, ganin bai motsa ba ya sanya ta fara kuka, a firgice ya dago kansa, gwanin tausayi ya bud'e bakin sa ta sanya masa abincin a ciki, duk da dadin d'and'anon da abincin ke da shi amma ji yake kamar madaci yake ci, da kyar yaci loma biyar ya kauda kansa, tayi_tayi ya kara yaki, dole ta hakura hadi da bashi ruwa ya sha, kana ta bar dakin, tana kissama abubuwa da dama a ranta....
*KAUYEN GOMBE STATE*
Haka Rayuwa ta cigaba da juyawa
su Indo da ma mutanen duniya baki daya, daga kwanaki zuwa satittika, daga satittika zuwa Watanin, a yau Anwar da Ammar suka cika Watanin uku da haihuwa, sunyi bulbul gwanin sha'awa kasancewar madaran shanun ya karbe su, ga kamanin Abraham da Nonye dake kara fitowa kullum a tare dasu..
Kamar yau Inna da Indo na zaune a karkashin bishiyar lemon tsamin dake dakin, ga su Anwar na ta bangala dariyar su a dalilin wasan da aysha ke musu, Inna da ta yi tagumi tana kallon su da murmushi hadi da jinjina tarin kaunar su ammar a ran diyar ta aysha Indo, sallamar baffa ce ta katse wa Inna tunani, direct dakinsa ya nufa, da kallo innah ta bishi domin wanna shine karo na farko daya shigo gida babu walwala a fuskar sa...
Mai da kallon ta ga Indo tayi, taga wasa take wa su Ammar bata ma lura da shigowar baffan ba, a sanyaye ta Mike zuwa dakin baffan, sallama dauke a bakin ta, amsawa yayi a hankali, kusa dashi ta zauna, cikin tsantsar ladabi, kulawa, hadi da soyaaya tace "baffan Indo lafiya? Meye same ka? ban taba ganin wanna fuskar a tare da kai ba, duk tsawon shekarun nan da Allah ya hada mu matsayin ma'aurata, Allah ya huci zuciyar ka ko zan iya sanin dalilin wanna sauyin a tare da kai"
Duk da ciwon da cikin baffa ke masa bai hana shi sakin murmushi ba, kana ya kamo hannun Innah yace "ko daya ba abinda kike tunani bane, koda an bata min rai a waje bazan zo ga iyalai na da fushi ko rashin walwala ba, Dan haka ki kwantar da hankalin ki, ciwon ciki nake wallahi tun fita ta da safe, naje kamis(chemist) din cikin gari an bani magunguna" ya fada yana fito da bakar leda mai dauke da magunguna.
Fatan samun sauki Inna tayi masa, sun zauna shiru na tsahon mintuna, idanun baffa suka sauka kan jakar da anty Sarah ta bari a bandaki, "wanna ba jakar da muka gani a bandaki bane?" baffa ya fada domin ya tabbatar.
"Eh itace" Inna ta amsa.
"dauko ta mu gani" baffan ya fada still idanunsa na kan jakar.
Dauko jakar Inna tayi, baffa ya karba ya zazzage jakar a kasa take abubuwan dake ciki suka zubo kasa...
https://chat.whatsapp.com/JwYkGXFKcLH95WSHP9QoUg
(Ga link ku shiga)
_har yanzu bamu shigo cikin labarin ba, kamar yadda na fada a farko salon Abraham daban ne da sauran novels dina, comment kadai nake bukata_
_sannan kuyi hakuri kun jini shiru kwana biyu, busy ne ya min yawa sosai wallahi, ga babu wuta transformer ya lalace, chaji nake kai wa, Dan haka ku kara hakuri, ba kullum zan dinga posting ba, Noor na muku sahihiyar kauna_💞
Share fisabilillah
Comment
Mai son nayi adding dinta *a Noor novelist world* ✍️📚ta yi min magana ta number'n dake kasa. 👇
07082281566
Monday, 10 January 2022
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*WATTPAD*
@NoorEemaan
Chapter 13-14
(Not edited)
Wani had'add'en album ne ya fado, sai wani sarka na zallan diamond har wani kyalli yake mai dauke sunan NONYE da manyan harrufa, an kawata rubutun sunan da wani irin salo mai matuk'ar kyau hadi da Jan hankali duk wanda yayi tozali dashi, hannu baffa ya saka ya dauki album din, shafin farko ya bud'e hoton Abraham ne yana da shekaru goma hadi da iyayen sa da katon cake a gaban su, an yi decoration a wajen daya fi kama da hall da balloon masu kyau, wanda hakan ya yi nuni da birthday part din cikar Abraham shekaru goma aka yi.
Haka baffa ya cigaba da bud'e ko wani shafi na album din yana ganin hotuna kala², wani ya ga Abraham shi kadai, wani ya gan su da iyayen sa da kuma madam gloria, wani ya gansu tare da dangin su, gasu nan dai kala-kala...
shafi na gaba ya bude wanda hakan ya sanya shi zaro ido cikin zallan mamaki a sak'amak'on tozali da ya yi da hoton Abraham hadi da Nonye a ranar auren su inda Nonye ke sanye da white wedding gown ta rike flower irin na bride yayinda Abraham ke sanye da suit black daya yi matukar yi masa kyau ya kuma fito da halittar sa na karfaffa kuma lafiyayyen namiji, duk da babu murmushi a fuskar sa hakan bai hana hoton yin kyau ba, sannan hoton ya fito da fuskar su tarr.
Abinda ya bawa baffa mamaki shine hango tsantsar kamanin yan biyu a tare dasu Abraham, take zuciyar sa ta raya masa cewa wadannan sune iyayen ammar da Anwar, amma meya dalilin raba su da akayi? Sannan a wani hali suke ciki a dalilin rasa gudan jininsu? Meye kuma dalilin daukar su da anty Sarah tayi zuwa nan ta ajiyesu? Tabbas yana bukatar sanin wadannan amsoshin...
Kasa cigaba da kallon hotunan yayi, domin album din babba ne, hoton masu yawan gaskiya ne, ga kuma jikin sa daya mutu "baffan Indo da alama iyayen Ammar ba Muslimai bane daga yanayin su" Innah ta fada cikin tabbaci.
Jinjina kai baffa yayi kana yace "tabbas ba karya, abinda ke raina Kenan, na kuma kara tabbatar da hakan ta dalilin matar da ta ajiye su ta gudu yanayin shigar ta kadai ya isa ya sanar da hakan, dama haka Allah yake ikon sa, ya fitar da mummuna daga cikin kyakyawa, haka Zalika zai iya fitar da kyakyawa daga cikin mummuna, banda ikon Allah 'yayy'an da iyayen su ba Muslumai, amma gashi sun shigo cikin Rayuwar Muslimai"
Jinjina kai Inna tayi cikin tabbaci, numfashi baffa ya sauke yace "ina ganin wannan album din zai taimaka mana kwarai wurin nemo iyayen su, in sha Allah zuwa gobe idan naji dama-dama zan fita cikin gari domin nemo gidan talabijin(television) ko redio domin mu bada cigiyar su, har ga raina banason rabuwa da yan biyu, domin ina so su taso cikin hasken musulunci amma hakan bazai hana mu nemo iyayen su ba saboda bamu San a wani halin damuwa suke ciki ba, kuma in sha Allah idan suna da rabo zasu samu shiga muslunci...."
"Assalama alaykum Innah ki........ laa baffana yaushe ka shigo" Aysha da ta shigo yanzu ta katsewa baffa maganar sa.
Murmushi baffan yayi kana yace "indon baffa Kenan, ai yanzu kin daina ji da baffan ki sai su Ammar" dariya tayi cikin jin kunya.
Mika masa Anwar dake ta tsalle yana kallon baffa tayi, kana ta zauna kusa dashi rike da ammar, take idaunta suka sauka kan sarkan Nonye, hannu tasa ta dauka kana cikin murna tace "wayyo baffa siyomin kayi, kalli kaga sai daukar ido take" ta fada cikin murna da yarinta.
"ke! ajiye" innah ta fada a dan kausashe
rau rau tayi da ido kana ta mai da dubanta ga baffa tace
"baffana"
a shagwab'e...
"ki bi maganar Innar ki kin ji ko ? Baya ga haka gobe nakeso In sha Allah naje na bada cigiyar iyayen su Ammar da taimako sarkan nan hadi da photo album dinnan, dan haka ki ajiye kinji idan naje cikin birni zan siyo miki mai kyau"
Ihu Indo ta fara yi hadi da shure² ita fa ba za a raba ta da su yan biyu ba, cikin fada Innah tace " ke rufemin baki a wajen kafin na make ki, ke kin san dadin su bakya son rabuwa dasu, mahaifan su fa? kin San a wani hali suke ciki? Kin San wani radadi suke ji a halin yanzu? mu kan mu bamu so rabuwa dasu ba, amma tunda mun samu shaida dole mu sada y'ayy'an ga iyayen su"
*1 hour later*
Ganin da gaske kukan yaki karewa ya sanya baffa yiwa inna sigina kana yace "yi shiru Indon ta baffalle, mun ji mun hakura bazamu raba ku ba, maza share hawayen ki"
Shiru tayi tana k'amk'ame Ammar hadi da sauke ajiyar zuciya, daga nan su Innah suka shiga Jan ta da hira domin ta manta da komai, ai kuwa ta saki jikin ta ta cigaba da wasan ta da su Ammar, fita tayi waje da ammar a hannun ta, still sarkan nan na zaune daram a ranta...
ganin fitar Indo ya sanya baffa kallon Inna yace "dole cikin dabara zamu fitar da yaran ta yanda Ayshatu ba zata gane ba, idan Allah ya bayyana iyayen su yaran nan"
Dariya Inna tayi tace "gaskiya dai, in ba haka ba rigimar Indo yafi karfina"
Murmushi baffan yayi yana kara jin kaunar tilon 'yarsa na shiga zuciyar sa.
Da magriba baffa ya lallaba ya tafi masallaci domin yana jin ciwon cikin na lafawa, anjima ya fara, Inna kuma ta shige bandaki domin kama ruwa, sadaf-sadaf lndo ta shige dakin baffa ta dauki jakar nan kana ta koma dakin ta, bude jakar tayi ta dauki sakar kana ta mayar da zip din ta rufe bata damu da ko kallon album din ba, zata fita ta mayar da jakar kenan, taji motsin Inna ta fito hakan yasa cikin sauri ta cusa jakar kasan kayan ta sannan ta raya a ranta cewa anjima zata mayar idan Inna ta shige bandakin, sarkar ta saka a wuyanta hadi da mayar da hijab dinta jikin ta, dama tunda ta yi Wayo bata fiye zama ba hijab ba....
WASHEGARI
6:00am
Bayan baffa ya dawo daga sallar asuba yaji ciwon cikin nasa ya matsa masa gadan-gadan ya kuma kara shan maganin yaji ciwon bai lafa ba, hankalin su innah ya tashi sosai, ga yan biyu dake ta kuka sosai wanda ya kara dagawa su Innah lissafi...
*kullun nafsin za'ikatul maut* da misalin 9:00am na safiyar juma'ar baffa ya amsa Kiran ubangiji, mutuwar data girgiza dubban jama'a, inda kowa ke masa fatan ya dace domin yayi mutuwar shahada, Inna tayi namijin kokari wurin danne zuciyar ta matuk'a, domin ko kuka bata yi ba, sai na zuci daya fi na fili ciwo, yayin da Indon baffa ta sha kuka har da suman ta, domin kowa yasan tarin kaunar dake tsakanin su, haka suka hakura suka fawwalawa Allah lamarin su, sannan suka bi baffa da addu'a domin abinda ya fi bukata Kenan....
*************************
BAYAN KWANA ARBA'IN
A yau baffa ya cika kwana arba'in da rasuwa, zuwa yanzu su Inna sun hakura har su fara sabawa da rashin 6affa, amma yana nan daram a ransu, domin manta baffa ba abu bane mai sauki, zai kasance a ransu har abada, Bayan an gama addu'o'i, an raba abin sadaka mutane duk sun tafi, amma banda yan'uwan baffa da suka rage, dakin Inna suka shige, inda wan baffa mai suna sule ne a gaba, kallon Inna da ta rame sosai yayi, cikin gadara yace "baya ga wanna shanayen guda biyar da rago biyun nan ina sauran kadaran Mijin ki"
A sanyaye Inna tace "yaya babu komai, baya ga abinda ka lissafo sai gidanan babu wani kadara da ta yi saura"
"toh ai shikenan, shanayen zamu tafi dasu, eh zamu tafi da su, domin mu ma dole mu ci gadon dan'uwan mu, ke da yarki Kuma ku rike rago biyun nan" yana fadin haka ya fita, sauran suka mara masa baya, wasu hawaye masu zafi inna taji sun zubo mata, meyasa mutanen yanzu suka shagalta da son duniya suka manta da lahira, yaushe baffan ya rasu da har zasu hau kan gadon sa? Hakika mutuwa tayi musu yankan kauna, da yan biyu basu yi wayo ba, dame zasu dinga shayar dasu tunda sun kwashe shanayen? Inda taji dadi sun dan fara cin abinci kadan² Indo dake kallon inna ta share mata hawaye, domin duk da kananun shekarun ta amma ta fahimci wasu abubuwan dake faruwa...
*************
A haka suka cigaba da Rayuwar su cikin rufin asirin Allah, da tafiya tayi tafiya kudin hannun Inna ya kare, dole basu da zabi daya fi su siyar da ragunan biyun nan kacal, kayan abinci Inna ta siyo, wanda ta San zai dade musu kafin ya Kare...
*IMO STATE*
Sanye yake da wando 3quarter blue-black, da riga body hug fara daya yi matuk'ar yi masa kyau, zaune yake kan daga daya cikin had'add'un kujeran daya kara k'awata falon, idanunsa a lumshe tamkar mai yin bacci, madam Gloria dake gefensa a zaune ta kurawa plasma screen din ido wanda ba wani kallo take ba, lokaci zuwa lokaci tana juyowa ta jefa Abraham da wani irin kallo mai dauke da ma'anoni masu tarin yawa...
Bata zata ba, bare tsammani ta tsinci muryar sa kamar kullum cikin turanci domin bai fiye magana da igbo ba yace "mummy cikin satin nan zamu bar imo zuwa kaduna state , bazan juri cigaba da zama a nan ba kuma, I think zan fi samun peace of mind idan nayi nesa da Imo, I want to start a new life, already na siyi gida da duk wani abun bukata a can" ya karasa ko motsi bai yi ba, kai ka rantse bashi yayi magana yanzu ba.
Gaban madam Gloria ya fadi ras! Cikin tashin hankali tace "why son? You can still live a better life here, just forget about the the past and face the future, you re too young for all this, and why did you even prefer Northern state, if you don't want to stay here in Imo, then we can move to delta state or other Eastern state, but why kaduna uhmm son?"
Boyayyen ajiyar zuciya ya sauke, shi ma bai San meye zo kan shi ba, hakan nan shi ma yaji yana son zama a arewacin Nigeria, abinda bai taba bashi sha'awa ba Kenan, amma yanzu yaji zaman imo ya fita a ransa gabadaya, dama baya da company ko daya a garin, baya ga gidan nan, wanda shi ma ya riga ya siyar dashi ga wani attajiri.
Mikewa yayi tsaye yana gyara zaman rigar sa kana ya bar wajen cikin takun sa na lafiyayyen namiji mai ji da kuruciya...
Da wani mugun kallo madam Gloria ta bi bayan sa har ya bacewa ganinta, ta San cewa shi din kaifi daya ne, baya magana biyu, Kwafa taja kana tace "da Sannu kai ma zaka bi bayan Nonye na more duniyata Dan taurin rai kawai, kaje ka siyi gida a wani gari ban sani ba sai yanzu, babu abinda ya bari a halin shegiyar uwar sa"
*I WEEK LATER*
Kaduna state unguwar barnawa
Yau kwanan su Abraham uku da dawowa kaduna, duplex house ne da ginin ya tsaru sosai, yayinda aka zuba abubuwan k'awa a ko wani lungu da sako na gidan, fadin kyau da haduwar gidan bata time ne, just mai karatu ya yi imagine din gidan masu hannu da shuni.
Zaune madam Gloria take a had'add'en kuma yalwataccen falon kan daya daga cikin kujerun, ta harde kafa daya kan daya tana shan wine, ta chaba ado sosai tamkar zata je gidan biki yayinda take latsa tsad'ad'iyyar wayar hannunta kirar iPhone 13promax.
ABRAHAM ne ya fito daga saman bene inda nan ne bangaren sa, sanye yake da kananun kaya ga key din mota a hannun sa da alama fita yakeson yi, dagowa madam Gloria tayi cikin fara'a tace "my handsome son, ina zaka je? Gashi ina son mu yi magana, na fadawa musa mai gadi ya nemo yan aiki, yace min akwai Wata mai aiki a gidan dake jikin namu, ya fadamaka, ta ma zo mun yi magana tace a bata nan da 1 week zata nemo su“
"zan fita shopping ne mummy, idan na dawo zamu yi magana" ya amsa mata a takaice kana ya bata side hug ya fita cikin sauri, mota ya fada, sabon mai gadin su musa ya wangale masa gate din ya fita, duk da bai San ko ina a garin ba, amma ya San bazai bata ba, tunda yanzu duniya ta cigaba, kuma in dai mutum ya iya karatu an gama, goggle ya shiga yayi browsering nearest supermarket, take kuwa goggle ta fito masa da ita, wuta ya bawa motar ya harba kan kwalta....
WANENE ABRAHAM?.....
*Note*
(karfa ku manta da yaren igbo hadi da turanci madam Gloria da Abraham suke duk Wata magana, ina yawan amfanin da hausa ne domin mai karatu ya gane, sannan ya fahimci inda labarin ya dosa)
Share fisabilillah
Comment for more typing...
Noor🦋
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥❤🔥
_Kamar yadda na fada, Abraham ba sabon Novel bane, hakan ne yasa ban bude masa group na musamman ba, ma'ana group iya posting Abraham din, amma saboda massages na min yawa kan ana son na bude group, amma ban bazan iya bude wa ba gaskiya, domin bana son tarkarcen groups da yawa, Ina da dai group ɗaya na novel wanda ga link nan zaku iya joining, Ngd sosai jazakallahu Khair, ina godiya da soyayyar da kuke nuna wa books dina_.
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JwYkGXFKcLH95WSHP9QoUg
#NoorEemaan
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
*WATTPAD*
@NoorEemaan
Banyi editing ba🤒
Chapter 15-16
Asalin Abraham dan kabilar igbo ne na jihar imo state, haka zalika iyayen sa, mahaifin sa (Patrick Samuel) shahararren dan kasuwa ne, wanda duniya ta San da shi, inda ya hadu da mahaifiyar Abraham (Victoria) a wani bussiness trip daya je Canada, inda ita kuma Victoria tana hada master's dinta ne a lokaci, inda ita ma yar mai kudi ce domin mahaifinta babban lawyer ne.
Basu dauki lokaci me tsayi ba suka fahimci Juna, Bayan ta gama hada masters dinta ta gabatar da Patrick ga iyayen ta, inda ba a samu wata matsala ba iyayen ta suka amince kasancewar suna kaunar farincikin diyar su, sannan kuma Patrick ya kwanta musu a rai kasancewar ya hada dukkanin quality's din da suke so ga namijin da zai auri 'yar ta su, traditional wedding din su aka fara yi, inda aka gudanar da dukkanin Wata al'adar su a yayin biki.
Bayan Wata daya aka daura musu aure ma'ana dai suka yi Church wedding, farinciki da kwanciyar hankali hadi da zallan kauna ne yake wanzuwa a gidan Patrick...
Auren su na da wata bakwai Victoria ta samu shigar ciki, inda ba karamin farinciki Patrick yayi ba, son duniya suka d'aurawa cikin, in da suke a K'age Dan ya fito duniya suyi tozali dashi....
Bayan wasu Watanin Victoria ta haifi santalelle kuma lafiyayyen dan ta, sosai murna ya karu a gidan Patrick, in da suka dora son duniya ga yaron, ranar suna yaro yaci suna ABRAHAM kamar yadda Patrick yaci burin saka wa dansa matuk'ar yayi aure ya haihu...
*************************
*10 Years Later*
A kwana a tashi babu wuya wurin Allah, domin shekarun Abraham yanzu goma cif, ya gama primary school a wani tsad'add'en makarantar private dake imo, inda baya taba zuwa na biyu a school dinsu saboda tsananin kwazon sa...
***********
Bayan an gama bikin birthday dinsa da kwanaki iyayen sa suka yi masa rakiya zuwa England inda zai cigaba da karatun sa har jami'a kamar yadda Patrick yayi masa sha'awar yin karatu a waje, aka kuma yi sa'a ra'ayin su yazo daya da Abraham, duk da Victoria bata son danta yayi nesa da ita amma babu yanda ta iya domin tafi kaunar farincikin sa fiye da nata.
Sai da suka tabbatar komai yayi daidai kana suka dawo Cike da kewar tilon dansu, a rana sai su yi video call dashi sama da goma, as time goes on suka fara sabawa da rashin sa a kusa, inda duk bayan Wata hudu suke zuwa duba Abraham....
*Bayan shekaru biyu*
Patrick na hanyar dawowa gida daga ma'aikatansa ya ga Kiran Victoria ya shigo wayar sa, inda take sanar dashi kanta na ciwo sosai bata samu yi masa girki ba, kuma ta San baya son abincin yan aiki, Sannu yayi mata cikin kulawa, gama wayar su ke da wuya ya hango wani gidan Abinci, umarnin ya bawa driver kan su karasa gidan abincin, sauka yayi ya nufi cikin wajen da kan sa inda ya samu Wata budurwa Wacce take bangaren serving din mutane, kallo daya mutum zai mata ya karanci cewa ta Bude ido da yawa, ga iya kissa, Gloria Kenan...
Fried rice with chicken da hadin salad partrick yace ta hada masa takeaway ba tare da ya lura da karairayen da take masa ba, ita kuwa Gloria lokaci daya taji ya tafi da ita, bata bari ya tafi ba sai da tayi iya yinta ta samu number'n wayar sa.
_12:05am_
Kwance suke suna bacci su cikin kwanciyar hankali Kiran Gloria ya shigo wayar Patrick, wanda hakan yasa ya farka a zabure domin wayar na saitin kunnen sa, saurin danna answer yayi, zai yi magana Kenan yaji Gloria tace "Am so sorry for calling you at this time, is just that I couldn't help i......" kit ya kashe wayar gabadaya, domin ya gane matashiyar gidan Abinci nan ce, banda bata da tunanin a wanna daren zata kira shi, ko da bashi da aure bare yana da, ko meya shiga kansa har ya dauki number ya bata oho ya fada a ransa yana Jan tsaki, mai da kallon sa ga Victoria yayi yaga bacci take, ajiyar zuciya ya sauke ya koma ya kwanta.....
*Washegari*
Zaune mahaifin Abraham Patrick yake a office dinsa yana duba wasu files Kiran matashiya Gloria ya shigo cikin wayar sa, dauke idon sa yayi daga kan file din ya mayar kan wayar, take ya fahimci number'n yarinyar jiya ce, latsa kore yayi hadi da kara wayar a kunne sa ba tare da yayi magana ba...
"kayi hakuri sir, na kira ka cikin dare, bamu tashi daga restaurant ba sai after 11 ni kuma ina son jin muryar ka shiyasa na kira, forgive me please " ta karasa cikin wani salo na jan hankali...
"is okay, amma ki kiyaye because ina da mata banason Kiran daren nan"
"mata!" ta fada azabure...
"yes of course" ya amsa hadi da katse Kiran, domin hakan nan yaji yarinyar bata kwanta masa ba.
Daga bangaren Gloria kuwa wani huci mai zafi ta furzar, domin bata taba kawowa a ranta cewa yana da mata ba, kasancewar yawanci mazan igbo da matan su basu fiye aure a kananun shekaru ba, shiyasa bata kawo masa cewa yana aure ba, take ta ji wani matsanancin kishin matar tasa, kuma bata jin zata iya hakura dashi domin sosai ta kamu da son sa, ga alamun tarin arziki data hango a tare dashi....
kawar ta Sarah ta kira inda ta bata wasu shawarwari ta yanda zata mallaki Partick din cikin sauki...
Haka Rayuwa ta cigaba da juyawa, inda kullum Gloria bata gajiya sai ta kira wayar Patrick, shima tun yana ignoring dinta har suka fara gaisawa sama_sama, Gloria macece shu'uma mai bud'add'en ido inda ta san hanyoyi da dabarun janye hankalin da namiji, sai dai Abu daya ne yake damunta har yanzu bata ga alamun yana nuna kulawa ko so ga ita ba, bare ta kai ga maganar aure, hakan yasa taje har gidan kawar ta kuma abokiyar shawarar ta wato Sarah, inda ta bata shawaran su je wajen boka domin a k'ark'ato da hankalin Patrick zuwa gareta sai abinda tace dashi, hakan kuwa akayi, cikin lokaci kalilan Patrick ya haukace a son ta...
**********************★★★
Victoria mum Abraham na zaune Patrick ya kawo mata zancen zai kara aure, inda kirjin ta yayi wani irin tsalle, bambarakwai taji abun, domin da wuya kaga namiji ya kara aure irin haka a al'adar su da ma addnin su, bayan akwai matar sa a gida ba wai mutuwa tayi ba.
Abu kamar wasa fa Patrick ya dage lallai shi fa aure zai kara, labari ya basu a dangi da abokan arziki inda suma sunyi mamakin hakan kwarai, domin kamar sabon Abu ne a wajen su kasancewar hakan bai saba faruwa a gare su ba, iyayen Victoria suka yi fushi kana suka ce yayi divorcing yar su, domin bazata zauna da kishiya ba.
Abu fa ya kara tsamari, inda har iyayen Patrick din suna fushi dashi amma Sam bai damu ba, baya ganin kowa sai Gloria.
Da kyar Victoria ta lallaba iyayenta kan su yi hakuri kar a raba su tana son mijin ta uban dan ta, zata cigaba da zama dashi komai wuya komai dadi...
A lokacin Patrick ya sanar da Gloria yana da d'a Dake karatu a kasar waje ba karamin tashin hankali ta shiga ba, domin Sam bata San ya ma haihu ba, amma bata nuna a fuska ba, sai dai kamar yadda ta tsani Victoria haka ta tsani Abraham duk da bata taba ganin daya daga cikin su ba...
Bayan auren su Gloria ta tare a gidan, a lokacin ne victoria tayi hannu riga da farinciki, sosai Gloria ta matsa mata, duk da cewa ba shiga harkan ta take ba, ga Patrick yanzu Sam baya da lokacin ta, amma daurewa take tana shanye duk wani bacin ran da suke sa mata.
Kamar ko wani wata hudu suna kai wa Abraham ziyara England, wanna karon har da Gloria aka shirya tafiyar....
Inda bayan sun je Abraham ya tambayi mummy'nsa cewa wace ce Gloria? ta gayamasa cewa sabuwar mummy'nsa ce, sannan ya dinga bata respect kamar yanda yake basu, Gloria kuwa sai kulawa hadi da soyaaya take nunawa Abraham kamar gaske, da kuma taimakon Victoria Abraham ya sake da ita, sosai kuma Patrick yaji dadin yanda Gloria ke son Dan shi, kwanan su hudu suka dawo Nigeria.
*10 YEARS LATER*
Abubuwa da Dama sun faru cikin Wadannan shekarun, ciki har da mutuwar Patrick shekara daya Kenan, sak'amak'on hadarin mota da yayi, sosai matan sa suka ji mutuwar sa, bare ma mummyn Abraham, duk da babu wata soyaaya a tsakanin su har ya mutu, haka zalika cikin shekarun nan Abraham yayi nasaran gama secondary school din sa
*****************
Lokacin da lawyer din Patrick ya zo yana zayyana musu tarin dukiyar da Patrick ya bari, ba karamin mamaki ne ya kama Gloria ba, sabanin Victoria da ta San cewa mijin ta zai iya tara fiye da hakan domin yana da zuciyar nema.
Tun daga wannan lokaci Gloria ke neman hanyar da zata bi domin hallak'a Victoria saboda ta mallaki dukiyar gabadaya, a cewar ta Abraham karamin alhaki ne, bata ci nasara ba sai bayan wata uku, ta yiwa fruit din da Victoria zata ci allurar guba, kasancewar Victoria akwai son kayan itatuwa.
Ta kuma San yawancin mutanen zasu zata cewa tunanin mutuwar mijin su ne yayi ajalinta....
A lokacin da ta mutu kukan da madam Gloria tayi ba kadan bane, Abraham ma ya shiga matsanancin hali, kamar zai haukace, domin ya mallaki hankalin kansa yanzu, sosai rashin son maganar sa ta karu, haka zalika bayason shiga jama'a ko kadan.
Yan'uwan Patrick sun so Abraham ya dawo hannun sa madam Gloria ta sa kukan zallan makirci tace a bar mata shi zata kula dashi tamkar Ita ta tsugunna ta haife shi, Dan sun ga Allah bai bata haihuwa ba za a raba ta dashi, basu musa ba suka bar mata shi, kuma sun yarda da son da take yiwa Abraham, tunda sun sha ganin tana nuna so ga Abraham din idan sun zo gidan.
*Bayan Wata Biyu*
Abraham ya koma England ya cigaba da karatun sa, wanda ko sau daya madam Gloria bata je ba, sai dai ta kira shi a waya, shima bai damu ba, bai kuma sake take kafarsa a Nigeria ba sai daya hada masters dinsa a bangaren business administration, inda ya fito da sakamako masu kyau...
Bayan ya dawo Nigeria ya cigaba da kula da harkokin mahaifin sa, inda cikin kankanin lokaci ya farfad'o da bussiness din, ya hab'aka sosai, har mutane na cewa Abraham yafi mahaifin sa Patrick iya bussiness...
Madam Gloria tayi iya yin domin ta hallaka Abraham ta yanda zata kwashe dukiya ta gudu amma har yanzu hakan ta bai cimma ruwa ba....
KO MADAM GLORIA ZATA CI NASARA??? MUJE ZUWA ABRAHAM FANS....
*************************
DAWOWAN LABARI
(BACK TO STORY)
Bayan ya dawo daga shopping mall din, madam Gloria ta kara taran sa da maganar yan aiki inda yace ta tsara komai yanda ya dace kawai, kana ya sanar da ita tafiyar sa zuwa dubai gobe zai kuma yi kwana biyu domin zai je ya duba company'n sa na turare dake can, inda an sake yin wasu designer's perfume, murna tayi masa duk da bai kai zuciyar ta ba, a kullum tana jin zafin cewa ba Dan cikin ta ke sabon wanna nasarar ba, a kullum tana bakinciki rashin haihuwar da bata yi da Patrick ba, da ta sani taje tayi adopting yaro ko da a gidan marayu ne a zuwan it's ta haifeshi, domin ta kara samun tarin dukiyar, kuma tasan cewa zai yarda tunda yana jin maganar ta, amma inaaaa bazai yu ba yanzu, tunda wanda za ta ce shine yayi mata ciki baya duniya, bare ta hada karyan ta, tabbas madam Gloria zata yin duk abinda take so, kuma ya tsaru kamar gaske, domin ta shahara a fannin iya tuggu....
Bayan sati daya aka kawo mata yan aikin inda ta raba wa kowa aikin sa, sai dai bata bawa kowa daman shiga kitchen ba, saboda a cewar ta bata yarda da tsabtar su ba.
*Gombe State*
_Bayan wata biyar_
Bangaren su Innah kuwa suna cikin matsin rayuwa, domin Abinci da innah ta siya ya kare, Dan sana'ar da take a cikin gida ma sun cinye jari, ga su ammar har Dan rama suka yi saboda rashin ingantaccen Abinci da babu, kullum inna cikin tagumi take, da gari ya waye zata fara fargaban dame zasu yi karin kumallo? bama ta kanta take ba, ta yaran take, gashi Sam batason fara dorawa Indo talla, domin tun baffa yana raye ya tsani wanna dabi'ar ta dora wa y'ay'a mata talla domin ba karamin lalata tarbiyar yaran take ba, kullum addu'ar ta shine Allah ya kawo musu mafita...
Ajiyar zuciya ta sauke, Bayan ta gama tunanin halin da suke ciki, wanda hakan yayi daidai da kwad'a sallamar wata matashiyar mata cikin gidan.....
Share fisabilillah
Comment for more typing✍️
Noor🦋
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
#NoorEemaan
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
*I dedicated this page to my anty, Anty hawwa(TM@shoprite ) a very nice woman with a heart of gold, duk da girman matsayin ta bata da pride, much luv 😘*💞
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 17-18
Wa'alaikumu Salam Inna ta amsa tana leken mai shigowar kana tace "a'a wa nake gani kamar Bintu?"
"Nice Inna wuro" matar ta fada da murmurshi saman fuskar ta.
Lale maraba, sannu da zuwa karaso ki zauna, idanki Kenan?" Inna ta fada tana k'akk'abe saman tabarman wa bintu domin ta zauna...
Zama bintu tayi kana suka gaisa da Inna cikin yaran fillanci, Jim suka yi babu wanda yayi magana tsawon mintuna uku kana bintu ta muskuta tace "ya muka ji da hakurin rashin baffa? Ashe baffa ya Riga mu gidan gaskiya, zuwa na gida jiya na samu labari, Kin San wannan aikin namu Bamu ba lokaci gashi ba a kusa ba, Allah ya masa rahama"
Murmurshi mai ciwo Innah tayi kana ta amsa da ameen tana kokarin mayar da kwallar daya cika idanun ta, tsaf bintu ta lura da ita, amma bata ce komai ba, domin wani kukan ma rahama ne, gashi kuma ta ga alamun sauyin Rayuwa a tare dasu Inna, girgiza kai tayi cikin tausayin su, yayinda hirar da suka yi da matar da ta tace ta nema mata yar budurwa mai tsafta domin gyara dakunan su da yin girki, ko da bata iya girki ba za a kawo k'wararriya domin koya mata, burin matar dai yarinya mai tsananin tsafta take so.
Hakan nan Indon ta fado mata a rai, kallon Innah tayi tace " kiyi hakuri Inna wuro idan na yi miki shishigi naga kamar kuna cikin wani hali na rashin babu, gashi kuma can kaduna kusa da gidan da nake aiki ana neman 'yar budurwa irin su Indo, duk da dai na kwana biyu ban gan ta ba, amma nasan ta kara girma. Da' yar gidan garko zan kai, amma na fasa, domin ban ma sanar musu ba, ya kika ce innah wuro? Kinga kudin zai taimaka muku kwarai wurin sauyin Rayuwar ku fiye Dana baya" bintu ta karasa tana kallon innah, tare da fatan samun amincewar ta.
Bata rai Inna tayi kana ta girgiza kai tace "a'a bintu bazan iya ba, bazan iya tura 'yata kwalli daya aikatau ba, me mutanen gari da yan'uwan mahaifin ta zasu ce? Baz....."
"innah!"
Indo dake tsaye tun dazu a gefen su ba tare da sun lura bata ta fada.
A tare suka mayar da duban su daga inda amon muryan indo ya fito, karasawa Indo tayi gaban Inna ta tsugunna, riko hannun ta tayi, hawayen zallan tausayin kansu ya zubo mata tace "innah ta! ki amince dan Allah, ki amince, kinji? zan iya yin komai matuk'ar halal ne domin mu samu sauyin Rayuwa, meye amfani na idan ban taimaka miki ba Inna? Alhalin zan iya yin hakan? A Rayuwar nan idan mutum zai yi abu kar ya duba abinda mutane zasu ce? Sati daya kacal ya ishe su yin duk wani surutun su da gulma su hakura, da Muke shan wahalar mu waya tallafa mana?, ki bani umarnin yin aikin nan Innah, ina ji a jikina cewa akwai alkhairi a tafiya ta aikatau dinan, dan Allah Innah" ta karasa cikin Sanyi murya mai cakude da Kuka wanda ya sanya innah yin laushi"
"tabbas Inna wuro abinda Indo ta fada gaskiya ne, kuma sanin kanki ki ne Inna cewa bazan taba bari tarbiyyar indo ya lalace ba, zan dinga shiga ina duba ta, tun fa ina karama Muke a amatsayin makotan juna, kin San halina, banda mutuwar Ashiru mijina da yanzu ina tare daku a kauyen nan, amma gashi yanzu da kudin aikatau din nake kula da yarana da kuma iyayena, dan Allah innah ki amince in sha Allah baza kiyi nadama ba.
Numfashi Innah ta ja, gabadaya jikin ta ya mutu, a sanyaye kana cikin mutuwar jiki tace "na amince Allah yasa hakan shine mafi alkhairi Nagode miki bintu"
"ameen Innah wuro, ai yi wa kaine Karki damu" bintu ta fada cikin farinciki da sakin fuska kamar yadda ya kasance nature dinta ne yawan fara'a.
"gobe zan wuce in sha Allah sai ki hada kayanki mu tafi ko indo"
"anya zata biki goben kuwa bintu, ina tunanin sai ga ta gaskiya"
Murmushi bintu tayi tace "ho hoo hooo Inna ta fara kewar Indon ta, toh bari na rubuta address din a takarda, sunan garin dai kaduna ne , amma bari na rubuta sunan unguwar sai ta nuna wa mai adaidaita sahu, unguwar sananene, sannan ga lambar waya ta idan kin sauka sai ki fadawa mai adaidaita ya kira miki lambar ni kuma sai na fito na mika ki gidan da zaki yi aikin kinji ko" ta fada tana kallon Indo bayan ta gama rubutun a takarda.
Murmushi kawai innah tayi bata ce komai ba, bintu ta kara awa daya a gidan suna shan hirar duniya kana ta Mike domin tafiya, jakar ta ta Bude ta zaro duhu uku ta bawa Inna, ta kyar Inna ta karba, kara zaro dubu goma bintu tayi ta bawa Indo kudin mota, Inna tace Sam ta barshi duk da cewa ba kudin garesu ba, Murmushi bintu tayi halin innar na matukar burgeta, Sam Abin duniya bai dame ta, sai da ta rantse wa Innah cewa Wacce zata dauke ta aiki ce ta bayar da kudin kana Inna ta amince, har soro lnna ta rakata tana godiya kana ta dawo cikin gidan tana addu'ar Allah yasa tafiyar Indo alkhairi ce .
************************
Indo kuwa sosai ta fara kewar yan biyu da Innar ta, sai ta shige dakinta tayi kuka sosai, amma bata bari Innah ta gani, domin ta San zata iya cewa ta fasa zuwa kaduna aikatau din.
*BAYAN KWANA UKU*
A gurguje ta fito daga wanka ta shirya domin inna tace ta hazantar su isa tasha da wuri kada motocin safiya su tashi, kayan ta take hadawa cikin sauri inda idanun ta suka sauka kan jakar data ciro sarkar dake wuyanta, shaf ta manta cewa bata mayar da jakar ba kamar yadda ta aiyana a ranar, take ta tuno da baffan ta wanda hakan yasa wasu hawaye masu dumi suka zubo mata, wanda hakan yayi daidai da kwala mata Kira da Inna tayi, cikin duburbucewa ta saka jakar cikin Ghana most go dinta, zuge zip din tayi ta fito, bayan ta share hawayen ta.
Da su ammar dake tsaye suna mata bangala mata dariya a tunanin su tare zasu tafi ta fara sauke idanun ta, murmushin ta mayar musu yayinda take jin zuciyar na karyewa, kewar su mai tsanani na ratsa ta, rungumosu tayi gabadaya da hannayen ta biyu kana ta sumbace su a goshi.
Maganar da Inna ta yi mata ne ya sanya ta Mike rike da hannun su Anwar, yayinda Inna ta dauki Ghana most go dinta suka fito, machine biyu hau inda ya fito dasu bakin titi, kana suka sake hawa wani daya kai su tasha, saukar su a tasha ke da wuya suka ji wani driver yana fadin "Kaduna! Kaduna!! Kaduna!!!" sauran mutum daya...
Cikin sauri Inna tace "Ayshatu ki kula sosai da tarbiyyar ki, Karki manta duk abinda na fada miki, Allah ya tsare ya kiyaye, ga wannan ki rike a hannunki innah ta fada tana mika mata dubu biyu, sannan ki rike takardan nan da bintu ta baki da kyau" karasawa gaban driver Inna ta, biya wa Indo kudin kujera tayi, amsar jakar ghanan driver yayi ya saka a booth, lokacin ne wani kuka mai ciwo ya kufce wa Indo, tunda aka haifeta yau ne rana ta farko da zata tafi wani gari, ganin haka yasa Inna kama hannun yan biyu suka bar wajen domin zuciyar bazata juri ganin Indo na kuka haka ba, su Ammar ihun kuka suka saka ganin da gaske Ammuh dinsu(Indo) zata tafi ba tare da su ba, haka suke kiranta da Ammuh.
Sosai suke kuka suna tirjewa alamun suna son dawowa wajen Indo, kasa juran kallon su Indo tayi ta shige motar hadi da kifa kanta kan cinyoyinta tana sakin kuka...
2:30 daidai suka sauka a tashar kaduna, kalle² Indo ta shiga yi domin ta rasa wani waje zata nufa, driver daya kawo su ne ya lura da ita yace "yarinya lafiya dai? Ko wani kike jira?" ya tambaya, yana goga aswaki a bakin sa daya dan rine, wanda hakan zai tabbatar wa mutum cewa shi din ma'abocin cin goro ne.
"hmmm uhmmm, wajen na cikin takardan nan" ta fada tana nuna masa takardan, domin ita ba karatun boko ta iya ba.
Sai dai a fagen karatun addini ba baya bace.
Kallon takardan yayi yace "ai can zaki tsallaka sai ki samu a daidai ta sahu ki bashi takardan zai kai ki har wajen domin ba boyayyen waje bane.
Godiya tayi mishi kana to dora Ghana most go dinta a kai ta tsallaka dayan bangaren...
********
Saukar sa Kenan a airport, Cikin takun kasaita ya bar filin jirgi rike da wani jaka karami irin ta matafiya, tun tafiyar sa dubai bai dawo ba sai yau, ba wai dan bai gama abinda ya kai shi ba, hakan nan yayi zaman sa a wani tsadadden hotel dake can kasar dubai din, burin shi kawai ya isa gida domin ya huta shiyasa ma ya kasa hakurin jiran driver ya zo, ya gwammace ya hau adaidaitasahu....
Isar sa babban titi kuwa sai ya fara Jin wani irin, ta yanda zai tarar mai adaidaitasahu, domin abu ne wanda bai taba yi ba, bai taba hawa motar haya ba, bema San abinda zai ce ba, yana cikin wannan tunanin yaji tsayuwar mai keke a gabansa yana tambayar sa tafiya ne? Ajiyar zuciya ya sauke kana ya fada ciki, juyowa mai keke yayi yace "oga wani area zamu je? " duk da kasancewar Abraham baya jin hausa amma ambatar AREA da Dan sahun yayi ya sashi fahimtar abinda yake nufi, motsa cute lips din sa yayi yace "barnawa" kana ya fito da bakin sunscreen dinsa ya manna a fuskar sa wanda ya kara masa kyau ainun.
*****
Tun daga nesa Indo da ta gaji da tsayuwa, fuskar ta har wani jaa yayi kamar na tumatir gwanin tausayi saboda rana da ta jima tsaye a ciki, abinka da farar mace, ta hango wani keken da alaman mutum daya ne a ciki ya sanya ta fara tsayar dashi tun kafin ya karaso, domin yawanci masu wucewa a cike take...
Mai Dan sahu kuwa hango yarinya daga nesa ya Sanyi shi yin slow kadan da kadan , kana ya juyo ga Abraham yace "oga drop ne ko a dau passenger?“
Shiru Abraham yayi, ba tare da yace uffan ba, kara maimaitawa mai keke yayi still ba amsa sai kawai yayi wa Indo alaman ta taho, cikin sauri ta taho tana me mika masa takardan, karba yayi ya karanta yace "kudin ki dari biyar hau muje"
Cikin sauri ta hau tana sauke numfashi, yayin da taji bugun zuciyar ta ya karu, runtse idanun ta tayi da karfi tana kara k'amk'ame Ghana most go dinta.
Ta bangaren Abraham kuwa fiye da abinda indo taji yake ji, amma kasancewar shi namijin gaske yasa mutum zai yi tunanin bai San da zaman ta kusa dashi ba, Abin ya bashi mamaki kwarai, ta yanda yake jin kirjin sa na bugawa da sauri² daga zaman yarinyar da ko fuskar ta bai kalla ba cikin keken.
Indo kuwa ta jima idanunta a runtse kana ta ware su a hankali ta saci kallon fuskar sa, inda lafiyayyen beard din shi kadai tayi nasarar hangowa, domin ya dan juya kan sa ne, gabanta ne ya sake fad'uwa tayi sauri dauke kanta, jakar ta ta ajiye a kasa domin ta gaji, da kuma alama wajen da nisa domin sai tafiya ta ga suna yi...
Masu bada hannu ne suka tsayar dasu, wanda hakan yasa tilas duka ababben hawa dake bangaren suka tsaya, domin bawa yan dayan barin damar wuce wa...
Karan takun dokuna dake ratsa motoci suna wucewa ta fara ji, inda take ta rasa nutsuwar ta, domin tana matukar Tsoron su, daidai ta jikin adaidaitasahun su ta ga wani ya taho, saboda tsananin Tsoron da take ji ya sa ta ga kamar ita dokin ke kallo, a zabure ta manne jikinta Dana Abraham hadi da kamkame shi sosai ta boye fuskar ta a kirjin sa tace "wayyo Inna ta doki! bawan Allah kayi hakuri wallahi tsoron doki nake"
Duk da Abraham yaji wasu bakin al'amura a jikinsa amma ko gezau bai yi ba, "wacece wanna yarinyar da nake jin komai nata daban?" Ya tambayi kansa, kasancewar kuma bashi da mai bashi amsa ya sa shi kara lumshe idon sa yana jin yanda take goga masa fuskar ta a jikin sa, mai Dan sahu dake kallon su ta cikin mirror dariya ma yarinyar ta bashi...
Sai da ta daina jin takun tafiyar su kana ta dago kanta, wanda yayi daidai da bada hannu da akayi domin su wuce...
A hankali ta kalli yanda ta yamutsa masa farar Rigar sa, har kwallin ta ya bata Rigar, kunya ce ta kamata, kallon gefen fuskar sa dashi kadai tayi nasarar gani har yanzu, mamaki take ta yanda ko motsi bai yi ba, kana bai yi magana ba, ko dai kurma ne? Ta tambayi kanta, kasa tayi ta kanta a sanyaye tace "bawan Allah kayi hakuri kaji, wallahi tsoro nake ji"
Shiru babu amsa, dauke kanta tayi tana tunanin dai kurma ne, mayar da idanun ta tayi ga titi tana kallon jama'ar dake ta hada- hadar su, ga gidaje masu kyau da suke ta wujewa...
Mai adaidaitasahu yana jiran yaji Abraham yace zai sauka ya ji shiru gashi sun zo unguwar barnawa, ya kuma San idan ya tambaya ba lallai ya bashi amsa ba, kawai ya shiga cikin Layin domin sauke Indo, yana jinjina miskilanci irin na Abraham.
Daidai kofar gidan da bintu ke aiki mai keke ya tsaya, yace "yarinya mun iso, ga gidan Alhaji Umaru Kwangila nan"
Sauka Indo tayi tace "Nagode sosai ga kudin ka, amma dan Allah ka kira min lambar nan"
Amsar takardan yayi yayinda Indo ta shiga kallon gidajen Alfarman dake unguwar....
Bude gajiyayun idanun sa yayi, ganin har an zo gate din kusa da gidan su ya bashi mamaki, domin bai sanar da mai keke hakan ba, domin duk a tunanin sa a titi mai keken zai sauke shi, sauka yayi ya zaro kudi da bai San nawa bane ya mikawa mai Dan sahu ya tafi, galala mai keke yayi ganin uban kudin daya bashi, "wani irin passenger na dauko yau ni zubairu" ya fada a hankali yana kara kallon kudin, sosai kuma yaji dadi, ya kuma sa a ransa cewa daga nan gida zai wuce domin ya tashi daga aiki yau...
Indo da ta gama kallon ta ta dawo da idanun ta cikin keken taga wayam babu bawan Allah nan, yaushe ya sauka ta fada a ranta tana mamaki...
"gashi ta daga" mai keken ya mika mata wayar sa kirar vivo, fuskar sa fess kamar gonar auduga, amsa tayi tace "Adda bintu gani a kofar gidan, Indo ce."
Tana gama fadin haka ta mikawa mai keken waya, bata ma jira taji abinda bintu zata ce....
Mai keke kuwa yaja Dan sahun shi yayi gaba cikin nishadi, mintuna biyar kacal bintu ta fito da fara'a kan fuskar ta, rungume indo tayi kana ta dauki jakar Indon suka nufi gidan su Abraham, tana yaba mata da kokarin kawo kanta da ta yi....
WASAN YA SOMA GUYS🤩
Not edited 🤒
Share fisabilillah
Comment for more typing
If you re interested in my group just chat me up with this number 👇and I will add you.
07082281566
8:06am
Sunday 23, January 2022.
NoorEemaan🦋
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
WATTPAD
@NoorEemaan
EDITING IS NOT ALLOWED❌
_assalma alaikum my lovely fans, musamman wadanda basu karanta Abraham ba sanda nake typing din shi, zan kara maimaita wa Abraham ba sabon novel bane reposting nake, ban kuma buɗe masa specific group ba kasancewar ba sabon typing bane, masu min magana private kan nayi adding din su a group din Abraham wasu na basu amsa Wasu kuma ban samu basu amsa ba domin abubuwan sun min yawa, to cut it short, Ban bude wa Abraham group ba, waccan maganar dana yi cewa duk mai so tayi magana ayi addinig din ta a group nayi shi ne lokacin da nake rubuta littafin, yanzu dai kara reposting nake, fatan kun gane, sai dai normal group Dina nan novels, idan kina so kya iya shiga, Ngd sosai da kaunar da kuke nunawa littafai na, jazakallahu khair_🫶🥰
Chapter 19-20
(Not edited)
K'wank'wasa karamar kofar Bintu tayi mai gadi ya leko da kansa, ganin bintu ce ya sa shi washe hakoran sa, bude musu kofar yayi suka shigo, a mutunce suka gaisa yana tsokanar Indo kasancewar shi mutum mai faram-faram da jama'a.
Sunyi dan tafiya kafin su kara so kofar da zai sada mutum da general falo, kallon gidan Indo take amma ba ta sigar kauyan ci ba, domin duk da cewa bata taba ganin gidaje masu kyau haka ba a kafatanin rayuwar ta amma still tayi behaving kanta, a kasan ranta kuwa jinjina tarin dukiyar da aka narka wurin gina wanna had'add'en gidan take...
Wani alarm dake manne a bango bintu ta danna yayi kara.
Madam Gloria dake zaune a daya daga cikin kujerun falo ta kwala Kiran daya daga cikin masu aikin ta da gurbataciyyar hausar ta , da ta dan koya a zaman ta a kaduna tace "Hajiyayye! Hajiyayye!! Zo ki Bude kofar falon nan"
Da gudu Wacce aka kira da Hajiyayye ta fito ta nufi kofar hadi da Bude wa, bintu ce ta fara shigowa kana Aysha ta biyo bayan ta cikin Sanyi da yanayin bakunta,
"ke hajiyayye! Komai ya zama neat ko? Domin banason son ya daga ko digon datti daga zuwan shi"
Cikin ladabi hajiyayye da har ta soma tafiya tace "eh madam mun gama gyara komai"
"good"
madam Gloria ta fada cikin Izza kana tayi wa hajiyayye alamar ta tafi....
Cikin isa da takama ta dago kanta, fess ta sauke su kan Indo dake manne da bintu, Wani irin mahaukacin bugu kirjin ta yayi wanda hakan har ya nuna a saman fuskar ta, take taji tsanar Indo a ranta wanda bata taba yiwa wani mahaluki shi ba baya ga Abraham, kamar tace bata son yarinya amma ta kasa, domin ta hada duk qualities din da take so ga housemaid, amma me yasa taji wani irin yanayi a kallon farkon da ta yi wa yarinyar?
"madam ina ta gaisuwa" bintu ta katse mata tunanin ta.
Dan sakin fuska tayi kana tace "yawwa lafiya, wanna ce yarinyar?"
"eh itace madam, sunan ta Aysha"
"Ok! Ku zauna mana" ta fada a gadarance, tana kokarin controlling fad'uwar gaban da ya riske ta.
Zama suka yi yayin da Indo ke shigewa bintu domin wani mugun Tsoron matar ne ya shigeta at once, yayinda take jin gaban ta na tsananta fad'uwa....
"ya ya kike ce sunan ta?"
"Aysha"
"OK, Aysha kin iya gyaran gida, komai ya zama neat?"
"eh ta iya....."
"ki bari tayi magana ko? Or is she deaf?"
Madam Gloria ta fada tana tauna chewing gum hadi da yamutsa fuskar ta.
Shiru bintu tayi kana ta zunguri Indo alamun tayi magana, "e.... eh... eh... na iya" ta fada cikin cracking voice.
"what about cooking?“ ta kara tambaya tana kallon Indo, rudewa Indo tayi ta mayar ta kallon ta ga bintu, "Addah me ta ce?" indo ta fada cikin rada.
"Cewa tayi kin iya girki" kasancewar bintu na Dan fahimtar turanci duk da cewa gidan bahaushe take aiki amma yaran gidan na son Rayuwar turawa daga nan take fahimtar wasu abubuwa.
"eh.. Na iya irin namu na kauye" ta fada gwanin tausayi.
Yamutsa fuska madam gloria tayi tace "wa zai ci na kauye? Kenan baki iya ba, anyway zan kira k'warariyyar mai girki domin ta koya miki"
"toh an gode kwarai madam, zan iya tafiya ko?" Bintu ta tambaya, yayin da a ranta tana fatan Indo ta iya zama da ita domin ta lura matar ba sauki, kuma yanzu ta fahimci hakan.
"eh! Zata fara aiki gobe, aikin ta shine gyara dakin na, da na yarona, girki da gyaran kitchen that's all, sannan salary dinta 70 thousand ne duk Wata"
Jinjina kai bintu tayi cikin jin dadi domin ko ita albashin ta bai kai haka ba, ta kuma yi wa Indo murna har ranta.
"toh Indo ni zan tafi, zan dinga shigowa duba ki bayan kwana biyu-biyu ki rike halayen ki na kirki, kar naji ance kin yi wani Abu mara kyau kinji ko?"
Jinjina kai Indo tayi tana kokarin hadiye kukan ta, da haka bintu ta fita, daya daga cikin masu aikin gidan mai suna lubabatu madam gloria ta sake kira domin ta nuna Indon dakin ta.
yarinyar mai shekaru ashirin da uku ce, har da taya Indo daukar ghanan most go suka bar falon, wani huci mai zafi madam gloria ta saki, domin tun ganin da ta yiwa indo gaban ta ke ta fad'uwa, wanda ta rasa dalilin haka.
Ta bangaren su Indo kuwa saman bene suka hau, inda dak'unan Abraham ne kawai a saman , sai wani daki can karshe Inda ba kowa, inda nan madam gloria ta sa aka gyara domin indo ta zauna, saboda a amatsayin ta na mai yi musu girki da gyara dakuna boys quarter yayi nisa, a cewar ta gwara tana kusa da su ta yanda ko wani Abu ake bukata ta dafa za a fi saurin sanar mata...
Daki daya ne babba inda aka yi masa paint da pitch color wanda ya fito da kyan dakin ainun, sai toilet dake cikin dakin, babu wasu tarkace a dakin daga dan madaidaicin gado sai wardrobe, hadi da dressing mirror da babu komai a kai, sai centre carpet dake shumfud'e saman tiles din kasa, ba laifi dakin ya hadu.
"yawwa ga sif dinki nan ki jera kayan ki a ciki, amma kafin nan bari na kawo miki abinci"
lubabatu na gama fadin haka ta bar dakin....
Kallon komai indo ke yi daki_daki, duk da cewa dakin yayi kyau sosai, sannan ko a mafarki bata taba shiga irin wanna had'add'en daki ba, kana bata taba sanin cewa zata mallaki irin wanna dakin ba, amma bai burgeta ba, kasancewar babu Innar da yan biyun ta a kusa, take hawaye ya biyo kucin ta sak'amak'on tuno su da ta yi, tun ba a je ko ina ba har ta fara shiga wani hali na tsananin kewa, jin alamun mutum ya taho wanda take da tabbacin lubabatu ce yasa ta share hawayen ta da sauri...
Ajiye Abincin lubabatu tayi tace "ga abinci nan ki ci"
"Nagode sosai" Indo ta fada kanta a kasa, murmurshi lubabatu tayi domin hakan nan taji lndo ta shiga ranta duk da cewa ta girme mata.
Shiru dakin ya dauka, ganin cewa indon bata ci abincin ba ya sanya ta Mikewa hadi da cewa "bari na tafi domin ki samu ki ci abincin ki, sunana lubabatu, kefa? “
“Aysha Indo" ta amsa mata a takaice.
"masha Allah suna mai dadi da daraja, toh na tafi sai anjima ko"
"toh Nagode sosai" Indon ta kara fada.
Ta dauki tsawon mintuna goma tana tunani kana ta ja ajiyar zuciya hadi da Bude kwanon abincin.
Tuwon semonvita ne hadi da miyar ganye daya ji namomi, sai lemon exotic hadi da swan water mai Sanyi.
Duk da yanda abincin ya yi dadi, loma biyar kawai tayi ta wanke hannun ta, domin tunanin su Innah ne ya cika zuciyar ta, "ko sun ci abinci?" Sanin bata da amsa ya sanya ta rufe abinci ta Mike, toilet ta shiga Inda shima ya hadu sosai bata wani tsaya kallo ba ta shiga daura alwala cikin nutsuwa....
Kallon dakin tayi taga babu alamar sallaya, can ta tuno yanayin madam gloria din babu alamar musulunci a tare da ita, gefen wajen karshen gado ta karasa, dankwallinta ta warware ta shimfud'a a kasa, in da take dogon gashin ta mai tsaho, baki, hadi da tsantsi ya bayyana, hijab dinta ta mayar kanta kana ta tada sallar azahar da la'asar da bata yi ba....
Bayan ta iddar ta zauna tayi addu'o'inta sosai, gashi bata taho da qur'anin ta ba, gashi ta saba duk bayan sallah ta kan yi tilawa, can sai ga lubabatu ta kara dawowa, abincin ta Bude ta ce
" la la la ai baki ci komai ba?"
"wallahi na koshi" Aysha
ta amsa tana murmurshi
"toh yanzu kina bukatar wani Abu ne?" lubabatu ta tambayeta.
"eh ina zan samu qur'ani in fansa Dan Allah, na manta nawa a gida"
"ai kuwa ina da guda biyu, ban ma fiye amfani dasu ba" ta fada a kunyace, domin sanin cewa hakan ba kyau, gashi kanwar bayanta ta fita himma wurin karanta littafi mai sarki, domin ita wani zubin a Wata bai fi tayi sau daya ba.
"amma kina kokarin yi kullum, ko da aya
biyar ce ko uku, lada zaki samu, sannan zai taimaka miki wurin rike haddar ki, bazai zube ba" Indo ta fada cikin cool voice.
"in sha Allah zan yi kokarin yi kullum, Nagode kinji kanwata? Bari na dauko miki"
Jinjina kai Indo tayi kawai hadi da zuba tagumi, Bayan mintuna shida sai ga lubabatu ta dawo dauke da qur'ani, amsa aysha tayi cikin farinciki da godiya.
Kwanukan Lubabatu ta kwashe tace "toh sai gobe idan mun sake haduwa, domin ba a bari mu hau saman nan any how, yau ma darajar ki na ci na hau kusan sau hudu madam bata min masifa ba"
Murmushi kawai Indo tayi, Bayan Lubabatu ta fita,Aysha ta Bude qur'anin ta cikin suratul maryam, Aya goma ta karanta kana ta Mike ta ajiye qur'anin saman dressing mirror.
D'an k'wallinta ta mayar kanta hadi da bud'e wardrobe ta shiga jera kayan ta da ba wani yawa ne da su ba, sannan basu cika sabun ta ba, Bayan ta gama jerawa idanun ta ya sauka kan jakar da ta dauko a dakin baffa, a hankali tasa hannu ta dauki jakar, ido ta zubawa jakar kana ta mayar cikin Ghana most go dinta, zuge zip din jakar tayi ta rufe, kana ta saka a kasan sif din inda babu komai a ciki, kofar sif din ta rufe kana ta dawo bakin gado ta zauna, haka ta wuni sukuku ba motsin kowa, har tunani take anya zata iya yin wannan aikin? Amma idan ta tuno innar ta da Rayuwar da suke ciki sai taji kwarin guiwar yin aikin...
*************
Haka ta dinga juyi da daddare ta kasa bacci, Kiran sallar farko a kunne ta, Mikewa tayi domin bata ga amfanin kwanciyar ba tunda ba baccin take ba, toilet ta shiga tayi alwala kana ta fito, nafilfili ta shiga jerawa har aka tada sallar asuba, Bayan ta iddar ta shiga rera karatun qur'ani cikin zazzak'ar muryar ta mai sanyin amo.
Shida saura mintuna biyar ta shiga toilet, wanka tayi, hadi da brush kana ta fito daure da zanin ta, kurawa kanta ido tayi ta cikin madubi inda direct kan sarkan nan idonta ya sauka, hannu ta kai ta shafa sarkan, kullum sarkan kara kyau da sheki yake duk da dashi take wanke kullum.
Pomade din stella (mai gurguwa) da ta taho dashi ta shafa a jikin ta, wanda Inna ce ta siya mata ana yi gobe zata taho kaduna.
Doguwar rigar atamfa roba-roba ta sanya, d'ankwallinta ta daura hadi da sanya hijab dinta, duk da babu Kwalliya ko digo a fuskar ta amma tayi kyau ba laifi, sai dai rashin tsad'add'en mai na gyaran fata da karancin wayewa ya tauye tarin baiwar kyawun da take dashi.
Dan gyaran dakin ta tayi duk da bai yi wani datti ba, zama tayi na almost 1hr kana ta sauko down stairs...
Da wasu yammata biyu ta fara cin karo inda suke gyaran yalwataccen General falo, gaishe su tayi suka amsa hadi da bin ta da kallo....
Madam Gloria ce ta fito cikin takun dai-dai, kallo daya tayi wa aysha ta dauke kai hadi da cewa "shiga ki gyara dakin, if you're done sai ki hau sama ki gyarawa son na shi, anjima chef din zata zo"
"toh!" Aysha ta amsa cikin ladabi, duk da bata fahimci kalmar "chef" ba.
Falon madam Gloria ta fara gyara mata, kana ta shiga bedrooms din daya kasance biyu ta gyara ta goge, sai toilet da ta wanke ta goge, komai dai fess sai gyalli yake kai baka ce this is her first time ba, inda aikin ya dauke ta tsahon awa biyu.
Bayan ta gama ta fito, ta tarar da madam gloria hakimce a dinning area da alama breakfast take son yi.
" idan kin hau sama ki kira min son ya zo yayi having breakfast"
madam Gloria ta fada da wani irin tune daya Dan tsorata Indo domin kamar da fada-fada tayi mata.
"toh!" ta amsa a sanyaye yayinda ta cigaba da taka step case din, duk da ba duka abinda madam gloria ta fada ta gane ba.
Sama ta hau inda ta ga wasu kofofi biyu d'aya na zallan glass ne, shi din ta nufa wanda take Kyautata zaton shine dakin sa...
Gabanta na bugawa ta shiga knocking shiru,... Jin shiru yayi yawa ba motsin kowa sai kawai ta tura kofar hadi da zura kafar ciki inda ya sauka kan lallausan door mat...
*kuyi hakuri sisters ban samu zama bane shiyasa kuka jini shiru, kuyi manage da wannan, sai mun hadu a next page*
Share fisabillahi
Comment for more typing
NoorEemaan
07082281566
Thank you for reading my novel 🍇Abraham🍓
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
https://chat.whatsapp.com/JwYkGXFKcLH95WSHP9QoUg
🍇🍇ABRAHAM 🍓🍓
*first edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
*please Don't forget to vote my story and also follow me on WATTPAD @NoorEemaan*
love you all guys.
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 21-22
(Not edited)
Lumshe sexy lulu eyes dinta tayi sak'amak'on sanyayyar kamashin room freshener daya daki hancinta, kana a hankali ta ware idanunta ta sauke su kan kayataccen falon daya gaji da haduwa, sai dai shiru ba motsin kowa sai k'aran Ac.
Wata kofa dake kallon gabas ta sauke idanunta a kai, a hankali ta fara takawa domin isa ga kofar, a gefe daya kuwa gabanta na tsananta fad'uwa...
Hannu ta dora kan handle din kofar da niyyar bud'ewa, sai kuma tayi saurin dauke hannun ta, a hankali ta fara knocking... Shiru ba amsa, sannan ba motsin kowa har na tsawon mintuna biyar, gajiya ta fara yi da tsayuwa kasancewar ta mutum mara jurar tsayawa, shahada tayi ta bud'e kofar a hankali, kana ta shiga....
Ya subhanallah! Ta fada tana runtse idanunta da karfi sakamakon hangoshi da ta yi kwance kasan tiles babu riga a jikin sa sai dogon wandon jeans kirar company'n gucci, wanda hakan ya bawa manyan six packs din sa bayyana hadi da karfaffan hayyensa daya yi mata shi dasu.
A kafatanin rayuwar ta bata taba ganin da namiji haka ba, duba da irin gidan da ta fito, ta dauki tsawon mintuna bakwai a haka, kana kamar mai tsoron ganin wani mugun abu ta shiga Bude idanunta a hankali ta sauke kan k'yak'yawar fuskar sa dake bacci a tunanin ta, wanna karon gabanta ya fi d'azu fad'uwa saboda ganin kamanin Ammar dinta da Abraham, ba tare da kuma ta san maganar ta ta fito fili ba tace "Ammarrr" cikin sautin amo dake bayyana zallan mamaki,
Ji tayi idan ta cigaba da tsayuwa a dakin komai zai faru, domin k'wak'walwarta ya gaza dauk'an abinda take gani, musamman kamanin su daya firgita ta, dan dai shi babba ne da ta ce tabbas Ammar din ta ne, cikin sassarfa ta juya domin barin dakin kamar a sama taji husky voice dinsa yace "hey! what did you want?" tilas ta tsaya cak! Gashi ya sake rudata da turanci sa da bata fahimci koda kalma daya ba... Abraham kuwa duk da yana cikin bacci, amma shigowar ta dakin ya sauya bugun zuciyar sa, wanda ya tilas ta masa farkawa daga dan baccin daya dauke sa, tabbas murya yarinyar daya ji a cikin adaidaita sahu ce, ya kuma sake tabbatar da hakan ta dalilin bugun zuciyar sa da ta sauya, wanda akan ta ne ya fara Jin hakan, mamaki yake kan meya kawo yarinyar cikin gidan su har dakinsa.
Jikin ta na bari, cikin rawar murya tace "ehm... Is your, is na mahaifiyar ka ta ce kazo kasan bene" ta fada cikin duburbucewa idanunta taf da k'walla...
Yamutsa fuska yayi domin ko kalma daya bai fahimta daga abinda tace ba, a hankali ya bud'e idanunsa da suka dan rine saboda jimawa da suka yi a rufe ya sauke su a kwanta, sai dai bayan ta kadai yake hangowa, ita kuwa jin bai sake magana ba yasa ta fita da gudu, ta nufi dakinta dake da dan nisa da nashi duk da saman bene ne.
ABRAHAM kuwa da kallo yabi bayanta, kana ya tabe bakin sa hadi da mikewa tsaye, toilet ya nufa domin yin wanka, shower ya kunna inda ruwan ya shiga dukan kansa zuwa jikinsa, a hankali muryata ya amsa kuwa a kunne sa "Ammarrr" ya maimaita kalmar can kasan makoshi, duk da bai san ma'anar sa ba, kawar da tunanin yayi ya cigaba da wankan sa inda mintuna ashirin ya dauka kana ya fito daure da farin towel.
Tsad'add'en lotion din sa ya shafa, kana yayi oiling kansa hadi da tajewa, gaban wardrobe din sa ya nufa, inda wayar sa ta fara ringing... Dubawa yayi ya ga MUM ce.
Amsawa yayi hadi da karawa a kunne sa,,
"Good morning Mummy"
"morning my son, I sent the house-maid to tell you breakfast is ready and.........."
"am coming mum" ya fada yana katse Kiran ba tare da ya bari ta karasa maganar ta ba, sai yanzu da mummy ta fada ya san dalilin shigowar Yarinyar nan dakin shi, wardrobe din ya bude ya fito da wani crazy Jean trouser white, sai bakin riga mai botira hadi da dogon hannu, cikin mintuna biyar ya shirya cikin su, gaban inda tarin takalman sa suke ya nufa ya dauki wani black palm sandals na company dolce and gabbana ya sanya, agogon zallan sliver ya manna a hannun sa, ba karamin kyau mai tsayawa a rai yayi ba , Bud'e kofar yayi ya sauko kasa...
Aysha da ta kasa kunne, jin motsin ya fito ya sanya ta fitowa da sauri, duk da faduwar gaba da Tsoron da take ji amma dole ta gyara masa dakin tunda aikin ta ne, baya ga haka bata ma so abinda zai hada ta da madam Gloria, dakin sa ta koma ta fara gyara falon da sauri² inda ba wani datti yayi sosai ba, bedroom dinshi ta nufa shima ta gyara kana ta yi mopping a ranta tana mamakin yanda ya iya kwanciya kan uban sanyin da tiles din ke da shi, domin ita kafar ta kadai dake taka shi yanzu ya sa ta jin Sanyi.
Bayan ta gama, ta wanke toilet ta fito, wani kofa ta gani by the left, Bude kofar tayi ta ga kitchen ne, a gyare yake babu wani datti, wani kofa ta sake gani ta cikin kitchen din ta bi, take ta bayyana a gyming room dinshi wanda ke gyare tsaf, "Dama makeri ne shi" ta fada tana kallon karafunan da abubuwan motsa jikinsa, wanda ita bata San amfanin su ba.
Sosai ta shagala ta kallon dakin motsa jikin, can ta tuno cewa zai iya shigowa yasa ta fita cikin sauri, dakinta ta koma tana sauke ajiyar zuciya, yayin da har yanzu tana mamakin wannan kammanin, daga kashe dai ta basar, tasa a ranta cewa kawai kama ce....
ABRAHAM kuwa tea kawai ya sha, dama shi ba ma'abocin cin abinci bane sosai, madam Gloria tayi-tayi yaki ci, dole ta hakura, fita yayi zuwa unguwar rimi, domin so yake ya je su yi magana da wani attajiri mai harkan filaye wanda ya ga ya dora wani fili mai girman gaske a Instagram din shi wanda na siyarwa ne, wanda tun yana dubai yaga tallan, luckily kuma yaga kaduna state ne , so yake ya siya domin ya gina company a nan kaduna, wanda hakan zai yi keeping dinsa busy...
Babu jimawa da fitarsa professional chef din da zata fara koyawa indo girki-girki tazo mai suna miss Zaynab Akindele yar jahar ogun ce, ba bata lokaci madam Gloria tayi Kiran Indo ta sauko suka shiga kitchen....
____________________
*Gombe State*
Bangaren su innah kuwa sosai suke fama da tsananin kewar Aysha indo, bare ma su Anwar, ranar farkon da basu kwana da Ammuh din su ba, cikin dare Inna ta ga ta kanta, domin zazzabi ne ya rufe su, babu abinda suke kira sai Ammuh! Ammuh! Suna kuka, innah bata taba sanin cewa haka suke da Wayo ba, domin ta yi iya yinta sun ki hakura...
Washegari da asuba zazzabin ya sauka, suka fara dan wasan su, amma abu kadan sun kira sunan Indo ko su je dakinta, lallaba su innah ta dinga yi tana musu Wayo da haka ta samu dan sauki.
★★★
*KADUNA STATE*
Kiamanin sati daya Kenan da miss Zaynab Akindele ta fara koyawa Indo girki, kuma ba laifi tana fahimta sosai wanda hakan ke sa miss zaynab kara himma wurin koya mata, domin ita macece mai son ta koyawa mutum abu ya dauka da wuri, ta bangaren Aysha kuwa tana jin nishadi a duk lokacin da ake koya mata girkin, karin dadi kuma miss Zaynab na jin hausa sosai duk da kasancewar ta yare, wanda hakan ke sa Indo saurin fahimta.
Ta bangaren Abraham kuwa yayi nasaran siyan filin nan, inda babu bata lokaci aka fara gini, abinka da kudi, sosai ya zama busy baya samun zama...
Ta bangaren madam Gloria kuwa tana nan tana shirya yanda zata kashe Abraham, sai dai kwatsam wani tunani ya zo ranta yasa ta dan dakata, domin tabbas Abraham ya wuce duk tunanin ta, shi din ta kasa kashewa har yanzu saboda taurin ransa, da asirin ta ya tono a idon duniya bata more dukiyar da ta dade da burin mallaka ba gwara ta sanja salo, sai kawai ta yanke shawarar amfani da AYSHA Wacce tasan yar gidan talakawa ce, domin kashe shi, ko da bincike yayi bincike aysha za a kama...
KO TA YAYA MADAM GLORIA ZA TA YI AMFANI DA AYSHA WURIN KASHE ABRAHAM??? KU BIYO ALKALAMIN NOOR...✍️😊
Share✅
Comment ✅
Vote ✅
Editing is not allowed❎
NoorEemaan🦋
07082281566
Thanks for reading my novel 🤝
🍇🍓ABRAHAM 🍇🍓
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
*WATTPAD*
@NoorEemaan
*NOTE*
*_dan Allah masu tura Abraham Daga page 30 zuwa gaba ku daina, kuna rudar min da reader's, ina ta samun tsakonnin a yau saboda kun fitar fiye da page din dana tsaya, Ni a page 23-24 na tsaya, baku fini son Ganin na kamalla posting din ba, mun sani cewa Abraham ba sabon typing bane, idan kin san kin karanta complete Fyn, ba sai kun turawa mutane ba, alhalin Ni ban zo wajen ba, saboda irin wanna issues din yasa ban mayar da complete ba tun da Yawan mutanen da suka bukaci hakan, saboda Wani dole Sai ya fitar, ina da both pages da document complete Amma ban mayar ba Saboda kada a rude, Ina bada pages biyu kullum still hakan bai isa ba har sai an tura daga Page 30 zuwa karshe, wasu ma pages din a hargitse, Dan Allah ku bari nayi reposting din yadda na tsara abu na, da sannu zamu gama Kamar yau, na san kauna ce tasa kuka yi haka, amma wasu na shiga rudani, ɗan Allah in dai ba daga farko zuwa inda Ni na tsaya aka nema ba, karku fitar, duk wanda baxai Iya jira ba, ya je Wattpad akwai complete a can, ngd habibte's_*🫶💖
Chapter 23-24
(Not edited)
Kimanin wata daya da kwana biyu Kenan da zuwan Aysha gidan su Abraham, inda yanzu ta iya kalolin girki² da Dama, domin miss Zaynab akindele na matukar Kokarin wurin koya mata musamman da ta ga Aysha na da interest akai.
Da safe ita ke preparing musu breakfast, haka zalika dinner, inda na rana ne kawai suke yi tare da miss zaynab, domin madam gloria ta kara cika miss zaynab da kudi kan ta kara koyawa Aysha har na tsawon wata uku gabadaya Kenan domin ta kara zama expact.
Ta bangaren Abraham kuwa ginin company'sa yayi nisa sosai saura kadan, kasancewar k'wararrun ma'aikata ya dauka masu sanin
makamin aiki...
____________________
Misalin karfe biyar na yamma Aysha na zaune saman bed dinta, ta kara kyau kana jikinta ya murje, duk da cewa har yanzu mai gurguwa take shafawa amma skin color dinta ya fito tarr yana shining sak'amak'on Air conditioner da take kwana tana wuni da shi.
Albashin ta da madam Gloria ta bata, ta kurawa ido... hawaye suka zubo a kuncin ta, a lokacin da madam Gloria ta bata kudin to tsorata, domin bata taba ganin kudi masu yawa haka ba balle ta rike, Wai yau ita ce ke da wanna tarin kudin...
"Alhamdulilahil-lazee tatimus solihat" ta fada a hankali hadi da mikewa, kudin ta mayar cikin farin envelope din da aka rubuta sunan ta da biro b'aro,-b'aro a kai, hijab dinta ta sanya kana ta sauka kasa, babu kowa a falo sai plasma dake ta yi shi kadai, waje ta fita inda tun zuwanta gidan bata taba fitowa ba, gaisawa suka yi da mai gadi ta fita da sauri domin so take ta yi ta dawo domin ta dora dinner.
Gidan da bintu take aiki ta nufa, k'wank'wasa Dan karamin kofar tayi, Bayan minti biyu mai gadi ya leko hadi da tambayar ta wa take nema, ta sanar da shi, ya Bude mata ta shigo hadi da nuna mata hanyar da zata bi domin yaga bakuwar fuska ce, bata San kan gidan ba.
Bakin kofa ta tsaya hadi da yin knocking, jim kadan wata yarinya ta bude Wacce aysha ta tabbatar itama yar aiki ce, bakinta dauke da sallama cikin siririyar murya ta shigo inda kamilar dattijuwar mata mai sanye da medicated glass ta amsa hadi da binta da kallo irin ban gane wanna fuskar ba, fahimtar hakan yasa Aysha kara so gabanta, durkusawa tayi ta gaishe ta hadi da sanar mata cewa tazo wajen Adda bintu ne.
Murmushi Matar tayi daya bayyana hakoran makkah ta biyu sliver da golden dake gefe da gefen hakorin ta kana tace "ke kanwar tace ko?"
"Eh" Aysha ta amsa mata kawai tana mayar mata da martanin Murmushi.
"masha Allah, bari na kira ta a waya domin suna can suna kiciniyar hada dinner" ta fada tana latsa tsad'ad'iyyar wayar hannun ta....
Mintuna biyar kacal bintu ta fito, ganin Aysha yasa ta kara fad'ad'a Murmushin ta...
"yau Indon baffa ce ta fito da kanta" bintu ta fada cikin zolaya.
Murmushi Aysha tayi tace "wallahi Addah, an biya Albashi ne, kin ganshi nan" ta dora mata a cinyar bintu kana ta cigaba
"ina so kudin su isa ga Innata basan ya zan yi ba"
Jinjina kaifin tunanin Aysha, bintu tayi a ranta, a fili tace "kinyi tunani mai kyau Indo, hakika kin cika y'a ta gari, abinda za a yi shine zan karbi cash din hannun ki, sai na yi wa jauro (kanin bintu) transfer yaje bankin cikin gari ya cira gobe ya bata tunda ya iya, dama gobe ina son zuwa bankin na ciri kudi, Kinga na huta, yanzu nawa kike so a tura mata? “
"duka Addah"
Dariya bintu tayi tace "A'a² ba za a yi haka ba, kin San fa kin girma yanzu, dole zaki kula da kanki, siyan pad, man shafawa, man gyaran gashi, da Dan kayan sawa haka Kinga duk kina da bukatar su, abinda za a yi shine za a tura wa Innah wuro dubu hamsi, saura dubu ashirin din sai a yi miki siyayyar dashi ko, gobe zanzo na yi wa madam magana kan zamu je kasuwa dake"
"toh Addah, Kema ki cire kudi a ciki kiyi amfani dashi"
"a'a² Allah ya kiyaye indo, tamkar kanwata ta jini na dauke ki, duk abinda na yi miki saboda Allah ne, dan haka ki bar kudin ki Nagode kinji"
"toh Addah Nagode Allah ya biya ki, amma nayi kewar Innah ta sosai da su y'ay'ana" ta fada hawaye na ciko idanunta.
"shagwaba ko? Toh Karki damu zan fadawa jauro idan ya kai mata kudin ya kira wayata a wajen sai na hadu ku, ai shikenan ko? "
Da farinciki Indo ta koma gida, jin gobe za ta yi waya da Innar ta, a k'age take goben yayi, cikin kwarin jiki da bata taba irin sa ba tun zuwan ta gidan ta shiga dora musu dinner.
*WASHEGARI*
Kamar yadda bintu ta fada tazo wajen madam Gloria tare da rokon Alfarma kan ta bar Indo su Je kasuwa, bata hana su ba, sai dai cikin isar da ji da kai ta ce Indo ta dawo kan lokaci...
Basu jima da hawa keke-napep ba, sai ga Kiran jauro, danna answer bintu tayi hadi da sallama, amsawa jauro yayi suka gaisa kana yace ga Inna wuron, amsa Inna tayi ta fashe da kuka, kana ta shiga yi wa Allah godiya, sannan ta dora da yi wa bintu godiya sosai hadi da yi mata addu'oi'n fatan alkhairi...
"Bakomai Inna, ai yi wa kaine, ga Indon" abinda bintu tace Kenan tana kara wayar a kunnen Aysha....
Rike wayar gam Aysha tayi a kunnen ta, kana cikin murya mai nuna zallan kewa da son mahaifiyar ta tace "Innata... Nayi kewar ku sosai" ta karasa tana sakin kuka....
Itama Inna, hawaye ne masu Sanyi ne suka zubo mata sak'amak'on jin muryar tilon yarta, "munyi kewar ki sosai Indon baffale, yi shiru Karki tada min hankali, kina lafiya dai ko?"
"eh Innata" ta amsa.
"toh alhamdulillah,na ga abun arziki, Allah ya miki albarka ya tsare min ke, Sannu yar albarka kin ji ko? "
"Ameen Innata kin cancanci fiye da haka, albishirin ki Inna? Aradu na iya kalolin girke² irin na yan birni masu dadi, idan na dawo zan yi mana shi ki ci, ki ji dadi ke da yan biyu na" ta fada cikin sakalci da kuruciya.
Dariya Inna tayi tace "toh Allah ya kowa mana ke lafiya, gashi kin aiko mana da duka albashin ki, dame zaki yi amfani?"
"ai inna da ragowar dubu ashirin, albashina dubu saba'in ne fa"
"saba'in!!!" Inna ta maimaita cikin mamaki hadi da zaro duka idanun ta waje.
"aradu Inna, mun zama masu kudi" tilas Bintu dake gefe tasa dariya, indo ba dai sakalci ba.
Itama Inna Dariya tayi a ranta tana kara godewa Allah, a fili tace "ga y'ayy'an ki nan sun ishe ni da Kiran Ammuh"
"wayyo Ammar da Anwar dina, nayi kewar su Inna ki bani su naji muryoyin su"
Anwar aka fara bawa wayan, banda Kiran Ammuh da gwaracin sa babu abinda yake, Lumshe ido Aysha tayi, kewa hadi da tsananin son yaran ya kara shiga zuciyar ta..
bayan nan aka bawa Ammar shima sai Dariya yake saboda jin muryar Ammuh dinsu, kuma abun mamaki sun gane ita ce, itama Aysha take ta tuno tsananin kaman Abraham da Ammar din ta, ta so bawa Inna labari sai tayi shiru.
Zuciyar Indo fess saboda jin muryar su Inna da ta yi, ba dan ta so ba, bintu ta kashe wayar, Bayan ta cewa jauro zata turo masa kati...
Daga bangaren Inna kuwa Dubu Biyu ta bawa jauro daga cikin kudin inda da kyar ya karba, kana yayi godiya ya tafi, itama innah bashin da ta dan ci ta biya, kana tayi musu siyayyar kayan Abinci masu yawa, sabulun wanki, sabulun wanka, man shafawa, man goge baki, har sabbin kaya ta siya musu masu saukin kudi sosai, ranar har da namomi cikin Abincin da suka ci..... (ni Noor nace talauci Nesa da mu ooo, arziki zo nan ga😹💔)
Su Aysha kuwa sha biyu saura suka dawo gida, inda bintu ta taya ta zaban man shafawa da ta San zai karbe ta da sabulun man, sai toothbrush da tooth paste, kayan make up, turare, palm shoe guda daya, sai wasu roba² ready made gown guda biyu masu saukin kudi......
Wanna Kenan.
____________________
*1 WEEK LATER*
_5:56 am_
Zaune take kan sallaya, ta tankwashe kafafunta, yayin da take rike da Kur'ani tana rera karatu cikin suratul-tawbah, cikin sanin ya kamata take bawa ko wani harafi Hakkin sa.., kasancewar kuma gari bai waye ba, ko ina yayi shiru yasa amon zazzak'ar muryar ta ke fita....
A kuma daidai lokacin ne Abraham dake gyming room din shi yana daga karfe ya fara jin tashin muryar ta na shiga kunnen sa, cak ya tsaya da abinda yake yi, hakika zai iya rantsewa bai taba Jin dadin wani abu a kunne sa kamar karatun da Aysha'n ke yi ba, duk da bai San menene ba, bai San me take cewa ba, bai kuma fahimci ko harafi daya ba, amma yana matukar son abinda take fada, Lumshe ido yayi, yana jin yanda ko wani mahuda na gargasan jikin sa ke mikewa, yayin da wani Sanyi ya fara shigar shi slowly, duk da gumin daya hada saboda motsa jikin da yake yi....
A hankali ya dire karfen a kasa, kana ya Bude lumsassun idanun sa hadi da bude kofar ya fita, bai San me yake yi ba, kawai dai ya tsinci kan shi da bin hanyar da yake jin sautin muryar ta...., duk taku daya da yayi, yana kara jin sautin muryar ta na kusanto shi, kana bugun zuciyar sa na karuwa....✍️
_kuyi manage da wanna please, wallahi am so so tired today, meye ra'ayinku kan wanna episode din? Mu hade a next page_....
Share fisabillahi✅
Comment for more typing.✅
Noor🦋
Wednesday, 2 February 2022
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da facebook su yi join ta wanna link din.
_Am so sorry for keeping you guys waiting, na San ba dadi, kun jira ni da yawa, amma ba laifi na bane, ban ji dadi bane kwana biyu, ga ba lokaci, amma kuyi hakuri in sha Allah bazan kara jimawa irin wanna ba, har in gama Abraham, ngd sosai da kokarin jirana da kuka yi🙏 much luv masoyan NoorEemaan_😍
Chapter 25-26
Cak! ya tsaya a lokacin ya isa bakin k'ofar dakinta, inda a yanzu amon sautin zazzak'ar muryar ta ya fi tashi, hannu yasa kan handle din kofar a kokarin sa na son bud'e kofar, sai kuma yayi saurin d'auke hannun sa hadi da murza su cikin na juna, a hankali ya jingina bayan sa da kofar dakin ta, sannan ya Lumshe k'yawawan idanun sa yana cigaba da sauraron kira'ar ta mai dadi....
Sosai ko wani mahuda na gashin jikin sa suka kara bude wa, kasancewar yanzu yafi kusanci da ita, wani yanayi mai kama da zubar tsigan jiki, da Sanyi ya shiga ratsa shi...
*40 Minutes later*
Wanda yayi daidai da lok'acin da Aysha ta rufe qur'anin ta, kana ta shiga yin addu'oi'nta...
A kuma lokacin ne Abraham dake tsaye a bakin kofar ya sauk'e wata k'arfaffar ajiyar zuciya, kana a hankali ya bud'e lumsassun idanunsa da suka dan rine sak'amak'on jimawa da suka yi a rufe.
Cikin yanayi mai kama da rashin jin dadin ya yamutsa fuska tamk'ar yaro dake son wani abu daga mahaifiyar sa, haka nan yaji ba dadi a dalilin daina jin amon sautin muryar ta dake rera karatun qur'ani.
A karo na biyu ya kara sauk'e numfashi kana cikin tafiyar sa ta ingarman na miji mai ji da lafiya da kuruciya ya bar wajen...
Aysha kuwa bayan ta iddar da addu'o'in ta ta Mike, a gaggauce ta shirya kana ta sauko kasa ta fara shirya musu had'add'en breakfast mai rai da motsi tamkar ba Indon baffa ba.
*********
9:00am.
ABRAHAM tare da madam Gloria ke zaune a had'add'en dinning area suna jiran Aysha tayi serving din su, a hankali cikin takun nutsuwa Ayshan ta fito daga kitchen hannun ta dauke da plates na tangaran da zata yi serving dinsu dashi...
Jin kamar ana kallon ta yasa ta a hankali ta dago kanta idanunta suka fad'a cikin nashi, gaban ta ne ya bada dam! Domin tun lokacin da ta fara serving madam Gloria abinci yau ne karon farko data ganshi a dinning table, gabadaya ji tayi idanun sa na yawo a jikin ta wanda hakan yasa jikin ta fara rawa domin sosai yake ladabtar da ita da sexy eyes d'insa masu masakaicin girma, hannunta ne ya fara rawa, ba tare da zato ko tsammani ba plates din suka kufce daga hannunta suka tarwatse kan tiles din...
A zabure madam Gloria ta mike, hadi da daga lukutan hannunta da niyyar marin Aysha da ta k'amk'ame jikin ta sannan ta runtse idaunta...
Ganin yasa Abraham mikewa, taku biyu kacal yayi ya kamo hannun madam Gloria ya sauke, kana ya kalle ta, ba tare da yace komai ba ya koma kan kujerar sa ya zauna, yana k'ark'ad'e hannun sa saman dinning table din...
Da kallo ta bishi kana tace "why son? Meyasa zaka hana ni? Daka barni na nunawa wanna Bush Village girl din hankali"
Juyawa tayi ta ga Aysha tace "ke! Baki da hankali ko? what's your problem? Hannun ki ciwo yake? Kina abu kamar zararriya, bari in gaya miki, this should be the last time da zaki kara fasa min plate, kin San nawa each one?... “
" mummy plssssssssss" Abraham ya fada a dake, yana rike da kansa, haka nan yaji fad'an da take wa Aysha na bata masa rai, be San mai dalili ba, baya ga haka shi mutum ne mara son hayaniya...
Shiru madam Gloria tayi, ta zauna tana sauke hucin bacin rai, amma ba halin magana, domin ta San Abraham kaifi daya ne, sannan ta yi Controlling kanta ne domin kada tsanar da take wa Aysha ya fito b'aro-b'aro, saboda har ita kanta Ayshar bata so ta San cewa ta tsane ta, ta kuma tsara hakan ne domin plan din ta ya tafi daidai yanda ta tsara...
Indo kuwa runtse idanunta tayi tana jiran sauk'ar mari, jin shiru ne yasa ta Bud'e idanunta cikin mamakin rashin marin da madam Gloria bata mata ba, cikin sheshek'ar kuka ta dauko Abin shara da Abin kwashewa ta shiga tattare fasashen plates din, cikin rashin sani ta taka wani fasashen plate...
Kara ta saki, inda a tare ita da Abraham suka runtse idanun su, wanda shi kanshi bai San yayi hakan ba.....
Saboda d'auriya irin na Aysha, ta kuwa Mike ta karasa tattara wajen ba tare da ta damu da cire broken plate dake tafin kafar ta ba.
Cikin k'ok'arin shanye zafin da take ji ta koma kitchen din ta dauko wasu plates din, wanna karon Sam bata yarda sun hada ido ba, duk da yanda take jin idanun sa na yawo a kanta, a nutse ta fara serving dinsu, amma tayi kokari matuka wurin controlling kanta domin sosai hannun ta ke rawa....
Bayan ta gama, ta jaa kafar ta zuwa sama tana zub da hawayen da bata San koma menene ba, domin indai fada da zagin madam Gloria ne ta fara sabawa, har hakan bai fiye damun ta ba...
Kan mad'aid'aicin bed dinta ta zauna tana sauke nishi, kafar ta daya ta d'ora kan dayan da niyyar cire k'walban, amma ta kasa saboda zafin daya ziyarci k'wak'walwarta....
Kwanciya tayi a gadon ta cigaba kuka, har wani wahalallen bacci da bata shirya zuwan sa ba ya dauke ta....
Ta bangaren Abraham kuwa, hakan nan yaji ransa ba dadi a dalilin abinda ya faru, duk da dadin dandanon da abincin ke dashi akan bai sa yaci da yawa ba, ruwan black tea yayi sipping kana ya goge bakinsa da tissue, sannan ya mike...
"wait! Son don't tell me you re full?" ta fada cikin rashin jin dadi da kulawa kamar gaske.
"yes mum! Am going out"
ya amsa a takaice kana ya haura sama cikin abinda bai fi 7seconds ba...
da kallo mai tattare da zallan tsana hadi da muradin cika mugun nufin ta a kanshi ta bishi, kana ta dawo da kallon ta ga plate dinta mai shake da chips with fried eggs, a hankali tace "shege mai taurin rai, dama kayi accident a hanya ka mutu idan ka fita, kaga ka sauk'ak'e min aiki, na rasa me yasa har yanzu na kasa cika burina akan ka, tabbas nayi kuskuren barin Dan zaki ya girma" ta fada cikin yaren igbo hadi da cizon yatsan ta mai dauke da artificial nails...
*ABRAHAM*
Har ya murda handle da niyyar shiga part dinsa, sai kuma ya tsaya cak! Sak'amak'on brain din sa daya tariyo masa lokacin da fasashen plate din nan ya caki kafar ta da karan da ta saki, Lumshe ido yayi a hankali ya furta "is it still in her leg? “(ko har yanzu yana tafin kafar ta).
Tamkar wanda ake ja, haka ya nufi hanyar dakin ta, a hankali ya tura kofar ciki...
Kwance ya hangota, jin bata motsa ba yasa shi fahimtar bacci take, wanda hakan ya bashi kwarin guiwan zuwa gareta duk da bugawar da kirjin sa ke yi...
Tafin kafar ta da yayi jaa ya kurawa ido, a hankali ya dire guiwar sa kasa, kasancewar rub da ciki tayi ya bashi daman ganin kafar da kyau, a hankali yasa karfaffan hannun sa mai laushi ya kamo kafar ta, sannan ya a hankali ya fara zare fasashen plate din...
motsa kafar tayi wanda yasa shi dakatawa, hadi da fatan kad'a ta farka har ya gama...
Sai daya bari baccin ta ya kara nisa kana ya cigaba, inda yayi nasaran cirewa, ajiyar zuciya amma boyayye ya saki, kana ya cilla fasashen plate din cikin wani karamin dust bin dake dakin, da haka ya Mike ya bar dakin zuwa nasa, inda cikin mintuna arba'in ya shirya cikin wani Turkish suit ya bar gida zuwa ginin company dinsa daya kammala, inda a cikin satin nan za a yi bikin bude shi....
*AYSHA*
Awa biyu ta d'auka cikin baccin da bata jin dadin sa ba Sam, kana ta farka...
mikewa tayi zaune tana marairaice fuska saboda zogin da ta ji daga kafar ta, a hankali ta kamo kafar, yayin da kwalla ta cika idanun ta, sai dai rashin ganin alamun fasashen plate din ya bata mamaki kwarai, a hankali ta kai hannu ta shafi daidai wajen ciwon, taji wayam babu alamun plate din a tafin kafar ta, sosai hakan ya tsaya a ranta domin iya tunanin ta bata cire da kanta ba, toh waye? ganin kanta ya fara tsarawa sak'amak'on tunanin da ta fara yasa ta mike tana Jan kafar ta har zuwa toilet....
*Bayan kwana biyar*
Zuwa yanzu Aysha taji sauki sosai a kafarta, domin tana yawan dannawa da ruwan zafi,, kuma tun daga lokacin da Abin nan ya faru bata sake ganin Abraham ba, wanda hakan yayi mata dadi, domin idan ta ganshi rasa nutsuwar ta take yi, ko gyaran dakinsa sai ta tabbatar baya nan take shiga ta gyara masa....
*madam Gloria*
Zaune take kan gadon ta, tana k'ark'ad'a kafa hadi da sakin murmushin zallan nasara, Bud'e tafin hannun ta tayi, inda wani karamin roba mai dauke da guba, wanda wanna gobar ke da hadari sosai, domin daga India tayi order din sa, inda ta hanyar sirri tayi har ya iso gareta, domin hadarin da gubar ke da shi, saboda idan aka yi kuskuren kamata tata ta kare, hakan yasa tayi taka tsantsan k'warai wurin ganin cewa ba a samu matsala ba har poison din ya iso gareta...
Duba agogo tayi ta ga karfe 5:30pm inda a yanzu ta San cewa Aysha ta gama dinner, ko tana daf da gamawa, mikewa tayi ta fito zuwa kitchen, inda maganin na tamk'e cikin tafin hannun ta....
Share fisabillah
Comment for more typing...
Thank you all for reading my novel 🍇Abraham 🍓
#Noor🦋
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da facebook su yi join ta wanna link din.
Chapter 27-28
Tamk'ar barauniya haka ta fito cikin sanda, jin shiru babu motsin kowa a falon ya sanya ta sakin ajiyar zuciya, kana ta ci mur ta nufi kitchen kai tsaye, nan ma shiru babu kowa, hakan yasa cikin sauri ta shiga bud'e poison din, amma ta kasa, dogon tsaki ta saki, saboda ba karamin dauri aka masa ba, karshe dai wuka tasa ta yanke saman robar da k'yar, atishawa ta jera sau biyar, saboda karfin gubar da ta shak'a, gumi ta share, kana ta mayar da kallonta ga tukunyar dake ta tashin k'amshi mai dadin gaske...
Leka waje tayi ta ga babu alamun tahowar kowa, hakan yasa ta bud'e tukunyar, inda porridge yam din ke ta tafasa, murmushi ta saki, domin hakan yayi mata daidai, juye robar guban gabadaya cikin tukunyar mai dauk'e da porridge yam din tayi, inda dama ta cewa Indo ayi wa Abraham shi kadai, dama ka'idar gidan ne mai girki bata d'and'ana abincin da za ta yi wa masu gidan, idan ma ka yi tasting a bakin aikin ka.
Babban spoon ta saka ta jujjuya, rufe tukunyar tayi ta fita da sauri, inda taje toilet din dakinta ta yi flushing robar hadi da wanke hannun ta da hand-wash sosai saboda karfin gubar, fadawa tayi flat kan gadon ta, yayinda katon cikin ta da kamar ana kara masa girma kullum yayi tsalle, dariya zallan mugun ta ta saki tace "you re dead already Abraham hhhhhhhhh"
★★★
Aysha da ta fito daga toilet kuwa, cikin sauri ta sauko tuno abinda ta dora kad'a ya kone...
Shigar ta kitchen ya haddasa mata wata fad'uwar gaba da har yasa ta dafe kirjin ta, "Ya Rahman" ta furta saman labb'anta masu taushi da kyalli.
Idanunta ne ya kai kan saman murfin robar guban da madam Gloria ta yanke, wanda ta manta bata dauka ba, a hankali ta tsugunna hadi da dauko shi, while kirjinta ke cigaba da bugu kallon robar tayi ta ga anyi rubutun, amma ko harafi daya bazata iya pronouncing ba, cilli tayi dashi cikin dan kwand'on shara dake kitchen din, ganin wuka cikin sink ya bata mamaki, domin ita dai ta wanke komai ta mayar muhallin sa, ganin spoon again gefen sink ya kara bata mamaki....
"waya shigo kicin (kitchen) din nan?“ ta fada cikin karyewar zuciya..
Bude tukunyar girkin tayi, kana ta mayar ta rufe tana sauke numfashi, ganin kuma ya dahu ne yasa ta yi turning off gas hadi da dauko had'add'en warmer ta juye ciki...
Wanke komai tayi ta kara kyar kitchen din, dama ta gama girkawa madam Gloria abinda take so, fito da komai tayi kan dinning table, sannan ta koma dakin ta saboda lokacin magriba ya kusa...
*6:55pm*
Cikin sassarfa ya shigo cikin falon, idaunsa har lumshewa suke, ga wata azababben yunwa da yake ji, domin tun safe ruwan Black tea ne kawai a cikin sa, a matuk'ar gajiye yake sosai, sak'amak'on gajiyar daya kwaso, domin bai taba zirga-zirga irin na yau ba...
Cikin kulawa madam Gloria ta tare shi hadi da bashi side hug, "welcome back my son, my son has suffered today, Undu nwamu nkwo (Sannu yarona kaji) " ta karasa da yaren igbo.
Murmushi saman labb'a kwai yayi, yayin da idaunsa na kara lumshewa, kamar wanda aka tilasta wa yin magana yace "mum am badly hungry"
Wani irin sanyayyar dadi ne ya ratsa zuciyar madam Gloria, kansa ta shafa tace "toh son bari na kira Aysha tayi serving dinka"
A hankali ya bud'e idanunsa kana ya lashe labb'ansa da suka dan bushe kadan yace "lemme fresh up first"
"OK son, zan sa ta kawo maka dakin ka"
Ta fada tana bin bayan shi da wani mugun kallo hadi da murmushin samun nasara, sai daya bacewa ganin ta sannan ta saki wata katuwar dariya amma kasa² har da buga cinyar ta, duk da bai kai ga cin abincin ba, amma wani dadi ne ke ratsa ta, domin ta hango alamun NASARA a yau, domin abu ne mai wuya Abraham ya nemi Abinci a k'aran kansa...
*ABRAHAM*
Yana shiga dakin sa ya shiga toilet hadi da cika ruwan dumi a bathtub ya fada ciki, ya dauki tsahon mintuna goma a ciki, yayin da yake jin gajiyar na warware wa yana barin jikinsa a hankali...
Madam Gloria kuwa sawa ta yi lubabatu Kiran mata Aysha, inda babu bata lokaci suka sauka tare da ita, a yatsine ta kalli Aysha tace "ki dauki Abunshin (Abinci) yarona ki kai masa part din sa"
Cikin ladabi Aysha ta amsa da "toh" duk da fad'uwar gaban da take fama dashi, wanda sai kara tsananta yake...
Kitchen ta shiga, ta d'auko wani k'yak'yawan tray, dinning area ta d'awo ta saka warmer din cikin tray hadi da plate da spoon, sai roban ruwa, sama ta hau dashi, madam Gloria dake binta da kallo ta saki dariya kasa² cikin farinciki.
Knocking tayi har sau uku shiru, hakan yasa bakinta d'auke da sallama d'aya zame mata sabo ta tura kanta ciki, Lumshe ido tayi, domin kamar kullum dakin na wani irin kamshin na musamman, ware idanunta tayi, daram! Kirjinta ya buga da k'arfi sak'amak'on hango faffad'an bayansa da tayi, wanda babu riga, domin tsaye yake da towel a gaban dressing mirror yana shafa lotion, duk da yaji shigowar mutum, sannan kirjin sa ya buga domin ta, amma ko juyowa bai yi ba....
Aysha kuwa kamar Wacce aka dasa, kasa dago kanta tayi, tun kallon farkon da ta yi masa, domin sosai ya cika mata ido, controlling kanta tayi sak'amak'on hannun ta dake rawa, gashi ta kasa ajiye tray din, kamar yanda ko motsi k'wak'wara bata yi.
ABRAHAM kuwa hankali kwance ya shirya abinshi duk da tana dakin amma ko a jikin shi...
Cikin dagon wandon fari kal, hadi da black singlet ya shirya, roll on mai suna *Old spices* ya Murza a hammatan sa hadi da taje kansa sama² ya dawo bakin gado ya zauna tsahon mintuna biyar ba tare da yace komai ba....
A hankali ya sauke ganinsa kan ta, inda baya ganin fusk'ar ta sak'amak'on kanta dak'e tsunkuye, dan cizan labb'ansa yayi ba tare da kuma ya sake kallon ta ba, yace
"Am hungry, serve me!"
Rud'u ta shiga saboda jin amon husky voice dinsa, da kuma turancin sa da bata fahimci ko kalma daya daga ciki ba.
Amma sai tunanin ta ya bata cewa abinci yake nufin ta tabatar masa...
Dan haka tamk'ar mai tausayin taka saman tiles din ta nufi inda yake zaune, a hankali ta dire tray din kan Wani tum-tum dake gabansa, plate ta dauka ta fara serving din shi...
Sirarran hannun ta dake ta faman rawa ya shiga rarraba idanun sa a kansu, yana mamakin meke haddasa mata wanna rawan jikin...
Aysha kuwa abubuwa da dama sun dame ta, na farko kusancin su dake haddasa mata shiga wani yanayi na loosing control, na biyu kuma haka kawai kallon Abinci ke sata fad'uwar wanda bata taba Jin hakan ba, hakan nan bata yarda da abincin ba, duk da kyau, hadi da haduwar abincin...
Bayan ta zuba masa ta ajiye gabansa, gefe tayi ta shiga murza hannun ta, domin ta kasa barin dakin, a hankali ta Lumshe idanunta hawaye suka gangaro kuncin ta, hak'ik'a abinda take ji a zuciyar ta ba karami bane a yau, saboda bata taba faduwar gaba irin wanna ranar ba.
Share hawayen ta tayi, ta Bude idanunta inda ta sauke su kan doyar daya raba biyu da spoon, maimakon taga cikin doyar fari sai ta ganshi yellow shaar, ga wani kyalli da cikin doyar keyi kamar maiko-maiko...
kanta ne ya kara d'aurewa domin lok'acin da take fere doyar fari kal sosai yake, ba wanna ba, iya Sanin ta dai ko an dafa doya cikin shi baya wanna yellow'n ko da faten sa ne kuwa...
Take k'wak'walwarta ta kara hasko mata yanda ta ga kitchen dazu, so take ta furta wani Abu amma ta kasa ganin ya kai lomar farko bakinsa...
Wanda ya kara hadd'asa mata wata faduwar gaba mai tsanani, ganin yana kokarin kai loma ta biyu bakinsa yasa da gudu ta nufe shi, ta ture hannun shi, inda Abincin ya zube har kan farin wandonsa...
AYSHA
duk da tsananin tsoron da take ji a dalilin abinda ta yi masa, amma bata da zabi, sannan bata damu da hukuncin da zai biyo baya ba matuk'ar ta samu ta hanasa cigaba da cin Abincin...
"ka... ka... ka... yi hakuri dan Allah da Annabi, wallahi hankalina bai kwanta da Abincin nan ba, duk da ni na dafa, kayi hakuri yanzu zan je in dafa maka wani Abu mai sauri kaji" ta karasa cikin yanayi na rud'ewa da zubar hawaye masu zafi...
*ABRAHAM*
Zuba mata ido yayi, yana kallon kananan labb'anta masu moving very fast, ba dan ya fahimci ko kalma daya daga maganganun ta ba, illa yana mamakin dalilin barar da lomar Abincin da yake kokarin kai bakinsa...
Me hakan yake nufi?
Aysha kuwa cikin sassarfa ta nufi hanyar fita daga dakin, har ta dora hannun ta a handle ta ji ihun sa...
"Arrrrrrrh!!!“
A razane ta juyo, inda ta gan shi har ya sauko kasa kan guiwar sa hannun sa biyu dafe da cikin sa, yayin da ya zuba mata idanun sa da suka yi wani irin jaa tashi daya hadi da tara ruwan hawaye cikin su...
(Not edited) 🤒
What's your opinion on this episode reader's???
Share✅
Comment✅
NoorEemaan🦋
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da facebook su yi join ta wanna link din.
_kuyi hakuri Na san page din yayi kad'an sosai am sorry, dan nayi alkawari ne shiyasa na cika, at least da babu gwara ba dadi , ba haka na so ba wlh, amma banda zabi daya huce haka, domin babu lokaci, kuyi manage da wanna in sha Allah ranar lahadi zan Baku update, karku yi korafi please_🤒
Chapter 29-30
(Not Edited)
Sandarewa tayi a tsaye sak'amak'on abinda take gani, "mike shirin faruwa ne yau ya Allah " ta aiyana a ranta yayinda hawaye wani na bin wani a fuskar ta, jin ya kara sakin wani karan hadi da sulalewa kasa dafe da cikinsa da yake jin wasu azaba a cikin su.
Cikin firgicewa hadi da tsantsar tsoro daya bayyana a fuskar ta karara ta nufi wajen shi da gudu, cikin rud'ewa ta tallafi kansa da ke kansa tiles ta rike a tafin hannun ta, fashewa tayi da kuka tace "Dan Allah yallabai ka tashi, ka rufa min asiri, ni Dama ban yarda da wanna abincin ba, duk da ni na dafa, dan Allah ka tashi wayyo Inna ta!!!" ta karasa cikin amon sauti mai matuk'ar taɓa zuciya, Abraham kuwa wata mahaukaciyar yamutsa cikin sa ke yi, yayinda yake jin kamar ana saka wuka mai kaifi Ana dasa ko wani jijiya dake cikinsa, kasan maransa kuwa ji yake kamar ana diga masa narkakiyyar ruwan dalma a kai...
Still idanunsa na kan Aysha da yake bin ta da wani irin kallo dashi kan shi bai San ma'anar sa ba, ruwan hawaye ne suka taro a cikin kwarmin idanunsa, amma basu zubo ba, duk da sanyin air conditioner dake dakin, hakan bai hana jikinsa hadi da singlet din jikin sa sun jike da gumi daya karyo masa all of a sudden ba, saboda tashin hankali mara misaltuwa da yake ciki.
AYSHA
Kuka sosai take tana jijjiga kansa, fadi take ya rufe mata asiri ya tashi, ganin abin kara gaba yake yasa ta ajiye kansa a hankali ta fice da gudu zuwa downstairs....
Madam Gloria da ta yi pretending cewa tana kallo TV , amma azahiri Sam ba haka ne, ta kasa kunne ne taji kyakyawar labarin cewa Abraham is no more...
Jin takun sauk'owar Aysha yasa ta dago kanta da sauri, yayinda ta saki boyayyen murmushi, domin tsantsar tashin hankalin data hango a fusk'ar Aysha wanda ko tantama bata yi, alamun samun nasarar ta ne.
Gabanta Aysha ta zube, cikin shesheka take nuni da hanyar step din, kana ta fisgo maganar daya makale a makoshin ta... "zai mutu, ki taimaka min ki zo, yana kwance cikin mayuwancin hali"
"ke nutsu ki fadamin, me yana faruwa, waye zai mutu, me kika yi wa yarona, ki sani duk abinda ya samu yaron na bazan bar ki ba" madam Gloria ta fada hankali a tashe, kamar gaske.
Cak kukan Indo ya tsaya sak'amak'on jin abinda madam Gloria tace, wani sabon kukan ta kara sawa, kana cikin raunataciyyar murya tace "wallahi Allah na rantse ban yi masa komai ba"
Madam Gloria bata kara cewa komai ta nufi hanyar step da gudu, burinta ta kawai ta isa dakin, ba Wai dan ta damu da halin da yake ciki ba, a'a a k'age take ta je domin ganin halin da yake ciki, wanda take fatan ransa ya bar gangan jikinsa...
A tare ita da Aysha dake biye da ita suka sanya kansu dakin, sai dai shiru dakin, ba motsin komai, rarrabe ido madam Gloria tayi har ta hango shi kwance flat a can gefe idanunsa a Lumshe inda zuwa yanzu dishi-dishi yake gani.
Da gudu madam Gloria ta kara sa gareshi, kukan zallan tuggu da makirci ta fara yi tana fadin, "please son wake up! don't do this to me, somebody help me oo!" ta karasa tana jijjiga Abraham, amma daga ta cikin zuciyar ta farinciki ne fal cikinsa.
Cikin son juye komai ya dawo kan Aysha baiwar Allah tace " kin k'ade, kin shiga goma sha biyar bama uku ba, matuk'ar komai ya samu son, zaki gaya min me kika saka masa a abinci, ji ki kira min driver da mai gadi su tayani kai shi mota" ta karasa a tsawace mai hade da kuka.
Da gudu Aysha ta bar dakin gwanin tausayi, madam Gloria kuwa ta dire kan shi da karfi cikin halin ko in kula, wanda hakan yasa idanunsa dake Lumshe suka dan bud'e kad'an amma Sam mutum bazai lura ba ya bi madam Gloria dashi, cikin sauri ta Bude drawer din shi ta yi sa'ar samun wani kyakyawan farin leda, abincin cikin warmer hadi da na plate din ta juye cikin ledar, kana ta kulla da kyau ta jefar cikin karamin kwandon shara dake dakin, wanda tayi hakan ne domin koda za a yi bincike bata so ya tsananta, domin tasan dangin mahaifin Abraham basu da wasa, baya ga haka, matukar aka gano kalar guban, ba karamin matsala bace...
Dariya ta saka, wanda yasa Abraham mamaki kwarai, Sam baya son k'wak'walwa da zuciyar sa su yarda da abinda suke son bijiro masa, so yake ya furta wata kalma amma labb'ansa sun yi masa nauyi ainun, wani bakin duhu ne ya rufe idanunsa, sama² yaji tace "Dan banza mai tarin rai, dama ka mutu na huta" daga nan bai kara sanin inda kansa yake ba....
Jin takun haurowar su Aysha yasa da sauri ta koma kan Abraham tana jijjiga shi, sannan ta cigaba da kukan ta.
Hankali a tashe suka kama Abraham da kyar zuwa kasa, domin ginanen jikinsa yasa yake da weight, ba kuma dan yana da kiba ba, a'a kasancewar sa giant ne kuma mai gymming yasa haka.
Babu bata lokaci suka bar gidan, yayinda Indo dake tsaye a compound din gidan ta bisu da kallo hadi da zubewa kan guiwar ta ta saki kuka mai tab'a zuciya, taso bin su asibitin amma madam Gloria ta ture ta cikin shammata a lokacin da take k'ok'arin shiga motar, ta jima sosai tana kukan, kana ta ja kafarta daya yi sanyin kalau zuwa cikin gidan, cike da fatan Allah yasa ya rayu, domin Sam bata son shiga tashin hankali har yaje ga kunnen Inna da ta dan samu farinciki, kuma ko da wasa bata son wanna farincikin ya gushe.
Ta bangaren su madam Gloria kuwa gudu sosai driver yake falfalawa yayinda madam Gloria ke kuka tana surutai cikin yaren igbo, wanda ba komai take fadi ba illa jifan Abraham da kalamai marasa kyau hadi da yi masa fatan mutuwa, driver dake tuki ya kalle ta hadi da girgiza kai cikin tausayin ta, tabbas a yanayin yanda take kuka tana maganganun dole ta baka tausayi, domin mutum zai yi tunanin abin arziki take fadi, sanin cewa driver baya jin yaren Igbo yasa ta fadi abinda take so babu ko sha yi
Tafiyar mintuna ashirin da biyar ta kawo su wani had'add'en private hospital, cikin sanin makamin aiki nurses din suka tura shi zuwa emergency ward ganin halin da yake ciki, kasa zama madam tayi, burinta kawai Doctor ya fito ya sanar mata mutuwar sa, da babu abinda zai hana ta fasa kukan murna...
_5 hours later_
Dare yayi sosai, kuma har zuwa wanna lokacin babu wani doctor ko nurse daya fito daga emergency ward din bare ta samu damar tambayar sa, safa da marwa kawai take a matukar kage, sai da aka sake dauk'ar wasu mintuna talatin din sannan doctor ya fito yana sharce gumi, kai kace ruwa ne a fusk'ar sa, cire medicated glass din idanunsa yayi ya kalli madam Gloria yace "madam follow me to my office"
*my wattpad fans keep the comment going and please don't forget to follow my account and also vote my stories thank you*
Share to other group's please 🙏
NoorEemaan
O7082281566
10:41pm
Friday, 18 February.
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
*WATTPAD*
@NoorEemaan
*Ku tayani da Addu'a my lovely fans🥺*
Chapter 31-32
Cikin zumudi ta bishi tana fata a ranta taji labarin mutuwar sa kawai...
"have a sit madam" doctor yace mata.
Da sauri madam Gloria ta zauna, numfashi ya sauk'e yace "am very Angry madam, ta ya ya za a yi poisoning din mutum da guba mai matuk'ar hadari irin wanna, taya ma gubar da babu a kasar nan ta shigo Nigeria? waya yayi masa wanna mummunar aikin, madam, lemme tell you idan baki dauki mataki ba, ni da kaina zan dauka, duk da ban hada dangi da ku ba, amma dole wanda yayi poisoning wanna saurayin a hukunta shi, domin ya zama izina ga duk wanda zai shigo mana da irin wanna abun mai hadarin gaske kasar mu" ya karasa cikin murya mai nuni da zallan bacin rai da kuma nuna hak'ink'anin abinda ke cikin zuciyar sa, wanda kai tsaye mutum zai fahimci cewa shi din ba iya likita bane mai duba mara lafiya, har kishin kasar sa da Al'ummar ƙasar sa yake yi.
Sosai cikin madam Gloria ya duri ruwa har wani dan motsi katon cikin ta yayi, domin bata ga alamun wasa a tare da shi ba, kuma yanayin sa kadai da ta gani ya nuna cewa shi din mai arziki ne sosai, cikin sauri ta fashe da kuka tace "makiya ne ke son ganin bayan tilon dana, ni kaina zan dauki mataki doctor, bazan bari ba, na kuma gode da kulawar ka ga Dana, yanzu a wani hali yake ciki doctor?" ta fada gwanin tausayi a fili, yayin da can kasan zuciyar ta take muradin jin cewa ya mutu...
Numfashi mai zafi likitan ya furzar domin haka kawai yaji maganar Abraham din har ranshi, wanda ba komai bane face haduwar jini da Allah kan hada mutum da mutum dashi, siririn farin medicated glass din shi ya cire, hadi da hade hannun shi waje daya kan teburi yace "hakika ban taba ganin JARUMI kamar dan ki ba, duk da hadarin da gubar nan ke da shi, amma har yanzu yana Numfashi wanda hakan ya nuna min cewa tabbas akwai muradi da fatan cigaba da rayuwar sa domin ya cimma wani babban buri nashi"
Gaban madam Gloria ya yi wata mahaukaciyar bugawa, she can't believe that Abraham yana raye, despite the fact that yaci gubar nan...
"This is unbelievable" ta fada a ranta yayinda gumi na tashin hankali ya tsatsafo a goshin ta.
Ba tare da ta San maganar ya fito fili ba tace "doctor kana nufin bai mutu ba, yana raye?"
Murmurshi doctor yayi ba tare da ya lura da yanayin kuncin da take ciki yace "kinyi mamaki ko? Ni kaina da abokan aikina munyi mamakin hakan qwarai, domin Bamu taba haduwa da patient hero(jarumi) irin wanna ba, yanzu dai yana dakin hutu, kuma karfin gubar ya tsinka masa y'ay'an hanji hudu, a cikin sa, wanda hakan yasa bazai iya tsaye kan kafafunsa yanzu ba, amma hopefully zai iya tashi in sha Allah matukar an dage da yi masa magani da kula da lafiyar sa"
Wani dunkulallen abu madam Gloria ta hadiya, hakika mutuwar sa kawai taso ji, "na rasa wani irin taurin rai ne da wannan yaron, ace duk karfin gubar nan bai mutu" ta fada a ranta kana ta maida kallon ta ga doctor, ta ga hankalin sa na kan cike wani file, cikin sauri ta fice daga asibitin gabadaya...
Sai washegari madam Gloria ta dawo asibitin, amma ba a bata damar ganin Abraham din ba, a takaice dai sai bayan sati hudu aka fito dashi daga dakin hutu, inda aka turo Abraham kan keken guragu zuwa waje, saboda baya iya tsaye kan kafafun sa, gashi ya dawo so cool baya fiye da baya, ko yin magana baya yi, domin babu yanda doctors basu yi ba, amma baya cewa komai, kullum kanshi na duke.
Da taimakon driver aka saka shi cikin motar da wasu doctors, kana suka fice daga asibitin.
AYSHA
Zaune take a dakin ta tayi zuru-zuru kullum cikin tunanin halin da Abraham ke ciki take, burinta kada wani abu ya same shi, bata San yanda zatayi ba, kullum raba dare take tana tunanin halin da yake ciki hadi da sa shi cikin addu'oi'nta, gashi ko ganin madam Gloria ta daina yi tun daga ranar da Abin nan ya faru.
A karo na ba adadi ta shara hawaye, dama ita mai rauni ce da Sanyi, amma yanzu raunin ta da sanyin ta sun karu fiye dana baya, tana cikin haka taji an danna horn, a zabure ta Mike tsaye hadi da dafe kirjin ta daya tsananta bugu, cikin sauri ta sauko kasa, wanda yayi daidai da turo Abraham da madam Gloria tayi zuwa cikin falon, a hankali aysha ta sulale kasa hadi da furta "Innalillahi wa innah ilaihi raju'un" ta kasa yarda cewa lafiyayyen Abraham data sani ne aka dawo turo shi kan keken guragu?
Wani mugun kallo madam Gloria ta jefawa aysha daya sa hantar cikin kad'awa, amma bata ce komai ba, domin burin ganin bayan Abraham ne a ranta yanzu, bata da lokacin bata wa, saman part din Abraham ta nufa dashi, kasancewar kuma benen ba mai tudu bane yasa ta hau saman da shi da kyar zuwa dakinsa kana ta sauko...
Aysha ta jima sosai tana kuka a wajen kana ta nufi dakin ta yayin da ta dafe kanta dake Sara mata sosai, kwanciya tayi tana sakin sheshek'a har wani wahalallen bacci yayi gaba da ita.
*BANGAREN ANTY SARAH*
Tana zaune har yanzu a asalin kauyenta, ta sanja sosai, domin Sam jin dadi da take a birni babu shi a kauyen, tayi duhu kamar ba ita ba, domin Matar yayanta take bi gona suna aiki tare, daga nan take samun yan chanji na kashe wa, kullum cikin damuwa da neman tuba take wurin Allah saboda zunuban data aikata, lokaci kawai take jira domin ta bayyana gaskiya....
*MADAM GLORIA*
Safa da marwa take a dakin ta yayinda take naushin iska da k'aurarran hannunta, irin na jin haushin nan, duk da cewa ta samu tayi nasara wanna karon a kan Abraham amma ba haka taso ba, so tayi ya mutu gabadaya...
Kwarab kake ji ta zube a gadon ta kana ta kada kai da harshe irin na zallan muguntar nan tace "a Sannu zaka karasa mutuwa matuk'ar ni Gloria ina raye"
Sai bayan la'asar ta tashi daga bacci, inda ta ji ciwon kan ya dan lafa kadan, tuno cewa bata yi azahar ba ga la'asar yasa ta Mike a hankali ta shiga toilet, alwala ta dora kana ta fito ta shiga yin sallah, Bayan ta iddar ta zauna tayi addu'ointa sosai kana ta Mike bayan ta dan yi tilawa kadan.
Kitchen ta nufa inda tayi musu abinci cikin kasa da awa biyu, gyara kitchen din tayi ta mayar da komai muhallin sa, abinci ta jera a dinning table kana ta bar wajen zuwa sama, har ta wuce taji cewa ya kamata ta leka dakin Abraham, duk da faduwa da gaban ta keyi amma haka ta shanye tsoro da fargaban da take ji ta murda kofar dakin, bakin ta dauke da sallama....
Zaune ta ganshi kan wheelchair kanshi na duke, tausayin sa mai yawa take ji na ratsa zuciyar ta, a hankali ta fara takawa zuwa gareshi, yayinda ko wani taku da zata yi yana tafiya da bugun zuciyar ta...
Bangaren Abraham ma kamar ko yaushe idan ta samu kusanci dashi ya kan ji bugun zuciya da wani yanayi da baya ji ga kowa sai ita...
Gaban shi ta tsugunna ta kama hannun wheelchair din, kanta a kasa yayinda ta kurawa kafar sa ido...
K'walla ta share, cikin rawar baki tace "ina wuni, ya jikin ka? dan Allah kayi hakuri ni kaina ban San abinda ya faru ba, k'wak'walwata ta toshe" ta karasa tana sakin kuka gwanin tausayi....
A hankali ya dago kansa yana jin kukan ta har kasan rashi, be San me yasa yake jin ta special ba a ransa, amma tuno poison din daya ci daga Abincin data serving din shi sai yake jin wani Abu mai kama da rashin yarda da ita, duk da babu wanda yafi bashi zunzurutun mamaki kamar madam Gloria, amma so yake zuciyar sa da kunne sa su karyata masa abinda yaji madam Gloria ta fada kafin ya suma, ya kasa yarda cewa mummyn sa mai matuk'ar kaunar sa ce ke son ganin bayan sa, daya takurawa kanshi da tunani sai yaji brain dinsa kamar zai tashi daga aiki, sosai yake cikin pain mai tsananin gaske, komai ma baya masa dadi, yanzu ne kewar mahaifiyarsa, mahaifinsa, hadi da Nonyen sa mai tsananin gaske ke kara lullubeshi, baya manta tarin son da iyayen sa ke masa, haka zalika baya manta kulawar Nonye gareshi...
Shiru dakin ya d'auka, sai kukan Aysha dake tashi kadan-kadan, a hankali ta dago da niyyar kallon shi jin bai amsa gaisuwar ta ba, ta ma manta cewa shi din ko digon hausa baya ji, ita burinta kawai ya amsa mata domin ta samu salama a ranta, karaf idanunsu suka fada cikin na juna, cikin sauri tayi kasa da kanta, gaban ta na kara fad'uwa Sam ta kasa fassara kallon da yake mata, a hankali ta Mike ta fice daga dakin cikin sanyin jiki...
Da kallo yabi bayan ta yana sauke numfashi a boye, ji yayi zuciyar sa ta kuntata, dama zai iya tashi kan kafafun sa, domin ya San ta yanda zai gano wace makiyar sa? sannan meye laifin sa? domin har yanzu he is totally confused.
*7:55pm*
A daidai lokacin Aysha ta iddar da sallah isha, Bayan ta gama addu'oi'nta, ta yamutsa fuska kamar mai son yin shagwaba tace "ko ya ji abinci?“ domin bata ga madam Gloria ta hauro saman ba balle ta ce ta bashi abinci, mikewa tayi da hijab dinta zuwa down stairs, Bude duka warmers din tayi taga alamun an dibi abincicikan kuma ta San madam Gloria ce, amma still tana tsoro hakan yasa ta dauki wani spoon tayi loma daya na ko wani abinci, idan ma akwai Abin cutarwa a cikin abinci ita zai fara cutarwa, domin har ga ranta yanzu tsoron gidan nan take...
*30 minutes later*
Sai yanzu hankalin ta ya kwanta da Abincin hakan yasa ta dibar masa komai ta jera a tray ta nufi upstairs...
_Jiya nayi alkawarin posting, amma wani bacci mai dadi ya dauke ni da ban shirya zuwan sa ba, am so sorry for the inconvenience_.
Share and comment please 🤒
Noor 🦋
07082281566
Thank you for reading 🍇Abraham🍓
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
_Making Dua for the others without knowing them is one of the exceptional beauties of Islam and in return, the angels would recommend to Allah for you. Keep praying. May this valuable day bring satisfaction in your heart and fill your life with the endowments of Allah_.
Happy New week my lovely fans
Chapter 33-34
Sanin cewa ba bata izinin shigowa zai yi ba yasa kai tsaye ta shiga dakin bakinta dauke da sallama as usually.
Gabansa ta ajiye tray din, kana cikin yanayin ta na Sanyi da nutsuwa ta fara serving dinshi cikin wani karamin bowl, Bayan ta gama ta dauke tray din ta ajiye a gefe, sannan ta kara matsowa daf dashi, spoon tasa ta dibi abincin ta kai bakinsa....
*ABRAHAM*
Kura mata ido yayi, yayin da wani yanayi mai kama da rashin yarda ya shiga ratsa zuciyar sa, amma gangan jikina sa taki yarda da hakan, Aysha kuwa ganin cewa har yanzu bai karba ba, yasa ta dago idanunta da suka cika taf da kwalla ta zuba masa, wanda ya sanya ruwan hawaye daya taru a idanunta suka diga kan abincin dake cikin spoon din hannun ta, tabbas ta fahimci yanayin sa kuma duk wanda yayi passing through irin abinda ya faru dashi hakan zai yi, saboda haka bata ga laifin sa ba, juyar da spoon din zuwa bakinta tayi, a nutse ta shiga tauna abincin har ta hadiye, cokali uku tayi, sannan ta kara diba ta kai bakin shi, Abraham daya kurawa kyawawan labb'anta ido tun daga lokacin data fara tauna abincin ya Bude bakinsa kamar wani karamin yaro ta zuba masa a baki ya shiga taunan abincin, hak'ik'a idan yace baya jin yunwa yayi karya, damuwa ce tayi masa yawa...
Aysha kuwa sosai taji dadi wanda har hakan yasa taji wani zallan dadi a ranta, hakan yasa ta cigaba da bashi har ya koshi, da ta kara debo na karshe ta nufi bakin sa dashi ya yi kasa da spoon din hannunta wanda yasa ta fahimci cewa ya koshi, ajiye cokalin tayi ta siyayi ruwa a cup ta dora masa a lips dinsa, ya Bude baki ya sha kadan kana ya cire bakin sa, tattara wajen tayi ta fitar da tray din kitchen, ta wanke komai, duk da cewa baya daga cikin aiyukan ta na gidan wanke-wanke.
Bayan ta haura sama, dakinta ta nufa kai tsaye, domin gajiya take ji a ko wani sassan na jikin ta, direct toilet ta shiga tayi wanka kana ta fito daure da towel a k'irjin ta, sosai skin d'inta ke shining, ga girma da ta d'an kara wanda hakan ya kara bayyana kyawun ta.
Hannunta ta daura a k'irjin ta-ta kurawa kanta ido ta mirror, sarkan nan mai dauke da sunan NONYE ta saka hannun ta daya ta shiga shafawa, sarkan na shinning tamk'ar yanda ta dauko a dakin baffa tuno baffan kuma yasa ta ji wani iri ba dadi ranta, sai dai tayi k'oka'rin k'awar da tunanin sa, inda ta shiga shafa lotion a sanyayye kan lallausar farar skin dinta, Bayan nan ta zira doguwar rigar roba ba tare da ta sa bra ba domin bata iya bacci da bra, wani farin hijab dinta medium size ta sanya kan kayan, kasancewar hijab din bai da hula hakan ya taimaka wurin bayyana gashin gaban kanta kwantaccen kamar na jarirai, kan gado ta hau ta kwanta tana nannade jikin ta tamk'ar mai jin Sanyi...
Lumshe ido tayi tana jin kewar su Innah, so take abubuwa su daidaita ta siyawa Inna da ita kanta waya koda karama ce domin ta dinga jin muryar su a lokacin da take so, ta fi mintuna arba'in tana sake-sake, sai kuma tunanin ta ya sanja ya dawo na Abraham, "yanzu idan yana bukatar wani Abu cikin dare ko anjima fa, wa zai bashi?" tayi wa kanta tambayar yayinda fuskar ta ke bayyana tausayin sa mai yawa...
Kamar Wacce aka tsik'ara ta Mike, hanyar dakin, sa ta nufa ta tura a hankali ta shiga, kallon tausayi tayi masa wanda hakan yasa hawaye suka cika idanunta, kamar yadda ta barshi, bai motsa daga inda yake ba, tunani tayi ko zai yi amfani da toilet, tunda shima Dan Adam ne kamar kowa, hannun ta - ta shiga murzawa tana tunanin Abin yi, domin ba jin yaren juna suke ba, bare ta yara masa.
Bayan sake-saken da ta Dan tsaya yi, bisa umarnin zuciyar ta ta nufe shi, a hankali ta tura shiga tura keken da yake zaune sak'amak'on zuciyar ta da ta bata umarnin yin haka, Abraham kuwa ko gezau bai yi ba, duk da cewa fitsari ya matse sa sosai amma saboda damuwa da halin k'uncin da yake ciki ya sa hakan bai dame sa ba.
Rufe kofar toilet tayi ta jingina kanta da jikin kofar, duk da cewa bata tab'a samun kusance da ko wani d'a namiji haka ba, in aka dauke baffan ta, amma tana jin Abraham har jininta, duk da cewa zuciyar ta na tsananta gudu a duk sa'ilin data samu kusanci dashi amma zuciyar ta da gangar jikin ta sun yarda hundred percent cewa ba zai taba cutar da ita ba, Sam bata jin bakon yanayi a tare da hakan, jin karan flushing yasa taji wani tausayin sa har hawaye ya gangaro mata, wato a matse yake tun dazu, amma bai nemi taimakon kowa ba, sai da ta kara mintuna goma sha biyar sannan tayi knocking hadi da turawa a hankali kamar mai Tsoron ganin wani mugun Abu, ganin shi zaune normal yasa ta tura keken suka fito, daidai bakin gadon ta tsayar da keken nasa sannan ta koma gefe ta hada kanta da guiwar ta...
Tsawon mintuna 5 dakin ya dauki shiru ba motsin komai, a hankali ya dago idanunsa ya zuba mata, sosai yake Jin wani yanayi na musamman da take kusa dashi, bai San abinda zai ce yana ji a tare da ita ba, amma tabbas yanayin bazai misaltu ko ya fadu ba.
Aysha kuwa tun tana duniyar tunani har jikinta ya fara saki sak'amak'on baccin daya fara dibar ta, gyangyadi ta fara yi gwanin burgewa da dariya wanda hakan ya kara bayyana yarintar ta, babu jimawa ta sulale kasan tiles din, wani bacci mai dadin gaske yayi awon gaba da ita ba tare da ta shirya ba.
ABRAHAM
Kallon ta yake tamk'ar ya samu hoto, domin ko kyafta idanunsa baya yi, kyawawan labban ta da ta tsuk'e yafi komai Jan hankalin sa musaman da ta dan turo shi gaba kad'an, cigaba yayi da Kallon ta har ya dauke idanunsa a kanta, ya Lumshe su hadi da yamutsa fuska domin ya gaji da zaman wheelchair din.
_1:22am_
Sanyin tiles ne ya shiga ratsa ko wani sassa na jikina sosai, wanda hakan yasa ta motsa hadi da ware idanunta, cikin sauri ta Mike domin Sam bata San cewa baccin ya dauke ta ba, a hankali ta kai idanunta kan shi, inda taji wani mugun tausayin sa, ace mutum tun safe yana zaune waje daya bai motsa ba.
Mikewa tayi kusa dashi taga idanunsa a rufe yana bacci, tunanin taimaka masa wurin kwanciya tayi, sai dai ta rasa yanda zata fara, domin shi din ingarman namiji ne, duk da cewa yayi jinya amma bai yi loosing weight ba sai idanunsa kadai da suka fada ciki....
Hak'ik'a ko wani bawa da zaka gani yace abu kaza yafi karfin shi, ko ya dinga tunanin anya zai iya? Toh sai dai idan mutum bai sa kansa ba, amma matukar kasa kanka Allah zai taimaka maka, domin ubangiji baya taba dora wa bawa Abin da yafi karfin sa...
Misali Kamar Aysha Kenan ta kara matso da wheelchair din kusa da gadon sosai ya zamana babu wani sauran space tsakanin gadon da kujeran, sannan tayi kamar zata kife kujerar da dukanin karfin ta, sai ya fada kan gadon, kasancewar gadon bai da mugun tudu sai fadi hakan ya sa ta samu saukin kwantar dashi, sai dai yayi ruf da ciki, tsaye tayi tana sauke numfashin gajiya kamar wacce tayi tseren gudu, zaman wheelchair din ta gyara kana ta rufe shi da duvet bedsheets, a hankali ta shiga takawa cikin sanda domin barin dakin gudun kada ya farka....
*ABRAHAM*
Sai da daya daina jin motsin ta kana ya bud'e idanun sa, da suka bata hours a Lumshe ba kuma dan bacci yake ba, duk abinda tayi yana jin ta, daga kwantar dashi data yi har zuwa fitar ta daga dakin, dan cije labb'ansa yayi saboda wani zafi da yake ji daga cikinsa, ba kuma komai ya janyo hakan ba sai irin yanda Aysha ta kwantar da shi, wanda kuma ya jinjina k'ok'ari da jarumtar ta, haka ya cigaba da jurewa har bacci ya dauke shi...
Manage pls, kaina ya dauki chaji, ban da time wallahi, ina wajen aiki, gashi yau ina Azumi, may be kuga typing errors... 🤒
Share fisabilillah
Comment
NoorEemaan
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din.
Chapter 35-36
*WASHEGARI*
Da safe sai da Aysha ta leko dakin sa taga yana baccin kafin hankalin ta ya kwanta, downstairs ta sauk'a domin d'ora musu breakfast, ta rasa meyasa ta damu dashi har haka, sosai maganar sa da fatan ganin ya samu lafiya ya tsaya mata a rai kwarai.
Tana shiga kitchen din babu bata lokaci ta fara hada breakfast, cikin har da light food da ta San cewa zai yi daidai da condition din Abraham yanzu.
Tana cikin soya potato omelet taji knocking daga bakin kofar, cikin sauri ta kwashe omelet din, domin already ya riga ya soyu, kashe gas din tayi ta wanke hannun ta a sink ta gyara wuyar hijab dinta ta fita izuwa kofar falon da aka kara knocking yanzu.
Tsaye taga wani saurayi mai kimanin shekaru 35 sanye da bak'ak'en suit. Da kallo ta bishi na yan seconds kana ta dauke kanta hadi da cewa "ina kwana" duk da bata taba ganin fuskar sa ba.
Saurayin kuwa cikin girmamawa ya russunar da kan sa, domin a tunanin sa Aysha Matar Abraham ce, duk da yaga alamun cewa ita din Musluma ce, amma ba Abin mamaki bane tunda hakan na faruwa, ma'aurata masu mabambamtan addin, kawar da tunanin yayi yace
"ina kwana Hajiya, suna na Kabeer Usman dama nazo neman sir Abraham ne, tun sanda ya dibi ma'aikata da kwana biyar Bamu sake ganin sa ba, ni ne personal assistant dinsa shine naso na duba ko lafiya domin na kira wayoyinsa basa shiga, yanzu ma ma'aikatan zan wuce na biyo ta nan"
Shiru Aysha tayi tana tunanin Kiran madam Gloria domin ita kam wanna abun yafi karfin ta, amma kasa da sixty seconds k'wak'walwarta ya bata cewa tun baya da madam Gloria ta dawo da Abraham daga hospital bata kara zuwa duba shi ba, shin ita wace irin uwa ce a gareshi? ta aiyana a ranta.
Zuciyar ta ce ta kara sauya tunani, kamar yadda yayi tunanin ita din Matar Abraham ce, a hakan zata tafiyar dashi, cikin sauri ta dago kanta duk da gabanta na faduwa sannan tana addu'ar kada Allah yasa madam gloria ta tashi daga bacci yanzu...
murmurshi tayi tace "ohh! Mijina ya bani labarin ka, ka shigo daga ciki"
tace tana juyawa izuwa ciki yayin da gabanta ke tsananta fad'uwa domin gani take kamar ba Indon baffa bace ke wannan abun, amma ta kasa sarrafa kanta, kamar Wacce ake bawa umarnin yin komai daga ta ciki.
Bayan ya zauna kan d'aya daga cikin had'add'un kujeran falon, kitchen ta shiga ta kawo masa shayi a kofin tangaran, kabeer Usman ya karba yana godiya hadi da yaba karamcin ta a ransa.
Aysha kuwa crossing legs dinta tayi tace "Am... kuyi hakuri bai sanar muku tafiyar sa ba, domin a gaggauce abubuwa suka zo masa, baya kasar shiyasa kuka ji shi shiru, tunda ya tafi nima jefi-jefi muke waya da lambar kasar domin baya da lokaci sosai, sakamakon Abinda ya kai shi kasar mai muhimmanci ne, sannan idan na samu lokaci zan zo duba kamfanin na ga yanda kuke gudanar da aikin, domin zai dauki watannin kafin ya dawo, duk da dama ya fada min cewa yana da mataimaki wanda zai iya kula da company's sa ko da baya nan wato kai, ina fatan zaki yi aiki tukuru wurin rike ragamar kamfanin da amana kamar yadda Mijina ya fada, ya kuma d'aura maka yarda"
Aysha ta karasa tana dan goge wani gumi daya karyo mata ya biyo ta gefen fuskar ta...
Shi kuwa Kabeer Usman murmurshin jin dadi yayi saboda kalaman ta na karshe, cikin kwarin guiwa yace "in sha Allah zan rike amanar company, har Allah ya dawo dashi, duk wani abu dake faruwa zan dinga tura masa ta gmail din sa".
"Na gode kwarai Malam kabeer Usman" Aysha ta fada, tana dan mazewa wanda hakan ya kara mata kwarjini, kai kace wata babbar mace ce.
Kabeer Usman kuwa kara sipping tea dinsa yayi, domin yayi masa dadi over, kana ya Mike yana goge bakinsa, sallama yayi wa Aysha ya nufi hanyar fita daga falon, inda Aysha ta take masa baya har izuwa bakin kofar falon kana ta dawo ta zube kan kujera tana sauke numfashi, sosai ta jinjina karfin hali irin nata, tuno cewa madam Gloria zata iya fitowa at any time yasa ta dauki kofin shayin data zuba wa P.A ta nufi kitchen, wanke wa tayi ta mayar muhallin sa kana ta shiga gyara kitchen din, tana kokarin jera warmers a tray taji takun takalmin madam gloria na tunkaro kitchen din...
Cikin sauri hadi da girmamawa ta shiga gaishe da madam Gloria, a yatsine ta amsa kamar yadda ta saba, Bude warmers din ta shiga yi, kana ta juya domin fita, har ta je bakin kofar kitchen din ta juyo cikin gurbataciyyar hausar ta tace "wa ya shigo gidan. nan dazu"
Waro ido Aysha tayi gabanta na fad'uwa, a hankali ta juyo tace "babu wanda ya shigo..." ta karasa cikin aro jarumta, ita kanta bata San dalilin boye mata ba, amma hakan zuciyar ta ke bata umarni.
"babu wanda ya shigo kika ce ?" madam Gloria ta fada tana bin fuskar Aysha da kallo a kokarin ta na son gano gaskiyar maganar ta.
"eh madam!" Aysha ta kara fada cikin dak'ewa fiye da dazu.
Kallon ta madam Gloria ta sake yi na mintuna biyu kacal kana ta jinjina kai tace "zo kiyi serving dina breakfast, zan fita yanzu"...
"toh" Aysha ta amsa tana cigaba da jera warmers din, a ranta tace
"na shiga uku ni Aysha, Mata da danta amma nafi zak'ewa akan al'amarin da ban San mafari ba" ta fada a hankali.
A sanyaye ta fita, ta serving madam Gloria kana ta haura sama domin yin wanka.
Tana cikin shiryawa taji fitar madam Gloria a mota, karasa shiryawa tayi a nutse kana ta leka dakin Abraham, kokarin mikewa taga yanayi amma ya kasa, instead sai ma zafi da yake ji, a sanyaye ta mayar da kofar ta rufe domin dama kadan ta bude shiyasa bai lura da ita, downstairs ta sauka, daga nan ta fita izuwa farfajiyar gidan, wajen mai gadi tace
"ina kwana"
"ah ah Indo ce, Kin tashi lafiya?"
mai gadi ya fada yana washe hakoran sa da suka sanja kala zuwa brown.
"lafiya lau, dama yallabai zaka taya ni dorawa kan keken sa" ta fada cikin marairaicewa.
"yanzu kuwa indo do, Allah sarki yallabai mai kirki, gashi waccen uwar tasa ta fita, yaro ba lafiya amma taci wata uwar Kwalliya sai kace yarinya ta fita, babu abinda ta iya sai masifa da iya daga hanci" ya fada yana k'waik'wayon yanda madam Gloria ke daga hanci.
Aysha kuwa duk da kalaman sa na karshe ya bata dariya amma Bata yi ba, sai ma gaba da ta yi, domin tana daya daga cikin Wacce bata so ayi maganar wani, ko aibata wani da ita.
Mai gadi kuwa take mata baya yake, ya ja bakin sa ya tsuke ganin Aysha bata bashi fuskar cigaba da kowa mata wata maganar ba.
Sabanin dazu da yake kokarin mik'ewa, yanzu kawai ya kwanta ne ya Lumshe ido cikin kunar rai, yaji shigowar mutane amma bai Bude idanun sa ba bare ya ga ko su waye , karasa jikin gadon mai gadi yayi yana cewa "sorry sir, how Body? your body go soon better you hear, sorry oga na" mai gadi ya fada cikin pidgin English daya koya a nan kaduna, duk da tune din hausa ya fito sosai a harshen sa wanda hakan zai sa mutum ya fahimci cewa shi din bahaushe ne.
Abraham kuwa shiru yayi still bai Bude idanun sa ba, da k'yar mai gadi ya fara kokarin daga shi, jajayen idanun sa sun firfito waje, kasa hakuri yayi yace "jar uba! Wallahi Indo oga ya shiga gasar dambe dole ya kad'a maza, karfi ne dashi sosai Al-k'uranin ubangiji"
Kasa d'aurewa Aysha tayi har sai da ta fashe da dariya cikin siririyar muryar ta da amon sautinsa ya fito, wanda hakan yasa Abraham Bude sexy eyes dinsa ya watsa mata su, saurin gimtse dariyar ta tayi, tana mai yin kasa da kanta.
Mai gadi kuwa bayan ya dora Abraham a keken sa da k'yar yace "Allah ya kara lafiya oga, Indo sai anjima" ya fada yana fita daga dakin cikin tafiyar sa ta sauri.
Shiru dakin ya dauka, can ta Kara sa wajen shi ta tura shi izuwa toilet, maclean ta matsa masa a brush, sabulu da soso ta ajiye masa a inda hannun sa zai kai, kana ta bar bandakin tana rufe masa kofa, gyara masa dakin ta shiga yi, ta goge masa komai, Airfreshna ta fesa a ko wani kusurwa na dakin, sannan ta shiga kitchen da gymimg room din sa ta goge hadi da gyara masa, domin babu wani datti sai kura kawai suka yi....
Bayan ta gama taji shiru bai fito ba, hakan yasa ta kara sauka ta dauka masa breakfast ta dawo, sai a lokacin ta fara jin alamun an Bude kofa, idanun ta takai wajen kofar inda yake fitowa, tozalin da ta yi dashi Yasa ta juya da sauri tace "Innalillahi wa innah ilaihi raju'un" sak'amak'on ganin shi data yi da short nicker kadai, domin ya cire rigar da dogon wandon jikin sa, domin sun ishe shi.
Da fari ya zata wani abu ta gani, sai daga baya ya fahimci abinda take nufi, sai ma ta bashi dariya, murmushi da iyakar sa labb'a yayi kana ya dawo da fuskar sa yanda take a had'e har girar sa na tattarewa...
Aysha kuwa ba tare da kara juyowa ba ta nufi wardrobe din shi, wani riga ta gani hadi da 3 quarter wando ta miko masa idanun ta a gefe, bai kalle ta ba ya karba hadi da sanya rigar, sai wandon daya sa da k'yar shi ma bai zauna da kyau a waist din shi ba, kasancewar a zaune yake wanda kuma bashi da ikon tashi domin hakan na daga cikin kaddarar sa a yanzu....
Sai da ta daina jin motsin saka kayan, ta shiga bude idanun ta a hankali ta kalleshi, take idanun ta suka fada cikin nashi, saurin dauke idanun ta tayi kunyar sa mai yawa na ratsa ta, hakan nan take ji a ranta cewa tana huce gona da iri wurin bashi kulawa, domin da bata yawan zuwa dakin sa bazata ganshi a haka ba, duk da cewa wanna ba shine karon farko ba, amma akwai bambamci da ganin data fara masa ba riga, sai dai bata da zabi daya huce kula dashi din, tunda babu mai kula dashi din baya ga ita, domin ko kafar mahaifiyar sa bata gani a dakin sa, wanda hakan ke daure mata kai sosai, kawar da tunanin tayi ta fara serving din shi Abinci, ta dora masa a cinya, Bayan ta caka fork kan Irish potato omelet din, sai tea data zuba masa a cup, dakin ya gauraya da kamashin mai shiga zuciya...
Idanun sa ta ga ya rufe ya dora hannun sa saman abincin ya fara addu'a irin na chiristian a lokacin da zasu ci abincin...
Kura masa ido Aysha tayi ganin abinda yake yi, domin ita kam bata da ilimi kan abinda yake yi, garin kallon nasa ne idanunta suka sauka kan cross(+) din wuyar sa dake rito, a ranta tace "Dama maza na sa sarka, oh ni Aysha Indo" ta fada a ranta tana cigaba da kallon sa, sai da ta ga yana k'ok'arin d'agowa tayi saurin dauke kanta zuwa wani bangare daban...
Da yamma Lubabatu ta samu Aysha a kitchen tana girkin dare, gaisawa sukayi, kana ta mikawa Aysha kudin albashin ta, inda Lubabatu ke sanar mata cewa tun jiya madam Gloria ta mata transfer na albashin su, amma iya su mata masu aikin gidan, domin yau tafiya zata yi ba kuma zata dawo yau ba, duk da Aysha tayi mamakin jin cewa madam tayi tafiya, amma ta 6oye mamakin ta hadi da yiwa Lubabatu godiya ta fita, domin bata taba bari hira mai tsayi ya hada ta da ma'aikatan gidan ba, domin daga nan kananun maganganun ke fara tashi har ta kai ga gulma, hakan yasa take tsaye kan Lane(iyaka)dinta.
Allah yaso ruwa kadai ta dora a gas din, sai kawai ta tafasa musu spaghetti, Bayan ta gama tayi musu egg sauce daya hadu sosai sai tashi k'amshi yake, daga nan tayi mango juice da zallan fresh mango sai flavour data saka, hadi da sugar kadan, sai da ta tabbatar komai yayi daidai, ta dauki warmers biyun da jug din mango juice din ta nufi up stairs dasu....
Dakinsa ta ajiye warmers din, kana ta nufi dakin ta tayi wanka, domin ya zame mata sabo matukar tayi girki sai tayi wanka take jin dadin jikinta, tana cikin wanka taji Kiran magriba hakan yasa ta d'aura alwala kana ta fito daure da towel a jikinta, mai ta shafa a jikinta sama-sama sannan ta saka inners hadi da riga da skirt na atamfar ta mai saukin kudi, dama ita ba gwanar Kwalliya bace, hakan yasa ta saka hijab dinta ta tayar da sallah...
*8:01pm*
Tana iddar da sallah'n isha ta fito domin zuwa dakin sa, ko ina shiru ba motsin kowa, a hankali ta nufi dakinsa, ta kama handle din ta shiga,
hango shi tayi a zaune idaunsa a Lumshe, girgiza kai tayi irin na tausayin nan ta shiga serving dinsa, sannan ta mika masa, karba yayi kamar dazu yayi addu'a sannan ya fara ci, lomar farko ya Lumshe idaunsa, saboda wani mugun dadi daya ratsa kwanyar sa, sosai yaci fiye da rabi kana ya ajiye, mango juice din ta siyaya ta bashi ya shanye, yana tand'e baki daya sa Aysha murmusawa a 6oye, Abraham kuwa a ransa yana yaba iya girkin ta, domin tun daga lokacin daya fara dandana girkin ta yaji cewa bana biyun ta a iya girki.
Aysha kuwa sai daya gama ta dauki plate mai dauke da ragowar abincin sa ta cinye ta kora da juice, a ranta tana jinjina karfin halin ta na yau, domin ko giyar wake ta sha bata isa cin Abinci a waje daya da Abraham ba, bare daga kwanon daya ci, matuk'ar madam gloria na nan, tana zaune a dakin shiru, sai goman dare ta koma dakinta ta kwanta...
Washegari da misalin karfe goma anty Bintu ta zo gidan, inda take sanar wa Aysha cewa gobe zata je gombe, amma kwana biyu zata yi ta dawo, tafiyar gaggawa ce ta taso mata, idan
Aysha nada sako ta kawo a kai wa Inna, domin yanzu haka kasuwa ta nufa...
Ai magiya Aysha ta fara yi cewa zata bi ta, dama tayi kewar su Inna, Anty bintu tace Sam bazata bi ta ba...
"waye zai dinga yiwa su madam girki? Indo kin San cewa aiki na wahala a wanna zamanin yanzu ko? Karki yi wasa da aikin ki fa"
Cikin sauri tace "wallahi Anty bintu madam bata gida, tayi tafiya kuma bata fadi ranar dawowar ta ba, dan Allah Adda muje zan biki, ai kwana biyu zaki yi, har mu dawo ma nasan bata dawo ba" Indo ta fada cikin marairaicewa ba tare da tunanin cewa akwai wanda yake matukar bukatar kulawar ta a yanzu ba, saboda zumudin ganin su Inna da twins din ta....
Ban wani yi editing sosai ba, idan kun ga typing error kuyi 🙏
*ko ina madam gloria ta je Readers?*
Muje zuwa...
Share fisabilillah
Comment for more typing
NoorEemaan
07082281566
Thursday, 3 March
7:36pm
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 37-38
Ganin tarin damuwa da hawayen da suka cika idanun ta yasa Anty Bintu ta sauke ajiyar zuciya hadi da cewa "toh ya isa, zamu tafi tare, amma Karki manta kwana biyu kacal zamu yi, kar mu tashi dawowa ki ce min baki San zance ba" anty bintu ta karasa tana mata hararan wasa.
Ihun murna Aysha tayi ta rungumi Anty Bintu kana cikin farinciki da wani kwarin guiwa ta mike da gudu hadi da fadin cewa "anty Bintu ki jirani bari na dauko kudi muje kasuwar tare"
Murmushi hadi da girgiza kai Anty bintu tayi tana bin bayan ta da kallo.
Aysha tana shiga dakin kuwa ta d'auko kudin albashin ta, rabawa tayi biyu duk da bata San ko nawa bane, kana ta zuro hijab dinta ta kara saukowa da gudu, anty Bintu ta Mike ganin ta taho , da haka suka nufi kasuwa inda a motar gidan da Bintu ke aiki suka tafi, hakan kuma umarni ne daga hajiyar gidan....
******
Sosai Aysha tayi siyaya, ta siyi kayan sawa wa su Anwar kala uku masu saukin kudi kuma iri daya, ta siyawa Inna atamfa da hijab hadi da takalmi flat, sai kayan Abinci hadi man shafawa na yara, da nata da na Innah duk ta Siya, sai man goge baki(toothpaste) da sabulu, har da spices sa veges ta siya wanda tace zata musu had'add'en girki da zaran ta isa gombe kamar yadda tayi wa Innah Alkawari, anty Bintu dai sai dariya take mata domin zallan zumudi yasa Aysha ke siyan ko me ta gani, sai da kudin hannuna ta suka dawo saura dubu uku sannan idanunta suka washe ta hakura hakan nan...
Kallon Anty Bintu tayi cikin marairaicewa tace "Anty Kinga Wai kudin hannuna har sun k'are, ni dana ce zan siya mana kananun wayoyi ni da Inna ta" ta fada, ta na zumburo baki kamar wani ne ya sata siyayyar dole.
Dariya Anty Bintu ta saki, "ho ho hoo Indo ba dai sakalci da yarinta ba, yanzu nawa kudin ki suka rage?"
Dan d'aga kanta sama tayi hadi da juya manyan fararren idanunta alamun tunani sannan tace "ina ji kamar dubu talatin ne, domin nayi siyayyar dubu talatin da bakwai"
"Na gane yanzu, a takaice dai kudin hannun ki saura 33 thousand ko?" anty Bintu ta fada.
"33! Menene 33 anty Bintu?"
Murmushi Bintu tayi tace " Toh dubu talatin da uku nake nufi"
"oho! Eh haka suka rage" Aysha ta amsa mata .
"toh bari na ara miki dubu tara anan, sai ki kara da dubu uku ki siya muku wayar ko yar dubu shida-shida ce, idan munje gida sai ki bani ko" anty Bintu ta karasa tana dafa shoulder dinta.
"yawwa Addah Nagode sosai"
Aysha tace cikin farinciki daya gagara buya a saman k'yak'yawar fuskar ta.
Da suka je wajen masu waya aka fito musu da kala uku, daya kirar techno, daya airtel, daya kuma bontel, aka fada musu price din, akwai ta 5,500 sai ta 7000 har da na 10k ma, anty bintu tace a basu airtel din dan 5,500 guda biyu, inda a nan suka siyi simcard a wani shagon register'n layi dake kusa da shagon wayar, sai da komai ya yi normal suka bar kasuwar Aysha sai murna take tayi keypad...
*****
Bayan sun iso Gate din gidan Aysha ta sauka, inda kayan da suka siya yake booth ba kuma za a fito dasu ba, tunda a ciki zasu tafi gombe, wanda hajiyar gidan ta ce a kai Anty Bintu a motar gidan ba sai taje tasha ba, hak'ik'a karamci da mutumcin hajiyar ya wuce misali.
Tunda suka dawo Aysha ta yi sallah ta sauka kitchen da wuri, inda ta dafa wa Abraham indomie da ya sha veges, hadi da kwai domin shi zai yi saurin dahuwa, ita gabadaya ta manta bai ci komai ba tun karin safe, Bayan ta gama ta zuba a plate ta rufe saman da wani plate din ta hau sama tana fatan kada yayi fushi duk da ba magana yake ba, har tana tunani a ranta cewa ko dai wanna cutar da yayi ya sa muryar sa samun matsala ne, domin Abin da matukar mamaki ace mutum kusan watanin Kenan baya ko gyaran murya bare ya kai ga furta wata kalma...
Zaro idanunta tayi sak'amak'on abinda ta gani, zaune yake kan gado ya jingina bayan sa bed din, a yanda yake zaune ba wanda zai taba tunanin cewa bazai iya tsaye kan kafafun sa ba, inda tunanin ta yafi bata cewa kila mai gadi ko wani daga cikin ma'aikatan gidan ne ya dora shi kan gadon...
Hada idanu suka yi tayi saurin yin kasa da kanta gabanta na tsananta bugu, saboda mugun jaa da kwayar idanun sa suka yi, ga jijiyoyin kansa da suka fito rudu-rudu.
A sanyaye da yanayi irin na tsoro ta ajiye abinci a gefen gadon, a hankali ta ciri murfin da ya rufe abinci inda k'amshin mai dadin gaske ya daki hancin sa, a hankali ya lumshe idanun sa, fork Aysha ta saka kan abinci ba tare da ta kalleshi ba tace "ga Abinci" duk da tasan cewa ba jin abinda tace yayi ba, amma bata da wani zabi daya fi tayi masa magana .
Sai dai ko motsi bai yi ba kusan mintuna biyar, a dame ta dago da idanunta masu kyalli ruwan hawaye ta kafe masa, a hankali ta kamo k'arfaffan hannayen sa a kokarin ta na bashi fork din, ya janye hannunsa da karfi, har hannun ta na buga fork din.
Mamaki tayi sosai, "me yasa yanayin sa ya sanja a yau, ko dan ban bashi abinci kan lokaci bane yasa shi fushi?" ta fada a ranta tana fashewa da kuka.
A fili tace "Dan Allah kayi......"
Katse ta ya yi ta hanyar daga mata hannu hadi da yi mata alamun ta fita ba tare da ya ko bude idanunsa ba...
Kamar Wacce kwai ya fashewa a ciki haka ta fice tana share hawaye.
Kan bed dinta ta fada tana kuka, daga nan ta fada duniyar tunani.
*ABRAHAM*
Sosai zuciyar sa ke suya, abubuwa da Dama sun cushe masa zuciya, yau kwana kusan uku bai ga Mummy ba, Matar da ke matukar bashi kulawa right from time amma Ashe fuska biyu ce da ita, Kenan maganganun daya ji tana fada rannan kafin hankalin sa ya gushe gaskiya ce, mummy tana so ya mutu, ya bar duniyar kan dalilin ta da bai sani ba, me yasa abubuwa suka taran masa lokaci daya haka, Aysha da yake jin motsin ta a kusa dashi amma yau tun safe bai sake ganin ta ba, ga kukan da ta fita tana yi yana taba sa matuka, Sam bai kamata yayi treating dinta haka ba, bai kamata dan zuciyar sa na zafi ya huce a kanta ta ba, ita din karamar yarinya ce mai tsananin kulawa da sanin ya kamata, basu hada dangi ba, basu hada addini, basu hada komai ba amma still tana kokarin kula dashi da dukkanin iyawar ta, "why did I make her cry" ya fada daga ta ciki yana cije lips dinsa, a hankali ya kai idanunsa kan noodles din, sannan ya kara kawar da kansa hadi da rufe rikitattun idanunsa, zallan damuwa, hadi da tsananin kewa ne suka yiwa zuciyar sa rubdugu...
_7:45pm_
AYSHA
A nutse ta iddar ta sallah isha kana ta Mike cikin sauri domin dauko Abinci ta bashi, saboda Sam bata so ya kara jin yunwa irin na dazu bare ya yi fushi da ita, domin tafi tunanin cewa barin sa da yunwa da ta yi ne yasa yake fushi da ita, Bayan ta isa kitchen ta dauko warmer mai dauke French fries hadi da chips sai wani had'add'en lemon k'wak'wa da madara da yayi Sanyi a jug kasancewar daga chest freezer ta jiro shi...
Bakinta dauke da sallama ta shiga dakin sa kamar yadda ta saba, gabanta na fad'uwa tana zullumin yanda zasu kwashe ta ajiye tray din kan gadon, inda idanunta suka sauka kan indomie daya sand'are, cikin rashin jin dadin ganin bai ci ko da loma daya ba, dauke indomie tayi daga kan gadon ta ajiye shi a kasan tiles.
"Ga...abin...cin...ka" ta fada cikin cracking voice da amon sa ke bayyana kukan dake son kwace mata...
Shiru babu Amsa bai kuma Bude idanun sa ba, a hankali ta sa dan knife ta yanki French fries din ta tura masa a bakin har yatsun ta na gogan miyau sa, a hankali ya shiga taunar French fries din
farinciki ya cika zuciyar Aysha, ware idaunsa da suka Dan fad'a ciki yayi ya watsa mata su, alama tayi masa da ido kan ga Abincin sa yaci, yayinda take langwabe kanta ba tare da San tana hakan ba.
Kamar karamin yaro mai jiran umarni ya dauki fork da knife ya shiga ci da sauri-sauri alamun ya jigata da yunwa, aysha kuwa zara-zaran yatsun ta masu dauke da ragowar Jan lalle a Farcen ta ta hade cikin na juna tana kallon sa da burgewa...
Yaci da yawa kana ya ajiye, lemon Aysha ta siyaya a tumbler ta mika Masa ya sha sosai har yana lashe baki, ajiyar zuciya mai tattare da farinciki ta saki ganin yaci Abincin.
Bayan ya gama tattara wajen tayi ta fita da kwanukan, ya bi bayanta da kallo kana ya Lumshe idanun sa...
Aysha kuwa ta cinye ragowar Abincin a kitchen ta wanke warmers din da plate hadi da jug ta mayar da komai a muhallin sa, har ta nufi kofar barin kitchen din ta tsaya cak! Saboda tunanin daya ziyarci k'wak'walwarta...
"tabbas ya kamata na yi masa wani abun kafin na tafi kafa yaji yunwa, domin ba lallai madam ta dawo da wuri ba" ta fada a sanyaye, tana ji kamar karta tafi saboda ta bashi kulawa, amma idan ta tuno twins dinta da Inna sai taji ba zata iya fasa tafiyar ba...
Ingredients din yin cake duk ta fito dasu, kasancewar zaynab akindele ta koya mata wasu abubuwan daya danganci baking, k'waba cake din tayi cikin kasa da 30min, sannan ta zuba a pan mai dan girma ta saka a oven, bayan mintuna arba'in kamshi ya gauraya kitchen din, fito da cake din tayi bayan ta saka hankici (handkerchief) wurin fito dashi, sinken sakace ta cak'a a ciki ta ga bai manne a jikin sinken ba, gyara kitchen din tayi sosai ya dawo hayyacin sa
Bayan ta gama ta dauko wani tray mai oval shape ta kife cake din a kai, sannan ta yanyanka madaidaita sannan ta rufe da wani tray din, wanke cake pan tayi shima ta mayar domin bata son barin ko da cokali mai datti ne, domin anty Bintu tace mata 6:00am daidai ta fito...
***
A matukar gajiye take taka matatak'alar bene hannun ta rike da cake din, burinta yanzu ta samu tayi wanka ta kwanta, a hankali ta tura dakin sa ta shiga.
Yana kwance flat kan gado, numfashin sa na sauka a hankali da alamun ya samu bacci, gajiyayyun idanun ta ta zuba masa tana kallon sa, yayi mata kyau fiye da yanda yake yin kyau idan idanunsa a Bude suke.... Sai kuma tayi saurin d'auke kanta tana gargadin kanta da yawan kallon shi da take yi....
Kan wani center table na zallan glass ta ajiye cake din, daidai yanda ta san hannun sa zai isa, sannan ta dauko lemon 5alive guda hudu na kwali, ta daukar masa Swan water guda biyu sai cup, komai ta jere kan table din, har ta kai kofa sai kuma ta tsaya saboda tuno cewa bai San zata yi tafiya ba.
"Gashi ni ba jin turanci, shi ba hausa, bare na tashe shi"
ta fada tana shagwabe fuska, da tunanin bai kyautu ta tafi hakan nan bai sani ba...
"ya ilaihi! Ya zanyi yanzu?"
ta dora hannun ta a kugu cikin nazari, can kawai ta nufi wajen bed side, ta dauko wani memo da biro da ta gani tayi rubutu a kai kana ta yagi daidai inda tayi rubutun, duk da ta San ba iya karanta wa zai yi domin mutumin da bai iya hausa ba tayaya zai iya karantawa, amma zuciyar ta tafi aminta data bar masa wasikan da haka ta fita, tana zuwa dakin ta ta fada kan gado sai bacci saboda tsananin gajiya ko wanka bata samu ta yi ba, ko mintuna goma bata yi ba bacci mai cike da gajiya ya dauke ta...
Washegari
Saura kiris ta mak'ara sallah'n asuba a kagauce tayi wanka hadi da brush, ta saka kaya hadi da tada sallah, Bayan ta iddar ne ta yi karatu kadan saboda karancin lokaci, ita da take cewa zata masa breakfast kafin shida tayi gashi ta makara...
Abubuwan amfanin ta- ta dauka daidai na kwana biyun ta sauko da sauri ganin shida har da mintuna biyar, duk da taso leka Abraham amma gani take da zaran ta kara bata wasu mintuna Anty Bintu zata tafi ta barta...
Tana fitowa mai gadi yace "ah! ah!! Ayshatu ina zuwa haka"
"barka da asuba, zan je gida ne amma kwana biyu kadai zanyi, anty Bintu na jirana sai na dawo"
Ta fada tana fita da gudu-gudu sauri-sauri...
"ai kuwa naji horn a waje, toh a dawo lafiya Allah ya tsare" mai gadi ya fada ba tare da ya samu amsa ba, domin Aysha ta riga ta fada mota, har driver ya ja motar suka harba kan kwalta....
*_mu hade a next page mah people, banyi editing ba, may be akwai typing error, bacci sosai nake ji shiyasa.. wallahi da k'yar na gama wanna episode din._*
Share fisabilillah
Comment
NoorEemaan🦋
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
*WATTPAD*
@NoorEemaan
Chapter 39-40
(Not Edited)
Farinciki ya cika zuciyar Aysha, burin ta kawai ta ganta a garin su tayi tozali da twins hadi da Innar ta, ita gani take ma driver baya sauri saboda zumudi.
★★★
Da misalin karfe daya na rana suka isa kauyen su, inda ta kofar gidan su Aysha aka fara zuwa, cikin sauri ta balle murfin Motar ta fita, Anty bintu har ma da mai gadi suka fara dariya, cikin muryar dariya Anty bintu tace "Tsaya Indo! A ciro kayan nan, domin ni wucewa zanyi sai da yamma zan zo mu gaisa da Inna"
Ba dan taso ba ta tsaya tana shagwab'e fuska, driver ne ya fito ya fara fito da kayan Aysha yayinda Anty bintu ke fada masa kayan dake na iya Aysha, kafin kace me yaran layin har sun zagaye motar tare da fara dauk'ar kayan suna shigar wa shi cikin gidan, gabadaya hayaniyar su ta cika wajen
"Indon baffa liman ce ta zo" ...
Sai da Aysha ta ga an shigar da kayan ciki duka kana ta mara musu baya, tozali ta fara yi da Inna dake tsaye rike hab'a ganin yara nata shigo da kaya, murmushi mai taushi Aysha ta sakar wa Inna kana ta mayar da kallon ta ga yaran, dubu daya ta bawa babban cikin su tace "harisu gashi ku raba dari biyu-biyu" ta fadi hakan ne kasancewar dama su biyar ne.
Ihu na zallan murna yaran suka fara yi kana suka bar gidan a guje, da gudu ita ma Aysha ta fada jikin Inna da fuskar ta ke bayyana farinciki ganin tilon yarta a lokacin da bata zata ba, ita ma Inna hannu tasa ta rungume yarta "Inna ta nayi...." kasa karasa maganar tayi saboda hango twins da ta yi sun tsaya hadi da zuba mata ido, duk da cewa sun shaida ta, amma rashin ganinta na watanin biyun da basu yi ba yasa suke jin wani yanayi kamar bakunta a tare da su.
"y'ay'a na!" ta fada cikin zakin murya tana ware musu hannuwan ta, fuskar ta dauke da murmurshi tana yaba yanda suka girma a ranta, ai kuwa kamar jira suke suka nufe ta, hadi da Kiran "Ammuh!" dire guiwarta tayi a kasa tana jiran isowar su gareta, hannayenta ta rufe a lokacin da suka shiga jikin ta...
Aysha ta Lumshe idanun ta a lokacin data ji dumin su a jikinta, dago fuskar su tayi tace "nayi kewar ku yan biyu na sosai, ku fa kunyi kewar Ammuh?"
washe bakunan su yaran suka yi suna kallon ta, domin ba wai sun iya magana bane sosai.
"toh tashi ku zauna kan tabarma ko mai y'ay'a" Inna ta fada tana kallon su da burgewa.
Dariya Aysha tayi ta Mike, yayin da yaran suka mara mata baya, kowannen su ya kama rigarta ta gefe da gefe har suka zauna, domin a ganin su zata kara tafiya ta barsu ne.
Sai kallon su Aysha take, ta tallafi fuskar su hagu da dama tana kallon su, masha Allah kuma sunyi kyau Abin su kuma fess suke alamun Inna na matukar basu kulawa, fadin dadin da ta ji a ran ta ba zai misaltu ba.
Mikewa tayi ta dauro Alwala ta yi sallah a nutse, Bayan ta iddar Inna da kanta ta kawo mata dambun shinkafa daya ji gyada, zogale, hadi da man kuli na asali, babu abinda ke tashi sai k'amshi, lomar farkon da Aysha tayi ta Lumshe ido saboda wani mugun dadi daya ziyarci harshen ta, hak'ik'a ta yi kewar dad'add'an girkin Innar ta, hakan yasa ta mai yawa, ci bana wasa ba, wanda ta manta rabon da ta ci irin shi, su Ammar ma na taya ta ci.
Sai bayan la'asar suka kunce kayan da Aysha ta kawo ta bawa kowa nasa, su twins sai murna suke sunyi sabon kaya, Albarka kuwa ta sha shi cikin k'wando a wajen Inna...
Inna har kukan farinciki tayi saboda ni'imar da Allah yayi musu na sanjin rayuwar da suka samu.
*ABRAHAM*
Sai karfe goman safe ya fark'a daga bacci, a hankali ya Bude sleepy eyes dinsa, tarr ya ga rana ya shiga ta window'n dakin hakan ya tabbatar masa da cewa gari ya waye sosai, ya kuma yi mamakin dadewar da yayi a baccin, turo kofar dakin da aka yi, a tunanin sa itace, tsabanin haka mai gadi ne ya shigo.
Ajiyar zuciya Abraham ya sauke, domin kwata-kwata baya jin dadin jikinsa da ma bakinsa, ganin mai gadin yasa yaji dadi a ransa, kamar kullum gaishe da Abraham mai gadi Yayi, Abraham ya amsa da kai, da k'yar ya dora Abraham kan keken sa ya tura shi zuwa toilet, kana ya fito, mintuna goma kacal ya gama abinda yake, mai gadi ya kara turo shi waje yace zuwa yamma zai zo kwantar da shi kana ya koma bakin aikin sa da gudu, domin dabi'ar sace baya abu a hankali...
Bayan fitar sa Abraham ya Bude idanun sa, ya fesa numfashi mai dumi daga bakinsa, inda ya shaki k'amashin toothpaste din daya wanke baki dashi a hancin sa.
Rashin ganin ta yasa shi jin wani iri ba dadi a ransa, wanda shi kan sa bai fahimci hakan ba, a hankali ya kai kallon sa inda ya ga drinks da wani tray a rufe, a hankali ya tura kansa ya bude tray din, kana ya sake rufewa.
Idanun sa ne suka sauka kan farar takarda, a hankali ya kai hannu ya dauka, ganin yanda rubutun ta yayi wani iri a wargaje kamar na yara masu koyon rubutu ya bashi nishadi, for the first time murmushi ya subuce masa, a ransa yace
"what on earth did this hausa girl wrote?"
ya fada a ransa domin shi dai bai fahimci ko da kalma daya ba, amma hakan nan yake son sanin abinda da ta rubuta, sai a lokacin wayoyin sa suka fado masa, tun bayan da aka sallamo shi daga asibiti bai gan su ba, bai kuma damu ba.
Akwai wata karamar wayar android dinsa da bai fiye abinda da ita ba, a hankali ya turo keken ya zuwa inda yake ajiye ta, tare da fatan ya ga wayar, kasancewar drawer bai da tsayi ya kai hannun sa ya ja shi, ya kuwa hango wayar, a hankali ya ciro shi, ya kunna, 30 percent ya gani, numfashi ya sauka ganin akwai 600mb, goggle ya shiga , ya yi searching Abin translation daga hausa zuwa turanci domin ta hakan ne zai fahimci abinda ke jikin takardan, ya fara typing a wayar, da k'yar yake gane rubutun.
"Assalama alaykum ina kwana, kayi hakuri ban sanar mana ba, na je gidan mu garin gombe domin ganin mahaifiyata da yan biyuna, kwana biyu kacal zan yi in dawo, nazo gayamaka jiya amma kayi bacci, yallabai Allah ya kara maka lafiya, sai na dawo"
A hankali yake murza takardan cikin hannunsa bayan goggle ta fito masa da translation din, duk da har ransa yaji ba dadi na rashin ta a gidan, amma kalaman ta na karshe ya bashi dariya matuka
"she has twins, really? “
ya tambayi kansa unbelievable yana murmushi da iyakar lips dinsa ne suka nuna, sosai Aysha ta bashi dariya daga short note din data ajiye masa...
Gabadaya baya jin dadin gidan, sai misalin karfe Daya yaci cake din yanka daya da lemo domin gabadaya baya da apatite, Abu kadan ya kai idon sa ga kofar, har gizon shigowar ta yake gani a idanun sa.
Bai tashi sanin cewa ya shaku da Aysha ba duk da ba magana ke hada su ba sai yau, hakika ko wani Dan Adam komai kankantar sa yana da amfani, ko da dabba ne, bare mutum mai daraja, a yau ya yarda da wanna maganar, haka ya wuni suk'uk'u gwanin tausayi.
*MADAM GLORIA*
Kwara State
Zaune take a wani kusurmin daji kan wani dutse da bai kai kasa ba, sannan shi ba a sama yake ba, ta saka wasu jajayen kaya yayinda aka zama mata wasu abubuwa a ciki da farin alli, duk da cewa ba wanna bane karon farko da take zuwa wurin bokaye amma tabbas ta tsorata da wanna bokan, domin hatsabibi ne sosai, kwanan ta biyu kan wanna dutsen ba tare da ta sauka ba, ko ta motsa ba, tamkar Wacce aka datsa, jajayen kayan jikin ta sai ji tayi an saka mata su ba tare da ta ga kowa ba, haka zalika abubuwa da aka zana mata a jiki, duk da cewa ta jigata da zaman amma kudurin da take da shi wurin son aiwatar da mugun nufin ta kan bawan Allah Abraham ke kara mata karfin guiwar cewa zaman ta a nan na dan lokaci ne...
Tana a haka wani mumunan halitta da tsayin sa bazai misaltu ba ya bayyana a gaban ta, har hakan ya firgita ta.
Hakoran sa, idanun sa da faratan sa sun fi komai muni a hallitan jikin sa, a hankali ya shiga zagaye madam Gloria yana mata wani kallo shi ba harara ba gashi nan dai, sosai jikin ta ke rawa, kamar Wacce aka warware mata jiki, ta budi baki da niyyar magana amma ya daga mata katoton hannunsa masu dauke da yatsu takwas, kana cikin Murya mara dadin amo yace "na San meke tafe dake, kuma kin zo wurin da za a share miki hawaye, matukar kike bi umarnin da zan gindaya miki, akasin haka kuma zan jefa rayuwar ki a mumunan yanayi da zaki gwanmaci mutuwar ki da Rayuwar ki a doron kasa"
ya karasa a tsawace, wanda hakan ya girgiza bishiyoyin wajen kana amon muryar sa ta amsa kuwwa.
Cikin rawar murya madam tace
"z...zan...bi duk umarnin da ka bani"
Dariya ya shiga k'yak'yatawa har na tsawon mintuna goma, yana yi wa kan sa kirari da wasu manya-manyan kalmomi, sai kuma ta ga ya bace bat, sai sautin dariyar sa dake cigaba da tashi duk da cewa baya nan, sai jin Murya tayi yana cewa "kamar yadda na fada miki, zamu kashe shi kamar yadda kike bukata, sai dai ki wayi gari ki ga gawar sa, babu Mai zargin ki matukar kika yi amfani da abinda zamu baki hhhhhhhhhhhhhhhh" dariya mara dadin sautin ya cigaba da tashi babu k'ak'autawa.
AYSHA
Dare ya tsala amma bacci ya kasa ziyartar idanun ta, Kwance take kan gado yayin da twins ke jikin ta a manne, kura wa fuskar Ammar ido tayi ta cikin hasken farin watan daya shigo ta window, tana gani kamar Abraham take kallo, musamman yanzu da ta dawo taga sun kara girma sai taga kamanin su ya dada fitowa, numfashi ta sauke hannunta kan gashin Ammar tana shafawa tana mamakin wanna kamanin nasu, Lumshe kyakyawa idanun ta tayi hoton fuskar Abraham kawai take gani, tabbas tayi kewar sa ba kad'an ba, tuno lalurar sa yasa hawaye suka cika idanun ta har suna biyo gefe da gefen kunnen ta...
"WAYESHI"
tayi wa kanta tambayar a karon farko, sosai kuma zuciyarta ta kwadaitu da son sanin waye shi, me yasa baya farinciki kamar kowani dan Adam, wacece madam Gloria a garesa domin ta kasa yarda cewa ita ta haife shi amma ace babu tausayi da jin kan uwa ga yayanta.
"ZAN TAMBAYESHI"
ta fada a saman labb'anta, sai dai rashin jin yaren juna da basa yi yasa jikin ta yin Sanyi har akan ya nuna kan fuskar ta, ta jima cikin tunani kana bacci ya dauke ta.
WASHEGARI
Bayan ta tashi da sassafe ta taya Inna aikin gida, sannan tayi musu abincin yan gayu kamar yanda tayi musu alkawari.
Bayan ta gama ta zubawa kowa, Inna da su twins sai santi girkin suke, Anwar da ya fi surutu cikin gwarancin sa yace "Inna! Ammuh ta fi ki iya giyiki(girki)"
Dariya suka yi kawai, sai da Aysha ta yi wanka ta zubo abincin, ta dibi loma daya zata ji sai maganar sa da hoton fuskar sa ta fado mata a rai, "ko ya ci abinci" zuciyar ta ta nemi sanin amsar da babu wanda zai bata"a sanyaye ta mayar da Abincin kwano cikin damuwa, ganin inna na kallon ta yasa ta daure taji spoon biyar ta ajiye, domin kwatata bata jin yunwa yanzu...
Bayan ta ajiye Abincin inna tace "zo nan Indo"
A sanyaye ta zauna zusa da inna, su twins kuwa na ta aikin jagwalgwala wayoyin inna da aysha.
"me ke damun ki ne?“
Cikin raunin murya tace
"babu komai Inna"
"ban gane babu komai ba, kar dai ki manta ni mahaifiyar ki ce, shin akwai damuwar da zaki boye min, amma idan kina ganin ban isa ba shikenan, tunda kina ganin kin girma da gaya min matsalolin ki" ta fada da yanayi fushi, domin ta San logon yarta bata kaunar fushin ta.
Ai kuwa cikin sauri Aysha ta kama hannu Inna tace "wallahi Inna kin isa dani, kiyi hakuri, kawai na damu da....."
Sai kuma tayi shiru ta tsunkuyar da kanta tana tunanin yanda zata sanar da Inna cewa damuwar ta Abraham ne, ta yaya zata dauki abun, me hadin su, anya bata tsawwala da yawa ba kuwa?
Boyayyen ajiyar zuciya ta sauke tace, Inna ta kalli yarta tsaf tace" uhmm gaya min menene,
waye shi? “
"Inna....dan Matar da nake wa aiki ne, kwanaki Dana kai masa abinci wanda ni na dafa da kaina...." daga nan dai ta shiga bawa Inna labarin daya faru da Abraham, shiru Inna tayi tana nazarin maganganun cikin hikima.
Labarin ya bata Inna sosai, kallon Aysha tayi tace" anya babu wanda ya saka guba cikin Abincin da kika girka masa kuwa? "
"Guba!" Aysha ta maimaita cikin zaro ido.
"kwarai, daga labarin da Kika bani na fahimci hakan, ina tsoran wanna Mahaifiyar tasa, akwai wani Boyayyen almari a tare da ita, ki iya takun ki da ita Dama kowa na cikin gidan, ki dage da addu'oi' sannan ki rike azkhar din safe da maraici, in sha Allah zai tsare ki da sharrin masu sharri har ma da mugaye, akwai wasu magunguna da baffan ki ya taba yiwa wani mutum mai shigen irin lalurar shi wanna mutumin, zan Baki shi, sai ki jika ki bashi ya dinga sha, zan miki bayanin yanda zaki yi amfani dashi, in sha Allah za a dace"
Numfashi mai fita da relief Aysha ta saki cikin jin dadi, har hakan yasa ta ware suka cigaba da hirar su da Inna, sannan sun sha wasun su da twins har take ji kamar kada gobe yayi...
Washegari da sassafe anty bintu ta shigo gidan inda ta tarar da Aysha a shirye tsaf, zaune take kusa da inna tana kukan rabuwar da zata yi dasu, Allah yaso su twins na bacci da abubuwan sun kara kacamewa.
Da kuka tana komai Allah suka dau hanya, Inna ta bi su da adduar sauka lafiya.
*12:40pm*
Daidai na rana suka shigo garin kaduna, kasancewar kayan aysha ba yawa kamar lokacin da za su tafi yasa a bakin gate ta sauka da kayan hannun ta, inda kuma su anty bintu suka shiga nasu gidan da suke aiki...
A mutunce suka gaisa da mai gadi, kana ta shiga gidan, falon shiru kamar ko yaushe, sai k'amashin air freshener na lavender da ke tashi...
A hankali ta nufi upstairs da kayan ta ta ajiye, kana ta cire kayanta ta daura towel daya tsaya iya cinyar ta, ya kuma bayyana madaidaicin hips dinta mai kyau da tsari, bata hims ba ta fito bayan ta daura alwala, ko mai bata shafa ba saboda zafi ta zira doguwar Riga bayan ta saka inner wears, sallah tayi hadi da addu'a, sannan ta Mike ba tare da ta cire hijab din ba ta nufi dakin sa, domin zuciyar ta sai azazalar ta take da son ganin sa.
_ban nutsu nayi editing ba, kila kuga typing error, sannan meye ra'ayinku kan wanna page din_?
Share fisabilillah
Comment for more typing...
NoorEemaan
07082281566
Thanks for reading my story 🍇ABRAHAM 🍓
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
Written by
NoorEemaan
WATTPAD @NoorEemaan
https://facebook.com /groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 41-42
A hankali ta tura kofar dakin sa ta shiga, idanun ta a Lumshe tana fatan ganin sa cikin kyakyawar yanayi.
cikin yanayi mai kama da fargaba ta shiga bud'e idanun ta...
Idanuwan su ne suka fada cikin na juna, tamk'ar dama jiran isowar ta Abraham yake, domin idanun sa na kallon kofar ne.
Kara Lumshe Idanun ta tayi, wani irin farinciki sosai take ji daga kasan zuciyar ta na ganin yana cikin koshin lafiya, a hankali kamar yadda ta saba tayi sallama kasa-kasa, duk da cewa tasan bai San ma'anar abinda ta fada ba bare ya amsa, amma ta saba yin sallama a duk inda ta shiga.
A hankali ta shiga takawa zuwa gare shi, zuciyoyin su na bugawa a tare, the more tana kara kusanta shi, the more zuciyar su ke kara bugawa a tare.
Kasa ta dire guiwowin ta tana jin yanda idanun sa ke yawo a jikin ta, sai ta kasa gaishe shi kamar yadda ta yi niyya, tattausan murmushi ya saki da har sautin sa ya fito saboda tuna cewa Wai tace tana da yan biyu, ta ya ya? Shi kam bai yarda ba, domin duk wanda yayi wa yarinya mace kamar ta aure a wanna kananun shekarun nata anyi mata child abuse a cewar sa, dauke idaunsa yayi daga kanta yana jin sanyin a ransa saboda ganin ta dawo.
Cikin sauri Aysha ta dago, jin sautin murmushin sa, tayi mamakin hakan domin abu ne wanda yake bako a gareta, "Dama yana murmushi?" ta fada a kasan mak'oshin ta.
Haka ta cigaba da zama a wajen tamk'ar Wacce aka dasa, ta ma kasa tashi, a hankali ta Mike ta shiga gyara dakin sa da ya d'an yi kura kadan, komai tana yi ne a tak'ure saboda idaunsa dake yawo a kanta, a ranta tana gulmar yaushe ya koyi kallo haka...
Bayan ta gama ta sauka kasa da tray din cake din da ba wani abun kirki yaci ba, tausayin sa ya kamata domin ta San ba karamin yunwa ya ji ba, yanka daya taci da lemo ta kai wa mai gadi ragowar, ya dinga godiya yana washe hakoran sa.
Kitchen din ta dawo, ta gyara, sannan ta kunna gas ta dora ruwa, duk da ba ta san actual abinda zata girka ba, dakin madam Gloria ta nufa da sauri domin ta gyara kafin ruwan ya tafasa, sai dai turin duniya tayi wa kofar taki budu wa, hakan ya tabbatar mata da madam Gloria ta rufe abin ta, kitchen ta dawo tana mamakin Wai wanna Wacce irin uwa ce, da bata tausayin danta, a hankali kalaman Inna suka Shiga dawowa kunnen ta, numfashi ta ja, abinda ya kamata ta girka take tunani, a hankali dad'add'an dambun Inna da ta ci ya dawo brain din ta, wani yawu ta hadiya saboda tuno dadin d'and'anon dambun.
Sai kuma ta bata fuska tace "gashi babu zogale da gyada, amma zan girka da su karas, Koren wake, da hanta" ta fada wa kanta a bayyane kana ta shiga hada dambun ta.
Sai daf da magriba ta gama domin har da cocktail drink ta hada masa, k'washe dambun a warmer tayi, kana ta dauki juice din dake cikin fridge ta nufi sama domin ta daina barin Abincin da zai ci a kasa saboda har yanzu bata San waye mai cutar da Abraham ba, gwara ta kiyaye ta kuma iya takun ta kamar yadda Inna ta fada mata.
Tana iddar da sallah'n isha ta nufi dakin sa domin serving dinsa.
Yana zaune idaunsa na kallon bakin kofar, ta shigowa suka hada ido, saurin dauke kanta tayi ta shiga serving dinsa, sai a lokacin tayi tunanin anya zai iya cin dambu? Tunda dai baya daga cikin cimmar su, musamman ma yaren su ta igbo, addu'ar ta daya Allah yasa ya yi masa dadi har ya iya ci da yawa.
A hankali ta shiga serving din sa hannuta na dan rawa saboda kallo ta da yake yi, Bayan ta gama ta dora masa abincin kan cinyar sa, numfashi ya ja a boye ya mayar da idanun sa kan abincin, ya bi abincin da kallo a ransa yana mamakin meye wanna?
Ganin irin kallon da yake yiwa abincin yasa ta dauki wani spoon daga tray din ta dibi loma daya ta kai bakin ta, sannan ta Lumshe ido hadi da cigaba da tauna, sai da ta taune ta bude idanun ta hadi da yi masa alamar yaci akwai dadi, kamar karamin yaro mai jiran umarnin ya dauki spoon ya dibi kad'an ya d'and'ana, dadin da ya ji a harshen sa yasa shi fara ci bana wasa ba, tausayi ya bawa Aysha domin yanayin sa ya nuna cewa yana jin yunwa matuka, sai da ya ci rabi ta zuba masa cocktail juice din ya sha yana lashe lips din sa, kallon sa Aysha take da gefen ido ba tare da ta bari ya ganta ba.
Bayan ya gama ta fitar da plate din ta dawo, ta share inda ya dan bata kad'an.
Ta mike domin tafiya, har ta dora hannu a handle din kofa ta ji gyaran muryar sa, cak ta tsaya hadi da juyowa domin tun bayan da aka dawo dashi daga asibiti bata kara jin ko da tarin nan yayi ba banda da zu da yayi murmushi mai sauti, tsayawa tayi tana kallon sa, inda zuciyar ta ke bata cewa wani Abu yake bukata shiyasa yayi gyaran murya, hannu ya daga ya yafutota, cikin nutsuwa ta kara so ta tsaya a gaban sa.
"Sit"
Ta ji yace cikin karamin sauti yana dan buga kan gadon sa, ba musu ta zauna tana jin ta a takure, a hankali ABRAHAM ya juyo da keken sa, sai ya zamana suna facing din juna, ajiyar zuciya ya sauke, yana so yayi mata godiya bisa kokarin da take yi wurin kula dashi, domin samun kamar ta sai an tono, ya sha jin labari da ganin yadda wasu muslimai musamman hausawan mu da suke nuna bambamci ga chiristian ko nuna kyama, ko wariya a garesu, wanda hakan bai kamata ba, ko wani dan Adam yana da daraja, dan mutum ba Muslumi bane babu dace wa ka ce masa wai
WANNA ARNE NE, KO DUK ARNAYE WUTA ZASU SHIGA WUTA.
*(Subhanallah! Wane mutum da zai yanke wa bawa hukunci, Allah kadai ke da wanna ikon, sannan dukkanin mu Allah muke bautawa, addini ne ya bambamta mu, ba a shiga tsakanin bawa da ubangijin sa, kar mu yanke hukunci ga ko wani bawa, komai laifi da kuma tarin zunuban sa, dan haka matukar mun ga mutum chiristian ne Kar mu nuna kyama a garesu hakan zai sa su san cewa addinin musulucin addinin zaman lafiya ne da kaunar juna, wanda har hakan zai iya sawa su yi kwadayin shiga Muslunci Allah yasa mu dace)*
"Thank you for everything, i really appreciate your efforts, God bless you"
A hankali ta dago kanta dake maiko, sakamakon ruwan hawaye daya taru a ciki, domin ita kam bata fahimci abinda yace ba.
Fahimtar hakan yasa Abraham bud'e tafin hannu sa, take farar takardan da ta yi rubutu a kai ya bayyana, cikin rashin fahimta ta zuba wa soft palm din sa ido, furzar da numfashi yayi, domin zai sha ciwon kai saboda ba jin yaren juna suke ba, wani tunani ne ya fado ransa, hakan yasa shi tura keken sa zuwa gaban drawer ya dauko memo da biro hadi da wayar sa dake kan memon ya dawo.
Play store ya shiga ya yi searching App din translation daga turanci zuwa hausa, take aka fito masa da su da yawa ya zabi daya ya yi installing kana ya shiga typing turancin da yayi mata...
babu jimawa aka fito masa da fassarar, yayi copying a memon ya dora mata kan cinya, a hankali ta kai idanun ta kan kyakyawar rubutun sa mai kyau da tsari.
"Nagode sosai da komai, na yaba da kokarin ki, Allah yayi miki Albarka"
karo na uku kenan da ta maimaita rubutun cikin ranta, a hankali ta dago tana masa kallon zallan mamaki wanda hakan ya kasa buya a saman fuskar sa "Dama ya iya hausa?" ta fada a ranta.
Ya karanci hakan ta fuskar ta , hakan yasa shi dago mata wayar, yana mata alamun daga nan ya rubuta, murmushi tayi tana sunkuyar da kan ta.
A memon ita ma ta rubuta
"Bakomai, kar ka damu."
Ta mika masa, karba yayi ya shiga typing abinda da ta rubuta, dama already ya sauke App din translation daga hausa i zuwa turanci tun ranar da Aysha ta tafi gombe...
ya shiga typing, bayan ta gama app din ya fito masa da amsa kamar haka...
"it's nothing, never mind"
Hakan nan yaji baya so ta tafi, so yake hirar kuraman ta su ta cigaba, a hankali ya rubuta da turanci
"is it true that you gave birth to twins as small as you re?"
Bayan fassaran ya fito ya rubuta ya mika mata, murmushin daya Bayyana siririyar wushiryarta tayi, saboda tuno lovely twins dinta, ga kuma kalaman sa da suka bata dariya wai ita karama, a hankali ta kara karanta abinda ya rubuta,
"da gaske ne cewa kin haifi yan biyu duk kankantar ki?"
Amsa ta bashi da "Eh! da gaske ne, ina da yara maza biyu, suna wajen mahaifiyata"
Bayan yayi typing fassarar ta fito da masa da amsa kamar haka "yes! It's true I have kids, two boys, they are with my mother"
Jinjina kai yayi, yana mamaki wanna abun, kamar ta ace tana da yara, sai yaji wani iri ba dadi, shi a ganin sa iyayen ta sun cutar da ita.
Aysha kuwa ta zabi boye wa ko ma waye gaskiyar lamarin domin ba ta so ko da wasa su Ammar su tashi su San cewa ba ita ce ta haife su ba har akan ya shafi rayuwar su, bata so suyi kukan maraici, ko a ina ne zata fada, idan ma aure zata yi sai ta fada wa Mijin da zata aura cewa tana da yara.
*ABRAHAM*
Sai after 11 yayi mata alamun taje ta kwanta, a hankali ta tashi ta fita, yabi bayan ta da kallo, numfashi pya sauke yana jin wani yanayi na musamman daga gareta, wanda har yanzu ya kasa gane ko na menene, domin Sam tunani da k'wak'walwar sa basu taba bashi cewa wata kalma ta SO zata shiga tsakanin su ba.
"amma meyasa na damu da rashin ta kusa dani?" ya tambayi kansa, sai kuma ya kau da tunanin daga ransa, kan wheelchair ya cigaba da zama har bacci ya dauke sa yana jin gab'obin jikin sa na masa ciwo, saboda zaman da ya jima yana yi a waje daya.
*(lafiya babban jari inji masu iya magana. Da Abraham na da lafiya yanzu zai tashi ya kuma kwanta a duk lokacin da yake so ko da babu mai taimaka masa, shiyasa komai da mutum zai yi maka ba zai taba zama yanda zaka yiwa karan kan ka ba, Allah ka wadata mu da lafiya)*
*BAYAN KWANA UKU*
Tsaye Aysha take a gaban sif dinta bayan ta fito daga wanka, Riga da skirt na wani lace din ta mai saukin kudi ja hadi da touches din fari a jiki ta sanya kana ta saka wani madaidaicin farin hijab mai roba, as usually fuskar ta fess babu ko digon make up, zata rufe sif din Kenan idanun ta suka sauka kan Ghana most go din ta mai dauke da photo album dinan, a hankali ta kai hannu da niyyar budewa domin ta ga abinda ke ciki, har ta fara zuge zip din taji horn daga bakin gate, mayar da zip din tayi ta rufe kana ta nufi window din dakin ta cikin sauri ta zuge, domin iya sanin ta dai babu bai shigowa babu kuma mai fita a mota tunda Abraham ba lafiya gare shi ba, Wacce ta gani ta fito daga mota ne ya sanya gaban ta fad'uwa fiye da ganin farkon da ta fara yi mata tun zuwan ta na farko gidan.
_Idan ina free gobe zaku iya ganin update_
Share fisabilillah
Comment
Vote
Thank you for reading my story #Abraham
NoorEemaan
07082281566
2:33pm
Saturday 12, 2022
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM 🍓🍓
*First edition*
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 43-44
"MADAM!"
Ta fada cikin cracking voice tana jin wani irin tashin hankalin sak'amak'on ganin ta, hakan nan taji rashin nutsuwa da ganin ta.
"ya Rahman!" ta furta a fili hadi da dafe kirjin ta dake bugu da sauri - sauri...
A sanayaye ta fito daga dakin ta, wani bangare na zuciyar ta na mata fad'an cewa "Aysha me kike yi haka ne? Mata da gidan ta amma kina jin rashin dadin ganin ta, bayan ita ce dalilin kawo ki wanna gidan"
Numfashi mai dumi ta furzar Kamar zautaciyya a fili tace "na sani, nima na san abinda nake ji a raina bai dace ba, amma na kasa sarrafa zuciya ta, ban San meya sa ba"
ta karasa kamar zata saki kuka, domin har ranta tana son daina jin wanna yanayin amma ta kasa.
Dakin madam Gloria ta nufa domin gaishe ta, saboda rashin zuwa gaishe'n ta kan iya janyo wata matsala da bata San abinda zai haifar ba...
A hankali ta shiga k'wank'wansa kofar tsahon mintuna hudu kana madam Gloria ta bud'e kofar, hadi da tsare hanya, kamar yadda zuciyar ta yake baka haka fuskar ta yake, Sam babu alamun fara'a bare Imani.
Cikin tsora da Aysha ke k'ok'arin boyewa ta dan russuna alamun girmamawa tace
"Madam ina kwana, Sannu da dawowa ya hanya?"
"Lafiya" Madam Gloria tace a dak'ile hadi da bango kofa, wanda hakan ya sanya Aysha firgita.
A sanyayye ta juya ta koma sama, tana jan Numfashi, saboda wani karni-karni da wari-wari da madam Gloria ke yi a lokacin da ta fito, inda har yanzu warin bai bace ba, sai ma yanzu ta tuno da maganin da Inna ta bata tace ta hada wa Abraham.
Madam Gloria kuwa lock ta saka wa kofar, domin a halin da take ciki bata kaunar ganin kowa har sai ta cimma ma burin ta, ga wani mahauk'acin tsanar Aysha da ta kara ji yanzu da ta ganta.
Wata bakar leda dake kan gado ta dauko a hankali, cire ledar tayi, inda wata madaidaiciyar k'warya ta bayyana, an zagaye k'waryan da Jan kyalle, murfin
K'waryan ta bude inda take wani hayaki ya fito, sai wani abu kamar kwallo karami mai tsakanin haske kamar an saka k'wan lantarki a ciki yana ta birgima cikin kwaryan.
Murmushin zallan mugun ta ta saki, tana mai rufe murfin, kasan gado ta mayar da k'waryan, kana ta nufi bathroom domin yin wanka, saboda ita kanta tana shak'an warin dake fita a jikin ta, wanda baya rasa nasaba da jimawar ta a garin kwara da kuma aikin da bokan ya gudanar a kanta, domin wasu abubuwa da bata San ko meye ba yake ta watsa mata a jiki...
AYSHA
Bayan ta dauko duk abinda Inna ta bata inda yake cikin Wata leda ta hado da qur'ani kana ta nufa dakin sa, Bayan ta Bude kofar ta jingina kanta da kofar tana kallon sa, duk da shi ma ita yake kallo amma a yau ta kasa janye idanun ta domin wani mugun tausayin sa take ji a ranta wanda bata taba Jin kamar sa ba, ajiyar zuciya ta sauke bayan ta karasa shigowa cikin dakin, ajiye jakar bakon tayi kana ta nufi kitchen dinsa inda yaune karon farko da za a fara amfani dashi, ta kuma zabi hakan ne saboda bata son madam Gloria ta ganta.
Ta San kowacce uwa da danta ke fama da irin wanna lalurar zata yi farinciki idan aka ce yau ga wani magani a jarrraba masa, ko wata hanya ta samun lafiiyar sa, amma ita kam zuciyar ta yafi kwanciya kan ta boye mata, ba tare da ta San dalilin hakan ba.
*ABRAHAM*
Da kallo ya bi Aysha yana ganin yanda fuskar ta ke bayyana damuwa. "what's wrong with her?" ya tambayi kansa, sai kuma ya Lumshe idanun sa yana tsammanin fitowar ta domin ya tambayeta waya shigo ko ya fita kasancewar daga gidan, kasancewar yaji horn dazu.
Aysha kuwa electric cooker dake kitchen din ta jona, tukunya ta dauko ta dauraye, kana ta tari ruwa a ciki, ta sink din dake kitchen ta dora a wuta.
Kara fitowa tayi, ba tare da ta kalle shi ba ta dauki wasu magunguna kana ta koma kitchen...
Abraham kuwa ya bita da kallo yana mamakin meya sanja mood dinta haka.
*AYSHA*
Ta bata wasu mintuna kana ta fito da maganin cikin jug sai ta dora karamin cup a saman sa, gaban sa ta zauna ta zuba maganin daya d'an huci a cup ta mika masa, k'urawa maganin dake da kalar ruwan hanta yayi, yana mamaki ko meye wanna.
Idanun ta dake cike taf da ruwan hawaye da bata san ko na menene ba ta kura masa, ba tare da ta damu da ya ji, ko kar yaji ma'anar abinda zata fadi ba tace "ka sha Dan Allah! magani ne, Inna ce tace na baka domin samun lafiyar ka in sha Allah, ka yarda dani, bazan cutar da kai ba, bazan taba cutar da kai ba, ka sha Dan Allah kaji"
ta karasa cikin zubar hawaye hannun ta har k'ak'arwa yake wanda yasa maganin cikin cup din ya shiga rawa kamar zai zube, bata san meyasa yau raunin ta ya fito fili ba, ji take kamar tayi kuka sosai.
Tunda ta fara magana ya kurawa cute lips din ta ido, ko kalma daya bai fahimta daga maganganun ta ba, dadin amon muryata dake fita daki-daki hadi da dark pink lips din ta sune suka ja hankalin sa har ya kasa d'auke idanun sa daga kanta, amma abu daya ne, abu daya ne ya sosa masa zuciya ganin hawayen ta...
Bai kara bari zuciyar sa ta yi wani tunani ba ya zagaye hannun sa kan hannun ta dake jikin cup din, hakan yasa hannun ta ke kasa, yayin da nasa k'arfaffan hannun yayi wa na ta rumfa.
Numfashi mai tafe da shesheka Aysha ta saki, sakamakon taushi da dan Sanyi da tafin hannunsa ke dashi wanda ya ratsa har tafin kafar ta, hakan bai taba faruwa da ita ba, baya ga baffan ta, Abraham shine mutum na farko daya fara taba mata hannu.
Abraham kuwa a hankali ya zare hannun sa, sannan ya zari cup din daga hannun ta, without even a second thought ya kai cup din bakin sa, ya sani cewa bazata cutar da shi ba, yayi yarda da ita hundred percent, zargin da yayi mata a baya na tunanin cewa ko itace tayi poisoning din sa kuskure ne, zama waje daya da yake yawan yi da ita ya fahimci wacece ita da kuma dabi'unta, dan haka baya shakku a kanta ko kad'an, a hankali ya shiga sha yana yamutsa fuska saboda baurin maganin, amma haka ya daure ya cigaba da sha saboda da ita, domin a ganin sa idan bai sha ba kuka zata cigaba da yi.
Aysha kuwa ganin cewa ya karba ya sanya ta sauke Numfashi kana ta fito da wani madaidaicin Allo hadi da tawadda Ledan, wasu surori cikin Alqur'anin mai girma da Inna ta fada mata ta shiga rubutawa cikin k'warewa, Bayan ta gama ta ajiye qur'anin kan dayan drawer, tashi tayi ta shiga kitchen ta dauko wani bowl ta dawo ta zauna, zama tayi ta dauko ruwan zam-zam dake cikin ledan kana ta shiga wanke rubutun cikin bowl din bayan tayi bismillah.
Duk abinda take Abraham yana kallon ta, sosai rubutun ya burge shi, bama kamar saurin daya ga hannun ta nayi alamun ta k'ware sosai, bai ankara ba yaga ta miko masa ruwan rubutun, kurawa ruwan ido yayi, musamman bakin daya ga yayi, a tunanin sa wani abu ne daban.
"Ka sha kajiiiii" ta karasa tana mai Jan karshen maganar.
Kawai kallon rubutun yake cikin wani yanayi, Aysha kuwa Dama tayi sammanin hakan, ta San Mawuyaci ne ya karba kai tsaye, Numfashi ta furzar tana kara matsowa kusa dashi, ta mika masa kawar da kan yayi domin scent Din tawaddar daya bugi hancin sa, kara mayar da kallon sa ga Aysha yayi, cikin marairaita tace masa
"Dan Allah!"
A hankali yasa hannu ya karba, toshe hancin sa yayi kana cikin sauri-sauri ya shiga shan rubutun, murmushi Aysha tayi ta kuma San kamshin tawaddar ne baya so shiyasa ya toshe hancin sa, ruwa ta bashi ya dan sha, sannan ya Lumshe idanun sa, Numfashi ya shiga saukewa kamar wanda yayi tseren gudu...
Aysha ta kai Ledan kitchen ta ajiye sannan ta wanke bowl da cup din hadi da tukunyar dafa maganin daya dan sanja wa tukunyar launi, Bayan ta gama ta fito, hanyar barin dakin ta nufa, kamar daga sama taji yace
"hey!"
cikin sauri ta juyo, hannu yayi mata alamun ta zo, ba musu ta dawo.
Da littafin hirar su ya rubuta mata tambayar da yake so bayan App din ta fito masa da amsa.
Karba tayi ta karanta sannan ta dan yi Jim kana ta masa reply da cewa
"MADAM ce ta dawo"
Bayan yayi typing fassarar ya karanta sai ya dafe kan sa kawai, yana jin wani daci a ransa sosai, har yau yana ganin kamar mafarki yake, kamar ba mummyn sa bace wanna.
*AYSHA*
ganin yanayin sa ya sanja ya sanya ta kasa tafiya, kasan tiles din ta zauna duk suka yi zaman kurame na tsahon mintuna goma, sannan tunanin Kiran Inna yazo zuciyar ta, contact list ta shiga inda lambobin mutane biyu gareta, daga na lnna sai na Anty Bintu, number'n Inna ta shiga sannan ta danna dialing hadi da sakawa a loudspeaker, domin taji da kyau Idan an bawa su twins waya.
Ringing uku kacal tayi taji kamilaliyyar murya Innar tayi sallama, amsawa Aysha tayi cikin farincikin jin muryar Innar ta, Bayan sun gaisa tace a bawa su Ammar taji muryoyin su, tana jin Inna tace
"karbi kai Anwar kuyi magana sai ka bawa Ammar, Ammuh dinku ce"
A rude yaran suka shiga Kiran "Ammuh! Ammuh!!“ babu k'ak'autawa tamk'ar zasu fasa wayar su shigo ciki...
Aysha kuwa dariya ta shiga yi, da k'yar tace " yarana ku nutsu, daya bayan daya zamu sha hira kun ji"
A tare da suka ce "toh" yayinda daga can bangaren Ammar yayi nasaran warcen wayar a hannun Anwar yace "Ammuh nah! Ammar ne"
Abraham da idanun sa ke a Lumshe yayi saurin bude ta, saboda muryar yaron daya tsaya masa a rai kwarai.
Ga kuma k'wak'walwar sa da ta tuno masa shigowar Aysha dakin sa na farko, idan bai manta ba wanna sunan ya ji ta fada.
"Ammar! what does that means?" ya fada kasan mak'oshin sa sannan ya kurawa fuskar ta ido, yana kallo yanda take waya cikin annushuwa "da alama tana matukar son yaranta" zuciyar sa ta raya masa hakan.
Aysha kuwa biye wa Ammar ta yi suka sha hirar su sannan tace a bawa Anwar da har ya fara fushi an ki bashi waya da sauri suka sha hira sosai, har kudin wayar ya kare ba tare da ta shirya wa hakan ba, wanda har rashin jin dadin hakan ya bayyana a fuskar ta.
Ajiye wayar tayi a gefen ta ta dago kanta, idanun ta suka fada cikin nashi, sauke kanta tayi kasa tana wasa da yatsun hannun ta, tsahon mintuna biyar ta ga ya miko mata littafin hirar su mai dauke da tambaya kamar haka...
"kina da hoton yaran ki, ki nuna min ina son ganin su, I just want to see them" daga yanayin rubutun mutum zai fahimci wanda ya rubuta daga kasan zuciyar sa maganar ta fito, Bayan mintunan da ta dauka bata ce komai ba, sannan ta shiga rubuta masa reply, bayan ta gama ta mika masa.
*Afuwan my ppl ba nan naso tsayawa ba, buh I just have to*...
Share to others please.
NoorEemaan
07082281566
Thank you for reading my story #Abraham
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
WATTPAD
@NoorEemaan
🌙EID MUBARAK TO ALL MY FANS, MAY ALLAH ACCEPT OUR IBADAT, AND GRANT US JANNATUL FIRDAUS🌙
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
chapter 45-46
"I don't have their pictures (bani da hoton su)" ta amsa masa a takaice.
numfashi Mai zafi ya furzar a lokacin Daya karanta fassarar abin da ta rubuta kasancewar da Hausa ta rubuta masa.
Hakan Nan yaji ba Dadi, sai kuma ya dafe Kansa domin sai yanzu ya tuna cewa karamar keypad ce a hannun ta, ba kuma zai dauki Wani hoton kirki ya zama clear ba, but aleast ya so ganin hoton ko da yayi dishi-dishi kuwa daya fi farinciki fiye da amsar da ta bashi, domin sosai maganar yaran ya tsaya a ransa.
Dan satar kallon Aysha da kanta ke kasa yayi, sannan ya ja numfashi a ransa yace "mother of two, I really can't believe this" ya fada a ransa da mamakin wai yar yarinyar nan (Aysha) tana da y'ay'a har biyu.
Sha biyu ya wuce da kad'an Aysha ta bar dakin ta sauka izuwa kitchen Domin daura girki, saboda Sam bata son yin kuskure ko laifi ga Madam Gloria, domin bata ga alamun sauki a gare ta ba.
Tsaye take a kitchen ta dafa kitchen cabinets tana tunanin abinda zata dafa, can tunanin dafa alale ya fado mata domin tunda ta fara yi musu girki bata taba dafa alale ba, wake ta debo ta wanke domin already Mai kyau ne Babu bukatar sinta, sannan ta cire duka wannan baki-bakin na Saman wake, bayan ta gama ta debo albasa da attaruhu Hadi da crayfish ta gyara sannan ta zuba cikin blender ta mark'ada su duka har da waken.
Kana ta zuba a Wani babban bowl, Man kuli da manja ta zuba kan markadadiyyar kullin, domin bata so yayi ja sosai, sannan ta zuba maggi seasoning da spices masu Dadin kamshi ta sa cokali babba ta juya ingredients din da kyau sannan ta dauko dafaffen kwai da kifi wanda ta gyara ta yanyanka cikin kullin, sai ta dauko wasu mazubi masu kyau da shape kala-kala ta shiga zuba kullin alalen.
Dama already ruwan da ta daura a gas kan babban tukunya ya Soma tafasa Nan ta shiga jera alalen ciki tun kafin ya karasa dahuwa har k'amshi ya cika kitchen din zuwa falo...
Daga nan ta shiga hada cucumber juice Daya Sha kayan Hadi.
bayan ta gama ta zuba komai a warmer, juice din dama ta zuba a jug ta saka a fridge, sannan ta gyara kitchen din, ya dawo fess.
Warmer daya ta ajiye a dinner da cucumber juice, sannan ta dauki na Abraham da juice din shi ta nufi sama ta ajiye masa.
bata Jin cin komai, Hakan yasa ta sauko kasa ta hada quaker oat ta koma sama, har zata wuce dakin ta sai ta dawo da baya ta shiga dakin sa.
Zaune yake ya kurawa tray din abincin ido ba Tare da ya taba ba, tausayin sa taji Mai tsanani a ranta, ajiye cup din quarter oat akan centre table tayi kana ta shiga serving din shi, bayan ta gama ta ajiye masa a gaban sa sannan ta dauki quaker oat din ta daya Sha Madara ta koma gefe ta zauna ta shiga Sha a hankali, duk da cewa bata fiye son quaker oat ba saboda dan yaukin sa, amma hakan ta daure ta shiga Sha kadan-kadan.
Abraham kuwa kallon ta kawai yake, sai kuma ya dauke Kansa yayi gyaran murya, saurin dago kan ta tayi ta kalle shi, ba tare da ya kalle ta ba yace
"come and join me"
shiru tayi tana tunanin abinda yace, sai dai nuni da abincin da yayi ya sa ta fahimci abinda yake nufi, cikin sauri ta girgiza kanta, hawayen da ba ta San ko na menene ba ya cika idanun ta.
Dan zaro mata ido yayi Hadi da Kara hade fuskar sa yayi mata nuni da abincin, Wata shakkar sa ce ya shige ta, a sanyayye ta shiga can guiwa har ta iso gefen sa, da kallo ya shiga bin ta cikin admiration, domin yanda take Jan guiwar ta ya fito da yarintar ta kwarai.
Addu'ar su irin na christian a yayin cin abinci yayi kana ya sa spoon ya yanki alalen ya Kai bakin sa, lumshe ido yayi saboda zallan Dadin daya ziyarci harshen sa, sosai yake yaba kwarewar ta a ransa, domin Babu girkin wacce ke masa dadi kamar na Aysha yanzu.
A hankali ya Bude idanun sa da tun sanda ya fara tauna abinci suke a rufe, ganin kanta a kasa bama ta da alamar cin abincin yasa a hankali ya debo alalen a spoon ya mika mata, a hankali Aysha ta dago ta kalle shi, sai kuma tasa hannu kan spoon din ta dauki alalen, a hankali tasa a baki ta fara tauna, bai kara kallon ta ba ya cigaba da cin abincin sa.
Aysha kuwa ta cigaba da shan quaker oat din ta domin bata so ya kara bata alalen domin bata Jin cin abincin yanzu...
Bayan ya gama ci ya sha cucumber juice dinsa ta tattara wajen ta fita da kwanukan, tana sauka ta hango Madam Gloria hakimce kan dinning table tana cin abincin, gabanta ne ya fadi, amma ta dake....
"ke! wa kika kai wa abinci?"
Madam ta tambaya cikin muryan ta Mai kama da fada-fada.
cikin rudu Aysha tace
"hm.....hmmm yallabai na...na kai wa"
"Hmmmm... ya ci iya cin sa a yanzu, domin daga rana irin ta yau zai bar wanna duniyar yabi iyayen sa, idan yana bukatar kari ma ki kara masa, bai dame ni ba"
ta fada a bayyana, amma cikin yaren Igbo wanda hakan yasa Aysha dake zaro ido kasa gane me ta ce.
Madam Gloria kuwa hannu tayi wa Aysha alamun ta bar gaban ta, cikin sauri Aysha ta nufi kitchen har tana tuntube.
Da gayya ta shiga wanke-wanke a hankali gudun kada ta fito ta tarar da madam Gloria, aikuwa sai bayan mintuna talatin ta fito, ajiyar zuciya ta sauke ganin babu Madam a dining table, hakan yasa ta nufi upstairs da gudu kamar wacce taga abin tsoro.
*********
6:00pm
Bayan Aysha ta gama dinner Mai sauki, ta ajiye na madam a dining table, sannan shima ta kai masa na sa dakin sa...
Dakin ta ta fada tayi wanka, bayan ta gama ta daura alwalan magriba ta fito, tana cikin shiryawa aka kira magriba.
Bayan tayi sallah ta kishingida da jikin gadon ta, ba tare da ta shiryawa Hakan ba Wani bacci Mai Dadi ya dauke ta.
*1:45pm*
AYSHA
A firgice ta farka cikin tsoro, sak'amak'on baccin da ta Yi Mai tsayi, cikin sauri ta mike salati dauke a bakinta, dafe gefen kanta daya tsara mata tayi, sannan ta nufi toilet domin daura alwalan Isha da bata Yi ba.
*********
Mintuna goma Sha biyar ya dauke ta yin sallah'n Isha Hadi da sha'afi da wutiri.
Bayan ta iddar ta zauna shiru, tunanin Abraham ya shiga yawo cikin brain din ta, kasa zama tayi Hakan yasa ta mike domin ta je gareshi, duk da cewa dare ne Amma ta San cewa matuk'ar bata je ba hankalin ta bazai taba kwanciya ba.
A hankali ta tura kofar dakin ta shiga, gabanta ne ya bada ras sak'amak'on ganin sa zaune ya kura wa hanyar shigowa ido, tamk'ar Yana jiran isowar ta ne.
Kallon gefen da ta ajiye masa abinci tayi, taga ko taba wa bai yi ba, sosai taji ba Dadi a ranta...
"Kila yunwa yake ji shiyasa ya kasa bacci"
Ta fada a ranta yayin da fuskar ta ke k'wabe kamar zata saki kuka...
A hankali ta karasa Wajen abincin domin zuba masa sai dai...
Karfaffan hannun sa Mai tsayi ya daga mata alamun ta barshi, mamaki Hakan taji, a sanyayye ta dago tace
"Dan Allah ka bari na zuba Maka, wallahi bacci ne ya dauke ni kaji"
Sleepyn face dinta ya kalla kana ya jefa mata Wani kallo daya sa ta sulale kasan tiles ta zauna.
Abraham kuwa Bai fahimci abinda tace ba, Amma duk Wanda ya kalle ta a wanna lokacin zai fahimci cewa bacci tayi, ba kuma fushi yake da ita ba, domin Yana ganin kokarin ta sosai, Hakan Nan tana da kima a zuciyar sa sosai, sannan baya jin yunwa ko kadan.
Duk da cewa ya gaji matuk'a da zaman wheelchair din, domin ba Abu bane Mai sauki, Amma ya yarda da kaddara mai kyau da akasin ta, yasan cewa Allah ne ya jarrabe shi, ba kuma zai Yi butulci ga Allah ba, illa yayi addu'a Allah ya bashi lafiya, domin yasan Babu kaddara mara kyau da zai dawwama.
Aysha kuwa kasa komawa dakinta tayi... karaf idanunta suka sauka kan qur'anin da ta ajiye a bedside drawer din sa tun da rana, ajiyar zuciya ta sauke domin zama shirun ya soma gunduran ta, cikin sauri ta dauko shi ta koma ta zauna, suratul yasin ta Bude tayi Bismillah ta shiga karantawa cikin zazzak'ar murya kasa-kasa tana bawa kowacce harafi hakkin ta.
A kuma daidai lokacin ne Madam Gloria ke tsaye a dakin ta rike da kwaryan nan Mai dauke da wanna abun Mai tsananin haske , sanye take da wasu jajayen kaya Mai ratsin Baki.
Wanna abun na cikin kwaryan ta Sanya a tafin hannun ta, sosai hannun ta ya shiga rawa saboda karfin abun, wasu kalamai marasa dadin ji ta shiga karantawa da Wani yare, idanun ta kyaar kan wanna abun na cikin tafin hannu ta....
💞NoorEemaan💞
Thank you for reading my novel #Abraham.
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 47-48
Ta dauki tsawon mintuna goma tana karanta suddabarun ta kana ta hura iskar bakin ta izuwa ga abin tsafin dake hannun ta, kamar a mafarki abin ya bar hannun ta ya shiga tafiya shuuuuu ya bi ta bangon dakin ya fita...
Murmushin farinciki Madam Gloria ta saki ganin burin ta na daf da cika. Bayan Mintuna biyu kacal murnan ta ya koma ciki, firgice da tashin hankali suka maye gurbin farinciki da take ciki sak'amak'on abin tsafin daya dawo hannun ta, Wanda hakan alamun rashin nasara ne.
Gabanta ne ya bada ras! domin lalacewar wanna aikin daidai yake da lalacewar dukkanin Shirin ta, kamar zararriya tace "meyasa? Meke Shirin faruwa ne, Wani irin taurin rai ne da kai Abraham, wallahi bazan bar ka ba, har sai na ga ka zama gawa!" Ta karasa a tsawace.
A karo na biyu ta Kara Yi, Bai je ko ina ba ya sake dawowa ya fada cikin tafin hannun ta. Wani fushi ya zo mata, dukkanin nutsuwarta ta tattaro ga abin tsafin kana ta shiga karanta suddabarun ta, sai ta hura iskan bakin ta izuwa ga abin tsafin, wannan karon abin tsafin ya koma cikin kwaryan, a hankali launin kwaryan da abin tsafin Nan ya dawo Wani bakinkirin, jikin ta ne ya shiga rawa, Hakan yasa kwaryan ya subuce daga hannunta ya fadi kasa ya tarwartse, zubewa tayi a kasa ta saki Wani Kara, yayinda hawaye Mai zafi ya biyo kuncin ta hugu...
Kamar zararriya ta shiga birgima a kasa tana surutai, so take ta mike domin zuwa duba Abraham ta ga abin sa ya hana aikin ta cika, domin ta ga dalilin da ya hana shi mutuwa, Amma ta kasa tashi saboda tashin hankali da fargaban da take ciki yasa jikin ta mutuwa, tsoro sosai ya shige ta domin bata manta da abinda bokan Nan yace Mata ba, kafin ta karbo kwaryan tsafin.
Kamar almara, wanna fashashen kwaryan nan Mai dauke da abin tsafi ya shiga tattara Kansa waje Daya, kana ya bace bat, daidai inda kwaryan ya bace Wani bakin hayaki ya tashi yayi sama Wajen pop'n dakin.
Duk Madam Gloria na kallon abinda ke faruwa Amma ta kasa motsa ko da yatsan ta ne, kamar wacce aka datsa haka ta kasance.
ABRAHAM
Cikin birgewa yake kallon Dan tsut din bakin ta dake karanta littafi Mai sarki, his attention is hundred percent with her, har lau Bai San abinda take karantawa ba, Amma Yana sintar Kansa cikin nutsuwa a duk lokacin da yake Jin zazzak'ar muryan ta Mai sanyin amo na karatun qur'anin, ji yake dama su dauwamma a haka, iska Mai sanyi ya furzar daga bakin sa Yana sake mayar da hankalin sa gare ta.
Aysha kuwa bata San ma Yana Yi ba, karatun ta ta cigaba da Yi tana Jin fargaban da ke damunta tun safe da bata San Kona menene ba na barin zuciyar ta, salama da Wani sanyin ni'ima daga Allah ya maye gurbin tsoron ta, haka ta dauki tsahon lokaci tana karatu, har bacci yaci karfin idanun ta, ba tare da ta shiryawa Hakan ba Wani bacci Mai dadin gaske ya dauke ta a zaune qur'anin ta na rungume a kirjin ta.
ABRAHAM
Kallon innocent face din ta yake, Yana Jin Wani nishadi da Bai San Kona menene ba na ratsa shi, yanda numfashin ta ke fita a hankali da yanda zararran eyelashes dinta ke rufe yafi komai Jan hankalin sa.
"Oh! Jesus Christ" Ya fada a hankali Yana lumshe idanun sa, haka ya cigaba da zama har akayi Kiran sallah daga masallacin unguwar...
Idanun sa da suka bata awannin a rufe, ba kuma bacci yake ba ya Bude a hankali, ya ga sai bacci take, domin zuwa yanzu ta sulale kasan tiles din Amma still qur'anin ta na rungume a kirjin ta.
A hankali ya tura keken sa zuwa gaban inda take kwance, yace "hey!"
Shiru Aysha na duniya bacci bata San Yana Yi ba, kafarta ya kalla, kana ya daga kafar sa ya Dora kan tafin kafarta...
Can cikin bacci Aysha ta ji Wani sanyi na ratsa ta, a hankali ta shiga Bude idanun ta, sai kuma ta sake rufewa alamun baccin Bai ishe ta,
"hey! Wake up it's time for your prayer (ke! Ki tashi, lokacin sallar ku yayi)" fada da turanci Yana Dan murza kafar sa kan na ta kafar.
Cikin sauri ta mike salati dauke a bakinta tana murza idanun ta, kalle-kalle ta shiga Yi, taga dai tabbas dakin sa ne, cikin muryan bacci tace" yaushe nayi bacci a dakin Nan ban sani ba?"
Ganin bata da Mai bata amsa yasa ta mike a hankali ta bar dakin tana waiwayen sa, da kallo ya bi bayanta Yana sakin ajiyar zuciya, Wani Abu kamar rashin jin Dadi game da barin ta dakin na ratsa zuciyar sa...
************************
9:05am
A daidai lokacin Aysha ke haurawa da breakfast din sa sama, a hankali ta shiga dakin bakin ta dauke da sallama, dago Kansa yayi ya shiga bin ta da kallo, bayan ta ajiye ta Dan risina tace
"Ina kwana"
Daga mata Kai kawai yayi, domin zuwa yanzu yasan Ina kwana kamar gaisuwa ce, duk da Bai San ma'anar ba, Amma ganin tana yawan fadin Kalmar ya sa ya zauna a Kansa..
Bayan tayi serving dinsa sannan ta Kara warming maganin jiya ta bashi, Babu tunanin komai ya karba ya shanye. Ganin Haka yasa ta barin dakin domin tayi wanka sannan tazo tayi masa rubutu. Da shigar ta wakan da shiryawan mintuna ashirin ya dauke ta sannan ta dawo dakin sa tayi masa rubutu a allo ta bashi, Nan ma babu musu ya karba ya Sha, domin ya gama bata dukkanin wata yarda...
Bayan Nan ta gyara masa dakin sa ta sauka da kwanukan, dakin madam Gloria tabi da kallo ta girgiza kanta kana ta hayo sama abinta, domin taje kofar dakin ta ta dinga kwankwansawa domin ta Yi mata gyaran dakin Amma bata Bude ba, dakin ta ta koma domin Wani mugun bacci take ji.
MADAM GLORIA
Sai safa da marwa take saboda tashin hankali, rashin cikar burin ta a daren jiya yafi komai daga hankalin ta, hanyar kofar ta nufa tana huci kamar wata zak'anya, cikin ranta take fadin "yaro yaro ne! Yaro man kaza, idan ka San wata baka San wata ba" ta karasa fada kana cikin sauri ta nufi dakin sa.
Tana shiga ta tarar da Abraham zaune Yana bacci a tunanin ta, , domin idanun sa a lumshe suke, sa dai abinda bata sani ba, duk Yana sane da shigowar ta, duk da idanun sa a rufe suke Amma Yana kallonta ta tsakankanin eyelashes dinsa.
Kallon shi take daga sama izuwa kasa saboda ganin Bai yi rama ko lalacewa kamar yanda tayi tunani ba, "Amma wake kula dashi haka?" Ta fada a ranta tana tabe Baki tare da Jin haushin ganin sa tsaf tsaf duk da bawai kamar lokacin da yake da lafiya bane, ganin zata bata lokacin ta yasa ta dauke kanta daga garesa.
Bincike ta shiga Yi a dakin, gabadaya ta birkita dakin, mukullan motar sa duka ta kwashe, sannan ta fara Neman dukkanin takardun company'n sa Amma bata gani ba, haka ATM cards din sa, domin ta San pin din sa kasancewar ya bata dukkanin wata yarda a matsayin mahaifiyar sa.
Numfashi ta shiga saukewa kamar wacce tseren gudu, saboda zirga-zirgan da ta Yi a dakin, kallon dakin take tana Neman Ina Zata samu takardun sa domin yafi komai muhimmanci cikin kadarorin sa, kallon ta ta Kai inda Abraham ke zauna ta watsa masa Wani kallon tsana, tayi mugun tsanar sa fiye da baya, domin shi kadai ke bata ciwon Kai, a yanzu tunanin kashe shi ba tare da Wani tsafi ba take tunani, Amma abin da kamar wuya, domin Abraham Wani irin powerful halitta ne, kashe shi kuma ba Abu bane Mai sauki duk da kasancewar sa a zaune kan keken guragu, haka Allah ya hallice shi gifted ne.
Kamar guguwa haka ta bar dakin fuuu da mukullan motocin, tana Jin haushin rashin ganin takardun sa...
A hankali Abraham ya shiga Bude idanun sa da suka Sanja launi saboda fushi da karyewan zuciya, mummy'n sa yake gani ta Sanja ta zama wata muguwar hallita, dama haka take duk tsahon shekarun Nan Amma ya kasa gane hakan...
Killer smile yayi Mai tattare da ciwo Yana cije labban'sa masu taushi, a hankali ya ga an turo kofar, dago Kansa yayi ya kalli Mai shigowar, ajiyar zuciya yayi ganin wacce ta shigo.
Share fisabilillah
Comment for more typing....
✨NoorEemaan✨
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
*WATTPAD*
@NoorEemaan
Chapter 49-50
*AYSHA*
Kallon dakin take ganin yadda ya hargitse ya tabattar mata da cewa an shigo dakin, amma bata ko yi magana ba ta shiga gyarawa, domin tambayar waya shigo ba hurumin ta bane.
Abraham kuwa zuba mata sexy eyes din sa yayi, Ya kuma fahimci abinda ke ranta, Amma Bai yi magana ba, tana cikin gyaran ne taji keypad dinta na ringing, sai a lokacin ta tuna cewa wayar na dakin Abraham, bata dauka ba, cikin sauri ta nufi Wajen wayar domin tana da tabbacin Inna ce, domin idan ma ba ita bace toh anty Bintu ce domin su kadai ke da numbern ta.
Tana dubawa kuwa ta ga Innar ce, cikin sauri ta yi picking Hadi da sawa a handsfree
"Ammuh!"
"Ammuh!!"
Muryan su Anwar ta cika wayar basu ma bari Inna tayi magana ba, siririyar dariya Aisha ta saki, hakan ya saka Abraham dagowa ya kalle ta, domin yau ne karon farko Daya ji dariyar ta haka, da alama tana matukar kaunar y'ay'an ta ya aiyana a ransa.
Tuno Nonye da cikin ta yasa ya hadiyi Wani abu Mai daci a ransa, yasan cewa da ace tana raye da yanzu yar su ko dan su tayi wayo, Jin muryoyin yaran yasa Wani mugun so y'ay'a da sha'awar su ya kama shi...
"Ammar! Anwar!!" Ku bari mu gaisa da Inna ko"
"Ammar!"
Abraham ya kira sunan da harshen sa na yan Igbo, tabbas wanna sunan yaji a bakin Aysha a ranar da ta fara shigowa dakin sa, a kuma duk lokacin da ta kira sunan sai zuciyar sa ta buga, me Hakan ke nufi kenan? Ya Yi wa Kansa tambayar da bai da amsar shi.
"Assalamualaikum, Innata! Ina kwana"
"Lafiya lou diyar albarka, yakike ya aikin?"
"Alhamdulillah Inna, fatan Babu wata matsala?"
"Alhamdulillah Babu komai, ya Mai jikin?"
Dan satar kallon Abraham tayi suka hada ido, saurin dauke kanta tayi kana tace "da sauki Inna"
"Masha Allah, toh Allah ya bashi lafiya, ki mai sannu"
"Toh inna"
"Yawwa, ga yaran ki ku gaisa, sannan ki dage dayi masa rubutun Nan da bashi maganin kinji ko" Inna ta fada daga dayan bangaren tana ajiye wayar gaban su Anwar domin raba rigima, saboda matuk'ar ta bawa Daya waya toh akwai rigima kenan...
"Toh Inna nagode, Yaran albarka, kun tashi lafiya?"
Hada Baki suka Yi wurin amsawa, "lafiya kalau Ammuh!" Nan suka shiga bata labari tana biye musu har kudin Inna ya kare, ba Dan sun so ba suka hakura.
Farinciki ne ya cika zuciyar Aysha Jin muryoyin yaran ta, ajiyar zuciya ta sauke murmushi dauke kan fuskar ta, sosai take kaunar su Anwar a ranta, domin kallon y'ay'a take musu da kuma kanne da bata dasu, ta dago kanta kenan taga sun hada ido, sauke kanta tayi kasa tace
"hmmm... Inna tace na Maka ya ji...." Sai kuma tayi shiru tuno cewa ba fahimtar abinda tace zai Yi ba, Abu mai sauki kawai ta dauki biro ta memo din shi ta rubuta, sannan ta hada da wayar sa dake gefen gado ta mika masa, domin sakon Inna ne dolen ta ta isar masa.
Karba yayi ya shiga app dinan mai fassara kalmomi daga Hausa izuwa turanci.
Amsar da app din ya bashi ya kura wa ido, ashe matar da bata San ko shi wane ne ba ta damu da sanin lafiyar sa haka? Amma wacce ya dauka a matsayin mahaifiya bata ko damu da lafiya da lafiyar sa ba, bama ta kaunar ganin sa a doran kasa, ashe Aysha ta dauki shi da muhimmanci har ta sanar da mahaifiyar ta rashin lafiyar sa.
"Oh God! This people are damn amazing" ya fada a ransa cikin yabon kyawun halayen su.
Dagowa yayi ya sakar mata murmushin sa mai kyau domin yaji Dadi har ransa da kulawar Inna garesa, itama murmushi tayi kana ta bar dakin.
Da misalin karfe uku na yamma madam Gloria ta fito daga gidan,, sai dai bata dauki mota ba, a bakin gate ta tsaya bayan ta fito kana ta saki murmushin mugunta a Fili tace "wanna karon ba za ka Sha ba, duk taurin ranka dole ne ka mutu a duk lokacin Dana dawo, domin a mugun shirye nake yanzu"
"Bayan kwana uku*
Cikin kwanakin Nan Abraham na Jin sanje-sanje a jikin sa, domin sosai Aysha ke kokari safe, rana, dare wurin bashi magani da rubutu.
Ranar daya cika kwana bakwai da fara Shan magani Abraham yaji kamar an yaye masa ciwon cikin Nan, sannan ko da ya Dan motsa jikin sa baya Jin zafi kamar da, tamk'ar an dauke masa dutse daga kan cikin na sa haka yake jin shi qwanin Dadi, duk da Bai gwada mikewa ba, Amma tabbas farinciki ya cika zuciyar sa, domin tunda yaci gubar Nan Bai kara lafiya irin na yau ba, dama daurewa ciwon kawai yake.
A kuma daidai lokacin ne Aysha ta shiga dakin ta domin yin sallar magriba... sai a sannan Abraham ya gwada mikewa, iKon Allah buwayi gagara misali, kamar almara lo magic haka ya mike.
"Thank you Jesus Christ" shine kalmar daya fara fita a bakin sa, yayin da husky voice dinsa ke bayyana tarin farincikin sa.
Taku uku yayi, ya sake dawowa gaban well chair din sa, kamar karamin yaro haka ya fada kan gado ya dunkule hannun sa yace "yes! Am back on my feet, Jehovah thank you, oh Lord! Thank you" Ya ma rasa kalmar da zan fada saboda tarin farinciki, gaban gadon ya dawo yayi kneel down worship song na christian ya shiga Yi kana ya Dora da addu'a, bayan ya gama ya mike ya shige toilet, domin tsaftace jikin sa.
AYSHA
Bayan ta iddar da sallah ta sauko kasa domin karasa musu abincin dare, yau kam ta makara bata gama da wuri ba, Allah ya taimake ta Madam Gloria bata nan, da ta banu a hannun ta yau.
Sai da ta sake daukar wasu mintuna ashirin a kitchen din sannan ta gama, had'add'en spaghetti🍝 da miyar stew Daya Sha zallan sokan namomi ta girka, ta zuba masa a warmer, sannan ta daukar masa lemo da ruwa ta nufi dakin sa, kamar kullum bakin ta dauke da sallama ta tura kofar dakin ciki....
Sam bata lura Babu shi kan wheelchair din sa ba, sai da ta ajiye abincin a centre table kana ta dago kanta taga wayam Babu shi...
Gabanta ne ya fadi ganin Babu shi kan kujerar sa, "toh Ina ya tafi?" Ta San dai ba tafiya yake ba bare tace ko Wani waje ya tafi, gabadaya k'wak'walwarta ya toshe, hawaye suka cika idanun ta, kamar status haka ta tsaya bata motsa ba.
Wani sanyayyar kamshi taji ya bugi hanci ta, hakan yasa ta waiwaya da sauri, fidda manyan zararran idanunta tayi waje, cikin zallan mamaki da al'ajabi sak'amak'on abinda ta gani.
_hey fans! Hope you all enjoyed this episode? let me know In your comment_
Share fisabilillah
Comment
✨NoorEemaan✨
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da facebook su yi join ta wanna link din.
*Powerful Dua Please Don't Ignore Or Skip*
Ya ubangiji Kaine kake azurtawa ka azurtamu da rabo Mai albarka, ka yafe mana ya ubangiji, ka haskaka zukatanmu da alkhairi ka biya bukatunmu na alkhairi kasa mu cika da kyau da lmani, ya ubangiji ka tsare mu daga aikata barna da aikin dana sani ka tsaremu daga saba maka ya ubangiji, kasa mufi karfin zuciyoyinmu da kuma sharrin shaidan, ya ubangiji ka tsaremu daga biyewa zuciya ka rabamu da aikin dana sani ka sanya mana tausayi da juriya da hak'uri a zuciyoyinmu.
Ƴa ubangiji duk Mai neman haihuwa da Mai bukatar aure darajar wannan watan Mai albarka ka biya wa kowa bukatar shi ta alkhairi, ya Allah Wandanda suke da auren ka zaunar dasu lafiya, ka basu farin ciki da yiwa junansu adalci tare da rike Amana da kuma biyan hakkin aure dake kansu, ya ubangiji ka karemu, ka yafe mana ka yi mana arziki ka mana budi mafi alkhairi a rayuwar mu ka yafe mana, ka sanyaya zuciyoyinmu ka rabamu da aikin dana sani, ya ubangiji ka biyawa kowa bukatar shi ta alkhairi.
Chapter 51-52
Abraham tsaye kan kafafun sa cikin shigar kananun kaya Yana kallon ta fuskar sa a sake, ja baya ta shiga yi, ta kasa yarda cewa Wanda ta bari kan keken guragu ne mintuna kadan da suka shude ne ke tsaye yanzu kan kafafun sa yanzu, ganin kamar da tsoro a tare da ita yasa Abraham zama a bakin gado, dama kafar sa bata gama kwari ba saboda watanin Daya diba a zaune bai taka ba.
"Da gaske shine ko kuma gizo idanuna ke mun? Ya rabb!" Ta fada a bayyana tana sulale kasa, sai kuma ta saka kuka, Wanda na zallan farinciki ne, tabbas tayi masa murnan samun lafiya, Amma har yanzu al'ajabi da mamaki bai sake ta ba, domin ba ta taba tunanin ko kawo wa a ranta cewa zai warke Nan kusa ba.
Jin kukan ta yasa shi dago Kansa da sauri, mamaki yake meya sa ta kuka haka all of a sudden, tabbas ba ta cancanci kuka ba a yanzu da yake da damar ba ta hakuri ba, domin ita din haske ce cikin rayuwar sa, sannan Mai zuciyar taimako, bai taba zama da mace Mai kyawun hali kamar ta ba, duk da karancin shekarun ta. Hakika bazai taba manta alkhairi ta gareshi ba, so yake yayi magana, amma rashin jin yaren juna yasa shi kasa yin maganar da ya yi niyya.
"Shhhh!" Yace yana dora hannun sa kan lips din sa, yayin da ya kura mata sexy eyes din sa.
Shiru tayi kamar ruwa ya cinye ta, cikin sanyi da calm voice yace "is alright, stop crying ok?"
Duk da bata fahimci abinda yace ba, haka ta shiga daga masa Kai da sauri...
"Good girl"
yace Yana Dan sakar mata murmushin sa Mai kyau, Dadi taji a ranta, Hakan yasa ita ma ta mayar masa da martani, littafin da suke yiwa juna magana ta dauko kana ta rubuta "na Maka murna yallabai da dawowa kan kafafun ka, Allah ya kara lafiya, ya kuma tsare gaba"
Tana gamawa ta ajiye a kusa dashi kana ta fita daga dakin cikin takun nutsuwarta, da kallo ya bita har ta fita kana ya dawo da idanun sa kan takardun bayan ya shiga app dinan ya Yi typing, fassasar abinda ta rubuta da turanci ya fito...
Sau uku Yana karanta rubutun kana ya yi murmushi, ya kuma ji dadi a ransa, saboda shi mutum ne dake matuk'ar son a nuna masa kulawa, ajiye takardan yayi sannan ya mike ya fice daga gidan gabadaya, duk da cewa dare yayi Amma Yana son fita ya tattaka kafar sa, bayan ya fito ya hadu da Mai gadi, zaune a bakin aikin sa...
Hannu Abraham ya daga wa Mai gadi ganin irin kallon da yake masa, Mai gadi kuwa cikin sauri ya nufo shi da cikin zallan mamaki da farinciki, sai da yazo daidai gaban sa ya ja ya tsaya sannan ya dan taba shi yace "ya salamullahi! ashe kai din ne da gaske oga, ba shakka Babu abinda ya gagari ubangiji, gaskiya oga I dey happy for you well well, Kai congrats, congrats Mai gidana" ya karasa cikin gurbatacciyar turancin sa.
Murmushi Abraham yayi, kana yace "Thank you" sannan ya fita ta karamin gate, ganin shi a waje yaji Wani yanayi Mai Dadi na ratsa shi, domim robon shi da waje har ya manta, sosai zuciyar sa ke cike da farinciki.
Mai gadi na kiran "oga ba zaka fita a mota ba?" Amma bai samu amsa ba, domin yallabai Abraham har ya gama ficewa.
Tafiya ya cigaba da yi a hankali cikin nishadi har yazo babban titi, sannan ya samu mai Keke napep ya tara ya shiga.
Supermarket dake kan hanyar da suka dauka ya sauka, ya biya mai dan sahu sannan ya shiga ciki, abubuwan amfanin sa da babu ya Siya, domin yana Shirin yin shopping ne dama ya ji gubar nan, har ya nufi wurin biya sai kuma ya dago da baya, haka kawai ya ga ta cancanci ya Yi mata shopping ita ma, duk da Bai San abubuwan da take so ba.
Man shafawa, shower gel, Dan karamin makeup kit da kuma ice cream babban roba ya daukar mata, yayi transfer kasancewar Babu ATM cards dinsa a tare da shi, bayan ya fito yaga a Wajen supermarket din ana siyar da gashashen kifi ya siyi Leda biyu, sannan ya kara tarar Mai Keke napep ya hau, inda tafiyar mintuna goma Sha biyar ne suka kawo shi kofar gida, Dari biyar din da ta rage a aljihun wandon sa ya bawa Mai napep kana ya shiga gida, Yana Jin Mai Keke na masa godiya domin ka'idar kudin sa 300 ne.
Mai gadi ya mika wa Leda Daya na kifi inda ya dinga Yi masa godiya, Amma Abraham Bai ko juyo ba, domin shi mutum ne da Bai son yayi abu a dinga Yi masa godiya.
Bayan ya shiga general falo, ko ina shiru babu motsin komai sai na Karan AC, sai kuma TV dake aiki shi kadai, remote ya dauka ya kashe Tv'n sannan ya fara hawa step case domin isa dakin sa.
Da shigar sa dakin sa kuwa ya ajiye kayan duka kan gado kana ya shiga toilet ya sake watsa ruwa yayi brush, sannan ya fito ya shirya cikin pyjamas blue black ya fesa body spray kana ya zauna a bakin gado, nannauyyar ajiyar zuciya ya sauke, yana kara gode wa Allah a ransa, hakika duk wanda yake da cikakkiyar lafiya ya dinga godewa Allah kullum, komai Taulacin sa kuwa, domin gashi Yana da Arziki da dukkanin ababen more rayuwa, Amma baya Jin dadin su saboda tafiyar da baya iyawa.
" Thank you lord, Thank you jesus!" Abraham yace a hankali.
Idanun sa ne ya sauka kan abincin da Aysha ta shirya masa, dan yamutsa fuska yayi, cikin sa dake lafe masu dauke da manya-manyan six packs ya shiga shafawa a hankali, k'watak'wata baya Jin yunwa, domin farinciki daya cika zuciyar sa.
Kallon ledojin daya shigo dasu yayi, ganin bata shigo ba yasa shi kwashe siyayyar daya Yi mata ya nufi dakin ta, ƙwanƙwansawa yayi ba tare da kuma ya Jira ta bashi izinin shigowa ba ya tura kofar ciki...
Zaune ya hangon ta kan sallaya, hannun ta a sama tana addu'a, yayin fuskar ta ya nuna farinciki, ta burge shi kwarai, musamman kwayar idanunta fare kal da suke kallon sama, sannan yanda ta bawa addnin ta muhimmanci ya burge shi ainun, domin ko kallon inda take Bai yi ba, bare ta damu da wanda ya shigo, addu'ar ta ta cigaba da yi, duk da cewa taji shigowar shi, janye idanun sa yayi kana ya ajiye ledojin ya fita...
*30Minutes later*
A hankali Aysha ta shiga cire hijab dinta, tana sakin murmurshi, Dadi sosai take ji ganin Abraham ya warke, so take ta kira Inna ta mata albishir sai ta kuma ta Yi tunanin sun yi bacci, haka ta hakura da tunanin gobe zata kira ta.
Ledojin ta bude ta fito da abubuwan ciki, duk da bata furta ba, Amma tayi farinciki da siyayyar da ya Yi mata, kifin da Ice cream ta ajiye a gabanta ta shiga ci, domin dama ita Mai son kifi ce, sosai taci har ya rage dan kadan, sannan ta Sha ice cream kwatan roban.
Bayan ta gama ta shiga toilet ta wanke hannunta, sannan ta sake Yin brush saboda Karnin kifin, rogowar Ice cream da kifin ta dauka ta sauka kasa ta ajiye ice cream a fridge, ragowar kifin kuma ta ajiye a kitchen, sannan ta koma dakin ta ta yi Shirin kwanciya ranta fari kal, tana Jin farincikin da ta jima ba tayi irin shi ba.
*** *** ***
*BANGAREN ANTY SARAH*
Zaune take a madaidaicin dakin ta, ta Kara lalacewa yayin da tsufa ya bayyana karara a fuska da jikin ta, musamman da babu gyara da ingantaccen abinci, muskutawa tayi sannan ta zabga tagumi, mafarkin da ta Yi kan Nonye yau ya kara firgitata, burinta ta hada yan kudin mota da zai ishe ta domin taje Imo state, Abraham kadai zata nema, domin ta tono asirin dake boye sannan su nufi gombe gidan da ta ajiye yaran ta gudu, domin shi kadai ne hanyar dazai sa ta samu dan kwanciyar hankali, ta sani cewa ita da samun kwanciyar hankali Mai dorewa sai Wani iKon Allah domin kashe rai ba abun wasa bane.
*Bayan kwana biyu*
_2:30am_
A yanda take kwance da kuma yanda take shura kafafun ta zai tabattar Maka da cewa, mafarki mara dadi take...
A firgice ta farka, gumi sai tsatsafo mata yake, gaba Daya ta jika yar T-shirt din jikinta daya gama tsufa saboda dadewa, "zan tona asirin da muka dade da binnewa, Dan Allah kiyi hakuri Nonye, Wayyo Allah ka taimake ni na tuba" Anty Sarah ta fada da yaren Igbo cikin fitar hayyaci...
**********
Da safe a sanyayye take komai domin mafarkin da ta yi Yana makale a ranta, gashi kudin bai taru bare ta tafi yau, Yan kayan abincin da take samu a gona ta dauka, sannan ta nufi makotan su, ta siyar musu a raha, musamman da suka ga tana da bukatar kudi, hakan yasa suka mata tayin wulakanci, Amma bata da zabi Daya wuce ta siyar din, domin a gobe take son tafiya.
Amma abin daya bata mamaki a yau shine lami lafiya ta kwanta bata yi mafarki ba.
Da misalin karfe shida na safe ta dau hanyar Imo state, sun yi tafiya mai tsayin zango sannan ta sauka a tasha, taxi ta tara ta shiga sannan tace ya kai ta wordbank estate...
Bayan sun iso, ta biya shi kudin sa sannan ta sauka, kallon gidan ta shiga yi, har abada bazata taba Manta gidan nan ba, yana nan yanda
Yake sai Dan abinda ba a rasa ba aka Sanja, sosai abubuwa da dama suka shiga dawowa brain din ta, musamman mugayen Abubuwan da suka aikata, hawaye ta share na nadama, sannan ta karasa jikin kofar gidan ta shiga k'wank'wansa wa a hankali, mintuna biyu kacal Wani katon mutum Mai sanye da blue da black uniform ya Bude kofar Yana muzurai...
"Madam how may i help you?" Ya fada da k'akk'auran muryan sa mai amon sauti.
Cikin rawar baki Anty Sarah ta ce....
Share fisabilillah☑️
Comment ☑️
NoorEemaan
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM 🍓🍓
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Page 53-54
"'ple.... p...le...ase can i see your boss, i mean Abraham"
Cikin rashin fahimta mai gadi ke kallon ta, domin iya sanin sa ba sunan uban gidan sa Abraham ba, ita kuma Anty sarah ta gane shi tsaf domin shi ne dai mai gadin Abraham na da, amma bata nuna ta gane shi ba.
Shiru mai gadi yayi kamar yace batan gida tayi, sai kuma yayi saurin cewa "oh! Oh!! Oh!!!" Alamun ya tuna Abraham tsohon mai gidan sa, nan ya shiga bawa Anty Sarah labarin tashin sa daga garin ba kuma ya san ina suka koma ba, yana gama bata labari ya rufe gate din ya ruga cikin gidan da gudu sak'amak'on kiran da matar gidan ke masa.
Anty Sarah sulalewa kasa tayi ta ɗora hannun ta akai ta sa kuka mara sauti yayinda hawaye ke sulalowa daga idanun ta, gwanin tausayi, ita kam ina zata je? Ta ina zata fara neman su a fadin duniyar nan?
Ta jima zaune a wajen cikin rashin sanin abin yi, ga duk wanda zan wuce sai ya dinga kallon ta, hakan yasa a sanyayye ta mike ta shiga tafiya domin komawa garin su....
••• ••• •••
Zaune yake a had'add'en office din sa dake cikin ma'aikatar sa, yau kwanasa uku da dawowa aiki, inda sosai ma'aikatan sa suka yi murna da dawowar sa.
A shirye yake cikin suit baƙi, sosai hakan ya fito da kwarjinin sa hadi da haibar sa, Google ya shiga yayi searching wani abu sannan lambar dake karshen rubutun ya dauka, wayar sa yasa ya danna kiran lambar, magana biyu zuwa uku ya ajiye wayar, sannan ya mike ya dauki key din mota da waya, sake gyara zaman rigar sa yayi, murya kasa-kasa yace "yeah! I guess this is the only solution" ya karasa fada yana bude kofar office din ya fita, parking space dake company ya nufa ya shiga Mota, security da masu gadi na masa a dawo lafiya, hannu kawai ya daga musu kana ya fice...
Tafiyar mintuna arba'in ya kawo shi babban ginin mai dake da rubutun *MM HARUNA ENGLISH ACADEMY* kallo daya yayi wa ginin kana ya dauke kansa, lambar dazu yayi dialling, bayan anyi picking ya fada musu yana wajen ginin...
Mintuna uku kacal wani matashi ya fito, cikin girmamawa ya gaishe da Abraham, fuska a sake Abraham ya bashi hannu ya suka yi musabaha, sannan suka jera cikin wajen, office din shugaban su matashin nan ya nuna masa kana ya koma...
Bayan sun gaisa da shi, Abraham yayi gyaran murya yace "am.... I want to register a girl here, i don't mind to pay extra money if she can be fluent in speaking English" Ya karasa Yana dan bugu teburin office din da yatsun sa biyu a hankali, bai sani ba ko Aysha zata yi na'am da wannan makarantar ta koyan turanci da zai sa ta ba, kawai yana so ta iya ne domin ya saukaka musu wajen magana da juna, ya lura cewa bata yi karatun boko ba, matuƙar ta bashi hadin kai, tana kuma kaunar karatun zai bata dukkan wata gudunmawa domin ta cigaba, domin tana daya daga cikin halittun da bazai iya taɓa mantawa ba a rayuwarsa, shiyasa take da dubbin darajar a idanunsa.
Maganar shugaban makarantar ce ta sa shi daga kansa, sannan ya daina buga yatsun sa kan teburin, cikin turanci mutumin yace...
"In Sha Allah zaka yi mamaki yanda zata kware a fannin turanci, karka damu, sannan kamar yadda kace za ka iya ƙara kuɗi domin ta fi saurin kwarewa. Toh zan yi making arrangement a saka ta a special class domin a koya mata komai yanda ya kamata, sannan yace zata iya farawa ranar juma'a, tunda yau Laraba, domin dama kwana uku kaɗai ake karatun juma'a, asabar, da Lahadi"
Hannu Abraham ya bashi suka yi musabaha, sannan ya biya dukkanin kuɗin da ake bukata, sannan aka bashi Form ya cike mata sannan a yi attaching passport din ta da filling foam din, karba Abraham yayi, domin bai san sunan ta ba, bare ya cike mata, baya ga haka ma babu passport din ta a wajen sa, hakan yasa ya karbi Form din yace zai je gida ya cike gobe zai dawo dashi, da haka ya bar wajen
Bayan ya koma office, babu jimawa P.A dinan na shi ya shigo bayan ya bashi izinin shigowa, a sake suke tattauna da Abraham kan abinda ya shafi business din su musamman da bayan nan, yana masa bayanin komai da komai, bayan sun gama maganar business din yace "boss!"
Abraham ya dage girar sa alamun amsawa.
"Wallahi matar ka tana da kirki sosai"...
Dan waro ido Abraham yayi saboda mamakin kiran kalmar *mata* da personal assistance din sa yayi, shi kuwa P.A bai lura da yanayin fuskar Abraham ba, nan ya shiga bawa shi labari tun daga zuwan sa gidan da karramawar da Aysha tayi masa, sannan maganar da suka tattauna kan yana k'asar waje, komai dai bai boye ba...
*Some minutes later*
Bayan fitar P.A "What!" Abraham yace Yana sakin murmushin gefen baki, "so this Hausa girl is smart as this, oh my goodness" sosai ta burge shi, musamman karkashin ta, dakewar ta, hadi da boye rashin lafiyar sa da ta yi, ya jima yana tunanin a kanta da irin hallacin data yi masa...
••••••• ••••••• ••••••
Da misalin ƙarfe hudu ya bar company'n sa zuwa gida. Biyar saura mintuna k'alilan ya iso gida saboda dan hold up dake hanya, a parking space ya faka motar sa, kana ya fito rike da brief case din sa, har ya fara tafiya ya tuna da Form din, ya kuwa ya d'auka sannan ya nufi cikin gidan.....
Kamar kullum fakon shiru sai plasma dake aiki she kad'ai, kamshi yaji ya bugi hancinsa wanda ya tabbatar masa da cewa tana kitchen kenan, bai ce komai ba, ya haura sama, bayan ya ajiye Form dinan a dining table ya ɗora remote control akan takardan.
_7:55pm_
A daidai lokacin Abraham ke saukowa sanye da fararen kaya na shan iska da suka yi matukar karban chocolate skin din sa, kan dining table ya zauna, yana jiran Aysha tazo tayi serving din sa, domin sosai ya fara jin yunwa tun abincin safe, a hankali ya daga kansa ya kalli sama, a ransa cewa kila sallah take yi.
Bayan mintuna goma ya ji takun tafiyar ta, sanye take da hijab ja har kasa, yayi matukar karban farar fatar ta, tamkar wata zinariya haka ta yi kyau.
Kallon ta Abraham ke yi, maganganun da P.A yayi masa ke dawowa ƙwaƙwalwar sa, innocent face dinta ya ke kallo, ba tare da sanin sa ba, murmushi ya subuce masa, tana da sanyi sosai, yayi mamaki kwarai data samu kwarin gwiwa har haka.
Gefen sa ta tsaya tace " sannu da zuwa! Ina wuni"
Daga maka kai kawai yayi, domin bai ji abinda tace ba, kwara ina kwana yafi gane mai, Aysha bata kara cewa komai ba shiga serving din sa, bayan ta gama ta fara kokarin barin wajen.
"Hey! Sit" yace Yana nuna mata kujeran dining table, a sanyayye ta dawo ta zauna, alamu yayi mata kan taji abinci, girgiza masa tayi sannan ta motsa kananan lips dinta tace "Na koshi"
Bai kara magana ba ganin har ta fara raurau da idanu, sai da ya ci fiye da rabi sannan ya mika mata wata takarda, Domin kafin ya sauko ya shiga app dinnan, yayi typing da turanci kan bayanai abinda za a cike Form da shi, abun ya fito da amsa da turanci, ya yi coping a paper, idan ta rubuta masa, she kuma sai ya cike mata Form din da kansa.
Duk da tayi mamakin mezai yi da sunan ta, shekaran ta, da sauran personal details dinta, amma bata tambaya ba ta shiga rubuta komai a inda ya bar space gashi rubutun da Hausa wanda Hakan yayi mata sauki kwarai...
Bayan ta gama rubutuwa ta lura da wasu rubutu still da Hausa a kasan takardan "Ban san yanda zaki dauki abun ba, amma na saki a wata makaranta ta koyan turanci, inda zaki dinga zuwa juma'a asabar da Lahadi, gobe zamu je ayi miki passport idan na dawo, amma idan bakya so zaki iya fadamin"
A hankali ta dago kanta fuskar ta dauke da murmushi, kasancewar ita yake kallo yasa shi ganin murmushin, wani sanyi yaji a ransa, hannayenta ta dage alamun godiya kana tace
"Nagode sosai, Allah ya saka...."
Hannun ya ɗora a lips din sa alamun tayi shiru, saboda ya fahimci godiya take kokarin masa.
Bayan ya gama ya sha lemo sannan ya janyo Form din da abinda ta rubuta ya shiga cike mata.
Aysha kuma ta mike ta gyara dining table, sannan ta kai plate da cups da yayi amfani dasu ta wanke kana ta fito...
"sai da safe" tace tana hayewa sama, bai je komai, domin bai fahimta ba, sai bin ta da ido yayi har ta bacewa ganin sa...
Numfashi ya furzar, kana ya kai idanun sa kan dakin Madam Gloria, wani abu ya daki zuciyarsa tuno wacce mummy, domin sai Yanzu ainihin hallayen ta suka bayyana, ashe duk zaman da suke fuska biyu ce! Bai sani ba, bata kuma taɓa nuna wata alama ba, ganin ransa zai fara ɓaci yasa shi daina tunanin Madam Gloria, sannan ya raya a ransa cewa da safe kafin yaje office zai biya bank ya sanja pin account din sa, saboda a ranar data kwashe ATM din duk yana jin ta, dama pretending baccin karya yayi...
Yana jima a zaune yana sake-sake kana ya kashe duka kayan wutan dakin da plasma ya nufi dakin sa domin bacci...
*WASHEGARI*
Hudu saura mintuna takwas Abraham ya dawo, domin ya yi alƙawarin cewa yau zasu je tayi passport, cikin dan sauri-sauri yake tafiya.
Dakin sa ya shiga dake a kimtse gwanin burgewa sai kamshi ke tashi, kayan jikin sa ya cire, daura towel, sannan ya jefa wanda ya cire a laundary basket kana ya shiga wanka, mintuna goma kacal yayi ya fito ya shiga shiryawa...
Bayan ya gama ya fito, har zai leka dakin ta ya kira ta, sai kuma ya hango ta zaune a downstairs, da alama shi take jira, bayan ya gama saukowa ba tare da ya kalle ta ba yace "let's go"
Duk da bata gane abinda yace ba, amma haka ta bi bayan sa ganin ya nufi waje, sai Yanzu take jin son turanci a ranta, musamman da Abraham ke yi, domin sosai take dad'i a bakin sa...
Har zata shiga baya, taga ya buɗe mata gaban motar, ba musu ta shiga ta zauna. Wani babban gidan hoto Mai suna *INFINITY* ya kawo su, Bayan yayi parking, kusan a tare suka fito daga motar, cikin wajen suka nufa, cikin girmamawa ake karɓe su, nan mai yin passport din ya sanar dasu cewa passport takwas 3,500 hake yake yin sa...
Wani had'add'en dakin hoton aka shigar da Ita, mintuna biyar ta fito ta zauna gefen kujerar da aka tanadar wa Abraham two sitter.
Bayan an gama hada komai aka saka mata envelope, Ya mika mata, karba Aysha tayi ta ɗan buɗe ta ga yayi kyau sosai kamar dai hoto normal saboda haduwar sa.
Maimakon su koma gida sai ta ga ya nufi wani restaurant yayi musu takeaway, domin sam Yau baya son tayi girki, yana matukar ganin kokarin ta wajen iya girki da kula da gida tamkar babbar mace, at least once in the while ya kamata tana hutawa.
•••••. ••••••. •••••
MADAM GLORIA
Tafiya take cikin wani kusurmin daji mai matukar ban tsoro da abubuwan al'ajabi kala ² tun jiya take tafiya amma har yanzu bata kara so inda take so ba, ko wahala bare tsoro bata ji saboda mugun nufin daya cika zuciyar ta...
Tana cigaba da tafiya taji wata murya ta fara dariya cikin wata amo mai ban tsoro hadi da ruda ƙwaƙwalwar mutum, juye juye ta shiga yi ko zata ga mai dariya amma bata kowa ba, can kuma dif cikin wata murya da amon sa ke fidda zallan fushi taji an ce....
Share
Comment
NoorEemaan
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 55-56
Tana shiga cikin fadar bokan nan mai sunan Nandera, ta ga macizai iri daban-daban na ta shawagi a cikin fadar.
Wani sabon tsoro ne ya sake kamata, domin duk bakin halinta idan akwai halittar da take matuƙar tsoro toh bai wuce maciji ba.
Kasa gaba bare baya tayi, sai k'ak'arwa jikin ta ke yi kamar an jona electric shock, domin macizan har zagaye ta suke, ba tare da sun mata komai ba.
Wannan karon wani abu mai kama da danasanin zuwa wajen boka Nandera take, ba wai kuma saboda Allah tayi danasanin ba, sai dan tsoro.
Boka Nandera dake zaune kansa a kasa ya fara sakin wata mahaukaciyar dariya mara daɗin amo, wasu Surutai ya shiga yi tsahon Mintuna biyar sannan macizan nan suka koma wani gefe suka lafe, basu ƙara motsi ba.
Bakar fuskar sa mai dauke da kasumba abin k'yank'yami ya d'ago, sannan ya kalli Madam GLORIA da jajayen idanunsa yan ƙanana yace "karaso da baya ki shigo fada ta mai cike da abubuwa iri daban-daban, hhhhhh"
Jiki na rawa Madam GLORIA ta karaso da baya ta zauna a gaban boka Nandera kamar yadda yace.
Gaba-daya ta birkice, sai faman waiwayon macizan dake gefe take, domin gani take da ta daina kallon su zasu kawo mata sara.
"Ke nutsu! Babu abinda zasu miki sai na basu umarnin haka, hhhhhh" ya fada cikin ƙatuwar muryan sa.
Dan nutsuwa tayi, cikin dake wa ta shiga mai wasu kirari da manya- manyan kalamai. (a'uzubillah!)
Boka Nandera kuwa sai faman buɗe kafada yake cikin takama da isa hadi da jin dadi.
Bayan ta gama boka yace " hakika na jima ba a min kirari irin wannan ba, hakan yasa zan yi miki aiki mai zafin gaske, duk wahalar da kika sha shekara da shekaru wurin hallaka dan kishiyar ki yazo karshe"
"Toh ya...."
"Kada kice komai, nasan matsalar ki, na kuma san abinda kike so, saboda haka ki jira ki ga abin mamaki, ba a cika ni da tambayoyi, sannan zamu rike ki na tsawon wata Biyar da kwanaki a nan, haka ka'idar aikin yake, hhhhhh"
Azabure Madam GLORIA ta kalle shi, tana maimaita wata shidan a ranta, yayi mata mugun nisa, tamk'ar shekara dubu sittin haka take ganin su saboda muradin cika Burinta"
Dago kanta tayi domin yin magana ko zai rage watanni saboda a gaskiya wata shida yayi mata mugun nisa, sai dai tana dago kanta suka hada ido da boka ta kasa magana.
Boka kuwa ganin ya samu nasara ya shiga sakin dariya da ƙatuwar muryan sa mara daɗin ji.
*KADUNA*
Zaune Abraham yake cikin motar sa a daidai building din MM HARUNA ENGLISH ACADEMY yana jiran Aysha ta fito, haka kawai yau yaji shi ya cancanci yazo ya dauke ta, kasancewar driver ke zuwa kai ta ya kuma dauko ta, dalibai sai wucewa suke, amma bai ga Aysha ba, har ya fara kosawa da zaman, sannan ya hangota ta mirror tana tafiya Cikin nutsuwar ta.
Kasa ɗauke idanunsa daga kanta yayi, duk da cewa yau kimanin sati biyu da fara zuwa makarantar ta kenan, amma yana ganin improvment daga gare ta, musamman yanda take dagewa wurin tilawar abinda ake koya mata, duk da cewa har abubuwan yan primary one ana koya mata domin ta fi gane wa sosai, amma yana ganin kokarin ta kasancewar bata taɓa zama a ajin boko ba.
AYSHA
Sai faman kalle kalle take ta ina zata hango driver, Sam bata ma lura da motar Abraham ba, shima ya fahimci hakan, sai ya zuge glass din window ya leko da kan sa, karaf suka hada ido, zaro idanun ta tayi saboda mamaki ganin sa, domin bata taɓa kawowa a ranta cewa zai zo daukar ta ba.
Dayan bangaren ta zagaya ta shiga ba tare da tace komai ba, shima bai ce komai ba ya tada motar suka bar haraban wajen.
Bayan sun iso gida Aysha ta buɗe motar, ta saka santala-santala kafafunta kasa sannan ta waiwayo ta ɗan rusuna kanta tace
"welcome tank" (ita nufin ta so take tace weldone thanks)
Jinjina kan sa kawai yayi yana matse dariyar sa, sannan ta fita izuwa cikin gida.
Ajiyar zuciya kakarfa ya sauke a lokacin daya daina hango ta.
Wasu lokutan yakan ji wani iri musamman idan ta kama shi yana kallon ta, amma ya kasa daina kallon ta, ya sani cewa ba wani abu ke burge shi a jikin ta ba bare ace shi yake kallo, domin idan diri ne bata kamo Chinonyen sa ba, amma kuma baya kallon Nonye kamar yadda yake kallon Aysha, ya rasa dalili, sai dai a kullum idan yana tambayar kansa game da yawan kallon da yake mata, his heart always tells him that hallaci da kyawun zuciyar ta yake kallon deep inside her.
Amma abinda Abraham bai sani ba shine ya kamu da son Aysha tun daga ranar da suka fara haduwa a adaidaitasahu, a kuma ranar ne zuciyar sa ta fara bugawa domin ta.
Haka ya kwashe tsawon mintuna a motar sannan ya kashe motar ya fito, direct dakin sa ya wuce, ya fada kan gado yana tunanin rayuwar sa, kewa sosai yake ji yanzu musamman da babu wani nasa da zai gani ya ji dad'i, dan ma Aysha na gidan yana ganin Allah ne ya kawo ta cikin rayuwar sa, ta masa abubuwan da ko wani dangin sa bazai iya masa ita ba, duk da cewa yana biyan ta Albashi...
Numfashi ya furzar tuno cewa kusan wata daya rabon da mummy ta bar gidan nan kenan, "where is she?" ya tambayi kansa, sanin ba shida amsa yasa shi lumshe idanun sa yana fitar da numfashi daya-daya.
Har lau yana jin mummy a ransa, yana mata kallon uwa da bai da shi, duk da cewa bai san dalilin ta na son ganin ta kashe shi ba, amma yana kokarin matuka gurin ganin ya cire ta a matsayin uwa daya ɗora mata, domin babu wata uwa ta gari da zata zo kashe danta.
Aysha dake kitchen tana girki kuwa kusan tunani ɗaya suke yi, ita mamakin wannan abu take, ace uwa ki fita ba tare da kin damu da sanin halin da ɗan ki ke ciki ba, shi ma daya warke, bai nema ta ba, kanta ya kulle ta rasa gane kan abun nasu, ganin wannan abun bai shafe ta ba ne yasa ta ta6e baki ta cigaba da hada masa had'add'en fish pepper soup daya ji vegetable da spices, sai pure orange juice da zata hada masa.
Wanna kenan!
•••• •••• ••••
*BAYAN WATA BIYAR DA KWANA GOMA*
Cikin wadannan watannin abubuwa da dama sun faru, ciki har da zuwan Anty Sarah Gombe gidan su Aysha, ko Allah yasa mutanen su taimaka mata wajen tayata neman Abraham, domin cikin watannin nan ta sha wahala gaba-daya ta sake fita a hayyacin ta, sak'amak'on yawan mafarke-mafarken ma rasa kyau da take yi, har abun ya fara mata gizo, gaba-daya ta rasa nutsuwar ta, hakan yasa ta zo Gombe, sai dai abin mamaki duk bulayinta ta kasa gane gidan, unguwar ya sanja mata, komai ya kwance mata, amma bata hakura ba...
Kullum daddadare sai ta je kasan gada in da mahaukata da masu Bara ke kwanciya, nan take shiga Cikin su ta kwanta, washegari ta kuma cigaba da neman gidan amma bata samu ba, amma still bata hakura ba.
***. ***. ***.
*KADUNA*
"Aysha! Aysha!!"
A hankali Aysha ta waiwayo da murmushi saman fuskar ta domin ta san mai kiran ta.
Ta kara kyau, girma, da wani wayewa daya bayyana ƙarara a tare da ita, komai yanzu cikin aji da wayewar addini take yin sa, saboda mu'amala da mutane musamman yammata iri daban-daban hakan yasa komai tayi tana burge mutane, gashi yanzu ta kara ilimi sosai, turanci daidai gwargwado tana yi, tana kuma ji, kana tana tana iya rubutawa, tsakanin ta da Abraham yanzu babu musayar rubuta da takarda, ta kan yi mai magana da turanci shima idan yana bukatar abu zai fada mata da turanci.
hakika MM HARUNA ENGLISH ACADEMY sun yi kokari matuƙa wurin koya wa Aysha turanci, musamman da suka ga Abraham ya sake musu kudi...
"Aysha! Why are you so In hurry, Ina zaki haka?"
Bola da ta kasance yar ajin su ta fada. Ta su ta zo daya da Aysha sosai, duk da kasancewar Bola bayerabiya amma musulma ce, tana amfanin da sunan Yaren ta ne a makaranta, kasancewar tun tana karama da sunan aka fi kiran ta.
"Bola! my boss is coming back from Dubai today, i have to rush home so that I can made him some meals"
"Oh yeah i remember, that's nice, shall well?" Bola ta fada tana mata nuni da hanya alamun su cigaba da tafiya...
Yanda Bola tayi da hannu sai ya bawa Aysha dariya...
Nan suka cigaba da hira har suka zo wajen driver, suka yi sallama da Bola, Aysha kuwa ta shiga Mota suka nufi gida.
Tana zuwa gidan jakar makarantar ta kawai ta ajiye ta shiga kitchen, tunani tayi tunda yaje dubai kusan wata ɗaya tasan ba lallai ya samu abinci irin na nan Nigeria ba, hakan yasa tayi tunanin dafa masa abinda zai rike cikin sa sosai, had'add'en miyar efforiro tayi masa daya sha namomi da ganda, sákwárá take son Yi Amma Allah ya gani bata da karfin dakawa, hakan yasa ta tuka masa *pando yam* na leda, ai kuwa sak sákwárá haka yayi danko ya kuma yi kyau, bayan nan tayi masa pepper chicken, ta zuba komai ta jera a dining table sannan ta gyara kitchen.
Dakinta ta nufa domin yin wanka saboda har an fara kiraye-kirayen Sallah....
A gurguje tayi wanka ta shower gel wanda Abraham ya siyo mata, har yanzu bai kare ba domin bata fiye amfani da shi ba, gashi 2.5L ne gashi da kumfa sosai, ita kam bata fiye son shower gel ba, sai mita take a ranta wai sabulun nan bata son shi sai ya yi ta sa jikin mutum sulbi kamar tayi wanka da klin ko da ruwan sama.
Bayan ta iddar da sallar ta sauko falo ta zauna shiru, so take ta kira Inna amma kuma bata son damun su, saboda kafin ta tafi makaranta sun yi waya.
Har aka fara kiraye-kirayen sallar Ishaq bai zo ba, har ta kosa da zaman sannan ta damu da rashin karasowar sa har yanzu, fatan ta Allah yasa lafiya.
Kasancewar ta na da alwala ga Kuma hijab a jikin ta yasa ta mike ta koma gefe ta kalli gabas ta tada sallah, cikin sallah taji abu na dan kauri daga kitchen, amma bata motsa ba, haka ta cigaba da salla domin bazata iya katse sallar ta ba.
Daidai lokacin Abraham ya karaso gidan...
tun kafin ya shiga falon yaji kauri sosai, mamaki ne ya kama shi, yana murda kofar ya shiga yaga Aysha tsaye a gefe tana sallah a nutse, taku biyu kacal yayi Cikin falon yaji bumm!!!
Ƙaran ya fito daga kitchen, ga wuta daya fara ci bal-bal...
Cikin sauri da tashin hankali ya kalli AYSHA a tsawace yace "hey! Run, i said run outside my friend"
Amma Ina Aysha'n ka bata ko motsa ba sai sallar da ta cigaba da yi nutsuwa.
Cikin sauri ya nufi abin kashe wutar nan da ake manna wa a bangon ( fire extinguisher) ya zaro ta ya shiga fesawa cikin kitchen din, shima ya kare, wutan bai mutu ba ya sake zaro dayan ya cigaba da kashe wutan har ya mutu, sai mugun hayaki daya cika kitchen din har ma da falo, fitilar wayar sa ya kunna da kyar ya karasa shiga kitchen ɗin domin hayakin yasa baya gani sosai, murda gas din yayi zuwa off, inda ya tabbatar Aysha ta manta ne bata kashe ba, tukunyar mai dake kan gas ne yayi mugun zafi har ya kama da wuta, Allah yaso wutar bata ratsa pipe din silinder ba da tuni labari ya sha bambam.
Fitowa yayi falo ya zube kan kujerar yana sakin tari saboda hayaki daya shaka over, ya kuma gode wa Allah daya takaita.
Sai faman fadin "Thank you Jesus, Jesus is Lord yake". (Allah ya ganar da duk Wanda yake hanyar bata Ameen!)
Sai da tarin ya lafa ya d'ago kansa, a razane ya kai idanunsa inda Aysha take dazu, so his greatest surprise har yanzu tana nan hankali a kwance tana sallah...
Zaro ido yayi, "Jesus Christ" ya fada kana ya nufi wajen ta, yana zuwa daidai wajen ta tana sallame shaf'i da wutri.
Hannun ta ya ja da karfi ya mikar da ita, cikin fadan da bai san ya iya ba yace "Are You insane? Did you want to kill your self huun? da ban zo da wuri ba haka zaki bari wutar ta kama ta kona ki, bayan Kina da halin guduwa, ki tsaya all in the name of praying, wait! like are you for real?" Ya fada unbelievable yana jijjiga dan kafadar ta da karfi"
Kuka mara sauti Aysha ta sakar masa, cikin rawar murya tace "Am sorry! My religion, or i should say Islam is beyond your expectations, i have already started praying, i can't run, na yarda cewa idan yau kwanana zai rage ko na gudu ko na tsaya zan mutu, addinin Muslunci ba kamar sauran addinai bane, zan iya guduwa na katse sallar sannan na roki Allah yafiya, amma katse sallar is not Good ln Islam sai da wata Babbar hujja da zai iya fadawa Allah idan ya mutu, but na zabi na tsaya ne, domin Ina son gwada zama muslumar kwarai, jaruma kan addinin ta, zan iya sadaukar da rayuwa ta ga Muslunci and I will be happy idan na mutu ta silar hakan"
Jikin sa ne ya mutu, zubewa yayi kan cushion ya zuba mata ido kamar ya samu hoto, tabbas addini Muslunci ya girmama tunanin sa kamar yadda ta fada, suna kaunar addini su, sannan suna bada dukkanin nutsuwar su wurin yin ibada basa wasa, Musliman kwarai zasu iya sadaukar da rayuwa da dukiyarsu wurin kare addinin su.
A duk lokacin daya ji Aysha na karatun qur'anin ya kan ji tana burge shi har baya son ta daina, amma a yau saboda jarumtar ta, son addinin Muslunci ne ya mamaye ilairin zuciyar sa. (Allahu Akbar!)
Cikin mutuwar jiki ya mike bayan ya gama tunani, daf da ita yazo yace "Am sorry too for yelling at you" ya karasa cikin sanyin murya sannan ya ra6a ta gefen ta cikin sauri ya haura sama...
Yana shiga dakinsa ya cire kayan jikin sa, Sannan ya nufi toilet, shower ya sakar wa kansa, ya shiga dukan kansa zuwa murd'add'en jikinsa
sanyayyar ajiyar zuciya ya sauke, fuskar Aysha ke masa gizo, murmushi tattausa ya saki, domin hakan ba bakon sa bane cikin kwanakin nan, musamman da yayi tafiyar nan, tunanin ta yaki barin zuciyar sa, da yayi tunanin ta sai ya dinga sakin murmushi shi kaɗai, tun yana ƙaryata cewa baya kaunar ta, basu dace da juna ba, addinin su da Yaren su ba daya, ta yaya zasu so juna har ya saduda, domin har lau abubuwa uku zuwa huɗu ke hana mu cigaba a ƙasar mu, nuna kabilanci, addinin, hadi da son kai.
Bai damu da kome mutane zasu ce ba, domin abinda mutane zasu ce bazai cuce kan sa ba, tunda ba abu mara kyau yake kokarin aikatawa ba.
Cikin wata murya mai cike da shauki yace "Yes!i can't deny or hide it any more, i love her, and I'm saying this from the bottom of my heart"
ya karasa faɗa yana shafa kirjin sa..
A gurguje ya gama wankan ya shirya cikin wasu pyajams masu taushi farare masu touches din green, ya fesa body spray din NIVEA DEEP FOR MEN.
Tun kafin ya karasa sauko wa ya hango ta zaune shiru tayi tagumi, sai ta bashi tausayi, bayan ya sauko direct dining table ya nufa, domin yayi missing abincin ta sosai, gyaran murya yayi, Cikin sauri Aysha ta taso ta fara serving din sa, Bayan nan ta nufi hanyar kitchen domin hayaƙin ya gama washewa, so take ta gyara.
"Where are you going to?"
" I want to clear up the kitchen" ta fada a sanyayye
"No come back, you can't do that alone" ya fada yana kai abincin bakin sa, bayan ya gama ci sannan ya ciro wayarsa dake aljihun wandon sa ya kira wani number inda ya ce gobe da safe yana so a zo a gyara kitchen din, sannan abubuwa da suka lalace a cire a saka sababbi...
Aysha dake jin duk wayar da yake taji ya bata tausayi, domin yayi tafiya mai tsayi ya kamata ace ya huta amma gashi daga dawowarsa ba hutu zai fara kashe-kashen Kudi.
Kasa shiru tayi, tace "Am so sorry please, it was a mist...."
"Shhhh! You don't have to apologize, you did absolutely nothing, and that's how God want it, so cheers ok?"
"Ok" tace tana jinjina kan ta, Sanyi taji a ranta ganin bai yi fushi da ita ba, hakika kyawawan halayen sa na burge ta, duk da kasancewar sa ba Muslimi ba, amma yana da zuciyar musulmai kwarai masu yarda da ƙaddara.
Mikewa yayi daga dining table, ya dawo falo ya zauna yace
"come with me"
"Okay" tace tana nufar kitchen, domin ajiye kayayyakin daya ci abinci dasu, sakin baki tayi tana kallon barnan da wutar tayi a kitchen, a sanyayye ta dawo falon ta zauna.
Gyaran murya yayi yace "so tell me about religion, i mean Islam"
Share
Comment
Noor Eemaan
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM 🍓🍓
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 57-58
Cikin zallan mamaki ta kafe dashi da ido, yayin da shi ma Abraham ita ya ke kallon hadi da gyada mata kai cikin tabbaci.
Zaro beautiful eyes din ta tayi cikin mamaki, domin bata taɓa tunanin abinda zai ce kenan ba, "amma shi da ba Muslimi ba, meyasa yake son sanin abinda ya shafi addini Muslunci?"
ta fada a ranta, amma ko ba komai taji daɗi duk da bata san dalilin sa ba, amma tana son hira ko magana kan abinda ya shafi addinin Musulunci.
"You...you... mean i should tell you about my religion?" Aysha ta tambaye shi domin ta kara tabbatar wa.
"Exactly that's what I want, tell me come on" ya fada cikin k'aguwa da son ta fara gaya masa.
"Okay" Aysha tace tana dan murmushi.
Gyara zama tayi, ta saki, jikin ta tama manta cewa gaban yallabai Abraham take zaune, nan ta shiga gaya masa Meye Muslunci, abubuwa da Muslunci ya koyar, da yanda Muslimi zai tafiyar da rayuwar sa, da yanda annabawa suka bauta wa Allah, sannan da yanda Mala'iku suka bauta wa Allah, da kuma yanda yan zamanin da suka shude suka yi rayuwar su, sannan ta bashi labarin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama.
Sannan ta ɗora da bashi labarai kan rayuwar iyalan gidan sa, kissoshi dai kala-kala ta dinga bashi, a takaice komai dai wanda ya shafi addini da ta sani ta fada masa, tsikar jikin Abraham sai tashi take saboda abubuwan da take fada duk suna shiga kwakwalwar sa, suna ratsa jijiya da tsokar jikin sa, sannan sun samu muhallin zama a zuciyar sa.
Aysha kuwa sosai tayi kokarin wurin hada turancin ta domin yi masa bayanin yadda zai fahimta, domin wasu manyan kalmomi dake cikin abinda take fada masa, fassara su da turanci wuya zai yi mata, amma tayi ƙoƙarin fassara masa da sauk'ak'ak'iyyar turanci, kuma Thank God ya fahimta.
Shiru falon ya dauka, babu mai magana, domin ita Aysha har bakin ta ciwo yake mata saboda dadewar da ta yi tana Magana, idan bata yi karya ba, zata iya cewa tun da aka haife ta bata taɓa magana mai tsayi irin wannan ba, kallon agogo Abraham yayi ya ga karfe biyu saura Mintuna biyar, kenan haka suka jima suna magana bai sani ba ya fada a ransa.
Duk da yasan dare yayi, amma bazai iya yin shiru bai yi mata tambayar da ta fi makalewa a ransa ba, dan gyara murya yayi wanda hakan ya zame masa dabi'a, hakan yasa Aysha dago kanta, domin ta fahimci matuƙar yayi hakan toh akwai magana a bakin sa.
" Am.....You said every child was born as a Muslim, expect lf his parents changes his religion, how sure are you. (Kin ce ko wani d'a ko y'a a Muslim ake haifan sa sai dai iyayen sa su sanja masa addini, taya kika tabbatar da hakan)".
Murmushi mai sauti Aysha tayi tace
"Am not the one who say it, Allah subhana wata'ala said so in the Qur'an(bani na fada ba, Allah subhanahu wata'ala ne ya fada acikin kur'ani)"
Jinjina kai Abraham yayi cikin gamsuwa da amsar ta, sannan yace "one more question, you said earlier that i was born as a Muslim right, but my parents changes my religion, does that mean am a sinner, and will i go to hell? (Tambaya ta karshe, kince dazu an haife Ni a Musulmi sannan iyayena sun sanja min addini, hakan yana nufin Ni mai zunubi ne, sannan wuta zan shiga?)" Ya tambaye ta cikin iyakar gaskiyar sa, domin har ga Allah yana son sanin komai...
Gyaran wuyan hijab dinta Aysha tayi, tace "of course yes! Allah will asked you when you died, because you are no longer a kid, you re now an adult, you know what's right, so you can determine the best for yourself if Allah's will, and about you asking if you re going to hell, i can't say, because no one enters in between God and his servant, so Allah alone knows the best. (kwarai da gaske, Allah zai tambaye ka idan ka mutu, saboda yanzu kai ba karamin yaro bane, kai Babba ne, kasan abinda yake daidai, zaka iya zabar abinda yafi maka alkhairi idan Allah ya amince, sannan game ta tambayar ka ta cewa shin wuta zaka shiga idan ka mutu? Bazan ce ba, domin babu mai shiga tsakanin Ubangiji da bawan sa )"
***. ***. ***.
*SOME MINUTES LATER*
Tun bayan lokacin da Aysha ta bashi amsar karshe basu ƙara wata magana ba, sai yanzu daya dago ya kalle ta, yaga har ta zube kan kujera bacci ya dauke ta, sannan daga yanda take baccin Zai tabbatar wa mutum cewa bata shirya ba, baccin ya ɗauke ta.
Mikewa yayi ya nufi inda take, sosai baccin ya kara mata kyau murmushi yayi cikin shaukin so, a hankali yasa hannu da niyyar daukar ta zuwa dakin ta, sai kuma ya tsaya da hannun sa cak! sak'amak'on tuno maganar da suka yi, domin ya tuna Aysha tace haramun ne namiji ya taba jikin mace matuƙar babu aure a tsakanin su"
Duk da yana ganin addinin Musulunci is somehow difficult to him, domin ba a ciki ya taso ba, shiyasa yake ganin haka, but Yana son yadda komai na addinin ke da tsari gwanin sha'awa.
Ajiyar zuciya ya sauke, kana yace "my life" cikin shaukin so mai tsanani.
komawa kan kujerar ɗaya tashi a kai yayi kana ya kafe ta da ido kamar ya samu plasma.
Mintuna talatin ya dauka yana kallon ta, kana ya sauke sanyayyar ajiyar zuciya hadi da lumshe sexy eyes din sa.
Bai san yadda Zata dauka ba, bai san ko zata amince ba, but he just have to spell it out ko zai samu sassauci a zuciyar sa, bai taɓa sanin cewa ya kamu da son ta ba sai tafiyar nan da yayi Dubai domin duba hark'ok'in kasuwanci sa.
Haka ya dinga tunane-tunane har bacci mai daɗin gaske ya dauke shi kan kujerar...
*5:20am*
Tarrr ya bude idanun sa da suka bata awannin a rufe, idanun sa ya kai kan kujerar da Aysha ke kwance tana bacci, kiran sallar ya ji a masallacin dake unguwar, lumshe ido yayi, sannan ya kara buɗe wa, mikewa yayi tsaye, inda take kwance ya nufa, ya tsugunna gaban kujerar da take kai, har ya mika hannu da niyyar taɓa ta domin ta tashi sai kuma ya fasa.
Kujerar da take kwance ya shiga dan bugawa a hankali, a dan firgice ta farka tana yamutsa fuskar ta, saboda wuyan ta daya k'age sakamakon irin kwanciyar da ta yi.
"Wake up! It's time for your prayer" ya fada cikin whisper.
Idanun ta a rufe cikin baccin da bai gama sakin ta ba ta gyada masa kai, ganin ta farka yasa Abraham mikewa ya hau sama domin zuwa dakin sa.
A hankali ita ma Aysha ta mike ta hau saman, cikin sauri ta watsa ruwa sannan ta daura alwala ta fito ta sanja kaya, hijab ta saka Sannan ta tada kabbara..
Bayan ta iddar ta yi addu'o'in ta, daga nan ta dauki qur'anin ta.
Ta bude Surah Al-mu'minun (The believers) kenan zata yi Bismillah taji an turo Kofar...
Dago kanta tayi taga Abraham ne, sai hakan ya ɗan bata mamaki amma bata nuna ba, jikin kofa ya jingina bayan sa, sannan ya hard'e hannun sa a kirji yace "sorry for distracting you, i just wanna listen to the recitation of the Quran if you don't mind "
Mamaki sosai Abraham ke bata tun jiya, duk da tana farinciki da kulawar sa ga addinin musulunci, amma bata san dalilin sa na son Sanin abinda ya shafi Musulunci ba, murmushi ta k'ak'aro tace "okay"
Sannan ta yi Bismillah ta fara karatu cikin sanyayya kuma zazzak'ar Muryar ta mai daɗin amo.
Mutumin kuwa wani dad'i sosai ya shiga ratsa shi, yayin da nishadi ya mamaye zuciyar sa, sai faman Kada kai yake, domin daɗin da yake ji daga karatun qur'anin nan ya fiye masa dadin busar sarewa.
Bayan Mintuna arba'in Aysha ta rufe qur'anin ta sannan tayi addu'a kamar kullum ta shafa, ta dago kenan ta hango shi tsaye kamar dai dazu, ita zuciyar ta naga karatun har ga Allah ta manta yana dakin har yanzu.
Kanta a kasa tace "good morning sir"
"Morning!" Yace, bai kara cewa komai ba ya bar dakin...
Da kallo Aysha ta bishi sannan ta mike ta ajiye qur'anin ta, dakinta ta shiga gyarawa kafin gari ya karasa wayewa ta shiga kitchen...
*WASHEGARI*
FRIDAY MORNING
# Unforgettable day
Abraham ke tsaye a kofar gidan Alhaji Umaru kwangila yana k'wank'wansawa...
Mai gadi ya leko,
ya kuwa shaida Abraham hakan yasa shi washe baki sannan ya gaishe shi, hannu Abraham ya bawa mai gadi suka gaisa sannan yace yayi wa mai gidan magana.
Da sauri mai gadi ya tafi domin iskar da sakon Abraham, ya kuwa tari Sa'a ya samu Alhajin zaune a general falo Yana breakfast da Hajiyar sa, nan mai gadi ya sanar masa cikin girmamawa, duk da Alhaji yayi mamakin dalilin zuwan Abraham wajen shi domin ya ga baya shiga harkan kowa a unguwar, amma yace mai gadi ya shigo dashi setting room kafin ya gama breakfast, cikin sauri mai gadi ya fita, can ya shigo da Abraham kamar yadda Alhaji ya bada umarni.
Mintuna takwas da zaman Abraham, Alhaji ya shigo, ya mika wa Abraham hannu suka gaisa sannan cikin zolaya yace Allah yasa ba laifi yayi ba Abraham yazo kamashi...
Murmushi Abraham yayi, sannan yayi gyaran murya cikin harshen Ingilishi yace " I don't know how to say it, buh I... i want to convert to Islam, basan ta yaya zan fara ba, ina son na shiga musulunci, shiyasa nazo domin ka fadamin yadda zan yi in shiga, domin ban san kowa a unguwar nan ba bayan kai"
"Allahu Akbar!"
"Allahu Akbar!!"
"Allahu akbar!!!"
Alhaji Umaru kwangila ya dinga fada cikin maɗaukakin farin ciki, siririn medicated glass din sa ya zare kana yace "come, come , come here" ya fada yana ware wa Abraham hannun sa...
Rungume shi Alhaji ya yi, farin cikin shi yaki boyuwa, nan ya dage ya shiga gaya wa Abraham wasu abubuwan cikin addinin Musulunci, sannan yace masa babban masallacin da yake zuwa sallar juma'a nan zasu je, da zarar an iddar da salla zai karbi shahada, da haka Abraham ya fito daga gidan, bayan Alhaji ya jadadda masa cewa kafin su tafi yayi wanka, sannan yayi niyya a zuciyar sa cewa wanna wakan shiga addinin Musulunci zai yi.
Alhaji na komawa cikin gidan ya shiga fadawa matar sa da y'ayy'en sa, farin ciki sosai suka yi, sannan suka yi masa murnar samun rahamar Allah.
***. ***. ***.
*2:pm*
Abraham ke zaune a farfajiya babban masallacin cikin motar Alhaji Umaru kwangila, kasancewar a motar sa suka zo, ko ina yayi shiru ga duban jama'a dake salla cikin jam'i gwanin burgewa.
Yana cikin motar yana kallon su tsigar jikin sa sai tashi take, musamman da yake jin muryan liman dake karanta Surah At-tin cikin raka'ar ƙarshe, abu yaji yana biyo kuncin sa, hannu yasa ya shafa, yaga hawaye ne, cikin sauri ya share, sannan ya cigaba da kallon su har suka idar da sallah'n.
Bayan liman ya gama addu'o'i an shafa, sannan yace "A saurara" hakan yasa wasu mutane dake shirin fita suka dakata da fitar da suke da niyyar yi.
"Alhamdulillah! Godiya ta tabbata ga Allah madaukakin sarki mai kowa mai komai, mai yin yadda yake so da kuma lokacin da ya so, a yau mun karu, eh mun karu kwarai, domin wani bawan Allah ne zai karbi Muslunci a yanzu haka, Kuma yana cikin masallacin nan"
kabbara aka saka bakunan mutane a washe saboda farin ciki, duk da Abraham yace kada a bari mutane su sani domin shi saboda Allah ya shiga musulunci, basai duniya ta sani ba, amma ina liman ya kasa hakuri saboda farin ciki, hakan yasa dole ya sanar wa jama'a.
"Nan liman ya shiga addu'a yace "ya Allah ka shiryar da wadanda suke hanyar bata kamar Yadda ka ganar da wannan bawan naka"
"Ameen!!!"
Jama'ar wajen suka hada baki Wurin fadin hakan, Alhaj Umaru kwangila yana kusa da liman yana ta faman sakin murmushi.
Nan liman yace aje mota a shigo dashi, ai fa nan jama'a suka yi zuga wurin zuwa dauko shi, bawan Allah Abraham na zaune cikin mota ya ga an bude kofar mota kowa so yake rike shi domin kai wa liman, da kallo Abraham ke bin su, ya ga fuskar su dauke da murmushi, son addinin Musulunci na kara ratsa zuciyar sa, ashe haƙa muslumai ke son mutane? Ya fada a ransa.
Har gaban liman suka kai shi sannan kowa ya zauna ana kallon shi wasu har video suke daukan shi ciki har da Alhaji Umaru.
"Sannu yaro dan albarka, welcome to Islam" liman ya faɗa fuska a sake.
"Thank you sir"
Abraham yace cikin girmamawa, da dan murmushi a fuskar sa.
"Can You tell us why actually you want to convert to Islam, and is any one dragging or forcing you into Islam?"
Cikin husky voice dinsa dake a dake yace "i just love Islam, i mean I love everything about it, and no one is dragging me into Islam, am doing it for the seek of Allah, i love Allah, and I love everything concerning Islam too".
Liman yace "Attak-bir ya jama'a"
Jama'a suka ce "Allahu Akbar!"
Domin duk suna jin abinda Abraham yace kasancewar akwai manyan speaker da Mic🎤 dake gaban inda Abraham ke zaune.
Kallon sa liman yayi yace "repeat after me"
Jinjina kai Abraham yayi, liman ya kara cewa "say! Ash-hadu Allah ilaaha illallaahu, wa Ash'hadu anna Muhammadan rasulullah"
Ta cikin loudspeaker Muryar Abraham ya kara de ko ina, ya fara fadin kalimatul-shahada kenan ya kasa karasa wa saboda kalmomin sun yi masa girma domin bai saba jin irin su ba, hakan yasa liman ya dinga faɗa masa kalma bayan kalma, tsaf kuwa ya fada, yana gama faɗa wasu hawayen dadi masu sanyi suka zubo masa.
Nan mutane suka saka kabbara.
Liman ya kara cewa wani suna yake so, nan yace "i have no choice" domin bai san sunan muslumai ba, bare ya zaba.
Liman yace "if you permit me, i will make a choice of better name for you"
"Okay, i will really appreciate it sir" Abraham ya fada.
Murmushi liman yayi yace "As from today your name is Abubakar Assadik"
"Abubakar Assadik" Abraham ya maimaita sunan domin sunan ya kwanta masa a rai.
Nan liman yace " Masha Allah, Alhamdulillah, You re now a Muslim. Congratulations Abubakar assadiq, welcome to the religion of peace"
Nan mutane suka shiga yi masa murna, hadi da fatan alkhairi, Abraham tsakayau yake jin sa tamkar an cire masa wani abu mai nauyin gaske a kan sa, wani iska na ni'imar Allah ke ratsa shi...
Bayan duk mutanen sun
watse, ya rage daga liman, Abraham da Alhaji Umaru, nan dai liman ya koya masa yan kananan abubuwa irin su alwala, wankan tsarki da sauran abubuwa masu sauƙin fahimta, tsaf kuwa Abraham ya rike, ya kuma ja Abraham sallar azahar sallar domin ya fara ganewa, daga nan ya bashi wasu littattafai na addini masu fassara da turanci, sannan ya karbi numbern Abraham din kan ya ware lokaci ya dinga zuwa suna karatu, da haka suka yi kyakkyawar sallama zuciyar kowa fal farin ciki...
Bayan sun iso gida, Alhaji Umaru kwangila ya kara mai yan wa'azi, sannan ya roki Abraham alfarman kan yazo yaci dinner yau a gidan sa, mutuncin Alhaji Umaru kwangila da Abraham ke gani yasa shi kasa musu masa, da haka suka yi sallama kowa ya shiga gidan sa...
Aysha dake tsaye tana jera warmers a dining table ta dago kanta ganin an turo Kofar general falo, Abraham ta ga ya shigo, abin da ya bata mamaki jin yace
"Assalamualaikum"
Kasa amsawa tayi, sai bin fuskar sa tayi da kallo, saboda wani haske mai ban sha'awa ɗaya mamaye tun daga kafar sa har izuwa fuskar sa, wanda ba komai bane face hasken Musulunci.
Murmushi Abraham yayi sannan ya kara cewa "Assalamualaikum" Hadi da nufo inda take tsaye...
Share fisabilillah.
Comment for more typing...
NoorEemaan
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 59-60
Daf da ita ya matso ya hura mata iskan bakin sa, sannan ya kara cewa "Assalamualaikum" a karo na uku.
Dan firgigit tayi daga tunanin da ta faɗa kana cikin cracking voice tace "wa...wa...'alaikum Sa...salam"
sai tayi kasa da kanta, bambarakwai haka taji a lokacin da yayi sallama,
domin abu ne wanda bai taba yi ba.
A hankali Abraham ya dire gwiwowin sa a kan tiles, kana ya kafe ta da kyawawan idanunsa, jikin Aysha ne ya fara rawa, ganin namiji babba a gaban ta kan guiwar sa, sannan ita da ta kasance yar aiki a gidan sa meyasa zai dinga yi mata haka?
Ta lura yanayin sa da komai nasa ya sauya, musamman a yan kwanakin nan.
"Ụwammmmm!" Abraham ya ja sunan da wani salo da bai san ya iya ba. (Ụwam yana nufin Duniya ta da Yaren igbo)
Aysha kuwa lumshe ido tayi, har wani bubud'ewa kofofin gashin jikin ta su ke yi saboda yadda sunan ya ratsa ko wani sassa na jikin ta, sannan taji sunan ya burge ta ainun ya kuma tsaru a kunnuwan ta duk da bata san ma'anar sa ba.
"Will you be my wife?" Ya tambaye ta kamar zai sakar mata kuka, domin ya kai gejin da bazai iya cigaba da boyewa ba.
Jin abinda yace ne yasa Aysha saurin ware idanun ta, ta kafe shi da kallo cikin rudu da daurewar kai.
Abraham kuwa kansa yake jinjina mata cikin tabbacin abinda ya fada, sannan ya ɗan ƙara motsa wa daf da ita sosai yace "will You marry me please, i love You. Since from the First day we meet in the tricycle my heart beat for you, don't say no please"
ya karasa yana kama kasan skirt din jikin ta ya damke, kamar ba Abraham ba, mamakin kansa yake.
Wani sabon mamakin mai tarin yawa ne ya sake lullube Aysha, murza idanun ta tayi, domin gani take kamar gizo idanunta ke mata, anya Abraham ne wanna, ko dai ya sha wani abu ne, ita Aysha indo yake so, yar aikin gidan sa, gaba-daya kanta ya kulle ta ma rasa wani tunani zata yi.
"Please say yes! i mean every single word i said to you, i have never sees you as a house girl or look down on you. I always sees you as a special human in my life, which my mouth can't explain or describe how special you are in my heart, please accept the love that i have for you"
Buɗe baki Aysha tayi tana kallon sa, ta zama so speechless, "yanzu wanna had'add'en guy ke Sona haka" ta fada a ranta yayinda wani hawaye Mai sanyi hadi da dariya suka zo mata a tare, sai tayi saurin rufe bakin ta cikin kunya ta ruga up stairs da gudu.
Da kallo Abraham ya bita yana sakin sanyayyar ajiyar zuciya, at least yaji sanyi a ransa, ko da bata son sa, amma kuma bata nuna tsanar sa ba, zai kuma yi iya kokarin sa Wurin ganin ya koya mata son sa, bazai kara mistake din da ya yi kan Nonye ba, a yanzu idan yana son abu zai fada, domin rashin fada zai iya sa ka rasa dama ko ka makara wurin fadawa wa wacce kake so ko wanda kake so.
Gashin sa ya shafa, sannan ya bi bayan ta cikin sauri.
*AYSHA*
Sam bata ji haushi da ya ce yana son ta ba, duk da bata san ko tana son shi ko a'a ba, amma taji wani sanyi a lokacin daya furta mata yana son ta.
"Ko hakan na nufin nima ina son sa?" Ta tambayi kanta a shagwabe.
Sai kuma ta ta6e baki kamar zata yi kuka, tuno suna da bambancin Addini.
"koda muna son juna bazamu iya auren ba saboda bambancin Addinin mu" ta fada a hankali cikin sanyin guiwa.
Dadai lokacin Abraham ya karaso bakin kofar dakin ya tsaya, yayi knocking har sau uku, jin shiru Bata ce komai ba, sai ya cije lips dinsa Yana kokarin yin dariya, domin abin na dan bashi dariya da mamaki a lokaci daya, ganin wai shi ke bin Aysha saboda ta bar shi ta tafi, ba kaɗan ba kuma yake jin daɗin yanayin da suke ciki.
Dan gyara murya yayi yace "Please come and serve me, am starving"
(Ki zo ki zuba min abinci, yunwa nake ji)
Yana fadin haka ya bar wajen, bai gama sauka daga step case din ba ya ga ta buɗe kofar ta fito, amma bai juyo ba, gudun kar ya kara mata kunya.
Aysha kuwa Sam bata so ta ji mutum na jin yunwa, duk da cewa ita din ba mai son abinci bace sosai.
Kamar mara gaskiya haka ta sauko sum sum ta nufi dining table inda yake zaune ta fara serving din shi, kanta a kasa sai jin idanun sa take yana yawo a kanta, hakan yasa hannun ta ke rawa.
Abraham kuwa kunya ba abu bane Mai burge shi a da, amma yana fara gani a fuskar AYSHA sai hakan ya zama ado dake kara masa son ta.
***. ***. ***.
Da misalin ƙarfe uku da da Mintuna arba'in Aysha ta iddar da Sallar la'asar ta fito, domin fara hada girkin dare, saboda girki mai dan ɗaukan lokaci take son yi yau.
Har ta fara taka matatakalar bene domin saukowa, but to her greatest surprise bayan Abraham ta hango tsaye ya fuskanci gabas yana sallah.
"Mahammadur Rasulullah! Kamar sallah na ga yana yi" Tace cikin zunzurutun mamaki.
Murza idanun ta, saboda gani take gizo yake mata, ga wani mugun kwarjinin daya yi mata gaba-daya ya cika idanun ta, duk da bata ga fuskar sa ba.
Da biyu, uku haka ta dinga tsallake matatakalar benen har ta sauko, tama manta babu kyau tsayawa gaban mai sallah, haka ta masa kuri da ido bata kuma motsa ba na tsawon seconds...
Can kuma kamar wacce aka mitsila ta fasa wani uban ihu, sannan kamar da a sigar waka ta fara cewa "wallahi shi ne, sallah yake, sallah yake, wayyo dad'i, ya zama Muslimi, maza idar da sallar ka bani labari, yaushe hakan ta faru bani da labari, alhamdulillah ya Allah"
sai ta dire gwiwowin ta a kasa ta yi sujjada tana godewa Allah, a gaba-dayan Rayuwar ta zata iya cewa babu ranar da yayi mata sugar kamar wannan, gefe ta koma ta dinga kallon yadda yake sallar a nutse kamar wanda ya jima a musulunci, ita kadai sai murmushi take na zallan farinciki.
Bayan Abraham ya idar da sallah, yayi addu'o'in sa da Yaren igbo da kuma turanci tunda bai fara koyan addu'ar Larabci ba, ya kuma yi imanin babu Yaren da Allah baya ji, sannan zai amsa in sha Allah.
Bayan ya shafa, ya juyo gare ta suka hada ido, ya ga fuskar ta dauke da murmushi, ya mayar mata da martani.
Sannan ya fada a ransa cewa har abada bazai taba manta wanna kyakkyawar murmushi da ya gani a fuskar ta yau ba sakamakon sallar da ta ga yana yi.
"Ụwammmmm! Nayi kuskure a sallar ko? I knew kina kallona, Please gayamin in gyara" ya fada yana kallon ta.
Wani abu mai girma gaske ta ji ya shiga zuciyar ta game da shi, wani tausayin sa taji musamman da tune din da ya yi magana.
"You did everything perfect, but when, how comes you didn't tell me? Ooh my God am so so happy for you gaskiya..." ta fada tana kallon sa
Mikewa yayi yana murmushi, sannan yace " Thanks you! is a long story, i will explain to you"
Shiru tayi, sai yanzu kunyar ihun da zu ya kamata, ya fahimci hakan sai kawai yayi murmushi dama yasan murna ne yasa ta dinga ihu daya kusan fasa dodon kunne sa.
Nan ya shiga gaya mata komai da komai, dadi sosai taji a ranta, ta kuma yi masa murna fiye da zaton mai zato hadi da addu'ar fatan alkhairi.
Dago kansa yayi ya kalle hadi da cewa
"tell me more about Islam, it make me feels happy" domin Yasan ta hakan ne kaɗai zata saki jikin ta su yi hira, saboda ya fahimci duk wata magana daya shafi addini tana son sa.
Aysha kuwa ta samu abinda take so, nan ta shiga gaya masa yadda zai yi ibadar sa tsarkake, saboda ta kara masa son addinin Musulunci sai ta ɗora da
cewa
"There's something you need to know, Christian always said Jesus which Isa Alaihissalam is the son of God, or they even called him God subhanallah! Which is prohibited.
Allah is alone, he has no son, no mother, no father not even a sibling.
(Akwai abinda ya kamata ka sani, kiristoci na yawan cewa Annabi Isa dan Allah ne, har ma su ce Allah, subhanallah!
Hakan haramun ne.
Allah shi kadai ne, ba shi da ɗa, ba shi da uwa, bashi da uba, ballantana kanne ko yayye)
Jesus is the servant of Allah, and if any Muslim doesn't believe in Jesus as the prophet of Allah there fore he's not a good Muslim.
(Annabi Isa annabin Allah ne, sannan duk wani Muslimi da bai yarda da Annabi Isa a matsayin annabi Allah ba, toh bai cika Muslimin kwarai ba)
What christians don't understand about Muslims is...
They thought we don't love Jesus, but the fact is we love him and we believe in Jesus as the prophet of God subhana wata'ala, not his son or God.
(Abinda kiristoci basu gane game da Muslimai ba shine, sun ɗauka bamu son annabi isa, amma gaskiyar maganar shi ne, muna son annabin isa, mun yarda cewa Annabi Isa Alaihissalam annabin Allah ne, amma bamu yarda cewa shi Allah ne ko dan Allah ba).
We also have four books Allah send to his prophet's which is
TAURAH
INJI
ZABUR
QUR'AN
(Sannan akwai litattafai guda hudu da Allah ya saukar ga Annabawan sa, sune...
INJILAH
ATTAURAH
ZABURA
ALQUR'ANI).
You see taurah was revealed by Musa Alaihissalam.
(Kaga an saukar da attaurah ga Musa Alaihi salam)
Inji, which Is the bible was revealed by Isa Alaihissalam who christian Called Jesus.
(An saukar da injila ga Isa Alaihissalam, wanda kiristoci ke kira Yesu)
Zabur was revealed by Dawood Alaihissalam.
(An saukar da zaburah ga Dauda Alaihissalam)
Qur'an was revealed by Muhammadur Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallama.
(An saukar da Alkur'ani ga Muhammadur Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallama).
Did you know among these four books, the christian has changes the inji which is the bible, if you go into the old statements there's a huge difference with the new statement now, they change almost everything, there's a chapter in the bible which i actually can't remember in the old statements, they describe how Jesus perform ablution and also faced the Qibla to pray, buh if you go through the new statement now it has totally changed, they edit those part which is also prohibited.
(Ko kasan cewa cikin littafan nan guda hudu, kiristoci sun sanja wurare da dama a injila, wanda suke kira da bible, idan ka duba ainihin injila da sabon da kiristoci suka yi akwai bambamce-bambamce masu yawa, sun sanja kusan komai.
Akwai wata surah a injila na ainihi wanda bazan iya tuna surar ba, an kwatanta yadda Annabi Isa yayi alwala sannan ya fuskanci alkibla yayi Sallah, amma idan ka duba sabon bible din yanzu an cire wanna wajen, wanda hakan haramun ne).
Numfashi Aysha ta ja Sannan ta sauke ajiyar zuciya, murmushi dauke a fuskarta ta cigaba da cewa
"i don't know how to say it, but am deeply happy you are now a Muslims, but there is one thing am afraid of..."
(Basan yadda zan fada ba, but ina matukar farin ciki daka dawo Muslimi yanzu, amma akwai abu guda da nake tsoro....)
"what's that?" Abraham yace yana dage girar sa daya.
(Menene shi?")
"How about your mum, ain't you afraid if she hears you re a Muslims now?"
(akan mahaifiyar ka ce, baka tsoro idan taji ka zama Muslimi yanzu).
Murmushi Mai ciwo Abraham yayi, sannan ya ce "shhhh!" You no nothing about Abraham's life, when the right time comes i will tell you ok"
("Shhhh! Baki san komai game da rayuwar Abraham ba, idan lokacin yayi zan gaya Miki kinji)
"Okay" tace tana jinjina kanta a sanyayye, yayin da kanta ke sake daure wa, ta ma rasa gane wanna wani irin uwa da da ne haka, domin bata taɓa gani ba Irin su ba...
*ƁAYAN KWANA ƊAYA*
Bayan Abraham ya gama breakfast ya kalli Aysha dake gefen sa a zaune, domin har ta saba matuƙar ta zuba masa abinci sai yasa ta zauna har ya gama, tun tana mita a ranta kullum yasa ta zauna kamar matar sa har ta daina.
As usually gyaran murya yayi yace "Ụwammm!"
Dagowa tayi ta kalle shi ba tare da tace komai ba.
A nutse cikin turanci ya fara cewa"ya kamata ki fadawa mummyn ki magana ta, ina so ayi bikin mu cikin satin nan, na gaji da zama cikin kaɗaici, ina so na gina sabuwar rayuwa mai cike da farin ciki, kuyi magana da ita Please, Ni Kuma zan sanar da Alhaji Umaru kwangila ya shige min gaba, domin bazan sanar da dangin iyayena yanzu ba saboda hakan zai iya bani matsala, ba kuma na son a samu jinkirta wurin mallakar ki, Please kuyi waya ki sanar mata komai game dani matukar kina son rayuwa Dani, zan ji amsa daga gareki idan na dawo, ki kula da kanki, i love You" Yana fadin haka ya bar dinner area zuwa waje domin tafiya aiki.
A sanyayye Aysha ke kallon sa har ya bace mata, gaba-daya tsoro ya kamata, bata san me Inna zata ce ba, har tsoron sanar mata take, tunanin zuwa wajen Anty bintu tayi hakan yasa ta mike da hanzari ta yi clearing dining table din, ta kai plates da cups daya yi amfani kitchen ta wanke, duk da Akwai mai wanke-wanke amma bata saba ayi amfani da abu ta dinga kallon sa ba tare da ta tsaftace shi ba .
Sama ta hau ta Sanja hijab dinta sannan ta nufi gidan Alhaji Umaru kwangila.
Bayan ta shiga gidan ta tarar da Hajiyar gidan ta fito da alama unguwa zata je, har kasa Aysha ta tsugunna ta gaida ta, a sake Hajiyar ta amsa sannan tace "tashi ki shiga, yar'uwar taki tana ciki"
"Toh, a dawo lafiya" Aysha tace, sannan ta nufi cikin gidan.
Tana shiga ta tarar da Anty bintu tana ƙoƙarin shiga dakin ta.
Dakin na ta suka shiga, suka zauna.
Cikin sanyin murya ta gaishe da Anty bintu, daga yanayin gaisuwar Anty bintu ta fahimci akwai abinda ke damun Aysha.
Bata yi kasa a guiwa ba, cikin kulawa ta tambaye ta mene ne ke damun ta.
Nan Aysha ta shiga sanar wa anty Bintu da komai har da auren ta da Abraham ke son yi.
Bayan ta gama mata bayani, anty bintu ta yi murmushi hadi da girgiza kanta tace "Indoooooo!!! Shine kike tada hankalin ki har haka, na zata wani abun ne, duk da akwai tarin kalubale, amma ki kwantar da hankali ki, yanzu ki kira Inna anan kiyi mata bayani mu ji me zata ce"
.
A razane Aysha ta kalli Anty Bintu, cikin Muryar wacce kuka ke son kwace Mata tace"wallahi tsoro nake ji Addah Bintu, bana son fushin Inna, ke kiyi mata magana Please"
Girgiza kai anty Bintu tayi, cikin son karfafa Aysha tace "karki ji tsoro, zan iya yin magana da Inna, amma ba zan yi hakan ba, zan fi so taji komai daga bakin ki, ki saka wa zuciyar ki jarumta, in Sha Allah alkhairi zamu je, amma kafin nan bari na tambayi ki, kina son shi"
Tambayar tayi matuƙar ba wa Aysha kunya, sai ta fada jikin Anty bintu tana cuwuikuye ta...
"Ke me haka? Oya tashi ki gayamin" Anty bintu tace tana danne dariyar ta.
Cikin shagwaba da sakalci tace"toh Ni ban san ko ina son shi, amma kuma Ban tsane shi ba"
Dariya anty Bintu tayi, ta lura Aysha na son Abraham, Amma yarinta bai bari ta fahimci hakan ba.
"Maza kira Inna toh" anty Bintu ta fada.
A sanyayye Aysha ta yi dialing number gabanta na bugawa, ringing hudu tayi sannan taji Inna ta daga, saboda tsoro ta ma rasa me zata yi sai ta fashe da kuka...
Salati Inna ta sa, cikin tashin hankali jin tilon yarta na kuka ta shiga tambayar ta damuwar ta.
Ganin haka yasa anty bintu ta bar dakin domin ta basu damar yin magana yanda ya kamata...
"Inna! kiyi hakuri, basan yadda zaki dauki maganar ba, ban zubar da ko ƙwayar tarbiyyar da kika bani ba, wanda nake aiki a gidan su, wannan da bai da Lafiya kwanaki"....
Katse ta Inna tayi da cewa "eh na gane shi, Meya faru?"
Nan Aysha ta shiga gayamata komai tiryen-tiryen har karshen, sannan ta ɗora da cewa auren ta yake son yi cikin satin nan.
Maimakon taji Inna tayi magana, sai ta ji kit ta yanke wayar.
Sabon kuka Aysha ta saka, wani sabon tsoro ne ya sake lullube ta.
Bayan Anty Bintu ta shigo, cikin kuka ta gaya mata yanda suka yi da Inna, dan jim tayi cikin wani tunani sannan tace "Aysha karki ƙara kiran ta, ki bari Inna tayi tunani kin ji ko, in Sha Allah zaku mallaki juna" da haka ta rarrashe ta hadi da karfafa mata gwiwa sannan ta koma gida.
Sukuku haka ta wuni, ko girkin dare bata iya fitowa ta yi ba, daga ta yi sallah sai ta koma gado ta kwanta.
•••••••••••••••••••••••••
Bayan Abraham ya dawo da kusan awa daya, tana ji yana neman ta amma tayi lamo kan gado bata ko motsin kirki, yazo ya bubbuga kofar shiru bata amsa ba, hankalin shi ne bai kwanta ba, domin yasan bata fita ko ina, cikin sauri ya sauka ka kasa, wuri mai gadi domin tambayar shi ko Aysha ta fita ne.
A kuma daidai lokacin ne kiran Inna ya shigo wayar Aysha, gabanta yayi wata mahaukaciyar bugawa, ta kasa daukan wayar har ta katse, kira na biyu ya sake shigowa, idanunta ne ya tara ruwan hawaye yayin da hannun ta ke rawa, cikin sanyin jiki ta daga kiran hadi da ƙara wayar a kunnen ta...
_ban wani nutsu nayi editing ba, kila ku ga typing errors_🤒
Share fisabilillah🙏
Comments☑️
Noor Eemaan
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
_idan na ga ruwan comments, zan sake baku sabon Page zuwa dare_
Chapter 61-62
*INNAH*
"Na amince miki auren sa matuƙar kina son sa, kin dauka nayi fushi dake ne?"
Sai tayi murmushi irin nasu manyan mutane ta cigaba da cewa "ko daya ban yi fushi ba diyata, illah ina bukatar nazari da kuma tunani mai zurfi, shiyasa kike na katse wayar ba tare da nace miki komai ba. Kasancewar ya Musulunta ba yana nufin bashi da damar auren mace muslima ba, dan mutum ya na sabon Musulmi ba shi ke nufin Wanda ya dade a Muslunci ya fishi ba, babu Wanda ya fi wani a wajen Allah sai wanda ya fishi tsoron sa, dan haka bazan hana ki ba, basan me Allah ke nufi da yayi haduwar ku ba, ba kuma zan shiga tsakani ba, na kuma san ko baffan ki na raye zai amince matuƙar shi yaron ya cika sharuddan zama miji a gareki, duk da basan halayen sa ba, na san bazaki zabi wanda bai dace ba matsayin abokin tarayyar ki ba, na yarda da tarbiyyar ki, ina kuma kyautatawa zaton ya zama miji abin alfahari agareki, ko yan'uwa baffan ki bazan gaya wa ba saboda tun lokacin da baffan ki ya mutu da suka kwashe abinda ya bari ban kara gani karfa kowa da niyyar zuwa duba mu ba, sannan zasu iya cewa basu amince da yaron ba, dan haka bazan aika musu ba, na amince Miki, Allah ya tabbatar da alkhairi"
Hawaye Masu sanyi ne suka zubo wa Aysha, tana matuƙar kaunar Innar ta, hawayenta ta share ta ce"Nagode Inna, Nagode sosai"
"Godewa Allah indon baffan ta, sannan ina so ki zo gobe, ki taho gida, bayan an Daura auren sai ki koma gidan sa, duk da abun yazo a kurarren lokaci, akwai bukata ayi miki kayan daki komai kankantar su"
"Toh Inna zan fada masa" Aysha ta fada. Sannan ta ɗora da cewa
"Inna ina y'a'yana suke?"
"Suna lafiya, na aike su nan makota gidan jauro su siyo min barkono"
"Inyeee! Yarana sun girma har sun fara zuwa aike" Aysha ta fada cikin farin ciki.
"Eh mana, kamar yadda maman su ta girma ba, ita ma zata yi aure " Inna ta fada a zolaye.
Cikin kunya Aysha ta katse wayar tana dariya...
Wani kuzari ne ya zo mata, hakan yasa ta diro daga kan gadon ta bude kofa ta fito, a kuma lokaci Abraham ya shigo da saurin sa domin sake k'wank'wansawa mata kofa, in kuwa bata buɗe ba zai balla kofar, tunda mai gadi ya sanar da shi cewa tana ciki, da wanna tunanin ya taho, daga nesa ya hango ta tana murmushi, hakan yasa ya tsaya, ya daura hannunsa sa a kugu yana balla mata hararan wasa hadi da cije lips dinsa...
Dariya tayi cikin jin kunya, kan kujerar dake general falo ya koma ya zauna.
Bayan itama ta gama saukowa ta zo gefen sa ta tsaya.
Cikin k'ank'anuwar murya ta zo gefen sa ta tsaya tace "Am so sorry please"
"Dago idanunsa da suka dan Sanja kala yayi, sannan ya sake balla mata harara, dariya ta fashe da shi ganin yadda ya dage yana hararar ta.
Nan Abraham ya lalace wurin kallon ta, sai da ta ga bai da niyyar kallon ta yasa ta gimtse dariyar ta.
Dan bata fuska yayi yace "why did you stop laughing, it fits you more than you expect, please continue"
Dan murmushi mai sauti ta saki ba tare da tace komai ba, kujerar dake gefen sa ya bubbuga sannan yace
"sit"
Ba musu ta zauna, Kallon ta yayi yace"oya tell me, did you spoke to mum?" (Yana nufin Inna)
"Yes i did"... Nan ta shiga gayamasa yadda suka yi da Innar.
fadin murna da farin ciki da Abraham ya tsinci kansa a ciki bata lokaci ne, ya kuma godewa Allah da bai samu matsala ta bangaren mahaifiyar abar kaunar sa ba, saura dangin sa, zai kuma shako kansu bayan daurin aure, saboda basu san ya ma karbi Muslunci ba, Bama ya saka Madam GLORIA a lissafin sa.
Gyaran murya yayi yace "ki fadawa mummy ta bar kayan dakin nan, duk da nasan al'adar ku ce, amma nima a al'adar mu iyayen mace Bata kayan daki sai dai mijin yayi, dan haka ba sai an kawo miki komai ba, ki bata hakuri Please"
Jinjina masa kai tayi alamun "toh" tana kallon sa ta gefen ido with so much admiration saboda ya iya wa mutum magana, Sam baya magana anyhow.
Nan dai suka tsara yanda abin zai kasance, ya kuma ce driver zai kai ta gobe da sassafe, duk da yayi niyyar zuwa kai ta da kansa amma hakan bazai samu ba saboda meeting Mai muhimmanci dazai gudanar a goben.
Bayan sun gama maganar, cikin marairaicewa tace "Please can you do me a favour?"
(Dan Allah zaka iya min wata Alfarma)
"Yes sure!" Ya fada yana mayar da hankalin sa gareta dan jin abinda zata ce.
Cikin turanci tace" Please ina son bayan bikin mu y'ay'ana su dawo zama tare damu, ina cikin tsananin kewar su, bazan iya sake nesa da su ba, karka ce a'a dan Allah"
maganganun ta sun tuno mai da iyayen sa hadi da Nonye da cikin jikin ta.
Murmushi yayi yace "Any thing for you my life, nayi alkawarin zama uba a gare su, zan maye musu gurbin uban da suka rasa, so cheers okay"
Cikin farin ciki tace " yeeeeh! thank you so much, thank you."
"You deserve ụwamm"
Dan lumshe ido tayi cikin jindadin sunan, ta kuma sa a ranta cewa zata tambaye shi ma'anar sunan wata rana.
***. ***. *** .
*Bayan kwana biyu*
Yau kwana ɗaya da daura auren Aysha da Abraham, wanda Alhaji Umaru kwangila ya shige wa Abraham gaba tamkar shi ne mahaifin sa.
A ranar da aka daura auren farin cikin Abraham bazai mitsaltu ba.
Tun karfe takwas Abraham ya tura motoci guda shida dauko masa amaryar sa, a matuƙar kage yake saboda kwana biyun da bata gidan ba ƙaramin kewar ta yayi ba.
Sannan duk da cewa basu yi gayyata saboda abun yazo a kurarren lokaci, amma duk da hakan yan'uwa Inna da kuma abokan arziki sun zo.
Bayan motocin ɗaukan amarya sun zo, aka fito da akwatunan da Abraham yayi mata guda takwas cike da kayan alfarma, tun ana yi jibi yasa akai kayan Gombe, ita kanta Aysha bata san da kyan ba sai da ta zo, kowa na kauyen ya6a lefen yake saboda babu wata diya a kauyen da aka taɓa yi mata lefe irin wannan.
Nasiha mai shiga jiki Inna tayi mata, sannan Anty Bintu ta shigo tace Inna ta hanzar ta motoci na waje tuni amarya kaɗai ake jira.
Tana kuka, Inna na kuka, yan biyu na kuka rabuwa da zasu yi Anty Bintu ta saka ta a mota, suka taho, babu yanda bata roki Inna kan ta bata su Ammar ta tafi dasu domin ta sanar da Abraham ya kuma amince amma Inna tace ina ta taba jin an yi haka, ta tafi daya baya zasu zo.
***. ***. ***.
Tun tana kuka cikin motar har tayi shiru tana tunani, ji take kamar Bata taba rayuwa a gidan Abraham ba, sai ganin take kamar yau ne farkon zuwan ta, ita kanta jin kanta take kamar wata sabuwar hallita ce ita.
Tun tana tunanin har bacci ya dauke ta, kasancewar lafiyayyun motoci ne yasa ba'a dauki lokaci ba suka iso Kaduna gidan Abraham.
An sauya kalar fenti gidan, da ɗan gyaran da ba a rasa ba, kowa sai santin gidan yake.
Abinci kala-kala da Abraham ya biya kudi masu yawa a wani had'add'en restaurant aka kawo, nan kowa ya dibi abinda yake so iya ransa, wasu har da zuba wa a leda zasu tafi da shi.
da misalin karfe hudu da rabi duk suka mike domin komawa Gombe, dama bada niyyar kwana suka zo ba, addu'a da fatan zaman lafiya suka yiwa Aysha sannan duk suka fito farfajiya gidan inda motoci ki jiran su domin mayar da su, aka bar Anty Bintu da Aysha kawai a gidan.
Bayan magriba itama anti Bintu tayi mata nasiha hadi da sallama sannan ta tafi saboda tana kyautata zaton Abraham na hanya, gidan ya rage saura Aysha
Da masu aiki biyu kacal mata, sai mai gadi da driver, da kuma mai gyaran farfajiya gidan, saboda duk ya sallami wadanda Madam GLORIA ta kawo domin bai ga amfani tara su da ta yi ba, gashi bata gidan.
Anty Bintu bata jima da tafiya ba Abraham yayi shigo, direct dakin ta ya nufa, domin yasan tana nan, ga dakin ya sha gyara sosai, ya kuwa same ta zaune a tsakiyar gado ta rufe fuskar ta da veil.
Wata dariya ce ta zo masa ganin ta a lullube, saboda abu ne wanda bai taba gani ba, kasancewar baya daga cikin al'adar su, sai ya ga abin ya mai wani iri.
Aysha kuwa da ta ji dariyar sai ta yaye mayafin a hankali tana cuno baki, gimtse dariyar sa yayi, sannan ya dawo kusa da gadon ya zauna.
Cikin turanci yace
"Meyasa kike rufe fuskar ki haka?"
"Hakan al'adar mu ce, ko wacce amarya idan aka kai ta gidan miji sai an rufe fuskar ta, shi kuma ango ya zo ya bude" ta karasa tana turo bakin shagwaba.
Jinjina kansa yayi alamun gamsuwa sannan yace "is like na ji wanna kalmar a wajen Alhaji Umaru, he was like Ango, where is your amaraya"
Fashewa Aysha tayi da dariya saboda yadda yayi magana da harshen sa na Igbo gashi ba Hausa yake ji ba.
"Why Are You laughing?"
Ya tambaye ta yana taya ta dariyar.
"It's called amarya, not amaraya"
"Ohh!" Yace yana dafe kansa.
Sannan yace "Meye ma'anar hakan"
Tace "amarya means bride, while Ango means groom"
"Wow! I will like to speak Hausa too" ya fada.
"That's nice, and i'm sure you will love it" Aysha tace tana murmushi.
Haka dai suka cigaba da hirar su ta masoya har karfe tara sannan Abraham ya kalle ta, cikin so mai tsanani yace
"Get up let's perform abulution"
(tashi muyi alwala)
Kasancewar Alhaji Umaru ya fada masa komai da sabbin aure ke yi.
Ta ɗan yi mamaki jin abinda yace domin bata taɓa tunanin ya san da hakan ba, ba ta ce komai ba taje tayi alwala, ta fito ta tarar ya shimfida sallaya, hijab dinta ta saka ya shiga jansu sallah.
Hakika Abraham yayi matuƙar kokari wurin ganin cewa ya yi sallar yadda ya kamata, duk da cewa bai dade a Muslunci ba, amma ya yi kokari, har Aysha ta yaba masa a ranta.
Yaso yi mata tambayoyi kan abinda ya shafi addini Kamar yadda Alhaji ya fada masa angwaye nayi, amma ya kasa, domin bai san me zai ce ba, saboda yasan cewa Aysha ta yi masa nesan zango a karatun Addini.
AYSHA ta fahimci hakan, saboda ta kara masa karfin guiwa sai ta ce
"yi min tambaya kaza"
Shi kuma sai ya maimaita abinda tace matsayin tambaya yake mata, ita kuwa a ladabce ta shiga bashi amsa, abin yayi matuƙar kayatar dashi.
Bayan nan ya mike ya shiga toilet ya sakar wa kansa ruwa mai sanyi, nishadi na ratsa zuciyar sa domin ya mallaki abar kaunar sa, ya dauki mintinan ashirin sannan ya fito sanye da bathrobe, kallon Aysha yayi ya watsa mata dan ruwan wankan hannun sa yace "it's your turn now, go and take your bath".
Murmushi tayi, Jiki a sabule ta mike, haka kawai take jin faduwar gaba da mutuwar jiki, tana daf da shiga banɗaki ta ji yace
"Ụmammmm!"
Juyowa tayi tana Fuskantar shi, cikin kulawa yace "why Are You so cold?"
Murmushi ta k'ak'aro hadi da girgiza kanta sannan ta shige toilet din.
Abraham kuwa numfashin ya furzar sannan ya cire bathrobe din ya daura towel a kugun sa, baya ra'ayin shafa mai, hakan yasa ya fesa body spray masu k'amshi da oil perfume.
Ajiyar zuciya ya yi, yana tunanin yadda kaddara ta haɗa shi da Aysha, da irin kalubale kala-kala daya fuskanta, da musuluntar da yayi, da auren su da Aysha, komai dai ya dinga dawowa brain din sa tamkar Film, sai gani yake kamar ba a kansa duk wadannan abubuwa Ya faru ba, ya dawo wani sabon mutum, domin tabbas Abraham din da ba shi bane na yanzu.
A hankali Aysha ta buɗe kofar banɗakin, kasancewar bathrobe ne a jikin ta baby pink, shaf ta manta bata dauki hijab ba, ga kayan jikin ta sun fada a ruwan toilet, hakan yasa bata da wani zabi daya wuce ta sa bathrobe, amma ta rasa yadda zata yi ta fito gaban Abraham a haka...
Ta bude kofar ta ga idanun sa a lumshe, sai ta ɗauka yana bacci ne, hakan yasa sadaf-sadaf Kamar mara gaskiya ta nufi inda ta ajiye hijab dinta dake gefen Abraham da niyyar ta ɗauka.
Ta sa hannu ta dauka kenan ta ji ya rike hannun ta hadi da janyota, ta kuwa fado a jikin sa, zazzaro idanu Aysha ta shiga yi, yayin da bugun zuciyar ta ya karu.
Cikin ƙoƙarin danne dariyar sa yace
"zaki mun wayo ko?"
K'ala ta gaza cewa, Abraham kuwa ya sake holding dinta so tight ta yadda bazata iya kwace kanta ba, ajiyar zuciya mai karfe ya sauke, wani dadi da bazai misaltu ba ya dinga ji, ganin Aysha a shimfide a kirjin sa, is the most sweetest thing he has ever came across with, ga wani kamshi mai sanyin dad'i da ke fita daga jikin ta yana ratsa hancin sa, gashin kanta irin na fulanin usul ya shafa, bai yarda cewa wannan uban gashin na ta bane, ya zata kari tayi, hakan yasa cikin shakakiyyar murya yace
"is this your natural hair?"
Jinjina masa kai tayi domin magana ma bata jin zata iya, bayanta ya shiga shafawa a hankali daya sa jikin Aysha daukan rawa, tausayi da dariya ta bashi a lokaci ɗaya, bai yi expecting wanna tsoro daga gareta ba, domin ita din ba budurwa bace a tunanin sa, sannan hakan ta sanar dashi.
Da zai iya, daya barta ba tare da yayi mata komai ba, amma ya kai gejin da ba zai iya hakura ba, kusan shekara biyu yayi hakuri.
cikin kunne ta ya sa harshen shi ya latsa sannan ya ce
"relax babe, i will be gentle ok"
Kamar mai shirin kuka ta gyada masa kai, tana ƙoƙarin danne tsoron ta, sai dai hakan na neman gagarar ta.
Lallaba ta ya shiga yi, domin a tunanin sa ya dauka ko tsahon mijin ta baya bi da ita a hankali ne yasa take a tsorace haka, kashe wutar dakin yayi, sai dim light daya bari, Sannan ya zare towel din jikin sa ya cillar, bathrobe din jikin ta ya cire mata, sannan cikin so da kauna mai tsanani ya haɗe bakinsu waje ɗaya...
Tun yana yi a hankali har ya dawo kissing dinta a zafafe kamar zai cire mata baki, Aysha kuwa numfashin ta ne ya dauke na wucin gadi kana ya dawo.
Ganin yana ƙoƙarin cire mata dan bakin ta yasa ta sa dan ragowar karfinta ta fisge bakin ta Hadi da fashe masa da kuka.
Sam Abraham baya jin ta, kara janyota yayi ya shiga bata wasu zafaffan romance Daya kusan haukata Aysha, domin ƙwaƙwalwar ta ya gagara dauka.
A lokacin da Abraham ke ƙoƙarin su zama abu ɗaya, sai dai bai iya addu'ar saduwa da iyali ba, abin mamaki, duk da halin da Aysha ke ciki bai hanata karanta addu'ar a ranta ba, domin koyi ga Annabi (S.A.W)
•••••••••••
A karo na uku Abraham ke ƙoƙarin neman hanyar sa, amma ya rasa, hakan ya yi matuƙar daure masa kai, Aysha kuwa har ta gaji da kuka saboda wuya.
Cikin fitar hayyaci Abraham ya rike kafadunta, yace "why are you so tight? Why?
meyasa kike a matsayin budurwa har yanzu, Bayan kina da ya'y'a biyu, what are you hiding from me, ki gayamin, gayamin nace" ya faɗa a tsawace.
Kasa magana tayi, sai kuka take tana girgiza masa kai.
"I said..." Kasa karasa maganar yayi saboda hango sakar nan mai dauke da sunan NONYE a wuyan ta yana kyalli, wayar sa dake gefen bed ya mika hannu da sauri ya kunna fitilar sannan ya haska wuyan ta domin ya tabbatar da abinda ya gani, gaban sa ne yayi wata mahaukaciyar bugawa, tunanin kala-kala ne suka zo brain din sa a lokacin daya.
Hannu yasa ya damki Sarkan ya kura mai ido tsahon Mintuna kamar yana neman wani abu a jikin sarkan, tabbas bazai taba mantawa ba, bazai taɓa manta wanna sarkan ba, domin shi da kansa ya sa aka ƙera wa NONYE Sarkan nan a Dubai.
" How comes Sarkan nan yazo wajen ta?" tunanin dake ta yawo a brain din sa kenan.
Dago kanta yayi da hannun sa, sannan ya kafe ta da jajayen idanunsa, a tsawace yace "now tell me, ta yaya kika samu wanna Sarkan, kina so na cire yarda da nake dashi a kanki ko? ki gayamin nace, wacece ke!"
"ki gayamin, who are you?"
saboda tsawar da yayi gashi kuma dare ne, hakan yasa sau uku Muryar sa ta amsa kuwwa a dakin.
Kuka mai sauti Aysha ta saka ga wani mugun tsoran sa daya shige ta yanzu, gaba-daya ya firgice, ya sanja mata, gashin kansa hadi da na jikin sa duk sun mimmik'e ga jijiyoyin kansa da suka fito rudu-rudu, cikin rawar baki gwanin tausayi tace...
Share fisabilillah
Comment
Noor Eemaan
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
_idan na ga ruwan comments, zan sake baku sabon Page zuwa dare_
Chapter 61-62
*INNAH*
"Na amince miki auren sa matuƙar kina son sa, kin dauka nayi fushi dake ne?"
Sai tayi murmushi irin nasu manyan mutane ta cigaba da cewa "ko daya ban yi fushi ba diyata, illah ina bukatar nazari da kuma tunani mai zurfi, shiyasa kike na katse wayar ba tare da nace miki komai ba. Kasancewar ya Musulunta ba yana nufin bashi da damar auren mace muslima ba, dan mutum ya na sabon Musulmi ba shi ke nufin Wanda ya dade a Muslunci ya fishi ba, babu Wanda ya fi wani a wajen Allah sai wanda ya fishi tsoron sa, dan haka bazan hana ki ba, basan me Allah ke nufi da yayi haduwar ku ba, ba kuma zan shiga tsakani ba, na kuma san ko baffan ki na raye zai amince matuƙar shi yaron ya cika sharuddan zama miji a gareki, duk da basan halayen sa ba, na san bazaki zabi wanda bai dace ba matsayin abokin tarayyar ki ba, na yarda da tarbiyyar ki, ina kuma kyautatawa zaton ya zama miji abin alfahari agareki, ko yan'uwa baffan ki bazan gaya wa ba saboda tun lokacin da baffan ki ya mutu da suka kwashe abinda ya bari ban kara gani karfa kowa da niyyar zuwa duba mu ba, sannan zasu iya cewa basu amince da yaron ba, dan haka bazan aika musu ba, na amince Miki, Allah ya tabbatar da alkhairi"
Hawaye Masu sanyi ne suka zubo wa Aysha, tana matuƙar kaunar Innar ta, hawayenta ta share ta ce"Nagode Inna, Nagode sosai"
"Godewa Allah indon baffan ta, sannan ina so ki zo gobe, ki taho gida, bayan an Daura auren sai ki koma gidan sa, duk da abun yazo a kurarren lokaci, akwai bukata ayi miki kayan daki komai kankantar su"
"Toh Inna zan fada masa" Aysha ta fada. Sannan ta ɗora da cewa
"Inna ina y'a'yana suke?"
"Suna lafiya, na aike su nan makota gidan jauro su siyo min barkono"
"Inyeee! Yarana sun girma har sun fara zuwa aike" Aysha ta fada cikin farin ciki.
"Eh mana, kamar yadda maman su ta girma ba, ita ma zata yi aure " Inna ta fada a zolaye.
Cikin kunya Aysha ta katse wayar tana dariya...
Wani kuzari ne ya zo mata, hakan yasa ta diro daga kan gadon ta bude kofa ta fito, a kuma lokaci Abraham ya shigo da saurin sa domin sake k'wank'wansawa mata kofa, in kuwa bata buɗe ba zai balla kofar, tunda mai gadi ya sanar da shi cewa tana ciki, da wanna tunanin ya taho, daga nesa ya hango ta tana murmushi, hakan yasa ya tsaya, ya daura hannunsa sa a kugu yana balla mata hararan wasa hadi da cije lips dinsa...
Dariya tayi cikin jin kunya, kan kujerar dake general falo ya koma ya zauna.
Bayan itama ta gama saukowa ta zo gefen sa ta tsaya.
Cikin k'ank'anuwar murya ta zo gefen sa ta tsaya tace "Am so sorry please"
"Dago idanunsa da suka dan Sanja kala yayi, sannan ya sake balla mata harara, dariya ta fashe da shi ganin yadda ya dage yana hararar ta.
Nan Abraham ya lalace wurin kallon ta, sai da ta ga bai da niyyar kallon ta yasa ta gimtse dariyar ta.
Dan bata fuska yayi yace "why did you stop laughing, it fits you more than you expect, please continue"
Dan murmushi mai sauti ta saki ba tare da tace komai ba, kujerar dake gefen sa ya bubbuga sannan yace
"sit"
Ba musu ta zauna, Kallon ta yayi yace"oya tell me, did you spoke to mum?" (Yana nufin Inna)
"Yes i did"... Nan ta shiga gayamasa yadda suka yi da Innar.
fadin murna da farin ciki da Abraham ya tsinci kansa a ciki bata lokaci ne, ya kuma godewa Allah da bai samu matsala ta bangaren mahaifiyar abar kaunar sa ba, saura dangin sa, zai kuma shako kansu bayan daurin aure, saboda basu san ya ma karbi Muslunci ba, Bama ya saka Madam GLORIA a lissafin sa.
Gyaran murya yayi yace "ki fadawa mummy ta bar kayan dakin nan, duk da nasan al'adar ku ce, amma nima a al'adar mu iyayen mace Bata kayan daki sai dai mijin yayi, dan haka ba sai an kawo miki komai ba, ki bata hakuri Please"
Jinjina masa kai tayi alamun "toh" tana kallon sa ta gefen ido with so much admiration saboda ya iya wa mutum magana, Sam baya magana anyhow.
Nan dai suka tsara yanda abin zai kasance, ya kuma ce driver zai kai ta gobe da sassafe, duk da yayi niyyar zuwa kai ta da kansa amma hakan bazai samu ba saboda meeting Mai muhimmanci dazai gudanar a goben.
Bayan sun gama maganar, cikin marairaicewa tace "Please can you do me a favour?"
(Dan Allah zaka iya min wata Alfarma)
"Yes sure!" Ya fada yana mayar da hankalin sa gareta dan jin abinda zata ce.
Cikin turanci tace" Please ina son bayan bikin mu y'ay'ana su dawo zama tare damu, ina cikin tsananin kewar su, bazan iya sake nesa da su ba, karka ce a'a dan Allah"
maganganun ta sun tuno mai da iyayen sa hadi da Nonye da cikin jikin ta.
Murmushi yayi yace "Any thing for you my life, nayi alkawarin zama uba a gare su, zan maye musu gurbin uban da suka rasa, so cheers okay"
Cikin farin ciki tace " yeeeeh! thank you so much, thank you."
"You deserve ụwamm"
Dan lumshe ido tayi cikin jindadin sunan, ta kuma sa a ranta cewa zata tambaye shi ma'anar sunan wata rana.
***. ***. *** .
*Bayan kwana biyu*
Yau kwana ɗaya da daura auren Aysha da Abraham, wanda Alhaji Umaru kwangila ya shige wa Abraham gaba tamkar shi ne mahaifin sa.
A ranar da aka daura auren farin cikin Abraham bazai mitsaltu ba.
Tun karfe takwas Abraham ya tura motoci guda shida dauko masa amaryar sa, a matuƙar kage yake saboda kwana biyun da bata gidan ba ƙaramin kewar ta yayi ba.
Sannan duk da cewa basu yi gayyata saboda abun yazo a kurarren lokaci, amma duk da hakan yan'uwa Inna da kuma abokan arziki sun zo.
Bayan motocin ɗaukan amarya sun zo, aka fito da akwatunan da Abraham yayi mata guda takwas cike da kayan alfarma, tun ana yi jibi yasa akai kayan Gombe, ita kanta Aysha bata san da kyan ba sai da ta zo, kowa na kauyen ya6a lefen yake saboda babu wata diya a kauyen da aka taɓa yi mata lefe irin wannan.
Nasiha mai shiga jiki Inna tayi mata, sannan Anty Bintu ta shigo tace Inna ta hanzar ta motoci na waje tuni amarya kaɗai ake jira.
Tana kuka, Inna na kuka, yan biyu na kuka rabuwa da zasu yi Anty Bintu ta saka ta a mota, suka taho, babu yanda bata roki Inna kan ta bata su Ammar ta tafi dasu domin ta sanar da Abraham ya kuma amince amma Inna tace ina ta taba jin an yi haka, ta tafi daya baya zasu zo.
***. ***. ***.
Tun tana kuka cikin motar har tayi shiru tana tunani, ji take kamar Bata taba rayuwa a gidan Abraham ba, sai ganin take kamar yau ne farkon zuwan ta, ita kanta jin kanta take kamar wata sabuwar hallita ce ita.
Tun tana tunanin har bacci ya dauke ta, kasancewar lafiyayyun motoci ne yasa ba'a dauki lokaci ba suka iso Kaduna gidan Abraham.
An sauya kalar fenti gidan, da ɗan gyaran da ba a rasa ba, kowa sai santin gidan yake.
Abinci kala-kala da Abraham ya biya kudi masu yawa a wani had'add'en restaurant aka kawo, nan kowa ya dibi abinda yake so iya ransa, wasu har da zuba wa a leda zasu tafi da shi.
da misalin karfe hudu da rabi duk suka mike domin komawa Gombe, dama bada niyyar kwana suka zo ba, addu'a da fatan zaman lafiya suka yiwa Aysha sannan duk suka fito farfajiya gidan inda motoci ki jiran su domin mayar da su, aka bar Anty Bintu da Aysha kawai a gidan.
Bayan magriba itama anti Bintu tayi mata nasiha hadi da sallama sannan ta tafi saboda tana kyautata zaton Abraham na hanya, gidan ya rage saura Aysha
Da masu aiki biyu kacal mata, sai mai gadi da driver, da kuma mai gyaran farfajiya gidan, saboda duk ya sallami wadanda Madam GLORIA ta kawo domin bai ga amfani tara su da ta yi ba, gashi bata gidan.
Anty Bintu bata jima da tafiya ba Abraham yayi shigo, direct dakin ta ya nufa, domin yasan tana nan, ga dakin ya sha gyara sosai, ya kuwa same ta zaune a tsakiyar gado ta rufe fuskar ta da veil.
Wata dariya ce ta zo masa ganin ta a lullube, saboda abu ne wanda bai taba gani ba, kasancewar baya daga cikin al'adar su, sai ya ga abin ya mai wani iri.
Aysha kuwa da ta ji dariyar sai ta yaye mayafin a hankali tana cuno baki, gimtse dariyar sa yayi, sannan ya dawo kusa da gadon ya zauna.
Cikin turanci yace
"Meyasa kike rufe fuskar ki haka?"
"Hakan al'adar mu ce, ko wacce amarya idan aka kai ta gidan miji sai an rufe fuskar ta, shi kuma ango ya zo ya bude" ta karasa tana turo bakin shagwaba.
Jinjina kansa yayi alamun gamsuwa sannan yace "is like na ji wanna kalmar a wajen Alhaji Umaru, he was like Ango, where is your amaraya"
Fashewa Aysha tayi da dariya saboda yadda yayi magana da harshen sa na Igbo gashi ba Hausa yake ji ba.
"Why Are You laughing?"
Ya tambaye ta yana taya ta dariyar.
"It's called amarya, not amaraya"
"Ohh!" Yace yana dafe kansa.
Sannan yace "Meye ma'anar hakan"
Tace "amarya means bride, while Ango means groom"
"Wow! I will like to speak Hausa too" ya fada.
"That's nice, and i'm sure you will love it" Aysha tace tana murmushi.
Haka dai suka cigaba da hirar su ta masoya har karfe tara sannan Abraham ya kalle ta, cikin so mai tsanani yace
"Get up let's perform abulution"
(tashi muyi alwala)
Kasancewar Alhaji Umaru ya fada masa komai da sabbin aure ke yi.
Ta ɗan yi mamaki jin abinda yace domin bata taɓa tunanin ya san da hakan ba, ba ta ce komai ba taje tayi alwala, ta fito ta tarar ya shimfida sallaya, hijab dinta ta saka ya shiga jansu sallah.
Hakika Abraham yayi matuƙar kokari wurin ganin cewa ya yi sallar yadda ya kamata, duk da cewa bai dade a Muslunci ba, amma ya yi kokari, har Aysha ta yaba masa a ranta.
Yaso yi mata tambayoyi kan abinda ya shafi addini Kamar yadda Alhaji ya fada masa angwaye nayi, amma ya kasa, domin bai san me zai ce ba, saboda yasan cewa Aysha ta yi masa nesan zango a karatun Addini.
AYSHA ta fahimci hakan, saboda ta kara masa karfin guiwa sai ta ce
"yi min tambaya kaza"
Shi kuma sai ya maimaita abinda tace matsayin tambaya yake mata, ita kuwa a ladabce ta shiga bashi amsa, abin yayi matuƙar kayatar dashi.
Bayan nan ya mike ya shiga toilet ya sakar wa kansa ruwa mai sanyi, nishadi na ratsa zuciyar sa domin ya mallaki abar kaunar sa, ya dauki mintinan ashirin sannan ya fito sanye da bathrobe, kallon Aysha yayi ya watsa mata dan ruwan wankan hannun sa yace "it's your turn now, go and take your bath".
Murmushi tayi, Jiki a sabule ta mike, haka kawai take jin faduwar gaba da mutuwar jiki, tana daf da shiga banɗaki ta ji yace
"Ụmammmm!"
Juyowa tayi tana Fuskantar shi, cikin kulawa yace "why Are You so cold?"
Murmushi ta k'ak'aro hadi da girgiza kanta sannan ta shige toilet din.
Abraham kuwa numfashin ya furzar sannan ya cire bathrobe din ya daura towel a kugun sa, baya ra'ayin shafa mai, hakan yasa ya fesa body spray masu k'amshi da oil perfume.
Ajiyar zuciya ya yi, yana tunanin yadda kaddara ta haɗa shi da Aysha, da irin kalubale kala-kala daya fuskanta, da musuluntar da yayi, da auren su da Aysha, komai dai ya dinga dawowa brain din sa tamkar Film, sai gani yake kamar ba a kansa duk wadannan abubuwa Ya faru ba, ya dawo wani sabon mutum, domin tabbas Abraham din da ba shi bane na yanzu.
A hankali Aysha ta buɗe kofar banɗakin, kasancewar bathrobe ne a jikin ta baby pink, shaf ta manta bata dauki hijab ba, ga kayan jikin ta sun fada a ruwan toilet, hakan yasa bata da wani zabi daya wuce ta sa bathrobe, amma ta rasa yadda zata yi ta fito gaban Abraham a haka...
Ta bude kofar ta ga idanun sa a lumshe, sai ta ɗauka yana bacci ne, hakan yasa sadaf-sadaf Kamar mara gaskiya ta nufi inda ta ajiye hijab dinta dake gefen Abraham da niyyar ta ɗauka.
Ta sa hannu ta dauka kenan ta ji ya rike hannun ta hadi da janyota, ta kuwa fado a jikin sa, zazzaro idanu Aysha ta shiga yi, yayin da bugun zuciyar ta ya karu.
Cikin ƙoƙarin danne dariyar sa yace
"zaki mun wayo ko?"
K'ala ta gaza cewa, Abraham kuwa ya sake holding dinta so tight ta yadda bazata iya kwace kanta ba, ajiyar zuciya mai karfe ya sauke, wani dadi da bazai misaltu ba ya dinga ji, ganin Aysha a shimfide a kirjin sa, is the most sweetest thing he has ever came across with, ga wani kamshi mai sanyin dad'i da ke fita daga jikin ta yana ratsa hancin sa, gashin kanta irin na fulanin usul ya shafa, bai yarda cewa wannan uban gashin na ta bane, ya zata kari tayi, hakan yasa cikin shakakiyyar murya yace
"is this your natural hair?"
Jinjina masa kai tayi domin magana ma bata jin zata iya, bayanta ya shiga shafawa a hankali daya sa jikin Aysha daukan rawa, tausayi da dariya ta bashi a lokaci ɗaya, bai yi expecting wanna tsoro daga gareta ba, domin ita din ba budurwa bace a tunanin sa, sannan hakan ta sanar dashi.
Da zai iya, daya barta ba tare da yayi mata komai ba, amma ya kai gejin da ba zai iya hakura ba, kusan shekara biyu yayi hakuri.
cikin kunne ta ya sa harshen shi ya latsa sannan ya ce
"relax babe, i will be gentle ok"
Kamar mai shirin kuka ta gyada masa kai, tana ƙoƙarin danne tsoron ta, sai dai hakan na neman gagarar ta.
Lallaba ta ya shiga yi, domin a tunanin sa ya dauka ko tsahon mijin ta baya bi da ita a hankali ne yasa take a tsorace haka, kashe wutar dakin yayi, sai dim light daya bari, Sannan ya zare towel din jikin sa ya cillar, bathrobe din jikin ta ya cire mata, sannan cikin so da kauna mai tsanani ya haɗe bakinsu waje ɗaya...
Tun yana yi a hankali har ya dawo kissing dinta a zafafe kamar zai cire mata baki, Aysha kuwa numfashin ta ne ya dauke na wucin gadi kana ya dawo.
Ganin yana ƙoƙarin cire mata dan bakin ta yasa ta sa dan ragowar karfinta ta fisge bakin ta Hadi da fashe masa da kuka.
Sam Abraham baya jin ta, kara janyota yayi ya shiga bata wasu zafaffan romance Daya kusan haukata Aysha, domin ƙwaƙwalwar ta ya gagara dauka.
A lokacin da Abraham ke ƙoƙarin su zama abu ɗaya, sai dai bai iya addu'ar saduwa da iyali ba, abin mamaki, duk da halin da Aysha ke ciki bai hanata karanta addu'ar a ranta ba, domin koyi ga Annabi (S.A.W)
•••••••••••
A karo na uku Abraham ke ƙoƙarin neman hanyar sa, amma ya rasa, hakan ya yi matuƙar daure masa kai, Aysha kuwa har ta gaji da kuka saboda wuya.
Cikin fitar hayyaci Abraham ya rike kafadunta, yace "why are you so tight? Why?
meyasa kike a matsayin budurwa har yanzu, Bayan kina da ya'y'a biyu, what are you hiding from me, ki gayamin, gayamin nace" ya faɗa a tsawace.
Kasa magana tayi, sai kuka take tana girgiza masa kai.
"I said..." Kasa karasa maganar yayi saboda hango sakar nan mai dauke da sunan NONYE a wuyan ta yana kyalli, wayar sa dake gefen bed ya mika hannu da sauri ya kunna fitilar sannan ya haska wuyan ta domin ya tabbatar da abinda ya gani, gaban sa ne yayi wata mahaukaciyar bugawa, tunanin kala-kala ne suka zo brain din sa a lokacin daya.
Hannu yasa ya damki Sarkan ya kura mai ido tsahon Mintuna kamar yana neman wani abu a jikin sarkan, tabbas bazai taba mantawa ba, bazai taɓa manta wanna sarkan ba, domin shi da kansa ya sa aka ƙera wa NONYE Sarkan nan a Dubai.
" How comes Sarkan nan yazo wajen ta?" tunanin dake ta yawo a brain din sa kenan.
Dago kanta yayi da hannun sa, sannan ya kafe ta da jajayen idanunsa, a tsawace yace "now tell me, ta yaya kika samu wanna Sarkan, kina so na cire yarda da nake dashi a kanki ko? ki gayamin nace, wacece ke!"
"ki gayamin, who are you?"
saboda tsawar da yayi gashi kuma dare ne, hakan yasa sau uku Muryar sa ta amsa kuwwa a dakin.
Kuka mai sauti Aysha ta saka ga wani mugun tsoran sa daya shige ta yanzu, gaba-daya ya firgice, ya sanja mata, gashin kansa hadi da na jikin sa duk sun mimmik'e ga jijiyoyin kansa da suka fito rudu-rudu, cikin rawar baki gwanin tausayi tace...
Share fisabilillah
Comment
Noor Eemaan
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 63-64
Cikin in-in na Aysha tace "Ni..ni...ni... Ba kowa bace, sannan bana boye maka komai, ba san komai ba ga me da sarkan nan ba" ta karasa cikin kuka mai ban tausayi.
"Tell me, ta yaya sarkan nan ya zo wuyan ki?" Abraham ya kara tambayar ta cikin tsawa domin ya fara loosing control.
"A dakin Baffana na dauka kafin ya rasu, dan Allah ka sakar min wuya, You re hotting me, wayyo baffana da na ji maganar ka da hakan bata faru ba" Aysha ta fada tana kuka sosai, domin bata manta lokacin da baffa yace Kada ta ɗauki sarkan nan ba.
Cikin daurewa kai ya maimaita kalmar "Baffa!' sannan yace "Who's baffa?"
"My father, but he's dead!" ta karasa cikin kuka sosai har wani shidewa take, musamman daya sanja mata lokaci ɗaya, ka kallon idanun sa bata son yi saboda tsoro, domin yanayin sa ya fi kama da na mai gushewar hankali.
Doga ta zaune yayi yana sakin wuyan ta, Sannan ya haɗe jikin su wajen daya ya matse ta cikin faffad'ar kirjin sa, dumin fatar jikin su na ratsa ta juna.
"I...i....i... Oh Allah! am confused, i don't know what to say, Please gayamin komai, i mean everything concerning ta yadda sarkan nan ya zo wajen ki"
Kara shigewa jikin sa tayi ba tare da ta san tana hakan ba, cikin sheshekar kuka tace
"ranar da bazan taba mantawa ba itace sha biyar ga watan Oktoba (October) shekarar dubu biyu, muna zaune da yamma Ni, Baffana, da Inna ta.
Sai muka ga wata mata ta shigo cikin gidan mu, daga ganin matar yare ce, cikin turanci tace tana son yin fitsari, duk cikin mu babu mai jin turanci, sai baffana dake ji kaɗan-kadan, ya kalle ni yace na zuba mata ruwa a buta tayi tsarki, bayan na zuba na mika mata, ta karba, Sannan ta shiga banɗakin...
Ta ɗauki wasu Mintuna bata fito ba, amma bamu kawo komai a ran mu ba, domin ko wani dan adam Akwai uzuri da yake yi a banɗaki, sai muka dauka cewa kila kunya take ji shiyasa tace fitsari ne, baffan ne ya mike, sannan Inna ta mike itama da alama wani abun take son dauko masa, ya rage Ni kaɗai a tsakar gida, nima mikewa nayi domin zaman ya ishe Ni, dakin na na shiga na kwanta, kuma abun mamaki sai muka manta da babin matar, domin mun ɗauka har ta tafi".
Wata ajiyar zuciya mai tafe da sheshek'a Aysha ta kara saki, sannan ta ɗora da cewa "bayan wasu Mintuna na fito daga dakina domin shi ga banɗaki nayi fitsari... kafata daya na saka cikin banɗakin mu, sai na tsaya cak! Ka san me na gani?"
Girgiza kai Abraham yayi, domin a halin da yake ciki yanzu sam baya jin zai iya magana,domin harshen sa ta yi masa nauyi.
"Yara yan biyu jarirai da ko Cibiyar su ba a yanke ba na gani kwance cikin farin towel a kasan banɗakin mu, sai wata jaka a gefen su, ihu na kwala daya fito da su Inna a guje, kasa magana nayi sai nuni da na musu da jariran da suke kwance a kasan jikina na matuƙar rawa kamar an jona min electric shock mamaki sosai ya kama iyayena domin duk cikin mu bamu lura da cewa da akwai jarirai hannunta a lokacin da zata shiga banɗaki ba, mun ɗauka cewa kila wani kaya ne nata da bata son ajiye wa a waje ne, domin ta lullube su ta yanda babu mai tunanin jarirai ne a ciki...." Nan dai Aysha ta cigaba da gaya masa komai daki-daki kamar yadda abin ya faru...
*Abraham*
Zufa ce ke karyo masa mai yawa har tana diga kan gado, abu ya ji yana biyo kuncin sa ya shafa yaji ashe hawaye ne, saurin goge idanun sa yayi Domin dai bai san ko kukan me yake ba, har yanzu akwai abubuwan da yake son sani, amma ganin jikin ta na rawa da alama zazzaɓi ne ya rufe ta saboda tsoro hakan yasa ya mike, ya nufi sif dinta daya sanja mata zuwa mai six doors ya buɗe ya dauko bargo, zai rufe kenan idanun sa suka sauka kan Ghana most din ta nan, cak ya tsaya yana kallon ghana most din, domin lokacin da ake hada mata sif dinnan ya ga jakar ghanan, ya so ya buɗe domin dubawa idan ba abu bane Mai muhimmanci ya fitar waje, har ya kai hannu da niyyar dauka, kira da ga kamfanin sa ya shigo wayar sa, hakan yasa ya manta gaba-daya...
Bargon ya rufa mata sannan ya dauko ghanan most go din, haka kawai yaji zuciyar sa na azalzalar sa ya buɗe, ya kuwa zuge zip din hadi da zazzage ta a kasa, abin ciki ya fado kasa...
Kamar mai tsoron taba wani abu haƙa ya mika hannu ya ɗauka, gabansa na tsananta bugawa Saboda ganin hoton album din sa, tabbas baya mantawa farkon zuwan su Kaduna ya nemi hoton album din nan bai gani ba, har Madam GLORIA tana cewa kila garin
kwashe kaya ne suka manta a Imo State.
Shafin Farko ya buɗe ya fara tozali da hoton sa, cikin sauri sauri ya cigaba da buɗe hoto album din yana kallo, fadin tashin hankali da mamakin daya shiga bazai fadu ba.
Mayar da kallon sa ga Aysha dake kwance idanun ta a lumshe yayi, sai da ya ɗan daidaita nutsuwar sa, sannan yace "ụmammmm!" Ya kira ta Cikin murya dake bayyana halin tashin hankali da yake ciki.
A hankali ta bude kumburarun idanunta ta kalle shi, idanun ta na sake yin raurau kamar mai shirin kuka...
(Kamar yadda kuka sani dama Abraham da turanci yake magana, ina saka Hausa ne domin sauk'ak'awa makaranta na) cikin Yaren Ingilishi yace "wannan album din ma a tare kika gan su tare da sarkan nan dake wuyan ki?"
Cikin rawar murya tace "eh! Yana tare cikin jakar da Matar ta bari a banɗakin gidan mu"
"Oh God!"
Ya fada yana hargitsa gashin kansa, daf da Aysha ya matso sosai har yana juyo bugun zuciyar ta yace "You no what? First thing tomorrow morning we are living to Gombe, i just need to finalize some issues, am so confused ụmammmm, am confused" Yana gama fadin haka ya bar daki kamar zai tashi sama.
(Kin san me? Abu na farko gobe zamu je Gombe, ina so na tabbatar da wasu abubuwan, na rude rayuwata, ina cikin rudu)
Jinjina kai Aysha tayi, tana kallon shi ya bar dakin, ta sani cewa yana bukatar kaɗaici, sam bata ga laifin sa ba, lumshe ido tayi wasu hawaye Masu dumi suka zubo mata.
Idanunta ta kai kan photo album din, tun da ta dauko a dakin baffa bata taɓa budewa ba, a hankali ta sa hannu ta janyo shi daga gefen gado inda ya bar shi, dan mikewa zaune tayi tana cije lips dinta saboda kanta dake barazanar fashewa, majina ta ja sannan ta bude shafin Farko, zuciyar ta ne ya bada dam! Tsoro, firgice, hadi da dimbin al'ajabi ne suka kama ta Saboda hoton Abraham da ta gani, duk da a kananun shekaru aka yi hoton, amma still kamanin sa basu sauya ba.
Toh Meye haɗin sa da matar nan da ta bar su Anwar ta gudu? Ya akayi photo album din sa yaje har Gombe, kuma a lokacin basu san juna da Abraham ba, infact Bama ta yi mafarkin fara aiki a gidan nan ba...
Maganganun da suke ta yawo a ƙwaƙwalwar ta kenan, sosai zazzaɓi mai zafin gaske ya kara rufe ta, saboda damuwa da tashin hankali, har kad'awa hakoranta ke yi dana juna.
A takaice dai haka kowane su ya kwanta ba tare da bacci ya dauke su ba cikin damuwa, firgice, hadi zullumin abinda zasu tarar gobe...
Karfe shida na safe sun ɗauki hanyar Gombe, inda Abraham ke tuka su, Aysha na zaune a gefe shiru, duk wanda ya kalli su biyun a lokacin sai ka tausaya musu, domin sai ka rasa waya fi wani tashin hankali a cikin su.
***********
Bayan wasu awannin suka isa garin Gombe, sannan suka dauki hanyar unguwar su Aysha, duk da ya gaji da tukin, Amma still Abraham Bai huta ba, burin shi kawai su isa gidan, hakan yasa ma ya kara gudun Motar.
Tun daga nesa yake danna horn ga wata mata dake tsaye a tsakiyar titin, inda Wannan matar tafi kama da mai tabin hankali, saboda yanayin shigar ta da kuma yanda kamanin ta suka sauya...
Kamar kurma haka matar nan ta tsaya, wasu mutane dake gefen titin har ihu suka dinga mata domin ta matsa amma inna, hakan bai yu ba domin bata tare da tunanin ta, ga gudun da Abraham ya keyi ya ma kasa taka birki, yana daf da buge ta Allah ya bashi nasara ya taka wani uban birki, amma duk da hakan sai daya buge matar a kafa, Allah ya takaita bai yi sama da ita ba, inda anan ne hankalin matar ya dawo jikin ta...
Ta kwala ihu saboda zafin da ta ji ya ratsa kafar ta, cikin sauri Abraham yace
"ya Allah!"
Sannan ya ɓalle murfin motar ya fito cikin sauri, Aysha ma ta fito, cikin kulawa Abraham yace "Am very sorry madam, please let's take you to the hosp...."
Sauri dago kanta matar tayi, wanda hakan yasa Abraham bai karasa maganar sa ba.
Cikin firgice, farinciki, hadi da mamaki tace
"Abraham!"
Cikin mamaki Abraham ya kalli matar jin ta kira sunan sa, ya kafe ta da ido, yana son tuno fuskar ta, amma hakan ya gagara.
Aysha dake ta zaro ido Saboda rudewa da tsoro, cikin Yaren Ingilishi tace itace! Itace ta ajiye su Ammar a banɗaki ta gudu, tabbas itace bazan taba manta fuskar ta ba" Aysha ta faɗa cikin tabbaci, nan aka shiga Kallon-kallo a tsakanin su uku.
_Manage pls, I'm damn tired, Kila ku ga typing error banyi editing ba_😩
*Guys new book Is loading next week, kuma paid ne #300*
Share fisabilillah
Comment for more typing
Noor Eemaan
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
*WATTPAD*
@NoorEemaan
Chapter 65-66
Sun dauki mintuna biyar masu kyau suna kallon-kallo ba tare da sun ce wa juna komai ba, musamman Anty Sarah dake kallon Aysha saboda jin abinda tace. Abraham da komai ya fara girmama ƙwaƙwalwa da tunanin sa ya zuba wa anty Sarah idanu dake ta sharban kuka abin tausayi.
Cikin kuka tace"Abraham baka gane ni ba ko? i knew bazaka gane ni ba" numfashi ta sauke, yayinda ta hadiye Wani abu mai kama da tsoro sannan ta ɗora da cewa "nice Sarah, kawar Gloria dake a matsayin mahaifiya a gare ka, na jima ina neman ka, har imo naje gidan ka amma na samu labarin kun tashi, sai dai ban san ina kuka koma ba"
Runtse idanun sa yayi sannan ya bude saboda sunan mahaifiyar sa da aka kira Madam Gloria da shi, a yanzu kam baya so a danganta shi da ita.
Sauke idanun nasa yayi kan Anty Sarah, tabbas ya gane ta yanzu, ko lokacin da take matsayin yar aiki a gidan ba wani kallon ta yake ba bare ya wani gane ta, ya kuma yi mamaki da ta ce ita ɗin kawar Madam Gloria ce, domin a iya sanin sa yar aiki ce.
Domin madam Gloria ta sanar dashi cewa Sarah yar aiki ce.
Kawar da wanna tunanin yayi, saboda Akwai abinda ya sake daure masa kai, yana son yayi nazari da kyau ta yanda akayi ta je gidan su Aysha ta ajiye jarirai, sannan jariran na waye? kuma a wani dalili take neman shi? Sosai yake son samu amsar wandannan tambayoyin, amma ya ma kasa magana, saboda abubuwan da yawa ya rasa ta ina zai fara.
Numfashi Abraham ya furzar sannan ya kalli Anty Sarah yace "come with us" yana gama fadin haka ya juya cikin sauri ya fada mota, Aysha ta mara masa baya ta zauna a kujerar mai zaman banza, yayinda Anty Sarah ta shiga baya ta zauna shiru gwanin tausayi kamar kazar da ruwan sama yayi wa duka.
Nan Aysha ta cigaba da nuna masa hanya...
sun dauki mintuna sha biyar suna tafiya sannan suka iso kofar gidan tace ya tsaya sun iso.
Ba musu ya tsaya hadi da daura kansa kan sitiyarin motar, kallo shi Aysha tayi, cikin sanyin murya tace "lemme inform Inna we re together"
(bari na sanar da Inna tare muke)
Bata jira amsar sa ba ta
bude kofar motar ta fice hannun ta rike da jeka mai ɗauke da hoton Album din nan, dama already sarkan yana wuyan ta bata cire ba, Anty Sarah kuwa kurawa gidan ido tayi, tana jin ƙwaƙwalwar ta na tariyo mata zuwan ta na farko, duk da akwai yan sanjin gine-ginen a layin, hakan kuma yasa gidan ya bace mata tun zuwan ta Gombe, ta wani ɓangaren kuma taji dadi, domin wahalar ta bata tafi a banza ba, tunda gashi Allah ya haɗa ta da Abraham.
Da sallama ɗauke a bakin Aysha ta shiga gidan, tsakar gidan su a tsaftace ko tsinke babu a kasa, Inna na zaune fess da ita tana soya wainar masa da su Anwar suka ce ita suke so yau.
Salati Inna ta yi a lokacin da ta ga Aysha, ko sallamar ta kasa amsawa tayi
"Indoooooo lafiya, mezan gani haka? Amarya da fitowa a washegarin kai ta gidan miji"
Murmushi Yake Aysha tayi tace " kwantar da hankali ki Inna, muna tare da shi ne"
"Ya Salam! in ce ba wani abu kika yi ba, lafiya ko?" Inna ta tambaye ta a dame.
"Banyi komai ba Inna, sai dai ba lafiya"
"Innalillahi wa Inna illahi raju'un, ku shigo toh Allah ya yi mana magani"
Inna ta fada hankalin ta a tashe, dama suyar karshe take yi, hakan yasa ta kwashe bayan ya soyu ta saka a kula, sannan ta ɗora kular miyan taushe da ta jima ta gamawa a sama ta wainar ta kai daki...
Ta ɗan gyara inda ya bace garin suya kana ta shige dakin baffa ta zauna tana jiran su shigo... tana zama kenan ta sake jin anyi sallama.
Aysha ce ta fara shiga ta zauna kan babban sallayar dake shimfid'e a kasa, sannan Abraham ya shigo, cikin karfin hali ya tsunkuyar da kansa alamar girmamawa ga surukar sa yace
"Good afternoon ma"
Inna da bata san abinda ya ce ba, amma daga yanda yayi ta fahimci gaishe ta yayi, kuma duk da bai tsugunna ba, hakan bai sa ta damu ba, domin ta san cewa kila ba al'adar su bace, ko kuma bai saba da hakan ba.
Kuma abin da ya sanyaya ranta shine ganin Abraham mai hankali, domin yanayin sa ya nuna cewa shi din mai nutsuwa ne, ya kuma dace da mijin Indon baffan! hakan yasa hankalin ta kwanciya, ko ba komai ta san kalar mijin da diyarta ta aura.
"Yawwwa sannu ku da hanya, zauna ko" tace wa Abraham.
Bai ji abinda ta ce ba, Aysha ta kalli shi, a hankali tace masa"Inna said you should sit down" ba musu ya zauna, Anty Sarah dake gefe a tsaye Inna ta kalle ta, tayi mamakin meya hada su Indo da wanna matar amma bata furta ba.
"baiwar Allah zauna mana" ba musu Ta zauna, domin dan zaman data yi a Gombe, ta na dan jin Hausa kadan-kadan.
Aysha ce ta muskuta hadi da kallon Inna tace "Inna kin gane wanna matar?"
Aysha ta faɗa tana nuna Anty Sarah da ta tsunkuyar da kanta.
Dan kankance ido Inna tayi tana kallon Anty Sarah, saboda dan tsufan daya fara kamata, kana ta girgiza kai alamun bata gane ta ba.
"Hmmm! Inna ita ce fa matar nan da ta ajiye su Ammar a banɗakin shekarun baya da suka wuce ta gudu"
Zabura Inna tayi, ta dafe kirjin ta kana ta saka salati. "Indo da gaske kike? Ta yaya kika gane ita ce"
Nan Aysha ta labartawa Inna yanda ta dauki sarkan wuyan ta da photo Album a dakin baffa, da haduwar da suka yi da da Anty Sarah yanzu, sannan ta sanar da Inna cewa ita kam bata manta fuskar ta ba.
Kuka mai dauke da abubuwa da dama Anty Sarah ta saki saboda taji wasu abubuwan da Aysha ta fada, nadama da kunya mai tsanani na sake lullube ta.
Fuskantar Abraham tayi cikin turanci tace "Waɗannan yaran da na ajiye a banɗaki gidan nan....."
wani abu mai daci ta hadiya, sannan cikin kunya mai tsanani hadi da sabon nadama ta ɗora da cewa "yaran ka ne daka haifa tare da Nonye!. Sannan ban ajiye su da mugun nufi ba, illa saboda na tseratar da rayuwar su daga hannun kishiyar mahaifiyar ka Gloria!"
A haukace Abraham ya kafe ta ido, yayin da bugun zuciyar sa ke ta karuwa yana bada sautin fat! fat!! fat!!! har yana nuna wa ta saman rigar sa, ya haɗa uban gumi, yayinda ya kasa ko da motsa yatsa ne, saboda dumbin al'ajabi daya tsinci kansa a ciki, ƙwaƙwalwar sa ta tsaya cak da aiki, bangaren Inna da Aysha ma suna cikin shock jin abinda ya fito daga bakin anty Sarah, Aysha mai raunin zuciya tuni ta fara kuka, infact dukkaninsu su shiga wani hali da damuwa mai tsanani bare ma Abraham da al'amarin ba mai sauke bane a gareshi.
Tsahon mintuna goma babu wanda ya sake magana, ko wa da abinda zuciyar sa ke saka masa, Abraham kuwa har yanzu bai dawo dai-dai ba, sai da anty Sarah ta ɗora da cewa "na san labarin da zan baka yanzu zai iya tarwatsa zuciyar ka, amma kayi hakuri ka yafe Ni, tun bayan da muka aikata mugun nufin Mu da Gloria na nemi salamar zuciya na rasa, burina na ganka na nemi yafiyar ka...."
Kamar yadda Kuka sani reader's tiryan-tiryan haka Anty Sarah ta shiga gayawa Abraham abinda ya faru....
Tun daga lokacin da Gloria ta hadu da mahaifin Abraham, da asirin da tayi masa, da yanda ta kashe mahaifiyar Sa, da yanda ta cigaba da farautar rayuwar Abraham domin malleki dukiyar sa, da yanda ta kashe Nonye, amma su Ammar na motsi a cikin ta duk da ta mutu, da yanda ta tseratar da su Yan biyu tun daga asibiti a imo har izuwan Gombe gudun kada Gloria ta gano komai, da hoton album hadi da sarkan Nonye data dauko a dakin ita Nonye a lokacin da zasu tafi asibiti cikin dare, da kiran Madam GLORIA data yi ta Sanja murya tayi karyan ta mu saboda duk kada Madam GLORIA ta gano komai ta biyo ta .
Haka dai ta cigaba da gaya masa komai tana kuka mai ban tausayi.
Jikin Abraham rawa yake kamar wanda zafaffan zazzaɓi ya kamasa, ya kai mintuna goma a haka, sannan ya ja guiwar sa har gaban Aysha ya dora kansa kan cinyarta, ya saka karfafan hannunwan sa ya zagaye waist (kugu) dinta dashi, ya matse ta sosai, mafaka yake nema, mafakan da zai samu ko da dan sanyin ne a zuciyar sa, cikin tausayi Aysha ta nausa hannun ta cikin gashin sa, tama manta Inna na zaune a wajen, sai a lokacin Abraham ya samu wani kuka mai sauti ya kufce masa, kukan da amon sa duk ya taba zuciyoyin su bare ma Aysha, hakika duk wanda ya ga Abraham a wanna halin dole ya tausaya masa ainun.
Inna kuwa kauda kanta gefe tayi, saboda kara, tunda Aysha na matsayin yarta ta fari kamar yadda aka san Fulanin Usul da kunya, amma ta tausaya wa Abraham sosai duk da bata gane komai da anty Sarah ta fada ba, amma ta tausaya masa matuk'a.
Ba tare da ta kalli Aysha ba saboda har yanzu Abraham yana runkumkume da ita, tace "Indo wai menene, duk ban fahimci abinda matar nan take fada ba" Cikin kuka Aysha ta shiga gayawa Inna komai, amma a takaice kamar yadda anty Sarah ta faɗa.
Girgiza kai Inna ta shiga yi, har kwalla ta zubar saboda tausayi, sannan ta jinjina rashin imani irin ta Madam Gloria cikin dumbin al'ajabin yadda mutanen yanzu suka fifita duniyar su fiye da lahirar su, bayan duka wanna abin duniyar mutum bazai tafi da su lahira ba, kana mutuwa shikenan, wasu ne zasu cinye abin duniyar, amma saboda imani da tausayi yayi karanci yanzu sai ka kashe rai Saboda kwadayin mata'ul hayat (kyale-kyalen rayuwa).
Anty Sarah ta ja hanci saboda mugun muran daya kamata a dalilin kukan da ta sha, kana ta hade hannayenta waje daya alamun roka, ta ɗora guiwarta a ƙasa tace "dan Allah kayi hakuri ka yafe Ni, kullum cikin tashin hankali nake da mugayen mafarke, matuƙar baka yafe Ni ba bazan taba ganin haske ko da kadan ne a rayuwata ba, ban kuma ajiye yaran nan a toilet din gidanan saboda wata manufa ba, a lokacin ina cikin wani hali ne, burina a lokacin kawai na nisantar da su daga GLORIA, sannan a ganina gwara na barsu na gudu ba tare da bayin Allah nan sun sani ba(, tana nufin su Inna) a ganina hakan zai sa su karbi yaran, sannan zasu yi nisan gaske daga wajen GLORIA, duk da an sanar mata cewa yaran sun mutu, amma nasan Gloria, shu'uma ce, zata iya gano komai, hakan yasa na iya takuna wurin ganin ba ta gane cewa yaran na raye ba, kullum tunanina a wani hali yaran suke, amma idan na tuno karamcin bayin Allah nan a zuwana gidan nan na farko sai hankalina ya ɗan kwanta, domin na ga suna da zuciya mai kyau, dan Allah ka nemi waje ko yaya ne a zuciyarka ka yafe min, na tuba, ka yafe min dan Allah!" ta karasa tana buga hannunta a kasa, alamun tayi nadamar abubuwan data aikata a baya, Sannan tana jin ciwon su.
Ido duk suka zuba mata, babu mai kuzarin sake magana ma a cikin su, domin Abraham har yanzu bai gama dawowa hayyacin sa.
*MADAM GLORIA*
Tun daga lokacin da ta je wajen boko Nandera kullum da irin aikin tsafin da yake yi a kanta, Burinta a kullum watanin daya diba hadi da kwanakin su cika domin ta bar wannan dajin, domin ta gaji sosai, sannan hankalin ta ba a kwance yake ba, saboda macizan nan dake ko wani kusurwa na fadar Boka Nandera, a haka ta cigaba da lallabawa tana jurewa har watanin da kwanakin daya diba suka cika...
Sai dai me, a ranar boka Nandera ya fito da abinda ya dade a ransa muraran.
Ma'ana dai yana bukatar ya kusance ta, a ranar Madam Gloria ta ga tashin hankali, ya Kada ya raya taki yarda, ita kam iskanci baya damunta, sam bata damuwa da shi ba, ita matsalar ta son kai, rashin imani, hadi da son abin duniya ne ya dame ta, ya kuma rufe mata ido.
Sannan kuma tana k'yank'yamin wanna bokan, ta ina ma zata fara kwana dashi.
Cikin tsoro da fushi ta bar fadar a kokarin ta na barin dajin, wanna karon kuwa zuciyarta ta k'ek'ashe ta Kuma gaji da aikin bokayen nan, sam basu da gaskiya, gwara ta nemi tantirai ta biya su, a kashe mata Abraham ta huta kawai.
Amma abin mamaki ta kasa gane hanyar barin dajin, da ta dau hanya sai taga babu hanya, sai munanan halitta da take ta gani suna bata tsoro, abin dai ba sauki domin har duhun dare ya gabato tana neman hanyar barin dajin... da ta ga ba wata mafita, haka ta dawo guiwa a sanyayye wajen bokan domin bata da wani waje daya fi nan din a yanzu.
Dariya boka Nandera ya shiga k'yak'yatawa cikin Muryar sa mara dadin amo a lokacin da ta dawo, dama yana kallonta ta cikin allon tsafin sa.
A takaice dai a wannan daren ya danne ta ta ƙarfi ya kusanci ta, kusan kwana yayi yana abu ɗaya, wuya iya wuya Madam Gloria ta sha shi.
Washegari again ta sake gwada barin dajin, amma ta kasa, saboda da ta fito sai komai ya Sanja ta rasa hanya, haka boka Nandera ya mayar da Madam Gloria kamar matar sa, kullum babu fashi, duniyar tayi wa Madam Gloria zafi, gashi irin warin da boka Nandera ke yi ya kama jikin ta tun daga lokacin da ya fara kusantar ta, haka ta cigaba da fama cikin mayuwancin hali.
*Bayan wasu kwanaki*
Da misalin ƙarfe takwas na safe madam Gloria ta tashi, kasancewar boka bai bari ta huta cikin dare ba sai kusan shida saura Bacci ya dauke ta...
Da fari wani mugun wari ta ji ya fara ziyartan hancin ta, ta kai kallonta ga inda ta ji warin...
Gabanta ne ya yi wata bugawa, Domin boka Nandera ta gani kwance flat a kasa babu numfashi a tare da shi, majizan nan sun kanannad'e jikin sa, da kyar ma ake iya ganin fuskar sa saboda Yawan macizan nashi, gashi ko wannen su na kai mai cizo ta ko ina a jikin sa, abin babu kyawun gani...
Ihu Madam Gloria ta shiga yi, yayin da tsigar jikin ta har tashi ya dinga yi, sai take jin kamar majizan nan na ya dawo a jikin ta itama, haka ta dawo zautaciyya, sai faman soshe-soshe take, duk wanda zai ganta a halin yanzu zai dauka mai tabin hankali ce da ta shafe shekaru talatin a cikin hauka.
Banda kananun surutai babu abinda take da alama ƙwaƙwalwar ta ya fara tabuwa...
A takaice dai madam Gloria ta ga tashin hankali, wanda tsaya fayyace wa makaranta bata lokaci ne, da kyar ta iya jan kafafunta ta bar cikin fadar da gudun ta...
Kuma abin mamaki hanyar lafiya lou take yau, kamar ranar data fara zuwa dajin.
Gudu sosai ta shiga yi, domin har gizo macizan nan ke mata, saboda gani tayi suna bin ta a baya.
Tafiya mai nisan gaske tayi, amma kamar bata yi, saboda ko alamar titi da gidajen mutane bata fara gani ba, da haka ta dauki kwanaki uku cur sannan ta fara ganin titi daga nesa sosai, shi ma sai da ta kara wasu awanni kafin ta fito aihinin babban titi.
Duk abin hawan da ta tsayar tsoron daukar ta ma suke, da kyar da sidin goshi ta samu wani taxi, dama akwai kudi a aljihun wandon dake jikin ta, nan ya chaje ta sosai, a hakan ma wai bazata zauna a sit ba, sai dai booth saboda wari take, sam Madam GLORIA bata damu ba.
Booth din ta hau, ita yanzu Burinta ta isa Kaduna, domin ganin bayan Abraham, saboda wata muguwar tsanar sa ne ya sake kamata, saboda a ganin ta duk wahalar nan da take sha saboda taurin ran sa ne.
**********************
*ABRAHAM*
A hankali ya d'ago kansa daga cinyar Aysha, ya dafe kansa dake sara masa, ya cije labban'sa da suka tashi daga pink izuwa red, komai da anty Sarah ta fada na yawo a brain dinsa one after another.
Sai da ciwon kan ya lafa masa sannan ya kalli Aysha cikin turanci hadi da raunin murya yace "dama ina da yara? Ina yara a doran duniyar nan ban sani ba, yaya suke Please, i want to see my kids, Ina yarana suke, please tell me"
Ya karasa yana rike hannun Aysha ga wani hawaye mai zafi daya biyo kuncin sa daya.
Komai gani yake kamar al'mara, cikin kankanin lokaci ya ji abinda ya kusan tarwatsa zuciyar sa, da ba dan yayi namijin kokari wurin danne zuciyar sa ba, da yanzu baya a zaune haka, da yana gadon asibiti a kwance.
Tabbas irin wannan abun yafi komai ciwo domin wanda baka taɓa expecting ba, kana ka bashi yarda da matsayin uwa ya ci amanar ka, ya fi ciwo sosai.
Aysha zata tambayi Inna ina su Ammar suka je kenan taji sallamar su cikin Muryar su ta yara, sun shigo gidan...
Gidan iyayen anty Bintu suka je wasa da yaran anty Bintu.
Dama wani zubin har sai Inna taje ta kanta ta dauko su, saboda sun saba da gidan sosai.
Cikin muryar kuka da Aysha ta sha ta kalli Abraham tace
"Oh! they are here already"
Cikin sauri Abraham ya mike ya leko su, sosai ya kura wa gudan jinin sa eyes dinsa da suka yi matukar yin ja, tun kafin su karaso...
duk takun dayan da su Ammar zasu yi, gaban Abraham ke cigaba da faduwa saboda tsantsar kamanin su, shi da Nonye da yaran suka dauko, ya kasa yarda cewa wadannan k'yawawan yaran na sa ne, amma bai san da su ba, babu zato ya ga hawaye na zubo masa, cikin sauri yasa hannu ya share, wani mugun soyayya irin ta ɗa da uba ta caki zuciyar sa, fiye da zaton mai karatu.
Hannayen sa ya ware musu, ya dire guiwowin sa a kasa... muradi, fata, hadi da burin sa yanzu yaran su zo gareshi domin yaji dumin su....
Share
Share
Share fisabilillah ☑️🙏
Comment for more typing.
✨NoorEemaan✨
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
Chapter 67-68
Maimakon su je wajen Abraham ɗa ya ware musu hannu, sai suka fada jikin Aysha bayan su karaso saboda basa san shi ba...
Cikin Muryar su ta yara suka shiga kiran "Ammuh Oyoyo" rungumesu sosai Aysha tayi a jikin ta, wani mugun son su da kaunar su fiye dana baya na sake ratsa zuciyar ta.
Abraham kuwa sauke hannun sa cikin rashin jin dadi da basu Wajen shi ba, ya kuma san rashin sabo ne yasa su hakan.
Sai ya kafe su Aysha da ido cikin burgewa ganin yadda yaran suka saba da ita, sai faman murmushi.
Aysha ta shafa kansu tace "na yi kewar ku sosai my twin" hakoran su suka washe mata suna dariya, juyo da su tayi ya zamana suna fuskantar Abraham sannan tayi musu nuni da shi tace "ga Daddyn ku, ku je ku gaishe shi"
Tsaye yaran suka yi suna kallon mahaifin su Abubakar Assadik cikin rashin sabo, sai da Aysha ta sake magana sannan suka tafi wajen shi a hankali, kana a tare suka shige jikin sa.
Wasu hawaye masu sanyi ne suka zubo kuncin sa, hakika yau ya dawo mai rauni, saboda abubuwa mabambamta masu cike da al'ajabi da ya ji cikin rayuwar sa a yau, ashe all this year's cikin duhu yake, sai yanzu haske ya bayyana, duhun ya yaye...
Kara rungume ya'yan sa yana basu sumbatar ta ko ina, abin so heart touching and lovely. Aysha ma sai ta data share hawayen tausayin su.
Muryar Anty Sarah ya ji tana sake bashi hakuri da neman yafe, su Ammar da suka lafe a jikinsa ya sake riƙe su da kyau sannan yace " bani da abinda zan ce miki, wadanda kuka zalunta basa duniyar, dan haka ki koma ga Allah kawai" yana gama fadin haka ya mike, sannan ya riko hannun yaran sa suka bar gidan izuwa masallaci domin ya ji kiran sallah.
Kuka mai suna kuka Anty Sarah ta fashe dashi, ina ma ina ma hannun agogo zai dawo baya da ta gyara kuskuren ta.
sai ta dawo bawa su Inna tausayi, domin duk da tarin laifukan ta, amma duk wanda ya ganta a halin yanzu zai matukar tausaya mata.
Baki suka shiga bata kan ta daina kuka, ta cigaba da neman yafiyar Allah, domin Ubangijin talikai gaffurul Raheem ne.
Nan Inna tace mata ta je tayi wanka, saboda maganar gaskiya wari take, bata Musa ba, saboda ita ma ba jin dadin jikin ta take ba, bayan ta yi wanka Inna ta bata wata doguwar rigarta ta atamfa ta saka, sannan aka zubar dana jikin ta a shara.
Abraham kuwa suna fita ya hango masallaci, nan suka karasa suka yi alwala a bakin masallacin domin akwai ruwa da butoci, a gurguje ya karasa alwalar domin har liman ya tayar, su Ammar ma suka yi alwalar su yanda yara suka yi ya rike hannun su suka shige masallacin.
Bayan sun iddar sun fito, yara da manya sai kiran Ammar da Anwar suke, yaran kuwa su dinga amsawa da na'am, yayin da wasu kuma mamakin kamanin yaran da Abraham suke.
Abraham kuwa abin yayi matuƙar kayatar da shi, ya kuma ji dad'i saboda yanda jama'a ke son yaran sa.
Yana so suyi hira amma basa jin wani turanci, shi kuma baya jin Hausa, sai yanzu rashin iya Hausar sa ke damun sa.
Amma yasa a ransa cewa yaran su iya turanci hadi da Yaren sa na Igbo, numfashi ya sauke, duk da bai san akwai su a doran duniyar nan ba, amma yaji dadi ganin su cikin koshin lafiya da kulawa.
Bayan sun iso kofar gidan, ya buɗe musu mota suka shige hadi da kunna musu Ac yaran suka hau murna, suka kalle shi suka ce "wannan motar ka ce?" Be ji abinda suka ce ba, amma haka ya daga musu kai alamun eh yana murmushi.
Su Twins suka hau murna wanda hakan ya sa zuciyar Abraham yin sanyi.
Kurawa Ammar ido yayi yana tuno ranar farkon da Aysha ta fara shiga dakin sa, tabbas wannan sunan ta faɗa, kenan ta ga kamanin su shi yasa cikin rashin sani ta kira shi da sunan Ammar....
Ya sake mai da duban sa ga Anwar, sak Nonye kamar an tsaga kara, nan fa Abraham ya maida su tv ya dinga kallon su, labarin komai da Anty Sarah ta bashi na dawo masa daki-daki.
Inna data ji shiru bai dawo ba, sai tace Aysha ta leka waje ko yana nan, su zo su ci abinci, ba musu Aysha ta mike, domin ita ma ta damu da rashin shigowar su, kawai ta maze ne kar Inna ta ga rashin kunyar ta.
Tana fitowa ta hango shi zaune ya kurawa yaran sa ido a mota, hannu ta ɗora a kugu tana kallon su murmushi dauke a fuskar ta, domin su burge ta, kai kace sun dade da sanin juna.
Jikin Abraham ne ya bashi ana kallon shi hakan yasa shi dago kan sa ya kalli direction din da take, murmushi yayi kana ya kira ta da hannu.
A nutse ta shiga takawa har tazo bakin motar, su Ammar na ganin ta suka shiga kiran "Ammuh!" Sannan suka fito daga motar suka rungume ta.
So take ya saki ransa, hakan yasa cikin tsokana tace "kazo kaci abinci inji Inna"
"What!" Yace yana kafe ta da ido.
Dariya ta sa, dama so take ta tsokane shi, kasancewar ba Hausa yake ji ba.
Ya fahimci tsokanar sa take, sai ya girgiza kansa yana murmushi.
Sai ta dawo serious ta fada masa abinda Inna tace da turanci, baya jin zai iya yin musu ga surukar tasa, saboda girman da take da shi a idanun sa, amma maganar gaskiya sam baya jin yunwa, amma bazai iya cewa a'a ba, fitowa yayi daga cikin motar ya sa key sannan suka jera zuwa cikin gidan.
Dakin ta dake a gyara suka shiga, domin duk da bata nan Inna na gyara mata.
suna shiga kuwa suka tarar Inna ta jere musu wainar shinkafa da miyar taushe da ya sha tantakwashi da nama, sai had'add'en fura da nonon kindirmo zallan sai ruwan randa mai sanyi.
Aysha ta zuba musu komai, tayi wa Abraham Bismillah, Dan yamutsa fuska yayi alamun baya ci, domin duka cimmar bai taba gani ba bare ya ci, nan Aysha ta shiga mai daɗin baki kan ya dandana akwai dad'i Sosai.
Domin ya faranta mata yanka daya ya ci na wainar bai kara ba, domin bai yi masa ba, ko dan bai taba ci bane.
ya sha fura ludayi biyu, sannan ya sha ruwan randa mai yawa bai yi k'yamk'yami ba.
Aysha dasu Ammar kuwa suka ci, duk da ita Aysha Bata wani ci da yawa ba, saboda ganin har yanzu da damuwa a tare da Abraham, wanda hakan kuma dole ne domin rasa uwa, da mata sannan kashe su akayi ba abu bane mai sauki da kuma saukin mantawa a gare shi bane.
Haka dai suka kasance har dare.
Bayan sun yi sallar isha Abraham yace Aysha da su twins su raka shi ya ga gari, ya kuma yi hakan ne domin ya rage damuwa dake damun sa.
Aysha ta sanar da Inna, sannan ta rike hannun Ammar, Abraham kuwa ya rike hannun Anwar suka fice...
Sunyi yawo ba laifi, sun je dandali sunyi kallo, Daga nan suka dan zaga gari Aysha na masa bayanin duk inda suka wuce, daga nan suka je kasuwar dare, Abraham ya siya musu tsire da doya da kwai, da haka suka dago gida gwanin sha'awa, su twins sai surutu suke musu a hanya, Aysha na biye musu, Abraham kuwa sai dai yayi murmushi, domin zuciyar sa cike da farin ciki, ya kuma godewa Allah da ƴaƴan sa suka fada hannun na gari.
Bayan sun iso, Abraham yace zai kwanta a mota, su Aysha su shiga ciki...ya sumbace yaran sa, ya shige motar.
Bayan sun shiga ciki Inna tace "ina mijin ki yake?"
Cikin kunya tace "Inna wai a mota zai kwana"
"A'a A'a ba za a yi haka dani ba, Meye amfanin dakunan nan? Maza ce masa ya shigo dakin ki ya kwana, sai mu kuma mu kwana a daki na"
"Toh Inna"
ta ce tana fita, Abraham da har yayi nisa a tunani ya ji ana k'wank'wansa kofa, glass din motar ya zuge ƙasa, ya ga Aysha tsaye hannun ta rungume a kirjin ta "ụmammm! Hope all this well?"
"Nothing much, Inna said you should come inside"
Dan shiru yayi sai kuma ya bude kofar motar ya fito, ya saka lock sannan ya mara mata baya zuwa cikin gida.
Har baƙin kofar dakin ta Aysha ta kara shi, sannan yta juya zuwa dakin Inna, ba tare da tace komai ba, ta lura har yanzu bai gama sake wa ba, ba kuma ta so ta takura masa.
Da kallo ya bi bayan ta, tana dab da shige dakin Inna taji Muryar sa yace ta kawo masa su Ammar su kwana tare, ba musu ta ce masa toh.
iska ya furzar daga bakin sa, sannan ya shige dakin ya fada kan gadon yana rub da ciki...
Bayan ta kawo su Ammar ta sake fita tana mai sai da safe ya amsa...
haka yasa yaran a gaba yana kallon su cikin kauna har suka yi bacci.
Shi kam babu alamun bacci a idanun sa, haka dai ya dinga juye-juye baccin yaki zuwa har aka kira sallar asuba.
*WASHEGARI*
Bayan duk sunyi sallah, Abraham da ya je masallacin tun asuba bai dawo ba, Aysha kuwa ta fara ɗora musu abincin karin kumallo, bayan ta gama ta share tsakar gida ta gyara sannan tayi wanka hadi da brush.
kayan jikin ta na jiye ta mayar, domin bata dauko kaya ba, sam basu zo da niyyar kwana ba.
Su Ammar ta taso tayi musu wanka da brush, kana ta shimfida tabarma babba a waje, tace su zauna bari ta dauka kayansu da man shafawa...
Anwar ta fara shafawa mai, sannan ta saka masa kananan kaya riga da wando, ta taje masa gashi, ya koma ya zauna, kana ta fara shirya Ammar kenan taji sallamar Abraham.
Amsawa tayi tana satar kallon sa, gefen su yazo ya zauna Aysha ta gaishe shi ya amsa cikin kulawa, su Yan biyu ma suke ce Ina kwana ya shafa kan su yana murmushi.
Inna ta fito duk suka gaishe ta cikin girmamawa ta amsa, Anty Sarah da tun jiya bata bari sun sake haduwa da Abraham ba saboda kunya ta fito yanzu a sanyayye...
gaishe su tayi, duk suka amsa, amma Banda Abraham, dake wasa da yaran sa kamar bai ji ta ba.
Ko da yaji bai ma san mezai ce ba, baya so ya dinga ganin ta, saboda yana tuno masa da abubuwan da suka aikata a gareshi, ana haka wayar Abraham yayi ringing ya duba ya ga mai gadi ne, ya picking call din inda mai gadi ke sanar masa cewa ga fa Madam Gloria ta zo, amma yaki barin ta ta shiga domin yaga kamar ta haukace, zuciyar Abraham na suyo, ransa ya ɓaci amma ya danne yace a barta ta shiga amma Kada su bari ta wuce farfajiyar gidan
gasu nan zuwa yana fadin haka ya kashe wayar sa.
Ya kalli Aysha da jajayen idanun sa yace ta shirya su wuce, Inna ta ce ya bari suyi karin kumallo, bai musu ba, duk bai iya cin komai ba, sai ruwa kadan daya sha, wanda ma ya kara kulle masa ciki amma bai damu ba, saboda halin da yake ciki.
Bayan ta shirya suka mike domin tafiya, Cikin turanci ya shiga yiwa Inna godiya sosai da yaba karamcin su, da ƙoƙarin su wurin kula da yaransa, ya kara da cewa bazai iya biyan su ba, Allah kadai ne zai biya su, ya kuma yi wa baffan addu'a sosai.
Inna bata ji duk abubuwan da ya ce ba, Aysha ce mai fassara mata, cikin jindadi addu'ar Inna ta shiga amsawa da Ameen.
Sai ya ajiye wa Inna bandir hudu na dubu ɗaya-daya, taki karba, da kyar da roko Inna ta karba daga hannun shi, da haka suka fito har bakin mota...
Su Ammar sai tsalle suke zasu shiga mota, basu wani damu da Inna ba tunda suna tare da Ammuh'n su.
Har zai ta da mota Suka tsinci Muryar Anty Sarah Cikin turanci tace "Abraham please zan bi ku, ba dan komai ba saboda na nuna wa Gloria cewa duk zakaran da Allah ya nufa da cara sai yayi, sannan ta gane cewa babu wanda ya isa ya kashe mutum sai lokacin da Allah ya dibar masa yayi" .
Shiru yayi ya ma kasa magana, Inna ce tasa baki kan ya tafi da ita, tana da gaskiya, jinjina kan sa yayi alamun amincewa.
Ta shiga bayan mota da su Ammar, kana ya ja motar, su Ammar suka fito da kansu ta window suna dagawa Inna hannu dake tsaye cike da kewar su itama tana daga musu hannu.
***********
Awannin ƙalilan ne ya kawo su Kaduna, saboda gudun da Abraham ya dinga yi a hanya.
Bayan sun shigo farfajiyar gidan tun kafin ya gyara parking yake jin hayaniyar Madam GLORIA da mai gadi daya toshe hancinsa saboda wari, amma hakan bai hana shi zazzaga mata rashin mutunci ba, domin yanzu haka kawai baya ganin girman ta bare tsoron ta.
Ta mirror motar sa ya hango yanda ta lalace, ta koma wata mahaukaciya girgiza kansa yayi sannan ya fito daga cikin motar, Aysha ta biyo bayan sa, Anty Sarah ta biyo bayan Aysha, sannan su Ammar ne karshen fitowa...
A zabure Madam Gloria ta nufo su, tana tafiya kamar barauniya dake tsoron aji takun tafiyar ta haka ta nufo su, cikin shock tana soshe-soshen.
Abraham ta fara gani tsaye kan kafafunsa, murza idanun ta tayi domin ta tabbatar, ta ga dai shi ne tsaye kan kafafunsa, sannan ga Aysha ta fito daga bayan sa, wani sabon mamakin ne ya sake rufe ta, tana mamakin Meye hadin Abraham da Aysha, bata gama shan mamaki ba sai lokacin da ta ga Anty Sarah ta fito daga bayan Aysha, wannan karon ta kasa rikewa.
Ihu tayi irin na rashin hankalin nan tace
"Wannan ba Sarah kawata bace? ba kin mutu ba, ta yaya kika dawo duniyar nan" sai ta sa dariya tana tafa hannu, da alama kwakwalwar ta ya soma tabuwa.
"Ni ba kawar ki bace, domin nayi nadama kulla ƙawance da mara imani irin ki, tabbas ina raye, ban mutu ba, sannan ina so ki sani cewa yaran da kike so kashewa tun bayan da kike kashe uwar su Nonye basu mutu ba, ga sunan da ran su cikin koshin Lafiya"
S daidai lokacin da Anty Sarah ta fadi haka, a lokaci su Ammar suka fito daga bayan ta suka manne a jikin Aysha.
Ƙwaƙwalwar Madam Gloria zai tarwatse, a kafatanin rayuwar ta bata taɓa ganin rana mai munin gaske irin wannan ba, ashe duk aikin da take yi da zuwa wurin bokaye a banza ne, tana ganin kamar Abraham kadai ya rage mata ashe ba haka bane? Kitson attachment din ta da kusan rabi ya warware saboda dadewa, hakan ya bawa cinyayen gashin kanta damar fitowa, ta shiga sosawa da karfi, kana ta saka ihu, kuka, hadi da dariya a lokaci daya.
Tana fadin "oh! No no this is not truth, i must be dreaming"
Sai ta matso daf da Abraham ya kauda kansa saboda wani bad odour Daya bugi hancinsa, cikin fitar zarewa tace "Kai kuma yaushe ka warke? Kana so kace bazan ci Nasara a kan ka ba? Toh karyar ka, Ni nan sai na kashe ka, sai na kashe ka, kuma na kashe banza, bari ma kaji ni ce nan na kashe uwar ka, na kashe Nonye, eh nice na kashe su Hhhhhhhhh" sai ta sa dariya tana rawa kamar yadda mahaukata ke yi.
Jikin Abraham ya shiga rawa, saboda ɓacin rai, Aysha ta rike hannun sa gam tana kokarin calming din sa down, Domin zai iya karya kasusuwan ta a halin da yake ciki yanzu, domin idan akwai kalmar daya fi TSANA ita yake wa Madam Gloria, ta kashe masa uwa, da mata, still hakan bai ishe ta, ina zata kai tarin zunuban nan?
Allah ne tsare su shi da ya'y'an sa, baya jin zai bari wata kalma ta hadu su da ita, domin a yanzu bata da mutunci, kima, da darajan da zai mata magana, ta gama ficewa a ransa tun lokacin da ya fahimci tana farautar rayuwar sa bare daya ji ta kashe masa mutane na musamman a garesa. Abu daya ya sani shine bazata kara rayuwa cikin gidan sa ba, ko ina zata je he don't bloody care, shi kam baya bukatar ta cikin rayuwar su.
Bayan ta gama haukar ta, ta kalli Aysha tace "ke kuma meya daku dashi, ta ina kuka hadu da har kika zama ta musamman a gareshi har kuka fito daga cikin mota daya, ai ni na kawo ki Kaduna ko? Toh maza koma kauyen ku, bana bukatar ki cikin gidan nan Kuma yar kau..."
Kafin ma ta karasa cikin son abin ya kona mata rai anty Sarah tace "ina kike so ta je? bayan nan gidan ta ne, ita din matar sa ce"
kasancewar Inna ta bata labarin auren su har da Musluncin da Abraham ya shiga.
Ai fa kamar an sake birkita ƙwaƙwalwar Madam Gloria nan ta ce "oho! dama son shi kike siyasa na zuba masa guba mai hadarin gaske domin yaci ya mutu, kika yi yadda kika yi bai ci dayawa bako" nan dai ta shiga surutai kala kala tana tona wa kanta asiri duk abubuwan data aikata, domin sauran notikan kanta masu amfani sun ƙarasa kuncewa.
Anty Sarah kuka tasa, domin HAKKIN RAI ke gara rayuwar Gloria.
Gashi duk abinda suka aikata babu riba.
Dama duk wani mai mugun hali baya cigaba ga misali nan a kansu ita da Madam Gloria, me ye ribar su? sun dawo kamar wasu halitta marasa cikakkun lafiya da hankali, gwara ita ma akan Madam Gloria data fara hauka tuburan...
Suna kallo haka madam Gloria tasa mugun gudu ta bar gidan tana faɗin zan kashe ka, ka jira Ni, yanzu zan dawo, yau zaka dawo gawa a Abraham!"
Da surutai kala kala dai wadanda suke binne a ranta take amayo su a yau.
Ko kallon gabanta bata yi, tafiya take tana fadin "zan kashe ka Abraham Patrick yau, Hhhhhhhhh" yau har da kiran sunan tsohon sa, tana fadin haka kuma sai tasa dariya.
Tana fitowa babban titi kamar wacce aka tura haƙa ta shige tsakiyar titi, babban mota ya kade ta, ya markade ta, babu mai iya gane kamanin ta abun babu kyawun gani, mai mota kuwa bai tsaya ba ya arce, haka madam Gloria tayi mutuwar wulakanci da Burin ganin bayan Abraham a zuciya da bakin ta.
(Ya rabb!!! Ka barmu da imanin mu, ka tsare mu da tsare war ka, ka kiyaye mu da kiyayewar ka, ka mana katangar karfe da mugayen mutane ya tawwabul Raheem)
Ta bangaren Anty Sarah kuwa sallama tayi musu ta nufin komawa garin su, ta kara neman tafiyar Abraham amma still abinda ya fada mata a Gombe ya maimaita mata, abu daya ya duba karamcin ta wurin tseratar da ya'y'an sa da ta yi, har ta fara tafiya ya biyo ta ya bata bandir biyu na dari biyar-biyar yace "Nagode da tseratar da rayuwar y'ay'a na da kika yi daga hannun kawar ki "
Da fari taki karba ya bar mata, domin ka'idar sa ce, idan ya yi niyyar bawa Mutum abu baya sake karba, Aysha da har yanzu suke tsaye ta ji dadin abinda yayi, bai jira godiyar ta ba ya goma wajen iyalan sa ya kama hannun su suka shige ciki.
Anty Sarah kuwa kuka tasa mai sauti tana waiwayon su, tabbas zuciyar Abraham mai kyau ce kamar iyayensa, har kalmar GODIYA ya furta a gare ta, bayan duk tarin laifukan ta.
Share share share Please
NoorEemaan
07082281566
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da Facebook sai kuyi join wan nan link din
*WATTPAD*
@NoorEemaan
Chapter 69-70
A sanyayye Abraham da Aysha suka yi wa kan su mazauni a kan kujerar general falo, domin al'ajabin Madam Gloria bai gama sakin su ba, yayinda su twins ke ta wasan su cike da farinciki hadi da yarinta da kananan throw pillow da suke kan had'add'un kujeru.
Abraham ya fito da wayar sa da bai fiye girma ba, amma sai mugun tsada ya latsa wata number ya kara a kunnen sa.
Bayan an daga, ya bada umarnin wa kamfanin masu decorations da hada daki su zo su hada masa dakin yara da dukkani abun bukatar su na wasa.
Ai kuwa mintuna arba'in na cika suka zo da motar company'n su, dakin Madam Gloria ya nuna musu, sannan yace komai na dakin a fitar su zubar, hatta fentin dakin sai daya sa aka Sanja, sannan suka shiga hada wa su twins daki.
Aikin da ya dauke su awa biyar kana suka gama.
Ya rabb! fadin kyau da haduwar dakin bata lokaci ne, tamkar babu halittar daya taba rayuwa cikin dakin saboda yanda komai ya dawo sabo fil gwanin kyau.
Bayan Abraham ya sallami mutanen da huge amount of money da suka chaje shi kana suka tafi.
A lokacin da su twins suka shiga dakin, Abraham ya sanar dasu cewa dakin su ne, suka dinga murna, wanda ya sanyayya ran mahaifin su.
********
Abraham da kanshi yaje nearest boutique ya siyo musu kaya masu kyau duk iri ɗaya, hadi dana bacci, sai kayan shafan su dangin su lotion, hair cream, shampoo da perfume duka na yara.
Aysha ce ta jere musu kayan a wardrobe dinsu, yayin da kayan shafar su kuwa ta jera musu kan dressing mirror.
Daga nan ta wuce kitchen domin ɗora musu girki, saboda yamma tayi sosai.
Amma hakan bai hana ta tuka musu lafiyayyen tuwo semovita da miyar ogbono daya sha ụgu,
stock fish, kayan ciki, jan nama da kpomo, tun kafin ta gama k'amshin girkin ya cika falon kasa gaba daya...
Tana cikin gyaran kitchen kenan bayan ta gama abinci, ba zato bare tsammani taji an zagaye hannu a kugun ta, saurin juyowa tayi ta ga Abraham ne.
Ajiyar zuciya ta sauke domin ta tsorata, sumba ya manna mata a gefen wuyan ta, sannan yace
"my Life"
"Uhmmmm!"
Aysha ta amsa domin ta kasa magana sakamakon hannun sa dake yawo a wasu sassa na jikin ta.
"i love You"
ya fada yana sake riƙe ta da kyau a jikin sa, hadi da birkita mata lissafi, wani yarrrrrrrrrr Aysha taji a jikin ta, duk da bata san me take ji ba, but tana karban sakonnin da yake aika mata.
Ganin yanayin sa ya fara sanjawa, ba kuma ya son ya ya katse mata aikin ta, sai kawai ya barta ya fice, ya koma dakin su Ammar domin suyi wasa. Yana so yaran su shaku da shi sosai, hakan kuma bazai faru ba matuƙar baya jan su a jiki.
*9:21pm*
A daidai lokacin Aysha ta fito daga dakin su Ammar da suka riga suka yi bacci, dama addu'a ta shiga ta tofa musu.
Sama ta hau ta shiga dakin ta.
Bayan nan ta tube kayan jikinta ta daura medium towel, ta saka shower cap, sannan ta shige bathroom ta sakar wa kanta shower, fuskar ta dauke da murmushi...
Farkon haduwar su da Abraham har izuwa yau da suke a matsayin mata da miji ne ke yawo a brain din ta. Ikon Allah da girma yake, komai daya faru yazo karshe kamar bai taba faruwa ba, sai dai labari kuma.
Bayan ta fito, oil perfume ta shafe jikin ta da shi kana ta saka riga da wando na bacci masu dan kauri, saboda yanayin sanyin da ake a daren yau.
Tana cikin jera pillow daya dan hargitse ta ji shigowar Abraham, bata juyo ba, ta cigaba da abinda take.
"Ụwammm!" Ya kira sunan ta.
A hankali ta juyo gareshi, zaro beautiful eyes din ta masu haske tayi sakamakon ganin sa a tsugunne a gabanta.
"Please stop! What are you doing?"
Ta fada cikin mamaki.
Bai bata amsa ba, bai kuma tashi ba sai ma hannun ta daya riƙe cikin nasa yana murza tafin hannun ta mai laushi.
Fuskar ta ya kurawa ido cikin wata murya mai dauke da abubuwa da dama ya fara cewa
"You re a gift from God to me, shigowar ki cikin rayuwata yayi sanadin haskaka min duhu dana jima a ciki, kin so yarana tun kafin kisan ni ne mahaifin su, kin basu tarbiyya kamar y'a'yan ki duk da karancin shekarun ki, Nagode sosai da wannan taimako da kike min, Allah yasa aljanna ya zama makoma gareki, da Inna, da baffa, sannan ki yafemin abinda nayi miki kafin mu tafi Gombe, I was not my self, sannan ina rokon alfarma, dan Allah ki so ni Ko da kaɗan ne, ki so mahaifin su Ammar please ụwammmmmmm!"
Kallon shi Aysha ke yi da burgewa, ita kam idan bata so mahaifin su Ammar ba wa zata so a wannan duniyar? gaban sa itama ta durkusa, ta ɗora dayan hannun ta kan na shi hannun dake rike da hannun ta ɗayan tace "baka min laifin komai ba, na fahimce ka, sannan bazan taɓa kin ka ba, nayi alkawarin rayuwa da kai komai rintsi komai wuya"
Ajiyar zuciya mai sauti ya saki, ko bata furta tana son shi amma yaji dad'i a ransa tunda zata iya rayuwa da shi.
Hannun sa ya zare daga cikin na ta, kana ya buɗe hannun sa yace
"come, come here"
Da sauri Aysha ta fada jikin sa domin wani shauki sosai take ji a wannan daren mai cike da iska mai dadi daga ni'imar Allah.
Daga runguma, salo ya fara sanjawa, Abraham ya birkice mata, yana ƙoƙarin birkita Aysha da ita ma ta fara karban sakonnin shi, da abu ya girmama cak ya daga ta sai kan gado yayi mata rumfa da fafadd'ar kirjin sa...
Ya jima sosai yana abu ɗaya sannan ya fara kokarin su zama abu ɗaya, nan Aysha ta dawo hayyacin ta, ta fara kuka tana roko, hadi sa ture shi amma ina gogan bai ma san tana yi ba....
*12:30*
Tana kwance a saman kirjin sa yana bubbuga bayanta, murmushi dauke a fuskar sa, a yau wani yanayi na nishadi sosai yake ji, yana kara gode wa Allah daya samu Aysha a cikakkiyar mace, wanda hakan yafi komai yi masa dadi domin bai taba Experiencing hakan ba.
A yanzu samun mace da mutuncin ta na matukar wahala a wannan zamanin na yanzu, wasu sukan siyar da mutuncin su domin abin duniya or wani dalili mara tushe.
Gashin ta daya rufe fuskar ta ya tattare mata zuwa baya, sannan ya leka fuskar ta, sai faman kananun koke-koken ta take a hankali, wanda har da zallan shagwaba domin Abraham ya bi da ita a hankali kasancewar yasan ita din yarinya ce kuma budurwa.
Shafa bayan ta yayi yace "Am sorry my heroine"
(kiyi hakuri jaruma ta)
Ai fa kamar kara tunzurata yayi sai ta fara didire kafafun ta a jikin sa cikin sakalci da shagwaban da bata san ta iya ba.
Danne dariyar sa yayi yana bata hakuri hadi da yi mata wata waka ta soyayya da Yaren Igbo, cikin abun da bai fi mintuna ashirin ba wani bacci mai daɗin gaske ya ɗauke ta.....
*(Kafin na cigaba bari nayi wata yar sanarwa, masoyan littafin NoorEemaan ina mai farin cikin sanar daku cewa in Sha Allah cikin satin nan sabon book dina zai fara sauka, wanna karon bazan tafi hutu mai yawa ba Saboda yanda hannun na ke k'aik'ayin fara rubuta wannan novel mai dauke da abubuwan mabambamta ba, ku san dai akodayaushe Noor da sabon salon nake zuwar muku dashi. Wannan karon tafiyar mai zafi ce, ina mai tabbatar muku da cewa zai yi sugar fiye da Rayuwar Faheemah, mijin Ammina ne sila, papi Ne, kyautar koda, da ma Abraham. Amma paid book ne kan dari uku kacal saboda tanadin dana yiwa book din yasa bazan iya sakin sa free ba, amma ina kaunar baku dukkanin wani book nawa a matsayin free, fatan zasu yi patronazing dina, much luv habibte's)*❤️
***************
Da asuba da kansa yayi mata wanka duk da tace zata iya amma bai bar ta ba, bayan ya gama yi mata wanka shima yayi, sannan suka daura alwala ya dauke ta suka fito.
Riga mara nauyi da iyakar sa cinye red color ya sanya mata, ganin ba a tayar da sallah ba sai ya jona hand-dryer a socket ya busar mata da sumar ta yana jin dadi a ransa, domin shi din mai kaunar gashi ne.
Yana gama wa yaji ana ƙoƙarin tayar da sallah, a gurguje ya saka kaya, sannan ya shimfida mata sallaya kana ya bata sumbata a lips mai tsayawa a rai ya fice da sauri.
Da murmushi Aysha ta bi bayan shi, kana cikin shauki ta rufe idanun ta da har yanzu basu gama sacewa daga kumburin da suka yi ba, Sakamakon kukan data yi a jiya, ta yi nisa a duniyar tunanin Abraham ba tare da ita kanta ta san tana hakan ba, sai ji tayi liman ya tafi ruku'u kana ta dawo hayyacin ta, cikin sauri ta mike ta tada kabbara...
Shida saura Abraham ya dawo ya ganta zaune tana karatun Alqur'ani, gabanta ya zo ya zauna hadi da tankwashe kafafunsa yana kallon ta cike da burgewa.
Sai da Aysha ta kai aya, ta dago ta ganshi ya kura mata ido, girgiza kanta tayi tana murmushi sannan ta daga hannu tayi addu'oi'n ta, a tare suka shafa.
Qur'anin ya karba ya ajiye a muhallin sa kana ya taya ta zare hijab din jikin ta, kanannad'ewa tayi a jikin sa tana boye fuskar ta.
Dariya sosai ta bashi, yana ƙoƙarin dagota tana sake shige masa jiki.
Abin dariya ma, wanda take jin kunyar sa kuma take kara shiga jikin sa, cikin muryar dariya yace
"Hey stop! Why are you doing this"
ai kamar kara tunzurata yake domin sake shiga jikin sa take, sai kawai ya gyale ta yana murmushi, can da dan jimawa ya ga tana kokarin barin jikin shi, kara riƙe ta yayi bai bata damar tashi ba ya tambaye ta ina zata.
Tace zata je duba ƴaƴan ta sannan ta ɗora musu breakfast.
Yaki yarda yace ta kwanta ta huta, zai je yayi duk abinda ya dace ta yi.
Ba dan ta so ba ta amince, ya kwantar da ita ya fita, bayan ya sake kissing dinta... tun idanun ta biyu har bacci ya dauke ta dama akwai sauran gajiya a jikin ta.
Abraham yana sauka ya ga mai aiki na gyara falo, cikin girmamawa ta gaishe shi ya amsa, kana ya shige dakin su Ammar.
A nutse ya tarar suna bacci, Anwar har da ɗora wa Ammar kafa a baki amma haka suke manne da juna, dariya yayi mara sauti yana girgiza kansa kana ya karasa a hankali ya gyara musu kwanciya hadi da basu sumbata a goshi sannan ya fita.
Kitchen ya shiga, hannu ya dora a kugu, shi kam idan akwai abinda bai iya ba ko yake bashi wahala toh girki ne.
Dankalin turawa ya fara ferewa, ferewar ma abin dariya domin sai ya haɗa dankali da bawo mai yawa ya fere ya zubar, bayan ya gama ko gishiri bai barbada ba ya shiga suya.
Bayan ya gama da dankali, ya fasa kwai goma ya saka albasa, attaruhu, da maggi da sauran kadan ya yi yawa a cikin kwan, kana ya hau suya, bai bari kwan ya soyu ba ya juya shi hakan yasa ya hargitse, dan bata fuska yayi irin ba haka na so ba.
Bayan nan ya kwashe, ya haɗa da dankalin a warmer daya ya kai dining ya dawo, sannan ya tafasa ruwa a kettle ya juye a flask ya Kai dining domin shikam bai iya dafa irin shayin ta ba, ya kuwa haɗa duban gumi, kamar wanda ya tuka tuwon mutane talatin.
Ya fito daga kitchen kenan yaga mai aiki tana kokarin komawa bangaren su, dama aiki kadai ke shigo dasu ɓangaren nan, saboda hatta girki a bangaren su suke yi, domin akwai komai a wajen, Idan sun girka sai su zubawa mai gadi da mai gyara farfajiyar gida, kuma lafiyayyen abinci suke yi.
Yace mata "ɗan gyara kitchen dinan please"
Cikin girmamawa ta amsa kana ta nufi kitchen din, a ranta tana jinjina saukin kan shi.
Dakin su Ammar ya leka ya tarar da sun tashi, da gudu suka fada jikin sa wanda ya ji dad'in hakan, suka gaishe shi ya amsa cikin tsananin son su,
Kana ya cire musu kaya suka nufi banɗaki domin yi musu wanka.
Ta bangaren Aysha kuwa ita ma a daidai lokacin ta tashi, mikewa tayi ta kalli dakin babu ko datti sai gadon daya hargitse a hankali ta shiga gyarawa, domin Abraham ya sanja bedsheet tun jiyan, bayan ta gama ta cire rigar jikin ta, ta daura towel inda hannun ta ya taba sarkan wuyan ta, dan shiru tayi kana a hankali ta sa hannu ta cire sarkan, ta kuma yi hakan ne domin tasan ganin sarkan zai dinga yawan tuno wa Abraham da rayuwar sa ta baya...
Ruwa mai zafi ta haɗa wa kanta tayi wanka kana ta fito ta shirya cikin wata gown ta atamfa mai ruwan ja da dark blue daya yi matukar karban farar fatar ta.
Powder da kwalli kadai ta saka, sannan ta yi simple dauri daya fito da gashinta ta baya.
Flat shoe red color ta saka yayi matuƙar yi mata kyau, musamman da jan kunshi kafar ta da aka mata a lokacin biki mai sellotape ya sake maroon.
Turare ta fesa sama-sama kana ta bude kofar ta fita, hakan yayi daidai da fitowar Abraham daga dakin sa da alama shima wanka yayi sai zuba kamshi yake, ga su Twins da ta hango zaune daga falon kasa a shirye su ma.
Sakin baki Abraham yayi yana kallon Aysha, domin bata taɓa yi masa mugun kyau irin wanna ba, cikin sauri ya karaso gabanta ya daga ta cak ya shiga juyi da ita yana fadin
"You re so beautiful Ụwammmmmmmmm!"
*AYSHA*
Rike shi tayi da kyau tana dariya, wanda dariyarta ta ja hankalin su Ammar, da gudu suka hau saman suka yi tsaye suna dariya suma, sai da Abraham ya gaji dan kansa kana ya sauke ta, sannan suka sauka kasa gaba-daya.
Bayan duk sun zauna, Aysha ta bude warmer domin serving din su, sai dai yanda taga dankalin yayi wani iri yasa wata dariya da bata shirya zuwan sa ba yazo mata, Abraham kuwa bata rai yayi cikin wasa shi da yake jiran ta yaba masa.
"Sorry" tace tana rufe bakin ta, girgiza kansa yayi irin zan kama ki dinan.
Murmushi tayi kana ta shiga zubawa kowa, sannan ta haɗa tea mai kauri wa kowa amma banda Abraham domin shi ya fi son Black tea.
Ta saka masa Lipton mai flavour din mix fruit, sai ta saka masa two cube of sugar.
Kusan a tare ita da Abraham suka kai lomar farko na abincin baki ba tare da sun hadiya ba...
kallon-kallon suka shiga yi a junan su kana suka fashe da dariya a lokaci daya, saboda yanda dandanon abincin yayi wani iri ba dadi, amma su twins basu damu ba ci suke sosai...
Ai kuwa Abraham da Aysha basu iya cin dankalin ba, gwara ma kwan sai shayi da suka kora dashi.
******
Abraham kuwa yau yaki fita office, wai zai kula da AYSHA duk da tace masa lafiyar ta kalau, amma yaki, sun kasance cikin farinciki da annushuwa har dare musamman da su Twins ke nan hakan ya kara wa abin armashi.
*TWO MONTH LATER*
A gidan Abraham kullum cikin farinciki suke, ga wata ingantacciyar dangantaka mai dauke da zallan so da ke kara wanzuwa a tsakanin su. Aysha ta jajirce sosai wurin ganin komai da zai kawo farinciki a gidan tayi shi.
Kamar kullum, a kowacce safiya da bayan sallar asuba sai Aysha ta yi wa Abraham karin Alqur'ani, duk da yana zuwa daukan karatu wurin limamun da ya karbi Musulunci, Amma tana kara masa da kuma wasu littattafai addini.
Kamar yau zaune take da farin hijab yayin da Abraham ke sanye da jallabiya baki suna fuskantar juna, dukkanin su da qur'ani dauke a hannun su.
Bayan ta gama biya masa kusan sau biyar, tana jiran shima ya biya ta ji ko ya rike, ya fara biya mata ayar farko kenan taji muryar sa na rawa kana kuka ya kwace masa...
A matukar rude ta ajiye qur'anin a gefe ta matso sosai ta shige jikin sa, hannun sa daya rufe fuska dashi ta cire, cikin sanyin murya tace
"what's it? Why are you crying"
Shiru bai bata amsa ba, Aysha ta kafe shi da ido kwalla na cika idanun ta, tasan halin mijin ta, ta sani cewa ba ƙaramin abu ne zai sa shi kuka haka ba.
Fuskar Aysha ya riko cikin tafin hannun sa, hawaye na zuba a idanun sa yace
"my parent are not Muslims...you no they love me a lot... and i love them too. Everyday before my dad dies he always tells me he loves me, my parents are dead! Where are they today? You could pray for your parents, but i can't pray for my parents.
This is the reality, don't underestimate the blessing Allah subhanahu wata'ala has given you"
(Iyayena ba Muslimai bane, kin San Ina kaunar su sosai, su ma suna kauna ta, a kullum mahaifina kafin ya mutu ya kan ce min yana sona. iyayena sun mutu, a wani makoma suke yanzu?
Ke zaki iya yiwa Iyayen ki addu'a, amma Ni bazan iya mu su ba, domin wanna shine gaskiya, kada bawa ya butulcewa albarka da Allah yayi masa)
Jinjina kai Aysha take tana kuka, domin tabbas dukkanin maganganun sa babu karya, ta kuma tausaya masa ainun, hakika duk wanda yake cikin Musulunci ya godewa ni'imar da Allah ya yi masa.
Hannu tasa tana share masa hawaye amma hawayen yaki tsayuwa, kamar ba Abraham ba.
Ganin kukan sa na taba zuciyar ta sosai, hakan yasa babu zato bare tsammani ya ji Aysha ta kama lower lips dinsa tana kissing din sa for some minutes kana ta hade bakin su waje daya, cikin aminci suka fada duniyar ma'aurata.
Bayan sun dawo nutsuwar su sun yi wanka, Aysha na kwance a jikin sa, yayinda Abraham ke shafa gashin ta in a circular motion ya tsinci murya ta mai dadi tace
" ina rokon wata alfarma daga gare ka, dan Allah, domin rintsi komai wuya Kada ka bari su Ammar su san cewa ba nice mahaifiyarsu ba, wallahi ranar dana fara ganin su na kamu da son su sosai, bana so su dauka cewa basu da uwa a duniya, bana so suyi kukan maraici ta wajen uwa Please"
A hankali ya ware idanun sa, ya kara shigar da ita jikin sa, murmushi dauke a fuskar sa na farincikin samun life partner kamar Aysha, son ta mai zafin gaske na sake ratsa shi yace
"ụwammmm! Har abada kece mahaifiyar su Ammar, i swear wasu lokutan ina manta cewa ba kece uwar su ba, in dai wannan ne, baki da damuwa"
Murmushi mai sauti tayi cikin jin dadi, kana ta lumshe idanun ta, babu jimawa wani bacci mai dadi gasken ya dauke su kusan a tare...
*Laifi dadi karewa😝 one more page left fans*
Share share share fisabilillah
CommentI'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
NoorEemaan✨
07082281566
🍇🍇ABRAHAM🍓🍓
*First edition*
*WATTPAD*
@NoorEemaan
https://facebook.com/groups/943534712916776/
Masu amfani da facebook su yi join ta wanna link din.
_@sis Mariam jumare, @Ak saraki, @sdeentm,@uncle Ismail, @sis Amina Kabir caps, ina godiya sosai da sosai, hakika kuna taimaka min da posting tun daga farkon fara posting book din nan har harshe ba tare da gajiyawa ba, Allah ya sa muku da alkhairi_.🤍❤️🤍
Alhamdulillah
#ending
Chapter 71-72
Baccin awa daya kadai suka yi. Abraham ne ya fara tashi, ya kura wa fuskar Aysha ido, gani yayi ta kara haske sosai kamar ka taba ta jini ya fito, har kumatu ta ajiye kai kace kwai ta boye a ciki, gwanin sha'awa da kyau.
A hankali ta fara buɗe idanun ta...karaf idanun su suka sarke dana juna, murmushin ta mai kyau ta sakar masa, ya sumbace goshin ta sannan ya mayar mata da martani yace
"Nwunye mm" (my wife/matata).
Murmushi tayi domin a duk lokacin data ji yayi yare abin burge ta yake, har tana ji dama ta iya ita ma.
"Meye ma'anar abinda ka fada yanzu" Aysha ta tambaye shi cikin turanci.
"It means my wife" ya mayar mata da martani.
Jinjina kai tayi alamun ta gane kana tace
"I love You so much my husband"
Cikin zallan mamaki Abraham ya kafe Aysha da ido, sai yake jin kamar kunnuwan sa ne basu jiye masa daidai ba, Aysha ta fahimci hakan sai ta kara maimaita masa tana kifa kanta a kirjin shi...
Wata wawuyar runguma ya sake mata, duk da tana saman kirjin nasa ya shiga birgima da ita kan gadon kamar wasu kananan yara sai faman dariya suke.
******************
Haka rayuwar su ta cigaba da tafiya, A kullum kaunar da suke wa juna kara yawa take.
*ANTY SARAH*
Bayan ta koma kauyen su, a ranar tayi kuka sosai kamar ranta zai fita, tayi nadamar mugayen halayen ta na baya ya fi cikin kwando.
Kudin da ABRAHAM ya bata da shi ta fara sana'a inda anan take samu tana rufawa kanta asiri, amma bata jin dadin komai a rayuwa, sakamakon mugayen halayen ta na baya, domin hakkin rai ba wasa bane, duk da ba ita tayi kissan ba, kullum cikin kuka da nadama take, a haka ta cigaba da rayuwar ta...
Bayan kwana biyu Abraham yayi musu booking flight suka je har wajen dangin iyayen sa, abin mamaki sun karbi shi hannun biyu-biyu, duk da ya sanar da su ya zama muslumi sannan ya auri Hausa Fulani
Ya basu labarin Madam Gloria, sun kuma yi mamaki da Allah wadai da mugayen halayen Madam Gloria.
sannan sun karbi Aysha a matsayin suruka a gare su, sosai Abraham yaji dadi dama tsoron sa kenan kada a samu matsala, kuma gashi alhamdulillah an samu akasin haka. Hak'ik'a addu'a bata taɓa faduwa kasa a banza...
*****★**********★******
*SOME MONTHS LATER*
A parking lot ya daidaita parking din motar sa kirar Mercedes Benz white color, kana ya fito rike da brife case a hannun sa, ya kara kyau hadi da dan jiki kadan wanda yayi matuƙar amsar sa, rufe motar yayi kana ya nufi cikin gidan.
Sallama dauke a bakin sa ya shige falon, inda ya tarar da Ammar da Anwar sun baza littafan su da alama home-work suke, da gudu suka ruga jin muryar mahaifin su suka dane shi, cikin kaunar ya'yan sa ya rungume su yace
"Uma aka mm how are you doing?" (Y'ay'ana ya kuke)
"We are Fine Daddy" suka amsa a tare, domin yana dan koya musu Igbo, kuma yaran na da kunnen ji, domin suna saurin rike wa.
Sauke su yayi ya shafa kan su... rarraba idanun sa ya shiga yi amma bai ga abinda yake nema ba.
Kallon su Ammar yayi yace "where is Ammuh?"
Suka ce "tana bacci".
Jinjina kai yayi cikin tausayin ta kana ya nufi saman, a ko ina zai fada cewa matar sa jaruma ce, domin duk da cikin ta ya tsufa amma haka take ƙoƙarin kula da su daga shi har su Ammar, wani zubin sai ya bata rai take barin aikin, domin shi kam tausaya mata yake amma ita kam ce masa take tana jin dadin aikin, wai motsa jiki take.
A hankali ya sanya kafar sa cikin dakin sanyi Ac da dadaddan k'amshin dakin ya bugi hancin sa, lumshe ido yayi kana ya ware su kan Aysha dake bacci da tulelen cikin ta haihuwa ko yau ko gobe.
Gaban gadon ya karasa ya zauna a kasan tiles ya tankwashe kafafunsa, kafar ta daya kumbura ya sumbata kana ya shiga yi mata tausa tsawon Mintuna goma, sannan ta motsa, cikin sauri ya matso gab da ita, yace "You re awake"
Jinjina masa Kai tayi tana Murmushi, dan kara kan sa yayi kan cikin ta dake ta motsi yace "how are my babies doing?"
Cikin shagwaba tace "babies? "
Dariya yayi yace "yes nah"
Dan ture kanshi tayi kana tace "i'm carrying baby, not babies" ta fada cikin iyakar gaskiyar ta, domin idan yace babies dinnan tsoro yake bata.
Dan girgiza kan sa yayi da murmushi kan fuskar sa, ya lura ta koyi rigima kwanan nan. Hannunta ya manna wa sumbata yace "A hụrụ m gị na ányá Ụwammm, i mara mma"
(I love you my life, you re beautiful)
Dan far da ido tayi cikin jin dadi, a duk lokacin daya ci mata yana son ta, tana da kyau wani girma kanta keyi, duk da cikin ya sata dan muni amma bai fasa gaya mata haka ba, kullum a sallar ta sai tayi godiya ga Allah daya bata miji kamar Abraham, ko a aljanna tana fata da addu'a ya zama miji a gare ta.
**********************
_*INNAH*_
Ta bangaren ta kuwa Abraham ya siya mata gida a nan Kaduna domin ta dawo kusa da su, amma tace ita kam bata so ta fi zama a tushen ta, Abraham ya bawa Anty Bintu gidan halak malak saboda hallacin data yiwa rayuwarsa (Aysha).
ANTY Bintu tayi godiya ba iyaka, tana kuma taya Aysha murnan samun miji ɗaya tamkar da dubu.
Abraham bai kyale Inna ba sai daya sa aka fasa gidan ta na Gombe aka dawo mata da komai ginin zamani, sannan ya bata kudade masu yawan gaske ta fara business. Inna fa ta dawo yar business ta yi sharrrr ta ita ainayin skin color dinta ya fito saboda jindadin rayuwa da kwanciyar hankali da ta samu .
Yan'uwan su baffa da suka ji Inna tayi arziki suka kwaso kansu suka zo suna bata hakuri cikin borin kunya, Inna abu ɗaya ta duba ta yafe masu darajar mijin ta baffa duk da baya raye, amma har gobe kaunar mijin ta na manne a ranta.
Wanna kenan.
____★________★ __
_*2:00pm*_
malam bahaushe yace dare mahutan bawa, ko ina yayi tsit sakamakon baccin da mafi yawan mutane ke yi, hakan take ga su Abraham, domin kwance Aysha take ta ɗora kanta kan kirjin sa suna baccin su cike da nutsuwa, can cikin bacci Aysha taji kamar wani abu ya karce ta, a dan zabure ta mike zaune, nan ta kara ji mararta ta kulle sosai, yarfa hannun tayi tana cije labb'an ta, domin zafin ya fara zama unbearable, hakan yasa ta saki kuka, ta shiga girgiza Abraham...
A rude ya tashi ganin tana kuka ya tada hankalin sa, take ya fahimci nakuda ce ta zo, cikin sauri ya mike ya buɗe sif dinta ya dauko mata daya daga cikin maternity gown dinta ya sanya mata, sannan shima ya saka riga da wando, mukullin mota ya dauko da jakar da suka hada kayan haihuwa kana ya dauke ta kamar yar jaririya suka sauka kasa...
Gaban Mota ya buɗe ya saka ta a ciki bayan ya kwantar da kujerar, sannan shima ya shiga ya danna horn wa mai gadi dake gyangyadi, a 360 mai gadi ya buɗe kofar Abraham ya cilla hancin motar sa waje, yama manta da su Ammar dake bacci a dakin su, Burin sa a yanzu shine matar sa ta rabu da wanna zafin da take ji.
Had'add'en private hospital ya kawo ta, inda cikin sauri da sanin makamin aiki suka karbe ta, kana suka yi *maternity ward* da ita ba tare da sun yarda ya shiga ba.
Safa da marwa ya shiga yi fuskar sa na bayyana tsananin damuwar da yake ciki, fata da muradin sa Aysha ta dawo gareshi, domin bazai iya juran rasa ta ba.
Daga karshe ma famfo dake cikin asibiti ya nufa yayi alwala kana yaje mota ya dauko sallaya ya dawo ya fara nafilfili...
Bayan ya gama ya zauna kan sallayar yana addu'o'in sa, ya ga wata nurse ta zo wajen shi murmushi dauke kan fuskar ta, boyayyen ajiyar zuciya ya sauke kana ya mike cikin sauri yana tambayar ta ina matar sa, nurse ta sake Murmushi tace
"congratulations sir, please come with me"
Nan Abraham ya bita zuwa dakin hutun da aka mayar da Aysha kamar zai tashi sama... Bakin kofar nurse din ta tsaya ta nuna masa ya shiga dakin yayinda ita kuma ta koma domin kula da wata patient da aka kawo Sakamakon barin cikin da ta yi, dama haka rayuwa take, wani yana farinciki at the same time wani yana kuka.
Buɗe kofar yayi ya shiga, kwance ya hango Aysha da fuskar ta yayi fayau tana jefan sa da murmushin kauna, da sauri ya karasa wajen ta, dan dago ta yayi hadi da rungume ta yana faman jere mata sannu, ga sumbata da yake ta faman sarkar mata a ko ina, shi kam yama manta da wani cikin jikin ta balle ya damu da abinda ta haifa, shi dai burin shi ya cika tunda tana cikin koshin lafiya.
"Wai ina su Ammar ne" ta tambaye shi cikin muryar ta da ta yi sanyi kalau saboda wuyan haihuwar da ta sha.
Sai a lokacin gogan ya tuna, dan shafa kansa yayi yace "wallahi yanzu na samu nutsuwa uwammm! suna bacci, kuma kin san gobe Saturday baza su tashi da wuri ba tunda ba school"
"Uhmmm uhmmm ban yarda ba, jeka dauko min yarana Please, su kadai ne fa" tace tana shagwa6e masa.
Zai yi magana kenan suka ji kukan jarirai sai a lokacin Abraham ya tuna ashe fa ta haihu, da sauri ya nufi gadon da suke kwance, wani murmushin farinciki ya saki kana yace "yes! I told you Ụwammmm! I told you that you re giving birth to twin but you don't believe me, thank you so much for giving me these babies... ooh my cuties welcome to the world, come, come, come to daddy" yace yana daukan su hadi da rungume su a jikin sa, yana jin kaunar su na ratsa shi.
Aysha kuwa ta zama yar kallo, murmushi take yi, tana kallon zallan farinciki da zumudin dake shimfide a kyakkyawar fuskar mijin ta.
Da misalin ƙarfe bakwai na safe aka sallami su, kasancewar an gwada su an tabbatar daga uwar har jariran suna lafiya.
Tun kafin su zo gida ya fara kira yana sanarwa yan'uwa da abokan arziki.
Suna shiga gida suka tarar tashin su Ammar kenan daga bacci suna neman Ammuh'n su, ai da suka ga jarirai suka hau murna wai sun yi kannai, Ammar yace ya dauki hassana itace tasa, Anwar ma yace ya dauki usaina, haƙa dai suka dinga shirme kala² cike da yarinta.
A ranar Abraham ya sanjawa Aysha waya zuwa kirar iPhone latest.
Murna sosai Aysha tayi, ta kuma gode masa sosai duk da ya nuna baya son godiyar.
A daren Abraham ya bawa Aysha damar zabar w yaran suna, ba kuma ɗan ba zai iya zaba musu ba, domin yayi zurfin a sanin addini sosai fiye da tunanin mai tunani, wasu lokutan Aysha tana yaba masa ta yanda baya wasa da addinin sa, babu wanda za a faɗa wa musulunta yayi ya yarda kai kace a ciki ya taso tun yana karami.
Kawai ya bawa Aysha daman ne domin ta cancanci fiye y hakan a wajen shi.
Suhailat da Safiyya Aysha ta zama musu. Abraham kuma ya saka musu sunan yare Amanda da Chioma... da Aysha taji ma'anar sunan sai ta kamu da son sunan sosai wani zubin da shi take kiran su...
Ranar da su Amanda suka cika sati Daya da haihuwa aka sha sunan su daya kawatu sosai sannan mutane sun hallara sosai, an ci an sha an raba kyaututtuka masu ɗauke da hotunan yan biyu...
*****. . *****. *****.
BAYAN SHEKARA BIYU
Hayaniya ke tashi a falo inda Abraham ke zaune cikin yaran sa hudu, Ammar, Anwar, Suhailat (Amanda), Safiyya (Chioma) suna buga game.
Yanda yake biye musu sai ka rantse ba shi ne mahaifin su ba, haka suke tamkar abokai, amma hakan baya hana idan sun yi laifi yaki hukunta su ba, duk da tarin kauna da shakuwa dake tsakanin su.
Aysha dake tsaye a kitchen cikin shadda tsad'ad'iyya maroon color tana girki sai faman girgiza kanta take tana jin draman su tana murmushi, kamar yadda akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin shi da yaran sa, haka itama ya dauke ta kawar sa, kanwar sa, abokiyar shawarar sa, sannan matar sa abin son da kaunar sa.
Aysha ta kara kyau, aji, wayewa, hadi da girma, soyayyar ta da Abraham kullum karuwa take, duk da ana samun sabani, saboda masu iya magana na cewa tsakanin haƙora da karshe na samun sabani, sai dai basa bari fadan su ya kai dare ba tare da sun shirya kan su ba.
"Ammuh!!!" Ta ji yaran duka sun hada baki wurin kiranta har da uban su.
Dariya tayi kasa-kasa tace "Am coming guys"
Wanke hannun ta tayi, ta goge da towel sannan ta fito, waje ta samu ta zauna cikin su tace "gani"
"Surprise!"
Suka hada baki wurin fadin haka, sannan suka fito da ticket da ke boye a hannunsu masu yawa, Abraham ta kalla ya kanne mata ido daya, dauke kanta tayi cikin sauri saboda yaran.
Sannan cikin farincki ta bashi side hug domin ticket din zuwa aikin hajji ne ya biya musu gaba-daya, sannan ya biyawa Inna da Anty bintu, kuma tare zasu tafi cikin satin nan...
Yaran ma gaba-daya suka rungume shi ya kuwa saka karfaffan hannunwan sa ya zagaye su duka.
Kallon Aysha yayi yace "how will I say i Love You all in Hausa?"
"Ina son ku duka" Aysha ta fada masa.
"i...in...a son....ku... du... ka" ya maimaita kalmar a rarrabe kamar mai koyan magana, har yanzu kam Hausa taki zama a Bakin sa.
Gaba-daƴa suka fashe da dariya jin yanda yayi Hausar, shi ma biye musu yayi suka dinga dariyar a tare, abin gwanin kyau da burgewa, what a happy family!.
I believe every ending is another beautiful begining.
Alhamdulillah!
Special thanks to:
Noor novelist world
Sarautar's library
Safrat group
Mijin yarinya group
Neat lady palace
Ranar nadama group
Aludra group
Elegant online writers group
Matan buri fans
Taskar real ladingo
Surrayhms novels
Taskar mammy Kabeer
Kwaila fans group
Nana haleema palace
Gidan girki da gyaran jiki group
Fitar rana comments section
Mi Amour world
Fataucin mata fans
Hausa novels group
Dama sauran groups da Abraham ya je ina godiya a gareku Allah ya bar kauna...
Bazan manta da wattpad fans dina ba, Nagode muku sosai.
*Ya rabb Nagode bisa Ni'imar ka gareni, ya rabb na gode daka bani ikon kammala wanna book na Abraham cikin koshin lafiya. Ya rabb kuskure dana yi cikin littafin nan ka yafe min, wanda na fada daidai ka bani ladan sa da Ni da reader's*
*Masoyan littafin NoorEemaan ina mai godiya a gareku da yadda kuke karban duk wani novel dana kawo muku hannu biyu-biyu, tabbas na ga kauna a Abraham, zan kuma cigaba da kawo muku d'ad'add'an labari mai cike da abubuwa da dama in Sha Allah, just keep on following my pen*🖋️
_in Sha Allah kamar yadda na fada new book zai fara sauka cikin satin nan, fatan zaku so shi kamar sauran domin zai yi matukar kayatar daku saboda salon daban yake, much love habibte's_
*Hoorain mai kusumbi (the hunch back girl) shine first paid novel Dina, yanzu haka Ina da complete pages da kuma complete document, duk wacce ta biya zata dinga ganin update kullum.
*Saboda farincikin yadda kuka karbi littafin Abraham dama sauran books dina, yasa xan siyar muku da Hoorain mai kusumbi a kan Naira dari daya (100) wallahi naji dadin addu'oi'n ku sosai, sannan nayi farinciki, amma a ka'ida book din Naira dari uku ne, haka na siyar wa mutane a farkon typing din, dan Allah duk wacce ta biya dari ta account number na zan sata a group wanda zata dinga ganin update kullum sau biyu in Sha Allah. 2261488155*
_Rukayya Haruna
Zenith bank, yan nijer Kuma zasu turo min da katin Airtel na dari biyu, ta Whatsapp number 07082281566, kar ku bari a baku labarin Hoorain mai kusumbi(the hunch back girl) sannan nan gaba zai iya dawowa real price din shi na dari uku, so hurry up and subscribe your's kafin in dawo da shi ainihin farashin sa, Ngd_.
Wed, may 11 2022
Reposted
On 20th Oct 2022.
Share share share fisabilillah.
I'm selling data to all Nigerian network Thank you for contacting Sdeendtm!
BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE
I'm
selling MTN data with this cheap price
MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
Dial *131*4# or
*460*260# to check Data balance Validity 1 month
Airtel,9mobile and Glo also available.
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills*
Whatsapp OR
Call 0806626851
No comments