Recent Updates

Zazzafan Kishi Sabon Salo


💥ZAZZAFAN KISHI...!*

        _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA
             *Dukkan godiya da yabo sun tabbata ga Allah madaukakin sarki. Tsira da amincin Allah su ƙara tabbata ga Shugabanmu Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallam ina ƙara godiya ga Allah madaukakin sarki da ya bani baiwa da ikon rubuta wannan littafi mai suna ZAZZAFAN KISHI sabon salo Ubangiji ya sanya 'yan uwa musulmi su amfana da faɗakarwa da ke cikinsa, kuskuren da ke ciki kuma ubangiji ya yafe mana*

*Special thanks to my one & only Aunty sis thank you so much for your love & kindness*
 
      _Na sadaukar da wannan littafi ga Zarah Bb alkhairi Allah ya kai miki a duk inda kike na gode kwarai da ƙaunarki gareni, Allahu yabar zumunci_

01....

Cikin Sanɗa ta tura Gate ɗin shigowa gidansu sai da ta fara leƙa tsakar gida ta ga Mama bata nan tana ɗaki muradinta ta shige ɗakinta kafin Wani ido ya ganta batasan cewa Mama tana nan tsaye a jikin ƙofar ɗakinta labulle da ya kare ta ne ya hanata ganinta, tana daff da isa ƙofar ɗakinta ta jin an kira sunanta cikin tsawa da sai da gabanta yai mummunan faɗuwa "Ke! Jeeddah zo nan munafuka yarinya wato ke har abada ba za a faɗa ki ji ba?" duk abinda na faɗa miki akan ki rabuda Bilal ta bayan kunne ki yake bi ya fita to wallahi kodai ki rabuda shi ta ruwan sanyi ko kuma jikinki ne zai gaya miki sakarya kawai.
Haɗe rai Jeeddah tayi ko kaɗan bataso ta ji Mama ta ambata mata kalmar rabuwa da Bilal. Ko yanzu jin maganganun da take faɗa jin su take yi tamkar ana yayafa mata tafasasshen ruwan zafi a sassan jiki sai wani cuno baki gaba take yi gami da gunguni ƙasa-ƙasa wanda ita kaɗai ke jin abinda take faɗa.
   "Da za ki ɗauke shawara ta Mama da kin daina yi wa Jeeddah rantsuwa don ni fa gani nake yi tamkar rantsuwarki ƙara zurfafa mata soyayyar Bilal shattima take yi.
Cewar Khairat wacce ta fito daga ɗaki.
Kafin Mama tai magana Jeeddah ta tasowa Khairat tamkar za ta kifa mata mari "Tou baƙar munafuka algunguma ina ruwanki zuga-zugi wutar maƙera ke kam kin shiga uku Khairat ace ba ki da sana'a sai ta zugi, da shiga abinda bai shafe ki ba kin dai ji haushi wallahi.
Jeeddah ta faɗa tana gallawa Khairat muguwar harara.
  Cike da takaici Mama ta saki labulle ta nufo wajen ta gadan-gadan, gani haka yasa Jeeddah ta ɓalla da gudu ta koma bakin gate tasan ba abu mai wuya bane Mama ta rufe ta da mugun duka.
Mama tai kwafa gami da furta "ashe karyar rashin kunya ki ke yi da ki tsaya ki ga yadda zan haɗa miki majina da jini sai na gurje miki baki nan naki mai tsiwa da rashin kunyar tsiya.
Tintsirewa da dariya Khairat tayi tana faɗin "Mama ki bi ta wallahi za ta iya komawa gidansu Bilal ta kwana kisan dai halinta ba wadatatce hankali ne da ita ba.
  "Mtsss.... Mama ta ja tsaki tare da nufar kitchen tana faɗin "Ta daɗe ba ta koma ba ai na fi so ta koma ɗin hakan zai ƙara tabbatar min da da bata ɗauke ni a bakin komai ba. Duk abin da take yi kar ta fasa ta ci-gaba Allah ya kawo min Ɗa nan shi kaɗai ne zai saita ta.
Sosai Khairat take kwasar dariya abinta saboda tasan karyar Jeddah ta ƙare muddin Mama ta faɗawa Ya Kabeer ta sake zuwa gidansu Bilal mai kwatar da hannunshi sai Allah saboda ko jiya sai da ya zaunar da ita ya kashe mata gargaɗi akan ta daina zuwa gidansu Bilal shattima, don ba mutuncinta bane tana budurwa ta dinga bin saurayi gidansu amma da yake kunne ƙashi ne da ita sai da taga Mama ta fita asibiti dubiya, ta fake da zuwa kitso wajen A'isha shattima ƙanwar Bilal wacce ta kasance ƙawarta.
Khairat ta juya ta koma ɗaki dama tana kallo BB naija ta ji yo faɗan mama shine ta fito kar ayi ba ita.
Da zarrar Mama ta hana Jeeddah fita zance wurin Bilal sai kawai ya tsira fushi ya ɗauke ƙafa, ita kuma rasa kunya beran toka ta ɗibi ƙafafuwa ba kunya balle tsoron Allah ta bi shi gidansu, da suna ta je wajen A'isha daga nan ta rarrashe abinta. Shekarar su shidda su na zuba soyayya ta fitar hankali kawo yanzu Bilal bai ajiye ko kwarar bulo guda ɗaya da suna gini ba. Idan kuma aka ce ya turo da magabatasa sai buge da cewa a ƙara mishi lokaci ya fara gini saboda ya fiso ya fara gina gidan da za su zauna, bayaso zama gidan haya kasancewar  Jeeddah da Khairat sun  kammala NCE Ya Kabeer ya samar musu da koyarwa a secondary School sau uku Jeeddah tana kwasar adashe 100k a ɓoye wanda suke yi a school ɗin da take teaching tana ba Bilal Shattima ba tare da gida an sani ba, da suna fara koda buga musu bulo ne, amma sai goga naku ya darganta ƙudin. Gaba ɗaya salary ta akanshi yake ƙarewa wani abinda zai ƙara ba ku haushi da takaici da zarrar ƙudi sun shiga hannunsa sai ka nemi su ka rasa shi kanshi Idan ka titse shi ba zai iya faɗa maka takamamin abinda yai da su ba. Sai kace mai caca ba kuma caca yake yi ba irinsa ne bahaushe yai wa laƙabi da mai rariya hannu.
Gashi dai ba aiki fari balle na baƙi barshi dai da tsalla wanka ya ji gogagu kaya ya fita zaman majalisa har kwatance sa ake yi a unguwa wajen iya wanka da gayu bashi da wani aiki da ya wuce ya koma majalisa ya zauna suna gardamar siyasa ko ta kwallon ƙafa da irin-irinsa marasa abin yi duk wani shige da fice na mutane unguwa akan idanuwansu. Duk yadda zan misalta muku lalacewa da mutuwar zuciya Bilal shattima ba za ku gane nan take ba dole sai na nusa da ku cikin ainihin tarihin rayuwarsa.
A karo na biyu da Jeeddah ta ƙara leƙowa bata ga Mama a tsakar gida ba tana kitchen tai sauri ta shige ɗakinsu tana zuwa ta jefawa Khairat jakkarta mai ɗauke da kayan kitso sai akan fuskar Khairat wacce ta shagala matuƙa da kallon da take yi akan akwatin talabijin robar man kitso da ke ciki jakkar ta bugi goshinta "ouchhh.....miye haka ba ki da hankali ne da za ki yi min irin wannan jifa da kin fasa min goshi fa?"
Khairat ta faɗa rai ɓace tana shafar goshinta.
    "Ai so nayi na fasa goshin naki baƙar munafuka, wacce bata ɓoye sirri duk yanda nai sirri da ke sai kin faɗawa Mama.
  Jeeddah ta faɗa tana wulgawa Khairat harara.
   "Kar ki sake kirana da munafuka.
"Me za ki yi idan na ƙara?"
Jeeddah tai magana gami da tunƙarar Khairat da ke zaune akan gado.
   "Sai na faɗawa Ya Kabeer yau ma kin je zance wuri Bilal Shattima.
Sosai ta tsorata da jin furucin Khairat cikin kwantar da murya ta shiga ba ta haƙuri "kar ki yi min haka Khairat kinsan Ya Kabeer ba hankali ne dashi ba zai iya karya min ƙafa ko hannu Don Allah ki rufa min asiri na tuba ba zan ƙara zuwa gidan nasu ba yau ma kitso naje kema kinsan da haka.
    Dariyar mugunta Khairat tayi gami da faɗin "A'a bansan ni ba kar ki lauye ni ki ja min laifinki ya shafe ni.
    "Ki ji tsoron Allah Khairat kafin na fita gidanan sai da na faɗa miki kitso zan je.
"Amma ai ba gidansu Bilal ki ka ce min za ki je ba, to ubanme ya kwashe ƙafafuwanki ya kai ki can, kafin ki zubar da mutuncin gidanan gara Ya Kabeer ya karya ki ko za ki dawo cikin hankalinki, kin ɗauki soyayyar duniya kin ɗora wa Bilal shattima sai kace shi kaɗai ne ɗa namiji, ga masu sonki da gaskiya wanda za su aure ki amma kin bi kin maƙalewa marar aiki yi
ki yi wa kanki faɗa. Wallahi na rasa me za ki tsinta a jikinsa ga muni ga uban talauci..
   "Ke dallah ya isa banaso shisshigi a al'amurrana in banda munafuci da tsugudidi ina ruwanki da muni da rashin aikinsa To ni a haka nake sonsa kyawawan da masu kuɗi kuma nace akai kasuwa bana yi.
Jeeddah ta katse ta cikin tsawa da tada harshe, ita ma Khairat cikin fusata ta tasowa Jeeddah, kamar za ta ɗauke ta da mari cikin ƙonar zuciya take faɗin
   "Ni Ko ke da ruwa har da tsaki banda daƙiƙanci  irin naki har kin manta da  rashin aiki nasa ne ya janyo min har yanzu nake zaune a gidan ubana da tuni na tsofa a ɗakin mijina, watakila ma da yanzu na haifa masa ɗa ko ɗiya haka kawai Baba ya kafe akan ba za min aure na bar ki a gida ba al'hali ke ce da kanki ki ka zaɓi zaman gidan.
   "To tun da kina gani an miki ba daidai ba kuma kin matsu aure ki ke so sai ki tashi ki tafi gidan Jameel ɗin ai ana haihuwa ko ba aure kin ga shikenan sauwaƙe ramar kaza sai ki fara haifa masa 'ya'yansa.
   Jeeddah ta faɗa cike da zallar sheƙiyanci.
   "Kam ubanan! Lallai Jeeddah sai yau na tabbatar da bakya ƙauna ta, mu fito ciki ɗaya amma kina min fatar haihuwa ba aure.
Khairat ta faɗa fuskar ta ɗauke da zallar mamaki furucin Jeeddah akanta.
   Taɓe baki Jeeddah tayi gami da yarfe hannu ta ce "Me kuma ya kawo zance rashin ƙauna, ai ƙaunar ce ma ta jawo na ba ki wannan shawarar da ki ta zama gida kina tsofewa kamar ni ba gara ki haifawa Jameel 'ya'yansa ba.
   Girgiza kai Khairat tayi  ta tabbata idan bata rarrashe zuciyarta ba ta kai ta nesa yanzu nan za su kaure da dambe dama sun saba da kyar su yi sati ɗaya currr ba tare da sun yi dambace ba har abin ya zame musu jiki.
    "Wannan dai mummunan fata kike min kuma in-sha-Allah a kanki zai ƙar....
Kafin Khairat ta ƙarasa Jeeddah tai kukan kura ta dafe mata baki tana faɗin "shegiya yarinya haɗiye saura kalaman ki su koma cikinki don wallahi ba zan bari ki ƙarasa faɗarsu ba ki lalata min rayuwa bayan nasan wannan shegen bakin naki ɗauke yake da kambu baka.
Khairat ta shiga ƙoƙarin cire hannun Jeeddah daga bakinta yayin da Jeeddah sai ƙara danne bakinta nata take yi da dukkan ƙarfinta kokawa ta kaure a tsakaninsu Khairat ta dana mata shegen cizo ga tafin hannu babu shiri ta sake ta, tana yarfe hannu. Dariya Khairat ta kyalkyale da ita tana kallon Jeeddah da ke kallon shatin haƙorata da suka fito raɗau-raɗau ga tafin hannunta ta ce "How market 'yar uwa?"
Ta ƙarasa magana tana dariya a fusace Jeeddah tayo kanta tana faɗin "Wallahi sai na rama shegiya mayya kawai.
Khairat ta rugu da gudu ta fice daga ɗakin tana cewa "ai ke ce babbar mayya da ta maƙalewa ƙato da bai da abin aurenta.
  Da gudu Jeeddah ta bi bayanta a tsakar gida suka tadda Mama tana haɗa zobo ta na sayarwa, Khairat ta nufi bayanta ta ɓoye tasan duk rashin kunyar Jeeddah ba za ta dake ta a bayan Mama ba.
  "Mama wallahi ki shiga tsakanina da Khairat nagaji da wulaƙanci da take min a gidanan.
Jeeddah ta faɗa cikin marairaice murya kamar wata mutuniyar kirki.
Kallon uku saura kwabo Mama tai mata gami da taɓe baki kana ta nuna ta da ƙaton ludayin da take jujjuya zobo dashi tana faɗin "Ke arrr...ko kunya ba kya ji ace ƙanwarki, ita ce abokiyar faɗanki gaba ɗaya kin jawo ta renaki bata gani girmanki.
   "Mama don taga kina goyon bayanta ne shiyasa take min abin da ta ga dama amma ba komai na rantse duk ranar da ta kaini bango sai kin yi jinyarta don dukan akawo wuƙa zan mata.
Jeeddah ta katse Mama tana matsar kwalla.
  "Mtsss....!
Mama ta ja tsaki tana mai ci-gaba da jujjuya zobonta tana faɗin "Ai Khairat ba raguwa bace  da za ta zauna ki yi mata dukan da za ta kwanta jinya idan ki ka sake kika kaini bango yanzu-yanzu nan sai na ware muku fili na tabbata ba za ki ɗibi komai a jikinta ba.
   "Haba.... Mama miyasa ki ke min haka?" wallahi in Baba ya dawo sai na faɗa masa irin cin kashin da ake min a gidanan.
Jeeddah ta faɗa cikin sigar shagwaɓa gami da bubbuga ƙafafuwanta akan floor. Yayin da Khairat sai gwalo take mata abinda ya ƙara harzuƙa ta kenan tai kwafa gami da nuna Khairat da yatsa tana cizon leɓɓe.
   Mama ta ɗago ta dube ta ta taɓe baki ta ce "uhmm....shi ma Baban naki ya gaji da zama da ke da za ki yi wa kanki ƙiyamullaili ki amince da auren Haidar da ya fi miki zaman jiran wannan gantalallen Yaro mai mugun baƙi kamar zunubi marar mafaɗi yana ɓata miki lokaci a banza sa'o'i duk su na ɗakin mazaje su, daga mai haihuwa ɗaya sai mai biyu ke ga ki zaune a gida kina zaman jiran tsammani.
    Kuka Jeeddah ta fashe dashi irin mai sautin nan ta juya rai ɓace ta shige ɗakinta.
  "Je ki mana ki fi ruwa gudu sakarya kawai ana nuna miki Annabi kina runtse idanuwa.
  Mama tai magana cike da takaici.
Duk duniya ba abinda Jeeddah ta tsana yake kuma saurin saka ta kuka bai wuce ta ji Mama tana kushe Bilal ɗinta ba. Da ka zagi Bilal ko ka aibanta shi gara kai ta lafta mata bulala tun dare har wayewar gari saboda Ita kaɗai tasan irin sirri da ke tattare da zaɓe shi da tayi a cikin dubban maza Bilal shi ne irin mijin da take so ta aura dashi kaɗai take jin za ta iya rayuwar aure muddin aka hanata aure shi sai dai ta mutu ba ta yi aure ba.
   Jeeddah tana shiga ɗaki ta faɗa bisa gado tai ruff da ciki nan take ta soma tuna ranar farko da ta fara haɗuwa da Bilal shattima. Rana ce da ba za ta taɓa mantawa da ita a cikin tarihin rayuwarta ba.
*Flash Back*
Kwana mu biyu da dawowa hutun makaranta ni da ƙanwata Khairat kasancewar boarding school muke yi, anan FGC Sokoto kuma ajinmu ɗaya saboda babu tazarar mai yawa a tsakaninmu shekara biyu kacal na bata a duniya. A wannan hutun da mu ka zo na haɗu da abin ƙaunata Bilal shattima haɗuwar da har abada ba zan manta da ita ba. Kafin na ba ku labarin zazzafar soyayyarmu bari na ba ku kaɗan daga cikin tahirin rayuwata. Sunana Jeeddah Usman maishadda na taso a gaban iyayena Baba da Mama sai kuma ƙanwata Khairat wacce ta kasance tamkar ƙawata saboda muna sharing secret wa junanmu.
Tun daga nursery har zuwa makarantar gaba da secondary class ɗinmu ɗaya sai dai kowane mu da ƙawayensa dama an ce sai hali yazo ɗaya ake ƙawance to kusan haka ce tafaru duk da uwa ɗaya uba ɗaya ne ya haife mu amma halayenmu da ɗabi'unmu sun sha bamban. Na kasancewa masifaffiya mai azababben taurin kai da tsiwa bana bari ko ta kwana balle ta tashi. A lokaci da muna secondary school nasha dambe da maza clasa ɗinmu kaɗan ne daga cikinsu da ban yi dambe dasu ba, balle kuma su mata ƙaramin alhakki kullum sai na fasa baki ɗiya.
Yayin da Khairat ta kasance mai sanyi hali shiru-shiru da ita ba ta da abokin faɗa in ba ni ba da wuya ka ji Khairat bata da kwaranniya ko kaɗan har mamaki mutane ke yi idan aka ce ƙanwata ce kuma uwa ɗaya uba ɗaya don ko kusan halayenmu ba su yi kamanceceniya ba.
Tun ina cikin tsuman goyana Ya Haidar ke sona yayin da ni kuma tun lokaci da na balaga nasan menene so na ji ba wanda na tsana a duniya irinsa. Kar ku yi tunani wani laifi ya yi min da nake nuna masa zazzafar ƙiyayya irin wannan ba wani abu bane kawai dai don ya kasance kyakkyawa ajin farko kuma ɗan masu kuɗi, sai anan gaba zan warware muku dalilina da yasa na tsani kyakkyawan namiji kuma mai kuɗi.
Mu huɗu iyayenmu suka haifa mahaifina Alhaji Usman maishadda haifaffen garin Sokoto ne kuma riƙaƙken ɗan kasuwa ya yi karatun addini da na zamani sai dai karatunsa na boko bai yi tsayi ba ya tsaya iya matakin ƙaramar diploma. Da farko ya fara karantawar a primary school kafin ya koma kasuwanci da ya taso ya iske mahaifinsa yana yi na sayar da atamfofin da shadda da leshi har ma da mayafai a kasuwa. lokaci da aka yi mishi aure yana da ƙarancin shekaru a lokaci yana da shekara goma sha takwas mahaifinsa yai mishi aure da 'yar amininsa Irin aure nan na gata da ada masu kuɗin ke yi wa 'yayansu. A lokaci Mamanmu primary school kawai ta kammala aka aurar da ita ga Babanmu, cikin yarda Allah suka haɗa kansu suna tsananin ƙaunar junansu tamkar auren soyayya suka yi ba auren haɗi ba. A yadda Mama ke ba mu labari sai da ta shekara goma sha ɗaya da aure kafin ta haifi Ya Kabeer sai da ya yi shekara goma kafin ta haifi Aunty Farida wacce ita ma sai da tayi shekara bakwai curr kafin a haife ni ina da shekara biyu kacal ta haifi Khairat wacce muka taso tamkar twins komai tare ake mana kasancewar banida girman jiki yayin da Khairat take da manyan ƙasusuwa shiyasa ta kamoni har ta zo ma tafi ni girma shiyasa wanda basu san mu ba suke tunani Khairat ce babba, yayin da duk lokaci da aka sami irin wannan akasi nake rufe idanuwa naci mutunci duk wanda ya yi mana irin wannan hasashe domin na tsani naji an kira Khairat da yayata.
  Da Babanmu da mahaifiyar Ya Haidar uwa ɗaya uba ɗaya suke asalima su uku ne kacal iyayensu suka haifa babbar yayarsu mai suna Mariya tana aure a Kebbi sai Babanmu sai autarsu Hauwa wacce suke kira da Turai ita ce ta haifi Haidar, kuma sunanta ne na ci. Tun banida wayau ake kirana da suna matar Haidar shi kuma mijina a lokaci bana fahimtar abinda ake nufi da hakan har na dawo na fara fahimta, ina farkon balaga a lokaci ne wani ɓoyayyen halina ya fara bayyana na azababben kishi, banaso ko Khairat da take ƙanwata ta raɓi Haidar yanzu nan zan tsira fushi na dinga cin rai na tai cika ina batsewa har da su ƙauracewa abinci sai Ya Haidar ya sha baƙar wahala Kafin ya shawo kaina na sauko daga fushi da na hau, gashi Allah ya zuba mishi farin jini 'yan mata kasancewar shi kyakkyawa azahirin gaskiya Ya Haidar yana da matsanancin kyau da ace kyawo na yawa da nace da ku nashi har ya yi yawa a lokaci da na fahimce kyawon shi yana ɗaya daga cikin abinda ke jan hankali 'yan mata sai na fara tsanar kyawon nashi daga baya kuma na gano har da kasantuwar shi ɗan masu hannu da shuni.
Ban ƙara tabbatar da hakan ba sai wata rana da mun zo hutun makarantar boko na je gidan Aunty Farida sai mijinta ya yi baƙo Aunty Farida ta aike ni na kai masa ruwa da drinks, kafin na kai da shiga parlourn Abban Siyama na tsince firar su inda abokin nasa ke faɗi "Yusuf ya kamata ka ƙara aure ka wani maƙallewa mace ɗaya sai kace pastor.
   Nan take na kasa shiga parlourn na laɓe jikin ƙofa tare da baza kunnuwa naji amsar da Abban Siyama zai bashi sai naji yana faɗin "mi zai sa na ƙara aure Habeeb bayan matata tana kyautata min wallahi ina matuƙar jin daɗi zama da Farida.
  "Kana da matsalar fahimtar abubuwa masu sauƙi fahimta Yusuf an gayamaka dole sai mace tai maka laifi za ka yi mata kishiya, Ubangiji ya ba ka komai Yusuf kana da kyau ga kuma ɗibin dukiya mai yawa babu abinda Allah ya rageka dashi, wallahi da nine kai da mata huɗu curr zan yi in yi ta gurgura abina hankali kwance.
Sai kawai na ji sun kece da dariya har suna tafawa kana Abban Siyama ya ce "Allah abokina?"
"Allah kuwa abokina ka fahimci wani abu guda mata wannan zamani sun fi so namiji kyakkyawa kuma mai 'ya'ya banki, kai kuma duka biyu Allah ya haɗa maka karka biyewa ta kyautatawar da Farida take maka ka cuci kanka.
Tsabar takaici ka kasa ƙarasawa parlour nan sai komawa kitchen nayi na dire tray ɗin Allah yasa Aunty Farida tana ɗaki, ba a ɗauki lokaci ba Abban Siyama ya yi ma Aunty Farida kishiya in takaice muku labari yanzu kishiyoyinta har biyu. tun daga wannan ranar da naji wannan ɓakar firar tasu na ƙudurtawa raina bani ba namiji kyakkyawa ko mai kuɗi.
Daga sanda na fahimci da gaske kuɗi da kyau sune dalili da ke sa wa ai ma mace kishiya na ji na tsani Haidar soyayyarsa ta fita daga zuciyata tamkar an wanke min ita da sosu da omo.
saboda azababben kishina sai nake gani kamar idan na aure talaka mummuna ba zai min kishiya ba tun da mata ba son talaka mummuna suke yi ba Shiyasa na zaɓi Bilal shattima kasancewar shi mummuna baƙi wulik ga shi kuma ba shi da aiki yi zauna gari banza ne.
Bai aje ba bai kuma ba wani ajiya ba.

*Please comments and share fissibilillahi*
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥 ZAZZAFAN KISHI.....!*
_{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattapad-jeedddahaliyu

©HWA

Assalamu Alaikum I'm Zarah Dange 07034400732  face behind LADY APHRODISIAC AND  MORE dealer in all kind of supplement and herbal aphrodisiacs kayan mata. Kayan mu will make you last on bed and permanently end the pain and embarrassment of weak eraction and premature ejaculation.

*Muna hadin bridal package and postnatal combination of natural herb's and supplement.

*Akwai hadin uwar gida mai da tsuhuwa yarinya
*Akwai hadi na infection (sanyi herbs).

*Akwai Zuma Mai saukar DA niima nan take tare da dandano Na mussaman.

*Muna kalolin gumbar Kamar gumbar madara, gumbar Aya, gumbar ridi, gumbar kasko, yar kicihi, Alhaji ba nan kake ba d.s .

*Akwai kalolin tsimi kamar Dan la'asar, tabaje, tsimin yar gata d.s .

* Muna DA kalolin gari nasha kamar sa buzu kuwa, sinadarin aya, abin sirri ne, emergency, rakumi DA akala, runbun dadi, kinfi Amarya d.s.

*Muna special kaza, danbu, ciccibi, Yan shila,zuciya d.s

*Akwai Na matsi different types DA sabulu na tsalki.

Ta bangaren supplement muna da na gyaran skin da kuma herbal aphrodisiacs supplement , akwai different oils both retail and wholesale, supplement Kamar su Juliet eve, royal jelly, ultimate maca, suprodine, frozen detox, frozen collegen, majakani, amirna, khusus, dara, cantik ayu, pesona d.s
We have capsules, pills, chocolate, and different coffee that will make you sweet, firm, tight, young, beautiful and healthy.
Delivery is nation wide 07034400732

_Na sadaukar da wannan littafi ga Zarah Bb_

02...

A wani yammacin ina kwance a ɗaki Mama ta kwalla min kira, na fito ina zunbure baki saboda a tunanina wani aiki za ta saka ni. Yau kwana mu biyu da dawowa hutu amma kauda kara ban yi mata ba ina daki na nade bisa gado, sai dai ta kashe ta bani naci, ɗan banza son jiki ne da ni ga shegiyar ƙiwa duk lokaci da Mama ta saka ni aiki sai ranta ya ɓaci saboda na dinga jan jiki kenan, tamkar banida lakka a jiki har sai ta hasala ta karɓe abinta tayi da kanta. Ba don Mama tana tsawata min ba da ba ƙaramar malalaciya ce ni ba. Yadda Mama taga ina zunburi baki gaba yasa ta galla min harara tare da faɗin "Sakin ranki magge uwar son jiki ba aiki zan saka ki ba aike ki zan yi shagon Bello Rahusa ki siyo mana sabulun wanki, gobe  da sassafe Musa zai zo ya yi wa Alhaji wanki sai yanzu na tuna da babu sabulu.
Jin Mama ta ambaci sunan shagon Bello Rahusa yasa na ƙara turo baki gaba, Saboda na tsani zuwa shagonsa a dalili majalisar samarin unguwa da ke kusa da shagon nasa masu masifar kallon tsiya haka kawai za su dinga bin mutum da shegun idanuwansu har sai ya ɓacewa ganinsu.
     "Je ki ɗauko hijabinki mana.
Mama ta katse min zance zuci da nake, gyara tsayuwa ta nayi gami da langwaɓe kai na yi narai-narai da idanuwa na ce "Gaskiya ni dai Mama ba son zuwa shagon Bello Rahusa nake yi ba, da za ki haƙura da dare idan Musa ya zo karɓa abincinsa sai ya siyo miki.
Na ƙarasa magana ina wani kwantar da murya.
    "Ai nasan da Musa zai zo karɓar abincinsa amma na aike ki, ke dai har abada ba za ki daina halin ƙiwa ba.
"Ba wai zuwan ne banaso yi ba Mama ƙarttin banza nan da ya tara gaban shagonsa ne banaso bi ta gabansu, sun dinga bin mutum da kallo kamar wasu tsofaffin mayyu...
   "Dallah...karɓi ki je ki siyo min abinda na aike ki ko ina ruwanki dasu balle har kallonsu ya dame ki.
Yadda Mama ta buga min tsawa yasa na karɓi kuɗin hannunta babu shiri na nufi ɗaki ina gunguni na sako dogon hijab har yana ja a ƙasa na saka wasu silifas na roba na Mama da ke aje a ƙofar parlour na fice rai ɓace ina tafe ina cin rai sai uban tsaki nake zabgawa tun kafin na ƙarasa shagon na hango majalisar kamar da gayya suka yi min don ta cika tafff babu masaka tsinke sai tashin muryoyinsu ka ke ji suna gardama har ba ka iya tantance mai magana a cikinsu, wani mashahurin takaici ya rufe ni har ji nake kamar na juya na koma gida, sai kuma na tuna da Mama muddin ban siyo mata aikenta ba za ta iya cin ƙaniyata tun kafin na isa kusa dasu na sadda kaina ƙasa, yanayi da naji ƙafafuwana suna harɗewa ya bani tabbacin su biyo ni da kallo musamman da na tsikayo muryoyi kaɗan daga cikinsu ne ke ci-gaba da magana. Da ko kafin na kawo kusa dasu tun daga nesa nake jin surutunsu sai kace masu cin kasuwa. "Tirrr......wallahi kun yi asara gantalallu banza da wofi marasa aiki yi.
Na faɗa cikin zuciyata, wani ƙarin abin takaici ina shiga shagon na tadda mutane cike tafff ba maza ba, ba mata ba kai in takaice muku har da ƙanana yara raina ya ƙara ɓaci ko kusa ba zan iya ratsa wannan tulin cikoson mutane don kawai siyen sabulun wanki, sai na nemi ɗaya daga cikin deep freezer da ke farkon shigowa shagon na jingina bayana gami da folding hannuwana a ƙirji "Kai wallahi mutane akwai su da shegen son banza tsiya don kawai Bello Rahusa yana siyarda kayansa akan farashi mai sauƙi tamkar dai yadda ake ba da wa akan sari a kasuwa shiyasa Mutane unguwarmu suka daina zuwa kasuwa har ma da na wasu unguwanni da muke makwabtaka dasu saidai su zo shagonsa su yi ta bin layi a wofi mtsss...!
Na ƙarasa zance zucina da siririn tsaki. Kamar daga sama na ji ana ture ni gami da ƙoƙarin buɗe murfi freezer da nake jingine akai, cikin tsananin masifa na yadda idanuwana akan mutumin da ke ƙoƙarin ture ni wani mummunan gajeren saurayin ne baƙi wulik dashi baƙinsa har wani naso yake yi tamkar ya shafa gawayi "Malam ba ka gani ne halan kai makaho ne da ba ka lura da ina jingina jikin freezer nan bane?"
Na watsa masa tambaya cike da tsiwa saboda masifa har wani ƙanƙace idanuwana ke yi.
   "Amma dai malama kina sane da nan wuri masana'anta ce ba wurin kwanciya ba, idan bacci ki ke ji ki koma gida ki kwata, amma haka kawai kin zo ki sami freezer mutane kin ɗale sai zuba gyagyaɗi ki ke yi.
Ya bani amsa yana min wani kallo da ke kama da na reni wayau.
Na yi ƙwafa gami da janyewa na koma gefe na bashi waje saboda na fahimci tsagerancinsa ya fi nawa ina kallonshi ta gefen ido ya buɗe freezer ɗin yana faɗi "Da dai yafi miki ki tsaya da ƙafafuwanki kamar kowa.
Ya ƙarashe magana tare da dauƙo Coke na gwagwani ya ɓalle ya shiga sipping na ɗan sace kallonshi karaff muka haɗa idanu nai saurin kawar da kaina gefe ina taɓe baki.
  Matsowa ya yi daff dani ya miƙo min Coke ɗin "Bismillah 'yan mata naga sai satar kallona kike yi kina haɗiyar yawu da dukkan alamu ta biya miki a rai.
A fusace na kalle shi tare da galla masa uwar harara cikin masifa da bala'in na ce "Ka ga bawan Allah karka nemi ka kaini bango nai maka rashin mutunci ba ruwanka da ni kayi sabgar gabanka.
  'yar dariya ya yi mai sauti kafin ya ce "Ke kam kin cika masifa halan sunanki Hafsah?"
"Bansani ba.
Na faɗa a fusace har ina haɗawa da murguɗa baki.
   "Mi kika zo siya na taimaka na karɓo miki domin na tabbata mutane nan ba raguwa za su yi ba sai ma su daɗa ƙaruwa?"
"Wai kai ba ka gane yaren hausa ne nace kyaleni banaso cusa kai ba kwarjini.
    "Da gaske?"
Ya faɗa yana ɗage girar ido, sai kawai na kawar da fuskarta gami da murguɗa masa baki, ban ankara ba na ji ya wafce kuɗin hannuna yana faɗin "Yanzu kam kuɗinki sun shigo hannuna ko bakyaso dole ki faɗi abinda aka aiko ki siya.
Narai-narai nayi da idanuwa Kamar zan sa kuka cikin rauni murya na ce dashi "Sabulun wanki.
Saboda banida wani zaɓi da ya wuce na faɗa masa ko banza ba zan iya ratsa yawan mutane da ke shagon ba.
"Wane irin sannan guda nawa?"
Ya faɗa yana leƙen fuskata, muryarta can ƙasa na furta "Viva dozen ɗaya.
Ba tare da ya sake magana ba ya nufi ainihin cikin shago ba a ɗauki longtime ba sai gashi ya fito da leda baƙa a hannunshi ya miƙo min na karɓa ya sake miƙo min canji shima na karɓa gami da furta "Nagode!
Ina ƙoƙarin bari shago ya ce "Ji mana 'yan mata.
Na tsaya tare da waigowa.
"Ba ki faɗa min sunanki ba, ba ki Kuma tambaye nawa sunan ba.
"Sani sunana ba sauƙi ne dashi ba kamar yadda ka wafce min kuɗi, sannan kuma ka adana sunanka bana da buƙatar ji.
Daga haka na juyo cikin sauri na fice daga shagon, na nufi hanyar gida ina tafiya ina mita abinda ɗan baƙi saurayi nan mummuna ya yi min.
Bayan kwana uku da haɗuwata dashi na fito da yamma liss zan tafi kasuwa ina cikin tafiya saura kaɗan na isa titi ida zan hau keke napep na ji ana min horn da machine a bayana, banza nayi ina mai ci-gaba da tafiyata cikin natsuwa saboda ina da tabbacin ba akan hanyarsa nake ba tsabar iskanci ne kawai yasa yake min horn.
   "Yan mata ki dinga tafiya kina waiwaya bayanki saboda machine ba ruwanshi da ke kyakkyawa ce buge ki zai yi ya rage miki sadaki.
Nan take na sheda murya mai magana shiyasa ma na kalleshi na watsar gami da taɓe baki ina faɗin "idan machine ɗin bai damu da kyawona ba ai ma mallaki machine ɗin ya damu tun da har ya iya tantance ni ɗin kyakkyawa ce a haɗuwarmu sau ɗaya takk!
  Dariya ya yi tare da ya rage gudun machine ɗinsa yana tafiya slow-slow, "Gaskiya kam ba karya ke ɗin kyakkyawa ce domin tun lokaci da idanuwana suka yi tozali da ke tun daga ranar kawo yanzu bana cikin natsuwata kin hanani sukuni ki haddasa min...
   "Dallah Mallam ya isa haka a'ahh!
Nai gaggawa katse masa hanzari ina maka masa uwar harara kamar ƙwayar idanuwana za ta diro ƙasa ta faɗo.
   "Tirƙashi! Gaskiya ke kam masifaffiya ce irin wannan harara ai sai ki sare min ƙarfi guiwa.
Yayi magana tare da zuba min matsakaita idanuwanshi wanda zan iya cewa sune kaɗai farare a cikin halittar jikinsa.
"Uhmm!
Na furta ina kyaɓe baki.
Na dai san labarin gizo bai wuce na ƙoƙi ba duk wannan kame-kamen da yake yi ƙarshenta cewa zai yana sona.
   "Ina za ki je da yamma nan ki ka ci irin wannan kwalliya salon wani yai min snatching.
Dama nasan za a yi haka shiyasa na juya a natse ina ƙare masa kallo sai lokaci na lura da kayan da ke jikinsa yana sanye cikin farin filtex material na maza irin mai taushi nan ɗinki boda kanshi ɗauke da baƙar hula ba laifi ya yi min kyau ainun, kun san dai tsarina ba son kyakkyawan namiji nake yi ba shiyasa ɗan baƙi saurayi nan na kan machine roba-roba yai awon gaba da rabin zuciyata. Tsakani da Allah ban taɓa cin karo da mummuna kamar sa ba, nan take naji nayi na'am dashi don shine ainihin kalar da nake wa kaina hasashe, kalar da ba wata ɗiya mace da za ta so sai kawai na saki mishi tattausan murmushi ina wani fari da idanuwa tare da faɗin "Kasuwa zan je ko kana da saƙo?"
"Kai haba! Ai kuwa faɗuwa ta zo daidai da zama nima Kasuwa na nufa hau mu je na rage miki hanya.
Ya ƙarashe magana gami da tsayar da machine ɗinsa yana nuna min bayan machine ɗin nasa da hannunshi.
Girgiza kai nayi ina masa kallon uku saura Kwabo haka kawai daga haɗuwar mu don ya yi insisting ɗina na hau machine ɗinsa, sai kawai na hau saboda gani Jeeddar mahaukata nufinsa kawai na ware ƙafafuwa na ɗale kai ina ba zan iya wannan kasadar ba.
  "Yi haƙuri ɗan samari don kuwa ka taki rashin sa'a bana hawa machine.
     "Haba wai da gaske kike yi?"
Ya faɗa yana min kallon mamaki.
      "Ai ya wuce wai don ga zahiri nan ka gani.
Na ƙarasa magana gami da tsayar da adaidaita.
   "Don Allah malam ka yi haƙuri ka tafi abinka mata ce mu sami misunderstanding ne shine tai fushi ta ƙi hawa machine ɗina.
Kamar daga sama na tsikayo muryarsa yana faɗawa mai adaidaita labarin ƙanzo kurege. Atoh dole nace Labarin ƙanzo kurege don bansan yaushe na zama matarsa ba. Kusan adaidaita uku na tara yana faɗa masu abin da ya faɗawa na farko zuwa lokaci raina ya kai maƙura wajen ɓaci, cikin fusata na ce dashi "Wai malam mikake nufi da ni ne?"
"Ba wani abu mai wahala bane na neman a gunki cewa kawai nayi ki hau machine ɗina.
"Gaskiya kai kam kana da matsala ina mamaki kai ba kurma ba amma ba ka fahimta abubuwa ciki sauƙi.
A tunanina zai hasala yai tafiyarshi ga mamakina sai kawai naga ya yi murmushi gefen baki ya ci-gaba da yi min magiya fahimtar nayi muddin ban hau machine ɗinsa ba zai kyale ni in hau adaidaita ba gashi kuma yamma sai ƙaratowa take yi ina jin tsoro a rufe kasuwa na haɗu da fushin Mama, bani da zaɓi da ya wuce na hau machine ɗin nasa har muka iso kasuwa yana zuba min fira tamkar ya shekara da sanina ni kan bayan uhmm ko a'a ba abinda nake cewa dashi a tunanina da ya sauke ni zai yi tafiyarsa saboda ina da yaƙini ya faɗi kasuwa zai taho ne don kawai na amince na hau machine ɗinsa, amma kuma sai naga saɓanin tunani nawa domin kuwa wurin da aka tanada domin ba da ajiyar ababen hawa ya kai machine ɗinsa duk ƙoƙarina nagani na shige cikin kasuwa sai da ya cimmin, muka jera side by side duk naji ni wani iri nakasa sakin jiki, ko ba komai ina gudun haɗuwa da idon sani ya ganni tare dashi ya je ya tseguntawa Babanmu.
Kasancewar underwears na zo siya asalima sune maƙasudin zuwa na kasuwa, sai Mama da zan siyawa kayan haɗin zobo da na kunun aya sai gashi na haɗu da wannan ɗan anace Sarkin naci mutum kamar mayye. Ni abinda yafi ɗaga min hankali bai wuce ta ya zan nufi shagon sayar da braziers da panties al'hali yana biye da ni gaskiya da kunya na siye waɗannan abubuwan tare dashi ai sai ajina ya zube a gabansa. Can dabara ta faɗo min na kalleshi cikin kwantar da murya nace "Mr bita zai-zai shagon Babanmu zan shiga saboda haka ka tsaya anan ka jira ni, saboda ba mutunci bane ya ganni tare da kai.
    "Haka ne amma gaskiya karki daɗe domin idan naga kin yi shaƙo zan biyo sawunki.
Ya faɗa with serious tone.
       "Karka damu duka ba zan wuce good 30 minutes ba.
"Shi kenan ki hanzarta please.
Na juya ba tare da na sake tanka masa ba, dama daga wuri da nace ya tsaya da shagon da nake siye underwears
babu tazara sosai sai dai ina da tabbaci ba zai gano inda na shiga ba domin sai da na fakaice idanuwanshi kana nai wuff na afka shagon.
Koda na shiga shagon 'yan mata uku na tadda a ciki suna duba braziers da panties bayan na gaisa da mai shago dama ya sanni saboda regular customer ɗinsa nake, nan take ya shiga jido min latest bra and panties na shiga duddubawa wanda ya yi min na kuma yarda da quality sa. Dozen biyu na panties na ɗauka mana bra Kuma na ɗaukawa kaina shidda Khairat kuma biyar.
    "Yunusa waɗannan nake so miye price ɗin su?"
Na tambaye mai shagon tare da nuna masa kayan da yatsana.
"Panties kowane dozen ₦6k amma ki bada ₦5500 su kuma braziers ki barsu duka akan ₦8500.
   "Cabdijam! Yunusa halan cin su ake yi da za ka zabga min wannan uban kuɗi?"
Na faɗa ina zaro idanuwa tamkar wacce taga abin tsoro kafin Yunusa ya bani amsa naji saukar muryarsa a bayana yana faɗin....

*Comments & share fisbilillah*
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥 ZAZZAFAN KISHI.....!*
  _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

Assalamu Alaikum I'm Zarah Dange 07034400732  face behind LADY APHRODISIAC AND  MORE dealer in all kind of supplement and herbal aphrodisiacs kayan mata. Kayan mu will make you last on bed and permanently end the pain and embarrassment of weak eraction and premature ejaculation.

*Muna hadin bridal package and postnatal combination of natural herb's and supplement.

*Akwai hadin uwar gida mai da tsuhuwa yarinya
*Akwai hadi na infection (sanyi herbs).

*Akwai Zuma Mai saukar DA niima nan take tare da dandano Na mussaman.

*Muna kalolin gumbar Kamar gumbar madara, gumbar Aya, gumbar ridi, gumbar kasko, yar kicihi, Alhaji ba nan kake ba d.s .

*Akwai kalolin tsimi kamar Dan la'asar, tabaje, tsimin yar gata d.s .

* Muna DA kalolin gari nasha kamar sa buzu kuwa, sinadarin aya, abin sirri ne, emergency, rakumi DA akala, runbun dadi, kinfi Amarya d.s.

*Muna special kaza, danbu, ciccibi, Yan shila,zuciya d.s

*Akwai Na matsi different types DA sabulu na tsalki.

Ta bangaren supplement muna da na gyaran skin da kuma herbal aphrodisiacs supplement , akwai different oils both retail and wholesale, supplement Kamar su Juliet eve, royal jelly, ultimate maca, suprodine, frozen detox, frozen collegen, majakani, amirna, khusus, dara, cantik ayu, pesona d.s
We have capsules, pills, chocolate, and different coffee that will make you sweet, firm, tight, young, beautiful and healthy.
Delivery is nation wide 07034400732

_Na sadaukar da wannan littafi ga Zarah Bb_

03...

"Ki daina la'akari da tsadar abu ki dinga duba quality da amfaninsa.
     A kunya ce na waiga bayana na kalleshi kana cikin sauri na kauda fuska, kunya mai tsanani gaske ta lulluɓe ni har bansan lokaci da brazier da ke hannuna ta subuce ta faɗi don tsabar rashin kunya da kai mutum maƙura iri na ɗan baƙi saurayi sai duƙawa ya yi ya ɗauko brazier ɗin yana jujjuya ta gami da faɗin "abokina zuba mana kayan a leda daga gani su qualities ne.
Cikin al'ajabi nake kallonshi yayin da shi ko a jikinsa sai ma zura hannunshi da yai cikin aljihunshi ya fito da kuɗi ya kirga ya mayar da raguwa kana ya miƙawa Yunusa gami da faɗin "Gashi abokina kayi haƙuri da 19k.
Da sauri Yunusa ya karɓe kuɗi yana godiya raina a ɓace na juya ina kallonshi na rasa me yake nufi dani sosai nake so nai masa tijara in yaso ya kama gabansa nima na kama nawa saboda naga shisshiginsa yana nema ya yi yawa shiyasa ina juyawa na fara magana a fusace "Look bawan Allah ban ce maka bani da kuɗi ba don haka ban ga dalili da zai sa ka biya min ba, kalli jakkata ina da kuɗina fal ciki saboda haka ka gaggauta karɓa kuɗinka ban maka kirarin banida kuɗi ba.
Matsowa ya yi kusa da ni ya haɗe tazarar dake tsakaninmu ya yi kalar tausayi ya shiga yi min magana ƙasa-ƙasa tamkar mai raɗa
   "OMG! Don Allah karki yarfani gaban 'yan mata nan ki rufa min asiri mu bar wannan magana in yaso muka fita daga shagon nan ko dukana ne za ki iya, kalli ki ga yadda hankalinsu ya dawo kanmu.
  Kallon gefen da 'yan mata suke nai sai naga suna magana ƙasa-ƙasa tare da dariya har suna tafawa da dukkan alamu gulmarmu ce suke yi, ba tare da na furta uffan ba na fice daga shagon ya biyo ni a baya riƙe da leda nesa kaɗan da shagon da muka fito na taka birki na haɗe fuska, gani yadda na murtuƙe fuska yasa ya sha jinin jikinsa "ka ga bawan Allah abinda ka yi min ko kaɗan ban ji daɗi sa ba saboda haka ga kuɗinka.
Na ƙarasa magana tare da zipping jakkata, na kirgo masa ƙudinsa na miƙa masa ƙi karɓa ya yi sai ma wani langwaɓe kai ya yi yana min wani kallo mai wuyar fassarawa, nai sauri kawar da fuskata kafin na sake mayar da idanuwana akansa "Don Allah ka karɓi kuɗinka domin idan naje gida Mama ta ganni da siyayya ga kuma kuɗi na dawo dasu wallahi mugun duka za tai min, saboda ta sha yi min gargaɗi kada na karɓi abu a hannu strangers.
Waro kyakkyawan idanuwansa ya yi indan ba ku manta ba na gayamaku idanuwanshi su ne kaɗai abinda zan iya bugun ƙirji nace yana da kyau a halittar jikinsa.
  "Ni da za ki yi min alfarma da nace ki bar wannan magana sai mun fita kasuwa, saboda public place ne duk wanda ya wuce sai ya kalle mu.
Ban ce komai ba na juya na nufi wurin da ake siyarda zobo da aya anan kam ban yi yunkurin biyan ƙudi ba, da alama gargaɗi da nai masa ya shiga kunnensa a takaice dai duk siyayyar da nai yana biye da ni sai kace jela har ga Allah naso na biya shagon Baba amma saboda shi na fasa, har muka ɗauki hanyar komawa gida ba wanda ya furta uffan a cikinmu muna shigowa farkon layin unguwarmu nace dashi "Sauke ni anan.
Ya taka birki na sauko kafin nai magana ya rigani ta hanyar cewa "Don Allah ki faɗa min sunanki.
    Nayi shiru na some seconds kafin na buɗe bakina tamkar mai ciwo haƙora na ce "Jeeddah Usman maishadda.
   "Wai dama sunan tsofaffin ne da ke shine kike ta yi min yanga da jan aji gashi sunan naki ko daɗi babu.
Murmushi nayi saboda na fahimci tsokanata  yake yi.
    "Ba ki tambaye ni sunana ba.
Yayi magana yana shafar kwantatce sajensa.
    Na taɓe baki gami da faɗin "Ai ba sai na tambaya ba nasan kai ɗin faɗi ba a tambaye ka  ne ina da yaƙini ko ban tambaya ba sai ka faɗa.
    'yar dariya ya yi mai ƙaramin sauti yana faɗi "Gaskiya ne Kuluwa ni ɗin faɗi ba a tambaye ka ne amma fa akanki ne kawai nake da wannan shisshigi shin ko kinsan dalili?
Na girgiza kai saboda banga dalili da zai sa nai ta zuba a gabansa tamkar wata marar class.
     Bai damu da rashin amsa masa da bakina da nayi ba sai kawai ya ci-gaba da faɗin "Zance na gaskiya Jeeddah ke ɗin kyakkyawa ce ajin farko tun lokaci da idanuwana suka yi tozali da wannan kyakkyawar surar taki na rikici na rasa natsuwa da kwanciyar hankalina banida buri da ya wuce ace na mallaki wannan haɗaɗɗiyar sura mai matuƙar jan hankali da sace zuciyar ma'aboci kallonta.
Wani irin tsoron Allah ne ya lulluɓe ni saboda yadda ya taƙarƙare yana describe jikina da hannuwanshi nan take zuciyata ta fassara shi a matsayin ɗan iska manemi mata, Allah na tuba banda tsohon ɗan iska da ya kware da iskanci wa zai dinga describing jikin mace haka, nan take na fusata iya fusatuwa cikin ɓaci rai na daka masa muguwar tsawa "Dakata malam! Dallah ka dakata nace An gayamaka kowa tintiri ɗan iska ne irinka, ko don ka ga na hau machine ɗinka shine za ka yi min maganar iskanci?"
  Kafe ni da idanuwansa ya yi mamaki ne ko tsabar kwarewa ne da iskanci oho, yana buɗe bakinsa kafin ya kai da furta abinda yai niyyar faɗa nasake daka masa tsawa "Rufe min baki ɗan iska kawai tsohon tambaɗaɗɗe da ya saba lalata 'ya'ya mutane wato shiyasa ka biya min kuɗi siyayya a kasuwa saboda kana da mummunan manufa akaina to bari ka ji ni ba 'yar iska bace ungo kuɗinka.
Na ƙarasa magana tare da kirgo ƙudinsa na watsa masa akan fuskarsa ina ci-gaba da faɗin "Kwashe tsiyarka ka je can ka nemi lalata irinka ka bata ba dai ni Jeeddah ba domin kuɗi basu isa su sa na zubar da daraja da ƙimata ba.
Na ƙarasa magana tare da fizgar raguwar ledojina da ke gaban machine ɗinsa na juya a fusace na nufi gida ina ji yana kwalla min kira ko waigowa ban yi ba balle ya sa ran zan tsaya, dole ya sauko daga kan machine ya tsince kuɗin sa ya mayar aljihu kana ya tashi machine ɗinsa ya nufi majalisarsu ta masu zaman kashe wando.
Ina shiga gida direct na wuce kitchen na ajiyewa Mama saƙonta, na wuce da namu ɗaki sai da na canza kayan jikina na nufi parlourn Mama na tadda Khairat tana goge hijabs ɗinmu yayin da Mama da ƙawarta Umma Asabe ke firar duniya, sallama nayi tare da gaida su "Mama na dawo ga siyayyarki can kitchen.
Na faɗa sa'ili da na kai zaune.
   "Ba zama za ki yi ba sarkin son jiki je ki tuka min tuwo.
Mama ta faɗa tana balla min harara, miƙewa nayi tamkar zan rushe da kuka, na fice ina kallon sanda Khairat tai min gwalo ban kula ta ba amma tabbas bashi taci, ina cikin tuka tuwo naji an rufe min idanuwa ko ban canka ba ƙamshin turarenshi ya gama sanarda ni waye "Ya Haidar!
Na kira sunanshi a daƙile.
Yana dariya mai ƙaramin sauti gami da cire tattausan tafin hannunshi mai tsanani taushi kamar auduga daga kan fuskata "Ya aka yi nan take ki ka sheda ni?"
Ya tambaya sa'ili da ya jingina jikinsa a kitchen cabinet, sai da na ƙare wa tufafin da yake sanye dasu kallo sky blue long sleeve ce haɗe da Black jeans trouser sun yi masifar karɓar jikinsa na taɓe baki gami da faɗin "Ta ya ba zan sheda ka ba bayan ƙamshin turarenka mai masifar hawa kai duk yabi ya cika min hanci.
Langwaɓe kai ya yi gaba ɗaya ya zuba min rikitattun idanuwanshi, ga wani annuri akan fuskarshi, yasan abinda na faɗa tsabar shirri ne kawai irin nawa cikin low voice ya ce "idan mu ka yi aure ba zan barki ki dinga shiga kitchen ba kalli yadda kika haɗa gumi wallahi ko kaɗan banaso naga kina aikin wahala.
Ya ƙarasa magana tare da ciro white handkerchief ya goge min zufa kan goshina, sai da ya yi kissing handkerchief ɗin kafin ya mayar dashi aljihunshi.
Kallon sama da ƙasa na masa na taɓe baki, na raɓa ta gefensa da nufi na ɗauko foodflask da zan saka tuwo a ciki karaff na ji ya riƙo damtse hannuna ya matso daff da kunnena ya raɗa min "Ina mugun sonki Jeeddah komai kike yi masifar burge ni kike yi sai naji kamar na cinye ki duka.
Wallahi soyayyarki tana azabtar da ruhina ba ranar da zan kwanta bacci ba tare da nayi mafalki mu yi aure ba, ki ji tausai na ki bani dama mu zama abu ɗaya.
Ya faɗa duk sai fuskarshi ta marairaice.
Juyowa nayi na zuba mishi idanuwana da ke cike da zazzafar ƙiyayyarshi "Wai miyasa Ya Haidar ka ke so ba kanka wahala ne?"
Ban jira ya amsa min tambayata ba na ci-gaba da faɗin "Na sha faɗa maka bana sonka bana ƙau....
Kafin na ƙarasa ya yi maza ya riƙo fuskata gami da connecting lips ɗinmu ya shiga kissing ɗina with passionate, duk yadda naso na kwace kaina kasawa nayi sai kawai na zubawa sarautar Allah ido. Duk wani lungu da saƙo na bakina sai da ya tsotse ya tanɗe shi tass!
Dama ba tun yau ba ya sha kissing ɗina ko ya rungumeni duk yadda na kai da son na kwace kaina, sai ya gwada min ƙarfi wallahi Ya Haidar shegen ƙarfi ne dashi tamkar ɗan wrestling ɗinan Roman Reigns, dole na saduda sai ya gaji don kanshi ya kyaleni nasha zaginsa da yi masa Allah ya isa amma hakan bai sa ya fasa yi shanye mini baki ba.
A hankali ya ciro bakinshi daga nawa ya riƙe cheeks ɗina da hannuwanshi biyu, yayin da idanuwanshi suka canza colour zuwa na wanda ke cikin zallar shauƙin so da sha'awa cikin sanyi murya yake faɗin "ina sonki Jeeddah ba zan iya jure jin kalmar tsana daga bakinki ba nasani Allah ya jarabceni da mugun sonki a zuciya rasaki tamkar rasa rayuwata ce domin duk wani bugun zuciyata yana buguwa ne da sonki da ƙaunarki.
Ture hannuwanshi nayi da ke riƙe da kumatuna na tattaro yawun bakina na tofar akan tiles ɗin kitchen, na ƙure shi da fusatattun idanuwana da suka kaɗa suka yi jajir "Wallahi na tsani wannan halin nacin naka Ya Haidar ka kyaleni kana taƙurawa rayuwata ka barni na shaƙi iskar 'yanci, ina shawartaka da ka je ka nemi mai sonka tun wuri balle ma kana da tulin 'yan mata masu haukar sonka saboda kai kyakkyawa ne mai kuɗi kou?"
  "Ba su da muhalli a zuciyata domin soyayyarki ta ri ga da ta mamaye ciki da wajen zuciyata ina miki wani irin so Jeeddah da matuƙar wahala fatar baki ta iya misalta shi ki bani dama mu zama abu ɗaya na rantse zan shayar da ke gundarin daɗi da garɗi da ke tattare a cikin soyayya.
    Ya ƙarasa magana yana ƙara marairaicewa gami da matsowa jikina, na watsa masa wulaƙantatce kallo kafin na ƙyasta yatsuna akan fuskarshi alamar gargaɗi "Ka buɗe tosasshiyar ƙwaƙwalwarka da kyau ka saurare kowacce kalma da za ta fito daga bakina ka tanadar musu da muhalli na musamman a cikin zuciyarka. Ya Haidar bana sonka ba kuma zan aureka ba koda kuwa ace duniya ce za ta taru akaina..
"Ya isa Jeeddah nace ya isa haka!
Ya katse ta cikin tsawa zuwa lokaci zuciyarsa tana daff da bugawa, da kyar yake iya fizgar numfashinsa kasancewar yana da matsalar ciwon zuciya.
Ko kaɗan ba ta ji tausayinsa ba sai ma fatar mutuwa take masa a can ƙasan zuciyarta, a fusace ta ɗauki foodflask ta sake raɓa shi tamkar za ta bangaje shi, Haidar ya sake jinginar da bayansa ga kitchen cabinet ya ƙure ta da idanuwanshi da suka ciciko da hawaye, sosai kalaman ta suka haifar masa da mutuwar jiki duk da ba yau ne rana ta farko da ya fara jin iri-iri waɗannan munana kalamai daga bakinta ba.
Ajiyar zuciya ya dinga saukewa akai-akai cikin taimakon Allah numfashinsa ya dawo normal, Jeeddah tana kammala Kwashe tuwo ta fice daga kitchen ɗin Haidar ya bi bayanta da kallo soyayyarta halitta ce a jikin jininsa da yana da yadda zai yi da tuni ya yakice sonta ko zai huta da masifar wulaƙanci da take masa, wani abu mai ɗumi ya ji yana bin kumatunsa yasa tafin hannunsa ya shafo hawaye da baisan lokaci da suka zubo masa ba. Cikin raunin zuciya ya fito daga kitchen ɗin.
Yana fitowa ya ga lokaci sallar magariba ya yi domin har an fara sallah a wasu masallatai alwala ya yi a famfo da ke tsakar gida cikin sauri ya fice yana so ya sami koda raka'a ɗaya ce a jam'i.
Jeeddah tana shiga ɗaki ta wuce bathroom ta ɗauro alwala tana fitowa Khairat tana shigowa ɗauke da hijabs ɗin da ta kammala gogewa.
Ko kallonta Jeeddah ba ta yi ba ta shimfiɗa praymat ta kabarta bayan ta kammala sallah tana cikin linke praymat Haidar ya shigo bakinsa ɗauke da sallama, Khairat da ke kwance tana chat a wayarta ta amsa mishi, fuskarshi ɗauke da murmushi ya ce da Khairat
    "Yadai 'yar uwa ba dai har sallarki ta riga ta liman ba?"
Tashi zaune Khairat tayi tana dariya gami da faɗin "Wlh kuwa Ya Haidar kasan gare ku sallah take dole mun kam an gafarta mana.
   "Mtsss....!
Na ja tsaki saboda ba ƙaramin haushi firar tasu ta bani ba, shi komai sai ya sa iskaci a ciki.
  "Ke kuma ke da wa?"
Khairat ta watsa min tambaya gami da harara.
Kafin na bata amsa Ya Haidar ya matso kusa dani ya riƙo gefen Hijabina yasa a bakinsa, ya datsa shi da haƙoransa yana min wani irin kallo mai kama da na 'yan iska sai faman lumsashe idanuwa yake, nan take tsigar jikina ya tashi yarrr!
A fusace nace "kai miye haka wannan wane irin salon iskaci ne, ya za ka dinga yi min iskanci a jikin Hijabi?"
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

_Na sadaukar da wannan littafi ga Zarah Bb_

04...

Wani shegen murmushi ya sake min wanda bashida bambanci da na 'yan iska, har wani jan iska yake daga bakinsa tamkar wanda ya ci yaji yana lumsashe idanuwa, kana cikin taushin murya ya ce "Soyayya ce kawai  Please ki daina danganta duk abinda nai miki da iskanci, wallahi tsabar so ne har ji nake kamar na cinyeki infact soyayyarki tana daff da zauta ni.
Harara na galla masa tare da jan dogon tsaki tamkar zan gutsere harshena.
    "Mtsssss....!
Kana na ɗora da faɗin "Ni dallah sake min hijabina banaso ƙarya da yaudara, da ace bansan yadda 'yan mata ke shawagi akanka ba da sai na yarda da maganganun ka masu cike da zallar yaudara, saboda haka nasan waye kai ba abinda zai fito daga bakinki na yarda dashi.
Na ƙarasa magana tare da fincike hijabina cire hijab ɗin nayi gami da  wulga shi bisa gado ya faɗa kusa da Khairat tsabar takaicin taɓa shi da ya yi yasa naji duk hijab ɗin ya fi ce min arai.
    Ƙara matsowa ya yi kusa da ni, cikin taushin murya ya ce
"Don Allah ki yarda dani Jeeddah wallahi-tallahi ban taɓa kama koda ɗan yatsan wata mace da nufi na ji daɗi ba, duk abinda zan faɗa ba lallai bane ki yarda saboda kin ri ga da kin gina zuciyarki da zargina amma inaso ki sani tabbas soyayyarki tai min illa matuƙa, ta yadda ba zan iya kallon ko wacce 'ya mace da sunan so ba.
"Kaga malam faɗawa kaji waɗannan zabi ne domin duk yadda kaso ka tsarani da yaudararrun kalaman ka ba za su taɓa tasiri akaina gara tun wuri ka adana abinka watakila ka haɗu da mai tosasshiyar ƙwaƙwalwa ka yaudare ta dasu.
Na ƙarasa magana gami da yi mishi kallon sama da ƙasa, na nufi ƙofar fita har na riƙo handle na ji sautin muryar Khairat tana faɗin
"Oh ni Ummul-khairi yau ina gani rayuwa waɗansu mutane ƙwaƙwalwarsu sam bata da bambanci da ta kifi, Don Allah Ya Haidar ka daina wahalar da kanka akan wannan matar mai ƙaramin kai kasan mutane masu ƙanana kawuna basu cika fahimtar masu sonsu da gaskiya ba bar su dai da mugun zafin kishi wanda idan basu yi hattara ba sai ya kai su ya baro.
Cikin tsanani fusata na juyo tare da sauke idanuwana akan fuskarta ina faɗin "Na rantse Khairat idan ba ki daina shiga sabgata ba sai na kwaɓar miki da haƙoran gaba.
   "Iyeee....lallai ma wai kina nufi ke ce za ki zubar min da haƙora?"
Yadda Khairat tai magana alama ce da ke nuna ba zan iya ba. Hakan ya ƙara fusata ni na tunƙarota gadan-gadan, da sauri Ya Haidar ya riƙo gefen ƙuguna ya jawo ni jikinsa sai zillewa nake yi yayin da Khairat ke ta faman tintsirar dariya cikin fusata nace "Sake ni na nuna mata tazarar shekaru biyu ba wasa bane nace ka cikani wallahi sai na zubarwa yarinyar nan da haƙora hankalina zai kwanta.
   "Yi haƙuri zakanya ai ke babba ce kina da hankalinki kada ki biyewa Khairat 'yar mitsitsiya da ita ta ɓata miki rai a banza, zo mu je waje na faɗa miki wata magana mai daɗi nasan za ta faranta miki kin ji Matar Haidar?"
Fizgewa nayi cikin tsawa nace "Dallah cikani malam ba matar Haidar ba kakar Haidar duk ka bi ka uziramin nace ka kyaleni ko ana so dole?" ke kuma Khairat za mu gauraya da ke wallahi sai kin sha mamaki abinda zan yi miki bai dai taƙamar ki shiga sharo babu shanu ba, za ki gane kuskurenki banza munafuka.
Ina gama magana na fice rai ɓace, harara Ya Haidar ya gallawa Khairat gami da faɗin "kin ganki kou Khairat so  ki ke ki kashe min aure.
Dariya sosai Khairat tasa tana rufe bakinta da tafin hannunta ɓata fuska ya yi ya ce "Zance gaskiya Khairat kin ɓatawa rabin raina da yawa ki ɗauko min aiki rarrashi da magiya ni dai tsorona ɗaya kada ki jawo min tasuɓali kamun kaza ga wutsiya ki tsinka min igiyar aurena.
Tsagaitawa tai da dariya tana faɗin
"Kwantar da hankalinka Ya Haidar kamar tsunma aranda duk duniya ba wanda ya isa ya kashe maka aure kai da aurenka da kaca aka daura shi tsinka shi sai an haɗa babbar runduna guda.
Murmushi ya yi yana shafar kwantatciyar sumar kanshi, gami da  ɗage gira "Allah kou ƙanwa?"
    "Allah kuwa babban yaya kasa wa zuciyarka salama domin har gaba da abada Jeeddah bata da wani miji bayan kai ta ka ce halak-malak, saboda haka ka sa ranka a inuwa ka daina saka damuwa akan shirmen da take maka duk ɗan banza kishi ne ke ɗawainiya da ita kasan dai hali mutuniyar taka da kafiri kishi bal-bal.
   Ajiyar zuciya ya sauke ya tako a hankali yayin da hannuwanshi ke zube cikin aljihun wandonsa ya tsaya gaban Khairat cikin yanayi na damuwa ya ce "Ba za ki gane bane Khairat ba ƙaramin tashi hankali nake ciki ba gami da wannan sauyawar da Jeeddah tayi farat ɗaya, ada dai nasan tana ƙaunata na rasa gano laifi da nai mata da yasa yanzu ta tsaneni duk lokaci da na kalleta ina hango tsanani tsanata a cikin ƙwayar idanuwanta. Khairat ina jin tsoro na rasa Jeeddah muddin hakan ta kasance Allah ƙadai yasan irin hali da zan shiga amma da matuƙar wahala idan zuciyata bata buga ba, idan kuma zuciya ta buga Khairat mutuwa ake yi wallahi so masifa ne.
  Ya ƙarasa magana hawaye na bin kumatunsa, tsananin tausayinsa ya lulluɓe Khairat, ita ɗin sheda ce akan irin mugun so da yake wa Jeeddah, tun bata mallaki hankali kanta ba, balle yanzu da ta zama ƙosasshiyar budurwa, rasata a gareshi tamkar dusashe duniyarsa ne cikin kwantar da murya ta ce "Ka fahimci wani abu guda Ya Haidar wallahi Jeeddah tana sonka kawai dai mugun kishinka ne yai mata yawa, ita fa gani take duk matan dake gari nan sonka suke yi.
    Murmushi gefen baki ya yi ya ce "Haba sai kace wani namamajo kawai dai ta daina sona ne shiyasa take fakewa da wannan labarin ƙanzo kurege.
"Koma mi take nufi ruwanta ne domin tuntuni Baba ya ri ga da ya ba ka ita jira kawai ake yi mu kammala secondary School a aura maka ita, duk wannan shirmen da kaga tana yi da zarrar kun yi aure za ka nemi shi ka rasa.
Khairat ta faɗa cike da son kwantar masa da hankali.
   Ajiyar zuciya ya sauke yayin da murmushi mai cike da zallar nishaɗi ya bayyana ƙarara akan kyakkyawar fuskarshi ma'abociya kyau da kwarjini, ba ƙaramin farin ciki maganganun Khairat suka haifar masa ba, ita kanta Khairat murmushi tayi tasa bayan hannunta ta goge masa hawaye haɗe da cewa"No more tears please she's only belong to you only you Ya Haidar.
"Thank you so very much sister ina alfahari da ke.
Tun lokaci da Jeeddah ta fice daga ɗakin bata ƙara dawowa cikinsa ba sai da taga Ya Haidar ya yi wa Mama sai da safe Sannan ta dawo ɗakin nasu, kasancewar tana ji gajiya a jikinta shi ya hana ta biyewa Khairat duk da irin tsokanata da take yi ta bi lafiyar gado ba daɗewa bacci ya yi awon gaba da ita.
Washegari kadaran-kadaham suka tashi kamar basu bane daren jiya suka dinga kwamza faɗa, bayan sun kammalawa Mama ayyukan gida da suke mata na yau da kullum suka yi wanka kowacce su ta shirya cikin riga da wando na Indian Pakistan iri ɗaya colour ne kawai banbamci na Khairat lemon green, na Jeeddah kuma red colour kowace su tayi matuƙar kyau na ban mamaki, gidansu ƙawar Jeeddah A'isha shattima za su je ta yi wa Jeeddah kitso. parlourn Mama suka leƙa Khairat ta ce "Mama mun tafi.
   "Allah ya tsare amma Don Allah Khairat karki biyewa Jeeddah ku nemi wuri ku zauna, ku barni da aiki tule a gida.
  "Tou Mama in-sha-Allah ba za mu daɗe ba.
"Shike nan sai kun dawo.
Daga haka suka fice akan hanyarsu Jeeddah ke ba wa Khairat Labarin haɗuwarta da ɗan baƙi saurayi mummuna, tana dasa aya Khairat ta dinga kwasar dariya, sai da tayi mai isarta kafin ta buge shoulder Jeeddah gami da faɗin "Kai ƙauyanci mugun abu ke yanzu Jeeddah kina nufi ba kisan idan saurayi ya yaba kyakkyawar halittar mace yana so ya nuna mata cewa babu kamarta a cikin dubbanan mata ba?"
  Zaro idanuwa Jeeddah tayi cikin kaɗuwa ta ce "Haba wai da gaske kike yi ko tsokanata kike yi?"
   "Wallahi da gaske nake miki yaba kyakkyawar halittar mace baya nufi iskanci, a takaice dai kamar so yake yace yana sonki ke kuma kwafasasshiya kika kwafsa masa wallahi ya kamata ki waye Jeeddah kullum kanki ƙara shiga duhu yake yi, banda azababben kishi da mugun hali ba abinda kika sani...
  "Dallah ya isheki banaso reni wayau.
"To kuwa wannan tauri kan naki da rashin karɓar gyara shine zai ta wahalar da ke har ƙarshen rayuwarki.
Khairat ta faɗa gami da taɓe baki.
     "Na dai ji duk abinda za ki faɗa go ahead, amma idan kika sake bakinki ya kuskure ya faɗi abinda ya sosa min rai na zage damtse naci ƙaniyarki.
Da Wannan taƙaddamar suka iso Gate ɗin gidansu A'isha shattima da kallon yanayi gate da zubin gini gida duk da sun tsofa hakan ba zai hana ka gano mamallaki gida ya yi tashe dukiya da alamu kariyar arziki ce ta same shi. Jeeddah ce ta fara tura Gate ɗin dai-dai yana fitowa daga ɗakinshi dake BQ zai fita yana sanye da boxer briefs da farar underwear vest, a jikinsa sosai muscles ɗin shi suka fito riɗa-riɗa dasu yayin da muninsa ya fito ƙarara, hanci nan nasa can sama karaf idanuwansu suka sarƙe.
Ya ɗage girar ido yana kallon Jeeddah gami da murmushin gefen baki.
Ina tozali dashi jikina yai wani tsamm...na kasa ɗauke idanuwana akansa hannuwanshi yasa ya tare min hanya cikin muryar ƙasa-ƙasa ya ce "Allah ya kama ki wato ke ga ki mai wayau kou?" kin hanani address ɗin gidanku shine ni za ki zo mana gida to ba za ki shiga ba.
   "Excuse me Please ni bansan cewa nan ne gidanku ba saboda haka bani hanya na wuce ko na ture ka don ba ƙarfi ka fini dashi ba.
   Da sauri Khairat ta ture ni gefe ɗaya ta shige gabana ta dinga ƙare masa kallo, tana ƙunshe  dariya mai kama da ta munafuci "Kaine Bilal shattima, yayan A'isha shattima kou?"
Khairat ta faɗa rass gabana ya faɗi tabbas sai yanzu naga tsananin kamanunsa da A'isha shattima musamman ɗan gajeren hancin nan nasu da alamu dai na gado ne domin kusan duk yaran gidansu haka hancinsu yake.
Ya saki ƙayatatce murmushi gami da faɗin.
   "Yeah! how do you know my name?"
   "Haba kai kuwa Ya Bilal tun da ba daƙiƙƙiya bace ni ace ina tare da A'isha shattima almost four years farat ɗaya na kasa gane blood relative ɗinta ai sai duniya tai min dariya.
   Daga jin yadda Khairat ta bashi amsa nasan da ni take "Bara mu koma gida za ki ga daƙiƙanci gani idonki kuwa dani kike zancen.
Na faɗa can ƙasan zuciyata haɗe da kwafa a bayyane kuma sai nace "Dallah malam ka ba mu hanya mu wuce ai ba wajenka muka zo ba balle ka ishe mu da karaɗi tsiya.
A ɗage ya kalle ni ya yi murmushi ya ce.
"Kafin na ba ku hanya sai na fara miƙo ƙoƙon barana babbar yaya naga wannan ƙanwar taki inaso da fatar za ki shige min gaba?"
Yadda yake magana yana kallon Khairat kana kuma ya nuna ni da yatsa take na fahimci abinda yake nufi bansan lokaci da na buga masa tsawa ba cike da takaici nace "Kai amma Allah ya wadaran girman idanuwanka da suka kasa haska maka ni ce gaba da ita ba ita bace gaba da ni.
    Yadda nai magana a hasale yasa ya janye gefe saida ya yi min wani kallo ni kuma nai masa kallo up and down na watsar na wuce abina, Khairat uwar 'yan kaudi da shisshigi tsiya ta tsaya yana zuba mata surutunsa marar kan gado.
A parlour na tadda mahaifyar su A'isha cike da ladabi na gaidata, ta amsa min ciki sakin fuska tana tamabyar lafiyar Mamanmu na amsa mata da lafiya ƙalau, A'isha ta fito daga bedroom ta tarbeni sai ga Khairat ta shigo tana dariya da sauri na banka mata harara, duk ƙoƙarina na gani bata  tasaki baki ta faɗi abinda ya wakana tsakanina da Bilal ba.
A'isha tana ciki yi min kitso yai sallama ya shigo.
Shigowarsa ke da wuya ya ce da mahaifiyarsa "Hajja ga fa surukarki nan ta kawo kanta tun kafin na kawo miki ita shiyasa nace bara na shigo na gabatar miki da ita in-sha-Allah da ita za a yi ki sa mana albarka domin ita ce Final choice ɗina.
Gaba ɗaya kunya ta dabaibaye ni na ɗauke gyalena da ke aje kusa dani da sauri na yane kaina tare da sadda kai ƙasa. Dariya Khairat da A'isha suka sa yayin da Hajja tai murmushi mai sautin gaske, da alamu abin yai mata daɗi shiyasa ta shiga faɗar "Kai Ma-sha-Allah! lallai Bilal ka iya zaɓe Allah yasa ayi damu.
    Duk sai kunya ta ƙara kamani kamar na nutse cikin ƙasa. Karaf Bilal ya amshe da "Amin ya hayyu ya ƙayyum Hajjarmu.
   Sai kuma ya ƙara da faɗin "A'isha ki tabbata kin mata kitso mai kyau sosai kinsan ita mai kyau ce dole komai nata ya kasance very special.
    "Iyeee... lallai Ya Bilal ƙawata ta ƙundume maka zuciya?"
A'isha ta faɗa tana zaro idanuwa.
    "Sosai ma kuwa A'isha saboda haka ki ci-gaba da yi min campaign har sai kin tabbatar tutar sona ta kafu cakk a zuciyarta.
    "An gama Ya Bilal ka dai ka tanadi ƙarafe campaign kasan gwamnatin ta hana aikin banza.
    "Ba ki da matsala ke dai ki tabbata naci zaɓe.
Hajja ce ta kalleshi tana dariya mai ƙaramin sauti tana faɗin "Tashi maza ka ba mu wuri duk kabi ka hanawa 'yar mutane sakewa.
   Langwaɓe kai ya yi gami da yi ƙasa da murya ya ce "Allah Hajja bangaji da kallon kyakkyawar fuskarta ba.
    "Idan kai bakada kunya ai ita tanada saboda haka sai anjima oya...ga ƙofa nan fita.
Hajja ta ƙarasa magana tare da pointing ƙofar fita da yatsanta ba don ranshi ya so ba ya nufi ƙofar yana faɗi "my final choice Hajja ta kore ni gashi ban gaji da kallon kyakkyawar fuskarki ba, amma ba komai zan koma kofar gida na jira har a kammala miki kitso mu sha firarmu ta soyayya.
   Har aka gama min kitso a takure nake na kasa sakin jikina tsakanin da Allah kunyar Hajja nake ji domin ɗanta ya yi min shi ne kalar mijin da nake mafalki mallaka.
Bayan su koma gida da dare bayan sallar isha'i almajiri ya shigo ya ce ana sallama da Jeeddah ƙofar gida, ina ɗaki amma sai da gabana ya faɗi take jikina ya bani Bilal Shattima ne mai kiran nawa. Ina jin lokaci da Mama ta ce ace nayi bacci sai duk naji ba daɗi har ji nayi tamkar nace idanuwa na biyu, amma kasancewar nasan saboda Ya Haidar yasa ta faɗi hakan dole na ƙunshe bakina nai shiru amma can ƙasan zuciyata naji zafin hakan ba kaɗan ba.
   Bilal Shattima da ke tsaye a ƙofar gidansu Jeeddah tare da abokinsa Abbas suna jiran ɗan aikensu ya dawo motar Alhaji Usman maishadda ta danno kai, wanda yaronsa na kasuwa Abdul-hadi ke driving ɗinsa parking ya yi da zimmar bude gate Alhaji Usman maishadda ya ga samari sababbin fuska tsaye a ƙofar gidansa, hakan yasa ya buɗe ƙofar mota ya fito tun kafin ya ƙarasa kusa dasu suka zube ƙasa suka kwashi gaisuwa.
     "Yawwa sannunku samari wa ku ke nema?"
"Baba wajen Jeeddah muka zo.
Abbas ya faɗa cikin kwantar da murya.
    "Uhmm....waye daga cikinku keso gani nata?"
    "Ni ne Baba sunana Bilal ɗan gidan marigayi Alhaji Ibrahim Shattima, ni ke sonta da aure in-sha-Allah.
Bilal Shattima ya tsince kanshi da faɗar haka a dalili kwarjini da Alhaji Usman maishadda yai masa.
Shiru Alhaji Usman maishadda ya yi yana nazari kafin ya ce "Ma-sha-Allah bari na turo muku da ita amma malam Bilal banaso yawan zuwa zance nan ka ji kou?"
   "Tou Baba in-sha-Allah za a kiyaye.
   "Madallah.
Alhaji Usman maishadda ya faɗa a takaice.
"Godiya nake Baba Allah ya ƙara lafiya da nisan kwana.
Bilal ya faɗa cike da farin ciki irin tarbar da ya samu daga mahaifin Jeeddah.
   "Amin ya hayyu ya ƙayyum!.
Cewar Baba gami da nufar ƙofar shiga gida yana shigowa ya soma kwalla min kira "Ke Jeeddah kina ina zo maza ga baƙi can a ƙofar gida suna jiran ki.
   Kamar jira nake nai wuff na fito riƙe da hijabina a hannu.
  "Alhaji ka manta ne da Jeeddah ayi mata miji banga amfani fitarta zance da wani ba shiyasa nace ace tayi bacci.
   Mama ta faɗa tana kallon Baba da ɗaurarriyar fuskarta don ko kaɗan bataso na fita gudun kada Ya Haidar ya zo ya ganni ransa ya ɓaci.
   "Ba komai Fatee barta ta je gudun kada yaro ya ɗauka an masa wulaƙanci.
Kafin Mama ta sake magana nai sauri ficewa da mamaki ta bi bayana da kallo domin taga yadda jikina ke rawa.
Bayan mun gaisa Bilal Shattima ya gabatar min da abokinsa Abbas a matsayin Best friend ɗinsa, yayin da shi kuma Abbas ya shiga zayyane min irin yadda Bilal ya kamu da soyayyata, ba tare da wani jan aji ba na karɓi tayin soyayyar tasa muka taɓa fira kafin Abbas ya ba mu wuri ya koma nesa damu kaɗan yana dannar wayarsa. Cikin kwarewa da iya tsara zance Bilal Shattima ya shiga jaddada min irin yadda ya kamo da sona, na fito ɓaro-ɓaro ba kunya balle tsoro Allah na faɗa masa banaso kishiya na gindaya masa sharaɗina idan ya amince ba zan min kishiya ba nima na amince hundred percent zan aurenshi.
Abinka da wanda ya kamo da sabuwar soyayya bai kawowar zuciyarsa komai ba ya amince daga nan muka tsunduma tsundun cikin kogin soyayya sai around 10 suka wuce da alƙawarin idan ya isa gida zai kirani a waya, wanda kafin mu yi sallama muka yi musayar number waya.
A takaice dai tun daga wannan ranar zazzafar soyayya ta shiga tsakaninmu, tun Ya Haidar bai gano ba har ya zo ya gane a lokaci har 'yar ƙaramar jinya ya yi yayin da Mama ta bi kowacce irin hanya domin gani ta datsa mana soyayya, ni kuma na kafe kai da fata sai Bilal Shattima.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

05...

Bilal Shattima ɗa ne ga marigayi Alhaji Ibrahim Shattima, ya yi karatunsa tun daga primary har zuwa degree duk anan gari Sakkwato.
Mahaifinsa mai kuɗin gaske ne domin sana'ar canji yake yi matansa na aure biyu Hajiya Bintu ita ce uwargidan mai 'ya'ya shidda duka mata a hali Yanzu biyar daga ciki sun yi aure autarta kawai tai saura sai Hajja mai 'ya'ya haɗu biyu maza biyu mata Faruk shi ne babban yana aiki da hukumar custom har ya kai matsayi controller sai Bahijja ita ma tayi aure har da albarka 'ya'ya biyar.
Bilal ne ke bi mata sai auta A'isha kafin Alhaji Ibrahim Shattima ya rasu ya haɗu da kariyar arziki a dalili 'yan damfara da ya haɗu dasu suka damfare shi kuɗi masu yawan gaske shi ne dalili kamuwarsa da hawan jini sai da ya yi jinya mai tsawo kafin Allah ya karɓi ransa kusan sai da jinya ta cinye ɗa abinda yai saura na daga dukiyarsa abinda ya rage bai taka kara ya karya ba.
Hajiya Bintu mace ce mai mugun kishi bala'i ga ta kyashi da hasada ga dan karen mugun hali ko kaɗan basu zaman lafiya tsakaninta da Hajja, wani irin zama suke yi wanda hakan ya shafi 'ya'yansu sosai suke nunawa junansu ƙiyayya tamkar ba uba ɗaya ne ya haife su ba. Tun kafin Alhaji Ibrahim Shattima ya rasu yaso matuƙa ya haɗa kan iyalisa sai dai hakan bai samu ba a dalili kowacce su tana da nata ɓakin hali.
Bayan rasuwarsa Allah ya daukaka Faruk ya yi kuɗin gaske sabon kishi da hasada Hajiya Bintu ya dawo sabo dal gani haka ta fantsama malaman tsibo da bokaye har tai nasarar raba tsakaninsa da mahaifiyarsa.
  Abincin da Hajja za su ci gagararsu yake yi akan idanuwanta zai aiko driving shi ya kawowa Hajiya Bintu kayan abinci haɗe da maƙudan kuɗi, ita da ta haifeshi ko kwara gero bai iya haɗa ta dashi hatta da karatun Bilal ita kaɗai ta dinga faɗi tashi har ya sami kwalin degree a fanni accounting, kasancewar lokaci da aka raba masu ɗan gado da yai saura daga dukiyar da Alhaji Ibrahim Shattima ya bari duk da ba wata abar a zo agani bace amma da yake Hajja tana da tanadi sosai ba ta saka nata da na yaranta gaba ta cinye ba sai tai dabarar siyen dabbobi shanu, tumaki da awakai ta kai ƙauyensu Yabour ƙaninta yana mata kiwo cikin amincewar Ubangiji yasa mata albarka a ciki.
Dasu ta dinga biyawa Bilal kuɗin makaranta har ya kammala degree successfully, yai bautar ƙasa a Anambara State a lokaci Bilal bashida buri da ya wuce ya kammala karatu ya sami aiki ya tallafawa mahaifiyarsa da Aunty Bahijja kasancewar ita ma cikin wahala take a dalilin lalura rashin lafiya da mijinta ya kamu dashi ya daina fita ko nan da ƙofar gida don ko magana ba kasafai yake yi ba. Tamkar mai taɓi hankali ko shafar jinnu Gashi matansa biyu Bahijja ita ce uwargidan mai 'ya'ya biyar amarya kuma huɗu sai rayuwarsu ta dawo kowa tasa ta fishe sa kai za ka nemo abinda za ka ciyar da kanka da 'ya'yanka har ma da mijin nasu duk yadda Hajja ta haɗa 'yan kuɗi ta ba Bahijja taja jari 'yar sana'ar cikin gida ciyarwa baya bari jari yai kauri saboda duk wani responsibilities na yara yana kanta, duk da makarantar Gwamnati yaranta ke karatu amma a cikin wahala take matuƙa.
  Shiyasa Bilal yaci buri samun aiki mai kyau da nagarta domin tallafa musu, duk lokaci da ya zauna yana kwantar wa Hajja da Aunty Bahijja hankali ta hanyar faɗin zarrar ya kammala karatu ya sami aiki wahalar su ta zo ƙarshe. Ranar da wannan furucin nasa ya faɗa kunnen Hajiya Bintu tai kwafa haɗe da furta saidai in bata raye, Bilal zai sami aiki daga lokaci tasa aka yi masa asiri da ya rasa mai ɗaukarsa aiki ya sha yin interview ba adadi amma daga karshe idan list ɗin wanda aka ɗauka aiki sai ya ga babu sunansa, duk da haka Hajiya Bintu bata barshi a haka ba sai da tasa bokan nata ya kashe masa zuciyar nema, balle ya nemi aikin ƙarfi tunda na Gwamnati ya kasa samuwa, komai  Hajja ce ke masa.
Ita ce ci da shansa hatta da sutura sai in ta bashi kuɗi yake iya ɗinkawa kansa, ko kuma Jeeddah ya ɗinka masa gaba ɗaya wahala ta taru tai wa Hajja yawa ga Faruk yana da shi amma bai iyawa taimaka musu da ko kwandala har ta kawo ko gida ya zo saidai ya tsaya iya sashen Hajiya Bintu kwata-kwata ya manta a rayuwarsa da yana da mata sauƙinsu ɗaya matarsa tana da kirki kuma tana ƙoƙarin taimaka masu lokaci da Hajiya Bintu ta gano saida ta nemo hanyar da ta bi ta dakile hakan. Gaba ɗaya an wanke wa Faruk tunani a cire masa mahaifiyarsa da 'yan uwansa a zuciya. Shigowar Jeeddah rayuwar Bilal ya kawo wa Hajja sauƙi wasu wahaloli, Domin kusan rabi salary ta wuri hidimarsa yake ƙarewa.
    *WANE NE HAIDAR?*
Asalin sunansa Aliyu Abubakar Ka'oje su shidda cif iyayensu suka haifa kuma dukkansu maza ne.
Mahaifinsa Alhaji Abubakar Ka'oje haifaffen garin Kebbi ne a cikin karamar Bagudo cikin garin Ka'oje, duk wanda yasan gari Ka'oje yasan Fulani ne farare masu masifar kyau, shiyasa Aliyu yake da tsananin kyawon domin ko mahaifiyarsa Hajiya Turai ba baya ba tana da matuƙar kyau gata fara sol shiyasa ma ake mata laƙabi da Turai kasancewar mahaifiyarsu buzuwa ce mahaifinsu shi ne haifaffen garin Sakkwato, kun ga kenan Aliyu Haidar gadon kyau ya yi gaba da bayansa.
Alhaji Abubakar Ka'oje Cikkaken ɗan boko ne ya riƙa manyan mukamai da dama a ƙasar mu ta Najeriya, kafin yai Retirement ya tsunduma kasuwanci man fetur da gina gidaje da manyan malls yana sayarwa, yana da manya kamfanonin da ke harka gine-gine, jahohi da dama a takaice dai babban ɗan kwangilar gina gidaje ne da shimfiɗa manya tituna da kwalbatoti a Najeriya. kuma yana cikin jerin gwano manyan masu kuɗi da suka yi sura a Najeriya ya yi fice sosai musamman yanzu da ya tsunduma harka siyasa gadan-gadan.
Haidar yana fama da matsalar ciwon zuciya wanda dashi aka haife shi, saboda ciwo da yake ɗauke dashi yasa mahaifanshi da 'yan uwanshi suke tausaya masa haɗi da ririta shi,  suna kan-kanfafa dashi shiyasa ya tashi a sangarce domin ciwo nasa baya buƙatar a ɓata masa rai sai abinda yake so ake masa ko kaɗan basa so ɓacin ransa, sakamakon wannan gata da suke nuna masa ya haifar masa da rashin juriya abu kaɗan ya isa ya saka shi kuka ƙiri-ƙiri ya dawo mai raguwar zuciya. Ko kaɗan bashi da juriya kamar ba namiji ba.
Ko wata mace ta fi shi juriya shiyasa da zarrar Jeeddah ta ɓata mishi rai sai ya saka ta a gaba yai ta kuka, har ciwonsa ya tashi shiyasa kullum yana gadon asibiti don kuwa ko da yaushe cikin ci masa mutunci take. Musanman da ta fahimci ciwonsa na tashi.
   Mustapha Abubakar Ka'oje shine babban ya yi aure har da 'ya'ya uku kasancewar matarsa tana ɗaukar dogon lokaci kafin ta haihu, yana zaune a Abuja shi ke kula da branch company ɗinsu da ke nan Abuja.
  Sai mai bi masa Suraj Abubakar Ka'oje shima ya yi aure matansa biyu yaransa shidda uwargidan ita ce mai yara huɗu amarya kuma biyu, shi kuma yana Kano shi ke kula da kamfanin su na Kano. Sai Abdulwahab Abubakar Ka'oje da ke zaune a Lagos da matarsa ɗaya da 'ya'yansa biyu, Sai kuma Sageer Abubakar Ka'oje shima matarsa ɗaya saidai bata taɓa haihuwa ba shi kuma yana Kebbi shi ke handle ɗin branch ɗinsu na Kebbi. Hisham Abubakar Ka'oje kuma shi ke riƙe da da na Kaduna shima bai daɗe da yin aure ba, don matarsa yanzu ma take ɗauke da cikinta na fari, Sai auta Aliyu Haidar Ka'oje da ke riƙe da kamfanin su na nan Sakkwato.
Aliyu Haidar ya yi karatunsa na primary school anan Sokoto ya yi secondary a Abuja a gidan Mustapha ya zauna har ya kammala karatunsa, kana ya wuce Emily Carr university of Art&Design Canada ya yi degree sa a fanni Zane. Aliyu tun yana yaro Allah yai masa baiwar zane-zane babu abinda bai iya zanawa duk abinda ya kalla sau ɗaya tak nan take zai zana sa ya fito rangaɗaɗau shiyasa yai karatunsa a wannan fanni yanzu haka duk wani gida da za a su gina ko malls shi ya ke fitar da zane, kuma a gefe ɗaya yana aikinsa personal yana aiki da wani Company ƙera motoci dake Canada yana musu zane, su na biyansa maƙudan kuɗi.
A takaice dai Aliyu artistic genius ne, don ba abinda baya iya zanawa, kwararre ne a wannan fannin.
Duk duniya bashida damuwa ko matsala face ta Jeeddah yana mata mahaukacin so yayin da ita kuma take masa mahaukaciyar zazzafar ƙiyayya.
*BACK TO STORY*
Har ya shigo ɗakin ya zauna kusa da ita bata sani ba a dalili tayi zurfi a nazarin tuno da rayuwarta ta baya. A hankali ya ɗora lallausan tafin hannunsa akan gadon bayanta ya shiga yi mata tafiyar tsutsa, ta zubara da sauri ta miƙe zaune sai yawo take yi da idanuwanta akan fuskarshi tamkar wacce taga abin tsoro, kafin ta ja tsaki "mtsss...!
Ta dauki ɗan kwalinta da zimmar rufe sabon kitsonta two step mai zigza da ya sauko akan kafaɗunta, ba ƙaramin kyau kitso ya yi masa ba shiyasa yai saurin fizge ɗan kwali ya duƙulƙule shi cikin hannunsa na hagu, a mugun fusace ta kalleshi da masifaffun idanuwanta wanda babu komai cikinsu baya ga tsana da haunshinsa kana tai kwafa tare da kawar da kanta gefe, tana wani cin magani.
Duk da kallo da take masa bai hana masa ɗora hannunsa na dama akan kitson kanta yana shafawa cikin shauƙi, wannan karon ma a fusace ta kai ma hannunsa bugu, kana ta ture shi sannan ta shiga zazzaga masa masifa tana faɗin "wai kai wane irin mugun mayye ne marar zuciya, da baisan ciwon kansa ba sau nawa zan gayamaka ka daina raɓar inda nake ka fita sabgata nace bana sonka ko ana dole ne?"
   A hankali ya shiga furta "innalillahi wa'inna illahim raji'un! Ya dafe saitin da zuciyarsa take wani irin bugawa tamkar za ta faso ƙirjinsa ta faɗo.
   Ko kaɗan bata ji tausayinsa ba sai ma kafiri tsaki da ta ja tace "Ba ciwon zuciya ba Allah yasa ciwon rai ke damunka ba abinda ya shafe ni matuƙar ba ka daina raɓar inda nake ba, na dinga kartama rashin mutunci kenan, gara ka yi wa kanka faɗa ko ka tsira da 'yar lafiya da tai saura gareka.
    Shiru Haidar ya yi still hannunshi na dafe da zuciyarsa, ya sassauta muryarsa ya ce "Miyasa kika tsaneni Jeeddah miyasa kika juyar da soyayyar da kike min ta koma zallar ƙiyayya me nayi miki, na roƙe ki a wannan karo ki ɗaure ki faɗa min laifi da nai miki da na cancanci irin wannan muguwar tsanar daga gareki domin haka kawai ba za ki tsaneni ba dole da akwai ɓoyayyen dalili da ke kaɗai kika san shi?"
Nai wani ɗage girar ido ina kallon sa a fakaice nace "sonka dai ne bana yi ko ada can da nace ina sonka soyayyar ƙurciya ce da rashin sani me so yake nufi a yanzu kuma da na gama mallakar hankali kaina sai na gano ni da kai sam bamu dace ba saboda haka ni da kai babu kare bi damo, ka je can ka nemi mai sonka.
   Murmushi yaƙe ya yi yana jujjuya kansa a kuma lokaci guda zazzafan hawaye na bin kumatunsa kai wallahi soyayya masifa ce. Har sai yaushe zai daina ɗanɗanar ɗaci da ke cikinta?"
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI...!*
         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

06...

🌑 *DUHU...*🌑
         ( *sark'akiya*)

*Daga marubuciyar*

🦎 *K'ADANGARUWA*🦎

rungumota yayi jikinsa sosai yadda jikinsa ke rawa itama haka nata keyi data rufe idanuwanta Abraham take gani daure da igiyar wuta,wasu hawaye masu d'umi ke zuba ta gefen fuskarta,kara manne jikinsa yayi da nata a hankali ya zare rigar dake jikinta ya mannata sosai a kirjinsa yana jiyo bugun numfashinta ya tallabo fuskarta idanuwansa sun kankace hawaye yake gani nabin gefen fuskarta yace "husnah kuka kikeyi ko?bakyason abinda nakeyi miki ne?"ta girgiza kai batare da tayi magana ba yace "tou mainene kike kuka"cikin tsananin damuwa da kuka tace "Abraham....."tsaki yaseer yayi cikin bacin rai yace "au tunaninsa kikeyi?aljanin kike tunani?shiyasa kike kuka husnah saboda ina taba jikinki kinfison na aljani akan nawa"yadda yayi maganar a kasashe yasa ta shiga girgiza kai ta bude idanuwanta cikin duhu take kallonsa tace "ah ah yana"shhhhhh yasa hannu a bakinsa yace "ni kinsan shekara nawa nayi cikin tsananin kunci cike da shauki na soyayyarki?shekara goma sha takwas cikin ta sha tara ina dawainiya da tsananin kaunarki ashe kinacan tare da aljani husnah,yanzun gashi kindawo gareni ina tsananin bukatarki saidai zuciyarki cike take da kaunar jinsin aljani husnah"ta fashe da kuka ya fincikota jikinsa cikin Kishi yacev"amma kinsan ni mijinki ne ko?"ta gyada masa kai a zucuyarta tace shima mijina ne saidai sam bamu dace da junaba sakamakon shi din ba jinsinmu daya ba,ran Yaseer yad'an baci yasa hannu ya tureta yana kokarin sauka daga gadon ta rukosa tana hawaye yayi mata wani kallo ta fad'a jikinsa tace "ya cutar dani sakamakon barina da yayi rayuwata cikin DUHU ya cutar da rayuwata sakamakon sawa da yayi na kamu da tsananin kaunarsa wanda fitar dashi daga zucuyata abune mai wahala dikda tsananin fushin da nakeyi dashi be hanani tunaninsa ba,yaya yaseer ka taimakeni ka ciremun son Abraham da tausayinsa daga cikin zuciyata"ran yaseer ya baci saidai yana hango gaskiyar maganarta cikin kalamanta kishi yaji ya turnukesa husnah da tasan yadda yake sonta da bata rinka fada masa kalamai akan yadda take tsananin son Aljani ba dikda baiga laifinta ba ta rayu dashi batare da tasan shidin waye ba,kwanciya tayi a bayansa ya runtse idanuwansa jin saukar nonuwanta a bayansa yasa bananarsa ta kara mikewa tsananin shaawarta yakeyi ji yakeyi idan be kusanceta ba mutuwa zaiyi ya zaiyi da momy da wani ido zai kalleta idan tagane hakan?gabansa ya fad'i mararsa yaji tana kokarin kullewa ya juyo da sauri ya rungumeta tsamm itama rungumesa tayi tana kuka mai ban tausayi cikin karfi da kuzari ya kwantar da ita ya sakko da kansa cibiyarta ya zura harshensa cikin cibiyarta yana tsotsa a hankali yana shafa mararta,wani ruwa taji yana gudu a cinyarta wani abu takeji na yawo a jikinta yana shafa mararta a hankali yana kokarin kai hannunsa hq dinta shafa kansa tayi jin haka yasa yayi ajiyar zuciya ya tabbatar tanajin dadin abinda yakeyi mata.....bude kafarta yayi jikinsa na rawa yasa bakinsa yana tsotsan gabanta cikin wani irin salo husnah hawaye basu daina zuba a idanuwanta ba Abraham shine mutumin dake tsotsan gabanta haka taji kamar zata mutu saboda tsananin dadi,dikda damuwar da take ciki da tsananin tausayin Abraham be hanata jin wani dadi na ratsata ba yana shafa cinyoyinta zuwa mazaunanta dagowa yayi tayi Nishi ahhhhahhh wayyooo ahhhh ya haye kanta ya dora bakinsa a nonuwanta yadan bude kafarta a hankali yake tura bananarsa cikin jikinta ruwa na bulbulowa wata shaawa ce take kara shigarta yadda yake tsotsan nononta da wasa da dayan yasa batasan sanda tayi yar karaba lokacin daya gama shigewa jikinta gaba daya lokacin taji wani radadi a kasanta bai cire bakinsa daga nononta ba da hannunsa haka yake dirzarta cikin wani irin salo,nishi yaseer keyi besan lokacin daya saki nononta ba yana fadin"wayyoo wayyoo husnah wayyo Allah dadi husnah zan mutu husnah wayyoo"wani irin dadi yaseer keji numfashinsa na kokarin daukewa kusan minti talatin lokacin da ya kai geji tuni ya tallabo kanta kamar mahaukaci ya  d'ora akan nononsa tasan mai yake nufi cikin radadin da takeji haka ta kama tana tsotsan nonon nasa yayi wata kara.......

*300 kacal zaki biya ayi wanan tafiyar dake sabon littafin DUHU da yanzun akeyi*

3126584401
FIDDAUSI MUSA
FIRST BANK

SHAIDAR BIYA TA WANAN LAYIN KO KATIN MTN 08036953516

*SLIMZY*✍🏻

_Ɗandano daga littafin Duhu_

Ya lumshe idanuwa a hankali a kuma lokaci guda ya buɗe su, sun kansu idanuwan nashi jin su yake yi sun yi mishi mugun nauyi sai da goge hawaye kumatunsa kana cikin raunanniyar muryarsa mai cike da karaya zuciya ya ce "Ban yarda ba Jeeddah wannan dalili naki bai isa ya zama gasasshiyar hujjar da za ki dogara da ita ki tsaneni har haka ba dole da akwai abinda kike ɓoyewa. Ni Wallahi kina bani mamaki lamarinki sai ya dinga  ɗaure min kai shiyasa a mabanbanta lukuta na kan zauna na zurfafa tunanina, domin ko zan gano da me wannan guntun mutumin ya fi ni dashi da kike sonshi ni kuma kika tsaneni.
   Na ɗage girar ido ina mishi malalacin kallo gami da yatsina fuska, cikin gadara nace "Ai abin a bayyane yake toshewar basira ne kawai irin naka tuntuni ya hanaka ganowa. Wannan guntu da ka ke gani yafi ka komai a wajena kai bara ka ji nan da ka ke ganinsa shi ne mahaɗin jini da ke gudana a jikina infact zan iya mutuwa akansa ina fatan ka gane?"
   Zazzafar iska ya fesar daga bakinsa kana shiga ƙoƙarin riƙo hannuna, da sauri na janye hannu nawa ina mai galla masa baƙar harara gami da faɗin "Kar ka sake ka ƙara tabani don ni ba 'yar iska bace da za ka dinga taɓa min jiki anyhow.
Allah sarki wallahi soyayya bala'i ce domin a maimakon ya kyaleta duk da ya ji zafin kalamanta sun kuma buge zuciyarsa, amma haka ya danne ya sake yunkuri riƙa hannunta a wannan karo kan yai nasarar kama hannun nata, jikinshi har rawa yake yi ya haɗe tafin hannunsa da nata ya jinƙe da ƙarfin gaske a sanyaye ya ce "Ba alfahari ba Jeeddah ba kuma yabon kai ba wallahi na fi wannan mutumin nesa ba kusa ba, yadda nake sonki ko kwatasa baya miki yadda kike tunani za ki iya mutuwa akansa nima zan iya mutuwa akanki don Allah ki tallafi rayuwata kada ki bari sonki ya zama sanadi datsewar numfashi da farin cikina.
   Tayi jim tana masa kallo lallai wahala bata ƙare maka ba kafin ta ce "Wallahi ban taɓa gani mutum mai baƙin naci da rashin zuciya irinka ba Ya Haidar, wato kai duk abinda nake faɗa ina sake nanawa kai sam ba ka fahimta to bari na sake yi maka gwari-gwari a manyan baƙi cewa nayi bana sonka ba zan aure ka ba saboda idan na aureka gaba baki ɗaya  rayuwata za ta ƙare cikin zulumi da fargaba don haka ka rabuda ni ka fita daga rayuwata fakatt!.
Ta ƙarasa magana tana galla masa uwar harara.
   Kamar mai raɗa ya furta "Ba zan iya ba Jeeddah wallahi ba zan iya rabuwa da ke ba. Da zan iya da tun a shekaru baya nayi hakan ki tausaya min.
Don Allah ki sawa zuciyarki salama ki sassauta min ko ba komai ni ɗan uwanki ne jinin jikinki nayi miki alƙawari ba wata fargaba da za ki yi idan kin aure ni sai ma cika ki da zan yi da ingantacciyar soyayya mai masifar daɗi da garɗi.
    "Uhmm..ka ji min wani mugun selfishness to wallahi bari ka ji in gayamaka zuciyar nan tawa dutse ce, duk magiya da daɗin bakinka ba za ka taɓa iya raunata ta da kalaman fatar bakinka ba. Haka kawai ina kallo ƙiri-ƙiri na bari maciji ya sare ni da rana tsaka cab ba zan taɓa barin hakan ta faru ba.
Ta ƙarasa magana tana murguɗa baki shi kan yanzu lamarin ta ya fara bashi tsoro yarinya sai kace mai iskokai. Ya sha jin Mama da mommy suna zargi ko asirce ta Bilal Shattima ya yi, shi kansa yanzu ya fara gasganta zargin nasu. Yo...banda aikin asiri me Jeeddah za ta tsinta a jikin mutumin da naira goma bashida ta kansa, shi muninsa bai dame sa ba domin haka Allah ya halicci sa damuwarsa ɗaya ta ya zai iya riƙe ta al'hali bashi da ko kwabo.
Jin tana ƙoƙarin fincike hannunta yasa ya dawo natsuwarsa, ya sauke shanyayyun idanuwanshi akanta wani irin sonta da tausayinta suka lulluɓe shi tsakani da Allah tausayin soyayyar da take wa Bilal yake yi, shekaru shidda suna barza soyayya duk da Mama ba son Bilal take yi ba goyon bayan Baba da ta samu shiyasa har yau Mama ta kasa raba su wani kayan takaici har kawo yau ya kasa neman aiki yi. Kuma duk wannan soyayya da take mishi za ta tashi a tutar babu ne domin ya tabbata ko tana so ko bata so shine mijinta ba wani banza jobless Bilal ba tun da har Babanta ya furta ya bashi ita ya sani ba zai saɓa alƙawari ba to ashe kenan za ta gama shirmenta ne ta dawo kan hanya.
Sai kawai ya lanƙwashe murya ya ce "Tou shikenan tun da ba za ki tausayi min ba in na mutu ai kin huta da naci na kou?"
  Cuno baki gaba tayi tana gunguni ƙasa-ƙasa "Da za ka mutu ai ni da sai na zuba ruwa a tiles ɗin bathroom nasha Allah ya rabani da ɗan anace sarkin sarakuna naci.
   Matse hannunta da yai da ƙarfi yasa tasaki ƙara "ouchhh....sake min hannu mugu kawai so kake ka karya ni ka jawo wa mijina aiki.
Tana rufe bakinta ya fizgota da ƙarfi ta faɗa jikinsa ya sakala hannuwanshi ya zagaye ƙugunta "To ai ni ne mijin koda na karya ki zan iya ɗora ki.
Ya ƙarasa magana tare da sumbatar kumatunta.
    "Dan Allah ka kyaleni Ya Haidar wallahi banaso abinda kake min...
"Shhhhhh....ya furta tare da ɗora yatsanshi saman laɓɓanta daga bisani ya shiga zagaye su. Ya matsa bakinsa a kunneta ya raɗa mata "idan kika kaini bango wallahi ina shanye miki baki, kinsan bakyaso na sha miki baki kou?"
Yadda yai magana with full confidence ta tabbata zai aikata, saboda haka tai shiru duk da haka bata tsira ba sai da ya tsotsa ɗan kaɗan ba da yawa ba a cewar shi kenan.
Kana ya fice zuwa parlourn Mama koda ya bar gida tayi bacci duk da haka sai da ya manna mata goodnight kiss a lips.
Washe gari da wuri Jeeddah ta tashi tun  7:20am ta kammala shirinta cikin brown abaya mai adon stones birjik kasancewar first period tana da class Kuma tana saka rai ta yi wa ɗalibai test shiyasa tasawa jikinta gishiri musanman sabon Principal ɗin aka kawo masu baya ɗaukar reni mutum ne mai zafin gaske, sam baya karɓa uzuri da zarrar ka sake ka ƙara koda one minute akan 8:00am ya dinga faɗa da cin mutunci kenan gashi baya jin haƙuri mafaɗaci ne lamba ɗaya gashi da mugunta kai tsaye yake kai reporting mutum a board sai dai kaga an riƙe ma salary, shiyasa take taka tsantsan da lamarinsa. A gurguje tasha tea ta leƙa parlourn Baba tadda Mama tana haɗa masa tea, ta runsuna ta gaida su"Ina kwana Baba, ina kwana Mama?"
        "Lafiya qalau Jeeddah.
Kusan a tare suka amsa mata kana Baba ya zarce da faɗin "Har an fito?"
  "Ehm!Baba yau za mu fara yi wa ɗalibai test.
   "Madallah Allah ya taimaka ga wannan ki yi kuɗi transport.
Ya ƙarasa magana tare da miƙa mata 1k ta karɓa da hannu biyu tare da godiya kana ta fice, luckily tana fita ta sami adaidaita koda ta isa ana assembly sai da ta zarce Principal office tayi sign-in kafin ta wuce staffs office, ta tadda teachers biyu a ciki suna fira tai musu sallama gami da gaida su kana ta ajiye side bag ɗinta mai ɗauke da lesson plan akan desk tare da jan kujera ta zauna tana jira a kammala assembly ta shiga class, ko kaɗan bata da juriyar tsayuwa shiyasa ba kasafai take zuwa assembly ɗin ba.
    Ana kammala assembly ɗalibai suka wuce classes ɗinsu, babu ɓata lokaci ta ɗauke bag ɗinta tai wa teachers ɗin sallama ta nufi class, bayan ta kammala masu test ta dawo staff office kafin 11:00am ta buga ta sake shiga Jss 2 suma za ta yi musu nasu test ta tarar da teachers uku a office ɗin yayin da Malama Hajara take basu labari gami da irin mugun zaman da suke yi ita da kishiyarta duk sallamar da Jeeddah take ta kwadawa basu ji ta ba domin hankulansu sun karkata ga labarin da Malama Hajara ke basu.
   "Wallahi ina gayamaku tun lokaci da Abban Amira ya ƙaro aure shekara biyu da suka wuce na daina gane kansa kullum cikin samu matsala muke wanda ada kafin ya ƙaro aure muna da kyakkyawar fahimtar juna. Amma tun da ya auro wannan ɗiyar shegiya tsinaniya, ta shiga ta fita ta rabani da mijina. Yanzu har ta kai ta kawo baya so ganina ni da yarana wata muguwar ƙiyayya yake nuna mana. A hali da ake ciki yanzu wallahi har ya fara fice min arai, a wasu lokuta sai naji kamar nace ya sake ni sai kuma tausayi yarana ya kamani ko yanzu da nake cikin gidan ubansu basuda 'yanci su wataya ina da na tafi na barsu. Jiya da dare bansan tuggun da makirar ta kula min ba har nayi bacci ni da yara ya shigo ɓangarena yana buga min ƙofar ɗaki tamkar zai ɓalla ta ina buɗewa, ya rufe ni da faɗa da zagi ya ƙare min zagi ciki da waje, har cewa yake yi nasani yanzu bana gabansa yafi ƙaunar amaryasa sau dubu dani, ke in takaici muku labari inda yake shiga ba ta nan yake fita ba sai da ya ƙare min zagin ƙare dangi kwana nayi ina kuka yadda naga rana haka naga dare, wallahi kishiya bala'i ce babbar masifa ce ko maƙiyi na bana fatar ai masa kishiya. Kuma wani abin takaice ba don Allah ta aure shi ba kyawonsa ne ya ja hankalinta domin ko kusa ba ajin aureta bane mahaifinta shahararren mai kuɗi ne me za tayi da ƙaramin ma'aikacin gwamnati, infact ta fi shi salary nesa ba kusa ba. Da zarrar faɗa ya haɗa mu da ita sai ya goyi bayanta koda ni ce da gaskiya sai ya dinga kirana da tsohuwar matsiyaci, kalmar nan tana min ciwo wallahi.
  Ta ƙarasa magana tare da goge guntaye hawayenta.
Tun da ta fara magana har ta dasa aya gaban Jeeddah yana dukan uku-uku wani irin abu take ji ya tokare mata maƙogwaronta da kyar take iya jan numfashinta ko kaɗan bataso ta ji ana zance kishiya Allah kaɗai yasan irin mugun yanayi da take tsintar kanta ciki.
  Jin Malama Zainab ta karɓe zance yasa Jeeddah tai sauri baza kunnuwanta tana sauraren abinda take faɗa.
    "Uhmm... bari kawai Hajara ni sai nake gani matsalar ki kamar shafi vasiline ce akan tawa, tun da duk tsiya yana ba ki hakken ki na aure saɓani ni da ko kallo ban isheshi ba ke in takaice muku labari tun da na aure Baban Hafiz nake rungumar takaici da baƙin ciki uwargidansa ta ri ga da ta asirce shi ta wanke gindinta ta bashi ya sha, juya shi take tamkar waina a tanda sai abinda ta faɗa yake yi. Ni da banza bazara duk ɗaya a wurinshi rabona da na haɗa shinfiɗa dashi tun kafin na haifi Ramlah gashi har Ramlah tayi shekaru biyu.
Wallahi nayi regretting aure mijin wata. Shiyasa ku ga ko an kawo talla kayan mata bana saya tun ni da wacce bata da miji duk ɗaya idan sha'awa ta dame ni sai dai na nemi ruwan zafi na gaggasa jikina ni ce kullum cikin shan lemon tsami Idan abin ya ishe ni nai yaji na tafi gidanmu a maimakon iyayena su tsaya su bincike matsalar da nake ciki sai su rufe ni da zagi gani suke yi Allah ya rufa min asiri na aure mai arziki  basu san gwara aure talaka da bashi da ci yau balle na gobe ba idan har zan sami kwanciyar hankali da natsuwar zuciya. Wallahi danasan abinda zan isko gidansa kenan da ban amince na auresa ba gara na aure tsohon saurayina Rabi'u da bai da ko kwabo ko ba komai zan more rayuwar aure.
    Cabdijam! Tashin hankali wanda ba a sa mishi rana, su ke zayyano matsalar gidajen aurensu amma jikin Jeeddah ke rawa ga wani ɗan uban gumi da ta haɗa gaba ɗaya ta jiƙa  abayar jikinta.
   Cikin ƙarfi hali na kai duwawuna kan kujera ɗabass...tabbas ko zan mutu ba zan amince na aure Ya Haidar ba, Bilal shi ne nake da tabbaci idan na aura shi ba zai min kishiya ba, ba zan fuskanci matsala kwatankwacin iri ta su Hajara da Zainab ba saboda Bilal ɗinta mummuna ne ajin farko gashi kuma bai aje ba bai ba wani ɗan banza ajiya ba, wanda bai da komai ina ga zance ƙaro aure tuno da haka da nayi yasa naji hankalina ya ɗan kwanta. Har na sami ƙarfi hali sauki numfashi.
Misali ƙarfe 3:00pm aka tashi ɗalibai nan ma sai da ta je tai sign-out tun kafin ta isa Gate ta hango Bilal Shattima zaune akan machine ɗinsa ya zo ɗaukar ta dama wasu lukuta yana zuwa dauƙar ta tun kafin ta ƙaraso ya shiga wanke ta da sanyaye murmushinsa,  ita ma ta mayar masa da martani  tana isowa wajensa ya shiga koɗata da zuba mata kirari da yake ƙara fasa mata kai, ya ƙara mata tanbaci ba zai mata kishiya ba.
      "Barka da fitowa sarauniyar matan duniya daga kanki babu wata na datse ƙofar zuciyata da ƙaton padlock na jefa key cikin tekun maliya, kifi ya haɗiye.
    Haba wa sai ga goganyar taku ta yage baki tana babbaka dariya, har wani rangaji take da kai kamar wata doluwa.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI...!*
           _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

07...

*💝EL HABEEB 💝*
        Part two

Baki kawai take turowa tunda Aunt Mimi ta fara magana, cikin tura baki tace
"Aunt Mimi shifa mutumin nan ba'a burge sa wllhy ko me mutum zaiyi".
Sai da Aunt Mimi ta harare ta kafin tace
"Waliyyi ne shi? ko kuma dutse ne da zai ganki cikin naked dress yace baiji komai ba? sai kin tashi tsaye yarinya mijinki ba irin sauran mazaje bane yanzun nan wata zata yi miki wuff dashi gara ki tashi tsaye tashi muje bedroom ɗin naki inga irin kayan daya dace ki dinga using dasu a gida wanda zaki rikirkita mana wannan Mr Habeeb Gashuan naki mara alƙibla.....

   _El Habeeb part two kenan for 300 hundred only Maryam Ibrahim first bank 3196848636_
_Masu buƙatar karanta part one zasu yi min magana akan wannan number 09139964697_
_Sai kunzo_

Oum Hanan
09139964697
*Kaɗan daga cikin littafin El-Habeeb*👆👆👆

Tsagaitawa da dariya tayi cikin nishaɗi take faɗi "Kada ka fasa min kai mana bawan Allah.
  "Ba wani fasa miki kai da zan yi Baby kin cancanci fiye da hakan. Ai yana ɗaya daga cikin dalillai da yasa duk lokaci da na kalli kyakkyawar fuskarki sai naji sonki da ƙaunarki na daɗa ƙaruwa a zuciyata, ina sonki Jeeddah sai dai ina fargabar kada Haidar Ka'oje yai nasarar rabani dake...
Uwar harara ta watsa mishi wanda yai sanadi da ya haɗiye raguwar kalamanshi, cikin yanayi na ɓaci rai ta ce
  "Don Allah ka tofar da wannan mugun yawun na bakinka ina mai tabbatar maka koda zan rasa raina ba zan taɓa amincewa da aure Ya Haidar ba, idan har kana gudun ɓaci raina karka sake ambata min sunanshi.
  Sauke numfashi ya yi gami da faɗin "Ki yi haƙuri Love amma nima ya kamata ki duba lamarina domin wasu daga tsirarun mutane gidanku ba son alaƙarmu suke ba. Kina dai gani abinda Mama tai min three days ago wallahi-tallahi da bana sonki da na haƙura dake domin wulaƙanci da cin kashi da ake min ya fara tsallake iyaka sai kace ni ne mutum na farko da a jobless.
   Ya ƙarasa magana cike da takaici tunawa da irin yankar ƙauna da Mama tai masa kwanaki uku da suka gabata, duk lokaci da ya tuna sai ya ji sabon ɓaci rai ya lulluɓe shi.
   Sai da ta fara hawa machine ya ja suka hau kan titi, kana ta sami damar furta "Kai ma Love da naka laifi fissibilillahi shekara shidda muna soyayya ba fa wata shidda bane ace ko baikon nan na banza babu a tsakaninmu, koma waye dole ya zargi yaudara ta kake yi.
   "Haba Jeeddah ya za ki faɗi haka kin manta sanda na taɓa turawa amsar da Baba ya bayar cewa ya yi fa ajira har ki kammala karatunki.
   "To amma tun yaushe na kammala karatu ko fara aikina almost two years kenan gaskiya ni dai ka turo kawai, don wallahi na gaji da zaman gidanmu sa'o'ina sai aure suke yi ni ina zaune gida.
Sosai jikin Bilal Shattima ya yi sanyi yasan duk yadda ake haƙuri Jeeddah tai haƙuri dashi, maganarta akwai ƙamshin gaskiya a ciki, amma shima idan za tai mishi adalci tasan cewa ba laifinsa bane ta ya zai aureta al'hali bashi da aiki yi. Cikin kwantar da murya ya shiga faɗin.
"Yadda nake ji sonki a zuciyata Jeeddah da ace da yadda zan yi da tuni kin daɗe a gidana wallahi don dai banda yadda zan yi ne da rayuwata aiki nan kullum cikin nema nake amma yaƙi samuwa. Sanin kanki ne  aure ba zai yu ba idan babu abin cinyar da mace, nasan kina sona kuma kin yi haƙuri jirana amma don Allah Jeeddah ki daɗa ƙara min lokaci in-sha-Allah zuwa cikin sabuwar shekarar nan da ke tafe za a san abin yi, ai na gayamiki akwai wani aiki na Company da nai apply to yau da safe sun turomin da message next week za su yi interview a Kano kin ga idan Allah yasa aka dace ko gidan haya ne sai na kama mana, yanzu damuwa ta ɗaya ce kuɗin mota.
    "Kuɗin mota ba matsala bane yanzu kafin mu rabu zan yi ma transfer na 20k sai kuma magana ta gaba inaso gaskiya kafin ka tafi ka turo ayi mana baiko, ni ko ba ka da aiki tun da ina dashi zan iya ɗaukar responsibilities ɗinmu na kuma tabbatar salary na zai wadace mu, a talauce ba a wahalce ba kafin Allah yasa kai ma ka sami aiki amma ci-gaba da zaman mu a haka bai amfani.
  Da sauri ya gangara gefen titi ya yi parking with so much shock ya juyo yana kallonta, ita kanta tana mamaki tsayuwar su da kuma irin kallo da yake mata.
Ba wai yana kallonta bane don za tai mishi transferred na 20k ba kawai dai yana mamaki furucinta na ƙarshe.
   "Wai abinda kika faɗa da gaske kike yi kuwa tsokana ce?"
"Me kenan?"
Na faɗa saboda ban fahimci inda tambayar tashi ta dosa ba.
   "Na cewa da kika yi mu yi aure za ki kula da gida da albashinki
    Sai da tayi murmushi kafin ta jinjina kai gami da faɗin "wallahi da gaske nake yi next month in-sha-Allah zan Kwashe adashena dubu ɗari biyu  kasan na gayamaka every month Ya Kabeer yana da tura mana da 5k ni da Khairat da suna mu dinga siye cosmetics, ni nawa haɗawa nake yi na zuba adashe. Zan ba ka kuɗin sai ƙara cikin hidimar biki. Amma don girman Allah this time karka min iri na wancan lokaci.
    Cike da shauƙin sonta da gundarin ƙaunarta ya riƙo hannunta ya haɗe da tafin hannunshi yayin da wasu hawayen farin ciki suka soma bin kumatunsa ya rasa gane wane iri mugun son Jeeddah take masa duk da ba yau ne karo na farko da ta fara bashi kuɗi ba, amma yau ɗinan ta faɗi abinda bai taɓa tunani faruwar sa ba sai dai fargabar sa ɗaya iyayenta za su amince da wannan ƙudirin nata. Sai kuma ya ji jikinsa ya yi sanyi duk wani farin ciki da yake ji ya fara dusashewa, cikin raunin murya ya ce "Jeeddah kina gani gidanku za su amince da wannan shawarar taki?"
  Sai da na yatsine fuska gami da taɓe baki, don na tabbatar koda Baba zai amince sai an sha artabo da Mama, ni kuma na ri ga da na shiryawa duk wani ƙalubali cikin ƙarfaffa mishi guiwa na ce "Ai ba fitowa fili zan yi na faɗa musu manufa ta kaitsaye ba kawai zan ce ka fara aiki a shagon siminti Yayanka Faruk, ka ga kafin lokaci In-sha-Allahu ka sami aiki.
    "Me za ki ce masu idan aka tambaye ki kuɗinki na adashe?"
Ya sake watsa mata tambaya saboda har yanzu yana jin shakku akan wannan ɓatatciyar dabararta ta.
"Cewa zan yi suna cikin account ɗina tun da dama ta account ake turawa duk wacce kwasa ya zo kanta, ka ga shike nan na ɗinke bakin kowa kuma don Allah zance kuɗi nan ya zama sirri a tsakaninmu.
   Duk yadda zai misalta farin ciki da yake ciki ba lallai bane a fahimta.
"Ban san da wacce kalma zan yi amfani da ita domin bayyanar miki da iri tsan-tsan farin ciki da nake ciki ba, babban burina a rayuwa na mallake ki a matsayin matata sai gashi kina ƙoƙari cika min wannan buri nawa. Fatana Allah ya bani ikon faranta miki ina mai sheda miki zan yi duk iya ƙoƙarina na wanzar da farin ciki wa rayuwarki Jeeddah ba za ki taɓa danasani zaɓe na a cikin masoyanki ba.
Zan rayu da ke kaɗai tak daga kanki ba wata 'ya mace da za ta sake huɗa cikin zuciyar nan tawa.
Ya ƙarashe magana yana nuna saitin da zuciyarsa take.
Wani iri daɗi ya ratsa sassa jikina, na ji duk duniya ba mace da ta kaini sa'a domin na yarda na kuma aminta Bilal Shattima shi ne namiji da zan rayu dashi ba tare da ya min kishiya ba. Ba kamar Ya Haidar ba domin lokaci da muke cikin ganiyar soyayya idan nace "Ya Haidar ai ba za ka taɓa yi min kishiya ba kou?"
A maimakon ya bani kyakkyawar amsa iri wacce koda yaushe Bilal Shattima yake bani da yake shi namamajo ne sai kawai ya ce da ni "Jeeddah ita rayuwa da kike gani ba fa mu 'yan adam ke tsarawa kanmu ita ba, ba zan miki wannan alƙawari ba domin bansan iri tsari da Allah subhanahu wata'ala ya tsara min ba. Amma ki sani koda Allah ya ƙaddaro min aure mace fiye da ɗaya ina mai tabbatar miki da cewa soyayyarki ba za ta taɓa dusashewa a cikin zuciyata ba, domin na fara sonki tun kafi ki zama cikakkiyar mace.
    Tunowa kaɗai da nayi da wannan zance nashi sai da naji ɗa karan ɓaci rai yana neman ya bata min mood, nai sauri kawai da zance nashi mai cike da zallar takaici da kayan haushi.
  Murmushi na saki gami da rausayar da kai ina mishi wani iri kallo mai tada hankali ɗan namiji, ai kuwa na tashi hankalin nasa don kuwa mantawa ya yi da muna gefen hanya sai kawai ya sumbace hannuna da ke jinƙe ciki nashi, abinda duk tsawo zama na dashi bai taɓa yi min ba wannan iskanci da gantallewa sai Ya Haidar don shi lungu da saƙo na bakina ba idan ba kai harshen sa ba, kun gani ko anan Bilal Shattima ya fita daban Ya Haidar kuma ko ban faɗa ba kun ga alamomin da suka nuna shi ɗin womanlizer ne duk lokaci da tsau-tsayi yasa na kalli hantsar wandonsa sai naga erection ɗinshi.
Shi fa kullum abinsa a tsaye take ta ya iri wannan jarabbbe ku ke tunani zai rayu da mace ɗaya kwalli kwal Gaskiya Allah ya taimake ni da nai sauri ganowa da wuri.
Girgiza min hannu da Bilal ya yi yasa nai sauri dawowa cikin natsuwata, sai da na lumsashe idanuwa na kafin na ce "Amma Love ka manta da muna kan hanya ne naga you're try to cross your limit?"
Na ƙarasa magana ina dariya, shi ma darawa ya yi gami da yi wa machine key sai da muka hau kan titi ya bani amsa ta hanyar cewa "Afuwan  Love sumbatar farin ciki ce kawai in-sha-Allah ba zan ƙara ba balle har na tsallake iyaka zan jira har akai min ke a wannan dare kan ba ɗaga ƙafa, na tabbata daga ranar da kika kwakwaɗa min zumarki shi kenan za ki ƙarasa dusashe hasken mata duniya a idanuwana, zan dawo ina kallonsu tamkar maza 'yan uwana.
  Cikin nishaɗi na kai masa duka a shoulder ina yaƙar haƙora kamar mai talla toothpaste na ce "Huhmm... Love kana zuzuta ni da yawa iri waɗannan daɗaɗda kalaman naka su na ɗaya daga cikin abinda ke ƙarawa sonka linƙaya a kogi zuciyata.
   "Ai ni haka nake so love ki ta zurmawa a soyayyata ta yadda babu wani mahaluki mai jini a jiki da ya isa ya farraƙa mu.
   "Gaskiya kam love babu shi don ko akwai shi a shirye nake da nayi fito-na-fito da koma waye, ni yadda nake da tabbaci akan ba za ka yi min kishiya ba idan aka yi yunkuri rabani da kai zan iya kashe kaina wallahi.
   Dariya ya tintsire da ita don shi kalamanta dariya suke bashi sosai yake nishaɗantuwa da wannan lafazin nata a ganinsa faɗa kawai take yi ba don za ta iya aikatawa ba.
Da haka suka ci-gaba da firar su mai daɗi kafin su iso gida ya tsaya a wani ƙaramin super market ya siyo mata fresh milk mai sanyi da su tarkace biscuits da chocolate dama matuƙar yana 'yan canji a jikinsa su ne kaɗai iri kyautar da ke shiga tsakaninsu, ko kuma ya siyo mata awara kunsan samari yanzu har da awara suke neman aure da ita.{lol😅}
Tun kafin mu iso ƙofar gidanmu na hango motar Mr ɗa anace a Parke duk sai na ji raina ya ɓaci saboda ba ƙaramar gajiya na kwaso ba yanzu kuma zai bi ya taƙura ni ya hanani shakattt!
Bilal Shattima ya yi parking a bayan motarsa na sauko ya miƙo min farar leda mai ɗauke da tambarin super market ɗin na karɓe tare da zuba godiya kamar wacce aka ba kyautar sarƙa gold. Sai da naga tafiyasa kafin na juya na nufi gate ina mai ƙara gyara zaman side bag ɗina da ke rataye a shoulder na.
   Ina shiri tura ƙaramar ƙofa da ke haɗe da gate na ji an kira sunana da kakkausar murya "Ke Jeeddah!
Wallahi sai da na tsorata don a firgice na juya, idanuwana suka sauka akan kyakkyawar fuskar nan tasa wacce na fi tsana fiye da duk wata halitta dake jikinsa, ya yunkura ya fito daga mota jikinsa sanye da blue jeans trouser da red colour shirt mai gajeren hannu, kansa ɗauke da p-cap blue colour kafin na kai idanuwana akan ƙafafuwanshi ya ƙaraso wajena a mugun fusace ya ce "Na gaji da wannan iskanci naki kina daff da ƙure min maleji wallahi.
Zaro idanuwa nayi gami da taɓe baki ina masa ƙasƙantatce kallo, cikin izza da gadara na ce "Wannan daga cikin iskanci nawa kasan suna yawa saboda ma yawansu ni kaina ba zan iya ƙididdige su ba kaitsaye.
  Sai da ya fesar da iska mai zafi daga bakinsa da alamu yau na kai shi maƙura dama abinda nake so kenan, ya yi fushi ko zai fita sabgata, saboda na ƙara tula mishi haushi sai kawai na shiga jujjuya jikina ya haɗiye wasu mugaye miyau kafin ya ce "Na fahimci ba ki san ciwon kanki ba ko kaɗan shiyasa kike tale abu mai tsada da daraja ki haye machine, to na gaji da gani wannan kayan takaici in banda wulaƙanci ina tattali da ba wa abu kulawa ta musamman ranar tsaka na dinga gani ana masa riƙon sakainiyar kashi to ba zan lamunci haka ba.
Da mugun mamaki, na waro idanuwa na shiga ƙare mishi kallo duk na fara hasashe abinda yake nufi domin na ƙara gasganta hakan ne yasa  nace "Excuse me please can you tell me exactly what you're saying.
   Muguwar harara ya galla mata don gani yake ta ma rena masa da hankali da ƙarfi ya finciko hannunta ya banki ƙofar gida da ƙafarsa ta buɗe  ya tura ta da ƙarfi tai tagal-tagal kamar za ta kife ƙasa yai sauri chafko hannunta, ya fizgota sai da ledar hannunta ta faɗi kayan da ke ciki suka tarwatse, ta dafa ƙirjinshi da hannuwanta yayin da shi kuma ya zagaye ƙugunta da hannuwanshi ya matse ta sosai.
    "Na fahimci kina so ki maida ni ɗan iska na dinga faɗar maganganu batsa kou?" to tun da su ki ke so ji bara na raɗa miki a kunne.
Ya ƙarasa magana gami da yi mata raɗa.
Dama nasan za a yi haka shiyasa lokaci da ya ambaci sunan abin ban wani girgiza ba, yo...ɗan Iska irinsa faɗar waɗannan abubuwan ai ba wani abu bane a wurinsa.
   "I hope you get me clear?"
Ya sake faɗa yana goga min tsini hancinsa akan nawa hanci, gyaɗa masa kai nayi don ni gaskiya lamarinsa ya fara fin ƙarfina tsorona ɗaya kada wata rana ya danne ni yai min fyaɗe.
  "Ki buɗe bakinki ki bani amsa ai ba cutar kurunta ke damunki ba ko ke kurma ce?"
  "Ka ji tsoron Allah Ya Haidar ka daina yi min irin waɗannan maganganu sai ka jawo girmanka ya zube a idanuwana.
Taɓe baki ya yi gami da ɗan mari kumatuna, yana faɗin "Ke ji ki da wani zance ba ki san cewa na fiso ki daina gani girman nawa ba idan kika ci-gaba da gani girmana ai da wuya ki barni na more first night ɗinmu da kyau.
  Miyau takaici na haɗiye  don ba ƙaramin kai ni bango ya yi ba, kuma komai zan masa na tabbata ba zai sake ni cikin sauƙi ba, sai kawai dabara ta faɗo min nai ƙasa da murya na ce "Ya Haidar dan Allah ka cikani fitsari nake ji wallahi ya cika min mara.
   Da sauri ya sake ni gami da ingiza ƙeyata yana faɗi "Ba dole fitsari ya cika miki mara ba kin je kin danne abu da seat ɗin machine dallah wuce zuwa fitsari kada ya kubce miki don ke ba gudun abin kunya kike yi ba.
   Sai da na galla masa harara kafin na duƙa da nufi tattara kayana.
   "Ke dallah shige gida mana kwaɗayayyiyar banza da wofi kalli wannan tarkace wofi da basu wuce naira duba ɗaya kacal ba kike ma rawar jiki, to ba za ki ci ba almajiri zan ba wa.
  Na fasa tsinci kayan na wuce cikin gida ina gunguni kuma duk manya-manyan zagi ne nake antaya masa.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

8...

Tafe nake ina ci-gaba da mita a zuciyata "Ka ji min shegen mutum wai har ni zai kalla ya ce bana gudun abin Kunya, tsaka ni dashi waye ne bai gudun abin kunya, shi da kullum bakinsa cikin faɗar maganganu batsa yake don tsabar reni wayau zai ce min bana gudun abin kunya sai da  ya faɗawa wanda bai san halinsa ba ba dai ni Jeeddah ba, da na gama sani waye shi.
Sai da na fara leƙawa ɗakin Mama na ce mata na dawo kafin na wuce  ɗakinmu, ina zuwa na cire kayan jikina na ɗaura brown towel, Khairat ce ta shigo dawowarta kenan daga wuri nata aiki jakkar hannunta ta jefa kan gado tare da cire hijabin jikinta, kasancewar makarantar da take koyarwa kusa da gida ne shiyasa take zuwa a ƙafa.
   "Washhh! Allahna yau akwai rana kamar za ta fasa ƙwaƙwalwar mutum.
Khairat ta faɗa sa'ili da take ƙoƙarin cire kayan jikinta.
   Na juya na kalleta kana nace "Bari kawai abin ba a cewa komai gara ma ke kina kusa da gida saɓani nida nake wata uwa duniya gaskiya idan nai aure transfer zan nema na dawo kusa da gidana da aurena ba zan iya jure tafiya mai nisa ba.
   Wata dariya reni wayau Khairat ta tintsire da ita gami da faɗin "Ma-sha-Allahu! Jiddon Baba yaushe kika yi miji har dasu gida ni da nake ƙanwarki kuma aminiyarki bansani ba gaskiya ki gyara halinki zama bai ce haka ba 'yar uwata.
Yadda Khairat tai magana ya tabbatar min da gatsali take min wato ta ma mayar da ni gantalalliya ko mahaukaciya. Nan take raina yai masifar ɓaci sai kawai na juya a fusace na nufi bathroom ina ji lokaci da ta sake kece wa da dariyar sheƙiyanci tana faɗin "Ashe dai su Hajiya Jiddo ana so aure miji ne kawai babu da za ki ɗauki shawarata da nace ki jingine wannan mummunan buri naki, ki rungume Ya Haidar ɗinki har wahalar fita teaching cikin uwar rana zai raba ki dashi, amma wallahi idan ba shi kika aura ba rayuwarki tana cikin kwalekwale, wallahi ba baki nai miki ba muddin kika aure ɗan kundalo  wahala duniya ce za ta zama ajalinki.
  A fusace na juyo tare da  hayyaƙo mata har towel ɗin jikina ya shirin zamewa amma tsabar masifa ko ta kanshi ban bi ba na ce "Ai sai ki zo ki aura min shi shegiya baƙar munafuka wacce kwata-kwata a rayuwarta bata nufi na da alkhairi. Ɗan kundalo nan da bakwa so shine dai zaɓina sai dai baƙin ciki ya wulla mutum kabari ehee.!
   "A'ah! tou maida wuƙa 'yar uwa ai kowa ɗebo da zafi bakinsa kuma duk wanda rai yai wa daɗi bai yi kamar mashi ba, mu kam 'yan araka yarima ne asha kiɗa Allah ya bada sa'a dama mai rabon shan duka ba ya jin kwaɓa.
  Ko kusan ban fahimci inda zaurance ta ya dosa ba saboda haka na dalla mata harara tare da jan guntun tsaki, na ce "Haka dai za a ƙare a sana'ar munafuci wacce bata da riba.
Dariya tayi haɗi da shewa tana wani jujjuya ɗuwawunta kana ta watsa min kallon banza tana yatsina ta fice tabar min ɗaki bayan tasan ta manna min hauka ai kuwa na ci-gaba da zaginta sai da nayi mai isata kafin na shiga bathroom nayi wanka sai da na gabatar da sallar la'asar kana na shirya cikin atamfar chiganvy style ɗin A-shape sosai ɗinki ya fiddo min da shape ɗin jikina duk lokaci da nasa kayan ba ƙaramin kyau suke min ba suna ɗaya daga cikin tufafina da nake bala'in so.
Ina cikin shafa turare Ya Haidar ya kunno kai ta cikin dressing mirror da nake tsaye na shiga watsa masa baƙar harara, na rasa yadda zan yi da wannan mutumin duk ya bi ya taƙurawa rayuwata, ya zame min ƙarfen ƙafa wallahi da yasan yadda na tsani ganinsa da ko biyansa aka yi da kuɗi ba zai kusanto inda nake ba.
Tun kafin ya ƙaraso na ɗauki ɗan kwalina da ke aje akan gado yana zuwa ya fizge ɗan kwali, yana min wani shegen kallo gami da murmushi ƙasa-ƙasa ya sassauta murya kamar ɓakin munafuki ya ce "iyeee...Jiddatuna mai kyau kinga yadda rigar nan ta karɓe ki tubarallah Ma-sha-Allah abubuwa sun fito gwani sha'awa ina da an zarga miki igiyoyi aurena
wallahi da ji kawai za ki yi nayi wuff dake sai tsintar kanki za ki yi a tsakiyar gadona uhmm! Bari kawai na haɗiye ɗaɗina fatana Allah ya kai damo ga harawa ko bai ci ba yai birgima abinsa.
Saboda tsabage takaici basan lokaci da na dafe goshina ina masa kallon tsana, kana na ja tsaki tare da faɗin "Ɗan iska dai bai ji daɗin zaman duniya ba kai kam a haka za ka ƙare to sai dai a mafalkinka wallahi.
Faɗaɗa murmushin kan fuskarsa ya yi tamkar bai ji zafin maganata ba ya ce "Daina faɗar haka Jeeddah kinsan abu ga Allah babu wuya gobe-gobe nan sai ki ji an shafa fatiha a tsakaninmu wallahi ina tabbatar miki a ranar tsabage zumuɗi ba zan jira sai an kawo min ke ba ko a ɗaki nan za mu iya bajewa abinmu.
   "Cabdijam! Wallahi ba dai ni Jeeddah Usman maishadda ba sai dai in da wata can daban za a shafa maka fatiha ka baje da ita.
"In-sha-Allahu dake za a shafa kuma da ke ɗinan zan baje wata tara ciff Hajiya kin haifa min little Jeeddah.
Ya ƙarashe magana yana wani shegen blushing mai ban haushi tsaki kawai na ja tare da zuzzuba mishi harara
Ko a jikinsa sai ma ci-gaba da magana ya yi
"Wallahi ina sonki Jeeddah irin so da baya faɗuwa balle a misalta shi... Don Allah ki so ni nima koda rabin kwatankwacin wanda nake miki ne.
Yadda ƙarasa magana yana narkewa kamar man shanu a wuta, kana ya haɗe tazarar dake tsakaninsu, ya riƙo hannunta ya ɗora saitin da zuciyarsa take ta ji zuciyarsa tana bugawa da ƙarfi "kin ji yadda zuciyata ke bugawa kou? Duk saboda sanadin sonki ne ki tausaya min ki tuna ba wadatatciyar lafiya ce dani ba, abu kaɗan zai iya tayar min da ciwona.
Ko darr kalamansa basu sa ta ji ba sai ma shegen haushinsa da ta ji ya ƙara turnuƙe ta da hanzari ta kwace hannunta gami da raɓa shi ta nufi ƙofar fita, ina gani ya biyo ni na rugu da gudu, duk da na shiga parlourn Mama bai hakan bai sa ya kyaleni ba sai da ya biyoni hatta da abinci da na ɗebo sai da ya saka hannunshi yaci, saboda shegiyar yunwa da nake ji yasa na haƙura muka ci tare.
Sai daff da magariba ya wuce sai lokaci naji kamar an gafarta min muddin Ya Haidar yana gidanmu, jina nake yi tamkar ina bisa ƙaya.
Bayan sallar isha'i muna zaune a tsakar gida muna fira saboda duk lokaci da babu wutar lantarki kuma ba a tashe gen ba anan muke zama har Baba kafin a dawo da wuta kowane mu ya koma ɗakinsa. A daidai ƙofar shiga parlourn Baba Mama ta shimfiɗa mishi carpet ya zauna yana sauraren labarai duniya a ɗan ƙaramin rediyon sa. Ni da Khairat kuma muka shimfiɗa tabarma a ƙofar parlourn Mama yayin da kowacce mu ke dannar wayarta hankali kwance.
Kiran Bilal ya shigo wayata, nayi picking gami da sassauta murya ƙasa-ƙasa "Hello... Love!
"Love gani a ƙofar gidanku.
"Okay Love just a minute ganina tafe.
"No problem Love take your time.
"Yeah!
Nai sauri tashi jikina na rawa na shiga ɗaki duk da babu wutar lantarki sai da na gyara fuskata  tare da fesa turare na sako zubulele hijab yana ja a ƙasa, saboda doka ce Mama bata bari mu fita zance da gyale.
Direct kitchen na shiga na buɗe deep freezer ɗin Mama na ɗauko robar kunu aya da zobo manya guda ɗaɗɗaya na dauƙo tray da cup garin rawan jiki da nake yi, cup ɗin ya subuce ya faɗi Allah ya taimake ni unbreakable ne bai fashe ba na ɗuka in ɗauke ina kai hannuna da nufi ɗauke cup ɗin, na ji sautin muryar Mama tana faɗin "Wai waye a kitchen yake min ɓari da kaya?"
Duk da sai da gabana ya faɗi hakan bai hanani furta "Mama ni ce.
"Da kyau sarkin taɓargaza dama nasan wannan aiki sai ke to ki yi a hankali karki yi min ɓarna.
"Tou Mama.
Na faɗa da sauri, kamar jira nepa ke yi na fito daga kitchen suka dawo da wuta, tuni duhun da ke lulluɓe da tsakar gidan ya yaye zuwa wadatatce haske, Mama dake zaune kusa da Baba ta waro min idanuwanta tana min kallon tuhuma.
Na sadda kai ƙasa ina tafiya kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki.
  "Wai ke ina za ki je da dare nan da kika kinkimo uban tray ga wani dogon hijab da kika baza?"
Cikin sanyi murya na furta
  "Mama Bilal ne ya zo shi ne na ɗauko masa abin jiƙa maƙoshi.
Uwar harara ta fara galla min gami da daka min gigitatciyar tsawa ta fitar hankali "Ina ruwana da zuwansa yo.. Allah na tuba da zuwansa da rashinsa duk ɗaya ne a wurina, wato shine kike ta ɓar-ɓar da jiki kamar wacce wani hamshaƙin mashahurin attajiri wanda kuɗi suka gama zaunawa a jikinsa ya kawowa ziyara, nan kuwa ɗan zaman kashe wando ne.
Shiru nai ni ban fita ban kuma koma kitchen ba, yayin da furucinta ya haddasa min ɓaci rai har wani dishi-dishi nake gani.
  "Ba ma wannan ba faɗamin wa ya ba ki izini buɗe min freezer hadda ɗauko min kayan sana'a? Wato ga Mama mai kayan banza kou? shine don tsabage so ki ƙarya min jari sai da kika dubi na manya-manyan robobi ki ka ɗauko masa ya zuƙe ya yada empty roba to Allah yasa na gani sai a mayar min da kayana na gaji da haihuwar 'ya'ya rana tana kashewa, nace ki mayar min da kayana kin wani tsaya kina zararr idanuwa kamar mayye ya yi baƙo.
Rai ɓace Jeeddah ta haɗiye miyagun miyau kamar za ta fashe da kuka, ta sassauta muryarta ta ce "Don Allah Mama ki yi haƙuri na kai masa wallahi Bilal yana matuƙar son zobonki da kunu aya duk lokaci da na kai masa ya dinga santi kenan yana yabawa kwarewarki, har cewa yake duk faɗin unguwar nan ba wacce take kai ki iya sarrafa kunu aya da zobo.
    "Mtsss......yo ba dole ya yaba min ba kullum yana sintiri a ƙofar gidana yana ɗibar banza, ai idan bai yabamin ba sai Allah ya kwashe masa albarka.
Mama ta faɗa cike da jin haushi tana taɓe baki.
A wannan karo Baba ne ya karɓe zance saboda maganganunsu da na rediyonsa suna neman su raba mishi hankali gida biyu "Haba Fatee miyasa kike da sha'awar muzanta yarinyar nan?
"Ba wani muzanta ta da nake yi kawai da so nake ta fara yi wa kanta karatun ta natsu ina amfani baɗi ba rai.
"Ke Jeeddah wuce ki tafi in don ɗan wannan zobo ne zan biya ta ƙudinta.
Baba ya yi magana gami da kallon Mama yana murmushi saboda yasan ya kashe bakin faɗan nata.
Ina fita ta kalleshi with serious face ta ce "Gaskiya Alhaji na gaji da gafara sa banga ƙaho ba.  Zaman Jeeddah a gidanan ya fara isata kana dai sane da gidansu Jameel mu suke jira su ji ta bakinmu kaine ka dakatar dasu kuma a gefe ɗaya ga Haidar sai sintiri gidanan yake yi, ko ɗazu Hajiya Turai ta kirani so take in da hali wata mai kamawa ayi bikinsu kowa ya huta, tun da shi wannan maƙale mata ba abin aure ne dashi ba ɗan banza sai afki zuwa zance kamar ɗan achaba.
Mama ta ƙarasa magana tana cika da batsewa domin gaskiya haƙurinta ya fara ƙarewa gara ayi ta ta ƙare.
Ajiyar zuciya Baba ya yi gami da kashe rediyonsa, ya fuskanci Mama da kyau ya kuma gyara zamanshi cikin natsuwa da kwantar da murya ya ce "Na ji duk abinda kika faɗa Fatee kuma zancenki akwai ƙamshin gaskiya a ciki, sai dai gaskiya ba zan ɓoye miki ba al'amari nan yana neman ya zarce wa tunanina.
"Kamar ya Alhaji?
Tai sauri katse masa hanzari.
"Game da zance aure Jeeddah da Haidar mana.
"Haba Alhaji ko ka manta kaine mai cikakken iko akan Jeeddah, sai abinda ka zantar kuma dole tabi walau tana so ko bataso.
   "Na sani Fatee tabbas na isa da Jeeddah kuma ina da damar da zan aura mata koma waye balle Aliyu da ya kasance ɗan 'yar uwa ta, sai dai banaso nayi abinda zan dawo daga baya ina danasani akansa.
    "Ban fahimce ka ba Alhaji shin kana nufi za ka bar Jeeddah ta aure zauna gari banza, wanda bai da madogara?"
Saida Alhaji Usman maishadda ya ja fasali kafin ya ɗora da cewa "Shakka babu idan har ta nace sai shi banida wani zaɓi da ya wuce na aura mata shi.
"Cabdijam! Gaskiya Alhaji da sake wai an yiwa mai dame ɗaya sata, bana ko tantama gantalalle yaro nan kai ma bai barka a banza ba. Wannan ai toshewar basira ne haka kawai za ka ɗauke 'yar cikinka ba ma 'yar riƙo ba balle a ce ka yi mugunta ka aurawa marar aiki yi tsakani da Allah wannan shawarar taka ko kaɗan bata karɓu ba. Tou shikenan naji a tafi a haka ka amince ta aure zauna gari banza ɗin to shi kuma Haidar ya za ka yi dashi?"
   "Ya ko zan yi dashi da yawuce in zaunar dashi na bashi haƙuri haɗi da nasiha na nuna masa illar da ke tattare ga auren dole, musamman shi da bashida wadatatciyar lafiya.
   "Uhmm....Tou naji ka bashi haƙuri ka kuma yi masa nasiha abin tambaya anan shin kana gani gayamasa da za ka yi ya haƙura da Jeeddah hakan ba zai taɓa lafiyar tasa da kake ƙoƙarin karewa ba?" ina mai tabbatar maka Alhaji muddin Haidar ya ji wannan mummunan labari daga lokaci ba wai iya ciwon zuciyarsa zai tashi ba rankatakaf zuciyar tasa bomb za tayi ta tarwatse gaba ɗaya sai ka faɗin me ya za ka yi a wannan lokaci?"
   Shiru Alhaji Usman maishadda ya yi gami da shassafa dogon geminsa, yayin da jikinsa yai mugun sanyi maganganun Mama suka ratsa shi gani haka yasa ta ƙara ƙaimi wurin gani ta wanke masa wannan mugun tunani nasa.
   "Gaskiya ka sake tunani Alhaji ina amfani ka sayar da Akuyar ka ta dawo tana cin maka danga, da irin wannan aure da kake shiri yi ma Jeeddah gara babu sau ɗari dashi zai fi alkhairi mu ta ganinta a gabanmu da kwana biyu ta dawo mana zauranci a gida ka natsu Alhaji ka saita tunaninka wuri ɗaya.
A hankali Alhaji Usman ya sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya ya sani duk abinda Mama ta faɗa gaskiya ne sai dai shi ma yana da hujja da yasa bayaso yi wa Jeeddah auren dole, domin shi ganau ne ba jiyau ba iri masifar da 'yar amininsa Alhaji Muda ta faɗa a dalili aure dole a takaice ma yana ɗaya daga cikin mutane da suka ƙara karfafawa mahaifinta Alhaji Muda kwarin guiwa don ganin ya aura mata ɗan uwanta daga ƙarshe sai gashi wani babban al'amari marar daɗi ya faru, wanda ya zama silar mutuwar auren da rushewar zumunci Alhaji Muda da ɗan uwansa yanzu haka ko ga maciji basa yi 'yan uwan juna, uwa ɗaya uba ɗaya sun dawo maƙiyan juna to ina amfani iri wannan aure shiyasa har kawo yau ya kasa aje zuciyarsa wuri ɗaya balle ya yanke hukunci da yake gani shi ne daidai.
Gashi yana matuƙar jin kunya haɗi da takaici bayyana wa 'yar uwansa  Hajiya Turai ƙudirinsa ba zai iya aurawa ɗanta Haidar Jeeddah ba a dalili bataso shi, a kuma gefe ɗaya yana cike da alhini aura mata mutumin da ba shi da madogara sai yake gani tamkar ɓatan basira ne.
To amma kuma ya iya saboda Jeeddah ta kafe kai da fata lallai ita sai shi 'ya'ya zamani kenan ka haife su ba ka haifi halinsu ba.
   "Ya kayi shiru Alhaji ba kace komai ba?"
Maganar Mama ce ta dawo dashi daga duniyar dogon nazari da ya afka.
Sai da ya yi gyaran murya kamar mai shirin kiran Sallah kana ya buɗe bakinsa cikin rauni murya ya ce "Fatee inaso ki sa wa zuciyarki tawakali ki sani tun ran gini tun ran zane, hakazalika wani baya aure matar wani kamar dai yadda kika ce bahaushe yana faɗa matar mutum kabarinsa, shi aure da kike gani nufin ALLAH ne duk yadda muka kai da so haɗa aure tsakanin Haidar da Jeeddah idan ALLAH bai nufa ba mu.....
"Dakata Alhaji!
Mama tai hanzari katse shi ta hanyar ɗaga masa hannu, yayin da idanuwanta har sun fara sauya launi cikin tsanani ɓaci rai ta ci-gaba da faɗin "Kada ma ka soma wannan ɓatan basira shin Jeeddah ta fi ƙarfinmu ne da ba za mu iya tankwarata ta ba tabi abinda muke so ne, ko kuma tsoronta muke ji da za mu bi son ranta?"
  "Ba ko ɗaya Fatee kawai ina duba da matsalar da za ta iya faruwa idan mu ka ɗage sai mu yi mata dole. Ni fa tun daga kan Alhaji Muda na ɗauki darasi kuma gani ga wane ya ishe wane tsoron Allah.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

9...

Haidar Ka'oje ya danno hanci motarsa a harabar gidansu direct ya wuce parking lot yai parking kana fito daga cikin motar walking majestically ya nufi entrance. A ƙaramin parlour ya tarar da Hajiya Turai tasha kwalliya cikin wani tsadadden blue lace, mai ado pink flowers lace ɗin yai masifar karɓar fatar jikinta kasancewar Daddy yana gari shiyasa ta caɓa wannan uban ado.
"Assalamu alaikum!Barka da hutawa Mommy.
Haidar ya faɗa sa'ili da ya ƙaraso kana ya zauna kusa da Hajiya Turai.
  "Wa'alaikum salaam!
Barka dai Auta halan daga wajen Jeeddah kake?"
  "Uhmm... Daga can nake Mommy dama so nake naji ya ki ka yi da Daddy saboda gaskiya nagaji aure nakeso inaso na dinga jin ɗumin matata kusa da ni.
Dariya Hajiya Turai tayi gami da shafar sumar kansa "Daɗina da kai Aliyu rashin ta ido ji yadda ka baro zance nan ba kunya balle tsoron Allah.
    "Kunyar me zan ji mommy tun da kema kinsan nayi haƙuri har haƙurina yana daff da ƙarewa, Don Allah ki yi wani abu akai banaso na rasata.
   "Kwantar da hankalinka Auta nayi magana da Daddynka in-sha-Allah gobe-gobenan zai je ya sami Alhaji Usman maishadda a tsayar da lokaci bikinku da so samu ne next month ayi biki nan kowa ya huta.
    Cike da farin ciki marar misaltuwa Haidar ya rungume Hajiya Turai, yana zuba mata godiya kafin ya ce "Mommy ina cike da fargabar irin zaman da za mu yi ni da Jeeddah ko yau da naje gidansu ba ki ji irin kalaman tsanar da ta dinga furta min ba, abin ba ko daɗi ji wallahi mommy ina ƙaunar Jeeddah matuƙa amma duk lokaci da na tuna da bata sona sai naji wani iri da zan iya haƙura da ita mommy da na haƙura na barta ta auri wanda take so, sai dai kashhh.... soyayyata ta ri ga da tayi nisa a zuciyata cire ta ba abu bane mai sauƙi.
Yadda ya ƙarashe magana cikin rauni murya ya haddasawa Hajiya Turai tsananin tausayinsa, cikin so ta kwantar masa da hankali ta shiga faɗin "ka ma daina tunani rabuwa tsakaninku domin gidan bai ƙoshi ba wa za a kai dawa ba. Yadda ka dinga danko ƙaunarta In-sha-Allahu ba zai tafi a banza ba sai ka aureta kun haifa min kyawawan jikoki masu kama da kai.
Har Hajiya Turai ta dasa aya a zance ta Haidar yana murmusawa kana ya ce "shiyasa nake daɗa ƙaunarki mommyna saboda goyo min bayan da ƙara min kwari guiwa da kike yi Allah yabar mana ke Mommy ya ƙara miki lafiya da nisan kwana.
   "Amin ya Rabbi Autan Mommy na Jeeddah.
Sako suna Jeeddah kawai da Mommy tayi sai da Haidar Ka'oje ya ji tamkar ya some saboda daɗi, har imagination ya fara ya hango shi da Jeeddah akan gado manne da juna a matsayi ango da amarya wani irin shauƙi na ban mamaki yai masa ziyara bazata.
Yayin da Hajiya Turai ta ci-gaba da ƙarfafa mishi guiwa tana ƙara jaddada mishi duk runtsi sai ya aureta.
   Cikin salon tafiyata mai cike da yanga ta iso wajen da Bilal Shattima yai parking machine ɗinsa yana zaune akansa kunnensa manne da waya yana magana cikin low voice ya ba wa ƙofar fitowa baya shiyasa, bai ga fitowar ta ba. Tun kafin ta iso kusa dashi ta haɗe fuska don gani yana waya tana zuwa ta tsaya ta bayanshi ta baza kunnuwanta tana sauraren conversation ɗinsa "Ke ma Asiya kina da matsala miyasa....
    "Kam bala'in nan Bilal da wacce shegiya ce kake waya da ita?"
A matuƙar tsorace ya waiga bayanshi, don ko kusa bai san da tsayuwar ta ba, yana ƙoƙari kashe wayar tai wani uban tsalle ta fincike wayar daga hannunshi cike da zallar masifa da ruwan bala'i ta ɗora idanuwanta akan screen ɗin wayar, taga sunan Asiya ɓaro-ɓaro wacce bata kashe wayar ba, tana sauraren abinda Jeeddah take faɗi.
Ɗora wayar Jeeddah tai a kunneta ta shiga antyo manya-manyan ashar ta ɗorawa Asiya "Ke don b*ubanki don uwar ubanki me ya haɗa ki da mijina shegiya tsinaniya ɓakar karuwa mai bin mazan mutane?"
Ita kam Asiya tana ji irin wannan mugun zagi mai haɗe da ƙazafi tai maza tayi disconnected, Bilal ya zabura ya sauko daga kan machine duk ƙoƙarinsa na gani ya karɓe wayarshi daga hannunta abin ya ci turo don sai sake kira Asiya take yi ita kuma ta ƙi picking don bata san wacece ba duk da iya saninta Bilal Shattima bashida aure.
Tsabar takaici da ya lulluɓe Bilal Shattima sai kawai ya koma jikin bango Ya jingina gami da harɗe hannuwa yana kallon ikon Allah wanda yafi gaban mamaki.
   Lokaci da na ci karo da mace ce Bilal yake waya da ita gaba ɗaya idanuwana suka rufe ruff, sai wani ɗan uban zazzafan numfashi nake saukewa kamar wacce tai gasar tsaren gudu ta zo ta ɗaya, na tunƙare inda yake jingine yana aikin kallona sai zazzaga masifa nake tsabar kishi ya ciyo ni ko gabana bana gani sosai sai faɗin nake
   "Ni za ka yaudara Bilal ni za ka ciwa amana, to wallahi-tallahi ka yi kaɗan ba ka isa ba. Ka sani ba a ci amana ta a zauna lafiya, da ɗiyar gidan uban waye ka ke magana ka faɗa min wacece ita?"
Na ƙarasa magana cikin shouting, ina zazzare idanuwa kamar mai cutar taɓin hankali.
Sai da ya ƙare min kallo tun daga sama har ƙasa kafin ya ce "Wai ke me ke damunki ne uhmm ni shikenan banida hali nayi waya da mace koda kuwa 'yar uwa ta ce sai ya zama laifi wato na gane nufinki so kike tun kafin mu yi aure ki rabani da 'yan uwana kou?"
  "Dallah malam dakata! Karka sake ka rena min hankali da 'yar uwarka ce miyasa da nasake kiranta bata ɗaga ba?"
     "Ai ba za ta ɗaga ba saboda hali hauka da kika nuna mata, ko nine a matsayinta ba zan ɗaga ba, gara tun wuri ki gyara halinki domin ni ɗan dangi ne gaba da baya ba zan lamunci raba tsakanina dasu ba.
Bilal ya ƙarashe magana yana taɓe baki, kallo mai cike da mamaki nake masa wannan shi ake kira a dake ka a hanaka kuka. Wato danginsa sun fi ni yafiso farin cikinsu akan nawa. Ban jira mamaki da nake yi ya ƙarasa saki na ba nace
   "Bilal ni za ka kira da mahaukaciya to wallahi za ka hauka gani idonka so ma kake ka nuna min rashin muhimmancina a fili to bari ka ji muddin na gano wacece wannan shegiya tsinaniya da ku ke cin amanata na rantse da Allah sai nayi sanadi kwanciyarta kan gadon asibiti sai dai dangin naka da kake tutiya dasu su yi ƙuli-ƙuli kubra dani.
Na ƙarasa magana tare da rushewa da matsanancin kuka domin ni kaɗai nasan irin zafi da ƙuna da zuciyata take min har wani dishi-dishi nake gani wallahi ji nake tamkar ana babbaka min wuta.
   Jin abinda ta faɗa yasa ya baro inda yake ya riƙo hannunta, sai ƙoƙarin fizgewa take ya tabbata idan bai yi da gasken-gaske ba wuri fahimtar da ita ta fahimci babu abinda ke tsakaninsa da Asiya to  tabbas kuwa abinda ta faɗa za ta aikata shiyasa ya shiga magana cikin kwantar da murya "Haba Jeeddah don Allah ki dinga tsayawa ki tantance abu kafin ki yanke hukunci, wallahi tun daga ranar da na haɗu da ke kawo yau ɗinan ban taɓa kallo wata 'ya mace da suna so ba. Wannan da kika tarar muna waya da ita budurwa Abbas ce sun sami rashin jituwa shine ta kira ni tana neman nai musu sulhu. Idan kuma ba ki yarda ba ki kira Abbas ki tambaye shi. Ki yi tunani Jeeddah da ina da ra'ayi dating da wata mace da ban share shekara shidda ina Soyayya da ke kaɗai ba.
   Ajiyar zuciya na sauke jikina ya mutu mutuss! Na miƙa masa wayarshi, domin duk abinda ya faɗa gaskiya ne da yana da ra'ayi son wata da tuni ya yi hakan, nan take naji wata mashahuriyar kunya ta lulluɓe ni, na sadda kai ƙasa.
Bilal ya karɓi wayarshi don ta ƙara gasganta shi ya kira Abbas yasaka wayar a speaker ya shiga zayyanowa Abbas ƙararsa da Asiya ta kawo, har suka gama waya akan kunnenta ya sake kiran Asiya cikin sa'a tai picking sai da fara bata haƙuri akan katoɓarar da Jeeddah tai mata kana ya faɗa mata yadda ya yi da Abbas, yana kashe wayarshi ya tsare ta da idanuwanshi tai sauri kawar da kai gami da lumshe idanuwanta a hankali a kuma lokaci ɗaya ta sake buɗe su ta watsa su kan fuskar Bilal ta buɗe bakinta da taji ya yi mata mugun nauyi tamkar an datse mata shi da ƙaton padlock tace "Ka yi haƙuri love wallahi ban yi haka don naci zarafin ka ba, tsananin sonka ne da ya yi min yawa yasa duk lokaci da naga wata 'ya mace ta raɓe ka sai na ji duk na fita hayyacina.
    "Uhmm....ke dai na fahimci ba ki yarda dani ba da kin yarda dani sau nawa ina faɗa miki zuciyata taki ce ke kaɗai.
Turo baki tayi idanuwanta har sun canza launi "To bana ce ka yi haƙuri ba.
Ta faɗa cikin sanyi murya.
   "Ai haƙuri ya zama dole tun da ni na kawo kaina nace ina sonki duk abinda za ki yi min dole na danne zuciyata.
  "Ba ka haƙura ba kenan?"
Yanzu dai mu ajiye wannan zance a gefe mu yi maganar da ta kawo ni.
Bilal ya yi sauri katse ta don bai ga amfani kalmar haƙuri da take ta faman maimaita masa ba.
  Sai lokaci Jeeddah ta ji natsuwata ta fara dawowa jikinta, sai kuma ta tuna da tray ɗin da ke riƙe a hannunta da ta watsar dashi can ta hango shi ya yi nasa gefe robobin kunu aya da zobo suma sun yi nasu gefe wato watsar dasu tai batasan ma tayi ba.
   Wani irin kallo Mama take wa Alhaji Usman maishadda, tabbas idan nufinshi ya aurawa Jeeddah Bilal to kuwa za su artabo a gidanan ba kaɗan ba.
Domin ta ƙara tabbatar da gaskiyar zarginta sai ta ce "Ni fa Alhaji kwata-kwata ban fahimce ka ba, ka fito fili kai tsaye ka warware min manufarka sai wani kwana-kwana kake yi?"
"Fatee ba duk fahimta manufata ce ba ki yi ba kawai dai ganewa ne bakya so yi, sai dai hakan ba zai sa na bi ra'ayinki ba na dawo daga baya ina danasani ba saboda ku mata gajeren tunani ne daku.
   Hankali Mama ba ƙaramin tashi ya yi ba domin bata da buri da ya wuce Jeeddah ta aure Haidar idan har Alhaji Usman maishadda ya rusa mata wannan daɗaɗɗen buri nata ya gama da ita, dole tai gaggawa nemo mafita tun kafin wankin hula ya kaita dare.
Rai ɓace ta shiga faɗin "Amma Alhaji ba ka gani wannan abin da kake shirin aikatawa ba daidai bane ka duba duk tsawon shekaru da Haidar ya ɓata yana jiran Jeeddah kwatsam....rana ɗaya ka ce ya haƙura da ita ni fa a ganina gida bai ƙoshi ba, ba za a kai dawa ba na roƙe ka kada ka yi abinda zai taɓa zumuncinku da 'yar uwarka.
  Murmushi gefen baki Alhaji Usman maishadda ya yi ya sake gyaran zamanshi a karo na biyu ya fuskanci Mama da kyau ya ce "Fatee ba za ki taɓa fahimtar abinda nake hangowa a auren dole ba saboda kina ƙaunar Haidar matuƙa shiyasa idanuwanki suka rufe kika kasa hango matsalar da nake guje mana, shi kanshi zumunci da kike tunani idan har aure nan bai yi daɗi ba da matuƙar wahala bai rushe ba. Kina gani Aliyu zai ta zuba idanu Jeeddah tana mishi wulaƙanci da cin kashi zuciya bata da ƙashi yau da gobe bata bar komai ba, a maimakon haɗa zumunci sai ki ga an rushe shi musamman hali Jeeddah da kika sani na taurin kai da kafiya gara mu barta ta aure wanda take so ina matukar jin tsoro kada abinda ya faru da 'yar Alhaji Muda ya faru akan tawa 'ya saboda haka na tsayar da matsaya ɗaya shine Jeeddah za ta aure wanda take so ba wanda muke so ba, na gama magana kuma babu ruwanki da Turai wannan tsakaninmu ne saboda banaso ƙanana maganganu don ku mata abin magana baya maku kaɗan.
   "Cabdijam! To wallahi Alhaji ka biyo hanyar da ba za ta taɓa ɓullewa da kai ba, akan wane dalili za ka ɗauki 'yata ka ba wa mutumin da bashi da aiki yi al'hali ga mai aikin yi a hannu wannan ai ɓatatciyar dabara ce a matsayina na wacce tayi kaya cikinta nasha ɓakar wahala naƙudarta, na dinga faɗi tashi akan tarbiyyarta har ta kawo muzalin aure nace ban amince da ta aure Bilal ba.
Daga haka Mama ta tashi a mugun fusace ta shige parlournta duk kira da Baba yake mata bata amsa ba, Khairat da ke zaune tana saurarensu duk sai ta ji ranta ya ɓaci tun daga ƙurciyarta har tai wayau bata taɓa gani Baba da Mama suna musayar yawu ba, kasancewar Mama mace ce mai matuƙar haƙuri da kawaici duk abinda Baba yace ya zauna ko da kuwa bai mata daɗi ba. Ba za ta taɓa nunawa ba amma tun da yau ta fito fili ƙiri-ƙiri ta nuna ƙin amincewarta ya kamata shima yai mata uzuri.
   Juyawa Khairat tayi jikinta a sanyaye ta shiga parlourn Mama ta tarar bata ciki kai tsaye ta nufi bedroom ɗinta, ta tura ƙofa bakinta ɗauke da sallama Mama dake zaune a gefen gado ta rafka tagumi ta amsa mata cikin sanyi murya kusa da ita Khairat ta zauna kana ta cire mata tagumin cikin kwantar da murya ta ce "tun daga yarinta ta har zuwa girmana ban taɓa gani Baba ya faɗa kin musanta ba Mama, koda yaushe kina bi ra'ayinsa koda kuwa hukunci da ya yanke bai miki daɗi ba. Mama kina da haƙuri tare da hangen nesa kada ki bari shaidan ya yi tasiri akanki ya wargaza muku kyakkyawar zamantakewarku da ku ka gina tun kafin zuwan  Jeeddah duniya, Baba yana da nasa dalili haɗe da hujjar da yasa ya kafe lallai ba zai yi wa Jeeddah dole ba hakazalika kema kina da naki dalillai da hujja, ita kanta uwar gayya tana da nata hujja da dalillai da yasa ta zaɓi Bilal Shattima duk da ta kwana da sani bashi da aiki ko sana'a da ya dogara da ita. Mama sha'ani na aure zaɓi Allah ake nema ba zaɓin rai ba ki yi haƙuri ki bi abinda Baba ya ce kada silar aure Jeeddah ya kawo ɓaraka a tsakaninku. Ki bi ta da addu'ar fatar alkhairi kuma ni sai nake gani Mama da kin fidda hannunki cikin lamari nan kamar yadda Baba ya buƙata ki kyaleshi da Mommy Turai ai sun fi kusa.
   Kyakkyawar ajiyar zuciya Mama ta sauke ta jinjina wa Khairat yadda ta tsara maganganu iri wannan cikin hikima da basira, har ga Allah so tai duk inda zance nan zai kai su da Baba sai dai ya kai su don ba za ta taɓa amincewa da iri wannan aure da yake shirin yi wa Jeeddah ba musanman yadda tasan Haidar yana matuƙar ƙaunar Jeeddah amma yanzu da Khairat ta tunatar da ita abinda ɓaci rai yasa ta manta sai kuma ta ji jikinta ya yi sanyi cikin mutuwar jiki ta ce "Shikenan Khairat Allah yasa shi yafi zama alkhairi agareta shi kuma Haidar Allah ya musaya mishi da madadin wacce ta fita. Ke kuma Allah ya yi miki albarka yasa ki gama da duniya lafiya Khairat ke 'ya ce tagari wacce samun irin ki sai an tona ina alfahari dake nagode da kika tunatar dani.
  Murmushin farin ciki Khairat tayi gami da furta "Nima Ina alfahari dake Mama domin duk abinda na zama tarbiyyarkice na barki lafiya.
Khairat ta ƙarasa magana tare da miƙewa ta nufi ƙofar fita har ta fice daga ɗakin Mama tana zuba mata albarka.
Khairat tana kwance Jeeddah ta shigo, ta bi ta da harara wani mugun haushinta take ji duk ta dalilinta ne yau iyayensu suka dinga musayar yawu. Cike da takaicinta  ta tashi zaune gami da zubo ƙafafuwan ta ƙasa rai ɓace ta ce "Ke kam Jeeddah kin zama haddasana kin zama silar haddasa fitina tsakani Baba da Mama sai ki zuba ruwa a ƙasa ki sha tun da dama haka kike so.
A fusace Jeeddah ta juyo dama tana ƙoƙari sauya kayan jikinta zuwa na bacci, saboda haka ta fasa cikin masifa ta ce "Khairat kanki ɗaya kuwa wannan wacce iri kalma ce kike jifana da ita ta ya na zama silar haddasa fitina tsakani Baba da Mama?"
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI...!*
        _{Sabon salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

010...

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

Naceba🙋‍♀️
Kina bukatan jikinki yazama so fresh ba kwarzane ko daya ballantana kuraje ko tabo, sunburn,acne, ko knuckles? Kije kigwada products na mg's insha Allah zakiga ynd fatarki zedawo fiye da tsammaninki zakigyara jikinki naturally batare da kinbata fatarki ba jikinki yayi fresh kiyi smooth kizama kalar Madara kirar models kiringa walwali kina haskawa duk inda kikayi😍
Kidena kokonto cewa kingwada baki Dace ba insha Allah kijaraba products dinsu bi'iznillah zakiji dadinshi🙏 kayansu akwai kamshi especially sabulun kamshin yakama jikinki ko kindade da wanka jikinki zaidinga fidda ni'imtaccen kamshi bayinki ma zakiji kamshin dazai Kama😍sunada kit special domin amare Wanda indai kinyi using kit dinnan Baki bukatar kikara Kai kudinki gurin dilke domin ainihin yanda fatarki zehaska yagoge kidinga shining abun sewanda yagani😍

Mai bukatar kayan mg's chat:08062991549,07046881166,07067210195
Call:08064532391
Hausawa nacewa adade anayi sai gaskiya Kuma siyan nagari maida kudi gida🤝
💯 tested nd trusted
Natural/organic🥰
Akwai discount a medium kit👇👇
Medium kit
Normal price 17k Now 15k
Babban kit 20k
Now 18k

Valid for only 2days.
  

Cikin tsiwa Khairat ta ce "Ba kin fiffita son zuciyarki fiye da zaɓi da iyayenki suka yi miki ba?" Ai sai ki zuba ruwa a ƙasa kisha don kuwa Baba ya aminta da aurenki da Bilal Shattima, amma ki sani Mama bata farin ciki domin Haidar take so ki aura saidai bata da yadda za ta yi tun da Baba ya ri ga da ya amince.
   "Al-hamdulillah!
Jeeddah ta furta very excited yayin da fuskarta ta cika da annuri sai uban murmushi take zabgawa, kallo takaici Khairat tai mata ta ja tsaki domin ta fahimci lamarinta hadda rashin sani ciwo kai yo....ban da rashin sani ciwo kai an  gayamiki mahaifiyarki bata farin ciki da aurenki amma tsabar sakarci kina hamdalla. "Tsakani da Allah duk wanda ya ce Jeeddah tana da cikakken hankali haƙiƙani gaskiya sai in tsoronta yake ji.
Khairat ta faɗa a cikin zuciyarta.
   "Tirƙashi! Amma gaskiya Jeeddah kina da taɓi hankali kou?"
Khairat ta tambaya saboda gaskiya ta kasa ɓoye mamakinta gara ta bayyana shi a fili da tai ta ƙunshewa cikin zuciyarta.
   "A'a kware ce akaina {asibitin mahaukata}.
Jeeddah tai magana gami da gallawa Khairat harara.
  "Ba shakka biri ya yi kama da mutum ba sai kin faɗa ba duk mutum mai cikakken hankali da tunani ba zai aikata  kwatankwacin abinda ke ɗinan kika aikata ba. Infact na kasa yarda Jeeddah wai farin ciki kike yi za ki aure zauna gari banza ɗan zaman kashe wando.
Khairat ta faɗa tana taɓe baki.
   Sosai furucin Khairat ya ɓata min rai na fahimce burinta a koda yaushe ta gani cikin baƙi ciki, tana ɗaya daga cikin mutane da ke adawar aurena da Bilal Shattima, ni kuma ko a jikina muddin dai zan kasancewa da zaɓin raina duk wanda zai shiga ɓacin rai ruwansa. Saboda haka na kalleta cikin rashin damuwa na ce "Duk abinda za ki faɗa ba damuwa ta bace dama muradin maji hajji sallah, burina na kasance da Bilal Shattima a ƙarƙashin inuwar aure to tun da Baba ya amince ita ma Mama da sannu za ta yi na'am dashi.
   Girgiza kai Khairat tayi yayin da takaicin Jeeddah ya ƙara ɗarsuwa a ranta bata taɓa gani mutum mai tosasshiyar ƙwaƙwalwa irinta ba amma ba komai a jure zuwa rafi da tulu wata rana zai fashe.
Khairat ta koma ta kwanta tana da yaƙini ko za ta kwana tana nunawa Jeeddah illar da ke tattare da iri wannan aure ba za ta taɓa saurarenta ba. Saboda ta riga da tasawa ranta Bilal Shattima shi kaɗai ne zai zauna da ita kaɗai ba tare da yai mata kishiya ba
Saboda haka Khairat ta shafawa kanta lafiya ta koma ta kwanta.
Ina gani Khairat ta kwanta har da su jan duvet na ja tsaki ƙasa ƙasa na cire kayan jikina na maye gurbinsu da na bacci, daga ni har ita kwana mu ka yi muna jin haushin juna.
Ko da safe ba wacce ta kula wata har suka yi shirin fita aiki, Khairat ta riga ta ficewa a parlourn Baba ta tadda ta zaune kusa da Mama.
Kaina a ƙasa na shigo tare da sallama Baba ne kaɗai ya amsa min, na sake gaida su nan ma shi kaɗai ya amsa min da fara'a saɓani Mama da ta amsa min adaƙile. Kusa da Baba na zauna saboda banga fuska ba a wurin Mama ba sai hira suke yi ƙasa, ƙasa ita da Khairat.
   Baba ya tattaro natsuwarsa gaba ɗaya akaina cikin sanyaya murya ya fara magana "Jeeddah jiya nida Mamanku mu yi magana akan zance aurenku, tsawon lokaci nan da nai shiru ban yi magana ba na zuba miki ido ne a dalili ina tunani ko za ki canza ra'ayinki, ki amince da aure ɗan uwanki sai dai kashhh...haƙata ta kasa cimma ruwa bani da wani zaɓi face na amince da naki zaɓi duk nasan iri matsalar dake tattare da zaɓin naki.
Baba ya ɗan numfasa gami da kallon Jeeddah so yake ya karanci yanayin ta yayin da Jeeddah ta sadda kai ƙasa tana wasa da babban yatsar ƙafarta.
   Kana ya ci-gaba da faɗin "shin kin amince za ki aure Bilal duk da bashida wata kwakwarar sana'a?"
   Ɗagowa Jeeddah tayi gami da satar kallon Mama da Khairat a lokaci ɗaya suka galla mata uwar harara sai da gabanta ya faɗi tai sauri maida kanta ƙasa, gani shiru nata ya yi yawa yasa Baba cewa "Ke nake saurare Jeeddah shin kin amince da Bilal ɗin ko kuma kin yarda za ki aure ɗan uwanki?"
Haba ji ya ambata mata Haidar tai sauri ɗagowa cikin sarƙewar lafazi ta ce "A'a Baba abar zance ya Haidar ɗinan na amince da Bilal.
Baba ya sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya dama yasan da matuƙar wahala ta amince da aure Haidar ya tambaya ne kawai saboda Mama ta ƙara tabbatar da ba laifinsa bane shima ya goye bayanta ne a dalili ba shi ke mata zaman aure ba gara a aura mata wanda take so shine kwanciyar hankalinsu gaba ɗaya.
   "Shikenan dama so nake na ƙara jin ta bakinki tun da kin aminta sai ki ce dashi ya turo da magabatansa banaso a  ɗauki dogon lokaci gara na aurar daku kowa ya huta. Amma da son samu ne ki shawarce shi ya nemi sana'ar hannu komai ƙanƙantarta yafi masa zama haka nan ke kuma tun da kin kafe lallai sai shi dole ki dinga tallafa masa da salary ki tun da ba abinda kike yi dasu nima in-sha-Allah zan taimaka da abinda bai fi ƙarfina ba. Allah ya sanya alkhairi ya ƙara haɗa kanku Allah  yasa mutuwa ce kaɗai za ta raba ku.
    "Amin Baba! Nagode Allah yasaka maka da gidan aljanna firdausi.
Jeeddah ta faɗa cike da farin ciki tana zabga fara'a kamar wacce aka yi ma bushara da gidan aljanna.
Takaicinta ya lulluɓe Mama da Khairat kasa haƙuri Khairat tayi saboda mugun takaici Jeeddah da take ji ta miƙe tare da yi wa Baba da Mama sallama ta fice abinta ba tare da ta sake ko kallon gun da Jeeddah take zaune ba.
Cikin karya murya  Jeeddah ta shiga sharowa Baba ƙarya ta hanyar cewa "Baba ai kwana nan zai fara aiki a shagon siminti na yayansa Faruk.
   "Madallah hakan ma ya yi Allah yasa ya fara a sa'a.
Baba ya faɗa fuskarshi cike da fara'a dama shi fargabarsa ɗaya rashin aikin Bilal to tun da ya sami sana'a, shikenan bashida wata damuwarsa ta ragu.
   Zuciyata fal farin ciki na miƙe tare da yi wa Baba da Mama sallama Baba ne kaɗai ya amsa min yayin da Mama ta bi ni da kallon takaici, ina fitowa wajen gidanmu jikina na rawa nai zipping handbag ɗina na ciro wayata cikin zumuɗi na yi dialling number Bilal Shattima.
Bilal Shattima dake kwance akan gadonsa ya yi rashe-rashe yana baccinsa na asara domin sai ranar ta fito hatse-hatse yake tashi, can cikin baccinsa mai daɗi ya ji ringing ɗin wayarsa yana ratsa dodon kunnensa kasancewar special ringing tone ya sakawa Jeeddah yasa ya gano ita ce mai kiran nashi da ba don ita bace koma waye ba zai katse baccinsa mai daɗi ya saurare shi ba, idanuwanshi a lumshe ya shiga lalluɓe inda wayar take har yai nasarar ɗora hannunshi akanta ya ɗan ware idanuwanshi kaɗan yai receiving tare da karawa a kunne cikin murya wadda bacci bai gama sakinsa ba ya furta "Hello.. Love!
"Good morning Love!
Jeeddah ta furta cike da farin ciki.
  "Morning Love ya aka yi ne?"
"Love do you know how happy I'm?
    Murmushi ya yi mai ƙaramin sauti kafin ya furta "Huhmm...tell me the reason please kinsan banaso jan rai.
   Sai da Jeeddah ta kai dubanta gefe da gefen hanya taga babu mutane sosai, tana gudun kada wani ya ji ta kana ta ci-gaba da faɗin "Albishirinka Love!
"Huhmm goro amma Please ki hanzarta faɗa min ko menene wallahi bacci nake yi kiranki ne ya tashe ne, kisan kuma idan ban yi bacci nan ba headache ya ta damuna.
Bata damu da korafinsa ba dama tasan hali kayanta da shegen bacci tsiya, cikin zumuɗi ta ce
"Nan da ɗan wani lokaci biyu za su zama ɗaya, wannan bacci da kake yi kai kaɗai zan dinga tayaka kana ji saukar numfashina ina jin naka a takaice dai Baba ya amince da aurenmu har ya umurce ni da na faɗa maka ka turo magabatanka, a sa mana rana Love ina cikin tsanani farin ciki burinmu ya kusa cika.
Ta ƙarasa magana very excitement.
Bilal Shattima dake kwance baisan lokaci da ya miƙe zaune ba, nan take ya wartsake daga raguwar bacci da bai ƙarasa sakinsa ba saboda ko kusan bai yi tsammanin Baban Jeeddah zai aminta da ƙudirinta ba. Lallai tashi ta same shi jego da kara.
   "Love ba ka yi farin ciki bane naga ka yi shiru ko duk tsabar daɗi ne ya ƙumeka ka kasa magana?"
"Huhmm...Love I'm very speechless saboda farin ciki na rasa me zan faɗa, lallai safiyar yau ta kafa tarihi a rayuwarmu.
Ya ƙarashe magana yana dariya.
   "Haka ne Love abinda muka daɗe muna zaman jira sai gashi ya zo mana ciki sauƙi, saboda haka kada ka sa sanya ka gaggauta turowa Don Allah. Wallahi I'm eager to have you as my wedded husband
   "in-sha-Allah Love ba zan yi wasa da wannan opportunity ba.
Daga haka fira ta tsinke a tsakaninsu sai da ta iso gate ɗin makaranta sannan suka yi sallama da alƙawari zai zo ɗaukar ta.
Tun da asuba da Haidar ya dawo daga masallaci ya kasa komawa bacci yana gani ƙarfe 9 tayi ya  shiga shiri saboda Daddy ya gayamasa da ƙarfe goma za su tafi gidan su Jeeddah, bayaso ya ɓata lokaci shiyasa ya shirya tsaf cikin manyan kaya na tsadaddiyar farar shadda. Ƙamshinsa ya gauraye ko'ina, ƙarfe 9:15am yai wa katafare parlourn Daddy tsinke fuskarshi cike da fara'a da ya kasa ɓoyeta yai sallama Daddy da ke zaune akan three sitter yana duba newspaper ya ɗago da mugun sauri ya sauke ganinsa akan fuskar Haidar baisan sanda ya tintsire da dariya ba "Gadanga ƙusar yaƙi yau kaine sanye da manyan kaya lallai ta tabbata aure kake so.
   Cikin sigar shagwaɓa Haidar ya ƙaraso wajen Daddy yana ya mutsa fuska "Wai Daddy kana nufi ba ka shirya ba?"
  "Ba ga zahiri nan ka gani ba gani sanye da jallabiya in tambaye ka mana wai yaushe gari ma ya waye Aliyu da har za mu fita neman aure?"
  "Daddy da ƙarfe goma ka ce za mu tafi gashi yanzu har 9:15am don Allah Daddy ka tashi kayi wanka.
Haidar ya yi magana gami da wafce newspaper da ke hannu Daddy ya jefa ta akan kujera da ke nesa da Daddy.
   'yar dariya Daddy ya ƙara yi tare da furta "Amma gaskiya Aliyu ka cika gaggawa da yawa dawo min maza da newspaper na ba yanzu za mu tafi ba sai 10 o'clock on dot kuma dole ka jira zuwan Alhaji Ahmed da Alhaji Bashir kasan dai ba daga ni sai kai za mu je neman maka aure ba?"
   "Mommy... mommy!
Haidar ya shiga kwallawa Hajiya Turai kira da sauri ta fito daga bedroom ɗin Daddy ta shirya cikin gown na sequence atamfa sai walwali da ɗaukar ido take don ba ƙaramin kyau atamfar tai mata ba. Jikinta sai fidda ƙamshi tsadaddun turaruka yake ga wuya da hannuwanta sun sha ado na Dubai gold.
    "Ya aka yi ne Auta iri wannan kira haka har ina?"
Hajiya Turai ta faɗa sa'ili da ta ƙaraso ta zauna kusa da Daddy.
"Mommy please karki zauna ki tashi ki ɗauko mayafinki, saboda kema dake za a je kuma dan Allah ki yi ma Daddy magana ya tashi ya yi wanka wallahi lokaci yana ƙurewa kuma Baba da ƙarfe goma yake fita kasuwa gara mu yi sauri kada mu tarar da ya fita.
Haidar ya ƙarashe magana cikin magiya da kwantar da murya ba ƙaramin dariya ya ba mommy da Daddy ba a tare suka shiga kyakyatawa daga bisani Daddy ya tsagaita da dariya ya kalleshi still da raguwar dariya akan fuskarshi ya ce "kwantar da hankalinka sarki zumuɗi tuni nayi wanka kaya kawai zan canza.
   Da sauri Haidar ya riƙo hannun Daddy ya shiga jan shi "Tashi mu je Daddy yau da kaina zan zaɓa maka kayan da za ka saka kasan yau special day ne kwalliya sosai za ka yi, ka fito uban ango sakk.
Miƙewa Daddy ya yi yana dariya shirmen Haidar.
Ƙarfe goma daidai suka isa gidansu Jeeddah tare da tawagar abokan Daddy hatta da mommy sai da Haidar ya taso ƙeyarta gaba, Mama na ganinsu sai da gabanta ya faɗi ko kaɗan bataso faruwar hakan ba. Sai dai bata da yanda za ta yi saboda mai gayya mai aiki ya gama zantar da hukunci. Jikinta a mace ta yi ma Mommy iso zuwa cikin parlournta.
Bayan 'yan gaishe-gaishe da ya shiga tsakaninsu kana Alhaji Bashir ya zarce da faɗar dalilin zuwan nasu "Alhaji Usman sai ku ganmu da sassafe nan ba sanarwa wallahi ɗanka ne ya fitine mu akan lallai sai mun zo a tsayar da lokaci bikinsu.
   Har Alhaji Bashir ya dasa aya a zancensa Baba yana kallonshi gami da shafa geminshi, can dai ya ga shirunsa ba shi bane mafita ba gara ya fito fili ya faɗa musu farar gaskiya.
Kafin ya kai da yin magana Alhaji Abubakar Ka'oje ya cafe ta hanyar cewa "Wallahi Alhaji Usman ɗa nan naka ba ƙaramin azalzalata ya dinga yi ba dole na taso su Alhaji Bashir nace gara dai ayita ta ƙare jiranan ya isa haka ka bashi matarsa mu huta da fitinarsa.
Alhaji Abubakar Ka'oje ya ƙarashe magana yana 'yar dariya.
"Ai Aliyu yana da gaskiya Alhaji Abubakar sauƙin mu ɗaya abin ya zo da na gida.
Cewar Alhaji Ahmed shima yana dariya gami da kallon Aliyu da ya sadda kai ƙasa yana ta faman zabga murmushi.
Ajiyar zuciya Alhaji Usman maishadda ya sauke kana ya gyara zama cikin muryarsa mai cike da dattako ya ce
  "Da ba ku wahalar da kanku ku ka zo ba da ni da kaina zan zo har gida na same ka Alhaji Abubakar domin maganar da kasani a baya a yanzu ta canza zani, Jeeddah dai tayi tsaye, tsayin daka ta tuma tara ta ce Bilal take so ba yadda ban yi da ita ba akan ta amince da ɗan uwanta amma ta ƙi. Wallahi duk tsawon lokaci nan da ka ga ina ta noke-noke don kawai su daidaita tsakaninsu ne ita da Aliyu, to kuma hakan ya gagara samuwa shiyasa na yanke hukunci a barta ta aure wanda take so gudun kada mu yi abinda za mu dawo daga baya muna danasani har ya zo ya taɓa mana zumunci, shi sha'ani aure da kake gani Alhaji Abubakar...
   "Dakata dan Allah Alhaji Usman!
Daddy ya katse shi cikin fusata kana ya zarce da faɗin
"Idan za ka yi magana ka tafi kaitsaye domin ni Kwata-kwata ban gane inda wannan dogon sarhin naka ya dosa ba, sai kwana-kwana kake yi.
Yadda Daddy ya yi magana kaɗai zai tabbatar maka da ransa ya fara ɓaci. Yayin da Alhaji Usman maishadda ko a jikinsa domin ya tabbata sai irin haka ta faru.
Lokaci da Haidar Ka'oje ya ji bayani da Baba ya fara take jikinsa ya ɗauki rawa, hankalinsa yai mugun tashi shikenan ya rasa Jeeddah, tun da ya ji Baba ya fara wannan dogon bayani da wuya ya aura masa ita wani iri tausayinsa kanshi ya lulluɓe shi. Ya tabbata sai ya sha baƙar wahala kafin ya iya yakice sonta a zuciyarsa.
Baba ya kalli Daddy cikin natsuwa da tausassa lafazi ya ce "Dan Allah Alhaji ka yi haƙuri nasan ba a kyauta muku ba musanman idan aka yi duba da tsawon lokaci da Aliyu ya ɗauka yana jiran Jeeddah, sai dai ba zan iya mata dole ba saboda haka ina mai ba ku haƙuri banaso ayi abinda zai zo ya taɓa zumunci.
    "Innalillahi wa'inna illahim raji'un.... innalillahi wa'inna illahim raji'un!
Haidar ya shiga furtawa yana sake maimaita wa yayin da hannunshi yake dafe da saitin zuciyarsa, idanuwanshi suka firfito jijiyoyin kanshi suka yi burɗu-burɗu gwani ban tausayi.
  "Ka gani kou Alhaji Usman ka ga hali da ka jefa ɗana kou?"
Alhaji Abubakar Ka'oje ya faɗa a fusace gami da miƙewa ya nufi wajen Haidar ya zauna akan hannu kujerar da Haidar ɗin yake zaune akai ya rungumo kafaɗarsa yana bubbuga gadon bayansa gami da jijjiga shi, kafin ya kalli gefen da Alhaji Usman maishadda yake ya shiga zazzaga masifa da tijara dama gashi mafaɗaci gaske "Amma wallahi Alhaji Usman ka bani mamaki ashe bare yafi ɗan gida infact yaushe aka haifi Jeeddah da har za ka kasa tankwarata ta bi abinda muke so. To wallahi idan wani ya abu ya sami yarona ba zan taɓa yafe maka kai da 'yarka ba saboda haka ka yi addu'a kada wani abu ya same shi.
   Daddy ya ƙarashe magana yana ɗaga harshe Mama da Mommy da ke parlourn Mama suka jiyo hayaniya, dama Mama tana cikin ba wa Mommy mummuna labari da gudu suka shigo parlourn yayin da Alhaji Usman maishadda ya lafe jikin kujera ya zubawa Alhaji Abubakar Ka'oje idanuwa, saboda yasan su aka yi wa laifi a yadda ya hau ɗinan kalaman haƙuri ba za su yi tasiri akansa ba gara ya kyaleshi ya faɗi iya abinda ke ransa. Sosai Alhaji Abubakar Ka'oje ya harzuƙa sai faɗar maganganu marasa daɗi yake yi Hajiya Turai ta fashe da kuka tana faɗin "Saboda Allah Yaya kana gani ka yi mana adalci kenan?" kana sane da yadda Haidar ya kwallafa ranshi akan Jeeddah, ka kuma san yanayi ciwonsa ba a son ɓaci ransa amma duk da haka ka yanke hukunci haramta mishi aurenta.
   Kafin Alhaji Usman maishadda ya yi magana Daddy ya cafe da cewa "Daina ɓata yawun bakinki Hauwa duk abinda ya yi da saninsa ya kuma yi ne domin ya ƙuntata mana kuma ki sani Hauwa na raga masa ne don kasantuwar shi ɗan uwanki da wallahi-tallahi sai na nuna masa ba a yi min haka a zauna lafiya.
Gani yadda Alhaji Abubakar Ka'oje ya harzuƙa yasa Alhaji Ahmed da Alhaji Bashir suka shiga bashi haƙuri suna kuma ɗorawa Alhaji Usman maishadda laifi, domin su a ganinsu babu dalili ko wata hujja da zai sa ya ce ba zai yi wa 'yarsa aure dole ba. Mata nawa aka yi wa dole kuma suka zauna sai 'yarsa ce zai ce ba zai mata dole ba sai kace tafi sauran mata.
    Haidar da ke dafe da zuciyarsa ya ciro idanuwanshi ya bi mutane dake parlourn da kallo Kowane da irin ɓaci rai da ya hango tattare akan fuskokinsu more especially Daddynshi.[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥 ZAZZAFAN KISHI...!*
       _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

011...

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

Naceba🙋‍♀️
Kina bukatan jikinki yazama so fresh ba kwarzane ko daya ballantana kuraje ko tabo, sunburn,acne, ko knuckles? Kije kigwada products na mg's insha Allah zakiga ynd fatarki zedawo fiye da tsammaninki zakigyara jikinki naturally batare da kinbata fatarki ba jikinki yayi fresh kiyi smooth kizama kalar Madara kirar models kiringa walwali kina haskawa duk inda kikayi😍
Kidena kokonto cewa kingwada baki Dace ba insha Allah kijaraba products dinsu bi'iznillah zakiji dadinshi🙏 kayansu akwai kamshi especially sabulun kamshin yakama jikinki ko kindade da wanka jikinki zaidinga fidda ni'imtaccen kamshi bayinki ma zakiji kamshin dazai Kama😍sunada kit special domin amare Wanda indai kinyi using kit dinnan Baki bukatar kikara Kai kudinki gurin dilke domin ainihin yanda fatarki zehaska yagoge kidinga shining abun sewanda yagani😍

Mai bukatar kayan mg's chat:08062991549,07046881166,07067210195
Call:08064532391
Hausawa nacewa adade anayi sai gaskiya Kuma siyan nagari maida kudi gida🤝
💯 tested nd trusted
Natural/organic🥰
Akwai discount a medium kit

Medium kit
Normal price 17k
Now 15k

Babban kit 20k
Now 18k

Valid for only 2days



Yadda yaga Daddy yana huci idan har bai yi gaggawa taka mishi birki ba, to kuwa gaba ɗaya komai za ƙara dagule wa, dauriya yasa ta hanyar faɗin "Daddy Dan Allah ka yi shiru ya isa haka koda Baba ya tilastawa Jeeddah ta aureni kasani bai isa ya tilasta mata ta so ni ba. Daddy duk aure da za a yi shi babu soyayya haƙiƙa ɓaci rai ne zai biyo baya a hali yanzu koda Baba ya amince da aura min ita a dole ni ba zan aure ta ba domin ko na aureta gangar jikinta kawai na aura zuciyarta na can ga wani. Saboda haka daga yau mai kama da rana ta yau na haƙura da Jeeddah kuma duk wani mai ƙaunata kada ya ƙunlaceta ko kuma Baba kawai inaso ku tayani da addu'a Allah ya cire min sonta a zuciya.
Ya ƙarashe magana cikin rauni murya da karaya zuciya ga kuma idanuwanshi da suka ciciko da hawaye, duk wanda ke ciki parlour sai da jikinshi yai sanyi babu kamar Baba da yake ji a can ƙasan zuciyarshi kamar bai yi wa Haidar adalci ba, wani ɓangare na zuciyarsa kuma ya ke gani hakan da ka yi shine daidai.
  A fusace Daddy ya kama hannu Haidar ya ɗaga shi ya tashi kana ya juya gefen da su Alhaji Bashir suke ya ce "Ku tashi mu tafi Alhaji Bashir don banga amfani ci-gaba zaman mu a parlour nan ba.
   Yana gama magana ya ja Haidar suka nufi ƙofar fita Alhaji Bashir da Alhaji Ahmed suka mara masa baya yayin da Alhaji Usman maishadda bai yi yunkurin hana su tafiya ba. Saboda yasan ko ya tsayar da su ba lallai bane su tsaya su  fahimci juna ba. Hajiya Turai ta kalli Baba tana kuka ta ce "Haba Yaya yanzu shikenan ka hanawa Haidar auren Jeeddah kana gani hakan da ka yi ka kyauta kenan?"
"Ki yi haƙuri Hauwa domin duk abinda zan faɗa a yanzu ba za ki fahimta ba saboda ranki a ɓace yake, idan kun huce ke da mijinki zan zo har gida na same ku.
   "Huhmm...ni kan ban taɓa gani idan gida bai ƙoshi ba aka kai dawa, ba amma ba komai Allah na nan.
Daga haka ta juya ta nufi ƙofar fita tana sharar hawaye da gefen mayafinta. Mama ta biyo ta har gate tana ƙara bata haƙuri.
Kasa komawa bacci Bilal Shattima ya yi yasaka farar jallabiya ya nufi ɓangaren Hajja, zaune a parlour ya tarar da ita tana jan casbi ransa a jagule ya zauna kusa da ita yana so ya faɗa mata abinda ya kawo shi sai dai ya rasa ta ina zai fara, sai nushin tafin hannunshi yake yi gami fesar da iska daga bakinsa. Hajja ta kalli shi gami da faɗin "Ya aka yi ne Bilalu naga sai faman nushin tafin hannu ka ke yi da matsala ne?"
"Huhmm... matsaloli za ki ce Hajja domin ba guda ɗaya bace.
Bilal ya faɗa tamkar zai fashe da kuka duk ya dawo wani abin tausayi.
  "Tou.....ina jinka faɗa min menene matsalolin naka Allah dai yasa ba zance interview ɗin ne aka soke ba?"
   Sai da ya sauke ƙarfaffiyar ajiyar zuciya kafin ya shiga zayyane mata yadda ya yi da Jeeddah hatta da kuɗi adashe da ta ce za ta bashi bai ɓoye mata ba.
Har ya dasa aya Hajja ba ta katseshi ba, ba ta kuma furta uffan ba sai jinjina kai kawai take yi. Bilal yana gani Hajja ta ɗauki lokaci bata yi magana ba ya sake cewa "Hajja kin yi shiru ba ki ce komai ba?"
Sauke numfashi Hajja tayi gami da aje casbinta akan hannu kujerar da take zaune akai, kana ta tattara dukkanin natsuwa da hankalinta ga Bilal ta ce "Dole ka ji nayi shiru Bilal al'amari ne ya zo min wani iri azahirin gaskiya ni kaina ina da buƙatar naga ka yi aure, sai dai bani da yadda zan yi saboda ba ka da aiki yi aure kuma ko a Addinan ce ba zai yu ba sai da ci da sha da saura buƙatotin rayuwa. Shiyasa ka ga tsawon wannan lokaci ban taɓa tuntubar ka akan zance aure ba. Sai kuma gashi yau ka zo min da wannan zance, Bilal nasan kana so Jeeddah matuƙar so hakazalika ita ma tana sonka duk mace da za ta so ka ba za kai ta ba. Ni kaina ina sonka da ita burina ta zama uwar jikokina, sai dai ina fargabar iri wannan zance da ka zo min dashi.
Sassauta murya Bilal ya yi duk ya bi ya narkewa Hajja ya dawo abin tausayi "Hajja Dan Allah kada ki ce a'a domin ƙi amincewarki yana nufin na rasa Jeeddah tun da har kika ga mahaifinta ya zo da wannan tsari to haƙiƙa ya gaji da jirana so yake ya aurar da 'yarsa. Kuma wallahi Hajja Jeeddah tana da ɗimbin masoya kawai dai Allah ne ya zuba mata ƙaunata, yanzu haka akwai ɗa ƙanwar Babanta da ke mahaukacin sonta gashi kyakkyawar ajin farko ga kuma dukiya mai tari yawa amma ta nace sai ni ɗin take so. Ko don wannan hallaci da tai min bai kamata na barta ba goyon bayanki haɗi da addu'ar ki kawai nakeso Hajja.
Hatta da alƙawarin kuɗi da tai mishi ya faɗawa Hajja bai ɓoye mata komai ba.
   Shiru Hajja tayi sai jinjina kai take yi bayan dogon nazari da tayi taga babu wata mafita da ta wuce ta amince domin ko ba komai Jeeddah tai musu hallaci ba kaɗan ba, ko a watanni baya da tai rashin lafiya da kuɗinta aka yi jinyarta a asibiti duk wasu hidindimo ita ce ta dinga yi kama daga kuɗin gado har zuwa kuɗin magunguna har aka yi discharge ɗinta.
"Shikenan Bilal na amince sai ka yi ƙoƙari ka je ka sanarda Baffanka Rabi'u sai ya sanarda saura ,'yan uwansa ranar juma'a sai su je gidansu Jeeddah ɗin Allah ya sanya alkhairi Allah ya ba ka ikon riƙe ta da gaskiya da amana. Sai ka yi ƙoƙari ka kira kawunka Dauda ya kama ɗaya daga cikin shanu uku da suka yi min saura ya siyar raguwar biyu abarma A'isha idan lokaci aureta ya yi sai ayi mata amfani dasu.
Ka ga sai mu ganganɗa a haɗa maka lefe daidai na talaka mai ƙaramin ƙarfi, ba zai yu ba ace ko ɗan lefe mu kasa yi mata tun da ba a kanmu babu ta yanke cibi ba.
  Sosai Bilal ya cika da murna sai godiya yake zubawa Hajja.
Tun lokaci da Haidar suka baro gidansu Jeeddah Daddy da mommy suka zaunar dashi su na rarrashiinsa a zahiri ya nuna masu ba komai amma a baɗili shi kaɗai yasan yadda yake ji   kafin ya miƙe ya wuce ɗakinshi ya ci kuka tamkar wanda ya rasa uwa da uba a lokaci guda  sai da yaci kukanshi ya ƙoshi kana ya hau gado ya kwanta sai faman juyi yake yi alamun ciwonshi naso tashi da kyar ya ja jikinsa ya buɗe bedside drawer inda magungunanshi suke ɗauka ya sha amma bai fasa jin nauyi da zafi a zuciyarsa ba. So yake ya yakice son Jeeddah ko ta ƙarfin tsiya ne. Bayaso ko kaɗan ciwonshi ya tashi saboda ita shiyasa yake ƙoƙari ya danne abinda yake ji musanman yadda ya ga iyayenshi sun ɗaga hankalinsu. Duk lokaci ya tuna da shikenan ya rasa Jeeddah sai ya ji ciwon da yake ji a zuciyarsa ya daɗa ƙaruwa ashe haka rabuwa da masoyi yake da zafi da ciwo da ya fahimci damuwa ba inda za ta kai shi face ta ƙara jefa shi ciki mayuwaci hali, ya tashi da kyar jiri na ɗibar shi ya shiga bathroom ya yi wanka koda ya fito ana kiran sallar Azhar ya shirya cikin ƙanana kaya cike da ƙarfin hali da so ɓoye hali da yake ciki ya ɗauki key ɗin motarsa sai da ya tsaya a masallaci da ke kofar gidansu ya yi sallah kana wuce ma'aikatar su abokinsa Shariff Yusuf Barade shi kaɗai ne aboki da yake iya gayawa  damuwarsa, ya kuma ba shi shawara.
  Kamar yadda Bilal Shattima ya saba zuwa picking ɗin Jeeddah yana zaune a inda ya saba zaman jira fitowarta tun daga nesa ta hango shi ta shiga zuba murmushi.
Akan hanyarsu ta zuwa gida yake bata labari yanda ya yi da Hajja sosai Jeeddah ta shiga murna farin cikinta ya kasa ɓoyuwa, cike da nishaɗi da walwala ta shigo gida as usual ta fara leƙawa parlourn Mama tai mata barka da gida ta amsa ba yabo ba fallasa kana ta wuce ɗakinsu, ɗauke da sallama Khairat da ke tsaye gaban dressing mirror tana gyara gashinta ta amsa mata adaƙile, ta kalleta sau ɗaya ta watsar gami da taɓe baki. Sosai hakan ya ɓatawa Jeeddah rai kasancewar tasan haushinta Khairat ke ji shiyasa bata kula ta ba infact tana cikin farin ciki ba za ta yi sake a gauraya mata shi da ɓaci rai ba.
   Kayan jikinta ta cire ta ɗora towel ta nufi bathroom, tana shiga taga babu ruwa a famfo mamaki ya kamata ta fito tana faɗin "Khairat ya aka yi yau babu ruwa a bathroom ɗinmu?"
  Ba tare da Khairat ta kalleta ba ta amsa da cewa "uhmm! Ta nufi wardrobe ɗinsu ta dubin kayan da za ta saka, ran Jeeddah ya sosu cikin fusata ta ce "kamar ya uhmm ba ki da bakinki ne da ba za ki buɗe baki ki amsa min ba ko asarar yi min magana kike yi?"
   "Tabbas ba ki faɗi ƙarya ba Jeeddah asarar yi miki magana nake yi, ba amfani magana da ke sai ma tarin takaici da abin haushi, ai ke yanzu ba wanda ya isa ya faɗa miki ki ji duk abinda ranki ke so shi kike yi Mama tana cikin ɓacin rai abinda kika yi wa Haidar amma ke ko a jikinki, na rasa kalar zuciyar da ke darshe a ƙirjinki?"
    "Duk abinda za ki faɗa wallahi ko a jikina, ni dai ke zaman aure nan ba wani ba saboda haka abarni da zaɓina mana.
   "Ka ji sakarci kou? Ke nan har alfahari kike yi da zaɓen wanda bai da sana'ar yi, to bari ki ji ba za ki san kin tafka gundumemen kuskure ba sai an zarga miki igiyar aure Bilal wallahi a lokaci za ki gano shayi ruwa ne.
  "Mugun fata kike yi min to a kanki zai ƙare ni da Bilal Shattima mutu karaba takalmin kaza, sai dai mahassada su rungume sorry.
Jeeddah ta ƙarashe magana tana gallawa Khairat muguwar harara.
Girgiza kai Khairat tayi tana taɓe baki, ba ta sake kulata ba domin ta fahimci al-amarinta sai du'a'i ta ri ga da tayi nisa bata jin kira, saboda haka tasaka kayanta ta bar mata ɗakin yayin da Jeeddah ta ci-gaba da faɗar baƙaƙen maganganunta.
  Tun shigowarsa Office ɗin SY Barade ya kifa kansa a kan desk ya kasa furta kalma ko ɗaya daga bakinsa sai faman sauke ajiyar zuciya yake, yanayi da SY Barade ya gansa a ciki ya tabbatar mishi da babu lafiya domin tsawon zamanshi dashi bai taɓa ganinsa a cikin mugu tashin hankali iri wannan ba. Gashi tun shigowarsa yake fama dashi da ya faɗa masa damuwarsa amma yaƙi magana, sosai hakan ya tashi hankali SY Barade.
  "Please Ka'oje ka yi min magana mana infact miye amfani zuwanka Office ɗina indan kasa ba za ka faɗa min damuwarka ba?"
  Da kyar ya ciro kanshi ya watsa rinannu idanuwanshi akan fuskar SY Barade da ke tsaye a gefen hagunsa, cikin raunin murya ya ce "SY na rasa ta shikenan wani za ta aura ba ni ba dan Allah ka faɗa min mi zan yi da zai cire min sonta kwata-kwata daga zuciyata?"
Cike da firgici SY Barade ya dafa shoulder Haidar Ka'oje muryarsa tana rawa ya furta
  "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Ba dai kana nufin Jeeddah ba?"
  "Ita ce SY na bi kowace hanya da za ta aminta ta aure ni amma ta ƙi a takaice dai yau mahaifinta ya fito fili ya faɗa min na haƙura da ita domin wanda take so zai aura mata.
Ya ƙarashe magana muryarsa na rawa tamkar zai fashe da kuka.
"Calm down abokina duk abinda ya yi zafi maganinsa Allah, dama nasan hakan sai ta faru da kai shiyasa tuntuni nake ba ka shawara ka rabuda ita tun da ta nuna bata sonka amma ka kafe sai kace ita kaɗai ce mace da tai saura a duniya.
  "Ba kasan yadda son yake ba shiyasa kake gani rabuwa da Jeeddah zai zo min da sauƙi.
Muguwar harara SY Barade ya watsa masa tare da jan guntun tsaki "mtsss...kai ba ka isa kace bansan so ba kawai dai nawa da naka akwai banbanci, domin ni inaso ana sona saɓani kai ke so ba a sonka kuma ka bi ka maƙale mata ai dole ta wulaƙanta ka.
   "Haka ma za ka faɗa SY a maimakon ka tausaya min sai ƙara gasa min maganganu masu zafi kake yi, domin ina da yaƙini za ka kwantar min da hankali shiyasa na zo gunka.
  Ajiyar zuciya SY Barade ya yi kana zauna akan kujerar da ke kallon Haidar ya sassauta murya ya ce "Ban san me yasa ba za ka goge babin Jeeddah a zuciyarka ba?" Ga mata nan wanda suka fi ta birjik kamar jamfa a jos sai ka zaɓa ka darje na rasa me ka gani a jikin Jeeddah da yasa ka maƙale mata har haka sai kwara kanka take yi kamar kwallo a raga?"
   "Ba za ka gane ba ko na faɗa SY saboda tun farko ba ka sonta.
Haidar ya yi magana yana kwantar da murya.
Girgiza kai SY Barade ya yi cike da jin mugun haushin Haidar ya ce "Ba sonta bane ba na yo Ka'oje tsanar da take nuna maka yasa na ji ta fice min a rai, duk mutumin da zai wulaƙanta ka Haidar koma waye shi ba za mu taɓa shan Inuwa ɗaya dashi ba.
   "I know my friend kawai ni yanzu shawara nakeso ka bani yanda zan cire ta a zuciyata na manta da na taɓa sonta so nake nayi rayuwa farin ciki kamar kowa, domin ba abinda na tsinta a cikin soyayya face baƙin ciki da ƙunar zuciya.
   "Gaskiya kam abokina gara ka yi gaggawa fitar da ita daga zuciyarka, saboda nan da ɗan wani lokaci ta zama mallakin wani. Yanzu shawara ɗaya ce da nake gani za ta sa ka manta da Jeeddah duk da mantawa da ita faratt ɗaya ba abu bane mai sauƙi kawai ka shirya kafin aurenta ka bar ƙasar nan ina gani hakan zai sa ka shafe babinta.
   "Na bar ƙasa kuma SY ina kake tunani na tafi?"
"Canada mana kaga za ka jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya za ka yi Masters ɗinka kana za ka ci-gaba da aiki da ZENN MOTORS COMPANY ya ka ga wannan shawarar tawa?"
Jim.... Haidar ya yi yana nazari maganar SY Barade kafin ya ce "Uhmm...shikenan zan yi tunani akai.
  "Wane iri tunani Ka'oje?"  Idan har da gaske kana so ka manta da Jeeddah Please ka amince kawai da wannan shawarar tawa.
  Haidar ya sauke ƙarfaffiyar ajiyar zuciya kana ya ce "Shikenan zan nemi visa gara nayi nesa da ita don gaskiya ban zan iya jure gani an ɗaurawa Jeeddah aure da wani ba. Na tabbata duk juriyar da na nuna za ta tafi a banza yanzu ma daga nan hospital zan wuce ayi min check up saboda ina jin canji a jikina.
  "Tashi na raka ka nima banaso ciwo nan naka ya tashi saboda ni kaɗai nasan iri hali da nake shiga a duk lokaci da naga kana sha wuya.
Haidar ya yi murmushin gefen baki yana ƙara jinjina girman ƙaunar dake tsakaninshi da SY Barade abota ce wacce aka gina bisa yarda da amince tun yarinta suke tare yayin da  abotarsu ta rikide ta zama 'yan uwan taka.
Jeeddah tana kwance waya take da Haidar sai kace ba ɗazu-ɗazu nan suka rabu ba. Khairat ta shigo fuskarta a murtuƙe ta ce "Ki zo inji Ya Kabeer?"
Sai da gaban Jeeddah ya yi mummunan faɗuwa tai sauri katse kira tana kalli Khairat cikin kaɗuwa ta ce "Ya Kabeer kuma me zan masa?"
  "Shi ya dace ki yi wa wannan tambaya ba ni ba.
Khairat ta faɗa kamar bataso magana kana ta fice daga ɗakin.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA
   
    *Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

012...

Jikina yai mugun sanyi saboda na tabbata zance aurena ne zai yi min, domin shima Ya Kabeer ɗin na daɗe da sani baya sona da Bilal shima yana ɗaya daga cikin team ɗin Ya Haidar raina a jagule na sauko daga saman gado na ɗauki hulata da ke kan pillow na mayar kaina tun kafin na shiga parlourn Mama nake jiyo maganganu da Mama take faɗawa Ya Kabeer duk kuma akaina. Na ji kamar na fasa shiga parlour na koma inda na fito sai dai ina bala'in tsoron abinda zai biyo ba domin ko kaɗan Ya Kabeer baya ɗaukar reni idan na ƙi zuwa zai iya iske ni har ɗakinmu yai min duka. Sai da na dauƙi some seconds a tsaye ina shawarwari kafin na yaye curtain bakina ɗauke da sallama Ya Kabeer ya amsa min gami da yi min mugun kallo. Ban san lokaci da na sadda kaina ƙasa ba kamar wata tsohuwar munafuka na nemi wuri na rakuɓe cikin ɗar-ɗar  na gaida shi ba tare da na kalle shi ba, bai tsaya amsa gaisuwa tawa ba ya wani zare manyan idanuwanshi cikin kakkausar murya ya ce "Wato ke kin zama taƙadariya mai taurin kai  ba wanda ya isa ya faɗa ki ji kou?
Cike da tsoronshi na girgiza kai alamar a'ah ba haka bane, saboda nasan halinsa sarai yanzu nan sai ya rufe ni da dukan akawo wuƙa domin halinsa sak iri na Mama ne da sauri hannu.
   "Ke yanzu abinda ki ka yi kin kyauta kenan? ace duk irin alaƙar gidanan da Haidar, ki ka zaɓi bare akansa. Ɗan uwanki ne fa amma kika guje shi ki ka fiffita auren wani matsiyaci da bai da ko kwabo. To wallahi bari ki ji tun da kika guje Haidar duk abinda ya biyo bayan ki kuka da kanki domin zaɓin ranki mu ka bi.
   "Ai ba laifinta bane ɗanan laifin Babanku ne da goya mata baya, sai anan gaba zai san ya tafka babban kuskure.
Mama ta faɗa cike da zallar takaici.
   Ai kuwa Ya Kabeer ya rufe ni da shegen faɗansa inda yake shiga ba ta nan yake fita ba, ni kam na sunne kai cikin cinyoyina ina rera kuka ya daka min gigitatciyar tsawa "Rufe mana baki shegiya yarinya munafukar banza da wofi butulu mai manta alkhairi kina kaini bango yanzu nan sai na tashi na hanɓarar da ke, na kasa gane wane irin daƙiƙanci ne ke ɗawainiya dake da ya rufe miki idanuwa ki ka nace sai kin aure mutum irin Bilal?"
  Cikin shassheƙar kuka na ɗago na ce "So ne kawai Ya Kabeer...
  "Rufe min baki sakarya kawai ke yanzu wannan kayan takaici da baƙin ciki har a kira shi da suna so kina dai ƙoƙari ɓata rayuwarki a wofi amma ba komai rayuwarki ce ke kin ka sani duk abinda ya biyo baya ba ruwanmu ba dai kin kafe lallai sai kin aure marar aiki ba? to ai shikenan ga ki ga shi, masu iya magana na cewa iya ruwa fidda kai Sai kun yi aure za ki gane wautar da kika yi, yanzu duk abinda za mu faɗa miki ba lallai bane ya shige ki ba.
   Mama da Ya Kabeer suka ci-gaba da faɗar maganganu marasa daɗi akan Bilal Shattima, ni kuma sai rusar kuka nake yi duk wannan faɗa da suke yi min ina jinsu ne kawai don ba tasiri zai akaina ba duk abinda za su faɗa ba zai sa na rabuda Bilal Shattima ba ko fahimtar hakan suka yi ne oho sai kawai Ya Kabeer ya daka min tsawa tare da furta "Tashi ki ɓace min da gani mahaukaciyar yarinya ana nuna miki Annabi kina runtse ido.
Da gudu na fice daga parlour na nufi ɗakinmu.
Ya Kabeer ya dawo da ganinshi akan Mama ranshi a matuƙar ɓace ya ce "Ban san me ke damun Baba ba da yasa ya yanke wannan ɗaye hukunci sai kace yarinya nan ta rasa manema iri wannan aure kwata-kwata ban ga amfaninsa ba, koda ace ba za ta aure Haidar ba bai kamata ta aure jobless ba.
   "Huhmm... Bari kawai ɗa nan idan ana sallah ba a magana lamarin Babanku sai shi tun da ya yi wannan furunci komai runtsi ba zai janye ba gara kawai mu kawo nagani mu zuba musu, ƙarshen ta duk wata ɗawainiyar su kansa za ta koma.
  "Ai ta ma fara dawowa kan nasa Mama yanzu haka ya yanke shawarar ɗaya daga cikin gidajenshi na haya zai basu su zauna, har ya yi min magana na tura masu gini su duba inda yake buƙatar kwaskwarima ayi musu hatta da painting gidan ya ce na tura painters su yi mishi estimating, ƙudin da za ci.
Ya Kabeer ya ƙarasa  magana gami da kyaɓe baki.
Sallati Mama ta shiga yi tana tafa hannuwa kafin ta ce "Ohni! Fatee indai ba ka mutu ba komai kana gani shi ko Alhaji irin wannan gantallewar da taɓarɓarewa ce ta cika da shi to Allah ya kyauta lamarin ya zama babba sai mu taya su da addu'a domin daga shi har 'yar tasa suna cikin tsaka mai wuya.
**** ** ****
Haidar Ka'oje tare da SY Barade asibiti suka nufa doctor Haneef ya duba shi ya ga zuciyarsa har ta fara kumbura sakamakon damuwa da tashin hankali da ya shiga, dole sai admitting ɗinshi ya yi  ya ɗora masa drip da allurai saboda indan ba a yi gaggawa tsayar da kumburi ba ciwo zai iya ƙamari, SY Barade ne ya zauna dashi har zuwa lokaci da drip ɗin zai ƙare saboda yana gudu kada ya kira gida ya tashi hankali mommy da Daddy shiyasa ya zauna dashi, nan take bacci yai awon gaba da Haidar sakamakon alluran har da na bacci.
Jeeddah tana shiga ɗaki ta faɗa bisa gado ta shiga rera kuka, ta tsani ta ji ana ambatar kalmar ɓatanci ga Bilal ɗinta sosai hakan ke ɓakanta mata rai, ta rasa dalili da yasa Mama da su Kabeer ke son shiga tsakaninta da farin cikinta.
Ranar juma'a iyayen Bilal suka zo gidansu Jeeddah kyakkyawar tarba suka samu daga wajen Baba domin shi kaɗai ne mai ƙaunar aure nata, ba tare da ɓata lokaci ba aka saka musu rana nan da watanni biyu, masu zuwa cike da karancin haɗe da karamawa suka yi sallama da juna.
Daga goro har dabino gami da kuɗi da suka kawo ko kallonsu Mama bata yi ba, a dalili wani iri ɓaci rai da takaici da ya lulluɓe ta.
Farida ce ma da ta zo ta raba ta aikawa 'yan uwa Baba da na Mama sai kuma makwabta, domin su ma su sheda su kuma sa albarka.
Bayan Farida ta kammala rarraba kayan ta sami Mama a ɗaki cikin girmamawa ta shiga bata baki gami da rarrashinta ta daina fushi da Jeeddah da kyar ta shawo kan Mama ta haƙura.
*BAYAN WATA ƊAYA*
yau ta kasance ranar Lahadi wacce ita ce ranar da za a kawo kayan lefen Jeeddah da Khairat, kuma a ranar Haidar Ka'oje ya ɗaga zuwa Abuja daga can zai hau jirgin Canada, saboda ba zai iya jure gani an ɗaurawa Jeeddah aure da wani ba shi ba. shiyasa ya yi wa kansa ƙiyamullaili tun kafin zuwan ranar ya haɗa kayansa ya bar ƙasar ga baki ɗaya.
Tun da sassafe gidansu Jeeddah ya kacame da 'yan uwa da abokan arziki sai girke-girke ake yi sai kace rana ɗaurin aure ce Baba ya kashe kuɗi sosai kusan dai yadda kullum bidi'a ke ƙara yawaita a ƙasar nan especially anan Arewacin Najeriya, yanzu idan za a kawo kayan lefe shahararren biki ake haɗawa.
Misali ƙarfe 2:30pm dangin Jameel suka iso gidanmu cikin tsadaddun motoci kirar zamani, kusan set uku na akwatuna suka kawo shaƙe da kaya a matsayin lefen Khairat hadda su gold necklace ƙirar Dubai, sutura ga su nan birjik kama daga atamfofi, laces, Abayas, shadda, materials a takaice dai kusan kala ɗari biyu da goma su kansu akwatuna har wani wrapping ɗinsu aka yi gwani ban sha'awa, ga kuma tsabar kuɗi har kimanin dubu ɗari biyar a matsayin hanjin lefe, da suka tashi tafiya sai kunga yadda dangin Baba da Mama suka yi musu sha tara na arziki ta hanyar ba su snacks da 'yan uban kalolin drinks ga naman kaza cikin manyan trays har guda biyar ga kuma wani ƙaton gasasshen rago, har da kuɗi dubu ɗari biyu wai duk tukuici ne.
Bayan dangin Jameel sun tafi aka buɗe akwatuna sai santi kaya ake yi, duk wanda ya zo sai ya yabi kayan ana faɗar Khairat ta yi goshi.
Bayan an gama gani lefen sai kuma aka shiga zuba ido zuwan nawa, da yawa sun kagara suka ga  ni kuma me za a kawo min masu gajin haƙuri har sun fara imagination, har aka yi sallar la'asar babu dangin Bilal babu samatar su yayin da wasu daga cikin 'yan tarar lefen suka fara gajiya da zaman jiran tsammani, tun su na korafi a cikin zuciyoyinsu har suka dawo yi a fili sai faɗar suke kodai sun fasa zuwa ne su kama gabansu. Gani ce-ce-kuce yana neman yin yawa yasa Aunty Farida ta nufo ɓangaren Baba da muke zaune tare da ƙawaye mu, ta kira ni muka shiga bedroom ɗin Baba cikin damuwa ta ce "Jeeddah har yanzu fa dangin Bilal ba su zo ba ko za ki kira shi mu ji ko sun fasa zuwa ne, kada mu bar mutane su ta jira daga ƙarshe su zo su ƙi zuwa kin ga an ɓatawa musu lokaci a wofi.
  Take naji gabana yai wani mugun faɗuwa damuwa ta bayyana ƙarara akan fuskata, jikina a sanyaye na ce "tou Aunty bara na kira shi ɗin.
Na juyawa na koma parlour kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki na ɗauko wayata, na dawo nasa kiran layinsa ringing ɗaya zuwa biyu ya yi receiving "Hello...Love ya aka yi ne?"
  "Uhmm!
Sai da na fara sauke gwaron numfashi kafin na ce "Love akwai damuwa fa har yanzu 'yan gidanku ba su zo ba ko sun fasa zuwa ne?"
  "A'ah ba su fa zuwa ba Love 'yar matsala ce aka samu ta abin hawa, dama na yi magana da Abbas zai kawo su a motarsa sai kuma tafiyar gaggawa ta kama shi zuwa Bodinga shine muke jira ya dawo sai su zo.
   "Haba.. Love wane irin abu ne?" sai kace shi kaɗai ne mai mota a cikin abokanai ka, ka nemo wani kawai ko kuma a nemo motar haya ba dole bane sai shi saboda anan mutane sai mita suke an shanya su.
   "Ki yi haƙuri Love banaso abin magana shiyasa ban nemo wani ba saboda kinsan lefen ba wani mai yawa bane, ina gudun kada su je majalisa a dinga gulmana.
  Sosai ran Jeeddah ya ɓaci da jin furuncinsa nan take ta harzuƙa cikin faɗa ta ce "To ai shiyasa tun farko nace da kai na yafe lefen duk abinda Allah ya hore maka ka kawo min da kanka, amma ka ƙi bin shawarata to yanzu ga irinta nan kasa mun tare jama'a kuma yanzu ka zo kana gayamin ba wasu kaya masu yawa bane. Bilal ka fahimci ni kai nakeso ba abin hannunka ba ko babu lefen na shiryawa aurenka.
   "Amma Jeedd...
"Dallah ya isa Bilal ka nemo motar haya kawai a kawo lefen nan kowa ya kama gabansa period.
Bata jira jin ta bakinsa ba ta kashe wayarta, Aunty Farida wacce tun farko da Jeeddah ta fara magana da Bilal ta kafe ta da idanuwa gani ta kashe waya, yasa ta dafa shoulder ta cikin kwantar da murya ta ce "meke faruwa ne Jeeddah naga kamar ranki a ɓace?"
  "Ba dole ki ga raina a ɓace ba Aunty tun farko sai da nace da Bilal na yafe lefe nan amma ya kafe lallai sai an kawo wai hajjarsa ce ta ce sai ayi min kayan lefe, shi kuma ba zai iya hanata ba. Sai gashi kawo kayan yana neman ya zama jan aiki wai babu motar da za a kawo lefen.
   Shiru Aunty Farida tayi tana nazari maganganu Jeeddah, kafin ta ce "idan basu da mota ba dole bane sai su nemi motar haya ko adaidaita, kada su bar mutane suna zaman jiransu al'hali ko gobe suka kai ba motar ce dasu ba, kawai su yi aiki da abinda a ƙarfinsu.
  Daga haka Aunty Farida ta fice daga ɗakin ina jin tana mita, sai naji raina ya ƙara ɓaci wato magana ce ta faɗa min a dunƙule da ko can ita kaɗai ce nake yabo a cikin jerin ahalina da bata nuna adawa aurena da Bilal. Tabbas sai na ƙara yarda da karin maganar nan da ake cewa ba a yabon ɗan kuturu sai ya girma da yatsa.
   Sai yamma lis 'yan gidansu Bilal suka iso zuwa lokaci masu tarbon lefen duk sun watse, kaɗan suka yi saura basu wuce mutane uku ba sai kuma Hajiya Turai da Umma Asabe suma don ya zama musu dole ne, duk wanda ke tsakar gidanmu zaune ya ji dirar adaidaita ba kuma guda ɗaya ba da alamu suna da yawa jim kaɗan sai ga mata zuga guda sun shigo ɗauke da trolleys guda biyu babba da ƙarama irin old design ɗinan da aka gama yayi su tun a 2008 duk uwar sallamar da suke rafkawa aka rasa wanda zai amsa musu a dalili kowa ya raja'a da kallon tambaɗaɗɗin akwatuna da ke hannunsu, sai can Mommy Turai da ƙawar Mama Umma Asabe su ka yi ƙarfin halin amsa musu har suna haɗawa da yi musu lale marhaban, kasancewar Baba ya je har can gidansu Ya Haidar ya ba wa Daddy da mommy haƙuri da taimakon Ya Haidar suka haƙura yayin da Baba fahimtar dasu hujjarsa ta ƙi yi min aure dole cikin hukunci Ubangiji suka fahimta suka kuma yi maslaha wannan shine dalili da yasa har Mommy Turai ta zo tarban kayan lefen mu.
  Mommy Turai tai musu iso zuwa wajen da aka shimfida manyan tabarmi na gwaggo munafuka suka zazzauna tare da aje 'yan akwatunan su.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

   *Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

014...

Sunkuyar da kai ƙasa Jeeddah tayi ranta in ya yi dubu ya ɓaci, wato dama Mommy Turai ta shirya cin zarafinta ne tai mata tozarci shiyasa ta zo tarbon lefenta saboda ta ƙi auren ɗanta Ya Haidar. Babban takaicinta bai wuce yadda suke ta kushe mata lefe ba gami da tofa kalaman ɓataci ga Bilal ɗinta bata dawo daga tunani da ta nusa ba, ta ji saukar muryar Mama a kunnenta tana cewa "Dan Allah Asabe zo ki kawar min da tarkace banza nan a gabana wallahi ko ƙaunar ganinsu bana yi duk lokaci da idanuwana suka sauka akan akwatuna nan sai naji wani iri takaici da ɓaci rai ya lulluɓe ni.
Tun kafin Umma Asabe ta kwashe akwatuna nai sauri bari parlourn ina toshe bakina da tafin hannu ɗakinmu na shige, na haye gado ina rera kuka ba kakkautawa saboda maganganun Mama da mommy Turai suka faɗa akan Bilal sun yi bala'in tsaya min arai.
Bayan fitar Jeeddah daga parlourn Mommy Turai ta kalli Mama a natse kana ta ce "Fatee yanzu kina gani ƙiri-ƙiri a ɗauki 'yarki akai gidan matsiyata irin wannan?"
Sai da Mama ta ja fasali kafin ta sami damar furta "Ya na iya Turai?" faɗa da yafi karfin ka dole ka maida shi wasa, tun da ubanta ya ɗaure mata gindi ni miye nawa a ciki?
  "ALLAH ya kyauta amma tsakanin da Allah Jeeddah ta gama cutar da kanta ba kuma za ta fahimci hakan ba sai anan gaba.
Hajiya Turai ta faɗa haɗe da yatsine fuska.
Da dare bayan Baba ya dawo yaci abincinsa Mama ta matsu ya kammala domin ta nuna masa lefen Jeeddarsa tana gani ya gama ta tattare kwanuka takai kitchen.
Daga kitchen ta zarce parlournta ta jawo akwatuna a wulaƙance ta kawo gaban Baba ta ajiye "Alhaji ga kayan lefen shalelenka nan kasa albarka.
"Ma-sha-Allah! Shi kuwa Bilal me zai sa ya wahalar da kanshi da irin wannan hidima?"
   Tsaki Mama ta ja kana ta ce "Ai kuwa dai da bai wahalar da kanshi ba, domin da wannan lefen nashi na ɓanar suna  wallahi gara babu. Saboda mugun talauci daga atamfofi har lace babu na ƙirki a ciki.
Mama ta ƙarashe magana tana huci.
  "Subhanalillah...! Me kike faɗa haka Fatee?" Irin waɗannan maganganu basu kamace ki ba yaronan ba wani aiki ne dashi ba  amma don kawai ya faranta wa 'yarki rai duk da bashi da shi ya ɗage ya yi mata kaya nan amma ke kuma kina aibanta wa. Lefe ba shi bane zaman aure domin ko ba lefe idan mace tana so namiji za ta aure shi su kuma zauna lafiya,  zance na gaskiya Fatee ki gyara halinki mace nawa aka yi wa aure ba kayan lefe suka zauna ɗakunan mazajensu cikin farin ciki da kwanciyar hankali. Tun da Jeeddah tana sonshi ina da yaƙini ko bai mata kayan lefe ba za ta taɓa nuna damuwarta ba. Domin gudun surutun mutane iri-irinku yasa Bilal ya ɗorawa kanshi wannan hidimar amma duk da haka bai tsira ba, ku dai mata ba a iyar muku.
Baba ya ƙarashe magana cikin faɗa-faɗa domin ba ƙaramin haushi Mama ta bashi ba.
   Yayin da furuncin Baba yai masifar ƙara harzuƙawa Mama rai sai  kallonshi take yi kafin ta ce "Duk da bakaso a faɗin laifin Bilal hakan ba zai hanani faɗa maka ka zauna ka yi nazarin gobe 'yarka kada son zuciya ya jefa ka a danasani.
  "Ke don kin tsane shi ne shiyasa duk bajintar da zai yi ba ki gani, ina kuma shawartaki da ki daina irin haka ko don albarkacin 'yarki, kuma in-sha-Allah da amincewar Ubangiji sai kin yi alfahari da goben Jeeddah.
Sosai Baba ya zage damtse ya wanke wa Mama allonta tass..daga ƙarshe baram-baram suka rabu. Washegari da Baba ya tashi dawowa daga kasuwa ya haɗowa Jeeddah tsadaddun kayan lefe na gani na faɗa set ɗaya na akwatuna irin ma na Khairat ne. Ya zuba mata laces, atamfofi, shaduddi da material gami da Abayas kusan kala hamsin da biyar haɗe da set ɗin shoes and bags designer masu tsadar gaske guda bakwai, sai veils kuma wani abin burgewa hadda ƙaramar gold necklace mai matuƙar kyau ya kawo kuɗi ɗinki 100k ya bata.
Saboda tsabagen farin ciki Jeeddah har da kuka tayi.
Lokaci da Mama ta kammala duba kayan ba ƙaramin ɓaci rai ta ji ba sai dai a wannan karon tayi ƙoƙarin danne ɓaci ranta gudun irin martani da Baba zai iya maida mata. Duk da haka sai da ta kira mommy Turai da Aunty Farida ta faɗa masu dukkansu su yabawa ƙoƙarin Baba domin suna gani yadda yayi shine daidai da bai yi wa Jeeddah kayan lefe ba da me za ta saka a lokaci biki. Sai lokaci Mama ta fahimci Baba ya yi ne domin ya fidda su kunya.
Ranar bata karya yau saura kwana uku a fara shagalin biki, zuwa lokaci Baba ya Kammala gyara musu gidan da za su zauna. Bilal Shattima sai rasa bakin godiya ya yi domin Baba ya gama mishi komai ya bashi 'ya kuma bashi muhallin zama. Ta bangaren kayan ɗaki komai iri ɗaya Baba ya siya musu kawai dai akwai banbanci colour, sai kuma Khairat da ke da four bedrooms gado huɗu aka sa mata Jeeddah kuma two bedroom ne, a maimakon gadajen da aka sakawa Khairat da ba a siyawa Jeeddah ba Baba sai da ya siya mata standard freezer da generator babba bayan already ya sai musu deep freezer, zuwa lokaci bakin Mama ya mutu mutuss...sai kawai ta zubawa sarautar Allah ido domin lamarin Baba ya fi ƙarfin ta. Sosai Baba ya kashewa 'ya'yansa miliyoyin kuɗi. Lokaci da za a kai gara gidajen angwaye Mama bata so akai yawa ɗaya ba ta so a bambanta a cewarta tuwon girma miyarsa nama tun da Bilal bai kawo lefen arziki ba babu dalili kai masa gara mai yawa ba. Sai da suka kai ruwa rana da Baba kafin ta amince aka kai 'yan uban tulin kayan abinci gidansu Bilal a matsayin gara.
A yau ne amare suka shiga lalle da yamma za a yi kamu a gidan Farida kasancewar compound ɗin gidanta yana da matuƙar girma. Kwararrun masu decoration ta yo booking tun daga Kaduna, aka tsantsara masu decoration na ji da gani.
Amare kuma sun sha gyara ciki da waje idan ka ga Jeeddah da Khairat sai ka matsa musu da kallo kafin ka yi nasarar gane su. Koda five o'clock ta buga an kammala musu makeover sun yi kyau na ban mamaki amarya Jeeddah sanye cikin wedding gown golding in colour kanta ɗauke da Royal blue turban Khairat kuma nata gown ash colour ce da turban irin na Jeeddah, kowacce su ta sanya gold necklace ɗinta. Lokaci da dangin Bilal suka zo kamu suka yi arba da amaryarsu sai da suka rena kansu, suka fara zargin anya Bilal bai yi tsaga da faɗi ba na aure mace kamar Jeeddah.
Sai daff da magariba taro ya watse yayin da Aunty Farida ba ƙaramar hidima ta yi ba domin ta raba souvenirs na gani na faɗa.
Ƙarfe 9 za a tafi dinner party wanda friends ɗin Jameel suka shirya masa shi da amaryasa Khairat amma sai gayyaci Bilal Shattima da nasa tawagar abokai, ko kaɗan Jeeddah bataso zuwa ba sai da Aunty Farida ta buɗe mata wuta sosai kana ta bari aka shirya ta.
Dinner tayi matuƙar ƙayatarwa sakamakon duk abokan angwaye da amare wayayu ne, sai around 12 o'clock kowa ya kama gabansa.
Washegari bayan an sauko daga masallaci juma'a ɗaruruwa mutane suka sheda ɗaurin aure Bilal Ibrahim Shattima da Jeeddah Usman maishadda akan sadaki naira dubu talatin sai kuma na Jameel Bello Sifawa da Ummul-khairi Usman maishadda akan sadaki naira dubu ɗari biyu. Sosai wannan sadaki da Iyayen Jameel suka bayar ya janyo ce-ce-kuce a tsakanin 'yan ɗaurin aure shi kansa ango Bilal Shattima sai da ya ji wani iri koda aka gama daurin aure ranshi a jagule sai murmushi yaƙe yake yi, wannan ita ce rana ta farko da Bilal ya ji baƙin ciki rashin aikin yi har ya sha alwashi duk inda aiki yake zai nemo sa kuma muddin ya yi kuɗi sai ya faranta wa Jeeddah fiye da tunanin duk wani mai tunani, kuma har gaba da abada ba zai so wata 'ya mace ba daga kanta ya datse ƙofar zuciyarsa.
Bayan isha'i amare har sun kammala shirinsu cikin lafayya fara sol sai ƙamshi na musamman ke fita daga jikinsu, zuwa ƙarfe takwas aka kai su part ɗin Baba nasihar zaman aure mai ratsa jiki ya yi musu kana ya ƙara tunatar dasu muhimmanci haƙuri da adana sirrikan gidajen su, daga Jeeddah har Khairat ba wanda bai zubda hawaye ba. Kana Mama ta ɗora daga inda Baba ya tsaya, lokaci da aka zo tafiya dasu Jeeddah kwacewa tayi daga hannun Mommy Turai ta faɗa jikin Mama tana rusa kuka tana faɗin "Dan Allah Mama ki ce kin yafe min ɓaci rai da na sakaki, idan ba ki ce kin yafe min ba Mama ba zan taɓa farin ciki ba a rayuwarta.
   Idanuwan Mama sai da suka ciciko da hawaye domin ba ƙaramin tausai Jeeddah ta ji ba, a hankali take ɗan bubbuga gadon bayanta "Ya isa haka Jeeddah daina kuka kada ki bata kwalliyarki, ni uwa ce mai ƙaunar farin cikin 'ya'yanta nasan illar dake tattare da fushina akanki shiyasa tun a wancan lokaci na sa wa raina na yafe miki, Allah ya yi muku albarka Allah yasa wurin zamanku ne har mutuwa, ina muku fatan alkhairi da wanzuwar farin ciki mai ɗorewa ke da 'yar uwarki. Tashi maza akai ki ɗakin mijinki dare na ƙara yi.
   Baba da Mommy Turai suka amsa da "Amin!
Kana mommy Turai ta ɓanɓare Jeeddah daga jikin Mama ta ja ta zuwa ƙofar gida yayin da Umma Asabe ke riƙe da Khairat ita ma sai faman gunji kuka take yi, Jameel ya aiko da tsadaddun motocin ɗaukar amaryasa saboda haka dasu aka yi amfani aka saka Jeeddah cikin ɗaya daga ciki, kasancewar ita ce babba sai da aka fara kai ta gidanta kafin aka wuce da Khairat zuwa nata gida.
Tun daga gate ɗin gidan Khairat za ka san naira tayi kuka, balle kuma ka shiga ainihin cikin gidan tsarin gini turawa ne sama da ƙasa a ƙasa akwai tamgamemen parlour haɗe da two bedrooms, ga kitchen da store room ga kuma dining room, a gefe ɗaya ga wurin shan iska idan kuma ka haura upstairs za ka tarar da parlourn maigida da master bedroom ɗinsa, sai kuma sashen Khairat ita ma akwai parlour da bedroom, sai kuma dining room idan ba ka buƙatar saukowa ƙasa kenan, gidan Khairat ya haɗu iya haɗuwa yayin da 'yan uban tsadaddun kayan ɗakin da aka zuba mata suka ƙara ba da gudunmuwarsu wajen ƙawata gidan.
Duk wanda yaga tsarin gidan Khairat sai ya tausaya wa Jeeddah, don gani suke kamar tana cikin akurkin kaji. Gidan da Baba ya ba su Jeeddah part haɗu ne da ka shigo gate part ɗin farko shine nasu Jeeddah, raguwar uku kuma akwai 'yan haya a ciki na kusa da Jeeddah na Jessica ne 'yar asali kwara state ce aiki ne ya kawo ta Sokoto tana aiki a access bank sai kuma mr Mahmoud da matarsa Hajara su kuma  'yan Kaduna ne shima aiki ne ya kawo su garin Sokoto, da yaransu uku, sai part ɗin ƙarshe na wani ɗan sanda ne officer Abdoul-ganiyu tare da matarsa Sharifa da ɗan su ɗaya duk mutane da ke gidan babu ɗan asali Sokoto dukkan su aiki ne ya kawo su. Kuma tun kafin Jeeddah ta zo gidan Kabeer ya gayamusu 'yar maigidan ce shiyasa kowanne su ya sha jinin jikinsa.
Kowane part yana ɗauke da ɗakunan bacci guda biyu haɗe da parlour ɗaya da kitchen sai kuma ɗan ƙaramin dining room mai ɗaukar ƙaramin dining set mai kujeru huɗu.
Tun kafin ƙawayen Jeeddah su baro gidanta wasu daga cikinsu masu gajin haƙuri suka fara keɓewa suna gulmarta Sakina Salis ce da Hafsah Bello ke tsaye a kitchen suna kallon 'yan uban kayan kitchen ɗin da ke shaƙe da kitchen cabinet, ba abinda yafi tsone musu ido irin manya-manyan warmers masu mahaukacin tsada da aka zubawa Jeeddah, hassada da baƙin ciki ya lulluɓe musu zuciya Hafsah Bello ta ja guntun tsaki tai ƙasa da murya tana cewa
  "Tirrr... wallahi an yi asarar kayan kitchen anan wuri, za su rube a banza domin wanda aka kawowa su cima zaune ne sai dai a nemo a bashi yaci.
   "Bari kawai Hafsah Bello ni kaina na kasa daina mamakin Jeeddah Usman maishadda ko uban me ta gani a jikin Bilal ɗinan, mutum sai ƙari talauci ga kuma  muni tsiya shegiyar fuskarsa kamar ta gwaggo biri.
   Dariya suka kwashe da ita har suna haɗawa da tafawa Sakina Salis ta sake cewa "Wai nan da yake cakuss dashi Jeeddah bala'in kishinsa take bata yarda ya raɓi kowacce mace ba.
  "Shi wannan mai gajeren hanci ni wallahi banga abin so a jikinsa ba dama ace yana da 'ya'yan banking sai kayi maleji saboda ƙudinsa.
Cewar Hafsah Bello tana yatsine fuska.
   "Ni ma shi na gani da yana kuɗi sai a sonshi ko don albarkacin ƙudinsa amma...
Jin takon tafiya an nufo kitchen ɗin yasa suka yi shiru tare da fitowa suna muzurai, A'isha shattima da Raliya Hassan suka gani, murmushin yaƙe suka yi da ka kalle su za ka gano basu da gaskiya, Sakina Salis ta ce dasu "har yanzu ango da abokansa basu ƙara so ba?"
   "Eh wallahi amma in-sha-Allah ko sun daɗe ba za su wuce 10 o'clock ba ku dai ƙara haƙuri dan Allah.
Cewar A'isha shattima.
Ƙarfe goma daidai Bilal da tawagar abokansa suka shigo ɗakin amaryasa Jeeddah jin sallamar su yasa tai sauri jan lafayyarta ta lulluɓe fuskarta..
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

    *Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

013...

"Sannunku da zuwa kunsha hanya.
Mommy Turai ta faɗa tana musu ƙasƙantatce kallo gami da yatsinar fuska.
  "Yawwa sannu Hajiya kun ganmu sai yanzu.
Cewar inna Rabi wacce ta kasance ƙanwar Mahaifiyar Bilal.
A wannan karon Umma Asabe ce tai magana tana yatsina "Wallahi kuwa ga ku nan zuga guda, yawan nan naku kaɗai ya isa ya gamsar da mu Bilalu ɗan dangi ne gaba da baya.
   Inna Rabi ba ƙaramar yarinya bace da za ta kasa gane magana ce Umma Asabe ta yada mata, take taji jikinta ya yi sanyi ta kasa cewa  komai sai kawai ta shiga murmushi yaƙe.
  "A'ah...ya haka jama'a kun tusa akwatuna lefenku a gaba, ai sai ku buɗe mu gani kada mu buɗe ku ce mu yi muku kaudi.
Cewar Hajiya Turai tana murmushin zallar takaici domin tun basu buɗe ba yanayi akwatuna su kaɗai ya isa ya zama shedar babu abin a zo a gani a ciki ta faɗin hakan ne kawai don ta ƙara cin zarafin su.
   Hajiya Bintu wacce ke zaune tana nuƙurƙusar baƙin ciki, saboda taga Bilal zai aure 'yar masu hannu da shuni sai yanzu da taga dangin Jeeddah su na yada masu da maganganu masu ɗaci sannan ta sami natsuwa ranta yai fari kal......ta wani zakuɗa manya mulamulai ɗuwawunta ta washe haƙora kamar wadda aka yi wa kyautar kujerar makka. Ta kai dubanta gefen da Bahijja take zaune tallaɓe da haɓa sai rarraba idanuwa take yi ta ce "A'ah... Bahijja me kike jira a zaune da ba za ki tashi ki buɗe musu akwatuna ba?" ai Bilal ya yi namijin ƙoƙari matuƙa mutumin da duniya ta sheda ba shi aiki fari balle na baƙi ya danƙaro ɗan uban lefen iri wannan ai dole a yaba masa kai tabarakallah ma-sha-Allahu yaro ya yi ƙoƙarinsa.
Wani irin gumi ne ya karyowa Bahijja domin tasan duk abinda Hajiya Bintu ke faɗa gatse ne da tsabar isgilanci da kuma so tadda zaune tsaye shiyasa tun farko bata so a zo da ita ba domin gudun iri wannan, sai gashi ta kasa ta tsare sai da ta biyo su. Jiki a mace Bahijja ta tashi ta fara zipping babbar trolley ɗin inda atamfofi da laces ke ciki duka ba za su haura kala goma sha biyar zuwa ashirin ba, tana ƙoƙari buɗe ƙaramar Umma Asabe ta dakatar da ita tana cewa "karki yi gaggawa Malama Bahijja ɗan dakata kaɗan mana mu gama gani wannan sai ki buɗe ta gaba, saboda naga daga budewarki har na fara cin karo da abin mamaki, gara ki bari mu sha kallo a tsanake ko ya kika gani Hajiya Turai?"
Ta ƙarashe magana tana kallon Hajiya Turai.
  "Wallahi kuwa Asabe saboda ni banga abin rawar jiki anan ba.
Umma Asabe ta ƙara yatsine fuska gami da sunkuyawa ta shiga fiddo kayan daga cikin akwati tana watsawa kan tabarma, kuma duk wacce ta ɗauko a wulaƙance take jefawa kan tabarma gami da kirgawa ta ƙarshen da ta ɗauko cikon ta ashirin ta miƙe tsaye tana jujjuya ta kafin tasaki sallati tamkar wacce tai mugun gani kana ta kalle Hajiya Turai cikin zaro idanuwa ta ce "Ikon Allah ikon ma'aiki ashe dai har yanzu da raguwar atamfar cote d'ivoire a duniya Hajiya Turai duba ki gani ita ce ko kuma idanuwana ne ke min gizo kinsan idanuwan tun na haihuwa ne?"
   "La'ilaha illallahu Muhammadur Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam! Wallahi ita ce  Asabe ba wani gizo da idanuwanki ke miki ai ni na zaci tuni kamfani ya daina bugata.
Hajiya Turai ta faɗa tana karɓa atamfar daga hannun Umma Asabe, sai wani zare idanuwa take yi kamar taga abin tsoro.
Jin iri maganganu da suke faɗa yasa Hajiya Amina wadda ta kasance 'yar ƙani mahaifin Baba, ta matso kusa tana leƙen atamfar daga hannun Hajiya Turai ta shiga tofa albarkacin bakinta.
   "Ai Hajiya Turai atamfar ce akwai quality da ƙarkon tsiya ga ta kuma da haƙuri wahala sai ki ga talaka ya daɗe yana morar ta.
  "Ikon Allah wanda yafi gaban mamaki.
Hajiya Turai ta furta tana wani girgiza kai.
Umma Asabe ta kalli Bahijja wacce ke rakuɓe ta ce
  "Malama Bahijja taso ki buɗe mana ɗayan akwatin mu gani duk da kyakkyawar juma'a tun daga Laraba ta ake ganewa.
Jikin Bahijja a mace ta taso ta sake buɗe musu ɗayan trolley ɗin, sai kawai suka haɗa baki suna rafka sallati gami da tafa hannuwa sakamakon gani tarkace da ke cikin jakkar ta farkon ma tafi kyau gani saɓanin wannan mai ɗauke da takalma set biyu haɗe da handbag guda ɗaya tak sai sabulai da man shafawa wanda basu wuce rabin dozen ba, sai wata mahaukaciyar necklace mai zuɓin gold mai haɗe da kwalamin zobe girmansa har ya wuce a misalta shi sai veils guda biyu old design da hijab guda uku. Duk cikin kayan ba abinda ya ja hankali Hajiya Turai iri fake gold necklace ɗinan, ta ɗauko ta tana kallo can kuma ta ce "Asabe tayani gani wannan haukar ko sun zaci mu jahilai ne da ba za mu iya banbance tsakanin real gold da fake one ba?"
Sai da Umma Asabe ta fara jan guntun tsaki kafin ta ce
  "Bari kawai Hajiya wannan kayan takaici da yawa yake tsakani da Allah Jeeddah ta gama cutar kanta kwata-kwata ba abin nunawa anan wuri lefe kala ashirin ba na babu na nuna wa sa'a tirr....da wannan kayan takaici.
  "Kema kya faɗa Asabe sauƙin mu ɗaya babu baƙon ido a gidanan da haka za a dinga yamaɗiɗi da mu gaba ɗaya unguwa ta ɗauka an kawowa 'yar mu lefen matsiyata.
  Ran Hajiya Bintu yai fari fess...har batasan lokaci da dariya da take danne wa ta subuce mata ba, ta shiga kwasar abarta hankali kwance sai da tai mai isarta kafin ta taso daga gun zamanta ta nufi wajensu Hajiya Turai cike da su haddasa fitina ta karkace baki ta ce "Kina da gaskiya Hajiya mutane wannan zamani basu gadonka amma suna gadon maganarka, yanzu nan sai ku ga ana yaɗa tarkace nan a waya {social media} amma zance na gaskiya yarinya nan ta cuce kanta ba kaɗan za ta yi asarar budurcinta a wofi ALLAH na tuba ko a zamanin mu ba a kai lefen iri wannan ni da farko na zaci ko bazawara ce sai da na tambaya aka ce min sabuwa ce dal a leda, to Allah ya kyauta shiyasa addini ya yarje da bincike kafin aure don gujewa irin wannan.
Inna Rabi da taga al'amarin yana neman wuce gona da iri ta taso cikin tausassa murya ta ce "Haba Hajiya Bintu ya kike neman ki zama haddasana shi fa arziki yana tsakani mata da miji ki ka sani ko ita ce abokiyar arzikinsa? Gaskiya ki gyara halinki domin duk mutum mai cikakken hankali ba zai aikata kwatankwacin abinda kika aikata ba.
Shiyasa Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallam ya hore mu da mu faɗi alkhairi ko mu yi shiru.
   Cike da masifa Hajiya Bintu ta hayyaƙo wa Inna Rabi tana faɗar "Ke rufe min bakin Rabi tun kafin na zage naci miki mutuncin anan wuri, wato ni ce karkatacciyar kuka mai daɗin hawa kou? In banda reni wayau kina dai ji da kunnenki iyayen yarinya ne suka fara magana don na tanka, na tofa albarkacin bakina shine za ki taso min da wani guntun wa'azi ki to wallahi ahir ɗinki. Kai...ku ji min mata dallah ban da guntun iskanci me ya hana Bilal ɗin ya nemi daidai ƙarfin aljihunshi saboda son zuciya da ya tsotsa a nono ya buge da yi ma 'yar mutane asiri to kuwa duk wanda ya hau motar kwaɗayi ba inda za ta sauke shi sai a tashar wulaƙanci, wallahi kaɗan ku ka fara gani. Ku kuma ku yi gaggawa raba 'yarku da Bilal idan ba haka ba kun dingi gani ƙasƙanci da kayan haushi kenan.
Ta ƙarashe magana tana kallon su Hajiya Turai.
  Baki buɗe inna Rabi da raguwar 'yan uwan Bilal ke kallon Hajiya Bintu wacce hankalinta kwance tamkar ba mummunan abu ta faɗa ba.
  "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Bintu ki ji tsoron haɗuwar ki da mahaliccinki.
Cewar wata Gwaggo Bilal  wacce tun fara taƙaddamar take kallonsu sai kuma yanzu da Allah ya bata ikon yi magana.
Saboda tsananin mamaki da ya lulluɓe inna Rabi da Bahijja kasa furta kalma ko ɗaya suka yi sai bin mutane da idanuwa suke yi shiyasa Gwaggo Sa'a ta samu damar yin magana.
  Uwar harara Hajiya Bintu ta watsawa Gwaggo Sa'a gami da cewa "Kin ji ki da wani zance Sa'a saboda tsananin tsoron Allah ne yasa na faɗin farar gaskiya da ku ɗin ku ke ɓoyewa ke ni fa ko a bakin kura nake idan gaskiya ta zo sai na faɗe ta ehee.
   "Kai dallah ya isa haka!
Hajiya Turai ta daka musu tsawa gami da ɗaga musu hannu tana ci-gaba da faɗin "Ai gaskiya Hajiya Bintu ta faɗa in banda aikin asiri me Jeeddah za ta tsinta a jikin ɗanku. Kin ga Asabe dan Allah ki sallame mutane nan nagaji da gani kayan takaici akwai, drinks da snacks da aka tanadar musu suna kitchen ki basu. Rago da kaji kuma ku bar mana kayanmu domin yawan lefensu yawan tukuici da za mu basu infact waɗannan tarkace nasu basu ma cancanci tukuici daga garemu ba. Basu kawai za mu yi ko don wannan uwar zuga da suka yo sai kace wanda suka kawo abin kirki, wannan tambaɗaɗɗe lefen nasu ko mutum ɗaya ya isa ya kawo shi amma saboda tsabagen kwaɗayi suka haɗa ayari guda ki basu snacks da drinks ɗin kada su yi zuwan banza.
Ta ƙarashe magana gami da shigewa parlourn Mama.
  Umma Asabe ta bi su da kallon wulaƙanci kana ta nufi kitchen ta fiddo musu da kayayyakin da Hajiya Turai ta umarce ta da ta basu, bayan ta kammala ɗaukowa ta kalle su da girar ido ɗage ta ce "To malamai da Hajiyoyi mun fa gode da ƙoƙari ga wannan in kun tashi ku tafi dashi.
Inna Rabi ce tai ƙarfin hali furta "Hajiya ai da kun barshi kawai.
  "To ai ke baiwar Allah ba ke kaɗai mu ka bai wa ba idan bakyaso raguwar abokan tafiyarki suna so.
Ba wanda ya ƙara tanka mata suka shiga jidar kayayyakin suna fita dasu ƙofar gida inda masu adaidaita ke zaman jiran su. Bahijja ita ce ta ƙarshe da tashi har ta kusa fita ta tuna da kuɗi da aka bata dubu goma ta bayar a matsayin hanjin lefe, sake dawowa tai ta miƙawa Umma Asabe wacce ke ta faman banbami faɗa sai da ta karɓe kuɗi kana ta tambaya na menene cikin sanyi murya Bahijja ta faɗa mata hanjin lefe ne, wata uwar harara ta buga mata gami da tsaki kafin ta samu furta wata magana marar daɗi Bahijja tai sauri barin wajen.
A ɗaki kuma Hajiya Turai ta tusa Mama a gaba sai zayyane mata kalar lefen take yi tsabar takaici da baƙin ciki Mama kasa magana tayi sai wani iri tuƙuƙi take ji a zuciyarta.
Bayan dangin Bilal sun tafi Umma Asabe da Amina suka tattare kayan suka mayar cikin akwatin, kana suka nufo parlourn Mama dashi sai a gabanta suka dira su Umma Asabe ta ce "Hajja Fatee ga lefen Jeeddatul Baba nan sai ki buɗe ki ganewa idanuwanki, domin gani da ido ya kore ji ga su nan daga atamfofi har laces babu na kirki a ciki duk tsofaffin yayi ne.
  Zuciyar Mama tamkar za tai tsalle ta faɗo ƙasa ana ciki haka sai ga Jeeddah da ƙawaye ta sun shigo ƙawayen keso gani kayan lefen Kafin su tafi shiyasa ta shigo dasu. Wani matsiyaci kallo da Hajiya Turai ta watsa musu cikin masifa gami da takaicin Jeeddah ta daka musu rikitatciyar tsawa cikin hargowa ta ce "Ku me ya shigo daku yi parlour nan? Jeeddah tana ƙoƙari buɗe baki tai magana ta sake daka musu tsawa wacce tafi ta farko ƙara "Dallah ku fita ku ba mu wuri ko ba ku ga magana mu ke yi ba? Kun wani faɗo mana gatsal ku dai yaran zamanin nan sai a hankali ba ku da ta ido ko kaɗan. Ba za ku fita bane ina magana kun ja ku tsaya wato sai na gama banbami faɗa kuna tsaye maza ku fice munafukai banza masu bin gidan ƙawaye domin ɗaukar rahoto daɗin abin kowane shege bai rasa guntun kashinsa a ɗuwawu.
   Haba wa tun kafin ta dire aya suka fice da sauri wasu su har suna haɗawa da gudu, Jeeddah ta juya za ta bi su a baya Hajiya Turai ta fizgota a fusace "Dawo nan munafuka wacce bata gudun abin magana banda shasshanci miye na gayyato ƙawaye me za su gani anan tarkace banza nan ko me?" Wallahi Jeeddah da wannan kayan takaici da aka kawo miki gara babu sau dubu dasu babbar atamfa a ciki lefenki ita ce chiganvy ita ma ba ta kwatano ba shine har da ɗebo ƙawaye su zo su gani su shiga gari su sami na yaɗawa.
   "Ai da ki bar su Turai su gani in yaso su shiga gari su ta yamaɗiɗi da 'yar banza mai kunnuwan ƙashi.
Mama ta faɗa cikin hasala jin take kamar ta taso ta rufe Jeeddah da mugun duka.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

   *Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

    *_Afuwan please kwana biyu ina busy shiyasa ku ka daina gani update ga ɗan wannan ku yi manage_*

015...

Bayan ka-ce-na-ce da ya zama al'ada a tsakanin abokan ango da ƙawaye amarya. Kana aka zarce da siyen baki, inda abokan Bilal Shattima suka siye bakin amarya Jeeddah akan zuzzurutun kuɗi naira dubu ashirin.
Kana suka yi wa ango da amarya sallama Bilal Shattima ya raka su har zuwa bakin Gate, ya dawo ya rurrufe ƙofofi da tagogi sannan ya nufo ɗakin da Jeeddah take zaune ya tura ƙofa bakinsa ɗauke da sallama.
Da sauri na waiga ido cikin ido mu ke kallon juna Bilal, ya saki min murmushi nima na mayar masa da marni take na ƙaryata masu cewa Bilal Shattima mummuna ne don ni gaskiya ban ga wannan muni ba. Sai ma naga yau yafi min kyau fiye da can baya ya sha farar shadda ɗinkin babbar riga sai damɓe yake da rigar da alamun yau ne farkon da fara saka babbar riga. Ya tunƙaro inda nake tun kafin ya ƙaraso na sadda kai ƙasa wai ni a dole kunya nake ji, cikin ɗoki da zumuɗi ya zauna daff dani har cinyarsa tana gogar ƙuguna.
  "Al-hamdulillah! Dukkan godiya ta tabbata ga Allah maɗaukakin sarki da ya nufe mu da gani wannan rana mai cike da tarin albarka. Kin ga ikon Allah ko Jeeddah?" Allah ya yi aure da marar kwabo 'yan sai mun gani kunya tabbata lahu agaresu.
Ya ƙarashe magana yana dariya tare da kamo hannunta, yana massaging tafin hannun nata take naji tsigar jikina ta tashi yarrr....har bansan lokaci da na lumsashe idanuwana ba. Duk maganar da yake yi ban ce komai ba sai murmushi nake yi saboda wata irin mashahuriyar kunyarsa da nake ji wai ni ce yau da jin kunya Bilal na kasa yarda da hakan. Shiyasa sai mamakin kaina nake yi.
  "Love lallenki ya yi min kyau na kuma san saboda ni aka yi shi kou?
Na ɗago ina murmushi murya can ƙasa nace "Love kenan wannan tambayar ai kana da amsarta.
Ya wani waro idanuwanshi yayin da fuskarsa ke ɗauke da murmushi ya ce "Wannan haka yake my Nurul-qalbi yanzu sai ki tashi ki shiga bathroom ki ɗauro alwala ki zo mu godewa mahaliccinmu da ya nuna mana tabbatuwar wannan rana.
Na yi jim na kasa tashi sai kallonshi nake ƙasa-ƙasa.
Bilal Shattima ya miƙe tsaye ya kama hannuwanta ya miƙar da ita tsaye yana gani ta tsayu da ƙafafuwanta ya matsu daff da ita ya haɗe tazarar dake tsakaninmsu ba ta ankara ba taji hannuwanshi akan waist ɗinta ya mannata a faɗaɗɗe ƙirjinshi, kyakkyawar runguma yai mata ta sunne kaita a ƙirjinshi.
Yayin da hannuwanshi ke yawo a gadon bayanta cikakku nonuwanta suka mannu da kyau akan ƙirjinshi, wani irin shegen daɗi ya ziyarci ƙwaƙwalwarshi bai san lokaci da ya ja dogon numfashi ba. Sannu a hankali yake bi gefe-gefen wuyanta yana shafawa mutsu-mutsu  ta dinga yi so take ta kwace tuni Bilal ya ganota sai kawai ya ƙara ƙamƙameta, cikin rawar murya ta dakatar dashi ta hanyar faɗin "Love sake ni fitsari nake ji.
Da kyar ya tantance abinda ta faɗa cikin mutuwar jiki ya sake ta kafin ka ce kwabo ta kai bathroom, sai da ya sake jan numfashi a karo na biyu kafin ya ce "Love karki manta da alwala.
  "Uhmm!
Ta faɗa sa'ili da ta ƙarasa kutsawa cikin bathroom ɗin. Ta ɗauki dogon lokaci a tsaye tana sauke ajiyar zuciya kafin tai tsalki kana tayi alwala, sai wata irin mafaffiyar sha'awa take ji tana taso mata hakan yana da nasaba da ɗan uban gyaran da suka sha, domin ba ƙaramin gyara su Aunty Farida tayi ba. Ta dirka masu maganin mata ba kaɗan ba. Shiyasa ɗan ya mutsata da Bilal ya yi ta fara kunnuwa duk ta ɓata panties ɗinta.
Panties ɗin da ke riƙe da hannunta tabi da kallo, motsi taɓa handle ɗin ƙofa da Bilal Shattima ya yi yasa tai sauri cukuikuye panties ɗin ta jefa shi bayan sink, tai maza ta nufi ƙofar fita daidai shi kuma ya kunno kai suka ci karo da juna Jeeddah tai baya kamar za ta faɗi yai saurin riƙo hannunta "Bi a hankali Love kada ki ji ciwo ki jawo min asarar wannan daren.
Murmushi kawai tayi tana wani sunne kai ƙasa ta bi ta gefenshi ta fito da mugun sauri ya zo ya shimfiɗa mata praymat sai wani mazari da rawar jiki yake yi ita kam Jeeddah sai kallon ikon Allah take. "Bismillah Love.
Ya faɗa gami da nuna mata praymat ɗin da ya shimfiɗa mata zuwa lokaci duk jikinta ya gama yin sanyi ta tabbata daren yau sai tasha gurza kamar kayan wanki a washing machine, ta ƙara gyara zaman laffayarta kana ta nufi praymat ɗin ya jogarance su sallah raka'a biyu kana ya zaryace da kwararo masu addu'o'in ɗorewar zaman lafiya bayan sun shafa addu'ar ya tashi ya ƙarasa cire rigar jikinsa dama tuni ya cire babbar riga ya dawo daga shi sai white vest da dogon wandon shaddar, parlour ya je ya ɗauko kaza da kayan tea haɗe da drinks da abokanshi suka siya mishi dama haka suke yi duk wanda ya tashi auren fari su na siya masa kaza, drinks da kayan tea, su kuma ba ƙawayen amarya kuɗin siyen baki, kafin ya baro parlour sai ya ɗauko ajiyarsa da ya adana bayan kujera wani haɗin tsimi ne na musamman daga Nijar Abbas yasa aka kawo masa shi a matsayin tsaraba, jikinsa na rawa ya ɓalle murfin gorar ya kafa kai duk da yana da ɓauri bai sa ya ɗago daga shan da yake masa ba. Sai da ya tabbatar da  ya shanye shi tass, ya nufi kitchen ya jefa empty robar a bin kana ya ɗauko musu plates da cup ya ɗauraye su a famfon kitchen ya haɗo kan ledojin ya nufi ɗaki dasu. Inda yabarta zaune anan ya sake iskota sai wasa da yatsun ƙafafunta take yi, yai sallama tare da dire ledar kaza da drinks a gabanta ya wuce da ta kayan tea ya aje akan bedside drawer, ya dawo ya zauna gabanta gami da jawo ledojin ya ciro kaza ɗaya daga cikin uku dake cikin leda ya ɗora musu a plate kana ya zuzzuba fresh milk a cups cikin tausassa lafazi ya ce "Love tashi ki rage kayan jikinki ki zo ki ci kazarki ta amarci banso ki ragewa su A'isha Shattima sarakan kwaɗayi.
Sosai maganarsa ya bata dariya har ta dara cikin ɗan ƙaramin sauti, kana ta rausarya da kai bata cuce kanta ba ta zage damtse ta yage kazarta son ranta ta ɗora da fresh milk mai sanyi gaske. Bayan cikinsu ya cika dam! Bilal ya tattara plates da raguwar kazar ya kai fridge yana fita Jeeddah ta tashi ta shiga bathroom tai brush, ta canza kayan jikinta zuwa sleeping dress, riga da wando cotton masu taushin gaske wandon ya tsaya iya guiwar ƙafarta. Tana shafa haɗaɗɗiyar humrata ya turo ƙofa ya shigo, Jeeddah ta ɗago idanuwanta suka sauka akanshi ya ƙarasa cire kayan jikinsa daga shi sai boxer briefs sai zabga ƙamshi yake yi, sosai Jeeddah ta ƙure shi da idanu ba ko kyaftawa sai yau tabbatar da sutura na ɓoye muni ɗan adam saboda yadda taga Bilal ɗinta ya yi wani dumm dashi muninsa ya fito ƙarara take ta tuna da kalaman Khairat da ta taɓa cewa da ita "Ina tausanki Jeeddah wallahi sutura ce ke suturta muni Bilal, sai ranar da aka kai ki gidansa bayan 'yan rakiyar amarya sun watse kowa ya kama gabansa daga ke sai shi ina tabbatar miki a ranar za ki gane tsananin munin Bilal Shattima da muke faɗa.  Ba ma za ki rena kanki ba sai ya yi zigidir tumbur haihuwar gyatumarsa, anan za ki ga gangariyar muni ɗan asali.
   A lokacin mugun fusata nayi na taso mata kamar zan rufe ta da dukan bala'i na zage ta tass! Ashe akwai ranar da zan tuna da maganarta har tai tasiri akaina domin kuwa ba ƙaramin bugawa zuciya tayi a lokacin da nai arba dashi a half naked shiyasa ina dawawo daga bulaye da na nusa nai maza na kauda fuska.
Ba kunya yana ƙarasowa wajena ya kai min runguma, ya haɗe bakinsa da nawa ya shiga tsotse ciki da wajen bakina musanman harshena duk tsoro da fargaban da na shiga da nayi arba dashi ya kau, domin saƙonsa ya sami karɓuwa a jikina.
Ci-gaba da murzata son ranshi ya yi ƙafafuwanta suka gaza ɗaukarta, da baya da baya ya soma tafiya yana ci-gaba da shanye mata baki ya jawo ta suka faɗa bisa gado ya bi ta ya danne yai mata kyakkyawar rumfa da faɗaɗɗe ƙirjinsa, ya ƙara ƙaimi wurin murza sassan jikinta, musamman nonuwanta da suka fi jan hankalinsa. Cikin fitar hayyaci ya raba ta da sleeping dress ɗinta hannunshi yana rawa ya kashe hasken ɗakin ya kunna deep light, ya tsotsa nan ya lashe can. Ba ka ji komai sai nishi da saukar numfashinsu sai da ya tabbatar da hankalinta ya gama gushewa ya lallaɓo addu'ar saduwa da iyali da kyar, ya kutseta lokaci da Jeeddah ta ji ya yaga budurcinta da ƙarfin da ALLAH subhanahu wata'ala ya albarce shi dashi ta kurma gigitatcen ihu. Bilal kam ko a jikinsa aslima bai san tana yi ba ci-gaba da naniƙarta ya yi  bai raga mata ko kaɗan ba. Domin kuwa sai da ya fashe duk wani dakon sonta da sha'awarta da ya dinga yi na shekaru shidda sai da tabbatar da ya sami gamsuwa iya gamsuwa ya barta, da kanshi ya haɗa musu ruwan wanka duk da Jeeddah ta nuna jarumta ba ta wasa ba, amma duk da haka kallo ɗaya za kai mata kasan ta jigata matuƙa, da taimakonsa ta sauko daga kan gado wani irin mugun zafi ƙasanta da nonuwanta ke mata. Yana riƙe da ita tana ɗingishi suka shiga bathroom suka tsaftace jikinsu ya sake riƙo ta suka fito ya goge mata raguwar dashin ruwan jikinta ya ɗauka mata wata doguwar rigar bacci tasaka suka kwanta ya rungume ta gam a ƙirjinshi sai zuba mata ruwan albarka yake yi, har bacci yai awon gaba da ita yana sa mata albarka.
Washegari gari sai ƙarfe takwas suka tashi su ango Bilal Shattima an kwashi gara yau ko sallar asuba bai fita ba. Bayan Jeeddah tayi wanka da sallah ta shirya cikin atamfar super exclusive ɗaya daga cikin kayan lefen da Baba yai mata. Atamfar tai masifar karɓar jikinta ta yi kyau na ban mamaki tana cikin canza bedsheet Bilal Shattima ya shigo cikin blue colour shadda hannunshi ɗauke da tray mai ɗauke da flask ɗin ruwan zafi sai soyayye kwai a cikin plate, wanda ya siyo bakin titi wurin mai shayi bayan sun kammala breakfast, suka fito parlour zuwa ƙarfe goma suka ji knocking on shi ya buɗe ƙofa neighbours ɗin su ne mazan na waje yayin da matan suka shigo Bilal ya fita suka gaisa Jeeddah ta saki fuska suka gaisa a mutunce, kowacce su ta gabatar mata da kanta da suka zo tafiya ta ɗebar musu chin-chin ɗin biki suka karɓa suna godiya ta yo musu rakiya zuwa bakin ƙofar fita. Sai da Bilal ya ga masu zuwa gani ɗakin amarya sun fara cika gidan sannan ya fita shima don abokansa wasa shi sun sako shi gaba da tsiya iri-iri da bai da niyyar fita. Jeeddah bata sami kanta ba sai kusan ƙarfe takwas da kowa ya kama gabansa gidan ya yi tsit sauƙinta ɗaya kafin A'isha Shattima ta wuce sai tai mata wanke-wanke da shara da batasan yadda za ta yi ba. Bilal Shattima Kuma tun Bayan la'asar da ya zo shi da abokinsa Abbas suka karɓi abincinsu tun lokaci bai sake dawowa ba. Ta ƙara kintse parlounta kana ta wuce bedroom tai wanka ta caɓa kwalliya cikin English wears wando da riga masu masifar kyau da jan hankali ta saki gashinta ya sauka mata gefe da gefen wuyanta, gaba ɗaya ta feshe jikinta da turaruka masu sanyi ƙamshi ta dawo parlour ta kunna kayan kallo ta nemi sofa ta hakince tana jiran dawowar Nurul-qalbinta.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

  *Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

     _*Gare ku masoyana ma'abota karantar litattafai na ga wata dama ta same ku ta karanta littafai na har guda uku a cikin farashi mai sauƙin gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune Kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga mai buƙatar guda ɗaya kacal_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250
*For those who have interest contact me on my cell phone number only WhatsApp 07032566172*

017...

Tana buɗe ƙofa taci karo da fuskar Ya Kabeer babu annuri kwata-kwata akan fuskar tashi. Take duk wani bala'i da masifarta ya rikiɗe izuwa tsoro har batasan lokaci da ta dafe saitin zuciyata ba saboda bugawar da take mata kamar za ta fashe. Cikin tsanani tsoron da ta kasa ɓoyewa ta sauke idanuwanta ƙasa cikin rawar murya ta furta "Ya Kabeer kaine sannu da zuwa shigo mana?"
Kusan duk a lokaci guda ta watsa masa waɗannan tambayoyi.
   Wani irin shegen takaicinta mai haɗe da zallar haushinta ya ƙara lulluɓe Ya Kabeer, dama tun ɗazu da officer Abdul-ganiyu ya kirashi a waya ya zayyane masa ta'asar da tayi yake ji haushinta yanzu kuma da yai ido biyu da ita sai ya ji haushin nata ya ƙara linkuwa fiye da ɗazu. Bai furta uffan ba ya raɓa ta gefenta ya shiga parlounta ya zauna, jikinta yana rawa ta maida ƙofa ta rufe ko ba a faɗa mata ba za ta iya cankar dalilin zuwan nashi gidanta a dai-dai wannan lokaci. A tsorace take matuƙar tsorata shiyasa ta kasa zama ta ja tai tsaye tana rarraba idanuwa. Wallahi sai yanzu nake nadamar abinda na aikata domin kuwa Ya Kabeer baya tolerating nonsense, yanzu haka na fi tsoronshi sau dubu akan Babanmu domin shi Baba komai girman laifi da mu ka yi masa sai dai yai mana faɗa da nasiha. Mama ce gwanar duka ita ma sai an kaita bango take duka, saɓanin Ya Kabeer da abu kaɗan zai wa mutum dukan mutuwa kuma wallahi idan yai duka sai mutum ya kwanta jinya shiyasa nake bala'in tsoronshi.
   "Ke don ƙaniyarki ba gunki na zo ba da za ki wani koma bayan kujeri ki laɓe maza dawo nan, shegiya yarinya mai neman ɗauko mana Dala da Gwauron Dutse.
Faɗa ya Kabeer ya katse min zance zuci da nake take naji tsoronshi ya ƙara kamani.
"Dan ALLAH Ya Kabeer ka yi haƙuri wallahi sharrin zuciya ne ba zan sake ba.
Ta faɗa cikin muryar son yi kuka.
  "Na rantse da Allah idan ba ki zo ba kika bari ni na zo mai hana na ɓalla ƙasusuwanki gidanan sai ALLAH.
Yana rufe bakinsa ta rugu ta zube gabanshi ko ta ina jikinta rawa yake yi, ta wani kwantar da murya tana bashi haƙuri kamar saliha yadda ya zuburo daga jikin kujera a fusace yasa ta ƙara tsorata ta zubura da suna ta miƙe tsaye tsananin tsoratar da tayi yasa ta kasa miƙewa sai kawai ta faɗi zaune daga zaune ta dinga jan ɗuwawunta sai jin tai taci karo da kujerar dake bayanta, babu saura wata hanyar guduwa dolenta sadakatt! Rai ɓace Ya Kabeer ya nuna ta da yatsa kafin ya ce "Ke don gidanku yaushe kika yi mijin da za ki iya kisan kai akanshi?" To wallahi bari ki ji in faɗa miki gaskiya wannan dabbaci da kika ɗaukowa kanki ba inda za kai ki sai ga halaka, in banda kina daƙiƙƙiya akan ɗa namiji marar tabbas za ki yankawa 'yar mutane wuƙa to ki godewa Allah da yasa Jessy tana da haƙuri da indan ta makaki kotu da duk ubanda da yai miki tsaye sai kin je prison. Mahaukaciyar banza da wofi. Ina tabbatar miki muddin Baba ya ji wannan maganar wallahi sai ya ci ƙaniyarki. Har yanzu na kasa yarda ke ɗinan Jeeddah za ki iya yankar jikin ɗan adam saboda kishi. Ban taɓa tsammanin rashin hankalinki ya kai har haka ba. To ki buɗe kunnenki da kyau ki saurareni nan gidan ba na mijinki bane kuma ba ki gadonsa ke kaɗai, ballantana ki hanawa 'yan haya sakatt! mu nan kasuwanci muke yi ba ki isa ki karya mana kasuwancinmu ba, idan ba za ki iya jure gani Bilal yana kula Jessy ba sai ki nema muku wani gida ba abinda ya dame ni. Ba gara Jessy daku ba tun da ita tana biyan kuɗin haya duk ƙarshen shekara ku kuma fa?" A batin sidam kuke zaune to wallahi ki kiyayeni. Ni ba Baba bane da ke jure iya shegenki ko yanzu kinci darajar igiyar aure da ke kanki da sai na nakada miki shegen duka. ko kallon banza kika sake yi wa Jessy sai kubar gidanan sai ku je can ku ƙarata ke da mijin naki ɗan gold autan maza, kuma ina ƙara gargaɗinki wannan mugun kishin da kika tsirowa kanki na jahilci tun wuri ki watsar da shi kin ji na gayamiki.
Sosai maganganu Ya Kabeer suka ci wa Jeeddah rai saidai bata da yarda za ta yi iyakacinta ta bashi haƙuri kuma duk yadda ta kai da bashi haƙuri hakan bai sa ya haƙura cikin sauƙi ba, sosai yacici mata mutunci ya wanke mata allonta ciki da waje, sai ga Bilal ya dawo bai ji mamaki gani Ya Kabeer ba saboda dama ya kwana da sani Jessica tace sai ta faɗa mishi, shima hakan ba ƙaramin daɗi yai masa ba gara tun wuri iyayenta su san hali da ake ciki gudun abinda zai iya faruwa anan gaba.
  Ya Kabeer ya kalli Bilal Shattima yana fitar da numfashi mai ɗan zafi, tsakani da Allah hadda Bilal ɗin haushinsa yake ji don gani yake yi shi ne ya sakarwa Jeeddah dama tai yawa shiyasa ta fara wannan mugun hali.
Shi ma Bilal bai tsira daga faɗa Ya Kabeer ba rufe idanuwa ya yi yaci masa mutunci iya son ranshi, kana ya miƙe ya ya saka su gaba zuwa apartment ɗin Jessica, sai da Jeeddah ta bata haƙuri, sannan Ya Kabeer yai tafiyarsa ko haƙuri da Bilal Shattima bi shi har wajen gate yana bashi bai tsaya sauraren shi ba ya faɗa motarshi yai tafiyarshi. Dama can Ya Kabeer jininsu bai haɗu da na Bilal ba. Jeeddah tana gani Ya Kabeer ya tafi a fusace ta shiga apartment ɗinsu sai cika take tana batsewa, domin ita gani take yi bata yi laifi da za ta bada haƙuri ba. Ya Kabeer ya yi haka ne don kawai bayaso aureta da Bilal. Take ta ayyanawa ranta ba za ta sake zuwa gidanshi ba. Kuma ko a waya ba za ta ƙara kiransa ba a takaice ma blocking ɗinshi za ta yi. Tana cikin zance zuci ta ji Bilal ya turo ƙofa ya shigo ya ci karo da ita tsaye riƙe da curtain rod na window ta cire hijabin jikinta, babu ɗan kwali akanta dama ta tsife rabin kitso kanta bata shace ba sai yai wani buzuzu, ga idanuwanta sun kode sai kawai ta dawowa Bilal Shattima abin tsoro musanman da ta tsare shi da mugun kallo da dakwa-dakwa idanuwanta. Sai da gabanshi ya faɗi rass! Sai kawai yai ta maza ya wuce ta batare da ya tanka ta ba kaitsaye ya wuce bedroom yana cikin cire kayan jikinshi tai bala'in banko ƙofa da ƙarfi ta shigo ta sake jingina jikinta ga bango. Tana harare-harare.
   "Wai Jeeddah miye haka ya za ki shigo min ɗaki ba sallama, sannan kuma kin wani tsare ni da kallon reni wayau dallah wuce ki gyara sumar kanki gaba ɗaya kin yi wani wujuga-wujuga dake ni wallahi tsoro ma kike bani.
  Bilal ya ƙarashe magana gami da jan guntun tsaki, kana ya nufi ƙofar shiga bathroom don har yanzu da raguwar haushinta shimfiɗe a ƙasan zuciyarshi, kafin ya kama handle Jeeddah ta rugu tasha gabanshi ganinsa da tayi yanzu ya dawo mata da image ɗin abinda ya faru da safe cikin masifa ta ce "Kai har ka isa kayi wanka a gidanan ai indan ka ga kayi wanka Bilal Shattima ka faɗa min alaƙar dake tsakaninka da Jessica da har ka iya ware yatsunka ka kwaɗa min mari saboda ita?"
   Kallon ƙasan ido yai mata kafin ya yi murmushin takaici yana girgiza kai, shi wallahi tausai ta yake ji gani yake yi kamar akwai noti da ya kwance a ƙwaƙwalwarta. Lamarinta sam bai yi kama da na lafiyayyun
mutane ba. Shiyasa ya rarrashi zuciyarsa ta hanyar riƙo damtse hannunta ya nufi gefen gado da ita duk yadda ta so ta kwace ta kasa saboda ƙarfinsu ba ɗaya ba, tana ji tana gani sai da ya zaunar da ita da ƙarfin tsiya. Kana ya zauna daff da ƙugunta yasa ɗayan hannunshi ya zagaye ƙugunta ya riƙe ta da ƙarfin gaske ya kwantar da muryarsa ya shiga faɗin "Jeeddah Please ki natsu ki bani aron hankalinki mu yi magana ta fahimtar juna...
  "Babu sauran wata magana da za mu yi a tsakaninmu kawai so nake ka faɗa min tsawon wane lokaci ka dauka kana cin amanata?"
  "Jeeddah ki daina jifa ta da iri waɗannan zafafan maganganun naki wallahi suna matuƙar sosa min rai. Kamata ya yi kafin ki tuhume ni ki tsaya ki yi nazarin girman laifin da kike zargina dashi...
  "Dallah ya isa kai har kana da wata kalma da za ka kare kanka da ita bayan da idanuwana naganka kuna musanya numfashi kai da ita hadda marena kayi akanta. Shine don ka gama rena min wayau za ka ce ina zarginka wato ma zarginka nake ko Bilal?"
Ta ƙarashe magana tare da rushewa da sabon kuka da sauri ya jawo ta jikinsa dama already ba kaya a jikinsa daga shi sai boxer briefs, da ƙarfi ya haɗe bakinshi da na ja'ira ya shiga bata zazzafan kiss yasan bai da amsa da zai bata da ta wuce wannan gara ya kashe bakin tsiyar nata, duk ture shi da take yi yaƙi sakinta da ƙarfi tsiya ya raba ta da kayan jikinta, duk yunwa da take ji sai da tasha murza ta jigata matuƙa a hannunshi. Jikinta ya yi mugun weak har ya yo wanka ya fito tana yashe bisa gado tana rera kuka.
Hayo gadon ya yi ya ɗagata yana faɗin "Love please I'm sorry wallahi-tallahi banso kuka nan naki. Ko kaɗan banaso abinda zai ɓata miki rai balle har ki zubda hawayenki, a tunanina ke ce wacce ta dace ta bada kyakkyawar sheda akaina amma sai gashi kina zargina da aikata abu mafi muni da ɗimbin zunubi zina...
  "Ni fa bance kana zina ba...
   "To ki faɗa min uban me zan tsinta a tattare da Jessy wanda babu shi a jikin matata?"
Ya katse ta a fusace gani yadda ya fusata yasa saitin ƙwaƙwalwarta ya fara dawowa dai-dai sai kuma jikinta yai sanyi musamman da ta tuna da Bilal Shattima ba mazinaci bane to miyasa ta kasa tuna hakan tuntuni gashi nan ta jawo kanta al-bala'u, domin muddin maganar nan taje kunnen Baba batasan wane iri mataki zai ɗauka akanta ba. Saboda abinda ta aikata ba ƙaramin abu bane da Baba zai zuba mata ido ba tare da ya ɗauki mataki ba. Cike da nadama ta kalli Bilal Shattima idanuwanta suna tsiyayar hawaye ta ce "Na shiga uku Love dan Allah ka yi haƙuri ka yafe min wallahi bansan me ya hau kaina ba. Na rasa dalilin da yasa idan naga wata mace ta raɓe ka sai na fita daga hayyacina. wallahi-azim Bilal ina matuƙar ƙaunarka ina maka wani irin so da zuciyata ba za ta jure ganinka da wata mace ba. Haƙiƙa zan iya haɗiye zuciya na mutu saboda azababben kishinka da nake ji dan girman ALLAH Love karka so kowa mace sai ni kaɗai. Idan ka riƙe min wannan alƙawari wallahi zan yi ta faranta maka, har izuwa ƙarshen numfashinta duk abinda kake so shi zan maka.
   Shi wallahi dariya ma ta bashi sai kawai ya rungume ta a jikinshi yana bin gaɓɓan jikinta ta ko ina da kisses, kafin ya ɗauke ta cakk zuwa bathroom ya taimaka mata tai wanka kasancewa jikinta bai da kwari a dalilin yunwar da ta yini da ita. Bayan ta gama wanka ta fito ɗaure da towel, ta zauna akan stool gaban dressing mirror kallonta ya yi cike da kulawa gani tana runtsar idanuwa hannunta dafe da cikinta yasa shi matsuwa kusa da ita ya dafa shoulder ta yana leƙen fuskarta yace "Love da alamu fitinarki yau bata barki kin ci abinci ba kou?"
Saidai ta harareshi kafin tace "kwanciyar hankali ke sa a ci abinci ni kuma bani dashi sai yanzu da na dawo cikin natsuwata na fahimci ina jin yunwa.
Ɗan guntun tsaki ya yi saboda ya ji haushin yadda ta zauna da yunwa akan wani kishinta na rashin dalili, sai da ya dungure mata kai kafin ya nufi ƙofar fita yana faɗin "ki kimtsa jikinki ki sami ni a parlour na haɗa miki tea ki fara da shi kafin na dafa miki noodless, na tabbata kishin Bilal Shattima bai bar ki kin mana girki ba.
Da kallon so ta bishi dashi kafin tai magana har ya fice da sauri, sai da tafara busar da sumar kanta da hand dryer da rabi yake a tsafe kana ta shirya cikin sleeping dress cotton half gown mai gajeren hannu, koda ta fito har ya haɗa mata tea mai kaurin gaske tana ƙarasa sha ya fito ɗauke da plate ɗin soyayyar indomie. Tare suka ci hatta da plate da mug ɗin da tasha tea sai da ya wanke su kafin ya dawo parlour ya zauna kusa da ita cikin kwantar murya ya ƙara nusar da ita kuskuren da ta tafka na yankar Jessica da tayi, haƙuri ta ƙara bashi kafin ta kwanta akan three sitter. Miƙewa Bilal Shattima ya yi yana faɗin "Love ina kika ajiye tsinke {Kibiya} da comb na ƙarasa tsife miki kitso nan don ba zan barki ki kwana da rabin kai a tsafe ba.
Shagwaɓe fuska tayi tana turo baki gaba tana faɗin "Love bacci nake ji ka bari sai gobe.
  "Ki yi baccinki ni kuma ki bar ni nayi aikina kawai ki faɗa min ina kika ajiye tsinken.{Kibiya}
Sai da ta ƙara turo baki kafin ta ce "zo ka duba bisa two sitter ɗinan ina gani kamar anan na barsu.
Ya duba cikin sa'a ya ga comb tsinke Kuma sai da duba under sofa ya ganshi, ya ɗauke kanta ya ɗora akan cinyoyinshi ya shiga tsife mata raguwar kitso kanta da kasa ƙarasa tsifewa saboda zazzafan kishinta da ya motsa.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA
     
    *Ga masu buƙatar a tallata musu hajarsu cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

    _*Gare ku masoyana ma'abota karantar litattafai na ga wata dama ta same ku ta karanta littafai na har guda uku a cikin farashi mai sauƙin gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune Kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga mai buƙatar guda ɗaya kacal_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦250
Da bansan asalinta ba ₦250
*For those who have interest contact me on my cell phone number only WhatsApp 07032566172*

016...

Sai ƙarfe tara daidai Bilal Shattima ya dawo. Lokaci da yai arba da Jeeddah  sai ya ƙure ta da rikitattun idanuwanshi yana mata kallo mai cike da zallar sha'awa, don ba ƙaramin kyau tai mishi ba. Shiyasa ya kasa haƙuri sai da ya jagwalgwalata iya son ranshi daga bisani ya wuce bedroom, ya yi wanka a wannan daren ma bai sassauta mata ba sai da ya sake tsallaka border. Bayan kwana biyu ta fara girki Kasancewar babu mai kawo musu abinci, lokaci da Bilal ya kawo mata kayan abinci tayi matuƙar mamaki saboda tasan adadin yawan garar da akai gidansu kusan buhun shinkafa takwas da buhun samovita huɗu catton superghetti da macaroni Kowane su guda biyar-biyar jarka mangyaɗa biyu na manja ɗaya bayan tarkace su maggi amma sai buhun shinfaka biyu aka basu na samovita guda ɗaya, sai superghetti da macorani ɗaɗɗaya mangyaɗa da manja sai ɗan ɗibar musu akayi a cikin ƙaramin galon ko maggi bai taka kara ya karya ba duka ba zai wuce yi musu wata ɗaya ba. Gaba ɗaya mamaki ya lulluɓe Jeeddah domin ita a tunaninta tun da sun san Bilal bai da aiki za su ɗiba garar ne kaɗan a kawo musu saura su yi maneji, kafin ta fara siya da ƙudinta sai taga saɓanin hankali da tunaninta dole ta ƙunshe mamakinta don babu halin furtawa.
Ƙiri-ƙiri Bilal Shattima ya daina fita kullum yana sinke cikin gida yana gurzar Jeeddah lamarinsa har ya fara bata tsoro bashi da wani aiki da ya wuce na naniƙarta da kuma zarrar ya biya buƙatarsa ya haye gado yai ta sharar bacci sai azhar yake tashi ya yi wanka ya cika tumbin sa ya fita zaman majalisa. Ada Haidar Ka'oje take ma kallon jarabbbe ashe Bilal Shattima shi ne asalin jarabbben Haidar Ka'oje bayyana nashi jaraba kawai ya yi a fili.
Tun kafin tafiya tai nisa ta fara gajiya da jarabarsa jurewa kawai take yi a dalilin bataso ɓacin ransa amma azahirin gaskiya ta gaji. Sati biyu ta koma bakin aikinta dama hutun three weeks aka bata ta cinye mako ɗaya a hidimar biki, tun da dare ta haɗa stew ɗin ta da safe ta dafa mishi superghetti ta kuma yi mishi breakfast ta aje mishi a dining table har ta fita gogan naku bai sani ba yana can ya tattake cikin bargo yana bacci abinsa.
  Sauƙin ta ɗaya yana zuwa picking ɗinta a haka suka ci-gaba da rayuwa yana nuna mata ƙauna gami da tattalinta hatta da wankin kayansu da goga shi yake musu amma fa sai ya tashi daga baccin nan nasa na azaliyya, a wasu lokuta idan tayi latti tafiyarta kawai take yi idan ya tashi ya haɗawa kansa breakfast ya kuma ɗora masu abinci rana. Kasancewar ya iya girki mai sauƙin girkawa sosai suke ji daɗin zama da juna soyayya suke zubawa ta fitar hankali. Sai da Jeeddah ta cika wata ɗaya ta je gida gaida su mama sai da Yamma liss ta je gidansu Bilal Shattima bayan isha'i ya zo ya ɗauke ta suka biya gidan abokinsa Abbas sai ƙarfe tara suka dawo gida. A kwana a tashi a sarar mai rai gashi auren Bilal da Jeeddah ya yi watanni uku ciff duk sanda aka yi salary sai ta ba Bilal atm ɗinta ya ciro kuɗi ya yo musu cafane, duk abinda ya siyo musu sai ya raba shi kashi uku ya kai ma Hajja kaso ɗaya Aunty Bahijja kaso ɗaya. Jeeddah bata damu ba saboda Allah ya yi ta cikin irin mutane nan da abin hannunsu bashi haɗa su faɗa da kowa, babbar matsalata guda ɗaya ce tak shi ne kishi.
Kasancewar yau weekend ne bata zuwa aiki tana zaune a parlour tana tsefen kanta Bilal ya fito cikin shirin fita da brown envelope a hannunshi ya samu labari wani kamfanin tomatos yana ɗaukar sababbin ma'aikata shine wani abokinsa da ke da connection da ɗa mai kamfani ya ce ya kawo CV ɗinsa zai kai wa abokin nasa ya taimaka masa. Yanzu nan yana kwance ya kira shi shine dalili tashinsa da sai 12 noon zai tashi Jeeddah ta kalle shi da wani mamaki a saman fuskarta kafin ta ce "Lafiya na ganka cikin shirin fita?"
   Sai da ya zauna kusa da ita kafin ya bata amsa ta hanyar cewa "Ina labari da na ba ki kwanaki baya ana neman sababbin ma'aikata a wani kamfanin tomatos shine Rasheed ya kira ni yace na kawo masa CV na.
   "Haba banza bata kai zomo kasuwa.
Jeeddah ta faɗa tana rufe mishi bottoms ɗin wuyar rigarsa.
Sai da ya kai mata kiss a laɓɓanta kafin yace
  "Me kike nufi?"
Ya ƙarashe magana yana harararta.
'yar dariya tayi gami da faɗin "Love kai da idan ka fara bacci sai ka hantse sai gashi ka tashi 10 o'clock dole nai mamaki ashe da walakin goro a miya.
Shima dariya ya yi tare da riƙo hannunta yana faɗin "Tuntuni na fahimci bacci nan nawa yana ƙona miki rai In-sha-Allahu da zarrar aiki ya samu sai kin nemi ni da kuɗinki ba ki ganni ba.
   Itama hararar wasa ta galla masa tana faɗin "kar ma ka fara Love don wallahi ba zan lamunci nesa da kai ba. Har kasa na fara jin tsanar aikinan tun kafin a sami shi, ni fa duk abinda zai nisanta ni da kai ba sonshi nake ba.
Jin abinda ta faɗa yasa dariya ta kama shi yana dariya ya ce "Ba ke bace kullum sai ki yi min korafi Love duk ka murje min bedsheet, Love ka tashi haka nan zan yi shara, anya kuwa Love ba ka da basir wannan baccin naka ya yi yawa ko ba haka kike faɗa ba? Yanzu kuma kin ga zai bar ki tsaron gida kamar yadda kike saba barina shine za ki fara wani zance na daban.
Turo baki gaba tayi tana ƙara zabga mishi harara ya miƙe tsaye da murmushi saman fuskarshi yana cewa "Ni dai na tafi saboda naga kina so ɓata min lokaci al'hali ƙarfe 10:30am mu ka yi appointment za mu haɗu da Rasheed.
Ya ƙarashe magana tare da nufar ƙofar fita "a dawo lafiya Allah yasa adace.
Ta faɗa tare da binshi da kallo.
  "Ba za ki yi min rakiya ba kou?"
"Ba ka ga kaina nake tsifewa ba?
"Ban gani ba.
Ya faɗa a takaice dariya kawai tayi gami da cewa "I love you Love!
Dai-dai yana kama handle ya juyo yana fara'a ya ce "I love you more baby girl.
Ya ƙarashe magana gami da yi mata blowing kiss ya ja ƙofa ya fita. Da iso wajen machine ɗinsa ya shiga lalluɓe aljihunshi bai ji key ba yana batun komawa ciki sai ga Jessica ta fito daga apartment ɗinta jikinta sanye da boomshort haɗe da wata fingilalliyar riga mai ƙaramin hannu tun kafin ta ƙaraso wajen shi ta fara zuba murmushi "Good morning oga Shattima yau kuma me ka manta dashi?"
Dariya ya yi saboda sau da dama suna cin karo da juna idan za su fita, tana kuma lura da duk lokacin da zai fita sai ya yi mantuwa. Kasancewar ta mace mai son raha da wasa yasa suke shiri sosai da Bilal saɓani Jeeddah da ke jin shegen haushinta gani yadda take shisshigewa Bilal shiyasa ko kaɗan basa shan inuwa ɗaya.
  "Kin ganki kou Jessy?" Gaskiya kina samin ido da yawa fa ko ina ruwanki da abinda na manta infact kema jiya da safe da za ki fita jogging ai mantawa kika yi da wayarki.
Jin abinda ya faɗa yasa ta tintsire da mahaukaciyar dariya dama ita abin dariya baya mata kaɗan Jeeddah taje ta dauki comb da ta ajiye a gefenta sai kawai taci karo da key ɗin machine Bilal, tayi murmushi tare da faɗin "Oh! Love sarkin mantuwa ji duk uban sauri nan da yake yi ya manta da key machine ɗinsa kuma gashi banga ya dawo nemansa ba.
Can kuma ta ce "maybe yana can waje yana wahala nema al'hali anan ya bar shi.
Sai kawai ta tashi da sauri ta ɗauki hulata tasaka ta nufi ƙofar fita ta buɗe, da buɗewarta ta ci karo da abinda ya ye ganinta ya kuma haddasawa zuciyarta bala'in bugawa Bilal da Jessica ta gani tsaye daff da juna sai hira da kwasar dariya suke yi da dukkan alamu duniya tai musu daɗi bata tsaya wata-wata ba ta juya da mugun ƙarfi ta nufi kitchen ko gabanta bata gani sosai, ta shiga dube-dube kamar mahaukaciyar sabon kamu can idanuwanta suka faɗa kan saitin wuƙaƙenta, hannunta yana rawa ta zari ɗaya daga cikinsu wacce bata taɓa amfani da ita ba sai kyali take, ta koma juyawa ta nufi ƙofar fita har ta dawo Bilal Shattima da Jessica na tsaye inda tabarsu yanzu kuma wani abu take nuna masa a wayarta. Sai kawai Idanuwan Jeeddah suka shiga ƙawata mata hannun Bilal rungume da ƙugun Jessica, kasancewar sun shagala da kallon wayar yasa ba su ji lokacin da ta iso wajensu ba. Cikin fitar hayyaci ta buge wayar Jessica ƙirar iPhone 11 pro max cikin sa'a wayar ta buge interlock, daga Bilal har Jessica wayar suka fara bi da kallo gaba ɗaya ta tarar ratse kafin suka dawo da ganinsu kan wacce tai ta'asar tana tsaye ƙiƙam! Tana aika musu mugun kallo wata uwar ƙara Jessica tayi tare da ɗora dukkan hannuwanta akai, kafin ta gama jimamin wayarta ta ji saukar tafin hannu akan kumatunta. A tsorace Bilal Shattima ya kai dubansa kan Jeeddah. Sai uban huci take zubawa kamar kububbuwa cikin ƙarfin hali da nuna mazantaka ya daka mata tsawa "Ke Jeeddah miye haka kin yi hauka ne me tayi miki da za ki fasa mata waya sannan Kuma ki bi ta har da tukuicin mari?"
   "Uban da kake yi rungume da ƙugunta tai min idan ranka ya ɓaci don na mari karuwarka sai ka zo ka rama mata.
Ba wai Bilal Shattima kaɗai maganar Jeeddah ta girgiza ba har Jessica sai da ta zaro idanuwa cikin kaɗuwa.
  "Jeeddah kina da hankali ko kuwa iskokai ne suka taka akanki, don ko kusa wannan maganar da ta fito bakinki bata yi kama da ta mutane masu cikakken hankali ba?"
   Bilal Shattima ya faɗa da zallar mamaki shimfiɗa akan fuskarshi, ai kuwa ba ƙaramin haushi ya ba Jeeddah ba. Sai ta ƙara harzuƙa idanuwanta suka ƙara rufewa wani irin bala'in kishi ke nuƙurƙusar zuciyarta, ta rasa ma ta ina za ta fara cin uban Bilal da Jessica don kuwa suna son su zo mata da reni hankali, ba kuwa irinta za ai wa haka a zauna lafiya ba. Sai kawai ta ayyanawa zuciyarta ta yankawa Jessica wuƙar hannunta duk abinda zai faru ya faru koda bata mutu ba za ta barta da tabon da duk lokaci da ta kalle shi sai ta tuna da ita. Tana gani shi kaɗai ne irin hukunci da take ji indan tai mata za ta sami sauƙi raɗaɗin da zuciyarta ke mata. Ba tare da Jessica ta ankara ba ta ji yankar wuƙa ga damtse hannunta, da ta fasa wani iri ihu mai haɗe da barazanar fasa dodon kunnen mutane unguwa tasa ɗayan hannunta ta dafe gun da Jeeddah ta yanka.
Dai-dai Jeeddah tana yunkuri sake yankarta Bilal Shattima yai kukan kura ya cukume ƙungunta suka shiga kokawa, da kyar yai nasarar karɓe wuƙar. Bai yi wata-wata ba ya ɗauke ta da bahagon mari zafin mari ya ratsa ƙwaƙwalwarta take ta dawo cikin ainihin hankalinta. Sai kawai ta kafe shi da idanuwanta da suka canza launi, yayin da tasa tafin hannunta ta dafe kunce ta da ya mara kasa ɓoye mamakinta tayi cikin dassahiyar murya ta ce "Bilal ni ka mara saboda karuwa 'yar iska wacce ke bin kwararo-kwararo lungu-lungu tana rabawa kare da doki gindinta?"
  "Hey-hey...stop calling me karuwa, ni ba karuwa bace.
Jessica ta faɗa cikin fusata da alamu wannan kalma tafi ci mata rai fiye da marinta gami da fasa mata waya da Jeeddah tayi fahimtar hakan da Jeeddah tayi yasa ta taso mata kamar zararriya tana cewa "Na faɗa don ubanki shegiya useless prostitute ashawo.
  Kafin Jessica tai wani yunkuri mutane gidan suka firfito, sai abin ya koma ɗan ƙaramin morning show idan Bilal ya ja Jeeddah neighbours su ja Jessica yayin da bakin Jeeddah yaƙi mutuwa sai surfa mata manya-manyan zagi take yi "Shegiya baƙar karuwa mai ruɓaɓɓe gindi duk randa na ƙara ganinki kusa da mijina sai naci uwar ubanki.
Itama Jessica tana mayar da martani.
   "Ke tafi can mai baƙin kishi ba abinda ta iya sai kishi muna nan dake sai mijinki ya ƙaro aure, mu ga ƙarshen kishin naki. Banza jahila kuma ki sani na raga miki ne saboda oga Kabeer da mijinki da wallahi-tallahi ko Inuwanta ba za ki yi gigi taɓawa ba.
Kafin Jeeddah ta bata amsa Bilal ya tura ta apartment ɗinsu ya ƙargame ƙofa. Sai dukan ƙofar take yi tana ci-gaba da zage-zage. Yayin da mutane gidan mamakinta ya kusan kashe su officer Abdul-ganiyu da Bilal suka kai Jessica hospital sai da aka yi mata ɗinki. Bilal yai mata alƙawari zai biya ta wayarta ko da me zai biya ta oho. Da yake Jessy na da hankali ta ce ta yafe amma tabbas sai ta faɗawa Ya Kabeer gara ya zo yai musu iyaka da Jeeddah, domin ba zamanta take yi a gidan ba. A gani Jessy Jeeddah taci mata zarafi ne kasancewar tana haya a gidan ubanta, idan Ya Kabeer bai ɗauki mataki ba za ta bar musu gidansu. Saboda bata saba da wannan haukar ba.
Jeeddah ta gaji da dukan ƙofa ta zube akan tiles sai lokaci ta sami damar rushewa da kuka, zuciyata sai raya mata take yi Bilal Shattima ya jima yana neman Jessica yau ne dubunsu ta cika abinka da mace mai baƙin kishi sai imagination take yi yadda suke Kasancewa tare da juna. Gaba ɗaya ta haddasawa kanta rashin natsuwa, ta tashi hankalinta cikin ƙanƙani lokaci ta dawo zararriyar ƙarfi da yaji. Idanuwanta duk sun kumbure saboda kuka. Maƙoshi da laɓɓanta suka bushe ƙamass...jiraye take da Bilal Shattima ya dawo yau ko shi ko ita a gidanan don ba za ta taɓa lamunta cin amana irin wannan ba. Har azhar tayi Bilal Shattima bai dawo ba tana dubi bayan la'asar ya dawo nan ma shiru wai malam yaci shirwa. Ta gama sallar isha'i kenan tana zaune akan praymat ta zabga ɗan uban tagumi taji ana knocking on kuma har izuwa lokaci bata ci komai ba ga 'yar uban yunwa tana ji bala'i da azababben kishinta ya hana mata taci abinci, ko wanka jikinta kasawa tayi hatta da kayan da ke jikinta tun safe sune a jikinta ta kasa canza su, iyaka idan za ta yi sallah ta ɗora zani akai.
Yanzu kuma ta ji knocking ta miƙe a mugun fusata ta nufi ƙofar domin ta tarbe Bilal Shattima da ruwan masifar da ta tanadar masa.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA
  
   *Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku ta karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune Kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya kacal_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

018...

Washe gari lafiya lau sun ka tashi tamkar saɓani bai taɓa shiga tsakaninsu ba. Sai nunawa junansu soyayya da tattali suke yi. Tana gama haɗa breakfast tayi wanka ta shirya cikin atamfar Hollandais vlisco ɗinkin skirt and blouse, kitso take so ta je gidansu Bilal Shattima A'isha Shattima tayi mata dama tun can asali ita ke mata kitso ko aure da tai bata canza ta ba. A dalilin hannun A'isha Shattima ya karɓeta sosai ta taɓa gwada sauya kitso wurinta gashinta ya fara karyewa dole ta dawowa gunta. Tana gama shirinta ta nufi kan gado inda Bilal Shattima ke lulluɓe cikin bargo yana sharar bacci sai ɗan ƙaramin minsharinsa ke tashi, sai da ta fara galla masa harara kafin ta ja bargon jikinsa ta yaye shi tare da ta linkewa ta ajiye shi a gefe kana ta hayo gadon dai-dai saitin kunnenshi ta ɗora bakinta ta kira sunanshi da ƙarfi "Bilallll!
A mugun firgice ya tashi zaune yana murtsuka idanuwanshi yayin da Jeeddah ta tintsire da dariyar ƙeta, nan take ya ƙarasa wartsakewa ya fizgota da ƙarfi ya shigar da ita jikinsa ya matse ta sosai sai ihu take tana mishi magiya "wayyo Allah kwalliya ta Love za ka ɓata min kwalliya please ka kyaleni.
   "Ba zan kyale ki ba sai kin biya tashina da kika yi infact kece kika jawo na ɓata miki kwalliya akan wane dalili za ki yi min ihu irin wannan a kunne wato so kike ki fasa min dodon kunne kou?"
Ta marairaice murya ta dawo kalar tausayi ta ce
  "Dan Allah ka yi haƙuri Love so nake ka tashi kayi wanka za ka kaini gida wurin kitso inaso naje da wuri saboda har lalle za ai min.
A kasalance ya ɗagota gami da zare ta daga jikinshi yana faɗin "Gaskiya Jeeddah ba ki da kirki yanzu saboda kitso da lalle ina cikin baccina mai daɗi za ki tashe ni.
Saukowa tayi daga kan gado ta ja hannuwanshi gami da faɗin "to ai kaine za a yi wa kwalliya saboda haka dole ne yau ka haƙura da bacci nan naka da baya ƙarewa.
Ba yadda ya iya tun da ta sako shi a gaba dole ya miƙe ya shiga wanka koda ya fito har ta kimtsa gado, a gaggauce ya shirya cikin brown colour filtex material a dining room ya tadda tana jiranshi su yi breakfast su na gama breakfast ta ɗauko handbag ɗinta. Shi kuma ya fito da machine tana cikin rufe ƙofa sai ga Jessica ta fito daga apartment ɗinta da plaster a damtse hannunta inda Jeeddah ta yanke ta da akayi mata ɗimki, a ɗan tsorace Bilal Shattima ya saci kallonta kafin yai maza ya dawo da ganinshi kan Jeeddah wacce ta kammala rufe ƙofa ta zare keys, ta nufo wajensa hango Jessica da tayi yasa ta murtuƙe fuska ta wani ɗauke kai tana zuwa ta ce "Mu tafi malam naga kana wani muzurai kamar marar gaskiya.
   Ɗan tari ya yi yana wani gyaran murya kafin cikin kwantar da murya ya ce "Love za ki yi min wata alfarma indan na tambaya?"
Wani kallon tai masa kafin ta taɓe baki gami da cewa "faɗi alfarmar taka kuma Allah yasa zan iya don ni ba kowace alfarma nake iyawa ba.
  Shiru ya yi sai faman shassafa kwantatce sajensa yake yi, alamar yana jin tsoron furta abinda ke ranshi.
  "Love ya ka yi shiru ka yi magana mana na faɗa maka sauri nake yi, kai kuma sai ƙoƙarin ɓata min lokaci ka ke yi wallahi banaso na rasa lalle nan gashi ƙarfe 11:00am muka yi alƙawari da mai lalle ɗin ta ce min tana da amare da za ta yi ma.
Sai da ya kauda fuskarshi don ba zai iya haɗa idanuwa da ita ba kana ya ce "Inaso da amincewarki mu je mu yi ma Jessy sannu da jiki, kinga abinda ya faru da ita ke ce sila kuma bai dace ba mu ganta mu wuce batare da mu tambaye ta jikinta ba.
A razane Jeeddah take kallonshi sai yau ta ƙara tantance reni wayau Bilal Shattima na musamman ne. In banda ya gama rena mata wayau zai wani nemi alfarmar zuwa gun wata ko wata wacce a yanzu ba wanda ta tsana sama da ita saboda haka a mugun fusace ta kalleshi ta ce "Ga hanya nan Bilal Shattima ai ba dabaibiya nai maka ba balle ka nemi alfarmata, kana da 'yanci yi duk abinda kake so Jeeddah bata isa ta hanaka ba je ka kawai abinka.
  Sani ya yi har gaba da abada ba za ta taɓa amincewa buƙatarsa ba. Muddin ya ce sai da amincewarta to tabbas ba zai yi abinda yake gani shi ne daidai ba, shiyasa bai ƙara tanka mata ba ya kafe machine ɗinsa ya nufi wajen Jessica.
Jeeddah wani abu taji ya daki zuciyarta tabi Bilal Shattima da idanuwa, fahimtar tayi idan ta sake furta wata kalma daga bakinta ba abinda zai hanawa zuciyarta bugawa saboda haka ta juya cikin sassarfa ta nufi gate ta tura ƙaramar ƙofa ta fita yadda ta maida ƙofar da ƙarfi ta rufe yasa Bilal Shattima waigawa hakan bai sa shi fasa tunƙarar wajen Jessica ba. "Jessy ya hannunki hope kin ji sauƙi?"
Ya faɗa sa'ili da isa wajen Jessica sai da Jessy tai murmushi kafin ta ɗauke idanuwanta daga kan gate ɗin da Jeeddah ta fita, kana ta ce "Na ji sauƙi sosai oga Shattima.
  "Thank God! Allah ya ƙara sauƙi za mu fita zan kai madam gida.
Bilal Shattima ya faɗa yana sake kallon ƙofar da Jeeddah ta fita.
"ALLAH ya kiyaye hanya.
Jessica ta faɗa tana murmushi.
Daga haka Bilal Shattima ya juya ya tashi machine ɗinsa ya fice koda ya fito Jeeddah har ta kusan kai bakin titi ya ƙara speed ya cimma ya taka birki a gabanta ya ce "Love shi ne kika yo tafiyarki ba ki tsaya jirana ba kou?"
A mugun fusace ta kalleshi kana tai kwafa gami da faɗin "Ai ni ba gantalalliya bace da zan tsaya ɓata lokacina ina zaman jiranka sai kace kaine mutum na ƙarshe da ya rage a duniya mai abin hawa.
  Duk da ya ji zafin maganarta sai kawai ya yi ƙoƙarin danne zuciyarsa ta hanyar kwantar da murya ya ce "Allah ya ba ki haƙuri ni banaso fitina zo ki hau mu tafi kada ki rasa lalle ƙarshenta ni za ki ɗorawa laifi.
   Sai da ta kalleshi ta watsar kafin ta ce "wallahi da na hau machine ɗinka gara na taka daga nan har gida a ƙafa.
Sororo ya yi yana kallonta kafin ya yi murmushi mai kama da na yaƙe ya ce "Da nai miki laifi me da za ki ce ba za ki hau machine ɗina ba naga dai lafiya lau muka fito daga gida?"
   "Ka ga Bilal Shattima karka nemi ka rena min hankali ni ba ƙaramar yarinya bace da zan kasa fahimtar manufarka ba....
"Dallah Jeeddah dakata!
Ya katseta cikin tsawa yanzu kam ya kasa controlling temper ɗinshi rai ɓace ya ci-gaba da faɗin "Ke wacce irin Fitinaniyyar mai rai ce? Duk yadda mutum ya kai da danne zuciyarshi akanki sai kin kai shi bango, kwata-kwata lamarinki ba kishi bane tsabagen reni wayau ne kawai da samun wuri. Ki zo ki hau machine mu tafi tun kafin raina ya gama ɓaci na nuna miki nawa kalar rashin mutunci.
  "Mtsssss....! Aikin banza wai kai kana tsammani wannan buyagi naka zai sa na hau machine ɗinka, ashe kuwa kana da sauran sani akaina.
Mamaki ne ya lulluɓeshi sai kallonta yake da baki buɗe, ta raɓa gefenshi ta tai tafiyarta yana gani tana ƙoƙarin tsayar da adaidaita yasa shi hanzarin parking machine ɗinshi. Yana zuwa wajenta bai yi wata-wata ba ya Riƙo hannunta tare da fizgota cikin ɓaci ran da bai taɓa ji irinsa ba ya ce "Enough is enough Jeeddah nagaji wallahi-azim na gaji da wannan mugun halin naki mekika ɗauke ni ne humm?" Sakarai ko mahaukaci ko kuma wanda bai san ciwon kanshi ba. Faɗin wannan kallo kike min daga cikin sunayen nan da na lissafa?"
Ya ƙarashe magana yana wani irin huci don shi ma Bilal Shattima mugun hot temper ne dashi, idan kuma yai fushi ya kan zama out of control idanuwanshi gami da zuciyarshi rufewa suke yi sai aikata abu ya dawo daga baya yana regretting.
   Itama goganyar taku ba baya ba saboda haka yadda taga ya fusata ko a jikinta, sun manta da suna kan hanya a bakin titi kowane su bala'in da masifa nacinsa. Cikin ɗaci rai ta fincike hannunta daga riƙo da yai mata kafin ta ce "Duk wannan ihu da tada jijiyoyin wuya da kake yi ba shi zai sa na hau machine ɗinka ba. Idan kuma har da gaske kake yi ka gaji dani ba sai ka ɗauki mataki ba. Wallahi gara na haƙura da fitar nan yafi  min da na hau bayan machine ɗin mayaudari irinka wanda bai san girman alƙawari ba.
  "Muddin ba za ki hau machine ɗina ba sai dai ki fasa fitar kuma ki sani duk randa kika kaini bango idan na shukka miki rashin mutunci duk zuri'arku ba za su iya taimaka miki wajen nome shi ba. Ki yi a hankali domin nima ɗan iskan kaina ne, juya maza ki koma gida kuma ki jira za ki ga abinda zai biyo baya, ba dai taƙamar ki rashin ɗa'a ba? To ni ne nan maganinki mahaukaciyar banza mai mahaukacin kishi.
   Cabdijam! Tun Lokaci da Bilal Shattima ya fara zari Jeeddah tai sanyi sai aikin kallonshi take yi,  bata taɓa tsammanin ya iya zari har haka ba. Saboda kafin sun yi aure muddin tsau-tsayi ya gitta ta ganshi da wata mace koda 'yar uwarsa ce, haka za ta saka shi a gaba ta ƙare masa rashin ɗa'a iyakacinshi yai ta bata haƙuri. Ashe kallon kitse take wa Rogo Bilal ɗin da take wa kallon salihi ba ruwanshi sai gashi yau ya shayar da ita zallar mamaki.
   "Wai uban me kike jira ne da kika yi tsaye kina zare ido, wuce ki koma gida daga yau na kashe zuwa kitso da lalle?"
Tsakani da Allah na tsorata matuƙa da jin fitar waɗannan zafafan maganganu daga bakin Love ɗina, ban ƙara shiga firgici ba sai da naga ya zaburo kamar zai doke ni. Babu shiri na juya da mugun sauri na nufi gida, ina shiga parlour na zube ƙasa nasa kuka mai sautin gaske "wai dan Allah dama haka aure yake yau farin ciki gobe akasin hakan ko kuma nawa ne ya zo da haka duka-duka yaushe muka yi aure da za a ce mun fara samun saɓani irin wannan?" Ni dai gaskiya nasan banda laifi ko kaɗan ko manafuki ɗan ƙasan wuta ba zai ce nayi laifi ba don kawai na nuna ina kishin mijina duk mace da tasan kanta dole tai kishin abinda takeso ashe nuna kishi wa abin ƙaunarka zai zama illah?
Ina ci-gaba da rare kuka ina wannan zance zuci don kuwa wani sashe na zuciyata har gaya min yake yi "Daina wahalar da kanki Jeeddah dama can Bilal Shattima ba sonki yake yi ba ki ce kika liƙe masa, shiyasa ya ke wulaƙantaki son ranshi.
Bilal Shattima yana gani Jeeddah ta koma gida cike da takaicinta ya ja machine ɗinsa ya ƙara gaba, da gangan ya ƙi komawa gida kaitsaye shagon abokinsa Abbas ya nufa, yana zuwa ya zayyane masa hali da yake ciki kasancewar baya ɓoyewa Abbas duk wani abu da yafe shi.
Cike da takaici Abbas ya buɗe bakinsa ya ce
  "Ka gani kou Shattima dama tun farko sai nai maka gudun irin haka, gashi nan aure duka wata uku kacal har kun fara samun saɓani Ina dalili wannan masifar?"
Abinda nake so ka sani Shattima mace mai baƙin kishi irin Jeeddah za ta iya kashe mutum, har lahira gara kayi taka tsantsan da lamarinta.
Harara Bilal ya gallawa Abbas sosai ya ji zafin maganganunshi akan Jeeddah a hasale ya bashi amsa ta hanyar faɗin
   "Subhanalillah...haba Abbas wannan ai mugun fata ne kake mata, Inaso Jeeddah kuma In-sha-Allahu har na koma ga Ubangijina ba zan mata kishiya ba wannan alƙawari na ne.
'yar bazawarar dariya Abbas ya yi gami da faɗin "Kai dai gaskiya ce ba kaso a faɗa kaima kasan da cewa Jeeddah za ta iya kisan kai akanka don gashi nan ka fara gani alama tun da har ta iya yankawa neighbour ɗinku wuƙa, ba fata nake maka ba amma muddin ba kayi saurin taka mata birki ba kaine next.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA
   
   *Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku ta karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya kacal_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina 300
Da bansan asalinta ba ₦250

019...

"Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Haba Abbas wannan wacce irin magana ce miyasa za ka dinga jifar matata abin alfahina da munana kalamai irin wannan?" To gaskiya banaso ka daina.
Bilal Shattima ya faɗa da alamu ranshi ya ɓaci da furuncin da Abbas ya yi akan Jeeddah. Fahimtar hakan da Abbas ya yi yasa yai saurin gyaran zancensa ta hanyar cewa "ALLAH ya ba ka haƙuri Shattima ni ban faɗin wannan maganar don ta ɓata maka rai ba na faɗa ne domin ka yi wa tufka hanci gudun abinda zai iya faruwa anan gaba. Amma naga alamar kamar ranka ya ɓaci ka yi haƙuri mu ajiye wannan chapter a gefe mu ɗauko wata kawai.
   "Da yafi gaskiya don ba abinda ke saurin taɓa ni irin na ji ana aibanta matata duk mace da za ta amince ta aureka bakada aikin fari balle na baƙi ta kuma ɗauki responsibilities ɗin kanta da naka ai ba abar zagi bace, wallahi abokina tun daga ranar da mu kayi aure da Jeeddah ta damƙa min ATM card ɗinta da zarrar an yi salary zan fitar da kuɗin albashin nata nayi duk yarda naga dama dasu bata taɓa tambayata ya nayi da ƙudinta ba. Hakazalika ko 'yan uwanta suka bata kuɗi sisi Kwabo ba za ta taɓa a ciki ba ni nake saka su gaba nayi yadda nakeso. Yanzu yaushe rabonka da ka ji nayi maka kukan rashin kuɗi?" Saboda haka Jeeddah tana da daraja da ƙima a idanuwana tayi min hallaci da ba kowa ce mace ce za ta iya ba. Shiyasa duk abinda take yi nake ɗaga mata ƙafa, domin mugun son da  take min ne ke haddasa mata zazzafan kishina.
Wani irin kallo Abbas yake masa kafin ya ja iska daga ƙofufin hancinshi kana ya fesar yace
   "Huhmm..lallai da sauran rina a kaba bari ma na tambaye ka Shattima shin Jeeddah kake so ko kuma abin hannunta, domin ni gaba baki ɗaya ka ɗaure min kai da waɗannan dalilai naka masu ɗan karan ban haushi?"
  "Wannan Wacce irin tambaya ce Abbas? naga dai duk mutumin dake tare da ni zai iya bada gasasshiyar shaida akan irin tsintsar so da nake mata. Balle kai da kake close friend ɗina duk wani sirri nawa ka sani domin bana ɓoye maka duk abinda ya shafe ni.
   "Amma Shattima dole nai maka wannan tambaya ba ni ba kowaye yaji yadda ka taƙarƙare  gaba gaɗi kana furta wannan maganar dole zai yi hasashe irin nawa. Ni fa ina guje maka kwaɗayi abin hannu mace wallahi ba a cin dukiyar mace a kwashe ta daɗi. Shawarar da zan baka daga kai har ita Jeeddah so ne ya haɗa ku saboda haka ka dinga nusar da ita illar da ke tattare da mugun kishin nan nata, domin gujewa faruwa wata gagarumar matsala anan gaba. Sai kuma magana ta gaba Shattima ni a ganina kamar kana shiga hurumin da ba naka ba domin ba kai ke tsarawa kanka rayuwa ba. Rubuta ƙadddarar mu ba a tafin hannunmu take ba balle ka dinga alƙawantawa Jeeddah ba za ka yi  mata kishiya ba. To idan ALLAH subhanahu wata'ala ya ƙaddaro maka auren mace fiye da ɗaya shin ya za ka yi kenan?" Wannan alƙawari ba daidai bane dan Allah ka daina ɗora matarka akan gurɓatatciyar turba da bata da tabbas ka ɗaure ka cire son zuciya ka nuna mata komai muƙaddari ne daga Allah. Sannan kuma ka dinga kauda kai daga abin hannunta gudun wulaƙanci.
  "Shikenan Abbas zan yi iya ƙoƙarina na gani na lurar da ita amma kasani zuciya da yanayin imani ɗan adam shi kesa ya ɗauki alƙawari ya karya ko kuma ya cika shi, ni kan na yarda da kaina In-sha-Allahu in dai ba mutuwa Jeeddah tai ba bani ba ƙara aure. Sannan kuma da kake zance abin hannunta Jeeddah fa matata ce  duk abinda ta mallaka ina da iko akansa da kai da kaya duk mallakar wuya ne.
Kallonshi kawai Abbas ya yi tsabar takaicinshi ya hana shi sake yin magana, sai kawai ya ja bakinshi ya ɗinke.
Kuka sosai Jeeddah tayi ita kanta tanaso ta dinga sarrafa kishinta musamman da ta fahimci kishin nata shine silar da ke haddasa musu rashin jituwa ita da Love ɗinta. Sai dai ta rasa ta ya za ta fara controlling kanta. Wayarta da ke cikin handbag tai ringing ta tashi daga inda take ta nufi jakkar da ta wulgar akan tiles ta ɗaukota ta dawo ta zauna inda ta tashi ta ciro wayar, A'isha Shattima ce ke kiranta cikin sanyi murya tace "Hello A'isha!
   "Jeeddah ya haka tun ɗazu mai lalle nan ta zo tana zaman jiranki ko kin fasa taho wa ne tai tafiyarta?"
   "A'isha in zai yu ko zo tare gidana tayi min.
Yadda A'isha Shattima ta ji muryar ƙawarta ta tasan akwai matsala, saboda haka tana kashe waya ta shirya cikin sauri ta nufo gidan Jeeddah ɗin. Koda A'isha Shattima ta iso Jeeddah tana bedroom ta nunawa mai lalle wurin zama a parlour kana ta wuce bedroom zaune a gefen gado ta tarar da ita idanuwanta sun yi luhu-luhu alamun tasha kuka har ta gode ALLAH.
   "Subhanalillah.....Jiddo me ya faru ne naga idanuwanki sun jajir alamun kin yi kuka?"
Ajiyar zuciya Jeeddah tayi gami da cizon leɓenta hawaye na kara-kaini akan kumatunta cikin muryar kuka taba A'isha Shattima ainihin labari abinda ya wakana tsakaninta da Bilal Shattima. "Ni Wallahi A'isha gidanmu zan tafi na fara gajiya da halin ɗan uwanki.
Jeeddah ta ƙarashe magana sabbin hawaye ba bin kumatunta.
   Kasancewar A'isha Shattima tasan halin mutuniyarta ta da mugun kishi, shiyasa ko kaɗan bata yi mamaki abubuwan da ta aikata ba saboda ta kwana da sani fiye da hakan ma za ta iya. Cikin kwantar da murya A'isha Shattima ta shiga bata shawarwari gami da 'yar nasiha ta hanyar cewa "Haba Jeeddah yanzu da hankalinki da wayaunki za ki bari wata matsala ta kunno kai a cikin zamantakewar aurenku. Kishi halak ne domin ko matan Annabawa Allah sun yi amma ba irin wannan naki ba, idan kika ci-gaba da nuna wannan hali naki to ki sani za ki waye gari soyayyarki za ta ficewa Ya Bilal a zuciya domin kin kasa bashi kulawa da kwanciyar hankali da kowane namiji yake mafalkin samu daga wurin matarsa. wallahi-tallahi Jeeddah Ya Bilal yana sonki yana miki wani irin so da fatar baki ba za ta iya misalta shi ba kema shaida ce akan haka. Saboda haka ki daina zarginshi domin zargi yana ɓata aure. Dan Allah Jeeddah ki tattare wannan zazzafan kishin naki ki watsar dashi ki rungume mijinki kada ki bari wannan dalili ya kawo ɓaraka a tsakaninku akwai da yawan mutane da suka sa muku ido abu kaɗan suke jira ya ɓullo su yi muku dariya, kinsan dai yadda aka yi aurenku. Ki yi duba da ƙanwarki Khairat tun da aka yi aurenku kin ji wani saɓani ya shiga tsakaninta da mijinta?"
Girgiza kai Jeeddah tayi A'isha Shattima ta ci-gaba da cewa "saboda haka ki rufawa kanki asiri zance za ki tafi gidanku bai ma taso ba. ki koyi yadda za ki dinga magance matsalolinki ba tare da kin fitar da sirrin aurenki waje ba. Yanzu tashi za ki yi mu je parlour ayi miki lalle na rangaɗa miki kitsonki, koda Ya Bilal ya dawo ki nuna masa komai ya wuce ki ba wa mijinki haƙuri domin ke ce ƙasa dashi.
  Doguwar ajiyar zuciya Jeeddah tayi tare da sa bayan hannunta ta goge hawayenta, gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi tabbas duk abinda A'isha Shattima ta faɗa babu ƙarya a ciki. Jikinta a mace ta tashi ta shiga bathroom ta wanke fuskarta ta fito cikin ƙanƙani lokaci aka kammala mata jan lalle hannuwa da ƙafafuwanta kana A'isha Shattima tai mata kitso sai bayan la'asar A'isha ta wuce gida kafin ta tafi sai da ta ƙara jaddadawa Jeeddah ta daina biyewa duk abinda zuciyata ta ayyana mata.
  Ko kaɗan Bilal Shattima bai yi marmari dawowa gida ba hatta da abinci gidan Abbas suka je ya cika cikinsa, kana da yamma suka taho zaman majalisa wanda ya zame musu jinin jiki. Tun zuwansu majalisar abokansu masu mata bibbiyu ke tsokanar Abbas dama haka ɗabi'arsu take idan kana da mata ɗaya sun dinga yi maka sharri kala daban-dabam kenan. Gami da zuga ka da ka ƙara aure koda kuwa bakada ra'ayi har sun cusa maka ra'ayi abin a zuciya to yau ma haka ce ta kasance daga zaman Bilal da Abbas, Rasheed ya fara cewa da Abbas "mai mata guda aminin gwaro haka kawai da ranka da lafiyarka Abbas ga kuɗi Alhaji ga wadatatce muhalli amma ka buge da zama da mace guda sai kace mai bakin uwa.
  Gaba ɗaya masu mata bibbiyu a wuri suka Kwashe da dariyar  shaƙiyanci sosai dariyar tasu ta ɓatawa Abbas rai saidai bashida yadda zai yi ya gwada neman aure yaso ya aure Asiya yana sonta tana sonshi haka kawai aka waye gari iyayenta suka kafe akan lallai sai 'yarsu tayi karatu a nursing school, shi kuma ya ce matarsa ba za tayi karatu ba. Shine suka rabu amma duk da haka kullum da irin sharrin da abokansa ke masa.
Murmushi mai cike da zallar takaici Abbas ya yi gami da faɗin "Surutunku ba zai harzuƙa ni ba naje na kwasowa kaina kara da kiyashi kamar yadda Sadik ya yi.
Abbas ya ƙarashe magana yana kallon gafen da Sadik yake zaune riƙe da mug ɗin black tea a hannunshi yana sipping, da sauri Sadik ya ajiye mug ɗin yana faɗin "A'ah yau ga iskanci banza da wofi ka rasa shegen da za ka buga misali dashi sai ni, to ba gara ni na ɗanɗani zaƙi da garɗin mata biyu ba kai fa?"
Dariya sosai suka kwashe da ita a wannan karon Bilal Shattima ne ya tanka "ka faɗi tsakani da Allah Sadik ɗañɗanawa kawai ka yi amma ba wani zaƙi da garɗi da ka ji.
   "Shattima ka rufe min bakinka idan ana irin wannan zance ka daina tofa albarkacin bakinka saboda kai har yanzu kana da sauran sani a wannan harkar.
   Cewar Sadik yana harara Bilal Shattima, Hisham ne karbi zance ta hanyar faɗin "tsakani da Allah duk mai mata guda anan wuri anbarshi tasha Alhaji bai kwashe romon dimokuraɗiyya ba. Wallahi ku je zuwa ƙara aure sannan ne za ku san kun yi aure amma mace guda kullum fa abu guda ne kacal kayi ta maimaitawa ai sai ya gundire ka.
Habawa yana dasa aya suka sake tintsirewa da mahaukaciyar dariya, sai tafawa suke yi sai kace waɗanda aka yi wa albishir da gidan aljanna.
Kiran sallar magariba ya tashe su daga firar tasu, bayan sun kammala sallar isha'i suka sake dawowa suka dasa sabuwar fira yanzu kuma chapter siyasar ƙasar nan suka buɗe musu da gardama ya kaure tsakanin magoya bayan jam'iyyar adawa sai sukar jam'iyyar da ke mulki suke yi yayin da kuma magoya bayan jam'iyyar da ke mulki, ke ƙoƙarin ƙare jam'iyyarsu. Zuwa wannan lokaci goganyar taku ido ya rena fata, tayi girki na musamman an caɓa kwalliya sai zaman jiran Love ake yi shi kuma yana can majalisar gantalallu yana gantallewa abinsa, sai around 10 o'clock ya waiwaye gida karar machine ɗinsa da ta ji yasa ta miƙewa da sauri ta nufi ƙofar fita daga parlour yana ƙoƙarin shigowa da machine ɗinsa parlour, dama anan yake ajiye shi gudun kada ɗan kande ya sulale mai dashi kallo guda yai mata ya ɗauke fuska, shi a dole fushi yake yi amma a can ƙasan zuciyarsa mugun daɗi ya ji don bai zaci za ta huce cikin sauƙi ba. Yana ƙoƙari gittawa ta gefenta ya wuce ya ji saukar muryarta ta ce "Sannu da zuwa Love.
   "Yawwa!
Amsa mata can ƙasan maƙoshi ya shigewarsa bedroom duk da haka bata yi fushi ba ta sake biyo shi a baya tana faɗin "Love na haɗa maka ruwanka da alamar yau ka kwaso gajiya?"
Bai tanka mata ba sai da ya ƙarasa shiga bedroom yana wani shan ƙamshi gami da hura bututun  hancinsa, a dakile ya ce "Ki barshi kawai nagode zan iya haɗawa da kaina.
  Shiru Jeeddah tayi yayin da Idanuwanta suka kawo ruwan hawaye, ko kallonta bai sake yi ba ya cire kayan jikinshi ya shige bathroom bata yi ƙasa da guiwa ba ta nufi jikin bango bathroom ɗin ta jingina tana jin saukar ruwan wankanshi lokaci zuwa lokaci take goge hawaye. Yana turo ƙofa ya ganta ya tsaye tana sharar hawaye abinka da so duk sai ya ji tayi bala'in bashi tausai amma azahiri bai nuna hakan ba, sai ma sake raɓa ta ya yi ya nufi gaban dressing mirror yana goge jikinshi. Tana gani yadda yake nuna mata halin ko in kula yasa ta sakin kuka mai ɗan ƙaramin sauti, tun tana yi a hankali har ta dawo yi da ƙarfi cikin sauri ya ƙarasa saka pajama ɗinshi ya fesa turare ya nufi ƙofar fita nufinsa ya bar mata ɗakin yana kai hannunshi kan handle ta rugu da gudu ta rungume shi ta baya tana kuka gami da bashi haƙuri tsananin kuka da take yi muryarta da kyar ta ke fita "Dan ALLAH Love ka yi haƙuri na tuba ba zan ƙara ba Dan ALLAH ka yi min uzuri wallahi ba yin kaina bane sonka ne ya yi min yawa shiyasa bana iya control kishina akanka.
Ta ƙarashe magana tare da wani irin gunji kuka. Da sauri ya juyo ya rungumeta gam yana bubbuga gadon bayanta yana faɗin "kukan ya isa haka Love kema kinsan banaso ɓacin ranki dole ce tasani fushi dake ba don raina yaso ba. Muradina ki rage wannan mugun kishin naki.
Ta ɗago idanuwanta ta kalleshi tana goge fuskarta da tafin hannunta, riƙo ta ya yi suka fito parlour.
  "Love mu je ka ci abinci yau favorite food ɗin ka na girka ma.
Ta faɗa cikin muryarta da ke nuni da tayi kuka.
Duk da baya jin yunwa gudun kada ranta ya ɓaci yasa ya washe baki, suka nufi dinning room haka nan ya dinga cusa abinci ba don yana jin yunwa ba sai don gudun kada ya sake tona wata sabuwar fitina.
***** **** ******
A kwana a tashi asarar mai rai gashi har auren Bilal Shattima da Jeeddah ya shigo wata na shidda, yau da daɗi gobe akasin hakan yau fari gobe ɓaki a haka suka ci-gaba da rayuwa, gaba ɗaya salary ta akanshi da mahaifiyarshi da 'yar uwanshi yake ƙarewa ta ɓangaren Babanta duk ƙarshen wata sai ya aiko Abdul yaronshi na kasuwa ya kawo mata foodstuffs, hatta da nama, kifi Baba na monthly yake siyo mata hakazalika 'yan uwanta duk ƙarshen wata sai sun turo mata da kuɗi ta account ɗinta. A dalilin mugun tausayinta suke ji a ganinsu bata tashi cikin rashi ba amma ta buge da aure marar aiki yi, duk ƙarshen wata sai Aunty Farida ta tura mata 20k ko ya Kabeer da baya son aureta 30k yake tura mata hatta da Khairat lokaci-lokaci tana tura mata da kuɗi sai dai kawai taga alert shiyasa gaba ɗaya Bilal Shattima ya tattara neman aiki ya watsar, daga shi har mahaifiyarshi da 'yar uwanshi ba abinda suka nema suka rasa in ka ganshi ya shirga uwar ƙiba yayin da ita kuma Jeeddah ta bi ta rame ta ƙanjame a dalili laulayin ciki da ya sako ta gaba hatta da ruwa indan tasha sai ta amayar dasu, ta dawo yau ciwo gobe lafiya. A gefe ɗaya Bilal Shattima sai wadaƙa da ƙudinta yake yi duniya ta dawo masa sabuwa tsabagen samun wuri hadda canzawa yaran Bahijja biyu school ya ciro su daga government school yasaka su a private.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*
  _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

  *Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku ta karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune Kamar haka*
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

Ina matan da suka amsa sunansu mata ba muna mata ba, gare ku haɗaɗɗun mata 'yan gayu da suka san kansu??
Ku garzayo domin farantawa mazajen ku rai
Ta hanyar ƙamsasa jikin ku da nau'ukan turarukan mu.
Muna da turaren miski mai kyau ɗan Sa'udiyya
Akwai oils perfumes masu dan ƙaren ƙamshi da ɗauke hankali maigida muna da na kamfanonin da suka amsa sunan su irin su :-
Kamfanin
Almas
Surrati
Naseem
Sannan da na fesawa
Kala daban-dabam
Duk a IHSAN COLLECTION'S and More
Muna turawa ko wanne gari 😊😊 domin ƙula hulda kasuwanci damu sai a tuntuɓe a waɗannan lambobin
08036487230
09071926759

020...

Yau tun da sassafe Jeeddah ta tashi sakamakon sauƙin da take ji jikinta yai mata, duk da haka adaddafe ta kammala shirinta na tafiya makarantar da take koyarwa. Kasancewar tayi kusan four weeks bata je ba sakamakon rashin lafiyar da take fama dashi, damuwarta ɗaya principal ɗinsu da ba kasafai yake karɓa uzuri ba. Shiyasa tun jiya da ta ji jikinta ya yi kwari sosai tasa aranta yau za ta je school ɗin musamman da ɗalibai sun kusa su fara third term examination ta kagara ayi hutu kafin a koma cikinta ya shiga four months watakila zuwa lokaci laulayi da take yi zai ragu.
Tana kammala shirinta  ta nufi kan gado inda basaraken nata ke kwance yana aikin nasa na bacci. Cikin kwantar murya ta shiga kiran sunanshi gami da ɗan bubbuga damtse hannunshi "Love.....Love! Na kammala shirina ka tashi ka sauke ni school dan Allah ka tashi mana kada nayi latti.
Ta ƙarasa magana cikin marairaicewa tamkar wacce ta tashe yaron goye tana tsoron kada yai mata kuka.
Ya tashi zaune yana yatsina fuska muninsa ya ƙara bayyana dama mutum mai muni idan ya tashi daga bacci fuskarsa batada kyau gani, hancin nan nasa ya ƙara maƙalewa can sama cikin murya wadda bacci bai wadace shi ba ya ce "wai miye haka ne Love?" ke dai wallahi ba ki ƙaunar ki ganni kwance ina bacci sai kin ƙiƙƙiro dalilai da zai sa ki tashe ni.
   "Ka yi haƙuri Love ba haka kawai na tashe ka ba dama so nake ka aje ni school, kasan rashin  fuel ɗinan da ake yi abin hawa na da matuƙar wahala samu musamman da safe.
  "OMG! Yanzu fissibilillah Jeeddah saboda tafiya school ne yasa kika katse min baccina bayan kinsan na tsani ina bacci a tashe ni?" Yanzu nan sai ki jawo min headache kina wani zance rashin abin hawa kin fita ne ba ki samu ba balle ki yi complaint ki je kawai In-sha-Allahu za ki samu ki jirani zan zo ɗaukar ki.
Ya faɗa gami da komawa ya kwanta har da jan duvert ya lulluɓe jikinsa, sosai ta ji ba daɗi a ranta ta zaci zai yi duba da ba wadatatciyar lafiya ce da ita ba ya kaita school ɗin in yaso idan ya kaita ya dawo ya ci-gaba da baccin nasa. Amma sai taga saɓanin tunaninta, ta miƙe jikinta a sanyaye ta ɗauki handbag ɗinta ta buɗe ƙofa tana dab da fita ta waiga ta kalle shi ya bata baya sai kawai taji zuciyarta ta karaya wani ɗan maraye kuka ya subuce mata, tai sauri maida ƙofa ta rufe gudun kada ta haɗu da ɗaya daga cikin neighbours ɗinsu su ganta tana kuka, ya zama abin tsegumi shiyasa ta gaggauta goge fuskarta da gefen hijabin jikinta. ALLAH ya taimake ta tun kafin ta ƙarasa bakin titi ta sami adaidaita, ƙarfe takwas dai-dai tana cikin makaranta, duk wadda ya kalleta farat ɗaya zai gano akwai damuwa a tattare da ita duk jikinta ya nuna bata da wadatatciyar lafiya amma hakan bai ɓoye damuwar da ta ciki ba. Cikin hukunci Ubangiji har aka tashi bata yi amai ba sai miyau ne kawai da take ta faman zubdawa akai-akai. Daidai inda Bilal Shattima ya saba tsayuwa idan ya zo ɗaukarta ta nufa saidai bata ganshi ba, sai kawai ta fito da wayarta daga handbag tai dialing numbershi wayar tana ringing har ta tsinke bai ɗaga ba. A takaice sai da tai mishi kira da ya kai  goma bai ɗaga ba. Ranta yai matuƙar ɓaci a hasale ta maida wayar jakka kana ta nufi gate ɗin fita duk gaisuwar da maigadi ke mata bata iya amsawa da baki ba sai hannu ta ɗaga masa. A gefen titi ta tsaya tana jiran abin hawa duk adaidaita da ta tsayar yana ɗauke da passengers ko kuma ya ƙi tsayawa sai kace abin magani ga jiri sai ɗibarta yake ga 'yar uban rana na kuɗarta, tun tana iya tsayuwa da ƙafafuwanta har ta zo tsayuwar na neman gagararta gani haka yasa ta soma tafiya a hankali a gefen titi, tana tafe tana tofar da yawu da ke cika mata baki. Tafiya tai mai nisan gaske kuma har zuwa lokaci bata sami abin hawa ba. Wani irin murɗawa cikinta ke yi mata ga wani irin amai da ya turnuƙe ta da sauri ta gangara gefen titi inda babu kwalta ta durƙusa ta shiga kwara amai mai kumfa a dalili bata ci komai ba. Sosai take kakkari tun tana fitar da kumfa har ta zo ba abinda ke fita sai azabar murɗawa da cikinta ke mata kamar hanjin cikinta zai tsin-tsike, sannu a hankali ta fara gani duhu yana mamayewa ganinta numfashinta nayi sama-sama tun tana iya fizgar numfashin nata har ƙarfinta ya ƙare ta ji komai ya tsaya mata cakk ta sulale ƙasa ɗan raguwar numfashinta ya bar jikinta. Gashi idan ta faɗi babu mutane sosai a dalili rana ta take, ba kasafai mutane ke wucewa a ƙafa ba. Sai dai masu wucewa akan ababen hawa, su kuma ba lallai bane su ganta ba.
A hankali ya gangara da motarsa gefen titi a dalili kira da ake yi wa wayarsa ƙa'idasa ce baya receiving call idan yana driving, gani yadda abokinsa Umar ke kiransa babu kakkautawa daga kiran ya tsike zai sake kira, hakan ya tabbatar masa da kiran nashi mai matuƙar muhimmanci ne sai kawai gangara gefen titi yai parking domin ya amsa kiran nashi, yafi 10 minutes yana magana da Umar kafin ya ajiye wayar  yana ƙoƙarin yi wa motar key ya hango ta yashe a ƙasa, shiru ya yi yana nazarinta yanayin suturar jikinta da kuma handbag ɗinta da ke yashe a gefenta ya tabbatar masa da mai hankali ce ba mahaukaciya ba. Da sauri ya ɓalle ƙofar mota ya fito sanye yake cikin shadda royal blue in colour babu hula akansa, sumar kansa baƙa wulik akanannaɗe ta kwanta luf-luf gwani sha'awa kyakkyawar fuskarshi ma'abuciya kwarjini ɗauke da kwantatce saje mai haɗe da gemi wadda tsawonsa zai iya kai kamu ɗaya da rabi bima'ana gemin nasa yana da tsayi sai da ba irin sosai ɗinan ba. Dogo ne fari tass yana yi tafiyarsa kaɗai zai tabbatar maka da shi ɗin mai ƙarfi ne domin ya tara kwanji duk da shadda ce a jikinsa hakan bai hanawa muscles ɗinshi bayyana ba. Ya soma tattaki tare da nufar wurin da take kwance duk taƙonsa ɗaya sai ya ji matsanancin faɗuwar gaba zai iya cewa tun rasuwar matarsa rabon da ya ji faɗuwar gaba makamancin wannan.
Yana isa wajenta ya sunkuya saitin inda fuskarta yake hijabin jikinta ya rufe mata fuska shi ya hana shi gani ainihin fuskarta ta, cikin zazzaƙar muryarsa ya ce "Bawar Allah lafiya kike kwance a gefen titi idan ba ki da lafiya ki ƙoƙarta ki isa gida, kwanciyarki anan ba daidai bane, kina ji na kuwa?"
Jin shiru bata amsa ba yasa ya yi kasadar kai hannunshi da nufi jaye hijabinta da ya hana shi gani fuskarta, hannunshi yana sauka akan hijab ɗinta faɗuwar gabansa ya ƙara tsananta kasancewar shi namiji shiyasa ya danne abinda yake ji. Sannu a hankali ya janye hijab ɗin. Fuskarta ta bayyana idanuwanta a rufe ruff, yayin da ya ƙura mata nashi idanuwa tsawon lokaci ya ɗauka yana kallonta kafin ya ja iska daga bakinsa ya fesar sai lokacin ya lura da babu numfashi a jikinta, yai sauri durƙusawa ya kama hannunta bai tsaya wata-wata ba ko neman taimakon wani ba, ya cicciɓe ta cakk ya nufi motarsa da ita a backseat ya shimfiɗe ta kana ya koma ya ɗauko mata handbag da takalminta da suka zame daga ƙafafuwanta. Cikin gaggawa ya zagayo ya shiga mota ya fizge ta da ƙarfi ya haura kan titi, kaitsaye wani private hospital ya nufa da ita cikin gaggawa suka karɓe ta babu ɓata lokaci suka dukufa dubata, ɗaki na musamman aka kaita tare dasa mata drip sai lokaci da yaga numfashinta ya dawo normal hankalinsa ya kwanta. Yayin da ita kuma sai sharar bacci take abinta.
*After some hours*
    {Bayan wasu awanni}
  "Congratulations sir madam tana ɗauke da three months pregnancy.
Doctor ɗin ya faɗa sa'ili ya da aka kawo masa test result ɗin ta, shine ya aika ɗaya daga cikin nurses ta kira masa shi.
  "Ba matata bace.
Yai sauri katse Doctor ɗin bai kuma karɓi result ɗin da yake miƙo masa ba. Da alamun ranshi ya ɓaci da dangantashi da ita da likita ya yi.
Gani yadda doctor ya tsare shi da idanuwa yasa shi cewa "Doctor bani da wata alaƙa ko dangantaka da ita tsintar nayi yashe a gefen titi shine na taimake ta na kawo ta asibiti, saboda haka ka ajiye result ɗin a wurinka kafin mijinta ko 'yan uwanta su zo.
Daga haka ya buɗe ƙofar ofishin likitan ya fita, kaitsaye ɗakin da take kwance ya sake komawa har yanzu bacci take yi numfashinta yana sauka a hankali alamun samuwar sauƙi.
Ya jawo plastic chair ya zauna saitin da yake iya gani fuskarta.
Can ya tuna da handbag ɗinta da ya baro cikin motarsa ya tashi da sauri ya fita jin kaɗan sai gashi ya dawo ɗauke da takalma da handbag ɗinta, ya zauna inda ya tashi ya yi zipping handbag ɗin wayarta ya dauƙo saidai kash! Wayar na ɗauke da security code ya ja ɗan siririn tsaki ya tsani wannan ɗabi'a da mutane ke yi na sakawa waya security code, yanzu ina amfani ga waya amma ba hali ya kira wani nata. Tun lokaci da ya zauna dai-dai da second ɗaya bai ɗauke idanuwanshi daga kanta ba. Kamar daga sama ya ji vibration ɗin waya akan cinyoyinshi da sauri ya kai dubanshi ga wayarta love shine suna da ya gani yana yawo akan sensor ɗin wayarta, a natse ya yi picking up...[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune Kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*Abishirinku mata 'yan kwalisa masu son su faranta wa mazajensu rai, ku gamsar da su iya gamsuwa to ga dama ta same ku da za ki saka maigida ihun daɗi da haɗaɗɗun kayan mata daga kamfani Manzil Alwafir masu kyau da inganci, Hajiya karki damu za ki mallake mijinki a tafin hannunki ba Boka ba malam maza ki garzayu wurin gimbiyar haɗa mata mai bada gudunmawar gyara shimfiɗar aure Hajiya Hassana Abdullahi*

*_Muna da kaya kamar haka_*

Smoked heaven
Asta
Ashana
Yaqtur
Nashwa
3rd Avenue
Back to honeymoon
Kazar Mata
Tsumi
Dambun mata
Sanyi herbs
Helwa
Anwar
Deep sea
Vibrationzz
Wet and tight
Ashwa
Halwa
Helwa
Garden knot
After dark intense
Bomb oil
Yoni balm
Swan
Taurariya
Lazeez
Persion hot
HD tea
Mazan Arewa
Tightening honey
Jego package
Bridal package
Durot

  _Muna tura kaya a duk gari da ku ke_

Domin ƙari bayani sai a tuntube mu a waɗannan lambobi 08036072970 08121555525

021...

Tun kafin yai magana Bilal Shattima ya riga shi cikin sauri da rawar murya ya ce "I'm very sorry for keep you waiting Jeeddah nasan kina fushi dani amma firstly ki tsaya ki fara jin uzurina kafin ki yanke min hukunci.
Bai yi gaggawar katseshi ba sai kawai ya kyale shi ya gama faɗi abinda ke ranshi, kafin ya yi wani gyaran murya cikin zazzaƙar murya nan tashi mai cike da izza da zallar taƙama yake faɗin "Na tsince matarka yashe a gefen titi cikin mayauwaci hali nayi ƙoƙari na kawo ta asibiti cikin hukunci Ubangiji likitoci sun yi nasarar shawo kan matsalarta. Ka yi gaggawa ka zo ka same ta a Saraki specialist hospital Ali Akilu road a room 03.
Daga haka ya dantse kiran ba tare da ya jira jin abinda Bilal Shattima zai faɗa ba. Haka kawai daga jin muryar Bilal da ya yi sai ya ji kwata-kwata bai kwanta masa a rai ba asalima wani shegen haushinsa na rashin dalili ya ji ya kanainaye masa zuciya shiyasa yai saurin katse layin.
Ta ɓangaren Bilal Shattima sororo ya yi gami da bin wayar hannunshi da kallo sake kiran layin Jeeddah ya yi saidai har ya tsinke ba a ɗaga ba. Cikin tsanani firgici ya ja machine ɗinsa ya nufo asibitin.
Ya mayar mata da wayarta cikin handbag ɗinta gami da miƙewa ya kai handbag ɗin akan bedside drawer ya aje juyawar da zai ya yi ya ji tana salati, da sauri ya isa wajenta "Sannu Maijidddah ya kike jin jikin naki?"
Ya kira ta da maijiddah ne a dalili ya ji Bilal Shattima ya kira ta da Jeeddah.
Sannu a hankali ta ƙarasa ware idanuwanta akanshi, tun daga kyakkyawar fuskarshi ta bi shi da kallo har ta dire idanuwanta akan ƙafafuwan shi da ke cikin brown sandal.
Ajiyar zuciya na sauke wacce ta fito fili, kafin na kawar da idanuwana daga kanshi inaso nai mishi magana sai dai babu halin yin hakan sakamakon miyau da ya cika min baki taff, sai kawai nai yunƙura na tashi zaune a dalili na fahimci ina bisa gadon asibiti ne, kuma jikina ya bani wannan mutumin shine ya kawo ni saboda na tuna da inda na faɗi sai kuma yanzu da na falka nagani kwance akan gadon asibiti, bana ko tantama cikin hasashena.
  "Za ki shiga bathroom ne na kira nurse ta taimaka miki?"
Sai kawai na tsince kaina da nuna mishi bakina da ɗan yatsa abin mamaki sai na ji ya ce dani "Kina so ki zubda yawu kou?"
Na sake gyaɗa kai, kafin na ƙarasa sauko da ƙafafuwana ƙasa har ya ɗauko tissue box ya zaro ta ɗan yawa, kana ya kananaɗe ta a maimakon ya miƙo min sai ya ce min "Zubar da yawu anan kada ki tashi ki jira na kira nurse ta taimaka miki, har yanzu jikinki bai yi kwari ba.
Sai da na ɗago na kalle shi kafin na maida ganina akan tissue da ke riƙe a hannunshi, ko ya fahimci ba zan iya zubar da yawu tissue yana hannunshi sai kawai na ji ya sake cewa "Kar ki damu maijiddah ki zubar kawai lalura ce kin ji?"
Na jinjina kai gami da matsowa na tofar da miyau akan tissue da ke riƙe da hannunshi ni kaina sai da naji kunya saboda yanayi miyaun nawa ga kumfa ga kaurin tsiya kusan dai yadda yawun laulayi ciki yake, amma sai naga shi ko a jikinsa hankalinsa kwance ya nufi dustbin ya jefa tissue ciki. Kana ya juyo ya kalle ni yana faɗin "watakila kina da buƙatar shiga bathroom bara na kira nurse ta taimaka miki.
Ya ƙarashe magana gami da nufar ƙofar fita ya buɗe ya fita, ƙofar na bi da kallo kafin na sauke wata ajiyar zuciya har tafi ta farko fitowa a fili lokaci guda na ƙarasa saukowa a hankali nake bin bango har nai nasarar shiga bathroom. Ina jin sautin muryar mutane su na magana ƙasa-ƙasa   nai sauri kus-kure bakina na buɗe ƙofa koda na fito har ya fice iya bayanshi kawai nagani, nurse ɗin da ke tsaye tai saurin zuwa ta kama shoulder na da taimakonta na koma bisa gado na kwanta.
Wani drip ta sake saka mata kana nurse ɗin ta fice bata daɗe da fita ba Jeeddah ta ji an turo ƙofa a tunaninta ko shine koda ta juyo sai kawai tai tozali da fuskar Bilal Shattima da sauri ta kawar da fuskarta, yayin da shi kuma ya ƙaraso wajenta da rawar jiki yana faɗin "Subhanalillah... sannu Love kin gani kou dama sai da nai gudun faruwar hakan amma kika kafe lallai-lallai sai kin je school ɗinan...
Tun kafin ya ƙarashe magana Jeeddah tai wani irin juyowa ta zuba mishi wani mugun kallo wanda hakan ne yasa shi haɗiye raguwar kalamanshi. Sosai ta ji wani irin haushinsa ya lulluɓe ta cikin fusata ta tashi zaune tana faɗin "Lallai sai yau nasan ba ka ƙaunata Bilal ba ma ta lafiya ta kake yi ba ƙoƙarin ɗora min laifi ka ke yi duk abinda ya faru dani ba kai bane sanadi kira nawa nai maka tsabar wulaƙanci ka ƙi picking shine za ka zo kana min wani borin kunya.
  A sanyaye ya kama hannunta ta fizge cikin tsawa ta ce "Ka fita banaso ganinka daɗin abin ba kai kaɗai nake dashi ba a duniya balle ka wulaƙanta ni. Ba don da ALLAH ya haɗa ni da mutum nagari ba mai kyakkyawar zuciya ya gani yashe a gefen titi kamar wata marar gata ya ɗauko ni ya kawo asibiti da yanzu ALLAH ne kaɗai yasan hali da zan shiga kai kana can kana sharar baccinka da yafi ni muhimmanci.
  "Jeeddah..... Jeeddah Dan ALLAH ki tsaya ki ji ta bakina wallahi-tallahi  neighbours ɗin mu ne suka yi gobara gidan Ahmad bank manager ɗinan na shirya kenan na taho picking ɗinki sai ga Officer Abdul-ganiyu ya yi min knocking koda na buɗe ƙofa naga yadda gidan ke ci da wuta shine mu ka je taimaka musu na manta da na bar wayana a charging da kyar aka samu wutar ta mutu komai basu fitar ba an dai auna arziki tun da rai ya fita kin ji dalili da ya hanani zuwa picking ɗinki in time. Wallahi sai in kin so ki ga laifina ne kawai amma tun kafin mu yi aure ban taɓa ƙin zuwa dauƙar ki ba sai in da babban uzuri kamar wannan. Amma Dan ALLAH ki yi haƙuri kin ji rabin raina?"
Ya ƙarasa magana tare da zaunawa kusa da ita, ya sake kama hannunta a wannan karo bata hana shi riƙe hannun nata ba saboda ta gamsu da kwakwaran dalili da ya bata, amma duk da haka taƙi sakin ranta. Shi kuma sai kanfa-kanfa yake da ita.
   "Please Love ki sakin ranki mana.
Ya faɗa yana wani kwantar da murya, ɗan murmushi tayi kafin ta koma ta kwanta.
  "Love ina mutumin da ya kawo ki asibiti nai masa godiya duk da tun a waya na fahimci ɗan reni wayau ne yana ji da kansa.
Ya ƙarashe magana yana wani taɓe baki.
Kallo mamaki ta bishi da shi kafin ta ce "Ban san inda yake ba sai in zuwa za ka yi ka tambaya nurses ɗin da ke on duty.
Yadda tai magana yasa ya gano har yanzu da raguwar haushinsa a zuciyarta sai kawai ya ja bakinsa yai shiru da yaga shiru nasu yana neman yi yawa ya fito da wayarshi ya kira Hajja da Aunty Farida ya faɗa musu hali da Jeeddah take ciki.
**** *** ***
  Zaune take gaban Bokanta da ke cikin wani ƙauye a cikin ƙaramar hukumar Binji local government, dama lokaci zuwa lokaci take kawo masa ziyara a duk lokaci da wata buƙata ta taso  mata wurinsa take zuwa. Cikin kwantar da murya ta fara magana "Ran boka jikan Baidu ya daɗe kamar dai yadda na saba zuwa da buƙata ta kuma a biya min ita yau ma na zo da wata buƙata ina fatan haƙata za ta cimma ruwa, duk da akasarin ayyukan da aka yi min a can baya ba a taɓa samun matsala ba. Shiyasa har gobe bani da inda nake kai kukana a share min hawaye face wurinka.
Hajiya Bintu ta ƙarasa magana cike da ladabi har wani sunkuyar da kai take yi, shi kuma jikan Baidu tun daga lokaci da ta fara magana yake aikin kallonta da jajjaye idanuwanshi kwala-kwala masu matuƙar ban tsoro, kana ya ƙara matso da ƙwayar dake cike da wasu koraye ruwa ya shiga faɗin wasu kalamai cikin wani yare. Tsawon lokaci ya share kafin ya ɗago ya kalleta cikin kakkausar murya ya shiga faɗin "Hajiya Bintu shekaru da dama da suka shuɗe mu ne muka yi miki aiki da kika shiga tsakani ɗan kishiyarki Faruq da mahaifiyasa, hakazalika mu ne muka yi miki asiri da Bilal ya kasa samun aiki muka kashe masa zuciyar nema ba ma wannan kaɗai ba hatta da mijin Bahijja mune muka tura masa baƙaƙen aljannu suka mayar da shi taɓaɓɓen. Saboda haka kada ki saka shakku akan aikinmu faɗin buƙatarki gaba gaɗi kowacce iri ce za mu tabbatar da mun biya miki ita?"
   "Godiya nake Boka jikan Baidu wadda yafi uwa da ubana domin su tuni suka shura gareni, yayin da kai har yanzu kake ganiyar share min hawayena. Boka na zo na gayamaka ne na kashe maciji na manta ban sare kai ba, wallahi ina cikin damuwa saboda sai yanzu na gano na tafka babban kuskure tabbas mu yi nasarar kashewa Bilal zuciyar nema kana mun dusashe kowacce hanya da zai bi domin yai dogaro da kanshi sai gashi kwatsam ya auro 'yar masu kuɗi, wacce take ƙoƙari rusa min daɗen burina na gani na hanawa Hajja cin moriyar 'ya'yanta Boka in takaice ma labari tun zuwan Jeeddah gidan Bilal daga shi har uwarsa da 'yar uwarsa Bahijja suka yi ban kwana da talauci, su ci mai kyau su sha mai kyau zuciyata ba za ta iya jure ganinsu a cikin walwala da wadata ba. Saboda haka na garzayu gunka domin kai kaɗai ne za ka iya magance min damuwata, Inaso duk yadda za ka yi Boka jikan Baidu ka wargaza jin daɗinsu ya koma baƙin ciki indan aka yi nasarar yi min hakan ni kuma na ɗaukar wa aljannu alƙawari shayar dasu jini na daga kowacce irin dabba suke muradi.
Wata irin kafirai dariya ya kece da ita sai da ya share lokaci yana tintsirar dariya, wacce ke nuni da muguntarsa ta wuce misaltawa kafin ya tsagaita da dariyar tasa ya kalleta gami da turɓune fuska, sai fuskar tashi ta dawo tamkar ta gwaggo biri "Buƙatar ki za ta biya Hajiya Bintu, yanzu faɗa min me kike so ayi musu?"
  "Boka so nake a shiga tsakani Bilal da matarsa ahana musu zaman lafiya, ka haddasa rashin jituwa a tsakaninsu ta haka za ta janye duk wani tallafi da take ba su.
Har ta dasa aya a zancenta Boka yana aikin kallonta, duk da ya kasance mushiriki amma sai yake gani rashin imanin Hajiya Bintu ya yi yawa bai taɓa gani bala'in kishi irin nata ba mutumin da take kishi akansa tuni ƙasa ta lulluɓe shi, baya gidan duniya amma ba ta saduda ba kullum cikin bin kishiyarta da 'yayanta da sharri take.
  "Ki sa aranki buƙatarki har ta biya domin matar Bilal da kike gani ita ma mace ce mai zazzafan kishi kamar ke ɗinan, saboda haka zan yi amfani da zafin kishinta na tarwatsa zamansu. Kuɗin aikina dubu ɗari sannan kuma za a yi wa aljannu yanka su sha jini na jan raƙumi idan kuma kuɗi za ki bada a siya musu sai ki bada dubu ɗari.
  "Shikenan Boka ai kafin na zo nasa ɗanta Faruk ya turo min da kuɗi saboda haka da ƙudinta ɗanta zan tarwatsa rayuwar ɗaya ɗan nata.
Ta ƙarasa magana tana dariya mugunta, nan take ta zuge jakkata ta fiddo da kuɗaɗen da ya buƙata wasu baƙaƙen layu guda biyu ya miƙa mata ki samu asirtatce wuri inda babu wanda zai gani ki binne su ki zuba ido za ki ga abinda zai faru...
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

Assalamu Alaikum Manyan mata masu kayan harka . Yau kuna tareda Manzil Alwafir Rep/ delegate . Sunana Gimbiya Hassana Abdullahi

Mata da dama su Kanyi Korafi hade da cewa basuda *taste* mata na shiga damuwa har ta Kai ga qaurace ma junansu Sabida wasu Dalilai .
Wadannan dalilai suka sa Manzil Alwafir ta ga ya kamata ta wayar ma ma’aurata Kai (Awareness kenan) domin a magance matsalolin/ rage samun mace macen Aure da matsalolin da ke damuwar mata agidan aure .

Kada ku manta da cewa acikin abincin mu Allah (SWT)ya sanya abubuwa da yawa acikin su, masu Bamu kariya da N’iimta ajikinmu

Jikin ya’ Mace ya kasance abun so ga da’ Namiji a kowanne lokaci.

Daga lokacin da mace ta rasa darajar Farjinta ma’ana ta barshi ba gyara ba kulawa tamkar ta warware passion da intimacy tsakanin ta da mijinta ne.

Products din manzil sun kasu kashi kashi ( categories ) kaman haka ;

*Qarin Niima* - Muna da su kala kala kaman su = Amor Carino ,Asta,smoked heaven, Vibrationzz, tsumi,Back 2 honeymoon, Taurariya,Swan, Bomb oil ,Anwar da Yaqtur.

*Matsewar Gaba* - *Matsi* -    Kaman su-Harisa,Helwa, tightening honey,Dorot,tighten Herbs da Kazar mata.

**Kuzari da shaawa** -HD-Tea,Tea 01, 3rd Avenue, Exclusive honey, Deep sea , ginseng , Nashwa

*Basir kit*- Pile kit &Yoni Herbs

*Infection kit*- infection curing herbs da Sanyi detox herb. Infection yana lalata Niimar Mace ya hana ta Jin sha’awa sannan ya saka mata bushewar gaba da rashin gamsuwa

*Mens Aphrodisiac* Yajin maza, Cold stone , Mens Magnet. Persion hot

*Jego package* - joy stick,Kazar mai jego,yajin jego da sauransu

Domin qarin bayani Zaa samemu a 08036072970/ 08121555525 call/WhatsApp
Taku har kullum *Manzil_ Alwafir Rep*.
*Hajiya Hassana Abdullahi* 💝


022...

Yana fitowa daga asibiti kaitsaye gidansa ya nufa yadda yake jin jikinsa yai masa wani iri kamar an ɗaɗɗaure masa shi baya jin zai iya zuwa inda ya yi niyyar zuwa. Shiyasa dole ya dawo gida yai parking motarsa a ɗan ƙaramin parking lot dake farfajiyar gidansa. Wanda yake zaune shi da mahaifiyarsa, ya fito daga mota ya nufi entrance yana tafe yana rangaji kamar wanda ya sha kayan maye, jin ƙarar motarsa yasa ummarsa ta taso daga kan sofa ta nufi jikin window ta ya ye labulle ta leƙa a hankali ta bishi da kallo har ya shige apartment ɗinsa, wani irin bugawa zuciyarta tayi a lokaci guda fargaba da tsoro suka lulluɓe ta tsawon shekaru goma rabonta da ta ganshi cikin makamancin wannan hali, ta ko ina jikinta rawa yake tai sauri sake labulle ta nufo apartment ɗinsa da sauri. Bai tsaya parlour ba ya wuce bedroom ɗinsa gefen gado ya zauna tare da kai hannunshi ya ɗauki ɗan ƙaramin frame da ke ajiye akan bedside drawer, mai ɗauke da hoton matarsa wacce ya ta rasu kusan shekaru goma. Tun daga lokaci da ta rasu bai sake marmarin ƙara aure ba. Asalima ya kudurta a ranshi ba shi ba ƙara aure, tun daga sanda matarsa maijiddah ta rasu bai sake haɗuwa da mace da ganinta ya rikirkita masa ƙwaƙwalwa da tunani ba sai akan Jeeddah duk da ta kasance matar aure hadda ciki take ɗauke da shi amma jin ta yake yi tamkar wani ɓangare na jikinsa. Shin wai meke shirin faruwa da ni ne?"
Yai wa kansa wannan tambaya jin an turo ƙofar ɗakin nasa yasa shi maida ganinsa akan ƙofar ya haɗa idanuwa da ummarsa wacce ita kaɗai ce ta kasance duniyarsa ba shi da kowa bayan ita, yai sauri mayar da frame ɗin inda ya ɗauko shi ya saki mata gajeren murmushi gami da faɗin "Ummana ashe kina gida na zaci kin tafi gidan Aunty Murja da kika ce za ki je?"
Sai da ta zauna kusa dashi ta riƙo hannunshi kafin ta shiga ƙare masa kallo ta ɗan numfasa cikin ƙaramin sauti ta ce "Ameer ba dai ciwon kan naka bane yau ya motsa naga ka dawo a sukurkurce?"
Murmushi ya sake yi gami da ƙoƙarin ɓoye mata hali da yake ciki "Ba shi bane Umma kawai dai ina cikin damuwa ki yi min addu'a.
  "Wacce irin damuwa ce wannan Ameer da za ta saka fita daga hayyacinka farkon shigowarka gidanan wallahi ba ƙaramin firgici na shiga ba, na zaci ko ciwonka ne yake so tashi?"
Girgiza kanshi ya yi tare da jinƙe hannunta dake cikin nashi ya ce "Ummana ki kwantar da hankalinki ba abinda kike zato bane.
  "Amma Ameer wannan wacce irin damuwa ce da za ta saka ɗimaucewa a ɗan ƙanƙani lokaci, don ba haka ka fita ba?"
Sai da ya ja numfashi kana ya fesar kafin ya shiga bata labari haɗuwar shi da Jeeddah da irin taimakonta da ya yi. Kana ci-gaba da cewa "Umma wallahi ganinta da nayi ya tuno min da marigayiya maijiddah saboda sun yi matuƙar kama kawai dai maijiddahta ta fi ta farar fata. Wannan kamanun nata ya haifar min da damuwa a dalili tuna min da maijiddah da tayi.
  Murmushi Umma tayi tare da shafa sumar kanshi "Oh! Ameer kai dai ba ka girma yanzu daga gani mai kama da maijiddah sai ka tashi hankalinka, maijiddah ta ri ga ta tafi tafiyar da ba a dawowa ka ci-gaba da yi mata addu'a ka kou?
  "Tou amma wallahi Ummana a duk lokaci da na tuna nine sanadin mutuwar maijiddah sai naji na kasa sarrafa kaina, musamman a yau da na ci karo da mai kama da ita.
   "Kul! Kar na sake ji ka danganta kanka da mutuwar maijiddah, kwananta ya ri ga da ya ƙare ko da kai ko babu kai sai ta mutu.
  "Amma Umma....
"Dakata! Ameer banaso na sake jin duk wata magana da ta danganci mutuwar maijiddah, ka yi mata addu'a kawai kuma karka manta da alƙawarin da ka ɗaukar min na kauracewa mata saboda haka daga yau na ƙara shata ma layi da taimakon kowacce mace, zuciya bata da ƙashi ina tsoron garin taimako ka faɗa soyayya saboda haka ba kai ba ƙare taimakon wata mace saboda gujewa komawa 'yar gidan jiya. Banaso abinda ya faru da maijiddah ya sake faru akan kowacce mace, gara ka ci-gaba da kame kanka gudun kada mutane duniya su farga da hali da kake ciki.
   Nisawa Ameer ya yi zufa ta karyo masa a gefen fuska, ci-gaba da tuna mishi da abin da ya manta umma tayi har Umma ta gama magana ta fi ce zuciyarsa sai bugawa take da ƙarfi.
*** **** ***
Cikin lokaci ƙalilan 'yan gidansu Jeeddah dana  Bilal suka cika asibiti, kulawa ta musamman take samu daga ɓangarorin biyu sai bayan isha'i Hajja da A'isha Shattima suka koma gida, aka bar Mama ta zauna a gunta hatta da Baba da ya dawo daga Kasuwa kafin ya wuce gida sai ya biyo  ya dubata, zuwa lokaci jikinta Al-hamdulillah! Ta ji sauƙi sosai hatta da aman da take yawan yi ya ragu sau ɗaya tayi tun daga kanshi bata ƙara yi ba. Hadda abinci an samu ta tsakura kaɗan.
Ƙarfe goma daidai Bilal Shattima ya baro majalisa kafin ya wuce gida sai da ya sake biyowa asibiti yai wa  Jeeddah sai da safe karo na farko tun aurensu da zai kwana shi kadai ba tare da ita ba shiyasa yake jin kansa wani iri.
Kwana Jeeddah biyar a asibiti aka yi discharge ɗinta zuwa lokaci ta sami sauƙi sosai sai dai abinda ba a rasa ba abinka da mai juna biyu.
*After one month*
_{Bayan wata ɗaya}_
Yau Jeeddah ta tashi da kwadayin ɗan wake shiyasa tai sauri kammala ayyukanta na yau da kullum kasancewar weekend ne bata zuwa school, ɗan wake ta ji tana sha'awar ci ta shiga kitchen kaitsaye store ta wuce  ta ɗebo garin ɗan wake da ke cikin rubber bucket mai murfi ta ɗiba adadin wanda zai isheta har ta juya sai kuma idanuwanta suka sauka kan sack ɗin shinkafa wanda dukka bai fi kwana biyu da Baba ya aiko mata dashi ba amma dukka yanzu bai fi rabin sack ba, ko shakka babu Bilal ne ya raba shinkafar nan take na ji wani shegen haushi da takaicinsa ya lulluɓeni. Ba yau ne karo na farko da ya saba raba foodstuffs ɗin Baba yake kawo min ba ya aika wa Hajja da Aunty Bahijja amma yau ne rana ta farko da naji ba zan iya ci-gaba lamunta hakan ba.
Saboda haka a fusace ta ajiye garin da ta ɗeba akan kitchen cabinet kana tai switch off ɗin gas, ta nufi bedroom inda Bilal Shattima yake, ta tura ƙofa da ƙarfi yana tsaye gaban dressing mirror ɗaure da towel a ƙugunshi yadda ta banko kofar yasa shi kallonta da sauri cikin ɓacin rai na ce "Love na shiga store naga sack ɗin shinkafa rabi kuma dukka bai fi two days da kawowa ba...
  "Wannan wane irin tambaya ce Jeeddah?"
Yai sauri katse mata hanyar da mamakin tambayarta ta shimfiɗe akan fuskarshi.
Cike da tsiwa na ce "Hausar tawa ce ba ka fahimta ba ko kuma amsar tambayar ce tawa ba ka da?"
Sannu a hankali ya ajiye comb ɗin dake hannunshi ya tako ya iso kusa da ita "Jeeddah lafiyarki qalau kuwa?"
  "A'ah daga turu nake ba nayi maka kama da mahaukaciya ba?
"Me kuma ya kawo zance hauka kawai dai naga kin min tambayar da kin daɗe da sani amsarta.
"Look Bilal ka daina wani iri kamar ba ka fahimce ni ba. Tsakani da ALLAH wahala tana neman ta yi wa Babana yawa ace duk ƙarshen wata sai ya aiko da foodstuffs a gidanan, da ace daga bakina sai naka ne da buhun shinkafa ɗaya zai iya mana three months cikin ma ba mu yi manage ba. Gaskiya ka canza tsari don ba zai yu ba Babana ya ci-gaba ciyar da ni da kai kuma ya haɗa da mahaifiyarka hadda ƙari wata lange. To kasani daga yau na kashe a ɗibar min abinci da ubana ya kawo min akai ma wasu, idan kana so ka basu abinci ba wanda zai hana ka amma da naka gumi ba da na Babana ba.
  Shiru Bilal Shattima ya yi ya kure ta da idanuwanta saboda saukar maganganu ta yake ji tamkar al-mara ko kuma iri a mafalki, ya kasa yarda Jeeddarsa ce tsaye a gabanshi sai yake gani kamar an musanya masa ita da wata Jeeddah ta daban.
Bilal Shattima dole rasa bakin magana ya yi saboda mamakin da ya gama cika shi ganin yadda Jeeddah ta gaggaya masa magana.
Ƙarar buɗe ƙofa yasa shi dawowa ciki natsuwarshi ya bi ta da kallo wanda da gani ba sai an faɗa maka ba na zallar mamaki ne. Kafin ya kauda idanuwanshi ya tako cikin mutuwar jiki, ko mai kasa shafawa ya yi kawai dai ya yi ƙoƙarin suturta jikinsa. Key ɗin machine ɗinsa ya ɗauka koda ya fito tana kitchen, machine ɗinsa kawai ya fidda waje gani ya yi koda mintina ɗaya ya ƙara a gidanan za su iya ɓatatciya da ita gara ya bar mata gida. Yana fitowa bai zame a ko ina ba sai shagon abokinsa Abbas inda yake sayarda electronics, har ya zauna a kujerar dake kusa da wacce Abbas yake zaune  zuciyarsa ba ta bar yi masa tuƙuƙi ba, jin yake kamar ya koma ya rufe Jeeddah da ɗan bala'in duka sai ta kasa tashi.
  "Ya aka yi ne abokina na ganka a harzuƙe ba dai Jeeddah ta sake yankawa Jessica wuƙa ba?"
Tambayar da Abbas yai masa ta ƙara linka masa ɓacin ransa, da kyar ya iya buɗe baki ya ce "Abbas wai ni yau Jeeddah za ta wulaƙanta sai yau na ƙara yarda da mace ba 'yar goyo bace, duk wanda ya daka ta mace wallahi rabonsa wahala.
   "Tou...ikon ALLAH! Yau kuma Shattima kaine da bakinka kake faɗar wannan magana?" Cabdijam...lallai duniya juyi-juyi ce in ji kwaɗo da ya faɗa ruwan zafi.
  "Uhmm! Bari kawai Abbas yau duk yadda ake cin mutunci a tozarta mutum Jeeddah tai min, ta nuna min ita ɗin 'yar kunama ce can you imagine Jeeddah za ta buɗe baki ta ce min kar na sake ɗibarwa su Hajja shinkafar da Babanta ya kawo, saboda ALLAH idan ban ɗibar musu shinkafar da Babanta ya kawo ba gidan ubanwa take so na je nema musu abinda za su ci?"
Ajiyar zuciya Abbas ya yi saboda yau ya ga abinda ya fi zare tsayi, bai taɓa tsammanin mutuwar zuciyar Bilal Shattima ta kai har haka ba. Sai da ya gyara zamanshi kafin ya ce "Zan faɗa maka gaskiya Shattima komai ɗacinta ba zan gaza faɗa maka ita ba. Duk abinda Jeeddah tai maka daidai ne ta ya za ka dawo ka tare gindin mace ka ci ka sha daga gareta kana kuma hadda haɗa wa da mahaifiyarka da ƙari 'yar uwarka haba wannan ai babban abin kunya ne. Ka ɗauki mutuwar zuciya ka ɗorewa kanka kowane namiji fatansa ya ɗauki responsibilities ɗin gidansa amma kai sai mace ce za ta ɗauka maka. Ta ya ya kake tunani wata rana ba za ta goranta maka ba?" To gaskiya idan ma bacci kake yi gara tun wuri ka mafalka ka je ka nemi na kanka, idan kuma ka ci-gaba da zama a haka wallahi-tallahi ba baki nai maka ba hatta da gidan da ka ke ciki tun da ba naka bane wata rana sai ta watsu ma da kayanka waje daga nan duniya za ta ƙara sani hali da kake ciki. Yanzu haka a majalisa idan ba su ga fuskarka ba gulmarka suke yi sai faɗar maganganu mararsa daɗi suke yi akanka. Shiyasa a koda yaushe nake ƙoƙarin lurar da kai ka nemi sana'a komai ƙanƙantar ta amma taurin kanka ya hana ka. To ga irin tanan tun tafiya ba tai nisa ba mace ta fara zabga ma kuturun wulaƙanci, ina da nan gaba kun fara tara Iyali wallahi abokina a lokaci za ka rena kanka a gaban 'ya'yanka za ta dinga yi fatali da mutuncinka. Ni dai a matsayina na childhood friend ɗinka kuma abokin shawarar ka ina shawartaka da ka gaggauta neman sana'a koda ta ƙarfin da ALLAH subhanahu wata'ala ya wadata kai dashi ne, duk yadda yake ka nemo ka  kawo sai ita kuma Jeeddah ta ƙara da wanda take ku ci-gaba da rufawa junanku asiri, tsakani da ALLAH Shattima hannu ɗaya baya ɗaukar jikka haƙuri za ka yi kada ka bari wannan abin ya ɓata muku kyakkyawan zamanku tun da kuna so junanku asalima SO NE ya haɗa ku.
Ajiyar zuciyar da Bilal Shattima ya yi ta fi a kirga, duk maganganu da Abbas ya faɗa yasan gaskiya ne amma duk da haka haushin Jeeddah ya kasa fita daga zuciyarsa.
Cikin fusata ya ce "Don banida abin yi ba shi zai bata damar ta dinga faɗa min duk abinda ya fito bakinta ba. Infact ai tasan banida aiki yi amma ta aure ni shine yanzu don iskanci za ta tsiro min da ɗibar albarka to wallahi na fi ta rashin mutunci nesa ba kusa ba da ni take zance.
  "Uh! Shattima kada ka biyewa fushin zuciya ka aikata abinda ba daidai ba.
  "Mu bar zance nan kawai Abbas domin ƙara min ɓaci rai yake.
Bilal Shattima yai sauri katse shi yayin da ɓacin ransa ke daɗa hauhawa.
Tun fitar Bilal Shattima daga gida Jeeddah ba ta sake bin ta kanshi ba, ko kusa zuciyata ba ta yi tunani rashin kyautuwar abinda ta yi ba. Sai ma sabgar gabanta ta shiga yi, da ta ga har ƙarfe biyar ta wuce bai dawo gida ya ci lunch ba. Al'hali ya saba da ƙarfe huɗu yake dawowa, har ta dauƙo wayarta ta kira shi sai kuma ta ji ta kasa. Abu kamar wasa har ƙarfen goma sha ɗayan dare Bilal Shattima bai dawo ba. Daga bedroom ta fito zuwa parlour ta nemi two sitter ta zauna, nan take zuciyata ta shiga kimtsa mata Bilal yana can tare da wata saboda tun da suka yi aure bai taɓa kai wa irin wannan lokaci bai dawo ba. Zubur! Ta miƙe ta kai gwauro ta kai mari ta kasa zaune ta kasa tsayi,  wani irin mugun kishi ke cinta duk inda hankali da natsuwata suke su ka gushe sai ƙarfe 11:35am Bilal Shattima ya shigo tun kafin ya ƙarashe kafe machine ɗinsa ta hayyaƙo masa cikin tashin hankali take faɗin "Malam daga wajen wacce 'yar iska ka fito miyasa ba ka kwana a can ba?"
Yadda ya juyo yana aika mata wani irin mugun kallo kaɗai ya isa ta gano a matuƙar fusace yake...
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

Assalamu Alaikum Manyan mata masu kayan harka . Yau kuna tareda Manzil Alwafir Rep/ delegate . Sunana Gimbiya Hassana Abdullahi

Mata da dama su Kanyi Korafi hade da cewa basuda *taste* mata na shiga damuwa har ta Kai ga qaurace ma junansu Sabida wasu Dalilai .
Wadannan dalilai suka sa Manzil Alwafir ta ga ya kamata ta wayar ma ma’aurata Kai (Awareness kenan) domin a magance matsalolin/ rage samun mace macen Aure da matsalolin da ke damuwar mata agidan aure .

Kada ku manta da cewa acikin abincin mu Allah (SWT)ya sanya abubuwa da yawa acikin su, masu Bamu kariya da N’iimta ajikinmu

Jikin ya’ Mace ya kasance abun so ga da’ Namiji a kowanne lokaci.

Daga lokacin da mace ta rasa darajar Farjinta ma’ana ta barshi ba gyara ba kulawa tamkar ta warware passion da intimacy tsakanin ta da mijinta ne.

Products din manzil sun kasu kashi kashi ( categories ) kaman haka ;

*Qarin Niima* - Muna da su kala kala kaman su = Amor Carino ,Asta,smoked heaven, Vibrationzz, tsumi,Back 2 honeymoon, Taurariya,Swan, Bomb oil ,Anwar da Yaqtur.

*Matsewar Gaba* - *Matsi* -    Kaman su-Harisa,Helwa, tightening honey,Dorot,tighten Herbs da Kazar mata.

**Kuzari da shaawa** -HD-Tea,Tea 01, 3rd Avenue, Exclusive honey, Deep sea , ginseng , Nashwa

*Basir kit*- Pile kit &Yoni Herbs

*Infection kit*- infection curing herbs da Sanyi detox herb. Infection yana lalata Niimar Mace ya hana ta Jin sha’awa sannan ya saka mata bushewar gaba da rashin gamsuwa

**Mens Aphrodisiac** Yajin maza, Cold stone , Mens Magnet. Persion hot

*Jego package* - joy stick,Kazar mai jego,yajin jego da sauransu

Domin qarin bayani Zaa samemu a 08036072970/ 08121555525 call/WhatsApp
Taku har kullum *Manzil_ Alwafir Rep*.
*Maman zahra* 💝

023...

Kaman zai yi magana sai kuma ya haɗiye abarsa, ya raɓa gefenta ya wuce zuwa bedroom, raina ya ƙara ɓaci fiye da farko na bishi da mugun sauri yana shiga ɗaki ina shigowa har wani huci nake yi yayin da ƙirjina yai min nauyi kamar an danne min shi da ƙaton dutse, cikin ƙunar zuciya nace
"Bilal gara ka faɗa min daga inda ka fito saboda shi ne kwanciyar hankalinka a gidanan.
   Fasa ƙarasa cire rigar jikinshi ya yi ya juya a fusace ya ce "Jeeddah banaso iskanci ki dawo hankalinki ke duk yadda za ki nemi masifa dani kinsani, wai kin manta da wulaƙanci da kika tatamin ɗazu ne? Saboda reni wayau shi ne har kike da zarrar tarɓe ni da wani sabo.
  "Idan har kana da gaskiya ka faɗa min daga ina kake sa'anan me ya tsayar da kai har tsawon wannan lokaci?"
Murmushin takaici ya yi kafin ya ce "Ai wuyanki bai yi kaurin da za ki min titse ba idan kuma kina gani isarki ta kai taho ki matse bakina ko kiyi min duka watakila idan na ji zafin duka na faɗa miki.
Yana ƙarashe magana ko kallona bai sake yi ba balle ya ga yadda idanuwana suka ciciko da hawaye ya shige bathroom abinsa sai faman jan numfashi nake yi duk yadda naso na hanawa kaina kuka hakan ya ci turu. Domin bansan lokaci da na durƙushe ƙasa na saki maraya kuka wani irin kishi ke cina a zuciya bansan iya adadin lokaci da ya share a bathroom ba sai ƙarar buɗe ƙofa na ji, yanzu ma raɓa ni ya sake yi ya nufi dressing mirror ya goge jikinsa ya yi 'yan shafe-shafensa kana ya saka kayan baccinsa, gaba ɗaya ɗakin ya gauraye da ƙamshin turarensa. Yadda ya nuna min halin ko in kula yaƙara min haushi, sai kawai na ƙarawa kukana sauti, duk da haka bai bi ta kaina ba ya kashe wuta ya haye gado harda su shigewa cikin duvert. Sai da nayi kuka na mai isata kafin na rarrashi kaina domin wanda nake yi kukan domin shi tuni ya yi bacci abinsa ya barni da tafarfasar zuciya. Abinda na fahimta kwata-kwata Bilal Shattima ya daina damuwa da damuwata wato nufinsa ko na mutu ko nayi raina ruwana. A maimakon na kyaleshi sai kawai na miƙe na nufe wurinshi ina cika ina batsewa wata sabuwa masifa nake ji in takaice muku labari a daren ranar daga ni har shi ba wanda ya yi bacci kirki kwana muka yi muna gubza faɗa kamar wasu sababbin ƙarnuka. Hakazalika a washegari ma haka muka tashi sai da muka share kusan mako ɗaya muna faɗa kafin mu daidaita kanmu amma fa na sha alwashi ba zai sake ɗibar min abinci ya kai gidansu ba. Shi kuma tun daga wannan lokaci ya ƙaurecewa ci abincina hatta a shimfiɗa ba ruwansa dani, yayin da ni ma ko a jikina tafi nono fari gara kowa ya riƙe kayansa.
A haka rayuwarmu ta ci-gaba da gudana kullum cikin faɗa da gani laifin juna muke, har ta kai ta kawo maƙota suka san hali da muke ciki, don ba zan manta ba a wani dare da faɗa ya kaure a tsakaninmu har da neighbours ɗinmu sai da suka shigo zance a dalilin kuwa bai wuce na duba wayarsa naga yana chat da Nusaiba 'yar ƙanin mahaifinsa duk da chat ɗin nasu ba na soyayya bane amma ba ku ga yadda na tashi hankalina ba. Da kyar da shudin goshi suka shawo kaina na haƙura.
Sannu a hankali cikina ke daɗa girma gashi har ya shiga wata na takwas amma har zuwa wannan lokaci ko ɗan kafai Baby Bilal Shattima bai siye ba kuma ga dukkan alamu bashi da niyar siya. A wani dare ne har mun kwanta bacci abin ya motso min na tashe shi da yake nayi ta haƙuri ina kallon gudun ruwanshi, domin na zaci ko da munafuci ne zai yi min magana amma ya yi shiru abinsa. "Ya aka yi ne Love ko ba ki da lafiya ne?"
Ya faɗa sa'ili da ya tashi zaune don ni tuni nake a zaune nai mugun ɗaure fuska, gudun kada ya kawo min wargi.
  "Love na gaji da zuba maka ido gara na fito fili nai maka magana domin wannan hali ko in kula naka ya yi yawa.
"Wacce magana ce wannan da ba za a yi min ita ba sai a tsohon dare?"
Sai da na kare wa mummunan fuskarshi kallo musamman da naga yana wani yatsinarta, da yasan yadda ya motsar fuska ke bayyana da muninsa tsakani da ALLAH da ya haƙura ya bar wa wanda yake yi wa kyau su yi. Kafin na ce "Dangane da zance kayan haihuwa da kowane maigidanci yake siya sa'ili da matarsa take ɗauke da ciki musamman ni da wata mai zuwa ne EDD na zai cika.
   Sai da yai min wani kallo wanda zan iya kiranshi na wulaƙanci, don har wani taɓe gungurumin baki yake kafin ya ce "Gaskiya Love kina da matsala na rasa gane abinda yake hawa kanki infact su kayan haihuwa ɗin da kike magana akai ba da kuɗi ake siyensu ba tuni kika kwana da sani banida shi, idan ba neman magana ba miye na tashina cikin tale-talin dare.
   "To shikenan ba ka da shi abin nufi anan haka za ka yi ta zama ba za ka nemi sana'a ba, sai dai kullum idan aka yi magana sai ka bugi ƙirji kace baka dashi, na fahimci har alfahari kake yi da babu ɗinan.
  "Ya isheki Jeeddah karke sake ki faɗa min maganar banza, ai tun kafin na aurenki kinsan bani da aiki kika yaudare ni da mayaudaran kalamanki na aurenki kafin mu yi aure ba cewa kika yi za ki ɗauki hidindimo gida ba?" Shi ne yanzu don tsabagen reni wayau za ki tashe ni cikin tsakiyar dare kina min zance kayan haihuwa. Shin bari na tambayeki miye amfani salary ki da kike bugun gaba dashi da ba za ki iya siyawa ɗanki ko 'yarki kayan sa wa ba ko kuma ki faɗawa hamshazaƙai gidanku su yi miki?" Babanku ma yana da shagon siyarda kayan jarirai ba sai ki faɗa masa ba, ya taimaka kamar yadda ya saba taimakawa ai shi aikin lada ba a gajiya dashi.
  Sosai na harzuƙa da jin waɗannan maganganu nasa, domin har wani zafi can ƙasan zuciyata ke min. ALLAH shi ne shaida ta na fara gajiya da halin Bilal Shattima ta ya duk lokacin da nai masa magana akan abinda ya shafi rayuwarmu sai ya dinga faɗa min maganganu banza. Cike da zallar masifa na hayyaƙo masa "Dallah dakata Bilal! Kai wane irin mutum ne mai matatciyar zuciya, shikenan tun da na ɗaure kaina nace zan dinga ɗaukar responsibilities ɗinmu shine zai ba ka damar ka watsar da neman dogara da kanka, wato kai nufi ni da Babana za mu ta yi ma hidima har ƙarshen rayuwarka? To wallahi idan ma haka zuciyarka ta kimtsa ma gara ma tun wuri ka falka, don ni manufata na ɗan lokaci ne kuma da kake zance Baba babu inda ALLAH ya ɗora masa ɗawainiyarka da ta ɗa da zan haifa.
Kuma ma ai yadda muka yi da kai zarrar mu yi aure za ka nemi koda sana'ar hannu ce ba dole sai aikin gwamnati ba. Amma kai kwata-kwata ba wanna a gabanka to wallahi gara kasani na gaji, Baba kuma ba zai sake taimaka maka da ko kwaldala ce ta ya zan ɗauki nauyi kaina kana na buge da hidintawa 'ya'yanka da ke tafe?"
   Shima jin abinda na faɗa yasa shi hasala ya shiga faɗar maganganu banza nima ina mayar masa da martani a wannan daren sai da muka yi kaca-kaca kafin kowanne mu ya kwanta gami da juyawa juna baya.
Washegari na shirya naje gidan Khairat domin na dubata saboda ta kwana biyu tana faman da zazzaɓi don har drip aka sa mata a gida, daga zuwana fira ta ɓarke a tsakaninmu har muka gangaro akan zance haihuwa da yake cikinta yana gaba da nawa domin ita this month EDD ta ni kuma sai next month.
Daga nan ta shiga nuna min 'yan uban tuli kayan Baby da Jameel ya siya mata ita da unborn child ɗinsu, ga kyau ga tsada sai kallo nake yi ina girgizar kai tare da yabawa a lokaci ta ke tambayata wane tanadi muka yi, tsakanina da Khairat babu ɓoye-ɓoye kaitsaye na fito na faɗa mata gaskiya ko abinda kare bayaso ba mu siya ba. Kuma Love ya ce bashida kuɗi na siyawa kaina ko kuma Baba ya bani. Ba ƙaramin kaɗuwa tayi ba har dasu salati da tafa hannuwa, ni dai sai aikin kallonta nake yi "Haba Jeeddah ai mai zurfin ido da wuri yake fara kuka ko masu babban ƙarfi da wuri suke fara tanadin zuwan haihuwa.
  "Me kike so nayi Khairat ni fa gaskiya nagaji da halin Bilal Shattima fissibilillahi mutum ace ba zai iya tabuƙa komai ba?
   Sai da Khairat ta saki murmushin gefen baki kafin ta matso kusa da ni gami da dafa ƙafaɗata cikin taushin murya ta  ce "Jeeddah kema kinsan ba abinda Bilal Shattima zai iya yi domin shi ba aikin gwamnati ba bai da kuma sana'ar hannu to da me kike so yai miki hidima ko so kike yi yai sata ya kawo miki? Tun farko abinda kowa yake guje miki kenan kika kafe sai shi.
Cikin sauri na katseta ta hanyar cewa
"Dan Allah Khairat abinda ya wuce ki daina tadda shi idan ma kuskure ne na ri ga na tafka shi yanzu hanyar warware shi nake nema don gaskiya ba zan iya ci-gaba da hidimar gidan Bilal Shattima ba. ke abinda ba ki sa ni ba yanzu haka fushi yake yi dani a dalili kawai na ce ya daina kwashe foodstuffs ɗin da Baba ke aiko min yana kai ma Hajja da Aunty Bahijja shikenan fa ya tsire fushi dani, yanzu haka ya daina cin abincina ya daina kusanta ta ni kuma wallahi ko a jikina..
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*EXCLUSIVE LACE AND ATAMFA*

INA KU KE MATA 'YAN KWALISA MA'ABUTA ADO DA KWALLIYA SHIN KINA SO KI BURGE MAIGIDA DA ADO NA KECI RAINI KO KUMA KINA DA BIKI NA MANYAN MATA, DA SUKA AMSA SUNAN SU MATA? TO SHA  KURUMINKI 'YAR UWA KAYANKI SUN TSINKE A GINDIN KABA GA DAMA TA SAME KI DA ZA KI SIYE TSALA-TSALA LACES DA ATAMFOFI KAI HAR MA DA SHADUDDI MASU INGANCI DUK A CIKIN FARASHI MAI SAUKI DA SAUƘAƘAWA DOMIN KAYANMU BA IRIN NASU BANE A EXCLUSIVE LACE AND ATAMFA NE ZA KI KECE RAINI KI YI FI CE DAGA SAURAN MATA.
MUNA DA ATAMFOFI DA LACES, SHADDA, MATERIALS, SHADDA KAMPALA GA MASU BUƘATAR ANKON BIKI KO SUNA SAI SU TUMTUƁEMU A LAMBAR WAYAR MU KO KUMA  KAITSAYE KU ANTAYA A GROUP ƊINMU DOMIN GANEWA IDONKU KALOLIN KAYANMU DOMIN GANI YA KORE JI EXCLUSIVE LACE AND ATAMFA COMPANY ƊAYA TILO DA BA SHI DA NA BIYU. MUNA MARABA GA MASU SIYEN ƊAYA KO SARI DOMIN KULA HULƊAR KASUWANCI DA MU👇👇👇

+234 701 342 5069

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/IKSykPjUQcGKH8HvAQhe4N

024...

Kallo mai cike da zallar mamaki Khairat take mata, ko a mafalki ba taɓa tsammani fitar waɗannan maganganu daga bakin Jeeddah ba. Lallai duk abinda ya ba ka tsoro tabbas wata rana shi zai ba ka mamaki. "Jeeddah ke ce da kanki yau kike faɗin kin gaji da rashin aikin Bilal Shattima ko kuma wata Jeeddar ce aka sauya mana ban sani ba?"
   Haƙiƙani gaskiya yadda nake ji kwata-kwata auren ya fara fice min a rai, danne wa kawai nake yi gami da gudun abinda zai je ya dawo, na sauke numfashi kafin na ce "Khairat ni ce dai Jeeddah da kika sani ba musanyata aka yi muku ba. Wahala ce ke sa mutum ya dawo kan hanya ki sa aranki nima wahala ce take neman ta mamaye ni ta tauye min duk wata ni'ima da jin daɗi da ke ciki ɗakin aure. Yanzu ace hatta da hidimar haihuwa da ta wajaba akan kowane magidanci, ni ce zan yi wa kaina haba wallahi wannan wahalar ta min yawa.
Jeeddah ta ƙarasa magana tamkar za ta rushe da kuka, ni abinda ban gane ba yadda Khairat ta ƙame ƙamm! Tana ta faman kallona ba ko kyaftawa shin ko na faɗin wani abu da ba daidai bane?"
Sai da na kai mata shegen duka a cinya tai wani firgigit kamar wacce ke bacci aka watsa mata ruwan sanyi  sai da ta sauke doguwar ajiyar zuciya tana sosa gun da na buga kafin ta ce "Cabdijam lallai in ba ka mutu ba ka sha kallo Jeeddah sai yau na gasganta zance Mama da Mommy Turai da suke cewa Bilal Shattima asiri yai miki, yanzu asiri ya fara karyewa shiyasa kika fara dawowa kan hanya...
"Kin ga Khairat dan Allah dan Annabi ki daina zance asiri nan wallahi-tallahi ba asiri da Bilal Shattima ya yi min kawai dai wahalhalu da ya sakar min ne ba zan iya ci-gaba da jan ragamar su ni kaɗai ba. Kamata ya yi ace ni ce nake hidintawa Baba ba wai shi ya buge da wahala dani ba.
Sai da Khairat tai shiru tana nazarin maganganuna kafin ta ce
  "Zancenki gaskiya ne Jeeddah amma ki yi duba da yanayi da mijinki yake ciki ki.
Ki sa a ranki duk abinda Baba yai muku ya yi ne domin ya faranta miki ba wai wahala bane da ba zai iya ba na tabbata ba ma zai fara ba. inaso ki sani Jeeddah duk wani uba nagari burinsa 'yarsa ta sami kwanciyar hankali a ɗakin aurenta. Shiyasa Baba yake min hidima. Ni dai shawarar da zan ba ki duk abinda ki ke ji dangane da Bilal Shattima ki yi ƙoƙari ki danne shi a zuciyarki, duk dai nasan abin da ciwo, haka za ki yi haƙuri kina dannewa haɗi da yi masa addu'a amma Dan ALLAH kada ki bari duniya ta gama sani sirrin zamanku.
  "Ai ko ban faɗa ba kowa gama ya sani don har neighbours ɗina sun sha tambayana halan oga Shattima baya zuwa aiki sun ga sai yamma yake fita, tsabar takaici kasa basu amsa nayi.
"Koma menene haƙuri nan dai nace tun farko ki yi shi za ki ci-gaba da yi kina haɗawa da addu'a har izuwa lokaci da ALLAH zai yanke miki wannan wahala, duk da kece kika gayyatowa kanki ita. Yanzu tashi za ki yi zama bai gano mu ba mu je mu siyo ɗan abinda ba a rasa ba kafin ALLAH ya sauke ki lafiya za a san abin yi. Amma Dan ALLAH Jeeddah kada ki faɗawa Mama wannan maganar ko Aunty Farida don wallahi ba ƙaramin ɓaci rai za su shiga ba. Musamman Mama da kika kwana da sani ba son aure nan naku ta ke yi ba.
   "Uhmm... kema Khairat da wani zance kike ai ko giyar wake nasha ba zan fitar da wannan magana ba balle har ta je kunne Mama. Kema na faɗa miki ne a dalili ba mu saba ɓoyewa junanmu damuwar da muke ciki ba.
   "Tou shikenan bara na canza kaya sai mu tafi.
   "Khairat ki barshi kawai nima ina da raguwar kuɗi a account ɗina don na karɓe ATM card ɗina a hannunshi In-sha-Allahu zan yi ƙoƙari na sai koda uniset ne.
  Khairat bata tanka mata ba kawai dai ta kalle ta gami da watsa mata muguwar harara ta wuce bedroom ta sauya kayan jikinta, key ɗin motarta da handbag ɗinta ta ɗauko, tun lokacin bikinmu Jameel ya siya mata mota mai kyau da tsada. Ta kalle ni ta ce "tashi mu tafi mana Jeeddah yamma sai ƙaratowa take yi yanzu nan za ki ji an fara kiran sallar magariba.
Dole na tashi nasa hijabina mu ka tafi kaitsaye wani haɗaɗɗen Kiddies boutique muka nufa, sosai Khairat ta kashewa Babyna kuɗi tun ina mata korafi har na ja bakina na tsuke na zubawa sarautar ALLAH ido.
Sai daff da magariba muka baro boutique ɗin da himilin kaya guda, a cikin tsadaddun boxes har guda uku ga kuma wasu a manya-manyan shopping bags tun akan hanyar mu na komawa gida nake lallaɓo kalmomin da zan godewa Khairat domin tai min abinda cikin sauƙi ba zan iya mantawa dashi ba. Musamman da na tuna lokaci da nake ganiyar haukar son Bilal Shattima banaso a faɗin aibunsa ko kaɗan, na sha ci mata mutunci akanshi na kira ta da munafuka bila-adadin, sai gashi yau  ta rufa min asiri lallai naka sai naka. Kaitsaye gidana muka wuto dai-dai ƙofar shiga apartment ɗinmu tai parking ta buɗe boot muka dinga fito da kayayyakin da muka siyo ina lura da lokaci da neighbours ɗina suka dinga leƙowa ta window suna kallonmu abinka da gidan haya ba dai gulmar tsiya da sa idon masifa ba.
Khairat bata baro gidana ba sai da tai sallah kana ta tayani muka yi arranging kayayyakin inda ya dace, na girka mana jellof ɗin macorroni taci sannan muka yi sallama ta wuce gida.
Yau ma sai ƙarfe 10:30pm Bilal Shattima ya dawo gida sannu da zuwa kawai nace dashi daga haka, ban ƙara kula shi ba. Na yi zato zai yi magana akan new boxes ɗin da ya gani cikin ɗakin baccinmu. Can na kasa haƙuri na fara magana da zuciyata "to ko dai bai lura dasu bane amma kuma ga Baby bathset, Baby hanger da Baby wardrobe, da ke aje a gefe da zai wuce ya shiga bathroom su ma nufinsa bai gansu bane ko dai tankawa ne kawai ba zai yi ba?" sai ma naga yana wani hura hanci, yana cika yana  batsewa sai kace wanda aka zagi uwarsa a gun da ba zai iya ramawa ba. Da dukkan alama abokin mutuwa yake nema. Ni kam yau bana ji masifa shiyasa nace ya bi wani sarkin ba dai ni ba. Don kuwa haye gado nai abina ina chat koda ya fito nayi bacci.
Bilal Shattima yana fitowa daga wanka yai arba da Jeeddah tayi bacci da wayarta a hannu ya ja siririn tsaki ya ɗauke wayar daga tafin hannunta ya ajiye mata akan bedside, kana ya dawo da ganinshi akan fuskarta gaba ɗaya Jeeddah ta canza mishi, har gobe yana jin mugun sonta a zuciyarsa amma ko kusa ba zai iya ci-gaba da jure waɗannan sababbin halaye da ta bijiro masa dasu ba.
Ya kammala shirinsa cikin kayan baccinsa ya ja pillow ya kwanta ya bar tazara mai yawan gaske a tsakaninsu, dama tun sanda suka fara samu rashin jituwa suke irin wannan kwanciyar kowane ya juyawa ɗan uwansa baya. Washegari tana tashi ta bar mishi ɗakin ta koma parlour ƙarfe 10:09am ta shiga kitchen ta haɗawa kanta breakfast kana ta koma ɗaki tai wanka ta shirya cikin atamfar grand satin ɗinki kaftan gown, style ɗin ya fito mata da cikinta sosai tana gama shiryawa ta dawo parlour tana cikin karyawa Bilal Shattima ya fito cikin sauri jikinsa sanye da milk colour jallabiya, hannunshi riƙe da key ɗin machine sosai nai mamaki tashinsa a dai-dai wannan lokaci wanda inda ya fara bacci sai ƙarfe ɗayan rana yake tashi. A hankali na bishi da kallo yayin da shi kuma ko kallona ban yi ba yadda yake sauri yai ya ƙara linka min mamakina yadda naga jikinsa ke rawa ya tabbatar min da babu lafiya.
"Ina kwana?"
Na faɗa da ɗan ƙarfi a dalili yadda naga jikinsa na ɓar-ɓar! Ba lallai bane ya ji ni shiyasa nai magana da ƙarfi.
   "Lafiya qalau!
Ya amsa min da sauri kuma a takaice sai kawai na taɓe baki na ci-gaba da cin abincina hankali kwance zuciya zaune. Ya fice da machine ɗinsa waje ina ji lokaci da ya tashi machine ɗin.
Ina kammala cika cikina na tattare plate da mug na kai kitchen kana na wuce ɗaki na ɗauko handbag ɗina, dama yau ne rana da zan koma asibiti awo, na rurrufe ƙofofi nai tafiyata.
Duk sauri nan da Bilal Shattima ke yi bai wuce kiranshi da Hajja tayi ta faɗa mishi Aunty Bahijja bata da lafiya tun jiya aka yi admitting ɗinta, kaitsaye asibiti da take ya nufa tun kafin ya ƙarasa ya hango babbar 'yarta Nafeesa tana tafiya riƙe da zungurarriyar takarda tana kuka, jikinsa na rawa don har zuciyarsa ta fara yi masa wasi-wasi ko Aunty Bahijja ta mutu ne.
Sai da ya ƙarasa kusa da ita take faɗa mishi jikin nata ya yi tsanani, magani da allurai aka ce ta siyo gaba ɗaya Bilal Shattima ya ruɗe ya karɓi prescription ɗin daga hannunta kana ya riƙo hannunta suka koma dakin da Aunty Bahijja take, Hajja tai mishi bayani likitoci sun ce sai an yi mata aiki a dalili typhoid ya taɓa mata hanji dole sai an yi gaggawa yi mata surgery, gashi anan buƙatar kuɗi kusan dubu ɗari da talatin. "Shikenan Hajja ki kwantar da hankalinki in-sha-Allah komai zai zo da sauƙi ke kuma Nafeesa kukan ya isa haka, ku jira ni yanzu nan zan je na dawo.
Bilal Shattima ya faɗa gami da gaggawar barin ɗakin, yana fita ya zarce wajen wani abokinsa mai suna Rufa'i yana sana'ar saye da siyarwa na babura. Aka yi wa machine ɗinsa ƙudi dubu ɗari da tamanin dama machine ɗin ya sha jiki ya hau adaidaita ya dawo asibiti cikin ɗan ƙanƙani lokaci ya biya kuɗaɗen da aka buƙata. Cikin nasarar aka yi wa Aunty Bahijja surgery sai fatan ALLAH ya tashi kafaɗarta.
Har na dawo daga asibiti banga wata alama dake nuni da Bilal Shattima ya dawo gida ba, ni kuma bana ji zan iya nemansa na ji lafiya, kitchen na shiga na dafa noodless da dafaffen kwai na cinye kayana don ko aje mishi nayi ba ci zai yi ba shiyasa tun farko iya cikina na girka. Sai around 10 o'clock ya dawo a lokaci ina zaune a parlour ina kallon wani Indian series nai mishi sannu da zuwa ya amsa min kamar yadda ya saba amsawa. Ya wuce bedroom jin kaɗan ya fito daga shi sai white vest da boxer briefs ash in colour, fuskar nan tashi a murtuƙe ya nemi kujerar da ke nesa da ni ya zauna tare da crossing legs ɗinshi tsawon lokaci ba wanda yai magana a cikinmu kamar daga sama naji saukar muryarsa a dodon kunnena yana faɗin "Love! Aunty Bahijja batada lafiya har an mata surgery, ki shirya gobe idan ALLAH ya kai mu ki dubota tana specialist hospital ɗaki mai lamba bakwai.
   Ba yabo ba fallasa na ɗago na kalle shi na ce "ALLAH ya kaimu gobe lafiya ita kuma ALLAH ya tashi kafaɗarta.
Ya amsa da "Amin Ya Rabbi.
Daga haka kowanne mu ya ja bakinsa ya tsuke ana gama haska series ɗin dama shi kaɗai ne ya zaunar da ni parlour na miƙe tare da ɗaukar wayata da ke aje akan centre table har na juya sai na ji ya ce "idan ban taƙura ki ba ina buƙatar ruwan zafi zan sha tea.
  Na sake dawowa na aje wayata akan centre table ɗin ina faɗin "Ba damuwa bara na kawo ma dama akwai su a flask.
"Please ki haɗu min da mug da tea spoon.
"Tou!
Na faɗa a gajarce kana na wuce kitchen duk abinda ya buƙata na ɗoro masa akan tray na kawo na aje masa a gabanshi, wata baƙar leda ya jawo dake aje kusa da ƙafafuwanshi ya fiddo da bread da madara da milo na sachet haɗi da ɗan ƙaramin ƙulin sugar, hankalinsa kwance ya haɗa tea sosai mamaki ya kamani domin saida na danganta lamarinsa a matsayin kashin kasuwa tun da yasan muna da wadatatcin kayan tea a gida shine don tsabagen wulaƙanci zai siyo a waje wato nufinsa duk abinda ya kasance nawa ba zai sake cinsa ba. Ashe kuwa yana da aiki don ni na fi so ya yi zuciya ya nemi sana'a, domin na tabbata waɗannan kayan tea ɗin ba kyauta aka ba shi su ba dole sai ya bada kuɗi za a ba shi. Ban ce da shi uffan ba na wuce bedroom abina koda ya shigo nayi bacci, can cikin dare wata irin mashahuriyar yunwa ta tashe ni kaitsaye kitchen na zarce na buɗe fridge na ɗauko rubber container mai ɗauke da spring rolls nasa a microwave na ɗumama na haɗa tea na dawo parlour Ina cikin sha idanuwana suka hasko min gun da Bilal ke ajiye machine ɗinsa, sai naga wayam! Ba machine ɗin nan take gabana ya faɗi sai na zaci ko barayi sun shigo mana gida ne ko kuma ya manta dashi a waje bai shigo dashi ba. Na zabura da sauri na dire mug ɗin tea na nufi ɗaki ina zuwa na shiga bubbuga kafaɗarsa haɗi da kiran sunansa "Love! Love ka tashi ka manta da machine ɗinka waje, walau kuma ɓarayi ne suka shigo mana don daga parlour nake na duba gun da kake ajiye machine ɗin wallahi babu shi a wurin.
Har na dasa aya a zancena sai kallona yake yana yatsine fuska sai da ya gaji da yatsina ya ce "Ki koma ki yi baccinki ɗazu na siyar da machine ɗin.
"Whats! ka siyar da machine fa to me za ka yi da kuɗin?"
Kusan a tare na hambuɗa masa waɗannan tarin tambayoyin.
Sai da ya yi miƙa mai haɗe da 'yar gajeriyar hamma kafin ya bani amsa ta hanyar faɗin "Na biya kuɗin surgery ɗin da aka yi wa Aunty Bahijja.
Sosai wannan furuncin nashi ya bani haushi wato zai iya sayarda machine ɗinsa ya biyawa 'yar uwarsa kuɗin asibiti amma ni ba zai iya sayar dashi ya sai wa unborn child ɗinmu kaya ba. Duk ɗan uban ciwon da na darza akan ciki nan nawa sai dai gidanmu su biya min kuɗi asibiti, kwandalarsa bai taɓa bayarwa ba. Hatta da awo idan zan tafi asibiti bai taɓa bani ko na hawa adaidaita ba. Idan ma na roƙe shi ya kaini sai ya ce dani nasan bayason tashi da sassafe. Amma sai gashi yau bayan tashi da sassafe har machine ɗinsa ya sayar lallai ma Bilal Shattima ya cika cikkaken ɗan reni wayau mai masifar son zuciya. Cikin fusata na ke kallonshi kafin na ce "Ba shakka Bilal sai yau na tabbatar da cewa rai yafi rai a wurinka sai yau na gansu da cewa lalurar 'yan uwanka ita ce lalura ita ce za ka iya faɗi tashi akanta har sai ka nemo mafita akanta. Saɓani ni da nake matarka ta sunnah.
Bilal dukka yau kwana nawa da nai maka magana akan kayan haihuwa?" Sai ce min kayi bakada hali yin amma kana da halin siyarda machine ɗinka ka biyawa Aunty Bahijja ƙudi surgery. Ba ma wannan kaɗai ba sau nawa ana admitting ɗina a asibiti ko kwandalarka bata taɓa ciwon kai ba. Da an yi maganar kuɗi sai dai ka naɗe hannuwa ka ce bakada shi, amma yanzu da yake rashin lafiyar na Aunty Bahijja ne ai gashinan ka siyarda machine ɗinka...
"Dallah dakata Jeeddah! Banaso tsohon iskanci da reni wayau. Wa Bahijja take da shi da ya wuce ni?" Idan ke kina da iyaye da 'yan uwan da ke miki ita bata da kowa sai ni saboda haka duk abinda na mallaka a faɗin duniya nan zan iya kaɗɗa dashi na nema mata lafiya.
   "To naji Bilal nace naji Aunty Bahijja ita ce dolenka ni ba kowan-kowa bace a wurinka, amma inaso ka sani nima nagaji da wahalhalu da ake min a gidanmu saboda haka dole ka nemi sana'a.
   Sai dai ya watsa min mummunan kallo kafin cikin shouting ya ce "Wai ke me ke damunki ne?
Wallahi na rasa ɗan iskan da yake hore miki kunne kike min ɗibar albarka kala-kala domin ada ba haka kike ba.

_Afuwan ina busy shiyasa kwana biyu ku ka ji ni shiru_
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250
      _ku ƙara haƙuri dani wayana ke bani matsala ga kuma matsalar rashin wutar lantarki abin ba a cewa komai sai godiyar ALLAH_

026...

Kujerar rubber Hajja ta dauƙo ta zaunar dani har zuwa lokaci ɗan banza ciwo mara da nake ji bai lafa ba. Sai ma daɗa ƙaruwa yake Babyna kuma tun sanda ya sha fizga daga hannun Babanshi bai sake matsowa ba. Har yanzu yana nan dunƙule a waje ɗaya. Ga uban gumi nake haɗawa gaba ɗaya wuyan hijabin jikina ya jiƙe sharkaf da zufa Aunty Bahijja da ke kwance ta kalloni tana faɗin "Hajja lafiya ba dai haihuwa za ta yi ba ai kuwa watan haihuwar ta bai kama ba da sauran lokaci?"
  Sai da Hajja ta rabani da hijabin jikina kafin ta maida hankalinta akan Aunty Bahijja ta ce "Ba haihuwa bace ba Bahijja rigima ce suke yi ita da Nusaiba har da dambe.
  "Rigima kuma Hajja ita Jeeddah tana cikin wannan hali ta ke da ƙarfin hali yin dambe ni fa da A'isha ta shigo ta kira ki wallahi na zaci naƙuda ce ta kama ta ashe haukarta ce kawai ta motsa.
  Sosai na ji haushin furuncin Bahijja na ƙarshe akaina, wato ita kallo mahaukaciya take min to shikenan a tafi a haka duk da ina jin zafin ciwon mara hakan bai hanani ɗagowa na watsa mata mugun kallo ba gami da yin ƙwafa tabbas bashi taci akwai ranar da za ta biya.
Hajja ta ci-gaba da faɗin "Ni na rasa me ke damunki Jeeddah yanzu banda lalacewa me ya kai ki dambe da tsohon ciki salon ki ji wa ɗa cikinki ciwo ki tashe mu tsaye Dan ALLAH ki dinga aiki da hankali mana.
Samun kaina nayi da ƙarewa Hajja kallo daga sama har ƙasa sai faɗa take yi tana wani kumfan baki da tada harshe sai ka rantse da ALLAH ɗan ta ke ɗauke da ɗawainiya ta. Akwai ɗan raguwar mutuncinta a idanuwana shiyasa na kyaleta ta ci-gaba da cin karenta babu babbaka. Sai da ta gaji don kanta tai shiru A'isha Shattima ce kaɗai ta goyi bayana don duk faɗa da Hajja take yi A'isha Shattima sai ƙoƙarin depending ɗina take yi.
Magana da Aunty Bahijja ta sake jefa min ta fi komai ci min rai ta ƙara linka min ɓaci saboda sosai na fusata ba kaɗan ba don har sai da idanuwana suka cicciko da hawaye.
"Hajja dama kin hutar da kanki da yi ma Jeeddah faɗa domin kina ɓata miyau bakinki ne a banza maganganuki ba wanda za ta ɗauka balle har tai amfani dashi, haƙuri kawai Bilal yake yi da ita domin shi kaɗai yasan irin baƙar wahalar da yake sha akan azababben kishinta, ba hali ta ganshi da mace koda kuwa 'yar uwarsa ce sai ta nemi ta ɗaga masa hankali. Sai kace kanta aka fara aure dama za ki daina wannan haukar yafi miki domin Bilal da kike gani mijin mace huɗu ne in-sha-Allahu ba zai lalace akan mace guda ɗaya tak ba. Gara tun wuri ki koyi yadda ake sarrafa kishi ake danne shi.
Sai yau zuciyata ta ƙara gamsuwa da cewa Bahijja bata ƙaunata duk da tun a can baya tasha nuna min abubuwan rashin ƙauna ni ce dai ban ɗauke su da muhimmanci ba tun da mijina yana sona amma yau da ta fito ƙarara ta juye min abinda ke ƙunshe cikin zuciyarta akaina sai na ƙara yarda lallai bata ƙaunata.
Duk inda raina yake ya gama ɓaci babban abinda ya ƙara harzuƙa ni bai wuce danganta mijina da mata huɗu da ta yi ba. Saboda haka a mugun fusace na kalleta cikin tsanani fushi idanuwana sun rufe ruff na ce "Sai yau na tabbatar da cewa Aunty Bahijja ke muguwa ce ko a cikin mugaye mutane kina cikin baƙaƙƙe wanda da matuƙar wahala su ji daɗi zaman duniya, in banda mugunta da mugun nufi me nayi miki da za ki dinga danganta mijina da wasu mata to kisani duk mugun nufinki da yarda ubangiji kanki zai ƙare don gashinan kin fara gani aya.
Na ƙarashe magana ina huci gami da wulga mata uwar harara.
Daga ita har Hajja salati da sallalami suka hau yi suna wani tafa hannuwa sai kace na faɗi mugun abu. To ko ma mugun abu na faɗa ai su suka jawo saboda haka a shirye nake da na faɗi abinda ya fi wannan muni matuƙar ba a daina danganta mijina da wata mace ba.
  "Jeeddah!
Hajja ta kira sunana tana wani zarar ido kallon sama da ƙasa nai mata na kauda fuska, sai uban huci nake ƙara zubawa ƙirjina sai ya yi sama ya dawo ƙasa. Sosai Hajja ta ƙure ni da kallo kafin ta ce "A'ah babu lafiya wallahi akwai damuwa ke Bahijja maza kama min bakinki banaso shiga sharo babu shanu.
  "Na yi shiru Hajja amma wallahi za ta san ta taɓo 'yar halak da ni take zance.
Da mugun ƙarfi na waigo na kalleta na ce "Ai ni na zaci da shegiya nake zance ashe da 'yar halak ne. Ikon ALLAH su 'yar halak manya to Dan ALLAH Dan Annabi 'yar halak idan har ba cika baki kike yi ba in gani a ƙasa kodai ki sa Bilal Ibrahim Shattima ya sake ni ko kuma ki aura masa Nusaiba wannan kaɗai za ki yi da zai gamsar dani kasantuwarki 'yar halak!
"Hajja kina ji sunan Babanmu ta faɗa gatsal ba ko kunya lallai Jeeddah ba ki da tarbiyya.
Aunty Bahijja ta faɗa cike da gundarin tsana da takaincin Jeeddah.
  Da sauri A'isha Shattima ta dawo kusa dani tana zungurar ƙafata da ƙafarta sai wani ƙiƙƙita min idanuwa take yi nufinta in yi shiru ita ma tasan aiki banza take yi don ba shiru zan yi ba. Matuƙar Aunty Bahijja ba ta saita shegen bakinta ba ta daina yaɓa min maganganu banza da na wofi nima ba zan daina mayar mata da martani ba tun ba tsoronta nake ji ba.
  "Bahijja kar na sake jin bakinki ki kyaleta tayi ta yi ita kaɗai in tagaji dole tai shiru ai ƙarfe ɗaya baya amo.
Hajja ta faɗa tare da jan kujera ta nufi kusa da gadon Aunty Bahijja ta zauna, tana ci-gaba da ba ta baki karta kula ni.
A'isha tai ƙasa da murya ta ce min
   "Dan ALLAH Jeeddah ki yi shiru ya isa haka ki tuna Aunty Bahijja yayar mijinki ce bai kamata ki biye mata ba ku dinga musanya yawu ba.
  "Shikenan don tana yayar mijina sai na kyaleta ta yaga min rigar mutunci? Da kike zance yayar mijina ce ai ba ita ta haife shi ba balle tai min gadara.
  "Shikenan koma menene ki yi shiru da bakinki faɗar irin waɗannan maganganu bashi da amfani.
"To na ji nayi shiru amma wallahi-tallahi daga yau na kula gaba mai tsanani tsakanina da Aunty Bahijja ko a lahira banaso ALLAH ya haɗani da ita.
Har A'isha Shattima ta buɗe baki tai magana aka turo ƙofa sai kawai ta huɗiye abarta.
Bilal Shattima ne ya shigo da 'yar gajeriyar sallama ɗauke da bakinsa Hajja da Aunty Bahijja ne suka amsa mishi sai kawai ya zuba min idanuwanshi jikina ya bani cewa yana kallona, don ni ko kallo bai isheni ba. Na ɗago fusatattun idanuwana na kalle shi dasu yadda ya ga ina aika mishi mugun kallo yasa yai sauri ɗauke idanuwanshi daga kaina. Hajja tayi gyaran murya gami da kiran sunanshi "Bilal!
  "Na'am Hajja.
"Ɗauki matarka ka kaita asibiti da take awo a dubata gudun faruwa matsala sannan kuma ka ci-gaba da haƙuri ka daina biye mata ka ji kou?"
  Da mugun sauri na maida hankali da idanuwana kansu mamakin furuncin Hajja ya lulluɓe ni kuttt....amma gaskiya matar nan 'yar bala'in so zuciya ce banda kafiri son zuciya irin nata wai ɗanta take ba wa haƙuri akaina ai ni ya dace ta ba wa haƙuri ni da aka ha'inta aka ciwa amana amma tsabagen son zuciya irin nata sai ɗanta take cewa yai haƙuri, kada ALLAH yasa ya haƙura ɗin ya ɗaɗe bai ɗauki mataki akaina ba.
Duk waɗannan maganganu ni da zuciyata ke yi su amma da ka kalleni za ka ga yadda bakina ke musu-musu ko ba ka tambaya ba kasan martani ne nake mayarwa.
   "Shikenan Hajja duk yadda kika ce haka za a yi amma duk da haka sai na nunawa Jeeddah kuskure ta na tozarta ni a bainar jama'a.
A fusace na kalleshi na watsa masa baƙar harara kana na ja guntun tsaki tare da taɓe baki, na miƙe rai ɓace duk da ciwon da nake ji a ƙasan marar ta hakan bai hanani fizgar hijabina ko sakawa ban tsaya yi ba na nufi ƙofar fita dashi a hannu duk kiran da Hajja  take min ko waigowa ban yi ba nai kunne uwar shagu da ita nai tafiyata, Bilal ya biyoni a baya ina jinshi a bayana, yana kwalla min kira shima nai banza dashi sai da na kawo reception kana na tsaya nasa hijabina tsayawar da nayi yasa shi haɗawa da gudu ya tadda ni reception ɗin. Yana zuwa ya rufe ni da faɗa cikin fusata yake faɗin "wai ke ba ki ji duk kiran da ni da Hajja muke miki bane?"
Sai da na kalleshi na watsar kafin nace "To sai aka yi yaya don naji kuna kwalla min kira, kai bari ka ji Love tura fa ta kai bango na gaji da wulaƙanci da ku ke min kai da danginka ya isa haka. Idan har ka gaji da zama dani babu dole. Amma wallahi-tallahi ba zan ƙara lamunta jin Aunty Bahijja tana danganta ka da wata mace ba, domin mataki da zan ɗauka daga kai har ita kai har ma da baƙar munafuka nan Nusaiba ba zai muku daɗi ba.
   Ina ƙarashe magana na juya na fice daga reception don bani da lokaci sauraren amsar da zai bani muradina ya ji abinda ke raina kuma na zazzage masa, da sauri ya biyo ni yana faɗin "wai za ki tsaya na kai ki asibiti ko za ki ci-gaba da nuna baƙin kishinki na hauka ne?"
A mugun fusace na juyo na galla masa harara gami da jan tsaki.... mtsssss!
Ina fita gate na sami adaidaita ina shiga Bilal yana ƙarasowa "kin ga Love ni ban damu da haukarki ko kaɗan ba damuwata ɗaya lafiyar Babyna.
Uffan ban ce dashi ba na umarci mai adaidaita ya ja adaidaita mu tafi, ana na barshi tsaye ya bi adaidaita da kallo har muka ɓacewa ganinsa kafin ya yi ƙwafa tare da cizon gefen baki ya koma cikin asibiti. Kaitsaye asibiti na wuce da kyar na sami gani likita sakamakon yamma tayi  scanning aka umarce ni da na je nayi in takaice muku labari ranar na sha wahala sosai bayan na kawo hoton likita ta tabbatar min da lafiyar Babyna. Tun kafin na iso gida naga alamar hakan domin sai kicking ɗina yake yi.
A tunanina Bilal zai dawo gida da wuri sai naga saɓani haka don har nayi bacci bai dawo ba a takaice sai da asuba na ganshi, ko kallon arziki bai haɗa ni dashi ba. Ban ƙara tabbatarwa da Bilal ya gaji dani ba sai yau domin ko ya tambaye ni ya nake ji hakan ya ƙara fusata ni na harzuƙa iya harzuƙa na ayyana wa zuciyata gidanmu zan tafi. Shiyasa yana fita na shiga tattara duk wani abinda yake da amfani gareni. Dama tun jiya a fusace nake na kasa goge hoton ganinshi da Nusaiba da nayi da kuma furuncin da Aunty Bahijja tayi...
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

025...

Sai da na ƙare masa kallon takaici kafin na hayyaƙo masa kamar zan cinye shi ɗaye, ina faɗin "Wato nufinka na zuba maka idanu mu yi ta zama a haka? To kasani ci da sha na sun rataya ne a wuyanka ba da na mahaifina ko 'yan uwana ba. Ita kanta Aunty Bahijja da ka ke iƙrarin akanta babu idan nauyin neman lafiyarta ya zama maka dole kawai dai za ka iya taimaka mata idan kana da halin taimakawa. Kuma da kake zance an hore min kunne ba wanda ya hore min kunne kawai dai na gaji da wahalhalu gidanka ya kamata zuwa yanzu ka zama namiji.
Yadda yake kallona yasa na gano ba ƙaramin takaici maganganuna suka haifar masa ba. Don har wani huci yake yi yana hura hanci, ni kan ko a jikina.
  "Gaskiya Jeeddah ke ɗin cikakkiyar mayaudariya ce kin manta ke ce da kanki ki ka yi min tayin na aure ki koda banida aikin yi, shine yanzu za ki zo min da zance banza dana wofi to idan kin gaji ba sai ki ɗauki mataki ba.
"Da bakinka ka ke faɗi na ɗauki mataki kou?
"Kwarai kuwa.
Ya sake tabbatar min akan abinda ya faɗa.
"To shikenan Bilal ka zuba ido za ka ga irin kalar matakin da zan ɗauka kuwa.
Daga haka na fizgi pillow na koma parlour ranar a parlour na kwana cike da kudurunka kala-kala.
Washegari ko ina kwana da ke haɗani dashi ban ce masa ba saboda tsabagen takaicinsa bai barni ba, tun cikin dare da na bar masa ɗaki ban ƙara komawa cikinsa ba. Hatta da wanka a ɗayan bedroom na shiga nayi inda ALLAH ya taimake ni ina da kaya a ɗakin. Sai ƙarfe ɗayan rana ya tashi daga shegen baccinsa na asarar na mutuwar zuciya ya yi wanka ya shirya cikin brown shadda ɗinki tazarce ya saka hula da ya dace da kalar shaddar, koda ya fito ina kitchen Ina haɗawa kaina lunch sai gashi ya shigo, yadda bai tanka min ba nima ban tanka masa ba, kaitsaye wajen flask ɗin ruwan zafi ya nufa ya ɗauki mug kana ya ɗauko raguwar kayan shayinsa na jiya ya haɗa tea da guntun bread ɗinsa ya fice zuwa parlour. Na bishi da mugun kallo na ja guntun tsaki gami da faɗin "kalli wannan kayan haushi da takaici tsakiyar rana hatsa-hatsa zai sha tea wannan dakarci har ina?"
"Mtsssss!
Na sake jan wani guntun tsaki
Don kada na ƙara gani fuskarshi dake bala'in ƙara min haunshinsa yasa na ƙi fita parlour sai da ya fita kana na fito, sai cin raina nake yi ni kaɗai wuraren la'asar na ji ana knocking ƙofa, da kyar na yunƙura na tashi a dalili nauyi da girman da cikina ya yi, ina tafe ina tura shi gaba na buɗe ƙofa da A'isha Shattima na ci karo murmushi na sakar mata gami da faɗin "Wata sabon gani su Shatu manya ganinku sai an cike Form yau an tuna dani?"
"Karki yi min sharri Jeeddaty kullum cikin tunawa dake nake ya jiki-jiki?"
Aisha Shattima ta faɗa ita ma tana murmushi.
"Al-hamdulillah! Gashi nan muna fama.
Jeeddah ta faɗa gami da maida ƙofa ta rufe koda ta juyo har A'isha Shattima ta ƙarasa cikin parlour tare da nemawa kanta matsuguni, kafin Jeeddah ta zauna sai da ta kawo mata ruwan roba da coke mai sanyi kana ta zauna akan kujerar dake kallon A'isha tana faɗin "A'isha ya gida dasu Hajja?"
"Lafiya qalau sai dai Aunty Bahijja aka kwantar asibiti har da surgery aka yi mata amma ai Ya Bilal ya faɗa miki kou?"
  "En! Ya faɗa min nufina sai zuwa anjima na je na dubata. ALLAH ya bata lafiya.
  "Amin! Ai da kin yi zamanki tun da ke ma bakida lafiya, ɗazu ne a asibiti da na tambaye ki Ya Bilal ya ce min ba ki jin daɗi shiyasa ma na zo in dubaki.
  Murmushi yaƙe Jeeddah tayi kafin ta amsa da cewa "Ayya da ma ba ki wahalar da kanki kin zo ba, ba wani ciwo bane mai tsanani ƙafafuwana ne ke min ciwo su ma yanzu na ji sun daina. In za ki wuce sai mu tafi tare.
"Tou Shikenan ALLAH ya raba ki da ciki nan lafiya Jeeddah.
  "Amin Aisha nagode.
Daga haka suka ci-gaba da zantawa akan ciwon Bahijja, sai yamma lis suka nufo asibiti cikin adaidaita a bakin gate aka ajiye su suka tako da ƙafa zuwa cikin ainihin asibiti ɗin. Tun kafin su ƙarasa ward ɗin da Bahijja take Jeeddah ta hango Bilal Shattima da Nusaiba suna tsaye daff da juna sai firar suke zubawa yayin da Bilal Shattima ke ta faman tintsira dariya kamar wanda aka yi wa albishir da yayewar matsalolinsa na rayuwa. Tun kafin mu ƙarasa kusa dasu na fara jin tuƙuƙi da ƙunar zuciya, har wani dishi-dishi nake gani, ƙirjina sai dukan uku-uku yake yi da kyar na haɗiye wasu miyau masu mugun ɗaci sama-sama nake jin maganar A'isha Shattima tana faɗin "a'ah ba dai Nusaiba ce nake hangowa da Ya Bilal ba?
Kasa amsa mata nayi domin tuni wani irin mashahurin kishi ya gama kanainaye min ciki da waje zuciya na matsu na kai kusa dasu. Shiyasa na ƙara sauri ina tunguɗa katon cikina gaba wallahi ko gani gabana bana yi duk inda na samu jifa ƙafafuwana kawai nake yi koda muka ƙaraso kusa dasu tempreture na ya haye sai huci nake kamar naci babu a gabansu na ja birki yayin da sun shagala da firar su ta arziki yoo...dole nace ta arziki domin yadda suke kwasar dariya tamkar waɗanda basu da wata damuwa a rayuwa na zuba masu fitinanu idanuwana dogon numfashi da na ja kana na sauke ya ankarar dasu  wanzuwa ta a gabansu, don haka Bilal Shattima ya bi ya ruɗe ko kaɗan bai yi tsammanin ganina a asibiti ba kuma a daidai wannan lokaci ya shiga ƙiƙƙiniya haɗa sunana cikin sarƙewa lafazi "lo...ve...! Ke ce ya me kika zo yi... a'ah ina nufi ke da wa kika zo okay ke da A'isha ne?"
Gaba ɗaya ya bi ya ruɗe ya dabirce alamun rashin gaskiyarsa ya bayyana ƙarara.
  Ya sake maida ganinshi kan A'isha Shattima yana faɗin "A'isha ke ce kika taho da ita kou bana faɗa miki bata da lafiya ba?"
Kafin A'isha Shattima ta bashi amsa Nusaiba tai karaf ta karɓe zance ta sigar wasa ita a dole abokiyar wasanshi ce ta ce "lallai sai yau na ƙara yarda Ya Bilal ka zama mijin tace kalli dan Allah yadda jikinka ke rawa don ka ga Aunty Jeeddah, to gara da Allah ya kawo ki Aunty Jeeddah ga ki ga shi ya faɗa miki abinda ya gama faɗa min yanzu nan ko in tona ne ya Bilal?"
Ta ƙarashe magana tana kallonshi tana ƙunshe dariya gami da fari da ido yayin da shi kuma sai wuƙi-wuƙi yake da idanuwa ya kalle ni kana ya kalli Nusaiba laɓɓanshi sai rawa suke yi kafin ya gama lallaɓo abin faɗa tuni na ɗauke ta da bahagon mari, kafin ta wartsake na sake dalla mata wani da alamu wannan yafi na farko zafi don sai da ta yi tangal-tangal kamar za ta kife ƙasa ALLAH ya taimake ta akwai pillar kusa da ita tai maza ta dafa pillar ɗin. Cikin tafarfasar zuciya nace "ke don uwar ubanki ni za ki nunawa karuwancin baƙar akuya ai ba tun yau ba na gama sani soyayya kuke yi a ɓoye wato duk abinda kuke yi a waya bai isheku ba har sai kin tare ni kin faɗa min ɓaro-ɓaro soyayya kike da mijina kou?" Ban yi ƙasa da guiwa ba ta hanyar cukumo hijabinta na makata jikin pillar ɗin na shiga dukanta babu ji babu gani sai lokaci A'isha Shattima tayo kanmu ta shiga ƙoƙari janye ni, a mugun fusace na juyo nasa hannuwana duka biyu na ture ta sai da ta faɗi ƙasa ɗabass....kana na koma kan Nusaiba wacce ke tsaye tana kallon ikon ALLAH don ba ƙaramin mamaki na bata ba. Kafin ta gama mamakinta na sake rufe ta da duka ta ko ina bugu nake kai mata. "Ya Bilal tsayuwar me kake yi da ba za ka shiga tsakaninsu ba ka tuna da hali da Jeeddah  take ciki kada ta ji ma ɗan cikinta ciwo?"
Haba wa sai lokaci ya dawo cikin natsuwarsa ya riƙo kafanɗuna duk iya ƙoƙarinshi na gani ya ɓamɓare ni daga jikinta ya kasa, ni wallahi kwata-kwata na manta da akwai wani abu wai shi ciki a jikina. Yayin da Nusaiba ta kasa rama dukanta da nake yi a dalili cikin da nake ɗauke dashi sai dai kawai tana  ƙoƙarin kare dukan da hannuwanta. Gami da zagina faɗin take yi "Wallahi kin ci arziki cikin da kike ɗauke dashi da wallahi irinki bata isa ta dakeni na kyaleta ba, kuma ki sani soyayya muke yi ni da mijinki idan kin isa ki hana shegiya mai tsinane kishi. Wacce bata iya kula da miji ba sai shegen kishi tsiya. Kuma wallahi-tallahi idan ALLAH ya yi duniya don Manzo sai na auren mijinki naga ƙarshen zazzafan kishinki.
Sosai na ƙara hasala da jin irin martani da take mayar min dashi idanuwana suka rufe ruff na dawo tamkar mahaukaciya sabon kamu, sai bugunta na ke yi ina surfa mata zagi ta uwa ta uba.
Tuni hankulan mutane dake harabar asibiti ya karkato kanmu suka yi dafifi suna ba wa idanuwansu abinci.
Da kyar Bilal Shattima ya ɓamɓare hannuwana daga wuyanta, ban fasa antaya musu manya-manyan zagi  daga shi har Nusaiba ɗin ba wanda na ragawa"ɗan iska kawai wadda baya gudun abin kunya ba tun yau ba nake zargin kana cin amanata da wannan 'yar iska mai siffar karuwan ƙauye to wallahi kasani yau ko ni ko ita a wurina don sai naci uwarta naga ubanda ya tsaya mata. Da na bar wannan shegiya gara a ɗauki gawa ta anan wuri.
  "Jeeddah ya isa nace ya isheki haka wai ke wacce irin mahaukaciya ce ba ki gani hali da kike ciki ko so kike yi ki kashe min  ɗa?"To wallahi idan wani abu ya sami cikina sai nayi shari'a dake taɓaɓɓiya kawai.
   "Dallah...rufewa mutane baki baƙin munafuki algungumi uban me ka taɓa tsinanawa cikin balle ka yi kirarin shari'a dani. Ko dai tabarmar kunya ce kake ƙoƙarin naɗe wa?"
Jin abinda na faɗa ya ƙara linka fushinsa ya yo kaina a mugun fusace kamar zai rufe ni da duka da gudu A'isha Shattima ta rugu ta shiga tsakaninmu tana faɗin "Dan ALLAH Ya Bilal karka koma kanta kasan halinta da zafin kishi ja Nusaiba ku bar waje nan. Kalli ka ga yadda mutane suka yi dafifi suna kallonku.
  Jin da nayi A'isha Shattima ta ce ya ja Nusaiba yasa na sake yi kukan kura na cukume  wuyan Nusaiba na danne maƙoshinta da dukkan ƙarfina har wani kakari take yi. Gani ina yunkurin kisan kai yasa Bilal Shattima yai min wata baƙar fizga sai da ɗa cikina yai hajijiya ya dawo ƙasan mara ta ya dunƙule waje guda. Bansan sanda na saki maƙoshin Nusaiba ba na kwatsama ihu gami da dafe cikina da dukkan hannuwana tare da durƙusawa akan gwuiwayina, cikin tsananin azaba nake faɗin "wayyo ALLAH cikina! Shikenan Bilal ka kashe min Baby wayyo jama'a ku taimake ni saboda karuwarshi zai kashe ni.
Wani matashin saurayi ne ya matso kusa damu hannunshi riƙe da foodbasket ya kalli Bilal yana faɗin
  "Haba malam miyasa za ka koma ɗaya da ita a tunanina taci ragi ko don albarkaci cikinka dake jikinta amma ka fincike ta haka ba ka ko tsoron ka ji ma ɗan da ke cikinta ciwo?" Ga dukkan alamu bakada tausayi balle ɓurɓushin imani.
Ya ƙarashe magana yana mai gallawa Bilal arniyar harara.
Ran Bilal ya ƙara ɓaci da jin furuncin wannan saurayi saboda haka cikin fusata ya ce "Ina ruwanka matarka ce ko matata kasan abinda take ƙoƙari aikatawa ne?"
   "Duk girman laifi da ta aikata bai kamata a matsayinka na mai wadatatce hankali ka biye mata ba kayi ƙoƙari ka ja ta ku tafi gida sai ku yi solving matsalarku a can musamman idan ka yi la'akari da nan asibiti ne wuri ne da ya tara dubannan mutane.
Kafin Bilal Shattima ya yi magana A'isha Shattima ta kwasa da gudu ta nufi ɗakin da Aunty Bahijja take ta kira Hajja, suka dawo tare yayin da wasu daga cikin 'yan kallo suke ɗorawa Jeeddah laifi  kaɗan daga cikinsu ne ke mara mata baya.
  "Subhanalillah! Bilal meke faruwa ne?"
Hajja ta faɗa sa'ili da ta iso wajen.
Kafin Bilal ya bata amsar tambayarta idanuwanta suka sauka kan Jeeddah dake durƙushe tana runtsar idanuwa gami da yarfe hannuwa na azababben ciwo da marar ta ke mata. Da sauri Hajja tayi kanta baiwar ALLAH jikinta har rawa yake yi ta kamata  da kyar Jeeddah ta miƙe tsaye, Hajja ta nufi ɗakin da Aunty Bahijja take da ita....

_Dan ALLAH ku ƙara haƙuri da ji ni shiru da ku ke yi in-sha-Allah yanzu na dawo da ƙarfina_
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

027...

Bilal Shattima har ya tari adaidaita sai ya tuna da ya manta da wayarshi dake charging a parlour. Sai haƙuri ya ba mai adaidaita ya juyo gida. Yana shigowa yaci karo da boxes ɗin kayan Jeeddah a tsakiyar parlour, idanuwanshi ya firfito dasu gabanshi yai mugun faɗuwa "ba dai Jeeddah tafiya za tai ba?"
Ya faɗa a bayyane daidai tana fitowa daga bedroom tana ƙoƙarin sanya hijabinta, ta ganshi  tsaye sake da baki a fusace ta zo ta gitta shi za ta wuce da sauri ya riƙo damtse hannunta ya jawo ta a hankali ta dawo gabanshi, ya tsare ta da kallo da yaudararin idanuwanshi cikin tausassa lafazi ya ce "Love ina za ki je da akwatuna haka ba dai yaji za ki yi ba?"
"Kwarai ma kuwa yaji zan yi don banga amfani zama na da kai ba gara na koma gaban Iyayena tun da nima ina dasu.
"Na shiga uku!
Ya faɗa har da wani dafe ƙirji ya ƙara firfitowa da idanuwanshi da sauri ta kauda idanuwanta daga kanshi nan take ya marairaice ya yi kalar tausayi, cikin kwantar da murya ya ce "mi ya yi zafi Love da za ki yi yaji dukka yaushe muka yi aure da har haka za ta ɓullo a tsakaninmu, ko so kike maƙiya su yi mana dariya?"
Da mugun sauri ta juyo ta kalleshi tsabagen takaicinsa bai barta ta jure kallon nashi ba sai kawai ta ja dogon tsaki, ta nufi cushion ta zauna, saboda nauyin cikinta ba zai barta ta daɗe a tsaye ba.
Gani haka yasa ya biyo ta ya durƙusa gabanta ya riƙo dukkan hannuwanta ya haɗe da nashi ya ƙara marairaicewa fiye da farko, tare da ƙarya murya yake faɗin "ban taɓa tsammanin bayan aure soyayyarmu za ta rikiɗe ta koma ƙiyayya ba Jeeddah. kwata-kwata a yanzu kin daina sona, na kuma rasa dalili ko laifi da nai miki da kika tsaneni har haka....
   "Dallah dakata Bilal!
Ta katse shi da sauri kuma a fusace kana ta ɗora da cewa "Kai yanzu har kana da bakin furta kalmar na daina sonka?" Bayan duk irin wulaƙanci da cin kashi da kake min kai da 'yan uwanka duk yadda ake nuna ƙololuwa ƙauna da sadaukarwa Bilal nayi maka, amma duk da haka kai da 'yan uwanka ba ku gani ba balle ku yabamin kullum cikin gani aibu na suke a takaice ma so su ke su liƙa ma 'yar uwarka Nusaiba to wallahi-tallahi muddin idan ka bari zugi da ingiza maikantu da Aunty Bahijja take maka yai tasiri akanka ka gauraya soyayya ta da ta Nusaiba ni da kai hayatan-hayatan mu rabu kenan rabuwa kuma ta har abada koda kuwa so da nake maka zai zama ajalina.
   "Subhanalillah! Dan ALLAH Love ki daina faɗar kalmar rabuwa a tsakaninmu ni dake tamkar hanta da jini ne ɗaya bayayi sai tare da ɗaya. Ban taɓa kallon Nusaiba da wata manufa face ta 'yan uwantaka ba.
   "Look Bilal ni fa banaso yaudara idan ma ba ka sonta ai Aunty Bahijja ta ce kai ɗin mijin mace huɗu ne. Sannan kuma rashin kulawar da kake nuna min ni da abinda ke cikina ya isheni gara na bar maka gida na tafi inda za a nuna min cikakkiyar ƙauna da kulawa. Gara na ba ka space ka ji daɗin nunawa Aunty Bahijja ita ce jininka tun da ni ba ka haɗa komai dani ba.
  "Haba....Haba! Love wannan wacce irin magana ce Dan ALLAH kada ɓacin rai yasa ki min sharri?"
Sai da na saki masa baƙar harara kafin na ce "Sharri ko wato sharri ma nake maka Bilal?" To shikenan mu tafi a haka nayi maka sharri dama kasan aikina ne...
Da sauri ya rufe min baki da tafin hannunshi ya daɗa lankwasa murya yana ci-gaba da rarrashina gami da sabunta alƙawari da yai min a can baya na ba zai taɓa yi min kishiya ba. Nan take na nemi fushina na rasa da kanshi ya jide akwatuna na ya mayar ɗaki, fitar da zai yi fasawa ma ya yi ranar hatta da girki shi yai mana wata irin kulawa ta musamman yake nuna min. Sai da yamma lis sannan ya fita kuma ƙarfe tara daidai ya dawo gida har da tsarabar kilishi ya riƙo min ranar kwana muka yi muna faranta wa junanmu tamkar mu dauwama a haka kada wani saɓani ko rashin jituwa ya sake shiga tsakanimu.
Washegari ya nemi na shirya mu je asibiti na duba Aunty Bahijja nan take annurin kan fuskata ya gushe dama muna karya kumallo ne yai min magana, duk sai na bi na haɗe rai ina shirin fara zazzaga masa tijara yai sauri katse ni ta hanyar cewa "ba sai kin ce komai ba Love na fahimci ki zan jira har ki huci ko bayan an sallame ta ne sai mu je gidanta ki dubata kin ji?"
Tsabar takaici kasa cewa komai nayi sai faman jujjuya mug ɗin hannuna nake.
_*AFTER THREE WEEKS*_
*{BAYAN SATI UKU}*
Tun da sassafe Aunty Farida ta kira ni da albishir ɗin Khairat ta haihu ta sami Baby girl, tsabagen farin ciki kwance nake ina fama da zazzaɓi amma bansan sanda na miƙe zaune ba. Duk ciwo da nake ji na nemi shi na rasa nan take na tashi na shirya ko Love ban kira ba sai da na isa asibiti da take sannan na kira shi. Da yake ita ta haihu da kanta daga ita har Babynta suna cikin ƙoshin lafiya, shiyasa tana gama hutawa aka yi discharge ɗinta, kaitsaye gidan Mama aka yo da ita domin wanka jego har dare ina gida sai da Love ya gama zaman majalisa ya biyo min muka dawo gida. Washegari ma gidanmu na yini sai ya kasance kullum gida nake wuni muna shirya yadda bikin suna zai guduna. Ranar suna Baby taci sunan khadijatul-iman.
Da yamma aka gudanar da walima mai jego da Babynta tsabar kyau da suka yi kamar ka sace su ka gudu sutura mai tsada ta kece suka sa, domin lace ɗin da Khairat tasaka kaɗai kuɗin sa kimanin dubu ɗari biyu yake. Ni kaina Khairat da 'yarta sun yi matuƙar burge ni sai dai ko kusa ba zan kwatata kaina da ita ba. Bayan sati biyu da haihuwar Khairat cikin dare na tashi da matsanancin ciwon mara abu kamar wasa sai gashi na kasa ɗaurewa dole na tashi Love daga bacci, duk ya bi ya ruɗe da gudunsa ya fita ya nufi apartment ɗin officer Abdul-ganiyu domin neman taimako kasancewar officer yana da mota da taimakon matarsa aka sanya ni mota sai asibiti tun abin ƙarfe biyu dare Jeeddah ta fara labour har garin ALLAH waye ba alama za ta haihu, gani haka yasa matar officer Abdul-ganiyu ta shawarci Bilal da ya kira gidansu Jeeddah ya sanar musu haihuwa ce tana asibiti. Ya kira Aunty Farida ko five minutes ban yi da kiran nata ba sai ga ta, ta zo tun kafin ta iso asibiti ta kira Mama da mommy Turai ta faɗa musu, cikin ɗan ƙanƙani lokaci danginta suka cika asibitin. Har ƙarfe 11 safe tayi ba ta haihu ba, gaba ɗaya hankalinsu Mama ya tashi. Sai baƙar wahala take sha gaba ɗaya ƙarfinta ya ƙare fahimtar da likitoci suka yi ba za ta iya haihuwa da kanta ba yasa suka faɗawa Bilal cs za a yi mata nan da 20 minutes kuma da gaggawa saboda ta jigata matuƙa ana buƙatar su gaggauta siyo kayan da za a yi theatre dasu sai kuma jini da za a yi amfani da shi.
Nurse ta kawo musu takarda mai ɗauke da jerin abubuwan da likita ya buƙata, har Aunty Farida ta karɓa Bilal Shattima ya ce ta kawo zai je ya siyo kafin tai magana ya kwace takardar al'hali ko kwabo ba shi dashi ya yi haka ne gudun kada dangin Jeeddah su rena shi gara ya je ko bashi ne ya karɓo, yana fita daga asibiti ya hau adaidaita ya kira Hajja da Aunty Bahijja ya gayamusu hali da ake ciki, kaitsaye shagon abokinsa Abbas ya nufa.
Aunty Farida ta kira Ya Kabeer ya zo ya bada jini saboda blood group ɗinsa ɗaya da Jeeddah, cikin abinda bai fi five minutes ba sai gashi ya zo aka ɗibi jini nasa duk wani shiri da likita zai yi kafin gudanar da cs ɗin ya kammala Bilal Shattima kaɗai ake jira, shiru-shiru gogan naku bai dawo ba har lokaci da za a shiga da ita ya yi babu Bilal Shattima babu labarinsa, Mama da Mommy Turai sai uban faɗa suke zabgawa suna kwashe masa albarka dole aka sake rubuta musu wani prescription yayin da likita sai masifa yake musu su na bashi haƙuri da mugun sauri Ya Kabeer ya je ya siyo yana dawowa aka shiga da ita.
Cike da zallar masifa Mama take faɗin "Tsawon rayuwata ban taɓa gani gantalalle matsiyaci irin miji nan na Jeeddah ba. Wallahi tun farko banso Farida ki bashi takarda nan ba domin nasan da wuya ya iya tabuƙa abin kirki.
   "Wallahi nima Mama ba a son raina na bashi ba ai kina gani kwata ya yi daga hannuna nurse tana miƙo min ya karɓe da ƙarfi.
Mommy Turai ce ta karɓe zance ta hanyar faɗin "Ku bar ni da ɗan Iska yaro muddin ya dawo ina cikin asibiti nan sai naci mutuncinsa daga sama har ƙasa mu rena wa hankali wato nufinsa ko Jeeddah ta mutu ko tayi rai ba abinda ya dame shi.
"Bari kawai Turai ni kaina wannan karo ba zan kyale Bilal ba da shikenan mu ma irinsa ne matsiyata da muna kallo rayuwar Jeeddah za ta salwanta kou?"
Mama ta faɗa cike da takaici hatta da Ya Kabeer ya fusata babban laifi Bilal da ya gani ya kuma bashi mugun haushi don me da zai karɓi prescription al'hali yasan a gaggauce ake so a shiga da ita theater zai je ya yi zamanshi sai ya danganta hakan a matsayin sakaci da wulaƙanci jira kawai suke ya dawo kowanne ya sauke masa haushi da takaicinsa da yake ji. Ana ciki haka sai ga Hajja tare da Aunty Bahijja da Hajiya Bintu sun zo a cikin reception suka tadda su Mama tsatsaye sun yi jigun-jigun kowanne su ka kalleshi za ka hango tsantsan damuwar da yake ciki, ko sallama da suka yi Aunty Farida ce tai ƙarfi hali amsa musu. Da suka tambaye jikin Jeeddah anan kan ba wanda ya amsa musu, sai kawai suka bi ayarin tsayuwa. Suna cikin wannan hali sai ga Bilal Shattima ya dawo tare da abokinsa Abbas, tun kafin ya ƙaraso wajensu gabansa ya shiga faɗuwa da mugun sauri kuma rai ɓace Ya Kabeer ya tarɓe shi yana faɗin "Kai don buhun wulaƙanci sai yanzu ka ga damar dawowa ai da karka dawo ka yi zamanka domin yanzu banga amfani da kaya da ke hannunka za su yi mana ba.
Kafin Bilal Shattima ya sami damar magana Mommy Turai ta karɓe zance tana faɗin "Ai ni Kabeer ban so ka fara masa ta kalaman fatar baki ba kamata ya yi ka fara tsinke baƙi munafuki da mari, in yaso daga bisani ka kora masa da jawabi.
Bilal Shattima ya sadda kanshi ƙasa sosai ya ji ya yi muguwa musanta, saboda daga Mommy Turai har Ya Kabeer kowanne su cikin ɗaga murya ya yi masa magana hakan ya jawo hankali wasu tsirarun mutane kansu.
Mommy Turai ta dawo da ganinta kanshi tana masa kallo mai cike da zallar wulaƙanci kana ta ce "Ikon ALLAH! wato kai Bilal dirka ciki kawai ka kware dashi ba ka san yadda ake ɗaukar wahalhalu sa ba kou?" To bari ka ji wallahi-tallahi idan wani abu ya sami Jeeddah ko da ɗa cikinta sai mu yi shari'a da kai baƙin matsiyaci marar imani kawai.
   "Wallahi Bilal ka bani mamaki tun farko kasan bakada kuɗi miyasa za ka karɓi prescription daga hannuna da sai ka bar mana mu masu kan ɗauka mu ɗauka, amma ina amfani baɗi babu rai wannan kayan takaici da yawa yake mtsss.... ALLAH ya wandam! Naka ya lalace.
Aunty Farida ta faɗa gami da jan guntun tsaki tsabar takaicin Bilal Shattima da take ji yasa tana gama magana bar wajen ta nufi bakin theater room ta tsaya don ji take kamar ta kifa mishi mugun mari.
Sosai Hajja ta kaɗu da jin irin maganganu da iyayen Jeeddah da 'yan uwanta suke faɗa akan ɗanta, yayin da Aunty Bahijja ta hasale jira take su sauke nasu ta ɗora nata, Hajiya Bintu kuwa farin ciki ne ya cika mata zuciya ji take kamar ta daka tsalle ta taka rawa. Hajja tai ƙoƙarin haɗiye duk wani abu da take ji cikin muryar lalama ta ce "Haba bayin ALLAH mi ya yi zafi haka da za ku dinga tozarta min yaro cikin bainar jama'a?" Yadda ku ke taƙama kuna da ikon akan Jeeddah shi ma yana da ikon akanta asalima ya fi ku iko da ita don kuwa shi matarsa ce, wannan hali da ku ke nuna masa zai iya jawo zubewar mutuncinku a idanuwansa.
A fusace Mama tayo kan Hajja tamkar za ta rufe ta da duka tana faɗin.
   "Eh! Ba shakka Hajja ai dole ki faɗi haka saboda ba 'yarki bace aka wofitar tana gaɓar mutuwa ba. Da yasan bai da kuɗi akwai uban da yai masa dole ai sai bar mana takarda magani amma ba ya karɓe ya tafi tsawon lokaci bai dawo ba, ko so yake likita ya dauwama yana jiransa ko kuma nufinsa sai ta mutu sannan ya dawo?"
   Zuwa lokaci hankula mutane da dama ya dawo kansu don sai kallonsu ake yi, yayin da Bilal Shattima ya cika ya yi tambatsa! Sai huci yake tun sanda ya sadda kanshi ƙasa bai sake ɗagowa ba.
Aunty Bahijja ta hayyaƙo tana faɗin "Gaskiya an zo gaɓar da ba mu ci-gaba da jure iri-iri waɗannan wulaƙanci ba. Wanda aka yi muna a baya muka jure ya isa haka sai wulaƙanta mu ake yi ana ci mana zarafi akan wata banza sai kace wata 'yar gwal....
Kafin Aunty Bahijja ta dasa aya Mommy Turai ta falla mata kafiri mari. Sai da ji da ganinta suka kaura gareta na ɗan lokaci kafin ta ɗago dafe da kunce fuskarta shimfiɗe da mamaki, tana kallon Mommy Turai wacce ta ke jira ta sake furta wata mummunan kalma akan Jeeddah ta ƙara ɗauke ta da wani mari "Ki ka mare ni?"
Aunty Bahijja ta furta da mugun mamaki.
   Sai da mommy Turai ta gagalla mata baƙar harara kafin ta ce "Ki godewa ALLAH da marin ya tsaya kanki bai faɗa kan uwarki ba wacce bata koya miki tarbiyya sarrafa harshe ba.
Da sauri Bilal Shattima ya ciro kanshi ya kalle Mommy Turai da fusatattun idanuwanshi, tsabar harzuƙa da ya yi jikinsa har rawa yake yi kamar wanda yaci tauri..
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

028...

Cikin kakkausar murya Bilal Shattima ya ce "Karki fara mommy billahill-azim kada ki sake hannunki ya sauka a fuskar mahaifiyata. Zan iya jure kowanne irin wulaƙanci daga gare ku amma ba zan lamunci wani daga cikinku ya ɗaga hannu ya dake mahaifiyata ina kallo ba.
   "Yawwa ɗan albarka gaya musu dai idan kuma su ka yi wasa, ka tsitsika igiyoyin aure 'yarsu ba abinda za a yi.
Cewar Hajiya Bintu tana murmushin gefen baki da za a tona zuciyata da an ga zallar farin ciki da take ciki ita fa bata ƙi ta kwaɓe musu gaba ɗaya  burinta a mutu har liman.
Mamaki ne ya kama Mommy da Mama sai kallon fuskar Bilal Shattima suke yi, cikin kaɗuwa mommy Turai ta tambaye shi "Bilal ashe rashin ɗa'ar naka har ya kai har haka? Kafin ya bata amsar tambayarta Ya Kabeer ya iso wajensa a hasale yasa dukkan hannuwanshi biyu ya daki ƙirjin Bilal dasu tare da ture shi ya yi tangal-tangal zai faɗi Abbas dake tsaye a bayanshi ya taro shi yayin da Ya Kabeer ya nuna shi da yatsa yana faɗin "Wannan shi ne kuskure mafi muni da za ka aikata a rayuwarka, bari na tambaye ka Bilal ka kuwa san wacece mommy Turai ka san irin matsayin da take takawa a wajen Jeeddah da har za ka buɗe baki ka faɗa mata maganar rashin ɗa'a, lallai Bilal bakada mutunci ko kaɗan?"
   "Ita ba mahaifiyata ta faɗa ma maganar banza ba ko kuwa uwa ta fi uwa ne?"
Bilal Shattima ya faɗa cikin ɗaga murya.
Gani al'amari yana so ya yi ƙamari yasa babu shiri Hajja ta jawo hannun Bilal cikin kwantar da murya take faɗin
  "Ka ga Bilal kada ka biye musu ku zama abu ɗaya dama abu kaɗan suke jira su shiga rigar mutuncinmu, su yaga ta saboda haka kar na sake jin bakinka ta lafiyar matarka muke yi ba wannan saida halin ba.
"Amma Hajja sai na zuba musu ido suna cin mana mutunci?"
Karaf mommy Turai ta karɓe zance ta hanyar faɗin "matsiyaci irinka mai matatciyar zuciya har wani mutunci ne dashi ai tun da ka yi sake zuciyarka ta mutu ka zo ka tare gindin mace ba ka siɗi ba ka saɗa, wallahi ka dinga gani cin mutunci da wulaƙanci iri-iri kenan.
Wata nurse ce ta taso ta nufo wajensu da nufi taka musu birki taga abin nasu ba mai ƙarewa bane. Cikin faɗa gami da tsawa ta ce "Haba! bayin ALLAH nan fa asibiti ce ba kasuwa ba ko kuma gidan biki tun ɗazu na zuba muku ido ne don naga iya gudun ruwanku ashe al'amari naku ba mai ƙarewa bane. To tun da lamarin naku babu tunani a cikinsa, maza ku tattara ku yi waje ba ma so hayaniya anan haba dallah duk kun bi kun cikawa mutane kunne.
Ta ƙarashe magana tare da nuna musu ƙofar fita da ɗan yatsanta.
Mommy Turai ta kalli nurse ɗin a lalace tana faɗin.
"Idan ma kora za ki yi ga waɗanda ya dace nan ki ingiza ƙeyarsu gaba domin banga amfani zuwansu da kuma tsayuwar da suke yi mana anan ba.
"Ki yi shiru kawai mommy ki ja bakinki ki tsuke mu jira har a fito da Jeeddah ni nasan irin mataki da zan ɗauka.
Ya Kabeer ya faɗa cikin muryar hasala.
Sai da mommy Turai ta kalle Bilal ta sakar mishi baƙar harara gami da yin ƙwafa kana ta juya a fusace ta nufi inda Aunty Farida take tsaye.
Mama ta dubi Hajja ta ce
"Ba ma buƙatarku anan wuri saboda haka ku ɓace mana da gani aiki banza kawai!
Daga haka ita ma Mama ta juyo ta bi sahun mommy Turai, aka bar Bilal Shattima da tawagarsa tsaye sai lokaci Abbas ya sami damar tofa albarkacin bakinsa ta hanyar faɗin "Hajja ku yi haƙuri ku zo mu tafi duk irin wulaƙanci da aka yi muku Shattima ne ya janyo muku ba irin ankarar dashi da ban yi ba akan Jeeddah nan amma yaƙi ji, domin nasan duk dare daɗewa sai irin haka ta faru.
Hajiya Bintu ce tayi sauri karɓe zance tana cewa
  "Atoh! Ba ga irinta nan ba da ya ɗauki shawararka Abbas da yanzu akwai ubanda ya isa ya zagi uwarsa, bai kwaɓar masa da haƙora ba, dama duk wanda ya hau motar kwaɗayi ba inda za ta sauke shi sai a tashar wulaƙanci kaɗan ya fara gani. Na rantse da ALLAH da yau ni ce na tsuguna na haife ka Bilal da sai ka saki Jeeddah ba saki ɗaya ba uku kaff! Za ka rubuta mata...
  "Kin ga Hajiya Bintu banaso zugi da tadda zaune tsaye mi ya kawo zance saki yaro yana so matarsa ita ma tana sonshi sannan kuma da kike faɗin saboda kwaɗayi Bilal ya auri Jeeddah, sai kin faɗa min munafuki da ya gaya miki haka?"
Hajja ta faɗa ranta a matuƙar ɓace.
"Ai abin a bayyane yake duk mai hankali ba sai an gayamasa ba da kansa zai iya gano wa.
"To naji duk ma ta yaya kike kallo wannan al'amari ba damuwa ta bace abu guda nake buƙata daga gareki muddin ba za ki faɗi alkhairi ba ki ja bakinki ki yi shiru. Ban gayyato ki zuwa wajenan don ki tsokano fitina ba.
   "To ai shikenan duk tsutsu da ya kira ruwa shi ruwa kan doka.
Cewar Hajiya Bintu tana wani taɓe baki, ta koma gefe ta rakuɓe ranta fari tass! Kamar auduga.
  Cikin ɓaci rai Bilal ya kalle Hajja ya ce "banga amfani tsayuwar da muke yi anan wuri ba Hajja gara ku zo mu tafi kawai, duk tsiyar su ba su isa su canzawa ɗa da Jeeddah za ta haifa uba ba. Ni matsiyaci nan  nine dai ubansa.
   "Ba za a yi haka ba Bilal kada ka biyewa fushin zuciya ko kuma ka biye musu saboda Jeeddah da ɗan cikinta mu ka zo don haka za mu ci-gaba da jira har sai an fito da ita.
  "Shikenan Hajja fatana ALLAH ya fito da Jeeddah lafiya wallahi sai na nunawa marasa mutunci iyaye nan nata nima ɗan zamani ne.
*After thirty minutes*
_Bayan mintuna talatin_
Wata nurse ta fito daga ɗakin tiyata tai yi wa su Mama albishir an kammala tiyata an fito da Bouncing Baby boy, a lokaci ɗaya suka yi hamdalla, bayan wasu 'yan mintuna aka fito da Jeeddah daga ɗakin tiyata nurse biyu ne suka turo ta akan gadon ɗaukar marasa lafiya, tana lalluɓe cikin farin mayafi kamar matatciya aka shigar da ita ɗaki na musamman Ya Kabeer aka kira ya kama aka kwatar da ita akan gado. Sai da likita ya kashe musu gargadi kada su cikata da surutu, hakan yasa Aunty Farida ce kaɗai ta zauna a ɗakin yayin da Mama da Mommy Turai suka koma bakin theater room su na jira a fito da Baby, Bayan an kammala shirya Baby nurse ta fito musu dashi yana sanye cikin white Baby bodysuit an naɗe da white shawl yaro ƙato gaske dashi kusan weight ɗin shi 5.9kg Mommy Turai ta karɓe shi daga hannu nurse ta leƙa fuskarshi tana faɗin "Kai Ma-sha-Allah! Fatee leƙo ki ga wannan ɗan lukuti dole yasa a yanka 'yarta, ga shi nan tubarakallah Ma-sha-Allahu!
   Washe baki Mama tayi tare da kallon Baby tana faɗin "ɗan nema ɓukeke wofi kawo min shi nai masa rankwashi ya wahalar mu da yarinya ba kaɗan ba.
Ya Kabeer yasa dariya tare da sauri karɓe shi daga hannu mommy Turai yana cewa "A'ah Mama kar mu fara haka dake daga zuwan sabon maigida sai a tarɓe shi da rankwashi.
Su duka suka sa dariya hango su ɗauke da Baby da su Bilal suka yi yasa suka nufo wajensu. Tun kafin su ƙaraso su Mama suka haɗe fuska yayin da Bilal da Hajja sai washe baki suke yi.
   "Al-hamdulillah! Ashe an fito da ita me aka samu ne?"
Cewar Hajja tana leƙe fuskar Baby dake hannu Ya Kabeer.
  A daƙile Mama ta amsa da cewa "ɗa namiji.
"Ma-sha-Allah! ALLAH ya bata lafiya ya tashi kafaɗarta ya bata lafiyar shayarwa.
Kusan a tare Hajja ta jero waɗannan addu'o'i.
Nan ma Mama ce ta amsa mata a takaice da
  "Amin;
Ya Kabeer ba shida niyar basu Baby su gani domin tuni ya gama yi mishi addu'a, yana rungume da shine kawai Hajja da ta fahimci manufarsa sai kawai ta ce "Kabeer kawo shi nima nai masa addu'a.
Ba a so ran Ya Kabeer ya ba ya miƙa mata shi ta karɓe shi tana ƙara washe baki baya tayi masa addu'a ta miƙawa Aunty Bahijja ta karɓe shi tana wani yatsine fuska kamar an mata dole sai ta karɓe shi, ko wani kallon kirki bata yi masa ba ta miƙawa Hajiya Bintu da sauri Hajiya Bintu ta ɗauke fuska tamkar bata ganta ba, gani haka yasa Bilal yai sauri tara hannunshi ta ɗora masa shi, lokaci da idanuwanshi suka sauka akan yaro sai yaji wani irin mashahuri daɗi yana bi sassan jikinshi yanzu wannan yaron ɗa shi ne gudan jininshi, sai da ya ɗauki dogon lokaci yana kallon yaro ba ko kyaftawa sai da Abbas ya zungure shi a kafaɗa yana cewa "Shin Shattima ba za ka bani yaro na ganshi bane ka bi ka wani tsure shi da idanuwa?"
Kusan a tare Mama da mommy Turai suka jefawa Bilal wani irin kallo mai cike da zallar takaici, kafin Mommy Turai ta dawo da ganinta kan Mama ta ce "Kin ga Fatee zo mu bar waje nan zuciyata ba za ta iya jure kallo wannan kayan haushin ba.
   "Humm wallahi kuwa Turai kayan haushi ba kaɗan ba.
Bari waje suka yi da tafiyarsu da kamar mintuna biyar Ya Kabeer ya zo ya karɓi yaro daga hannunsu, duk yadda Hajja take dannar Bilal sai da ya kasa haƙuri domin kuwa su na dosar ɗakin da Jeeddah take Mommy Turai tai sauri taka musu birki da cewa "Ya haka malamai ina za ku je haka zuga guda ba kun ga yaronku ba?" to likita ya ce bataso dogon surutu ku tafi sai gobe idan ta farfaɗo kwa dawo ku dubata.
A fusace Bilal ya kalleta da zimmar mayar mata da magana amma sai Hajja ta kwaɓe shi, dole suka baro asibiti ba tare da sun ga Jeeddah ba.
Sai misali ƙarfe 5:04pm Jeeddah ta farfaɗo a lokaci ta fara jin zafi da raɗaɗi gun da aka yanka, ga ƙishi tana ji ba hali shan ruwa domin likita ya ce kar su bata ruwa sai ƙarfe 6:00pm tayi.
Tun lokaci da Bilal Shattima ya baro asibiti tare da su Hajja bai ƙara komawa ba, tun Jeeddah bata dawo hayyacinta ba har ta dawo ta fahimci baya asibiti sai kawai ta bar abin cikin ranta. A washegari ma tun safe take zuba ido ganinshi har rana ta take bai zo ba  kasa haƙuri tayi ta tambaye Aunty Farida domin ita da Mommy Turai suka kwana da ita yanzu ma mommy ta tafi gida shine ya bata damar tambayar Aunty Farida.
Kai tsaye Aunty Farida ta labarta mata abinda ya faru, nan take yana yi Jeeddah ya sauya ta ji wani irin mugun haushin Bilal ya turnuƙe ta, musanman da ta tuna lokaci da ya sayarda machine ɗinsa don kawai a yi wa Aunty Bahijja surgery, wato ita ce kawai bai damu da ta ta rayuwa ba.
Su na cikin tattauna maganar sai ga A'isha Shattima ta zo dole suka yi shiru, amma Jeeddah tana gani Aunty Farida ta fita ta soma yi wa A'isha Shattima ƙorafi A'isha kam sai haƙuri kawai take bata.
Bilal Shattima bai zo asibiti ba sai da yamma liss shima bai so zuwa ba Abbas ne ya matsa mishi, domin tun jiya yake cike da takaici wulaƙanci da aka yi musu. Lokaci da suka shiga ɗakin bakunansu ɗauke da sallama Aunty Farida ce kaɗai a ɗakin tana riƙe da Baby sai Jeeddah da ke zaune da mug ɗin liptom a hannunta tana sipping a hankali. Kallo ɗaya nai musu na ɗauke fuska yayin da suka gaida Aunty Farida ta amsa musu ba yabo ba fallasa ta miƙawa Abbas Baby ta bar musu ɗakin. Abbas ne ya fara cewa dani "Maman Baby ya lafiyar jiki?"
    "Al-hamdulillah!
na faɗa ba tare da na ko kalle gefen da suke ba.
  Bilal ya matso kusa dani har yana haɗawa da dafa ƙafaɗata yana faɗin "Love ya jikinki?"
Sai da na fara ture hannunshi daga kafaɗata kafin na ɗago idanuwana da ke cike da takaicinsa na wani kafe shi dasu, shima haka ya kafe ni da nashi idanuwa tsawon lokaci na kasa kauda ganina akansa wani irin tuƙuƙi nake ji a cikin zuciyata. Da ƙyar nayi ƙoƙari danne zuciyata ta hanyar kauda fuskata ina faɗin "Sai yanzu ka ga damar zuwa dubani ai da kasani kayi zamanka ba sai ka zo ba?"
Bilal ya yi shiru bai amsa mata ba sai faman shasshafa sajen shi yake yi Abbas yai ƙarfi hali furta "Haba Jeeddah daga farfaɗowarki za ki fara neman tada zaune tsaye.
   "Ka ga Abbas ka ja bakinka ka tsuke ba ruwanka wannan lamari ne da shafi tsakani mata da miji ba huruminka bane. Domin kai ba haka kake yi wa taka mata ba.
  Sai da Abbas ya haɗiye miyau bakinsa kafin ya ce "ALLAH ya ba ki haƙuri ni gyara ne aiki na ba ɓatawa ba.
"To nace banaso gyaran naka ka riƙe kayanka..
   "Jeeddah!
Bilal ya kira sunanta a tsawa ce kana ya ɗora da cewa "wai ke miyasa har abada ba a miki dai-dai duk yadda mutum ya kai da nuna ƙoƙarinsa akanki da ke da 'yan gidanku sai kun nuna gazawarsa?"
   "A'ah! Shattima kada ka biye mata ka tuna da irin condition ɗin da take ciki.
"Kowanne irin condition take ciki Abbas sai na zuba mata ido ta gaya ma magana?"
   "In don ta nine karka damu Shattima ranta ne a ɓace karɓe shi ka zauna ku yi sulhu a tsakaninku zan jira ka a waje.
Daga haka ya miƙawa Bilal Baby ya fita, na raka shi da mugun kallo kafin na ja guntun tsaki gami da furta "Baƙi munafuki kawai!
  Kallona kawai Bilal ke yi daga bisani ya jawo kujera ya kawo daff da gadona ya zauna "Love kada ki biyewa zugar maƙiya su ɓarraka mu dama ba so aurena dake suke yi ba. Ina iya ƙoƙarina amma basu gani kullum cikin aibanta ni suke shin arziki na waye?"
  "Dallah dakata malam! Kada ka sake ka ƙara furta mummunan kalma akan iyayena da kana tsinana abin arziki don me za su dinga aibanta ka? A koda yaushe lalura idan ba ta mahaifiyarka bace da 'yar uwarka ba ka nuna damuwarka akai  Riƙo sakaniyar kashi da kake yi min ya kai maƙura ina kwance a gaɓar rai ko mutuwa ka wofitar dani saboda haka Bilal tun kafin mu kai mataki tara yara da yawa ka cuceni ka barni da ɗaukar ɗawainiyarsu gara kowa ya kama gabansa na gaji. Wallahi haƙuri na ya ƙare ALLAH ya haɗa kowa da rabonsa. Don ba zan iya ci-gaba da zama da kai a haka ba...
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

030...

Lokaci da za a tafi gidan amarya jere Jeeddah bata so zuwa ba. Amma Aunty Bahijja ta kira ta dole ta wanke hannunta tare da ɗauko mayafinta ta bi su, Aunty Bahijja tayi haka ne domin ƙara tulawa Jeeddah haushi da takaici ta nuna mata su kaɗai Bilal yake iya hidintawa ai kuwa ta yi nasarar hakan domin har suka baro gidan amarya Jeeddah bata cikin walwala, ga ɗan uban mamakin Bilal da ya lulluɓeta sai dare ta koma gida a gajiye liƙiss! Kasancewar ta kwaso gajiya yasa tana shiga gida wanka shi ne abu na farko da ta fara yi kana ta shiga kitchen ta girka farar spaghetti pasta tana da stew a fridge ta ɗumama a microwave, a gurguje ta haɗa salad ta zubawa kanta a plate anan kitchen ta tsaya ta cika cikinta. Ta dawo parlour ta zauna hannunta riƙe da glass cup mai ɗauke da pineapple juice tana sipping on, har zuwa lokaci mamakin Bilal sai daɗa ƙaruwa yake a zuciyata. Ta ɗauki lokaci mai tsawo a zaune tana tufka da warwara yayin da zuciyarta ta kaso kashi biyu a ɓangare ɗaya tana ji da ya dawo tai masa titse ta ji ina ya sami kuɗi da ya yi wannan uwar hidimar a wani sashe na zuciyarta yake kwaɓar ta da ta zuba mishi ido duk zaman da tayi ta kasa tantance wanne daga ciki za ta ɗauka. Bata ankara ba ta ji sallamar shi ta amsa mishi ba tare da ta bari ya fahimci halin da take ciki ba. Kasancewar shi ma a tsorace yake da ita domin har ya wuce ta ya shiga bedroom da addu'a ɗauke da bakinsa yana gudun tai mishi tambaya dangane da inda ya sami kuɗi domin har ya shigo gida bai tanadi amsar da zai bata ba. Shiyasa yana shigowa yai sauri shigewa bedroom ya yi wanka ya saka kayan baccinsa, kasa komawa parlour ya yi ya nemi gado ya kwanta har da su lulluɓewa da bargo gudun kar ta shigo ta sami damar yi masa magana.
Shiru-shiru ina jira Bilal ya dawo parlour domin na zazzage masa abinda ke cina a zuciya duk naso na rinjaye zuciyar tawa na haɗiye mamakina. Amma fitinaniyyar zuciyata ta kasa aminta da hakan. Gani shiru nashi ya yi yawa yasa na dire cup ɗin hannuna akan centre table, koda na shiga ɗaki ya kashe wuta saboda haka na lalluɓo switch na kunna bulb haske ya gauraye ko'ina na cikin ɗakin. Jin motsin shigowar ta yasa shi sauri lumshe idanuwanshi tamkar mai bacci al'hali ido shi biyu na ja numfashi na sauke kana na zauna kusa da cikinsa "Love nasan ba ka yi bacci ba ka tashi za mu yi magana.
Na yi tunani zai ci-gaba da pretending ne sai naga ya tashi zaune yana ya motsa fuska gami da wuƙi-wuƙi da idanu ya wani dafe forehead ɗinshi alamar da ke nuni headache ke damunshi, hakan bai sa na fasa antaya mishi tambaya dake raina ba "Love naga hidimar da ka yi wa A'isha ka burge ni matuƙa gayya ALLAH yasaka ma da alkhairi kana fa ƙoƙari akan 'yan uwanka.
Na ƙarashe magana ta da gatse ina mai ƙara aika mishi kallo mai cike da gundarin tuhuma.
  Tun zamana kusa dashi sai lokaci ya ya ɗago idanuwanshi ya kalle ni da guntun murmushinsa da bai wuce fatar bakinsa ba,  ya ce "Amin!
Duk da na fahimci ba son maganar yake yi da ni ba hakan kuma ba shi zai sa na tsuke bakina ba, sai ma ƙara zakuɗa ɗuwawuna nayi suka zauna daram! Fuskar nan tawa babu annuri ko kaɗan na ce "Love ina ka sami maƙudan kuɗaɗen da ka yi wa wannan uwar hidima dasu?"
Shiru ya biyo bayan tambayata domin shi bai tanka ba ni kuma ban ƙara furta uffan ba. Kawai dai na tsare shi da idanuwa ina jiran amsar da zai bani. Wani dogon numfashi ya ja tare da saukewa kafin ya yi ƙasa da murya ya ce "Gun Abbas na karɓo bashi....
  "Bashi fa kace Bilal to ka biya shi da me? Love kada son zuciya yasa ka jefa kanka a rikici kai da ba kada takamaiman sana'a shine za ka karɓi bashi maƙudan kuɗi irin wannan.
   Kafin ya yi magana sai da ya fara riƙo hannuwana ya matse cikin nashi ya ƙara lanƙwasa murya kamar wani munafuki ko mayaudari na ma kasa tantance farat ɗaya a mizanin da zan ɗora shi, can na tsikayi muryarshi yana faɗin "yarjejeniya mu ka yi sai na sami aiki zan dinga biyan shi da kaɗan-kaɗan har ALLAH yasa na biya duka. Kin ga ba zai yu ba saboda gado da kujeru a kuma fasa auren A'isha ga kuma furuncin da iyayen Al'ameen suka yi kuma ni ba ni da mafita da ta wuce na karɓi bashi daga wurin Abbas.
"Uhmm.... ALLAH ya ba ka ikon samun aiki ya kuma ba ka ikon biyan wannan uban bashi da hannunka, amma inaso ka sani Bilal ko ɓatatciyar dabara ma dabara ce ALLAH ya tashe mu Lafiya.
  Ban jira jin abinda zai sake faɗa ba na miƙe tare da shigewa bathroom, ya bita da kallo yayin da zuciyarsa ke ci-gaba da luguden aradu tabbas ya tsallake yau bai kuma san me gobe za ta haifar ba domin bai faɗa mata takamaimiyar gaskiya ba, ƙarya ce ya lafta mata domin kare kanshi, fargabar sa ɗaya idan ta gano gaskiya akwai ƙura ba kaɗan ba.
Ta fito daga bathroom ta sauya kayan jikinta zuwa na bacci ta raba kusa dashi ta kwanta, kasancewar akwai gajiya a jikinta shiyasa nan take tai bacci.
Washegari aka ɗaura auren A'isha da angonta Al-ameen sai fatan ALLAH ya basu zaman lafiya. A kwana a tashi asarar mai rai cikin hukunci Ubangiji Jeeddah ta kammala first semester examination, su ka sami hutun three weeks shiyasa yau tun da sassafe ta tashi da kwalemar ɗaki ta jawo wannan ta fiddo wannan yawan kwaranniyar da take yi ya hanawa gogan naku baccinsa na asara, ya tashi zaune ransa a ɓace a tunani sa ta ƙirƙiro aiki nan ne domin ta hana shi bacci, shiyasa ya sauko daga kan gado a fusace ya shiga bathroom ya yi wanka, ko breakfast bai yi ba ya bar mata gida yayin da ta bishi da murmushin mugunta.
Kai tsaye gidan Hajja ya nufa bayan sun gaisa ta kawo masa koko da ƙosai ya cika cikinsa, suna cikin fira sai ga ƙaramar 'yar Aunty Bahijja wacce tun bayan auren A'isha Aunty Bahijja ta tadawo da ita hannun Hajja domin ta dinga yi mata 'yan aikace-aikace, hannunta ɗauke da 'yar ƙaramar tukunyar laka mai murfi tana faɗin "Hajja duba ki gani yanzu nan da na zubar da ruwan wanke-wanke a bayan ɗakin Hajiya Bintu sai naga hayaƙi yana fita daga cikin ƙasa kuma fa ba wuta aka kunna ba shi ne na haƙo gun ashe wannan 'yar tukunyar ce take fidda hayaƙi, na shiga ɗakinta nayi ta sallama na nuna mata watakila ko nata ne amma ban ji ta amsa min ba shi ne na kawo miki ki ajiye.
   Daga Hajja har Bilal mutuwar zaune suka yi domin har zuwa lokaci tukunyar tana fidda baƙin hayaƙi ga mufeeda riƙe da ita hankalinta kwance {kuruci dangin hauka}
Da kyar Hajja tai ƙarfi hali furta "mi nake shirin gani haka mufeeda mi ya kai ki ɗauko mana wannan masifar da sanyi safiya?
  "Hajja ba masifa bace kalli ki gani tukunyar hayaƙi ce....
  "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Bilal ya faɗa a mugun tsorace ya taso yana sanɗa jikinshi sai kakkarwa yake yi dama gogan naku akwai shi da mugun tsoro kamar farar kura, ya leƙa murfi tukunyar gun da hayaƙi yake fita ya zaro idanuwa kana ya ja da baya yana faɗin "kam bala'in! Hajja wallahi hayaƙi nan daga 'yar ƙaramar tukunyar nan yake fitowa abin mamaki menene ke fidda wannan baƙin hayaƙi?"
Sai lokaci Hajja ta sami damar tasowa gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi bakinta ɗauke da kalmar shahada "La'illaha inlallahu Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam! Kai jama'a yau mi nake shiri gani haka?" Mufeeda wannan ai tukunyar tsafi ce wallahi wani aka yi wa asiri kika haƙo Mufeeda.
Bilal Shattima yana ji Hajja ta ambaci kalmar asiri ya daka wani uban tsalle sai bakin ƙofar fita, yana faɗin "Amma Mufeeda ke ɗin ba ƙaramar 'yar banza yarinya bace muna zaune qalau za ki ɗauko mana masifa, don ubanki yau ɗinan sai kin koma gidan ubanki ba za ki kashe mana uwa a banza ba.
  "Kai ya isa haka banaso shashasha matsoraci wofi Mufeeda da kake zagi ta ma fika jarumta maloho kawai.
A bakin ƙofa Bilal Shattima ya ja tunga yana gunguni ƙasa-ƙasa "Haba! Hajja haka kawai saboda ganganci ina kallon maciji da rana ƙiri-ƙiri kuma na barshi ya sare ni, wannan kasadar ba da ni ba wallahi.
  "To na ji zo ka karɓi tukunyar hannun Mufeeda ka buɗe mu ga menene a ciki.
  Saboda tsanani kaɗuwa Bilal bai san sanda ya zaro idanuwa tamkar kwayar idonsa za ta faɗo ƙasa "Na buɗe fa kika ce Hajja?"
"En mana ko ba za ka iya bane?
"Gaskiya ba zan iya ba amma bara na fita ƙofar gida ya na nemo maza, su shigo su taimaka mana..
"Kai arrr! Matsoraci wofi kai ba namiji bane?
Kafin yai magana Hajja ta furta "Bismillah! Gami da karɓar tukunyar daga hannun Mufeeda ta ajiye a tsakar ɗaki kana ta karanta Ayatul-kursiyyu ta tofawa tukunyar, murfi ya yi tsalle ya faɗo ƙasa yayin da wani siriri baƙi hayaƙi ya fito ya bi ta window ya fita, jikinta Hajja ya ɗauki rawa ita kanta a yanzu a tsorata gogan naku tuni ya kai ƙofar shiga bedroom ɗin Hajja ya laɓe ciki labulle a hankali Hajja ta leƙa cikin tukunyar ta hango layoyi birjik a ciki da wani busasshe kadangare an bi jikinshi an sossoke da dogaye allurai, ga kuma wata ƙaramar laya cikin bakinshi. Ta maza Hajja tayi ta miƙa hannunta ta shiga fiddo da tarkace yayin da bakinta bai gushe da karanto Ayatul-kursiyyu ba. Ɗaya daga cikin layoyin ta ɗauka ta warware ta taga wata farar takarda mai ɗauke da zane uwa da ɗa a tsakiyar su an yi musu jan rubutu da rubutun ajami ta juya ta kira Bilal "zo ka gani Bilal da ajami aka yi rubutu nan ko za ka iya karantawa.
*** ** ****
Sosai Jeeddah ta gyara gidanta ya yi tsaf ko ina ya ɗauki ƙamshi, kana ta dawo kan closet ɗinta ta shiga fiddo kayanta tana sake arranging ɗinsu. Haka kawai na ji ina sha'awar ɗauko jewelry box ɗina na goge 'yar ƙura da tayi ina kammala gogewa har nayi niyar na maidata sai kuma na fasa na nemi gefen gado na zauna tun kafin na buɗe ta naji gabana yai mugun faɗuwa sai da na dafe saitin zuciyata, nan take jikina ya bani akwai matsala cikin sauri na ƙarasa buɗewa saura kiriss! Numfashina ya fita daga gagar jikina a dalili box ɗin gold necklace ɗina da ban gani ba. Jikina yana rawa na tashi tsaye na zazzage duka sarƙoƙina akan gado, abin mamaki babu box ɗin amma kuma ga extra earring da zobe da nake da su a ciki su ma na gold ne lokaci da Mama ta je Umrah ta siya mana su a matsayin tsaraba sai dai su ƙirar Sa'udiyya ne saɓani necklace ɗin da take ƙirar Dubai duka necklace ɗin bata wuce nine months da siya ba. Baba ne ya ba mu kyautar dubu ɗari biyar-biyar ni da su Khairat da Aunty Farida dama yana mana haka duk ƙarshe shekara yake raba mana kuɗi kafin mu yi aure sai Mama ta siya mana kitchen utensils. A wannan karo da ya ba mu sai Mama ta ce nawa Ya Kabeer ya karɓi ƙaramar necklace ɗina ya saida ya haɗa da nawa kuɗi ya siya min babba na ajiye a matsayin kaddara domin a cewar tasan ƙarshenta Bilal zan ba wa kuɗin ya cinye, a lokaci har gida Ya Kabeer ya zo ya ɗauke ni muka tafi shagon sayar da gwala-gwalai, na zaɓi wacce nake so ƙudinta ya kama 1.1 tsohuwa ta aka saye ta akan dubu ɗari huɗu da naga ƙudina bai kai kuɗin necklace ɗin ba har nace a kawo min wata dai-dai kudina Ya Kabeer ya ce na ɗauka kawai zai cika min raguwar dubu ɗari biyu. Sau ɗaya na taɓa sakata domin ni mace ce da bata cika saka necklace ba. Abu kamar wasa aka ce ƙaramar magana ta zama babban domin kuwa kaura wambai na dubu banga necklace ɗin ba. Ta ci tudu taci rafi kuma hatta da receipt duka an ɗauke domin ita ma a cikin jewelry box ɗin na ajiye kuma ban ganta ba. Yayin da na dawo tamkar mahaukaciya sabon kamu ɗaki da na ɓata lokaci ina gyarawa, gaba ɗaya na hargitsa shi a tunanina ko na sauya mata mazauni ne da na fahimci da gaske an sace min sarƙana sai kawai na ɗora hannu aka na kwatsama ihu, nayi faɗuwar 'yar bori ina gunji kuka...
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*      _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

029...

Da mugun mamaki yake kallona don ko kaɗan bai kawowa ransa cewa zan iya furta kalmar rabuwa a tsakaninmu ba. Sai da ya furzar da iska mai zafi daga bakinsa kafin ya sami damar furta "Mu rabo fa kika ce Love shin bakinki ne yake faɗin wannan kalma ko kuwa a mafalki ne nake ji saukar ta a dodon kunne na?"
   Kallon sama da ƙasa na fara bin sa dashi kafin nace "Ba mafalki ka ke yi ba Bilal idonka biyu don ga ka nan zaune kusa dani, na faɗa na sake nanatawa gara mu rabo dama rabon Muhammad Aiman ne ya kaini aurenka to tun da an haife shi gara kowanne mu ya kama gabansa.
  "Ɗan dakata mana Jeeddah! Waye da wannan sunan?"
  Yadda ya tambaya kasan cike yake da mamaki, a lalace ta kalleshi tare da furta "waye kuwa ban da ɗa da na haifa, ai sunan da ni mahaifinsa nasaka mishi kenan.
Da sauri ya sauke idanuwanshi akanta tsawon mintuna yana kallonta don ba ƙaramin mamaki ta haifar masa dashi ba kafin ya ce "Ɗanki kika ce fa Jeeddah wato ɗanki ne ke kaɗai? To bari ki ji ba wanda ya isa ya nuna min fin ƙarfi akan ɗana. Kum duk tsiyarki da rashin mutunci da kike taƙama dashi ba ki isa ki samar da ɗa ke kaɗai ba. Asalima na fi ki iko akanshi saboda haka ƙaryarki tasha ƙarya Jeeddah ba ki isa ki sawa yarona suna al-ahali ina nan da raina da lafiya ta. Ke bari ki ji tun ranar da aka haifeshi nai masa huɗuba da suna mahaifina, saboda haka yarona sunanshi Ibrahim-Khaleel. Sai ki jira idan ALLAH ya nufe ki da sake haifar wani sai ki sa ma sunan da kike muradi amma wannan kam mahaifina nai takwara.
  "Uhmm....halan sunan mahaifin naka yafi suna da na saka mishi daraja ne?"
  "Wannan wacce irin tambaya ce Jeeddah?"
Ya faɗa cikin ɓaci rai.
"Irin wanda ta dace da tambayarka ce. kai bari ka ji Bilal idan duk duniya za ta taro akaina ba wanda ya isa ya sauyawa yaronan suna daga Muhammad Aiman, don haka gara tun wuri ka haƙura da wannan buri naka domin ba mai yiwuwa bane.
  Shiru ya yi ya kasa magana sai faman kallonta yake yi, yayin da wani sashe na zuciyar shi ke ingiza shi ya furta mata abinda ta neman tun farko ya lumshe idanuwanshi tare da buɗe su ya ja zazzafar iska ya fesar kana ya ce "wannan ai maganar banza ce kike faɗin Jeeddah, kar fa ki manta matsayina na uban yaronan ko a addinan ce na fi ki ƙarfin iko akansa.
Cikin ɓacin rai na kalle shi na watsar tare da faɗin "Ƙarfin ikonka na banza da wofi tun yaro nan yana ciki faɗi min wata tsiya da ka taɓa tsinana masa, hatta da ranar da zai zo duniya wofitar dashi ka yi, sannan kuma ni kaɗai nasan irin baƙar wahala da nasha yayin kayan cikinsa da haihuwar sa sai da aka ɓarka ni sannan ya zo duniya shine don ba kada ta ido za ka zo kana jayayya dani.
   Kasa furta uffan ya yi a hankali ya kwantar da Babyn kusa da ita kana ya miƙe tsaye ya kalle ta da idanuwanshi da suka fara canza launi saboda ɓacin rai yana faɗin "Na fahimci so kike sai lamari nan ya kai mu da yadda ba a so.
"Ya kai mu mana ai ba tsoronka nake ji ba ko kuma tsoron irin hukunci da za a zantar ba.
Tai sauri katseshi tana wani zare ido.
"To shikenan tun haka kika zaɓa mu zuba ni da ke ɗan halak ka fasa.
Daga haka ya fice abinsa yayin da Jeeddah ta bi shi da mugun kallo kana ta ja tsaki ta ɗauki ɗanta ta rungume, a matuƙar fusace ya buɗe mota ya shiga Abbas ya kalle shi tare da yi wa mota key sai da suka ɗauki hanya yake tambayarshi "Ya naga fuskarka a turɓune halan ba ku sulwanta kanku bane?"
  "Bari kawai Abbas jikina yana bani aurena da Jeeddah ya zo ƙarshe domin ko kusa ba zan ɗauki reni hankali da ta zo min dashi ba.
  "Subhanalillah....! Haba Shattima kada ka bari sheɗan ya yi tasiri a zuciyarka, ka aikata abinda za ka dawo daga baya kana danasani duk girman laifin da Jeeddah da iyayenta suka yi maka bai kamata ka kunno da zance saki a tsakaninku ba.
Sai da Bilal ya ja dogon numfashi kana ya sauke gami da faɗin.
   "Dangane da zance suna da za a raɗawa yaro nan ne takeso ta kawo min reni wayau, already na yi wa yaro huɗuba da sunan mahaifina, shi ne ita kuma a dole Muhammad Aiman take so na nuna mata hakan ba mai yiwa bane, ba ka ga yadda ta hayyaƙo min ba. Yadda ba za ta bi abinda nake so ba nima ba zan bi ra'ayinta ba.
   "Wallahi kana da matsala Shattima yanzu akan suna da za a raɗawa yaro sai ya zama abin fitina a tsakaninku ku kenan kullum cikin samu rashin jituwa akan abin da bai taka kara ya ƙarya ba. Duk duniya babu wani suna da ya kai Muhammad daraja da ƙima saboda haka ka haƙura ka bar sunan yaro nan Muhammad fatanmu ALLAH ya raya shi cikin aminci idan da rai da lafiya nan da wata shekara za ka ga ta sake haihuwa sai saka mishi Ibrahim-Khaleel ɗin. Infact duk ɗa fari Muhammadu ne saboda haka a wannan karon Jeeddah tafi ka gaskiya.
Yayin da Abbas ya ƙarashe magana yana dariya.
Murmushin gefen baki Bilal ya yi kafin ya ce "Wallahi Abbas inaso matata so matuƙa ALLAH ma shedata ne akan hakan, amma na rasa dalilai da ke sa muke yawan faɗa.
  "Dalilai ba su wuce rashin dogara da kai ba. Da za ka nemi sana'a komai ƙanƙantar a ganina shikenan ka magance wannan matsalar.
  "Zan yi nazari akai naga wacce irin sana'a ce ta dace ni.
"Kullum haka kake faɗa Shattima kwana biyu ka wofitar da zance.
  "Na rasa gane me ke hawa kaina Abbas duk lokaci da nai yunkuri neman sana'ar hannu sai naji tamkar an ɗaɗɗaure min sassan jikina da igiya mai mugun ƙarfi, kasala da mutuwar jiki su lulluɓe ni. Sai na ji na kasa kawai ka tayani da addu'a domin ina ji a jikina kamar da akwai abinda ke damuna.
   "Koma menene shi ALLAH yaye maka shi, yanzu dai mu sake ɗauko zance da muka fara ka bar yaro nan da suna da mahaifiyarshi ta zaɓi mishi.
  Shiru Bilal ya yi yana nazari maganganu Abbas bi da bi kafin ya ce "Ni in dai ta nice banida matsala Hajja da Aunty Bahijja nake tunani domin shawarar su ce na bi nai wa yaro huɗuba da Ibrahim yanzu kuma idan suka ji kwatsam an sauya mishi suna kana gani hakan ba zai sake kawo wata matsala ba?" Don ni wallahi na gaji da ƙanana matsalolin nan.
"Karka wani damu duk abinda Hajja da Aunty Bahijja za su yi na ɗan lokaci ne saɓani matarka da kuke rayuwa a wuri ɗaya saboda haka wannan matsalar mun magance ta sai kuma ta gaba.
**** *** *****
Kwana Jeeddah biyar aka yi discharge ɗinta al-hamdulillah jikinta yana da kyau domin ɗinki har ya soma haɗewa, duk wani abu na al'ada da miji yake kawowa a haihuwar fari da kuma yayin zaman jego ba wanda Bilal Shattima ya kawo gidansu Jeeddah. Hatta da kayan fitar suna Aunty Farida ce tai mata, sai ana gobe suna da dare sannan Bilal ya aiko ragon suna gidansu Jeeddah guda ɗaya shima wani ɗan tamurrarre dashi. Da Mama ta fara faɗa Baba ya taka mata birki ya kira Ya Kabeer a waya ya umarni ya nemo sa guda da rago ɗaya, tun a cikin dare nan Ya Kabeer ya cika umarnin sa ya siyo washegari da aka yanka ba wanda yasan cewa ba Bilal Shattima bane ya kawo su.
  A haka Jeeddah ta ci-gaba da wanka jego ita da Khairat duk lokaci da Bilal zai zo gani Jeeddah da Aiman sai ya fita da ɓacin ran Mama don da kyar take amsa gaisuwar shi amsarwa ma a wulaƙance. Khairat tana yin arba'in da kwana shidda ta koma ɗakinta, yayin da Mama ta ce Jeeddah sai tayi wata huɗu da tayi wata uku da Baba yaga zaman yaƙi ƙarewa ya ce ta haɗa in-nata-in-nata ta koma ɗakin mijinta, ko kusa Jeeddah bataso haka ba domin ta sha faɗawa Bilal muddin bai nemi aiki ba ko sana'a ba za ta koma gidansa ba. Sai gashi kwatsam Baba ya buɗe mata wuta ala tilass! Ta koma suka sake shimfiɗa sabuwar rayuwa sai ya zamana saɓani da suke samu har yafi zamansu na farko kullum rashin jituwa  daɗa ƙaruwa yake yi a tsakaninsu.
A haka rayuwa ta miƙa yau fari gobe baƙi Aiman yana cika wata biyar Jeeddah ta koma bakin aikinta, domin salary nan ba ƙaramin taimaka rayuwar aureta yake ba shiyasa bata wasa dashi. Ana ciki wannan yanayi ta bijiro da buƙatar komawa makaranta tayi degree Bilal bai hanata ba domin ba ko Kwabo sa a cikin Aiman yana cika wata tara ta sami admission a Usmanu danfodiyo University duk lokaci da za ta je lecture wurin Mama take kai Aiman, a haka ta ci-gaba da karatunta ta ɓangaren Bilal Shattima ba abinda ya canza zani kullum jiya iyau ba wani canji ko ci-gaba. A duk lokaci da Jeeddah ta tashi masifarta sai su share mako fiyye da biyu suna gaba sai sun gaji sannan su sulwanta kansu. Aiman yana da shekara ɗaya da wata Uku ta yaye shi gaba ɗaya ya koma hannun Mama da zama domin Mama tana masifar ji da Aiman ubansa ne har yau ta kasa jin ƙaunarsa a zuciyarta.
Ana cikin wannan rungutsumi aka sake saka date ɗin auren A'isha Shattima, domin a can baya an yi ta sakawa ana fasawa a dalili basuda kayan ɗaki, a wannan karon 'yan gidan ango su jaddada masu matuƙar suka sake ɗage auren to su nemawa 'yarsu wani miji ɗansu ya fasa ga A'isha tana matuƙar son Al-ameen duk a cikin samarinta shi kaɗai ne yai mata hallaci ya ɓata shekaru masu yawa yana zaman jiranta domin tun tana makarantar sakandare suke tare. Babbar matsalar da aka samu 'yan dabbobi da akewa Hajja kiwo a ƙauye iftala'i ya faɗa musu duk sun mutu.
Watan da aka saka na auren A'isha Shattima ya yi daidai da wata da Jeeddah ta kwashe adashenta dubu ɗari da hamsin ba tare da sani Bilal ba ta kira A'isha har gidanta ta damƙa mata su a hannu, a matsayin ta ta gudunmawa A'isha kuka ta fashe dashi ta rungume Jeeddah tana zuba godiya, da tashi tafiya ta bata wasu daga cikin kitchen utensils ɗinta wanda bata yi amfani dasu ba ta kuma haɗa mata da wani centre carpet ɗinta da ke ɗayan bedroom dama bata yi amfani dashi ba sabo ne dal kawai dai ya yi 'yar ƙura da zarar an wanke shi dal zai dawo. Duk wannan hidimar Jeeddah ta yi wa A'isha Shattima tayi ne a dalili kasantuwarta ƙawarta tun ta yarinta sannan kuma A'isha ɓata taɓa goyon baya duk wulaƙanci da Aunty Bahijja take wa Jeeddah ba, asalima a duk lokaci da Aunty Bahijja take zagin Jeeddah A'isha tare mata take yi shiyasa Jeeddah bata da kamarta.
Lokaci da A'isha Shattima ta je gida da tulin kaya da sunan Jeeddah ce ta bata tsabar mamaki daga Hajja har Aunty Bahijja kasa furta uffan suka yi domin ko kaɗan ba su zaci wannan alkhairi daga Jeeddah ba. Hajja da kanta ta zo har gida ta yi wa Jeeddah godiya, shima Bilal ya sha mamaki da yaga kuɗi da kayan, shiyasa yana shigowa gida ya shiga yi mata godiya.
Har aka saka A'isha Shattima a lalle gado kawai aka siye mata shi ma na katako mai sauƙin kuɗi, irin wanda ake bugawa akan titi, babu kuɗin siye kujeru shima gadon da taimakon kuɗin Jeeddah ta bata ne aka haɗa da gudunmawa da 'yan uwa da abokan arziki suka kawo.
Ana gobe ɗaurin aure da yamma lis 'yan biki sun   cika gidan Hajja babu masaka tsinke, yayin da mutane sai gulma suke yi ba a yi wa amarya jere ba. A dalili bata da kujeru da labulle har yanzu fafutukar nema ake yi.
Kwatsam sai ga Bilal Shattima ya zo tare da motar ɗaukar kaya ɗauke da kujeru masu matuƙar kyau da chinese bed mai ɗan karan kyau da tsada, kasancewar gidan na amarya A'isha ɗaki biyu ne da parlour ɗaya, dama rashi ne yasa aka siya mata gado guda amma tun da yanzu ga wani sai aka haɗa mata duka biyu lokaci da Bilal ya shigo gida ya yi wa Hajja albishir ga gado da kujeru da gadon ya siyowa A'isha sosai farin ciki ya lulluɓeta, ta ma ƙasa tambayarshi ina ya sami kuɗi tun da ya fidda su kunya koma menene bayan biki za ta tambaye shi ta ɓangaren Aunty Bahijja karku so ku ga yadda ta dinga yi wa  mutane habaici kuma duk da Jeeddah take domin a lokaci Jeeddah tana zaune cikin 'yan biki suna gyara tomatos ɗin da za a yi miyar masa {waina} ba ƙaramin kaɗuwa da firgici Jeeddah ta shiga ba lokaci da tai arban da irin kayan da Bilal ya siyawa A'isha.

_shin ina Bilal ya sami kuɗi?_
_shin kodai ya sami aiki ne?"_
_ko kuma ya faɗa wata mummunan hanyar ne_

*Duk waɗannan amsoshi tambayoyin suna cikin shafi na gaba amma kafin sannan ina so naji naku hasashe akafta[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

031...

Cikin sanɗa Bilal ya iso ta bayan Hajja ya leɓe tare da leƙo da kanshi ta kafaɗarta yana kallon takarda da ta warware ya ƙura wa rubutu idanu, sai kawai ya zazzare idanuwanshi cikin kaɗuwa gami da rawar murya yake faɗin "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Hajja wallahi sunanki ne da na Ya Faruk aka rubuta.
  "Subhanalillah! Suna kawai ka gani ko da wani abu?"
"En! To ga wani dogon jawabi nan a ƙasan sunaye.
"Maza karato min shi ai ina gani wannan tukunyar jikina ya bani ni ce aka yi wa, kuma wallahi koma waye ya tarowa kanshi bala'i da masifa.
*_"Daga yau mai kama da rana ta yau Faruk babu kai ba mahaifiyarka Hajja, ka manta da ita, ko gawarta za ka gani shimfiɗe a gabanka kada ka tausaya mata ko ka taimaka mata. Dukiyarka kada ta amfana da ita Faruk ka nisanci mahaifiyarka da 'yan uwanka ka tsane su tsana mai tsanani ta yadda duk hali da ka gansu ciki ba za ka iya taimaka musu ba_*
Tun sanda Bilal Shattima ya fara karantawa Hajja takarda jikinta ke kakkarwa kamar mai jin sanyi haƙoranta har haɗewa suke yi da kyar ta iya furta "innalillahi wa'inna illahim raji'un! Ashe duk abinda Faruk ke mana ba yin kansa bane aikin asiri ne?" Amma kuwa Hajiya Bintu ta cikakkiyar azzaluma, muguwa, mutaƙambira tsakanina da ita ALLAH ya isa ba zan taɓa iya yafe mata wannan zalunci da tayi min ba. Sai ALLAH yai mana hisabi shegiyar mata la'anana wacce babu ALLAH da Manzonsa a zuciyarta. Haba wannan kishi na masifa har ina mutumin da take kishi akansa ya mutu baya duniya amma bata barni ni da iyalina muka sheƙi iskar 'yanci ba. To Wallahi-azim nima a wannan karo ba zan kyaleta ba. Ke Mufeeda shiga ɗaki ɗauko min hijabina da ƙaramar jakkata tana nan akan gado a ƙarƙashin pillow, kema ki sako naki hijab yau ni zama bai ganoni ba.
Bilal ya rurrufe ƙofofi suna fitowa wani mugun kallo Hajja ta aikawa ɓangaren Hajiya Bintu tare da yin ƙwafa su na zuwa bakin titi suka tare adaidaita suka shiga sai lokaci Bilal ya sami damar tambayar Hajja inda suka nufa, kai tsaye ta bashi amsa da "Yabo za mu je na kaima malam Alti mai rahunnai layoyi nan ya ƙarya asiri da ke cikin su idan da hali so nake yai mata ƙaiƙai koma ma masheƙiya, duk wani mugun aikinta ya koma kanta.
  "A'ah! Hajja kada ki yi haka adai ƙarya asiri ita kuma ga ta ga duniya da iznin Ubangiji ƙarshenta ba zai yi kyau ba.
"Yi shiru kawai Bilal duk abinda zan faɗa ba lallai bane ka fahimci irin mugun ta'adi da matar nan tayi min ba. Yanzu dai kira min Bahijja ta fito ƙofar gida mu ɗauke ta don ba zan yi tafiya nan ba tare da ita ba.
Bilal ya fito da wayarshi daga gaban aljihun rigar shi sai lokaci ya lura da bashi da enough charging battery shi 7% ya rage ya kira Bahijja ya faɗa mata saƙo Hajja koda suka iso ƙofar gidanta tana tsaye rungume da hannuwanta a ƙirji mai adaidaita yana parking tana ƙarasowa, Hajja ta kalle Mufeeda ta ce "Mufeeda shiga gida ki jirani har na dawo ke kuma Bahijja shigo mu tafi.
Mufeeda ta fita Bahijja ta shigo mai adaidaita ya ja suka tafi kafin su isa tasha Hajja ta zayyanowa Bahijja abinda ke faruwa, sosai Bahijja ta shiga firgici da tashin hankali.
**** *** ****
Tun Jeeddah tana gunji kuka a hankali har ta dawo da dukkan ƙarfinta bata taɓa sani haka sata take da cin rai ba sai yau, taci kuka har ta godewa ALLAH can kuma ta tuna da abokin kuka ba a ɓoye masa mutuwa saboda haka ta tashi da gudunta ta nufi parlour ta ciro wayarta da ke charging, mutum na farko da ta fara kira shi ne Bilal, sai dai kashhh! Layin shi baya shiga gani bata same shi ba yasa ta kira Mama koda kiranta ya shigo wayar Mama Ya Kabeer ya zo gidan dama kowacce wayewar safiya sai ya zo ya gaida Mama, su taɓa fira sannan ya wuce kasuwa suna fira cikin sa'a kuma akan Jeeddah ne suke magana, dangane da rashin aiki Bilal Mama tana ba Aiman tea yayin da wayarta ke aje akan tv stand Ya Kabeer ya miƙe ya ɗauko wayar sai kawai yasa dariya yana faɗin "Yar halak taƙi ambato Mama Jeeddah ce fa ta kira ki.
Ita ma Mama dariya tasa gami da faɗin "Jeeddah kenan wannan abin ai a jini jikinta yake da matuƙar wahala ka ambaci sunanta ba ka ganta ba kodai ta faɗo ga wuri kwatsam ko kuma ta kira wayarka.
Ya Kabeer yana dariya ya amsa kira nata gami da ɗora wayar a kunne shi kafin ya yi magana ya ji  shasshekar kukanta gaba ɗaya ya karaɗe mishi dodon kunne har bai ya ji abinda take faɗa "Subhanalillah! Jeeddah me ke faruwa kuka me kike yi haka? Bana ji abinda kike faɗa idan da hali ki tsagaita kukan nan ki yi min bayani ta yarda zan fahimci dalilin kuka naki.
Cikin shasshekar na ja dogon numfashi muryarta tana sarƙewa na ce "Ya...Ka..beer...!
Sai Kuma wani sabon kuka ya koma kubce min.
  "Please Jeeddah control yourself ki natsu ki yi min magana wallahi-tallahi kukan nan naki yana mugun ɗaga min hankali fiye da ke da ka rera shi domin ke kinsan dalili da yasa kike yi sa.
Da sauri Mama ta dire Aiman ƙasa ta taso hankali tashe ta tsaya kusa da Ya Kabeer gani haka yasa yasaka wayar a speaker, yayin da Mama take jiyo yadda Jeeddah ke gunji kuka ba kakkautawa hakan ya tabbatar mata da babu lafiya cikin tashin hankali Mama ta ce "Jeeddah kina ji na kuwa?"
  "En! Mama.
"To ki natsu ki faɗa mana takamaiman abinda kike wa kuka kin ji 'yar albarka.
"Mama an sace min sarƙana na gwal na nema sama da ƙasa banganshi ba..
Ta ƙarashe magana da wani irin kuka mai cin rai.
"Innalillahi wa'inna illahim raji'un!
Kusan a tare Mama da Ya Kabeer suka furta Mama kam abin ya dake ta sosai saɓani Ya Kabeer da yake namiji, da baya-baya Mama ta soma tafiya har tai nasarar kai wa ga kujera ta zauna daɓass! Tana sake maimaita "innalillahi wa'inna illahim raji'un!
Ya Kabeer ya kwantar da muryarshi ta sigar rarrashi da son kwantar mata da hankali ya ce "Jeeddah ki natsu ki sake dubawa wani gun dabam koda kin sauya mata mazauni ne kin manta da inda kika ajiye.
"Wallahi Ya Kabeer ba inda ban duba ba banganta ba kuma ni wuri guda nake ajiya gwal ɗina cikin jewelry box.
  "To shikenan ga mu nan zuwa gidan naki ni da Mama amma kafin mu zo ki daina kukan nan haka domin kukanki ba zai sa gwal ɗin ya dawo ba.
"Tam Yaya!
Ta faɗa tare da datse kira Ya Kabeer ya kalle Mama ya ce "Mama ko za ki shirya mu tafi can gidan nata domin wannan uban kuka da take risga tana buƙatar ki kusa da ita?"
Ajiyar zuciya Mama ta sauke kafin ta miƙe jiki ba ƙwari ta ɗauki Aiman ta nufi bedroom ɗinta, dashi ta sake wanke mishi jikinshi da ya ɓaci da tea dama already ta yi mishi wanka ta canza mishi tufafi, sannan tasaka hijabinta suna fitowa Baba yana fitowa daga ɓangare shi yana riƙe da hularsa yana gyara karinta.
   "Alhaji yanzu nan Jeeddah ta kira tana kuka wai ɓarayi sun shiga mata gida har sun yi nasarar ɗauke mata sarƙata ta gwal. Shi ne za mu je gidan nata ni da ɗa nan.
Tana nufi Ya Kabeer kasancewar shi ɗa fari bata faɗar sunan shi, sai dai ta kira da ɗa nan saboda alkunya.
   "Subhanalillah! ALLAH ya mayar mata da sabon arziki ki jajjata mata kafin anjima idan na taso daga kasuwa na biya ta gidan nata.
Baba ya faɗa yana ƙarasa kafe hularsa aka.
  "Wallahi Alhaji Jeeddah ta bani tausai ba ka ji yadda take gunji kuka ba gwani ban tausayi.
Ɗan guntun murmushi mai sauti Baba ya saki yana faɗin "Ashe Fatee har kin manta da hali Jeeddah kin tuna sanda tana yarinya ko slippers ɗinta suka ɓata, ta dinga risgar kuka kenan ko wani na siyo mata ba za ta daina mita ɓatar wancan ba. Ai yau aikin rarrashi ya same ku amma ki faɗa mata tasa haƙuri da dangana a zuciyarta Ubangiji da ya bata wancan shi zai sake bata wani, duk abinda haƙuri bai ba ka ba rashinsa ma ba zai ba ka shi ba. Rai ma ya ƙare aka dangana balle abinda rai ya mallaka saboda haka ta daina wahalar da kanta da koke-koke tun da ba mutuwa aka yi mata ba.
Baba ya faɗa tare da nufar ƙofar fita Mama da Ya Kabeer suka biyo shi a Mama tana cewa "Ina zan manta Alhaji amma wannan satar ko babba aka yi wa ita sai ya koka.
Dariya kawai Baba ya yi da sauri Ya Kabeer ya buɗe mishi murfin mota ya shiga kana ya buɗe mishi gate ya fita sannan ya dawo ya buɗewa mama motarsa ta shiga ya ja suka nufi gidan Jeeddah. Kafin su isa Ya Kabeer ya kira Aunty Farida da Khairat ya faɗa musu kowacce su hankalinta tashe ta nufo gidan Jeeddah, yayin da Mama ta kira mommy Turai ta sanar mata.
**** *** ****
Koda su Bilal suka iso Yabo kowanne su ido ya rena fata domin ba su san kalar cakwakiyar da za su tarar a gidan malam Alti mai rahunnai ba. Suna shiga garin Yabo kai tsaye gidan malam Alti suka yi wa tsike, sun tarar da dandazo mutane masu neman biyan buƙatar duniya kasancewar Malam ɗan uwa Hajja ne ta ɓangaren mahaifinta, shiyasa suka kutse cikin gida basu tsaya a ƙofar gida ba. Bayan wani lokaci Malam Alti ya shigo gida ɗakin uwargidansa aka yi wa su Hajja masauki saboda haka a can ya same su kowanne su ya daka ɗan uban tagumi. Bayan sun gaisa Hajja ta kora masa bayani kana Hajja ta fiddo da tarkace tsibance-tsibance ta miƙa mishi a hankali yake nazari akan su kafin ya shiga warware layoyi ɗaya bayan ɗaya ya tattaro dukkan natsuwa shi ya kalle su sun yi jigun-jigun dasu ya ɗago laya ta farko wacce Hajja ta fara warwarewa ya ɗaga ta sama ta yadda za su ganta da kyau ya ce "Wannan layar an yi ta ne domin raba tsakaninki da ɗan ki Faruk da kuma 'yan uwarsa wannan asiri duk wanda aka yi wa shi da wuya yaga daraja da ƙimar mahaifiyarshi, kuma yana ɗaukar dogon lokaci kafin ya ƙarye.
Wannan kuma mai kadangare ana yi shi ne domin taɓa lafiyar gangar jikin ɗan-adam kamar a saƙo mishi ciwon tabin hankali, kuma mijin Bahijja ne aka yi wa shi. Sai kuma wannan na mutuwar zuciya ne da ɗusasshe tauraron ɗan-adam za ki ga mutum yana neman aiki yi ya kasa samu ko kuma zuciyarsa ta mutu ya kasa neman na kansa. Wannan asiri yana nuni da Bilal aka yi wa shi domin naga sunansa ɓaro-ɓaro a ciki amma yanzu Al-hamdulillah...tun da ku ka zo nan ku ƙaddara komai ya zo ƙarshe amma kafin sannan wa kike zargi da yai muku wannan aika-aikar?"
Kusan a tare suka sauke numfashi kafin Hajja ta gyara zamanta tana faɗin "Malam ai babu batun zargi a cikin wannan al'amari sai dai tabbatar wa bana ko shakka abokiyar zamana ce Hajiya Bintu domin tun Alhaji yana raye muke taƙon saƙa da ita ai kasan komai Malam, domin gunka nake zuwa neman taimako amma ban taɓa cutar da ita ko wani daga cikin 'ya'yanta ba, iyakacina taimakon da zan mallake Alhaji a lokaci ikon faɗa nakeso a gidan ba ikon cutarwa ba. Kuma tun daga lokaci da Alhaji ya rasu na watsar da makaman yaƙi na. Ashe ita har yanzu da muguntarta danƙare a zuciyarta, saboda haka wallahi bata ci bulus ba, tun da ba malamai ta fi ni sani ba nima sai nai mata uban wanda tai min.
"A'ah Hajja kada ki biye mata tun dai ALLAH ya toni asirinta sai ki barta dashi za ki ga yadda ƙarshenta zai kasance.
Bilal ya faɗa yana mai tsare Hajja da idanuwanshi baƙar harara ta sakar mishi kafin ta kora shi waje ta shiga zayyanowa Malam Alti muradinta.
**** *** ****
Kafin kace kwabo gidan Jeeddah ya cika da Iyaye da 'yan uwanta fuskar Jeeddah har ta kumbura Idanuwanta sun luhu-luhu alamun tasha kuka ba kaɗan ba. Cikin dusasshiyar murya ta shiga basu labari yadda ta nemi sarƙa bata ganta ba. Duk da haka basu haƙura ba sai da suka rankaya gaba ɗayansu zuwa ɗakinta suka sake bincika wa sai lokaci Ya Kabeer ya shigo ɗakin yayin da Jeeddah ta nuna mishi safe ɗin da ke  cikin closet ɗinta anan take saka jewelry box ɗinta, kuma safe ɗin sai da code yake buɗewa shiru Ya Kabeer ya yi tare da nazarin safe ɗin kafin ya kalle Jeeddah with serious face yana faɗin "ke kaɗai kika san code ɗin safe ɗinan ko kuma har da mijinki?"
Kamar saukar aradu haka naji tambayar Ya Kabeer yayin da gabana yai mummunan faɗuwa, kuma a lokaci ɗaya su Mama suka dawo da ganinsu akaina sai na haɗiye wasu busassu miyau kafin nace "Shi ma yasani Ya Kabeer yanzu haka ma idan ka duba ciki za ka ga credential ɗinshi a ciki.
"Yana da labari ɓatan gwal ɗin naki?"
"Ba shi da Yaya domin a lokaci da na duba banganta ba shi ne mutum na farko da na fara kira amma wayarshi bata shiga.
Ɗan guntun murmushi Ya Kabeer ya saki kafin ya maida ganinshi akan su Mama da tuni suka kakkafe shi da idanuwansu ya ce "Mama ku zo mu je parlour idan har lissafina ya hau daidai na gano ɓarawo sarƙar Jeeddah.
Yana gama magana ya fice da sauri su Mama suka mara mishi baya, yayin da naji faɗuwar gabana ya ƙara tsananta da kyar na cira ƙafafuwana na biyo su. Kowa ya zauna banda ni domin wani irin sabon yanayi nake ji kaina a ciki. Sai da mommy Turai ta umarce ni da na zauna sannan na nemi kusa da ita na zauna gaba ɗayan mu muka tattara hankali da natsuwar mu akan Ya Kabeer. A natse ya shiga faɗin "ina da hujjoji kwarara da ke nuni da Bilal mijin Jeeddah shi ne ɓarawo sarƙarta.
   "Innalillahi wa'inna illahim raji'un!
Kusan a tare suka furta yayin da ni kam suman zaune nayi na saki baki da idanuwa na zama speechless and shock sai rarraba idanuwa nake yi da na kalle wannan sai kuma na dawo da idanuwana akan wannan.
Aunty Farida ce tai ƙarfin hali furta "uhmm...Ya Kabeer kada ka faɗin abinda ba ka tabbatar ba domin gujewa zubewar mutumci.
mommy Turai ta ce "A'ah Farida kada ki katse masa hanzari mana ki tsaya ya faɗin hujjojin nasa, amma ai ba abin mamaki bane idan aka zargi Bilal da sata domin mutumin da bai da aiki bai da sana'a ga mutuwar zuciya ai dole ka same shi da sata..
  "Dan ALLAH Mommy kada ku liƙawa Love sata wallahi ba sh....
"Kada ki yi sauri rantsuwa Jeeddah ki tsaya na kwararo miki hujjoji da nake dasu.
Ya Kabeer yai sauri taka min birki.
  "Haba Ya Kabeer ta ya zan yi shiru bayan ina da tabbaci mijina ba ɓarowa bane.
"Ke! Dallah rufa mana baki sakarya kawai duk yadda kika so ki kare shi ba za ki taɓa iyawa ba gara ki tsuke baki mu ji abinda ɗa nan zai faɗa.
Mama ta faɗa cikin tsawa babu shiri na tsuke bakina.
Yayin da Ya Kabeer ya shiga faɗin "idan har ku ka natsu ku da kanku za ku fahimci abinda na fahimta dangane da satar nan.
Abu na farko da za ku duba tun daga cikin parlour nan akwai abubuwan da dama da ya dace ace ɓarawo ya sata amma sai duk ya bar su kai tsaye ya shiga bedroom. Na biyu kuma da ya shiga bedroom kafin ya kai ga buɗe closet anan ma akwai abubuwan da yawa da zai iya sata amma duk ya wuce su sai ya tafi kai tsaye ga closet da ɓarawon na gaskiya ne dole sai ya fasa safe ɗin kafin yai nasarar ɗaukar sarƙar, amma ba wata alama da ke nuni da an fasa ta, saboda haka da code aka yi using. Da ɓarawo na gaskiya ne da ba yadda za a yi yabar zobe da 'yan kunne da ke ciki al'hali suma na gwal ne duk mai hankali da tunani idan ya natsu zai tabbatar da hujjoji da na kawo tabbas Bilal Shattima shi ne ya saci gwal ɗin Jeeddah saboda haka duk inda ya shiga wallahi-tallahi sai na nemo shi ya dawo mata da gwal ɗinta.
Gaba ɗaya su Mama suka ɗauki salati sai faɗa suke suna sake nanata wa yayin da na ƙara shiga firgici da tashin hankali, nan take ƙwaƙwalwa ta ta shiga tuno min da irin maƙudan kudi da ya siyawa A'isha Shattima kayan ɗaki, lallai biri ya yi kama da mutum babu sauran shakku ko kwakwato tabbas Bilal ne ya ɗauke min sarƙar gwal ɗina ya yi wa ƙanwar sa kayan ɗaki, wani iri ƙaton ƙololo na ji ya zo ya tokare min maƙoshi....
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

033...

Har muka iso gida kuka nake yi tsawon rayuwata ban taɓa kuka irin na wannan ranar ba. Nayi kuka har idanuwana sai da suka fara yaji-yaji gashi sun kumbure sun yi luhu-luhu muna shiga gida na shige ɗakinmu nasa na datse ƙofa da sakata, banaso kunnuwana su ci-gaba da ji min abinda zai ƙara linka min ɓaci ran da nake ciki. Na kwanta akan gado tare da yi rub da ciki na tsunduma tunani makomar rayuwar aurena, nasan inaso mijina amma wannan halayyar ta beraye da ya ɗauko sai na ji duk zazzafar ƙauna da nake masa ta fara dusashewa a zuciyata.
A police station kuma Bilal Shattima bai wahala da 'yan sanda ba kai tsaye ya amsa laifinshi aka ɗauki statement, ya tabbatarwa da 'yan sanda ya sayar da gwal ɗin akan kuɗi Naira dubu ɗari takwas lokaci da Ya Kabeer ya ji adadin kuɗi da ya saida gwal ɗin ji ya yi kamar ya kife shi da mugun mari sarƙa Naira miliyan ɗaya da dubu ɗari ita ce ya siyar akan dubu ɗari takwas, idan ba a ci riba ba bai kamata a faɗi ba, musanman yanzu da kullum grand ɗin gwal ƙara hauhawa yake yi.
Ya Kabeer ya kalle Bilal ya ce "Kai dai ayi mugu na ƙarshe lissafi na tabbata a jikin receipt ɗin sarƙar ka ga ko nawa aka siye ta saboda ba guminka bane shine ka siyar da ita a wulaƙance to wallahi bari ka ji duk ubanda yai maka tsaye a faɗin gari nan sai ka biya gwal ɗinan ko ka tafi gidan yari akansa.
Shiru Bilal ya yi sai wuƙi-wuƙi yake da idanuwana wani constable ya karɓe zance yana faɗin "Kai dai ka ji kunya wallahi ka yi asara banda mutuwar zuciya ka rasa inda za ka yi sata sai a ɗakin matarka, mummunan banza mai ƙaton hanci da gani mummunan fuskar nan taka ba gwal ba ko mutum ɗan adam za ka iya sata iri-irinka ne idan ba a farga ba ku ke zama mugaye 'yan ta'adda, ku addabe jama'a.
  "Yallaɓai ba sata nayi ba ara nayi in-sha-Allahu nan ba daɗewa ba zan dawo mata da abarta watakila ma wacce ta fi ta ta da na ɗauka.
Bilal Shattima ya faɗa cikin tausassa lafazi.
A fusace inspector da ke on duty ya daka masa tsawa domin tun shigowar da aka yi da Bilal a station ɗin ya ji laifi da ya aikata ya ke ji mugun haushinsa.
"Kai dallah! rufe mana baki tsohon ɗan iska masu ja mana zagi a wurin mata, a dalili iri-irinka yasa yanzu mata suka rena mu basa girmama mu ka zubarwa da kanka daraja da ƙima ana magana kana wuƙi-wuƙi da idanuwa, da wani shegen ɗangalalle hancinka.
Haka Bilal ya ci-gaba da shan zagi iri-iri daga bakuna 'yan sanda yayin da daga mai zagin fuskarsa sai mai zagin hancinsa musanman hancinsa ya sha zagi na fitar arziki.
Ya Kabeer ya jaddada wa 'yan sanda kada su sake su bada belinsa har sai ya fito da kuɗi ko sarƙar gwal ɗin.
Tun abin ƙarfe ɗayan rana Bilal Shattima yake a ƙargame a cell har ga shi yanzu ƙarfe 5:30 na yamma, tun ɗan koko da ya sha da safe shi ne a tumbin sa wata uwar yunwa yake ji kamar zai ci babu da ya ji uwar bari babu shiri ya shiga roƙon constable da ya bashi wayarsa ya kira gida ya faɗa musu hali da yake ciki ko abinci ne a ya kawo masa kada yunwa tai mata illa. Da farko constable din yaso ya hana shi gani yadda yake ta faman yi masa magiya yasa ya bashi wayar, abokinsa Abbas ya kira ya sanar da shi yana police station sai dai ya ɓoye mishi ainihin gaskiya abinda ya faru, da cikin gaggawa Abbas ya iso police station ɗin hankalin shi a tashe, lokaci da ya ji laifin da Bilal Shattima ya aikata sai da ya girgiza. Ba irin  kalar magiyar da bai yi ba akan abashi belinsa amma suka ƙi daga ƙarshe sai nuna masa suka yi sai da amincewar Ya Kabeer. Abbas bai yi ƙasa da guiwa ba ya karɓi phone number ɗin Ya Kabeer daga wurin inspector ya kira shi da farko sun gaisa cikin mutumtaka Abbas yana fara zayyano maƙasuɗi kiran nashi Ya Kabeer yai sauri datse kiran, da Abbas ya ci-gaba da kiran nashi sai kawai yai switch off ɗin wayarshi. Sai kawai Abbas ya kwantar wa da Bilal da hankali ya ba shi tabbaci zai shiga ya fita har sai an bada belinsa, yana baro police station ɗin kai tsaye gidansu Bilal ya nufo yana tura ƙofar shiga gidan da Aunty Bahijja  ya fara cin karo ta fito za ta tafi gidanta, bayan sun gaisa ya tambaye ta Hajja ta ce tana ciki "Aunty Bahijja idan ban taƙura ki ba mu shiga daga ciki akwai matsalar da ta kawo ni.
Ya wuce gaba Aunty Bahijja ta biyo shi a baya koda suka shigo Hajja tana bathroom suka nemi wuri suka zauna suna jiran fitowar ta, bata ɗauki dogon lokaci ba ta fito Abbas ya gaida ta amsa tare da faɗin "Abbas kaine a gidan namu?
"En! Hajja.
"To ALLAH yasa lafiya.
"Da dama za a ce Hajja domin Bilal yana police station.
   "Police station kuma?"
Kusan a tare Hajja da Aunty Bahijja suka furta kowanne su tashin hankali ya bayyana ƙarara akan fuskokinsu.
"Kwarai kuwa Bilal yana hannu 'yan sanda a dalili sarƙar gwal ɗin matarsa Jeeddah da ya ɗauka ba tare da saninta ba ya sayar ya yi wa A'isha kayan ɗaki. To shine ta nemi sarƙar ba ta gani ba daga ƙarshe aka yi bincike aka tabbatar da shi ne ya ɗauka. Su kuma 'yan uwanta suka haninta shi ga 'yan sanda su kuma 'yan sanda sun tabbatar min ba zu bada belinsa ba har sai in Ya Kabeer ɗin ne ya janye ƙarar.
  "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Oh! Ni Hajja shi kuwa Bilal me ya kai shi taɓa abinda ba nashi ba?"
Aunty Bahijja ta ƙarbe zance ta hanyar faɗin "ƙaddara ce Hajja in banda aikin ƙaddara me zai sa shi taɓa kayan Jeeddah balle har ɗan uwanta yasa a kulle shi wallahi Hajja daga Jeeddah har danginta rankataf ɗinsu basu da mutumci basu kuma gade sa ba.
"A'ah! Aunty Bahijja kada ki ɗauki laifi kacokan ki ɗora akan su idan ma su na da laifi na Bilal ya fi su nasu yawa miye kayan ɗaki da zai sa ya ɗauki gwal ɗin matarsa ba tare da saninta ba. Hakan fa yana nufin sata kenan...
"Dakata Abbas ni kam ban haife ɓarawo ba. Kowa ya sani abin mata na mijinta ne hakazalika duk abinda miji ya mallaka na matarsa ne da 'ya'yanta, ba kasan iya adadin hidindimo da faɗi tashi da yake yi akanta ba. Kawai dai sun yi haka ne domin su ci zarafinsa to kuwa kansu suka yi wa domin muddin aka kira Bilal da suna ɓarawo to tabbas sai Jeeddah ta amsa sunan matar ɓarawo..
"Hajja haƙuri fa za ku yi dole ku kai zuciyoyinku nesa idan ku ka ce za ku fusata to gaskiya al'amari nan gaba ɗaya lalacewa zai yi.
"Ni fa shiyasa tun farko banso aure Jeeddah nan ba saboda 'yar gidan ƙanana mutane ce banda ƙaranci saboda wani banza gwal za ta yi ƙarar mijinta.
Aunty Bahijja ta faɗa zuciyarta fal da tsanar Jeeddah.
Abbas ya ja bakinsa ya tsuke sai kallon Hajja da Aunty Bahijja yake yadda  suka murje idanuwansu ga gaskiya suna gani amma sai suka take ta suka ɗauki laifi tare da ɗorawa Jeeddah da 'yan uwanta, sai zagi da tsinuwa suke bin su dashi sai da suka yi mai isarsu kafin suka biyo Abbas zuwa police station ɗin. Lokaci da Bilal ya yi arba dasu duk sai ya ji kunya ta mamaye shi, musamman da ya tuna ƙaryar da ya sharawa Hajja da tambaye shi inda ya sami kuɗi kayan ɗakin A'isha.
Hajja kuka ta fashe dashi yayin da 'yan sanda suka gargaɗa ƙeyarsu waje, gani yamma ta kawo jiki yasa ta kira Baffan su Bilal ta faɗa mishi. Sosai ya dinga faɗa tare da ganin laifin Bilal kuma ko kaɗan bai ga laifi ƙarar Bilal ɗin da aka yi ba. Duk yadda so abashi belin Bilal 'yan sanda suka ƙi dole sai da amincewar Ya Kabeer. Abbas ya kawo shawarar su tafi kasuwa su isko mahaifin Jeeddah domin da matuƙar wahala Ya Kabeer ya janye ƙarar cikin sauƙi. Baffa ya amince da shawarar tashi gudun kada lokaci bada beli ya wuce yasa suka hanzarta suka tafi  Kasuwa a ɗaya daga cikin shaguna Baba suka tadda shi suna lissafi da Abdul Baba yana ganinsu yasan babu lafiya, bayan sun gaisa Baffa ya nemi su keɓance, kana ya kora masa dalilin zuwansu. Sosai ran Baba ya ɓaci a fusace ya kwaɗa wa Abdul kira ya ce ya je ya kira masa Ya Kabeer a ɗayan shagu, tun kafin Ya Kabeer ya ƙara so gun da suke ya hango Abbas tare da Baffan Bilal ga kuma fuskar Baba a haɗe yana zuwa Baba ya rufe shi da faɗa inda yake shiga ba ta nan yake fita ba. Duk da Baba yasan irin muguwar ta'adi da Bilal ya yi amma haka ya ɗorawa Ya Kabeer laifi ya zazzage shi tass! Kana ya tisa ƙeyarsa gaba suka taho police station aka bada belin Bilal, suna fitowa daga cikin police station adaidaita yana sauke Hajja da Aunty Bahijja ɗauke da foodflask sun kawo masa abinci. Haƙuri Baba ya shiga basu sai wani fizgar kai Aunty Bahijja take yi yayin da Hajja ta ji kunya zagin da suka dinga yi wa mahaifin Jeeddah suka sun zargi cewa da sa hannunshi aka rufe Bilal, sai gashi ya tabbatar musu da cewa bai ma da masaniya akan abinda yake faru cike da kunya gami da nadama Hajja ta kalleshi ta ce "Alhaji ai mu ne ya dace mu ba ku haƙuri wallahi-tallahi bansan cewa gwal ɗin Jeeddah Bilal ya ɗauka ba danasani ko kusa ba zan bari ya aikata wannan kuskure ba.
  "Ba komai Hajja ai ba a shiga tsakanin mata da miji duk wanda ya shiga rabon shi kunya, shi Bilal rashin kyauwarshi ɗaya ne da bai tambaye ta ba. Malam Bilal sai ka kiyaye  ko anan gaba kada ka ɗauki abin matarka ba tare da sani ta ba. Ka ga rashin faɗar abinda ya janyo maka.
Baba ya ƙarashe magana tare da kallon Bilal.
Saboda tsanani kunya kasa amsawa Baba Bilal ya yi sai sadda kai ƙasa ya yi.
Tsabar takaici da ya lulluɓe Ya Kabeer yasa yai sauri bari wuri ya nufi inda ya yi parking mota yana jiran Baba.
Daga nan Baba yai musu sallama tare da jadadda wa Bilal bayan sallar isha'i ya zo ya tafi da matarsa.
Ina sallame sallar isha'i Mama ta shigo ɗaki da nake tana ɓaɓɓatun faɗa sai cewa take yi "Na rasa Alhaji wane irin Mutum ne? Fissibillah a zalunci 'yarka ka kasa kwata mata hakkinta sannan kuma wanda ya ce zai bi mata hakkin nata shi ma ka hana shi wannan wane irin sanyi hali ne?"
Ina jin abinda ta faɗa na fahimci tana magana ne akaina kafin na ɗago idanuwana da har yanzu basu ƙarasa sucewa daga kumburin da suka yi ba na kalleta ina faɗin "Mama ni dama nasan da maganar nan ta je kunne Baba laifin Ya Kabeer zai gani amma wallahi-tallahi komai dare daɗewa sai Bilal ya biya ni gwal ɗina ba dai ya ce ara ya yi ba shikenan mu tafi a haka...
"Ke dallah! rufe min baki ba abinda za ki iya ai duk ke ce kika janyo tun farko ba yadda ban yi dake ba akan ki haƙuri da shegen yaro nan matsiyaci ne bai gadi arziki ba, amma ki ka ƙi to ga irin ta nan ɗauki ɗaɗɗaya zai dinga yi miki da kaya har sai kin waye gari ba ki da kayan ɗaki ko ɗaya.
Haka Mama ta dinga faɗar maganganu mararsa daɗi akan Bilal kafin ta ce min na tashi naje Baba yana kirana.
Ina zuwa parlour Baba ya ce na zauna rarrashina ya dinga yi gami da yi min nasiha "Jeeddah ki yi haƙuri da mijinki wata rana sai labari nasan abinda ya yi miki bai kyauta ba kuma ko waye aka yi wa haka dole ya ji zafi amma idan kika yi haƙuri sai ki ga ALLAH ya musanya miki da wani gwal wanda yafi naki na farko da ki ka rasa.
Duk maganganu da Baba yake faɗa iyakacina na gyaɗa kai a fakaice kuma ina sharar hawaye, ina baro parlourn ba daɗewa  sai ga Bilal Shattima ya zo ba kunya balle tsoron ALLAH ya iya zuwa gidanmu, sake haɗa mu Baba ya yi yai mana nasiha kafin ya ce na tashi na bi mijina mu tafi gida zuciyata kamar za ta fashe saboda haushi da takaici Bilal, muna fitowa daga gidanmu nai gaba abina da sauri ya biyo ni ya jera dani sai magana yake min nai banza dashi cikin sa'a muna isowa bakin titi na tare adaidaita ina shiga shima ya shigo ya zauna kusa dani ƙoƙarin kama hannuna yake yi na  daka masa rikitatciyar tsawa gami da faɗin...

*Just to manage*

_Ku yi haƙuri kwana biyu kun daina ji na bani da lokaci typing bikin aure muke yi_
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

032...

Sai dambe nake da numfashina tsawon rayuwata ban taɓa shiga tashin hankali kai har ma da takaici da zallar baƙin makamancin wannan ranar ba. Ban san sanda na ɗora hannu aka na kurma gigitatcen ihu na zube gwuiwayina kan tiles sai rizgar kuka nake yi a yanzu ba wai ina kuka ne saboda ɓata gwal ɗin ba ina kuka ne a dalili wai mijina ne zai min sata, wannan masifar da kayan takaici ya yi min yawa zuciyata ba za ta iya ɗauka ba. Mommy Turai ta dafa kafaɗarta cikin sigar so haifar min da natsuwa take faɗin "Kukan nan ya isa haka Jeeddah kada ki ja wa kanki wani ciwo na daban, mu shiga uku. in-sha-Allah duk gidan uban da ya kai miki gwal ɗinki za mu tusa ƙeyarsa gaba ya karɓo miki kayanki, ɗan iska Yaro maƙetaci tsohon azzalumi wallahi idan bai fito da sarƙa nan cikin sauƙi ba hukuma ce za ta raba mu dashi.
Ina ji maganganu da ke fitowa daga bakin Mommy Turai na sake fashewa da kuka.
Gaba ɗayansu suka saka ni a gaba sai aikin rarrashina suke yi da kyar na yi shiru amma wallahi can ƙasar zuciyata har yanzu kololo nan da nake ji yana nan ba inda ya tafi.
A gajiye likis su Bilal suka dawo gida suna shigowa a matuƙar fusace Hajja ta nufi ɓangaren Hajiya Bintu duk ƙoƙari Bilal na gani ya dakatar da ita amma abin ya ci turu tana gaba Aunty Bahijja na bin ta a baya cikin sa'a suka tadda Hajiya Bintu zaune a parlour ta Hajja tana zuwa ta soma zuba mata ruwan tijara "To baƙar munafuka algunguma wacce ƙarshenta ba zai yi kyau ba duk abinda ki ka daɗe kina shuka wa yau ALLAH ya toni asirinki wallahi Bintu da matuƙar wahala ki ji ƙamshin aljanna. Me na tare miki ni da 'ya'yana da za ki tarwatsa mana rayuwa?"
Kin shiga kin fita gidan bokaye kin yi nasarar raba tsakanina da ɗana Faruk, ki hanawa Bilal ya sami aiki yi, ki taɓa lafiyar mijin Bahijja shin wannan kishin naki wane iri kishi ne shi? Ko a tarihin jahiliyya ban taɓa cin karo da labari kishi kwatankwacin naki ba, to wallahi-azim ba zan kyale ki ba yadda kika tarwatsa mana rayuwa nima sai na tarwatsa miki taki, muguwar mata wacce babu ALLAH da Manzonsa a zuciyarta..
Jikin Hajiya Bintu ya ɗauki rawa ta miƙe tsaye ta fuskanci Hajja fuskarta babu alamar nadama, sai ma hayyaƙo wa Hajja da ta yi tana faɗin "Ke dakata Hajja! Ke har kina da baki yi min gori bin bokaye bayan a gunki na koya, ko kin manta badaƙalarki ta baya ne na tuna miki? Ke har kina tsammani na ƙauna ce ki ke da 'ya'yanki ai har gaba da abada ba zan so ku ba kuma zan so ci-gabanku ba. Ke kin manta da lokaci da Alhaji yana da rai irin mulki-mallaka da kika shimfiɗa to ai mutuwa ce kawai tai wa Alhaji sauri da wallahi ya yi jinkiri mai yawa da sai kin raina kanki sai kin gwammace ki kasancewar cikin kushewarki da zaman ki duniya.
"Amma Bintu duk mugun zama da muka yi a can baya ai yaci a ce mun manta dashi domin wanda muke kishin akanshi ya mutu baya duniya to miye amfani kishin mutumin da ke cikin kabari?" Kawai dai hasada ce ke ɗawainiya dake Kuma in-sha-Allah kin dinga gani yadda ba ki so kenan, kuma duk mugun nufinki akanki zai ƙare.
Hajiya Bintu tayi ihu gami da shewa kana ta tafa hannuwa ta kalle Hajja a wulaƙance ta ce "Ai Hajja zaman kishi yanzu muka fara ba dai kin yi nasarar haƙo wannan asiri ba to ki jira zuwan na gaba.
  A fusace Bahijja ta kalle Hajiya Bintu tana faɗin "Wallahi Hajiya kin yi asara kuma in-sha-Allah ƙarshen makirci ki ya zo wancan ma da kika yi nasara ki sa aranki bashi kika ci kowa da kike gani mugun kansa sai dai in ya so a zauna lafiya tun da kika nemi bala'i da masifa da kuɗinki to ki sani kin tara kin samu, ba dai kika ƙarshen mu a gidanan ba sai dai mu mu ga ƙarshen ki la'anana kawai.
   Aunty Bahijja ta ƙarashe magana tana huci kamar wata kububbuwa. Hajiya Bintu ta kalle gami da taɓe baki ta ce "Ke Bahijja dawo cikin hankalinki ki san da wacce kike magana ko uwarki ta buga dani ta barni balle ke ƙaramin alhaki, maza ku tattara ku ɓace min da gani tarkace banza 'yan wahala.
  "Ga ki nan muguwar 'yar wahala ma da farko naso a kashe maganar nan amma tun da kika nuna mana ke tantiriya ce ba ki gudun abin kunya to kotu ce za ta raba mu dake in-sha-Allah sai kin girbi abinda kika shuka, ku zo mu tafi Hajja za ta ga abinda zai biyo baya.
Bilal Shattima ya faɗa yana wani zare ido, daga haka suka fito kowanne su rai ɓace.
Duk yadda Jeeddah taso abi al'amari a tsanake amma su Mama sun ƙi su saurare ta, musanman Ya Kabeer da Mommy Turai sun fi kowa ɗaukar lamarin da zafi, don kuwa Ya Kabeer har rantsuwa ya yi ba inda zai tafi har sai Bilal ya dawo ya same shi a gidan, har aka yi sallar azhar yana gidan.
Da taimakon Aunty Farida da Khairat suka gyarawa Jeeddah ɗakinta da ta wargaza.
Bilal ya kalle Hajja yana faɗin "Hajja ki kwantar da hankalinki in-sha-Allah kamar yadda Malam ya faɗa kwana nan za ki ga Ya Faruk ya zo kuma Dan ALLAH kada ki sake kula wancan jakar matar ki jira har mu ga Ya Faruk ya dawo ainihin natsuwarsa sai mu ɗauki duk mataki da ya dace. Ke kuma Aunty Bahijja ki ɗage da ba Haruna maganganu da Malam ya ba ki shima da yarda ubangiji zai sami sauƙi. Ni zan wuce gida don wallahi wata muguwar yunwa nake ji.
Ya ƙarashe magana tare da miƙewa tsaye Hajja ta kalle shi tana faɗin "Gara ka tafi gida ka sami abin taɓa wa domin gidanan tashin hankali bar barmu mun girka komai ba.
"ALLAH yasa gantalalliyar matarsa ta girka dashi naga yanzu taƙamar rashin mutumci take duk da Malam Alti ya ce ita ma an shiga tsakaninta da Bilal. Amma wallahi rashin mutumci Jeeddah a jini jikinta yake asiri kwabai sa kawai yasa.
Aunty Bahijja ta faɗa tana wani yatsine fuska.
Haɗe fuska Bilal Shattima ya yi domin sosai ya ji zafin maganar da Bahijja tai akan Jeeddarsa "bana jin daɗi irin yadda kike faɗar kowacce magana ta fito daga bakinki akan matata Aunty Bahijja Dan ALLAH ki daina wallahi yana ɗaya cikin dalillai da yasa Jeeddah bata girmama ki.
Bilal ya ƙarashe magana yana mai ƙara tanke fuskarshi.
   Kallon uku saura Kwabo Aunty Bahijja ta watsa mishi gami da taɓe baki tana faɗi "Ai kai Jeeddar nan ta ri ga ta wanke ta ba ka ka shanye shiyasa sam ba ka gani aibunta.
Ba tare da ya tanka mata ba ya juye a fusace ya fita, ta ƙara bi shi da zafafan maganganu duk akan Jeeddah, yana fita ya tare adaidaita ya nufo gida yana tafe yana zabga addu'a a zuciyarshi ALLAH yasa girkin da Jeeddah tayi ta musu farfesu kaji domin jiya ya ga lokaci da Baba ya aiko yaronshi na kasuwa Abdul ya kawo mata figaggu kaji aƙalla za su kai biyar zuwa bakwai, da kwaɗayi su ya tashi ɓata mishi rai da tayi shi ya hana ya faɗa mata ta zaɓarɓaka mishi su. Shiyasa yanzu yake ta faman zuba addu'a. Suna shigowa layin gidansa ya ji wani mugun faɗuwar gaba, har sai da ya furta "innalillahi wa'inna illahim raji'un! Tun daga nesa ya hango motoci 'yan gidansu Jeeddah ai kuwa faɗuwar gabansa ya tsananta ko kusa bai kawowa zuciyarsa gwal ɗin da ya sata ne ya kawo su ba domin yana da yaƙini akan Jeeddah bata so saka necklace, kafin ta ankara da ɓanar da yai mata an ɗauki dogon lokaci. Sai kawai ya shiga wasi-wasi meke faruwa da 'yan uwan Jeeddah da za su cika masa gida, musanman da ya ga hadda motar Ya Kabeer da motar Mommy Turai, wata zuciya ta ce dashi ko Jeeddah ce ba lafiya har adaidaita ya sauke shi gabanshi bai fasa faɗuwa ba. Ko canji shi bai tsaya amsa ba ya kwasa da mugun sauri ko gabanshi baya gani garin sauri yaci ɗan uban tuntube da dutse saura kaɗan ya faɗin sai da ya gurje da ɗan yatsan shi har da jini ya yi amma hakan bai dame shi ba muradinsa ya isa cikin gida, jikinsa yana rawa ya tura ƙofar parlour. Suna zaune jigun-jigun kowanne su fuska ba annuri kamar waɗanda ke zaman makoki. A lokaci ɗaya suka kallo shi, kowanne su da yana yi mugun kallo da yake aika masa, nan take ya ji wani iri tsoro ya lulluɓe shi musamman da yai arba da Jeeddah yaga yadda idanuwanta suka koma alamar tasha kuka ta ƙoshi. "Shin meke faruwa a wannan gidan ga dai Jeeddah na ganta cikin ƙoshin lafiya ga kuma Aiman yana wasar shi da Ball?"
Bilal ya faɗa a zuciyarshi ashe bai san cewa tambayar tashi ta fito fili ba sai da ya ga Ya Kabeer ya taso a mugun fusace ya nufo shi yana faɗin "Idonka kenan tsohon ɓarawo to ai tsayuwa za ka yi ba kana tambayar kanka da kanka mune ya dace ka tambaya mu ba ka amsa, ai sai ka shigo domin tsayuwa bata gano ka ba ka fayyace mana ina ka kai wa Jeeddah gold necklace ɗinta da ka sata.
  Saura kiriss numfashin Bilal Shattima ya fita daga gangar jikinsa maganar ta zo masa a bazata ba a yanzu ya shiryawa zuwan ta ba. Sai gashi ta zo mishi a kwatsam! Babu shiri.
Ya haɗiye wasu busassu miyau marasa ɗanɗano a maƙogwaro. Cikin firgici da fitar hankali ya shiga ja da baya-baya a nufinshi ya cikawa wandon shi iska, sai dai kafin ya kai ga cimma manufarsa Ya Kabeer ya daka tsalle ya damƙe hannunshi, kamar makaho da ɗan jagora haka Ya Kabeer ya jawo shi izuwa tsakiyar parlour, Mommy Turai tai zubur ta miƙe tsaye ta shiga yi mishi ƙasƙantatce kallo kafin ta shiga tafa hannuwa tana faɗin "Sannu da zuwa ɓarawo tun ɗazu muke tsumaye zuwanka, finally sai ga shi ka zo. Sai ka samu damar ɗauko wa baiwar ALLAH nan sarƙata tun kafin mu yi maka yekuwa duk da bana tunani hakan zai taɓa ka tun da dama can an saba da 'yan dauke-dauke.
Gani yadda mommy take gaggaya wa Love maganganu marasa daɗi yasa ni miƙewa da sauri na nufo gunta, cikin kwantar murya nake faɗin.
"Mommy Dan ALLAH ku yi masa a hankali wallahi Love ba ɓarawo bane ni har yanzu ban gamsu da da hujjojin da Ya Kabeer ya faɗa ba wallahi love ba zai min sata ba ni fa matarsa ce abin ikonsa...
Tun kafin na ƙarashe magana Mommy Turai ta daka min gigitatciyar tsawa, har na zaci gwaɗa min mari za ta yi.
"Rufe mana baki Dan ubanki Jeeddah, ka ji min sakarci banza da wofi, mutumin da ya raba ki da kaddararki ya saka ki kuka tun safe zuwa Yanzu shine don tsabagen lalacewa you still call him love kai kuma wai har kina ƙoƙari kare shi wannan dakarci da yawa yake, wai Dan ALLAH Dan Annabi Bilal ka faɗa min gaskiya ba ka yi wa 'yar nan asiri ba?"
Tun sanda Bilal ya sadda kai ƙasa, bai sake ɗagowa ba, wata irin mashahuriyar kunya da danasani ne suka lulluɓe shi a lokaci guda. Da za ki tambaye shi a lokaci tabbas da zai iya cewa yau ce rana mafi muni a rayuwarshi. Kuma duk maganganu da iyayen Jeeddah da 'yan uwanta suka faɗa akanshi bai ji zafi ba bai kuma ga laifinsu ba. Ya cancanci fiye da hakan domin son zuciyarshi ne ya kai shi da hakan.
Duk da ni Bilal ya yi wa katoton laifi amma na rasa dalili da yasa nake jin zafi cin mutuncin ake masa, nake kuma ƙoƙari na kare shi na kasa jure zagin da ake masa sai kawai nasa kuka Aunty Farida ta taso cikin fusata ta rizgo ni tamkar za ta ƙarya min hannu, tana faɗin "Idan ba ki rufe mana baki ba sai nayi ƙassa-ƙassa dake a nan wuri.
"Kyaleta kawai Farida tun bata so a kwata mata hakkinta ga ta nan ga shi ba dai Bilal ba wallahi sai ya sa ki kukan da za ki rasa hawaye zubarwa.
Mama ta faɗa cike da takaincina.
Ya Kabeer ya ƙarbe zance yana faɗin "Bata isa ba wallahi Mama tun da ta kiramu dolensa sai ya fito da gwal ɗinan walau ta daɗin rai ko akasin haka, saboda haka Jeeddah ki ja bakinki ki tsuke idan kika kuskura ki ka ƙara sa mana baki a magana na rantse da ALLAH sai na tattaka ki.
Ina jin yadda Ya Kabeer ya ƙarashe magana na koma wurin zamana na faɗa bisa kujera gami da kifa kaina a hannu kujera na buɗe sabon babi kuka, duk irin zagi da cin mutuncin da suke wa Bilal ko kwakwaran motsi ya kasa yi balle na sa ran zai kara kanshi. Hakan ya ƙara tunzira Ya Kabeer ya ce "A karo na ƙarshe Bilal ina mai gargaɗinka da ka faɗa min ina gwal ɗin ƙanwata idan ba ka buɗe baki ka bani gamsasshiyar amsa ba wallahi-tallahi zan haɗa ka da hukuma.
Bilal Shattima yana jin Ya Kabeer ya ambaci hukuma ya ciro kanshi da sauri ya kalle shi da idanuwanshi da tuni suka sauya colour, tamkar zai fashe da kuka yake faɗin "Dan ALLAH Dan sonka da Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallam Ya Kabeer ka rufa min asiri kada maganar nan tafita, domin ita ta fita wallahi mutumcina da ƙima ta za su zube a idon jama'a.
  "Ai ni na fi so duniya ta gama sani kai mugun miji ne azzalumi, ban da zalunci miyasa za ka ɗauke mata gwal ba tare da saninta ba, ko kuma kana nufi ka ce dani bakasan cewa ɗaukar kayan mutum ba tare da sani mai shi ba sata ne koda kuwa kana kyakkyawan kusanci dashi?"
Zuwa lokaci Bilal Shattima ido ya rena fata ba don ya kasance namiji mai taurin zuciya ba da tuni ya fara ambaliyar hawaye, cikin kwantar da murya ya sake cewa.
"Na sani Ya Kabeer amma wallahi banida mafita a lokaci kuma ina tunani idan na faɗa mata ba lallai ta amince da buƙata ta ba. Kuma na ɗauki gwal ɗin ne da zimmar aro idan ALLAH yasa na sami aiki sai na biya ta wallahi bana nufi na cuce ta ALLAH shi ne shaida ta akan hakan.
Ya ƙarashe magana kamar zai fashe da kuka.
  Mama ta ja guntun tsaki cike da takaici ta ce "kana nufi ka sayar da gwal ɗin to me ka yi da kuɗin?"
Tirya-tirya ya zayyane masu yadda ya sayar da gwal ɗin da yadda ya yi da kuɗin. Gaba ɗaya suka ɗauki salati, ban da ni domin tuni na gano abinda ya yi da kuɗin da kuma tun farko nasan shi ya ɗauki gwal ɗin da ba zan sanar a gidanmu ba. Zan ja bakina nayi shiru gudun kada mutumcin mijina ya zube amma aikin gama ya gama masu iya magana suka ce rashin sani yafi dare duhu, takaicina ɗaya miyasa da ba zai tambaye ni ba ai ko don albarkaci ƙauna da ke tsananina da A'isha Shattima zan iya bashi gwal ɗin.
Wulaƙanci da ƙasƙanci ba irin wanda ba su yi masa ba zagi kala daban daban, hatta da Khairat da ke matsayin ƙanwata ina ji ina gani tana yaɓawa mijina maganar banza sai dai banida yadda zan yi domin shi janyo wa kansa. Duk yadda ake wulaƙanta ɗan adam a tozarta shi Bilal Shattima ya yi min naji kunya naji baƙin ciki, na kuma ji takaici da ya kasance shine mijin da nake aure. A takaice ba zan iya misalta muku irin baƙin ciki da na shiga ba sai dai kawai nace da ku kwatanta kanku a matsayina shin ya za ku ji idan aka ce mijinki shine ɓarawo ki wanne mataki za ki iya ɗauka?" Ba zan ɓoye muku ba wallahi sai na ji duk na tsani ganinsa, hakan yasa na tashi a mugun fusace na shiga ɗaki na ɗauko hijabina da wayata na fito, na kalle Khairat cikin ɗusasshiyar muryata nace "Khairat tashi mu tafi banaso na ƙara daidai da second ɗaya ina kallon fuskar mutumin nan wallahi zuciyata za ta iya bugawa.
Kafin Khairat ta miƙe Bilal ya riƙo hannuna cikin zallar tashin hankali yake faɗin "Dan girman ALLAH Love ki yi haƙuri kada ki guje ni saboda wannan abun, wallahi-tallahi zan shiga na fita koda zan rasa raina na dawo miki da gwal ɗinki ki bani dama dan ALLAH.
A fusace na fizge hannuna cikin muryar kuka nake faɗin "miyasa Bilal miyasa ba za ka tambaye ni a lokaci da ka shiga matsala na ba ka gwal ɗin da hannuna shin kana gani ba zan bane shiyasa ka sata?
"Saboda ina tunani ba za ki bani ba Jeeddah shiyasa na ara ba sata nayi ba m amma wallahi zan dawo miki dashi.
"Ka ri ga da ka makaro Bilal domin na bar ka bari na har abada ba wai don saboda gwal ɗina ba. Zan bar ka ne a dalili sata da kayi saboda haka ka sa aranka ka rasa ni domin ba zan iya ci-gaba da zama da ɓarawo ba.
Ina ƙarasa faɗa haka na juya da sauri Khairat ta biyo ni a baya Bilal yana ƙoƙarin ya bita Ya Kabeer ya cafko shi ya dawo dashi ya fito da waya daga aljihunshi ya kira Asp Saddam wanda ya kasance classmate ɗinshi ne, duk haƙuri da Bilal Shattima yake bashi hakan bai hana shi haɗa shi da jami'an tsaro ba. Yayin da house neighbours ɗinshi suka firfito daga apartment ɗinsu suna kallo tare da kus-kus a tsakaninsu...
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

034...

"Ka ga malam ka yi sha'ani gabanka banso taƙura.
Langwaɓe kai ya yi yana kallona har muka iso gida idanuwanshi suna yawo a kaina, a fusace na fito daga adaidaita na nufi cikin gida dama key yana hannuna, na buɗe ƙofa kaitsaye bedroom na shiga ina cikin cire tufafin jikina ya shigo da wata guntuwar sallamar shi har wani maƙe muryar yake yi. Nayi tamkar ban ji shi ba ya jingina jikinshi a bangon gami da folding hannuwanshi sai faman kallona yake yi, ni kuma ko a jikina a gabanshi na dawo halfnaked daga ni sai pant da bra da mugun sauri ya nufi bathroom ya ɗauko min towel ya miƙo min na kalleshi tare da banka mishi baƙar harara, na raɓa ta gefenshi na wuce abina.
Ya bi ta da kallo tuni hankali gogan naku ya tashi musamman yadda ya ga mazaunanta na jujjuya wa, nan take ya ji matsananciyar sha'awa tai mishi dirar mikiya har sai da yasa cinyoyinshi ya matse hantsar wandonshi sani kanshi ne yadda take fushi dashi ko zai mutu ba za ta bashi ba. Shiyasa ya shiga ƙoƙari haɗiye kwaɗayi sa.
Bayan wasu 'yan mintuna ta fito ɗaure da towel iya cinyarta, yayin da raguwar ruwan wanka ke dinga daga jikinta. Sake gitta shi tayi ta nufi dressing mirror ta zauna ƙaramin towel da ke riƙe da hannunta tasa tana tsane ruwan jikinta. Bilal Shattima ya haɗiye wasu busassu miyau gami da lashe laɓɓanshi har ta shirya cikin kayan bacci cotton riga da wando irin boomshort ɗinan ne ɗuwawunta suka zauna ɗass cikinsa. Jikinta ya ɗauki ƙamshi turaruka masu shegen ƙamshi da tada hankali ɗa namiji. Bilal ya ja gwaron numfashi kana ya yi wa kansa ƙiyamullaili ya shiga bathroom ya sakar wa kansa ruwa koda ya fito har ta kashe bulb ta shige cikin bargo.
Ya nufi switch ya kunna bulb din da ta kashe, hasken ya kashe mata idanuwa tai sauri lumsashe su. Yadda ta lumshe idanu ba ƙaramin burge shi tayi ba don sai da ya saki ɗan ƙaramin murmushi.
Ina gani ya yi min murmushi na ja guntun tsaki tare da juya masa baya har ya kammala shirinsa ban sake juyawa ta gun da yake ba. Wallahi haushinsa nake ji marar misaltuwa duk lokaci da na kalleshi sai naji tamkar na rufe shi da ɗan bala'in duka.
Nayi nisa da tunaninsa ban san lokaci da ya iso kusa da ni ba har ya zauna sai jin nayi ana min massage a gadon bayana, sosai naji daɗin massage ɗin. Domin throughout kwance na yini a gida dole bayana ya yi ciwo, sai lumshe idanuwa nake yi can na tuna da Bilal Shattima ne fa yake min tausa sai kawai na zubura na tashi zaune, ina galla mishi harara "Miye haka?"
Na faɗa ina yatsine fuska.
"Massage ne nake miki Love naga kamar akwai gajiya a jikinki.
Ya yi magana cikin tausassa lafazi gami da langwaɓe kai.
  "Ni nace da kai ina jin gajiya balle ka yi min massage?"
"A'ah! Kawai naga dacewar nayi miki ne.
"To hell with you kai da massage ɗin ka Bilal idan har kana da kunya a idanuwanka bai kamata ko ɗan yatsana ka yi ƙoƙari taɓawa balle har ya kai ka da yi min massage.
    "Haba! Jeeddata tun da na karɓi kuskure na na kuma bada haƙuri a duba lamari nan ayi min afuwa matar na tuba bata rasa mijin aure.
Zan iya jure duk hukunci da za ki yi min amma ban da nisanta ni daga gare ki domin hakan zai iya taba garkuwar jikina...
    "Kai dallah dakata!
Nai sauri taka masa birki tsakani da ALLAH na gaji da mayaudarar kalamanshi da babu komai a cikinsu face zallar yaudara, cikin ɓaci rai na ci-gaba da cewa "Bilal inaso ka sani jiya ba yau ba tuni na dawo daga rakiyar mayaudarar kalamanka, saboda haka don ALLAH ka kyaleni bacci nake ji.
    "Ba zan iya ba Jeeddah domin rayuwata idan babu ke incomplete ce nasan ban kyauta ba ban kuma yi miki adalci ba amma ki sani komai muƙaddari ne daga ALLAH ki yafe min kin ji rabin raina.
   "Mtsssss! Ka ji da muguwar yaudarar ka.
Na faɗa tare da matsawa nesa dashi na kwanta ina ci-gaba da mita.
Bai daddara ba ya sake matsowa sai jin shi nayi cikin jikina da ƙarfi tsiya ya rungume ni a ƙirji shi duk bore da nake masa bai saurara min ba. Sai da ya yi connecting bakinshi da nawa ya shiga kissing ɗina with passionate, wallahi Bilal mugu ne na ƙarshe sai da na fashe mishi da kuka sannan ya kyaleni yana sake ni na daka tsalle na sauko daga gado, da rigata a hannu da ya cire min na kalle shi da idanuwana da suke tsiyayar hawaye na ce "Da ka yi min fyade Bilal Shattima da wallahi ba zan taɓa yafe maka ba mugu kawai wadda baya tausayina, duk irin ƙaunar da na nuna maka irin sakamakon da za ka saka min dashi kenan, nagode Bilal nagode sosai.
Na ƙarashe magana tare da mayar da riga ta na juya da nufi bar mishi ɗakin gaba ɗaya gara na koma ɗayan bedroom na kwanta, domin ba zan taɓa bashi abinda yake so ba dama shi ne amfanina a wurinshi da ya gama more ni wani sabon wulaƙanci zai kunno min dashi.
Kafin na kai bakin kofar fita yai sauri sauko wa daga gado, ya cafko min hannu muka shiga kokawa kasancewar yafi ni ƙarfi shiyasa yai nasarar ɗauka ta, sai shusshura ƙafafuwana nake yi ina halɓin iska yayin da hannuwana ke kai masa duka ta ko ina sai faɗin "Na ke yi Bilal ka rabuda ni banaso Dan ALLAH ka kyaleni ka bar min zuciya ta huta haka nan wai me nai maka ne da ka rantse sai ka taƙura wa rayuwata?"
   Duk abinda nake faɗa ya yi biris dani sai da ya kaini bisa gado ya shimfiɗe kana ya haye min jiki, da sauri na kauda fuska don na tsani kallon shegen bututun hancinshi ada mugu gani kyau hancinsa nake yi amma a yau sai na ganshi wani ɗan tsurut ga ƙofofin hancin nashi a wage kamar rijiya.
   Hannunshi naji cikin rigata yana min ta'asa don kuwa sai murza min nipples yake yi, da dukkan ƙarfina na kai masa duka cikin sa'a na sami hancinsa babu shiri ya wutsile gefe, yana faɗin "Wayyo Jeeddah kin fasa min hanci.
"Mtsssss...! Na fasa maka hanci ko dai na buge tsoka.
  Na faɗa ina galla masa uwar harara.
  Murmushin ya yi mai sauti tare da mirginowa ya yi matashin kai da hannun shi na haggu, yasa ɗayan hannunshi yana shafa gefen fuskata.
   "Love me ya haɗa hancina da tsoka?"
"Ai hancin naka ne Bilal ba shi da bambanci da tsokar nama ko ba ka duba madubi ne?"
Sosai ya kwashe da dariya sai kwasar abinsa yake yi ni kuma na ja guntun tsaki don banga abin dariya anan ba. Kamata ya yi ya ji haushi sai kawai ya buge da dariya anya kuwa notin ɗin kan Bilal bai burge ba.
  "Ina bala'i mugun sonki Jeeddata.
Ya faɗa cikin muryar dariya.
   Sai na ƙara jan tsaki da mugun takaici na ce "Ni kuma bana sonka gara ka nemi mai sonka tun dare bai maka ba.
    "Faɗa kawai ki ke yi ɗiyar Baba domin sona halitta ne a cikin jini ki.
"Wato shiyasa ka ke min wulaƙanci iri-iri kou Bilal?" To shikenan ka sa aranka daga yau na daina son naka period.
Dariya kawai ya yi tare da sake rungumo ni yana kissing wuyana da fatar kunne na duk yadda naso na ture shi na kasa ina ji ina gani ya matse ni a ƙirjinshi ya raɗa min "Love ALLAH ya ba ki ciki ki haifa min Baby girl mai irin hancina.
Ya ƙarashe magana yana dariya a fusace na amsa da cewa "Ba Amin ba!
Nan ma dariya ya yi sai naga kamar nishaɗi maganganu na suke haifar mishi, sai kawai nai banza dashi tun ina jin tsokanata da yake har bacci ya yi awon gaba dani.
Washegari ina kammala sallar asuba na bi lafiyar gado, kasancewar weekend ne kuma muna hutun makaranta sai around 11:00am na falka nayi miƙa tare da doguwar hamma kana na kalle gefena ban ga gogan naku ba. A zuciyata nace lallai yau za a yi ruwan sama hadda ƙanƙara malam Bilal an yi sammako tashi, sai kuma na taɓe baki a bayyane na ce "ALLAH yasa ba wata sabuwar kitimurmura ya sake shirya min ba don ni wallahi yanzu tsoronshi nake ji.
Na sauko tare da shiga bathroom nayi wanka a gaggauce na shirya cikin ƙanana kaya wandon  Palazzo dark purple na saka top mai dogon hannu light pink mai watsi white flowers a jiki na yane kaina da scarf purple colour, ni kaina da na kalle kaina a jikin mirror sai da na yaba wa kyau da nayi. Tun kafin na ƙarasa parlour na fara jin ƙamshi girki yana tashe na zaro idanuwa da sauri na nufi kitchen na hango Bilal ya taƙarƙare yana yanka albasa daga shi sai boxer briefs da farar underwear vest ya ɗora apron akai, ƙara zare idanu nayi, cikin kaɗuwa nake ƙare masa kallo ƙamshi turaren ta ya sanar dashi zuwanta, saboda haka ya juyo fuskar shi cike da murmushi yake faɗin "Good morning Love! Ashe kin tashi?"
Wani malalaci kallo na watsa masa tare da taɓe baki, gami da faɗin "uhmm! Sabon salo wai gemi a ƙafaɗa yau kuma da wannan iya yi aka tashi?"
'yar dariya mai sauti ya yi tare da tunkaro ni da sauri na ja baya ina ya motsa fuska duk da haka bai fasa nufo ni ba yana zuwa ya riƙo ƙafaɗuna yana faɗin "Kin yi matuƙar kyau matata kamar na cinyeki.
  "Ashe kai maye ne ban sani ba.
"En! Amma mayenki ba na mutane ba.
Taɓe baki nayi tare da kauda fuska.
  "Mu je ki yi breakfast Love.
   "Breakfast Kuma to me ka ke girkawa ne?
"Farfesu kaji da Baba ya aiko mana ne nace bara na faranta miki yau ki ci farfesu da yafi naki daɗi da garɗi.
  Kallonshi nai a lalace kafin na juya ina yaba rashin kunyarsa kai har ma da rashin zuciya, wato shi har ya manta da baƙin ciki da ya ƙunsa min, jiya-jiya nan da har zai daka sammako ya hau kaji da mahaifina ya kawo min da dahuwa sai kace wani tsohon maye.
Ya biyo ni a baya sai wani iya yi yake min ni kam sai kallo nake binshi dashi, muna shiga dining room yai sauri jawo min kujera "Zo ki zauna my Love yau ranar ki ce sai abinda ki ka ce zan yi.
"Uhmm!
Na faɗa gami da watsa mishi harara na zauna ina ƙara tanke fuska, soyayyar doya ce ya yi haɗe da sauce mai haɗe da hanta ya zuba min a plate kana ya ce dani "Love kunu gyaɗa za ki sha ko na haɗa miki tea?
   "Tea!
Na faɗa a takaice kuma a yatsine.
Yana cikin haɗa min tea aka yi knocking on, har na miƙe ya mayar dani zaune yana faɗin "Koma ki zauna bara na duba waye yake so shiga hakkin ma'aurata da sanyi safiyar nan, mtsss! Wasu mutane sam basu da tunani, basu sam lokaci da ya dace su kawo ziyara ba.
Ya ƙarashe magana tare da nufar ƙofa yayin da na bishi da kallon mamaki kafin nayi ɗan gajere murmushi na ɗauki fork na shiga cin abincina. Bilal Shattima yana buɗe ƙofa ranshi a ɓaci sai kawai yai tozali da Hajja tare da A'isha Shattima da Aunty Bahijja.
  "Hajja ya na ganku ku dukka ALLAH yasa ba wani abu kuma ya sake faruwa ba?"
  "Lafiya qalau ba abinda ya faru mun zo ne domin mu ba Jeeddah haƙuri akan abinda faru.
Hajja ta faɗa tana ƙoƙarin kutsa kai cikin parlour kafin Bilal ya sake magana su Aunty Bahijja suka shigo....
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

035..

Kowanne su ya nemi kujera ya zauna daga dining area ina iya hango  cikin parlour, saboda kujerar da nake zaune tana facing cikin parlour ne. Shiyasa akan idanuwana suka shigo har suka zauna ina kallonsu.
Aunty Bahijja ta kalle Bilal da ke sanye da apron ta taɓe baki kafin ta ce "Kai kuwa Bilal wacce irin lalacewa ce ta sami ka da ka ke sanye da rigar girki tun da sassafe ko hatta da girki kai ke yi mata?"
Ƙasa da murya ya yi yana faɗin "Kin ga Aunty Bahijja banaso tadda zaune tsaye kun ce haƙuri ku ka zo bata ke kuma gashi kina ƙoƙari shiga abinda bai shafe ki ba. 
   "Daga tambaya sai cibi ya zama ƙari to maida wuƙar ka kira mana hanshaƙiyar taka, don ba gadin parlour muka zo yi muku ba.
Bilal bai tanka mata ba ya juya gami da nufar dining room, suka bi shi da kallo sai lokaci su ka hango ni.
A'isha Shattima tai sauri tasowa ta nufo wurina, kujerar da ke kallona ta ja ta zauna "A'isha amarya ya amarci?"
Na faɗa fuskata shimfiɗe da murmushi.
A maimakon ta bani amsa sai kawai ta buge da faɗin.
"Jeeddah na zo ne na ba ki haƙuri akan abinda Ya Bilal yai miki ko kaɗan ji daɗi ba ace ta sanadi na kin rasa abu mai matuƙar muhimmanci da tsada, dukkan mu ba mu san cewa gwal ɗinki ya Bilal ya siyar ba. Da wallahi ba zan taɓa amincewa ya salwanta miki shi ba. Shiyasa na je gida na zo tare da Hajja da Aunty Bahijja domin na yanke shawarar a kwashe furniture ɗin a sayar a dawo miki da kuɗin duk da ba lallai bane kuɗin gwal ɗinki su dawo gaba ɗaya ba. Amma za ki iya rage asara.
   Tun kafin ta ƙarashe magana nake girgiza kai, kafin na dire fork ɗin hannuna cikin plate, na kalle gefen da Bilal Shattima yake tsaye rakuɓe da jikin bangon dining room ya yi wani iri dashi domin shi kanshi bai yi tsammani fitar wannan maganar daga bakin A'isha ba.
  "A'isha abinda ya wuce bai kamata mu dinga dawowa dashi baya ba. Zance a sayar da furniture ɗinki a dawo min da kuɗi wannan magana banaso na sake jin ta daga bakinki, ki ƙaddara a ranki haka ALLAH ya tsara ni ke da gwal amma ke ce za ki amfana dashi. Takaicina ɗaya da yayanki ya ɓoye min ya barni a duhu har sai da na nemi gwal ɗin. Da tun farko ya fito fili ya faɗa min da duk bata kaimu da haka ba.
  "Gaskiya bai kyauta ba shima idan kika dube fuskarshi ya yi nadama hakan Dan ALLAH ki yafe mishi Jeeddah.
  Ɗan bazawari murmushi nayi tare da miƙewa tsaye na riƙo hannunta gami da faɗin "Zo mu je parlour na gaida Hajja mu bar su zaune sai zuba muke yi.
A hankali suka sauko daga kan steps din dining room suka shiga parlour.
Duk firar da ta shiga tsakani Jeeddah da A'isha Bilal yana ji duk sai ya ji tausayin Jeeddah da wata irin mashahuriyar ƙaunarta suka ƙara linkuwa a zuciyarshi ya ji ta ƙara samun babban matsayi da ya zarce wanda take dashi tun farko a gareshi.
  "Ina kwana Hajja?"
Na faɗa gami da ɗan runsunawa.
   "Lafiya qalau.
Hajja ta amsa ba yabo ba fallasa gani yadda amsa min gaisuwa yasa daga haka na ja bakina na tsuke sai kawai na nemi kujera na zauna.
   "Jeeddah mun zo ne akan gwal ɗinki da 'yan gidanku su ka ce Bilal ya sata wacce ya yi sata domin ta ta ce a kwashe kayan ɗakin a siyar a ba ki kuɗinki. Domin ke kam ba matar rufin asiri bace  ni a tunani ko duk abinda kika mallaka Bilal ya sayar ba za ki ce uffan ba. Saboda ke ce kika liƙe masa ba yadda bai nuna miki bai tashi aure ba ki ka kafe lallai sai ya aure ki ashe dama so ki ke ki tallata shi a duniya a dinga yi masa kallon ɓarawo to ki sani kanki ki ka yiwa domin duk lalacewarshi yana nan a matsayin mijinki.
  Da sauri na ciro kaina ina kallon Hajja da baki buɗe ba ƙaramin mamaki ta haifar min dashi ba.
Kafin na sami lalluɓo kalmar furta wa Aunty Bahijja ta ri gani ta hanyar cewa
  "Kwarai kuwa gara a siyar a baki kuɗinki don mu ba ma so harka da fallasa da tono asiri da iyayenki da 'yan uwanki suka kwarai da shi, ban da kuturun wulaƙanci da reni wayau shi Kabeer yaushe ya yi Kuɗi da zai sa a rufe Bilal a police station.
Tana dasa aya ina miƙewa tsaye domin maganganun su ba ƙaramin ƙona min rai suka yi ba. Sosai idanuwana suka rufe, na ce "Duk abinda za mu yi da ke Aunty Bahijja ya tsaya iya ni kaɗai domin ni nake auren ɗan uwanki amma Iyayena ba sa'ar yin ki bane don haka kada ki sake ki furta magana banza akansu.
  Ita ma Aunty Bahijja miƙewa tayi dama tun faru al'amari take jiraye da Jeeddah, saboda haka a wulaƙance take kallonta kafin ta ce
  "Iyaye naki har wata jar duniya ne su da ba za a furta maganar banza akansu ba, ai sun ri ga sun zama mutane banza tun da suka kasa ba ki tarbiyyar da za ki rufawa mijinki asiri.
Gaba ɗaya jikina ya ɗauki rawa saboda tsanani fusata da nayi har ji nake yi kamar ƙafafuwana ba za su iya ɗauka na ba. Bansan lokaci da na ƙundumo ashar na  antaya mata ba
  "Babba*b....ubanki Aunty Bahijja 'yar iska marar mutumci uwarki ce ba ta yi miki tarbiyya ba ke har kin isa ki zo har cikin gidan ubana sannan ki zagi Iyayena, na zuba miki ido.
   Da mugun mamaki Hajja ta miƙe tsaye domin su dukkan su ba su yi tsammani fitar waɗannan manya-manyan zagi daga bakina ba, Hajja ta shiga tafa hannuwa tana salati. Yayin da A'isha Shattima tai sauri riƙo ni domin har na tunƙare inda Aunty Bahijja take.
   "Ni ki ka zaga Jeeddah?"
Aunty Bahijja ta faɗa tana nuna ƙirjinta da yatsa.
"Na zage ki kin ci kutumar *b....ubanki 'yar iska banza baƙar matsiyaci, munafuka algunguma, baƙar almura wacce bata gadi arziki ba. Maza ki fice min daga gida don ba na ɗan uwanki bane kuma daga yau kada na sake gani shegun ƙafafuwan ki sun tako cikin gidanan.
   Na ƙarasa magana ina huci.
      "Tabbas kin zage ni Jeeddah ta uwa da uba amma inaso ki rubuta ki ajiye ba ki zagi banza ba. Don wallahi-tallahi sai na mayar miki da martani da sai kin yi kuka da hawayenki.
  "Haba Aunty Bahijja miyasa ki ke yi haka ne Dan ALLAH? Ni fa na kawo ku gidanan ne domin neman maslaha sai gashi kin buge da zagin matar gida wallahi Aunty ki gyara halinki domin banga abinda baiwar ALLAH nan ta tare miki ba..
   "Ke rufe mana baki marar zuciya wacce bata kishin kanta, kina jin yadda take zagina ni da mahaifinku da ke kwance a kabari, don tsabagen lalacewa shi ne kike goyon bayanta. To daɗi abin uwa da uban da ya haifi Bahijja shi ya haife ki sakarya kawai.
Hajja ta faɗa tana gallawa A'isha harara.
Ni ma cikin tsanani fushi na ce da Aunty Bahijja
  "Idan ba ki mayar min da martani ba Aunty Bahijja ALLAH ya tsine miki albarka.
Hayaniyar mu ce ta fito da Bilal daga wanka ko kaya bai tsaya saka wa ba ya fito ɗaure da towel, dama yana bari dining room bedroom ya wuce ya yi wanka tun yana cikin bathroom yake jin kamar sauti faɗa ashe kuwa kunnuwanshi gaskiya suka jiyo masa, ya yi tsaye turus! Tsanani mamaki da tsoron ALLAH suka lulluɓe shi sai kallonmu yake yi. Hajja tana zagina Aunty Bahijja tana tayata ba irin kalar zagi da ba su yi min ba. Yayin da ni kuma nake mayar wa da Aunty Bahijja martani da nawa kalolin zagi, don ba zan iya zagin Hajja ba ko ba komai har yanzu da igiyar aure ɗan ta akaina tana da raguwar darajar da ba zan iya zagin ta ba. Sai dai a madadin ta na zagi 'yarta kuma dole ta ji zafi.
   "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Hasbunallahu wal-imal wakil! Na shiga uku ni Bilal me nake shiri gani haka?"
Bilal Shattima ya faɗa cikin kaɗuwa.
   "Gara ka da ka fito Bilal taho ka ji da kunnuwanka yadda matarka take zuba min ruwan zagi yau ba kalar zagi da ba ta yi min ba ni da Bahijja.
Hajja ta ƙarashe magana tare da rushewa da kuka.
    "Wallahi Bilal idan ba ka ɗauki mataki akan zagin da matarka ta yi mana ba to ka sani ni zan ɗauka ko ba yau ba.
   Cewar Aunty Bahijja tana maida numfashi.
Nima Ina huci na ce "Duk tsiyar ki bai wuce ki ce ya sake ni ba to nima a shirye nake da ya sake ni ɗin haka kawai zan zuba ido a zo har cikin gidana a zagi iyayena....
   "Jeeddah ya isa haka wuce ki shiga bedroom.
Bilal ya faɗa cikin ɗaure fuska, har na buɗe baki zan yi magana A'isha Shattima tai sauri rufe min baki ta ja ni da ƙarfi tsiya ta shigar dani bedroom.
Bilal Shattima ya kalle gun da Hajja take tsaye tana sharar hawaye da gefen hijab ɗinta, ranshi a matuƙar ɓace ya ce "Haba Hajja! Haba Hajja! Wannan wane iri abu ne Miyasa za ki biye wa Aunty Bahijja bayan kin daɗe da sani kanwarta da Jeeddah bata gamu ba?"
Bai jira ta bashi amsa ba ya ci-gaba da faɗin "Gaskiya ban ji daɗi wannan zuwan naku ba. Hajja, Aunty Bahijja ku tuna da irin girman laifi da na yi wa Jeeddah amma ta haƙura ta zauna da ni shi ne don kawai ku ƙuntata mata ku sake haddasa fitina a tsakanin mu za ku zo da sassafe ku ci mata zarafi, gaskiya ba ku kyauta ba.
   "La'illaha inlallahu Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam! Bilal bakinka ne yake faɗa waɗannan maganganu ko kuwa wani Bilal ne aka musanya min dashi?"
Hajja ta faɗa tana zarar ido.
  "Ni ne Bilal ɗinki Hajja ba musanya aka yi miki ba. Kawai dai inaso ki fahimci irin rashin gaskiyar da ku ka shimfiɗa.
  "Uhmm! Hajja kin gani kou kin ga irin illa da nake nuna miki tuntuni akan aure nan nashi kou? To gashi nan yau kin gani da idonki kin haifawa wata 'yar iska ɗa sai yadda tayi dashi.
   "Ya isa haka Aunty Bahijja wai me Jeeddah tai miki da ki ka tsane ta har haka? Domin iya sanina wani saɓani bai taɓa shiga a tsakaninku ba da zai sa ki dinga nuna mata ƙiyayya irin wannan.
  "Shikenan Bilal tun da ka goyi bayan matarka ni zan tafi ga ka nan ga ta ALLAH ya ƙara muku danƙo soyayya.
Hajja tana gama faɗin haka ta juya a fusace Aunty Bahijja ta biyo ta a baya.
Da sauri ya bi su yana kiran sunayensu ba wacce ta tsaye balle ta saurare haƙuri da yake basu, kasancewar towel ne a jikinshi yasa ya kasa bin su ya dawo jikinshi a sanyaye, ya shiga ɗakin da Jeeddah take, ina zaune sai rera kuka nake yi yayin da A'isha Shattima ke rarrashina Bilal ya kalleta gami da faɗin "A'isha tashi ki tafi gida.
Ba tare da ta ce komai ba ta miƙe tare da ficewa, ya  yi tsaye tare da folding hannunshi yana kallona, tsawon lokaci ya ɗauka a tsaye yana ta faman kallona bai yi min magana ba. Daga ƙarashe ya nufi closet ya saka jallabiya milk colour, ya fice abinsa.
Ina gani yadda yai banza dani sai na ji wani sabon haushi da takaincinsa  na tashi a fusace na janyo ɗaya daga cikin akwatuna na shiga loda tufafina a cikin ina yi ina rera kuka, har ga ALLAH ina ji a jikina yau ne ƙarshen zamana da Bilal Shattima...
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*AHAYYE NANAYE SHIN KINADA LABARIN SHAHARARRIYAR MARUBUCIYAR NAN MAI NISHADANTAR DAKU TARE DA FADAKAR DAKU WATO AMINA SLIMZY BAA KAN RUBUTU KAD'AI TA TSAYA BA?KO KUNSAN CEWA IN MATSALARKI NIIMAH CE KO INFECTION KO MALLAKA TA HANYAR ZAFAFAN MAGUNGUNAN MATA ITADIN GWANA CE?*

*HMMM KAR IN CIKAKU DA LABARI MAZA KI HANZARTA KI NEMI SLIMZY DAN BIYAN BUKATARKI TARE DA SAMUN MAI GIDANKI A TAFI HANNUNKI,DIK KARANCIN NIIMARKI DIK RASHIN DAD'INKI INSHA ALLAH KIKAJE WAJEN SLIMZY DA BUKATARKI TO MATSALARKI TAZO KARSHE.....*

*KAD'AN DAGA CIKIN SAHIHAN MAGUNGUNANTA WADANDA TAFIYAYYU NE DAGA KASAT NIJAR SUNE KAMAR HAKA:*
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*ZUMAR RAKUMI DA AKALA*
*GARIN DAKA B'ATA GABAN KISHIYA*
*TSUMI DAN AGADAZ*
*MAN LALLE INGANTACCE*

*DA SAURANSU,MAZA HANZARTA KI NEMETA A WANAN LAYIN DAN SAMUN CIKAKKEN BAYANI DAGA GARETA TANA TURA KAYA KO INA A FAD'IN NIGERIA*

07042277401

*HAZIK'A KUMA FASIHIHAR MARUBUCIYARKU SLIMZY*✍🏻

037...

Akan Centre table da ke girke a tsakiyar parlourna na nufa na ɗauki kyautar da na tanadarwa da Ya Haidar, da farko ban yi niyyar bashi kyautar komai ba. Sai da Khairat ta kira ni a waya take tambayana wacce kyuta zan bashi nace babu sai take faɗa min ita da Aunty Farida kowacce su ta tanadi iri kyautar da za ta bashi dole nima naje da tawa kyauta ba don raina ya so ba na fita zuwa neman abinda zan bashi a matsayin tawa kyauta da ke nuna nayi farin ciki da dawowarshi.
Madaidaci kwali ne anyi wrapping ɗinshi na ɗauka kana na fito tare da rufe ƙofa na nufi gun motar Bilal wacce a yanzu ta zama mallakina. Kasancewar motar automatic ce shiyasa ban daɗe ina koyo ba. Kaitsaye gidan Mommy Turai na nufa maigadi yana tsaye wangale da Gate sakamakon mutane da ke ta shigowa da ababen hawan su, nima na bi ayari na nemi wuri nayi parking na fito a natse nayi using remote ɗin da ke saƙale a jikin key motar nayi lock ɗin ƙofufi, na rungume gift ɗin a ƙirjina yayin da ɗayan hannuna ke riƙe da handbag. Sosai aka ƙawata compound ɗin gidan da decoration table aka ajiye an zagaye shi da four chairs jama'a na zaune ana serving ɗinsu da haɗaɗɗun dishes, yayin da slow music ke tashi a hankali.
Tun da na nufo wuri nake ji matsanancin faɗuwar gaba, wanda na rasa na menene.
Inda na hango su Aunty Farida a zaune na nufa ina saki murmushi ba don ina jin daɗin yi sa ba.
  "Halau dai kin zo a makare.
Khairat ta faɗa sa'ili da na kai zaune taɓe baki nayi gami da faɗin "Ki ma godewa ALLAH da na zo don wallahi ban yi niyyar zuwa wannan dinner ba.
   "Cab! Ai duk wanda bai zo dinner ɗinan ba sai Mommy ta saka shi a blacklist.
Aunty Farida ta faɗa tana 'yar dariya daga nan suka ci-gaba da fira duk akan Ya Haidar yayin da na tsinci kaina da kasa furta uffan sai saurare su nake yi.
Mc ya shiga sanarwar fitowar Ya Haidar, tun Kafin ya ƙaraso cikin filin jama'a suka miƙe tsaye suna masa tafi da sowa, sai da Khairat ta zungure ƙafata da ƙafarta tai min signal sannan na yunƙura na tashi tsaye a kasalance nake tafa hannuwana, a hankali idanuwana suka sauka akan kyakkyawar fuskarshi ma'abociya kwarjini da cikar kamala Ya Haidar ya ƙara kyau na ban mamaki fiyye da yanda nasanshi a baya skin ɗinshi kamar ka taɓa jini ya fito, bashi da bambanci da balarabe ƙasar Labanon ban taɓa gani mutumin da kyau yai masa yawa irin Ya Haidar ba, sanda ya tunƙaro cikin taro sai ji ka ke yi jama'a na yaba matsanancin kyawon shi musamman 'yan mata da na ga sun fara tururuwa daukar hoto dashi. Ban san miyasa na ji wani irin mugun ɓaci rai yai min zuwan bazata ba. Duk sai na ji na tsani zama wuri ji nake yi tamkar ina zaune akan ƙaya. Muryar Aunty Farida na tsikaya tana faɗin "ku tashi mu je mu yi hoto da Haidar.
Khairat da matar Ya Kabeer suka yi sauri tashi yayin da ni kam nayi Kamar ban ji abinda Aunty Farida ta faɗa ba sai da ta sake maimaita maganarta sannan na ɗago na kalleta ina ya mutsa fuska na ce "Ku je kawai Aunty bana jin daɗi headache ke damuna.
  "ALLAH ya sauƙawa amma ya kamata idan kin koma gida ki nemi koda Panadol ne ki sha nasanki da rashin so magani kin gwammace ki ta zama da ciwo, ku zo mu tafi.
Aunty Farida ta ƙarashe magana tare da kama hannu Khairat da sauri na ɗauki kyautar da na kawo masa na danƙa wa Khairat ina faɗin "Khairat Dan ALLAH ki ba Ya Haidar ki isar min da sakon taya murna kafin headache ɗin ya lafa na zo da kaina.
Khairat bata ce komai ba ta karɓi gift din na bi su da kallo har suka isa wuri Ya Haidar ina kallonsu, yana ganinsu ya ƙara faɗaɗɗa murmushin sa ba ƙaramin ƙara masa kyau murmushi ya yi ba. Daga nesa nake kallonshi amma sai naji ba zan iya jure ci-gaba da kallo nashi ba, a dalili wani iri bugawa da ƙirjina ke yi sai kawai na kauda fuska ta na ɗan wani lokaci kafin nasake ɗagowa na kalle su sai  hotuna suke ɗauka idan ci-gaba da kallonsu na tabbata zuciyata tarwatse wa za tayi sai kawai na miƙe na bar wuri na nufi entrance ɗin gidan.
Na kutse cikin parlour Mommy Turai na tarar da wasu daga cikin ƙawaye ta suna cin abinci, da kyar na buɗe bakina nai musu sallama, na wuce cikin ɗaya daga cikin bedrooms ɗin Mommy ina zuwa na faɗa kan gado rabin jikina yana bisa gadon yayin da na sauko da ƙafafuwana ƙasa.
Bayan su Aunty Farida sun gama ɗaukar hoto kowacce ta miƙa shi kyautar ta tare da taya shi murna, daga bisani Khairat ta miƙa mishi kyautar Jeeddah ta kai bakinta daff da kunnenshi ta raɗa masa "Wannan daga Jeeddah ta ce a madadin ta na miƙa mata saƙon gaisuwa.
Ta ƙarashe magana tana blushing, shi ma murmushi ya yi ya ƙara dafe kyautar kamar yadda tai mishi raɗa shi ma haka yai mata "Kina nufi kyauta da gaisuwa kaɗai za ta aiko min ita ba za ta zo ba?"
"Tare muke da ita kanta ke ciwo ga ma ta can zaune.
Ta ƙarashe magana tare da pointing gun da suka baro Jeeddah zaune, Haidar Ka'oje ya bi yatsa ta da kallo, sai da Jeeddah bata wuri da sauri Khairat ta ce "Ba ta wuri watakila headache ɗin ya matsa mata ta shiga cikin gida bara na dubo ta.
Da sauri Khairat ta nufi cikin gida, ta duba parlour bata ganta ba sai kawai ta shiga nemanta a bedrooms ƙarar buɗe ƙofa yasa ni buɗe idanuwana, na kalle Khairat da ta nufo ni da sauri tana faɗin "Jeeddah ba dai ciwo kan bane?"
Sai da na ya mutsa fuska kafin na ce "shi ne Khairat gida zan tafi.
Da taimakon Khairat na miƙe tsaye muna fitowa muka ci karo da Mommy Turai na tayata murna kana nayi sallama da ita a bisa uzuri da na kawo mata, tai min fatan samun sauƙi. Khairat ta kira Aunty Farida a waya ta sanar mata na wuce gida, tun kafin na ƙarasa waje da nayi parking motata na hango Ya Haidar shi da Zarah 'yar abokin Daddynshi ce sun jinginar da jikinsu ga motata.
Tun ba yau ba nasan irin matsananciya ƙaunar da Zarah take masa, sai surutu take zuba mishi yayin da shi kuma sai zabga murmushi yake yi sosai naji ɓaci raina ya ƙara linkuwa, kamar daga sama naji Khairat tana faɗin "ashe dawowar nan da Ya Haidar ya yi aure zai yi ga ma shi can tare da amarya tashi wallahi sun yi matuƙar dacewa da juna.
Kamar saukar aradu haka naji maganar Khairat ta saukar min a kunne, har wani dishi-dishi nake gani hakan yasa naci wani ɗan uban tuntube saura kiriss! Na kife ƙasa Khairat tai sauri taro ni "Sannu Jeeddah halan  jiri ki ke ji?"
Na ƙasa amsa mata sai motsa laɓɓana nake yi kamar zai yi magana amma kalma ɗaya ta ƙasa fitowa daga bakina.
  "Anya kuwa za ki iya driving ko za ki bar motar ki anan na maida ki gida?"
Shiru nayi na ɗan lokaci kafin na amsa mata da cewa "Ki bar shi kawai zan lallaɓa da kaina.
"Kin tabbata?
Na gyaɗa kai Kamar an ce da Haidar Ka'oje ya ɗago idanuwanshi sai kawai yai tozali da Jeeddah, kasa janye idanuwanshi ya yi daga kanta gaba ɗaya ya tattara dukkan natsuwa da hankalinsa akanta, a hankali Zarah ta bi gun da yake kallo, tana gani Jeeddah ta tunƙaro su ta haɗe fuska domin bata manta da wacece Jeeddah da matsayinta a wurin Haidar Ka'oje. Bata kuma manta da artabo da suka yi ba don har dambe sai da suka yi ita da Jeeddah duk akan Haidar. Tun daga lokaci gaba mai tsanani ta shiga tsakaninsu ko sau dubu suka haɗu ba za su yi wa junansu magana ba.
Muna isowa nayi kamar ban gane su ba na raɓa gefen su na buɗe murfin mota na shiga, Khairat ce ta tsaya iya yinta ina ji lokaci da take faɗin "Iyeee Love birds! Ashe nan ku ka ɓoya abinku kuna zuba soyayya to ALLAH ya toni asirinku na kama ku.
Ta ƙarasa magana tana dariya su ma darawa suka yi haushinsu haɗe da takaici ya turnuƙe ni kafin su kai ga bata amsa nayi reverse da ƙarfi dama Ya Haidar hankalinsa yana kaina ya ga abinda nake shirin yi cikin zafin nama ya janye Zarah yayin da Khairat ta daka tsalle ta koma gefe, da ƙarfi na ƙarasa reverse da mugun speed na nufi gate, suka bini da kallon mamaki.
Haidar ya dawo da ganinshi akan Khairat kafin ya ce "ƙanwa yaushe Jeeddah ta zare har haka ai ni na zaci aure ya gyara ta tayi hankali?"
Dariya Khairat tasa, gami da cewa "Ta nan yadda ka san ta ba abinda ya sauya.
  "Uhmm! Ai kuwa ga alama nan na gani.
Haidar Ka'oje ya faɗa yana murmushi yayin da Zarah ta ja guntun tsaki gami da faɗin "Ya kamata a kaita asibitin kwararru a duba ƙwaƙwalwarta don gaskiya bata da cikakken hankali.
Kallon sama da ƙasa Khairat tai mata kafin ta ce "Ni kam 'yar uwata lafitarta qalau duk mutum mai hankali ba zai kalleta ya danganta ta da rashin hankali. Karki ji Ya Haidar ya faɗa ki zaci abinda ya faɗa gaskiya ne abokin wasanta ne.
  "Uhm!
Zarah ta faɗa a hasale murmushi Khairat tayi tare da maƙe ƙafaɗa alamar wannan ruwanki zuwan SY Barade wuri ya kawo ƙarshen taƙaddama tasu yayin da Haidar Ka'oje ya yi kamar baya jin su sai faman danar wayarsa ya ke yi.
Da taimakon Ubangiji ta iso gida lafiya rai ɓace ta wuce bedroom ko kayan jikinta bata cire ba ta bi lafiyar gado, sosai nake mamakin kaina domin wannan yanayi tun ina 'yar ƙanƙanu nake ji makamancinsa akan Ya Haidar kuma har yau na kasa tantance dalili da yasa nake ji hakan.
Bilal Shattima yana bisa hanyar zuwa gida kiran Nusaiba ya shigo wayarshi yai biris da ita ya rasa dalili da yasa Nusaiba take so taƙura wa rayuwarshi tana so ta haddasa masa fitina tsakaninsa da Jeeddah.
Nusaiba tayi aure shekaru haɗu da suka gabata sai dai bata haihuwa ba duka bai fi watani shidda da aure nata ya mutu, tun lokaci da ta kammala iddarta ta shiga bibbiyar Bilal Shattima gani yadda ya yi kuɗi yasa ta fara kai masa hari yayin da Aunty Bahijja ke ƙara ƙarfafa mata guiwa, ta bi ta takurawa Bilal ta hana shi sakatt saboda tsananin nacinta tun baya kulata har ya dawo yana amsa wayarta, shi ne yau ya je gidansu duka bai wuce 15 minutes da rabuwar su ba shi ne don naci za ta sake kiranshi gudun kada ta tsokana masa masifa da dare nan ya yi switch off ɗin wayarsa.
Jin an turo ƙofa yasa ni buɗe idanuwana Bilal ne ya shigo bakinsa ɗauke da sallama na amsa mishi can ƙasan maƙoshi kusa da ƙafafuwana ya zauna yana faɗin "Love ashe kin dawo ai ni na zaci sai na bi bayanki?
Na tashi zaune tare da ya mutsa fuska cikin yana yi marar daɗi na ce dashi "Headache ya taƙura ni shi ne na dawo tun ba a kammala ba.
  Cike da kulawa ya hayo gado ya jawo ni cikin jikinshi yana tattaɓa gefen wuyana "Sannu Love amma ban ji jikinki da zafi ba kodai stress ne yai miki yawa? Tashi ki yi wanka da hot water za ki ji karfe jikinki bara na je kitchen na haɗa miki coffee.
  Ƙara yatsine fuska nayi kafin na ce "Me ya haɗa Headache da zafi jiki?" Ba wani stress da yake damuna.
Na ƙarashe magana ina turo baki murmushi kawai ya yi tare da miƙewa ya shiga bathroom ya haɗa min ruwan wanka sai da ya ga na shiga wanka sannan ya wuce kitchen koda na fito, ya rage kayan jikinshi daga shi sai boxer briefs ya ɗora plate ɗin kilishi akan stool yana ci, ina tozali da tumbin sa ya yi wargajeje na ji wani shegen haushin sa. A hasale na ce "Wai kai Love wane irin mutum ne da baya kula da fitness maintenance ɗinshi?" Dallah kalli yadda ka dawo wani narkeke da kai kullum weight ɗinka ƙara hauhawa yake yi kai kenan cikin cin nama sai kace wanda kura ta yaye mtsss...na gaji da wannan mummunar ɗabi'a taka.
Na ƙarashe magana tare da ɗauke plate din kilishin na ɗamƙwarar akan mirror, har na shirya cikin sleeping dress ina balbala faɗa ina cikin fesa turare ya taso ya kama kafanɗuna ya juyo dani muna facing juna cikin tausassa murya ya ce "Love waya ɓata miki rai domin da gani yadda kike faɗa nan akwai wanda ya yi miki wani abu na ɓaci rai?""
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*AHAYYE NANAYE SHIN KINADA LABARIN SHAHARARRIYAR MARUBUCIYAR NAN MAI NISHAƊANTAR DAKU TARE DA FAƊAKAR DAKU WATO AMINA SLIMZY BA A KAN RUBUTU KAƊAI TA TSAYA BA, KO KUNSAN CEWA IN MATSALARKI NI'IMAH CE KO INFECTION KO MALLAKA TA HANYAR ZAFAFAN MAGUNGUNAN MATA ITA ƊIN GWANA CE?*

*HMMM KAR IN CIKA KU DA LABARI MAZA KI HANZARTA KI NEMI SLIMZY DAN BIYAN BUKATARKI TARE DA SAMUN MAI GIDANKI A TAFI HANNUNKI,DUK KARANCIN NI'IMARKI DUK RASHIN DAƊINKI INSHA ALLAH KI KA JE WAJEN SLIMZY DA BUKATARKI TO MATSALARKI TAZO ƘARSHE.....*

*KAƊAN DAGA CIKIN SAHIHAN MAGUNGUNANTA WADANDA LAFIYAYYU NE DAGA KASAR NIJAR SUNE KAMAR HAKA:*
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻

*ZUMAR RAƘUMI DA AKALA*
*GARIN DAKA ƁATA GABAN KISHIYA*
*TSUMI ƊAN AGADAZ*
*MAN LALLE INGANTACCE*

*DA SAURANSU,MAZA HANZARTA KI NEMETA A WANAN LAYIN DAN SAMUN CIKAKKEN BAYANI DAGA GARETA TANA TURA KAYA KO INA A FAƊ'IN NIGERIA*

07042277401

*HAZIƘA KUMA FASIHIHAR MARUBUCIYARKU SLIMZY*✍🏻

036..

Ina janye da akwatina na fito parlour Bilal Shattima dake zaune yana magana a waya ya waigo ya kalle ni gani na da ya yi janye da ƙaton akwati yasa shi katse wayar ya nufo wurina da sauri yana zuwa ya riƙe handle ɗin akwati yana min kallon tuhuma.
   "Ka sake min akwatina gidanmu zan tafi kada ka ɓata min lokaci ko ka nemi hanani na gaji da wulaƙanci da ake min akanka.
Na faɗa cikin muryar kuka sai kawai naga ya girgiza kai da ƙarfi ya cire hannuna daga jikin akwatin ya mayar dashi ɗaki, da sauri na bi shi a baya ina faɗin "Bilal ka dawo min da akwatina wallahi na gaji da wannan aure haƙuri na ya ƙare gara mu haƙura da juna iyaso su aura ma wacce take da tarbiyya.
   Bai kula ni ba sai da ya mayar da tufafina kaff cikin closet kana ya riƙo hannuna ya zaunar dani a gefen gado cikin tattausar murya ya ce "Bakina bai zai gaji da furta miki kalmar ban haƙuri ba nasan abinda mahaifiyata da 'yar uwarta suka yi miki ba su kyauta ba. Haƙiƙani gaskiya ban ji daɗi ba na kuma nuna musu hakan. Jeeddah ina sonki ina miki son da fatar bakina ba za ta iya misalta shi ba. Jeeddah ina so mu samu zaman lafiya a tsakaninmu mu yi rayuwar aurenmu cikin fari ciki kamar yadda sauran ma'aurata suke yi a gidanjen su. Sai dai kashhh! Domin a duk lokaci da na tsara mana hakan sai wani mummunan abu ya wargaza mana hakan.
Ina mai ƙara ba ki haƙuri  akan abubuwa marasa daɗi da ki ke ta fuskanta ta dalilina.
Bilal Shattima bai yi ƙasa da guiwa ba haka ya ci-gaba da rarrashinta da bata haƙuri, cikin daɗɗaɗa kalamai yini ranar gaba ɗaya ba inda ya je yana manne da ita yana nuna mata sabon salon so. Har sai da ta saki jikinta tamkar wani abu marar daɗi bai taɓa shiga a tsakaninsu ba. Zazzafar soyayya suke nunawa junansu tamkar dai farkon aurensu, ita kanta Jeeddah da ta zauna tai nazari sai ta fahimci irin son da Bilal Shattima yake mata kawai dai maƙiya da mahassada ne suka yi musu rudugu a zamantakewar aurensu, shiyasa suka kasa samun zaman lafiya. Tun lokaci da ta fahimci mijinta yana mugun sonta danginsa ne kawai suka hana musu jin daɗi, don haka ta sha alwashi ba wanda ya isa ya sake shiga tsakaninta dashi.
  *BAYAN SATI ƊAYA*
A wani yammaci Jeeddah tana zaune a parlour sai ga Ya Kabeer ya zo, bayan ya zauna ta kawo mishi ruwa da drinks da suka gaisa ya miƙa mata wata ƙaramar shopping bag ya ce "Gashi saƙo ne daga Babanki, ai ke yanzu Jeeddo kin zama 'yar gata Baba gwal ɗin ki da mugun mijinki ya salwantar miki ita ce Baba ya yi miki replacement da wata karɓi ki gani wannan ta fi taki ta farko saura kuma ki sake sakaci, azzalumi mijinki ya sace miki.
Ya ƙarashe magana tare da miƙo min shopping bag duk naji zafin maganar shi ta ƙarshe, amma hakan bai hanani nuna farin cikina a fili ba. Cike da zumuɗi na ciro jewelry box ɗin na buɗe idanuwana suka yi tozali da ƙatuwar sarƙar gwal da ta fi tawa ta farko kyau da girma don wannan hadda zobe da two bangles take da, tsabar farin ciki har bansan lokaci da na taso daga wajen zamana na rungume Ya Kabeer ina ihun murna dariya Ya Kabeer ya yi tare da dungure min goshi gami da faɗin "ke cikani banaso shashanci bansan sai yaushe za ki yi wayau ba.
Ina dariya hawayen farin ciki na sauka akan kumatuna, lokaci da Ya Kabeer ya danƙa min receipt ɗin necklace ɗin idanuwana suka kakkafe na kasa magana, Ya Kabeer ya sake dungure min goshi a karo na biyu yana faɗin "Miye na zaro idanuwa? Baba da kanshi ya siyo miki sarƙar nan ni kaina da na ganta na kuma duba receipt ɗinta sai da na shiga yana yi nan da ki ka shiga har ban san lokaci da na furta price ɗin sarƙar a fili ba "2.5 million. Gani yanayi da na shiga yasa Baba ya dafa ƙafaɗata ya ce dani "Kabeer na siyawa Jeeddah wannan gwal ɗin ne domin na kwantar mata da hankali banaso ko kaɗan ta silar gwal ace aurenta ya sami matsala na tsani naji an ce aure ya mutu, shiyasa tun farko na bi ra'ayinta na barta ta aure Bilal. Duk abinda na mallaka na daga dukiya naku ne saboda haka kada ka yi mamaki don na siya mata wannan gwal ɗin farin cikinku kawai nake so.
  "Lokaci da Baba ya ƙarashe magana sosai nai masa addu'ar gamawa da duniya lafiya, saboda a wannan zamani ba kowanne uba ne mai kyakkyawan hali irin nasa ba, saboda haka ina rokonki da ki ci-gaba da haƙuri da sakarai mijinan naki mai abin haushi.
Turo baki nayi ina faɗin "uhmm! ALLAH Ya Kabeer yanzu Love ya canza ba ka ga yadda yake nuna min kulawa dama can asiri kishiyar Babarsa tai mana, ta shiga tsakaninmu ta hana mana zaman lafiya yanzu kuma da asiri ya ƙarye....
   "Ke banaso ƙaryar banza da wofi wannan mijin naki ko babu aikin asiri sauna ne na ƙarshe kada ki sake ki ce za ki yi masa kwaskwarima a gabana.
Sani nayi ko zan kai gobe ina gyara Bilal a gun Ya Kabeer ba zai taɓa gyaruwa ba, ya ri ga da ya ɓata rawarsa da tsalle.
Da Ya Kabeer zai wuce sai da ya bani kyautar kuɗi Naira dubu ashirin, har bakin gate na raka shi. Da Love ya dawo na nuna masa gold ɗin sosai ya tayani murna har ya kira Baba a waya yai masa godiya. Washegari na je gida na yi wa Baba godiya, bayan Baba ya fita Mama tasani a gaba ta dinga yi min gargaɗi akan gold ɗin har cewa tayi na kai bank ajiya ko na kai ma Aunty Farida na amsa mata da to don a zauna lafiya.
**** *** *****
Hajja tana zaune a tsakar gida tana yanka kuɓewa yayin da Mufeeda ke tankade gari tuwo, kamar daga sama suka ji sallamar Ya Faruk, wata irin zubura Hajja tayi har tana ɓararda robar da take yanka kuɓewa a ciki. Faruk yana zuwa ya zube gwuiwayinsa ƙasa ya fashe da matsanancin kuka, cikin shasshekar kuka yake faɗin "Hajja ki dubi girman ALLAH da Manzonsa ki yafe min wallahi bansan abinda ya hau kaina ba na wofitar daku. Yanzu na gane kuskurena IN-SHA-ALLAH hakan ba za ta sake faruwa ba.
Duk maganar da Ya Faruk yake yi Hajja tana tsaye a gabanshi sai faman kallonshi take yi, kafin ta rushe da kuka ta kama kafanɗunshi yana miƙewa tsaye ya rungume ta. A takaice ta  bashi labari asirin da  Hajiya Bintu tai masa, ai kuwa ya harzuƙa ya juya a mugun fusace ya shiga ɓangare Hajiya Bintu ya ƙare mata zagi ta uwa da uba ba don da Hajja ta riƙe shi da tuni ya rufe Hajiya Bintu da duka. Dama duk a cikin 'ya'ya Hajja shi da Bahijja su ne masu baƙar zuciya da mugun hali, Bayan komai ya lafa tuni Hajja ta kira su Bilal ranar kwana farin ciki suka yi a washegari Ya Faruk ya kira masu gini aka ja katanga tsakanin Hajja da Hajiya Bintu yasa aka fitar mata da nata Gate daban. Hakan da ya yi ba ƙaramin ƙara fusata Hajiya Bintu ya yi ba, ta kuma sha alwashi wasan yanzu aka fara.
Dawowar Ya Faruk ya canza rayuwar Hajja da 'ya'yanta tuni Ya Faruk ya miƙa ragamar kasuwancin shi a hannu Bilal duniya ta dawowa Bilal Shattima da 'yan uwanshi sabuwa.
   *BAYAN SHEKARA BIYAR*
Bayan waɗannan shekaru abubuwa da dama sun faru wasu masu daɗi wasu kuma akasin hakan, daga ciki masu daɗi akwai ƙofar budi da ta buɗewa Bilal Shattima sosai yake samun kuɗi na ban mamaki, domin yanzu har kamfanin siyar da motoci na zamani suka buɗe a garin Sokoto ga kuma shagunan siyar da cement da manyan plaza duk mallakin Faruk Shattima yayin da Bilal ke kula dasu ta ko ina kuɗi ke zuwa masa. Idan ku ka ga Bilal a yanzu ba lallai bane farat ɗaya ku sheda shi ba. Ya yi 'yar uban ƙiba ya aje wani ƙaton tumbi kamar mai ciki wata shidda, naman fuskarsa ya cicciko kumatun nan nasa suka cika kamar an hura masa iska yayin da hancin shi ya ƙara buɗewa, dama kusan gogan naku da son jin daɗi, kullum cikin yagar kaji yake ba ranar da za ta zo ta wuce bai ci kaza ba. Jeeddah har mamakinsa take yi yadda baya gajiya da cin nama, sai kace ya haɗe jinsin da kuraye a duk ƙarshen wata sai an gasa masa ƙaton raggo. Ba don yana ɗan gaye ba yana buga wanka da very expensive clothes da wallahi ba zai yi kyau gani ba saboda yadda muninsa ya ƙara bayyana sutura ce ke taimako sa wajen adana muninsa da abin ba zai yi kyau ba.
Cikin hukunci Ubangiji Jeeddah ta kammala karatun ta Allah ya taimake ta da result ɗinta ya fito, Ya Kabeer yai mata tsaye ya shiga ya fita ta sami aiki a Shehu Shagari College of education a matsayin staff member. Salary ta ya ƙara kauri musamman suka haɗa jari ita da 'yan uwanta suna kasuwanci a online na siyar da tufafin yara da manya atamfofi da shaduddi haɗe da laces a gun Baba suke sari ALLAH yasa musu albarka a ciki sai gashi har boutique suka buɗe. Shiyasa Jeeddah sam bata dogara da abin hannu Bilal ba duk da yana ƙoƙari wajen kyautata mata, domin bai manta da halaccin da tai masa a baya ba. Hatta da motar hawa da ya siya ita ya bar ma shi kuma sai da ya hau motocin su na sayarwa hakan ba ƙaramin ciwa Hajja da Aunty Bahijja tuwo a kwarya yake yi ba. Shiyasa kullum cikin nuna masa suke yi da ya ƙara aure domin ta haka ne kawai suke gani za su iya ƙuntata wa rayuwar Jeeddah amma sai ya yi biris dasu. Tuni Bilal Shattima ya fara yi musu gini na 'yan ƙarya dole nace na 'yan ƙarya saboda upstairs ne, duk wanda ya ga gini da yake yi sai ya ce bai kai matsayin da zai gina gida kamarsa ba.
  Da sauri na fito daga bedroom cikin shirin fita domin yau ne Mommy Turai ta shirya kwarya-kwaryar liyafar cin abinci dare a dalilin dawowar Ya Haidar gida Nigeria bayan ya share tsawon shekaru bakwai a Canada.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*Ya ALLAH ka jiƙan Abba Bello ALLAH ka sada shi da Rahamar ka Ya ALLAH ka haskaka kabarin sa Ya ALLAH ka albarkaci 'ya'ya da ya bari ka ba wa 'yan uwanshi da masoyansa dake faɗin duniya haƙuri rashinsa ALLAH ka sanya mana dangana ga Zuƙatan mu. Ina daɗa miƙa saƙon ta'aziyya ga ɗaukaci masoya magoya bayan Abba Muhammad Bello tabbas mu yi rashin ɗan takara nagari. Oh! ALLAH forgive him, have mercy on him grant him with Aljannatul Firdausi we loves you Abba but ALLAH loves you more We’re still proud of You you’re gone but your good heart and kindness towards other peoples still remains in their hearts.*😭😭😭😭😭

_Dan ALLAH ina barar addu'a zuwa ga Abba Muhammad Bello ga ma'abota karanta wannan littafi_

038...

Banza tayi dashi gami da ture hannuwanshi daga kafanɗunta. Ta wuce ta gefen shi ta nufi kan gado ta kwanta duk da haka Bilal Shattima bai daddara ba ya sake biyo ta ya kwanta a bayanta tare da rungume ta. Cikin sanyi murya ya ce "Love please banaso fushinki ki faɗa min abinda ke damunki sai ki yi ta cin rai kina fushi ko ni ne na ɓata miki rai?
Rai ɓace ta tashi zaune tana ya motsa fuska "I'm fine ba abinda ke damuna banaso yawan tambaya Please ka kyaleni nai bsccina.
Yanda ya ga tana amsa mishi magana kamar bata so sai kawai ya yi wa kanshi ƙiyamullaili ta hanyar furta
   "Shikenan ki kwanta ki yi baccinki.
"Uhmm! Ta faɗa tare da sake bin lafiyar gado.
Ya ɗauki dogon lokaci a zaune yana kallonta kafin ya tashi ya shiga bathroom.
Washegari wasai Jeeddah ta tashi ba kamar yadda ta dinga cin rai a daren jiya ba. Ta kammala ayyukan ta na yau da kullum kana tai shirin tafiya office.
Bilal Shattima ya fito daga bathroom ɗaure da towel ya kalle Jeeddah da ke tsaye a gaban mirror tana rolling veil mahadin brown Eypyt Abaya da ke sanye a jikinta ta cikin mirror ta kalle shi gami da faɗin "Love breakfast ɗinka yana kan dining ni zan wuce office banaso nayi latti.
  Ta ƙarashe magana gami da ɗaukar handbag ɗinta.
  "Idan kin dawo daga office ki biya gida ki duba jikin Hajja jiya hawan jininta ya tashi.
   "Subhanalillah! ALLAH ya bata lafiya. in-sha-Allah idan na taso zan wuce ta can na duba ta.
   "Shikenan ALLAH ya tsare.
Bilal ya faɗa tare da ci-gaba da goge jikinshi.
Daga haka ta fice abinta.
Da Jeeddah ta taso daga office sai da ta tsaya akan hanya ta siyawa Hajja fruits mai kyau sai da aka cika babbar leda baƙa kana ta nufo gidan. Wuri ta samu a Kofar gidan tai parking kana fito da ledar da ke ɗauke da fruits ɗin ta shiga gidan tun a tsakar gida take kwaɗa sallama har ta iso ƙofar parlour Hajja ba wanda ya amsa mata sai kace wacce ta shigo gidan kurame alhali tana jin surutun mutane yana tashi a cikin parlour. Ta daɗe tsaye a bakin ƙofa sakamakon ba a bata izinin shiga ba can sai ga Mufeeda ɗiyar Aunty Bahijja ta leƙo ta gaidata ta amsa mata gami da miƙa mata ledar hannunta. Mufeeda ta koma ciki kana Jeeddah ta biyo ta a baya Hajja tana kwance a tsakiyar parlour kan  ƙatuwar katifa. Aunty Bahijja tana a gefenta a zaune. Sake yi sallama Jeeddah tayi tare da durƙusa wa ta gaidata Hajja gami da tambayarta lafiyar jikinta. Can ciki ta amsa mata ta miƙe tare da zaunawa akan kujera batare da ta kalle Aunty Bahijja ba ta gaidata ta amsa mata a wulaƙance.
Dama ban saka ran za su amsa min a mutunce ba domin a yanzu ba wacce suka tsana suke nuna wa zallar ƙiyayya sama dani, tun abin yana damuna har ya zo ya daina saboda nasan dalili da yasa suka tsane ni ɗin.
Mufeeda ta ajiye ledar fruits kusa da katifar Hajja Aunty Bahijja ta daka mata mahaukaciyar tsawa cikin hargowa take faɗin "Ke Mufeeda zo maza ki ɗauke mana wannan shegiyar ledar ki fita da ita waje, banda kuturun wulaƙanci a rasa abin kawo wa Hajja sai lemo da ayaba mtsss! Aikin banza kawai.
Ko kallonta ban yi ba domin kulawa ma yabawa ce sai kawai na fiddo wayana daga handbag na buɗe Data, na shiga WhatsApp direct group ɗinmu na family na shiga a dalili tarin messages ɗin da nagani sai na zaci wani abin kirki ne ake tattaunawa, ashe pictures ɗin da aka ɗauka a wajen dinner ne ake turowa duk wani wanda ya ɗauki pic da Ya Haidar idan har ɗan uwa ne kuma yana cikin group ɗin ya turo. Sai ƙara taya shi murna ake yi sai lokaci na fahimci ba wai iya dawowarshi ake taya shi murna ba hadda sabon kamfaninsa na motoci da zai buɗe nan da two weeks. Har zan fita daga group ɗin sai kuma na fasa na shiga buɗe pics ɗin ɗaya bayan ɗaya sai da na buɗe kusan guda bakwai kafin na ci karo da wanda ya ɓakanta min rai ya haddasa min bugawa zuciya gami da sanya ni takaici shine wanda Ya Haidar ya ɗauka tare da Zarah hannuwansu sarƙe da juna, da sauri na kashe data ɗin na maida wayana jakka. Ina shiri tashi sai ga Nusaiba ta shigo niƙe-niƙe da kaya hannuwanta dukka biyu ɗauke da manya-manyan shopping bags har guda huɗu fuskarta shimfiɗe da fara'a, tana shigo wa ta fara faɗin "Aunty Bahijja albishir ki.
   "Goro.
Cewar Aunty Bahijja tana zuba murmushi kafin na ji abinda za ta sake faɗa nai sauri miƙewa tsaye gami da ɗaukar handbag ɗina na ari murmushin dole na yafawa fuskata ka na ce "Hajja ni zan wuce ALLAH ya ƙara afuwa yasa zakkar jiki ce.
"Amin!
Hajja ta amsa mata a takaice daga haka Jeeddah ta juya har ta kai bakin ƙofar ta tsince muryar Aunty Bahijja tana faɗin "Faɗa min Nusaiba haƙƙarmu ta cimma ruwa ko kuwa da saura? Don da gani wannan farin ciki da 'yan uban kaya nan da ki ka shigo dashi tarkon mu ya kama tsuntsuwa.
Kafin na ji irin amsar da Nusaiba za ta bata har na bankaɗa labulle na fice, wani irin mutuwar jiki nake ji shiyasa na kasa wucewa gidana na wuto gidanmu. Tun kafin na iso ƙofar gidanmu na hango wata dalilliyar mota ƙirar Benz a parker nesa da ita kaɗan nai parking, tun a tsakar gida na fara shaƙar ƙamshin turarensa gabana yai mugun faɗuwa har sai da na dafe ƙirjina da hannu, a kasalance na nufo parlour Mama duk takona ɗaya sai na ji gabana ya ƙara faɗuwa sai da na ja iska mai zafi daga bakina kana na fesar ta ƙofufin hancina, a maimakon na ji sauƙi sai naji na ƙara shiga wani yanayi mai wuyar fassarawa da kyar nai sallama gami da yaye labulle.
Mama ta amsa min yayin da Ya Haidar ko ɗagowa bai yi ba balle nasa ran zai amsa min sallama Aiman dake kwance a jikinsa yana game a wayar Ya Haidar ɗin ya taso da gudu ya rungume ni yana faɗin "Mommy oyoyo! Saura kaɗan ya ya jefar dani kasancewar babu ƙarfi kirki a jikina nai sauri dafa hannu kujerar dake kusa dani. A hasale na ture shi gami da kai masa rankwashi "Miye haka Aiman wai kai miyasa kullum ba ka yi abu cikin natsuwa kalle yanda ka tashi kada ni?"
Na faɗa a tsawa ce tuni jikinsa ya ɗauki rawa domin ba ƙaramin razana shi nai ba. Mama ta ɗauki ƙaramin throw pillow kujera dake kusa da ita ta jefa min ranta a ɓace ta ce "Ke dai kin shiga uku da zafin rai duk lokaci da ki ka shigo gidanan sai kin ɓatawa yaro nan rai, ko ki sa shi kuka ina dalili wannan mugun hali kin ɗauki zafin rai kin ɗorawa kanki.
Turo baki nayi ina gunguni ƙasa-ƙasa jikina ne ya bani yana kallona shiyasa nima na maida ganina akanshi, tabbas kuwa rikitattun idanuwanshi da tun fil'azal suke rikita ni su na kafe akaina, sai faman kallona yake ba ko kyaftawa hakan yasa na kasa tantance me kallon nashi yake nufi muryarsa ce ta daki dodon kunnena sai natsuwata ta dawo jikina har nai nasarar jin abinda yake faɗa "Zo nan my boy zo ka ci-gaba da game dinka, da nasan zaluntar ka za ta yi da wallahi ba zan bar ka ka je gunta ba.
Wani mugun kallo na watsa masa kafin na taɓe baki na ingiza ƙeyar Aiman ina faɗin "je ka inda ba za a zalunci ka ba tun da ni kallon azzaluma ake min.
   "Wallahi Jeeddah idan ki ka saka shi kuka sai ranki ya yi mummunan ɓaci.
Mama faɗa cikin hasala.
Ya Haidar ya baro wurin zaman shi ya ɗauki Aiman tare da komawa wajen zamanshi ban san abinda ya raɗa mishi a kunne ba sai naga Aiman yana dariya, na galla musu harara karaf sai akan idon Ya Haidar ya yi min wani kallo mai kama da na wulaƙanci-wulaƙanci, kai na ma wulaƙanci ne domin bai yi kama da na arziki ba, ya wani kauda fuska.
Na zauna akan kujerar dake kusa dani, sai lokaci na gaida Mama ta kwaɗa min harara gami da faɗin "Sai da kika gama sa min yaro kuka sannan za ki gaida ni to riƙe abarki banaso.
    "ALLAH ya ba ki haƙuri Mama.
Na faɗa ina murmushi.
   "Shin ba ki ga Aliyu bane da ba za ki iya gaida shi ba?"
Mama ta watsa min wannan tambaya gami da tsare ni da idanuwanta, cuno baki nayi ina faɗin "Na ganshi mana Mama gaba yake dani shiyasa nima na share shi don banga amfani gaida mutumin dake gaba dani ba.
Na ƙarashe magana tare da murguɗa baki, cikin sauri ya ɗago idanuwanshi ya kalle ni fuskarshi dauke da tsantsa mamaki, kafin ya girgiza kai gami da maida dubanshi ga Mama yana faɗin "Wallahi mama ƙarya take min tun dawowa na bakina bai haɗu da nata ba ko a wajen dinner kowa ya tayani murna dawowa na banda ita.
Na ɗago na banka mishi baƙar harara, kafin na ce "ƙarya yake min Mama ki tambaye Khairat har da gift na bashi tsabar wulaƙanci ko ya nuna min ya gani.
  Daƙuwa Mama tayi min tana faɗin "ungo nan! Kin ci gidanku Jeeddah ka ji min sakarci Aliyu sa'an ki ne da za ki ce yana miki ƙarya wallahi ki kiyayeni dole sai ya nuna miki ya ga kyautar taki.
  "Kyaleta kawai Mama dama mai hali baya bari halinsa, da wannan gift ɗin nata gara babu
Harara na sake galla mishi ji nake kamar na tashi na wanka mishi mari naji dalili da zai sa ya riƙe hannun Zarah har su ɗauki hoto wallahi na kasa daina jin haushi riƙe mata hannu da ya yi.
Mama tashi tare da faɗin "Aliyu bari na kwashe tuwona kada ya ƙone na dawo mu ci-gaba da zance da muke yi kada ka biyewa wannan sokowa za ta haifar maka da ciwon kai da maganganunta na wofi.
Mama ta ƙarashe magana haɗe da ficewa "Kai Mama!
Na faɗa da ƙaramin sauti ina ƙara cuno baki shiru ya biyo baya ba abinda ka ke ji sai bugun zuciyoyin mu sai kuma karar Ac dake parlourn.
    "Mtsss! Wai ke nan har tutiya ki ke da wannan ƙazamin gift ɗin naki?
Kamar daga sama na tsince maganar shi da mugun sauri na ɗago na kalle shi sai nunawa Aiman yanda zai buga game ya ke yi tamkar maganar ba daga bakinsa ta fito ba.
Kalmar ƙazanta da ya kira ba ƙaramin sosa min rai tayi ba duk ɗazu na ji sanda ya ce gara babu da gift ɗin na kyaleshi ne saboda mama ta nan yanzu kuma da bata nan dama ta ce da zan wake masa allon sa, a mugun fusace na ce "Kyautar da na ba ka za ka kira da ƙazanta?" lallai ma Ya Haidar wulaƙancinka ya wuce yanda na zata to ka dawo min da kayana dama can tilas ta min aka yi ba da son raina na ba ka ba.
Ya ciro kanshi da sauri ya kalleta zuciyarsa na mugun harbawa furuncin ta na ƙarashe ya tsaya masa rai ya girgiza kai kana ya runtse idanuwanshi na ɗan wani lokaci kafin ya buɗe su tass! Akan fuskarta sai faman gunguni take yi da ya rasa gane me take faɗi.
Wani iri abu yake ji yana masa yawo a maƙoshinsa da kyar ya iya buɗe bakinsa ya ce "Waye ya tilas ta miki?
     "Aunty Farida da Khairat!
Na faɗa gaba gadi har wani hura hanci nake yi domin na ƙara tabbatar mishi da bashi da wani muhimmanci a gareni. Wani irin kallona yake yi ya kasa ɗauke ganinsa akaina ya sake girgiza kai yana cewa...

_ku yi manage da wannan IN-SHA-ALLAH anjima zan sake wani update_
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*IDAN KAJI GUƊA DA LABARI...!!!*

_INA MASOYAN ASMY B ALIYU? ALBISHIRIN KU? KUCE GORO....! OHO... HO.. HO... KO KUNSAN A SABUWAR SHEKARAR NAN TA SHIRYA KAWO MUKU DADDAƊAN LABARI MAI SUNA Muhabbatil Qalb? TAFIYAR TA FARA NISA, WASAN KUMA YANA TA DAƊI._

_*SHIN KINSAN YADDA AKE SHIGA CIKIN RAYUWAR ƊIYA MACE A LALATA MATA MUTUNCI, A TARWATSA DUK WANI KYAWU NA TA? KUNSAN YADDA ZAMANI YA CANZA? KI SHIGO CIKIN TAFIYAR DAN KISHA ROMAN ILIMI DA KUMA HANYOYIN DA ZAKI SAN ANA BI DAN SHIGARKI CIKIN WANNAN HATSARIN.*_

ASMY B ALIYU KUNSAN BATA WASA A CIKIN TAFIYAR TA. KARKI BARI AYI TAFIYAR BABU KE. SAMUN ILIMIN KADAI ABIN ALFAHARINKI NE MAI SIYA.

*MUHABBATIL QALB*🔥
*MUHABBATIL QALB*🔥
*MUHABBATIL QALB*🔥

AKAN  NAIRA 300 Kacal ne.

0004157137
Asma'u Buhari Aliyu
Jaiz bank

Ko katin waya ta 07043079282
Shaidar biya ta 07065283730 view WhatsApp

040...

Washe gari da misali ƙarfe biyar na yamma tsirarun mutane suka shaida ɗaurin aure Bilal Ibrahim Shattima da Nusaiba Salisu Shattima akan sadaki Naira duba hamsin. Kamar saukar aradu haka Bilal Shattima ya ji zancen daurin auren sa, jikinsa ya ɗauki rawa ya zama speechless and shock har aka kammala addu'ar ɗaurin auren bai san inda yake ba. Abokinsa Abbas ya matsa daff dashi ya zungure kafaɗarsa gami da cewa "Ya haka mutumina kar dai a ce kaima abinda ake yayi ne ya faɗa kanka?"
A gigice Bilal ya yada firgitattun idanuwanshi akan fuskar Abbas muryar shi tana rawa ya ce
  "Inna lillahi wa'inna illahim raji'un! Wallahi-tallahi Abbas bansan da zance ɗauri aure nan ba. A dalilin Hajja ta kafe yasa na amince ayi mana baiko.
    "Ikon ALLAH! Amma wannan al'amari akwai ɗaure kai. Duk da a yanzu shi ake yayi da ka zo tambayar aure bazawara koda bakada sadaki a hannu ubanta zai baka aro, sai kawai malam ka ji an zarga ma igiyoyin aure da ba ka da shiri akan sa.
     "Hasbunallahu wal-imaal wakeel! Na shiga uku Abbas ya zan yi da Jeeddah!
Bilal Shattima baisan sanda wannan kalmar ta fito daga bakinshi ba, kuma da ɗan ƙarfi ya faɗa saɓani da farko da suke magana ƙasa-ƙasa. Da sauri Abbas ya zungure shi da ƙarfi domin maƙotan Baffa Salisu da ke zaune kusa dasu har sun fara kallonsu. Abbas ya tashi da sauri ya riƙo hannun Bilal yunƙura ya tashi da kyar yayin da makotan na Baffa Salisu da suka halarci ɗaurin aure suke dinga miƙa masa hannu suna musabaha tare da taya shi murna dole ya ari murmushi ya yafawa fuskarshi, da za ka tsare shi da kallo nan take za ka gano murmushin nasa na dole ne.
Bayan an watse daga Baffa Salisu da babban amininsa kuma maƙocinsa sukayi saura jikin Bilal Shattima har rawa yake yi ya nufi wajen Baffa, yayin da Abbas ya take masa baya yana zuwa cikin tsanani tashin hankali ya ce "Ya haka Baffa miyasa za ka yanke irin wannan danye hukunci ba tare da ka tuntube ni ba ka ji nawa ra'ayi?" Gaskiya ni ban shirya yin aure yanzu ba saboda ban ƙarasa gini gidana ba.
    Ɗan guntun murmushi Baffa Salisu ya yi tare da dafa ƙafaɗar Bilal ya yi ƙasa da murya yana faɗin "Hoo! Ja'iri kai gini ne damuwarka ni kuma zaman Nusaiba babu aure a gabana shi ne damuwata ni yanzu na magance tawa damuwa kai ya ragewa sai kama jikinka ka ƙarasa gini naka ALLAH sanya alkhairi ka ji?"
Shiru Bilal ya yi ya kasa magana sai faman kallo Baffa Salisu ya ke yi Abbas ya kama hannunshi ya ja shi zuwa wajen mota tamkar raƙumi da akala, hakan Abbas ke jan shi.
Abbas ne yai driving ɗinsu domin gaba ɗaya jikin Bilal ya saki bashi da kuzari ko kaɗan. Gani hali da ya shiga yasa Abbas ya shiga kwantar masa da hankali ta hanyar ƙarfafa masa guiwa "Abokina kada ka bari ka haifar wa da kanka damuwa akan wannan aure, tun da an riga da an daura kawai dai ka yi kokari ka fahimtar da Jeeddah yanda ba za ta ɗauke shi da zafi ba...
  "Ba za ta ɗauke shi da zafi ba ka ce Abbas shin ko ka manta da wacece Jeeddah na tuna maka?"
Bilal Shattima ya yi magana cikin rauni murya.
    "Ban manta ba Shattima amma wannan ba shi zai sa ka kasa takwara ta ka nuna mata ka isa da gidanka, kaine miji ba ita ba. Sai fa ka jajir ce ka zama namiji gaske ka fitar da tsoron Jeeddah kwata-kwata a zuciyarka ta hakan ne kawai, zai sa ka magance matsalolin ka da wuri.
    Dogon numfashi Bilal Shattima ya ja kana ya sauke kafin ya kalle Abbas da idanuwanshi da suka fara canza launi zuwa jajjaye saboda tashin hankali da ya riske kanshi a ciki.
   "Duk abinda zan faɗa Abbas ba lallai bane ka fahimta kai kana min kallon wanda ke tsoron Jeeddah ni kuma ina hango irin tashin hankali dake tunƙaro ni. Tun farko na ri ga da na tsara hanyar da zan ɓullo mata wacce nake tunani za ta kawo min rangwame ya kuma sassauta mata kishinta...
  "Wacce hanya ce za ta sassauta wa Jeeddah kishinta da ta wuce shawarar da na ba ka?"
Abbas yai sauri katse shi domin shi har ga ALLAH yafi yarda da cewa Bilal Shattima tsoron Jeeddah yake yi.
   "Tun lokaci da Hajja da Aunty Bahijja suka cusa min ra'ayi ƙara aure na yanke shawarar zan biyawa Jeeddah Makkah kafin ta dawo nayi aurena duk wani tashin hankali da za ta yi ni da Nusaiba mun ri ga mun zama abu ɗaya, kuma duniya za ta sheda na yi mata hallaci.
   "Hahaha!
Abbas ya Kwashe da dariya har yana haɗawa da dukan dashboard ɗin mota kafin ya tsagaita da dariyar tashi ya kalle Bilal Shattima yana girgiza kai sosai tausayinsa ya kama shi saboda Tsaka mai wuyar da ya tsinci kansa a ciki.
   "Gaskiya ba taɓa sani kai soko bane sai yau in banda sokanci ta ya za ka yi tunani biyawa mace Makkah al'hali kai ba ka je ba. To ka godewa ALLAH da ba ka aiwatar da wannan ɓatatciyar dabara ba. Gara ma tun wuri ka jingine wannan shirmen naka. Ka fuskanci gaskiya ina so sani Shattima mace mai zafin kishi irin Jeeddah cin hanci baya tasirantuwa akanta. Su fa mata da ka ke gani kowacce su tana da kishi domin halitta ne a jini jikinsu kawai dai kowacce da yanda take iya sarrafa nata, ka ma daina wannan gurgun tunani naka.
Shiru Bilal Shattima ya yi gami da dafe kokon kanshi gaba ɗaya duniya tai masa zafi sauƙi shi ɗaya baya Abbas ba wanda ya gayyata tun daga abokansa har 'yan uwa balle a sami wani mugun munafuki ya je ya fesa wa Jeeddah. Domin bai shirya sanarda ita yanzu ba. Sai bayan sallar isha'i Bilal ya je gidan Hajja, zaune ya tarar da ita a parlour tare da Aunty Bahijja da Ya Faruk wanda zuwan shi kenan.
Fuskar Bilal a turɓune ya miƙawa Ya Faruk hannu suka yi musabaha kafin ya nemi wuri ya zauna.
   "Kai lafiya ka shigowa mutane da fuska a martuƙe kamar wanda aka aurawa jaka ba 'yar adam ba?"
Cewar Hajja tana galla masa harara, sai da Bilal ya sauke numfashi kafin ya ce "Gaskiya Hajja gara ace jaka ce ki ka aura min da wannan danye hukunci ku ka yanke min ni dai gaskiya ba ki kyauta min ba. Domin na tabbata da haɗin bakinki Baffa ya ɗaura min aure da ban gama shirya masa ba. Haka kawai za a zantar da hukunci akaina ba tare da an bari an ji ta bakina ba. Magana ta gaskiya bana farin ciki da wannan aure.
    "La'illaha inlallahu Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam! Hajja kina ji abinda yake fitowa daga bakinsa ko? Dama na sha faɗa miki Jeeddah ba banza ta barshi ba, ta ri ga ta gama dashi ta asiri ce ko kuma ta wanke ta bashi ya sha.
Aunty Bahijja ta faɗa tana wani zare idanu iri na munafuci da haɗa husuma.
Kafin Hajja tai magana Ya Faruk ya karɓe zance yana murmushi ya ce"tun farko malam Bilal ka san ba za ka shiryawa aure ba miyasa ka fara soyayya da 'yar mutane?" Ban da ɓatan basira irin naka Bilal kai da ka tsince dami a kala kai ba ka da ko kwabo ka amma ka sami kyakkyawar mace irin Jeeddah shine don kana wawa za ka bi zugin mata wallahi sai, sun kai ka sun baro. Ka ganni nan matata ta ishe ni rayuwa ba zan iya haɗa soyayyata da kowacce mace ba, ita kadai ce a cikin zuciyata. Ko yanzu Bahijja tana fara yi min zance na ƙara aure ban bari ta ƙarasa magana ba na shiga rigar mutuncinta, iri-iri su Bahijja da ka ke gani ba abinda suka iya sai haddasa husuma...
   "Ya Faruk!
Aunty Bahijja ta kira sunan shi a fusace, harara ya galla mata gami da faɗin "gaskiya ce bakyaso na faɗa ko me?"
   "Wace irin gaskiya Faruk kana ƙoƙarin haɗa ta faɗa da Bilal hakan ba daidai bane.
Cewar Hajja.
   Taɓe baki Ya Faruk ya yi gami da miƙewa tsaye yana faɗin "Shikenan tun da ba a so na faɗi gaskiya dama can ɗaci gareta ba kowa ke so a faɗa masa ita ba. Bilal zo na ganka za mu yi magana Hajja sai da safe.
Daga haka ya juya ya fice abinsa dama tun yarinta haka ALLAH ya yi shi da faɗar gaskiya komai ɗacinta sai ya faɗa shiyasa tun a makarantar sakandare ake masa laƙabi da Faruk mai gaskiya, har kawo yau sunan yana bin shi.
  Bilal ya tashi jikinsa a mace ya bi bayan Faruk sun daɗe suna tattaunawa akan sabuwar plaza da Faruk keso buɗewa kafin ya yiwa Bilal sallama ya nufi gidanshi. Shi ma Bilal gida ya nufo ba tare da ya koma cikin gida ya yi sallama da Hajja ba.
  Koda Bilal ya shigo gida ya tarar dani a parlour Ina kallon wani India series da nake bibbiya a tashar zee world, na shagala sosai gaba ɗaya na tattara dukkanin natsuwa da hankalina akan akwatin talabijin saboda ina masifar son drama ɗin shiyasa ban lura da sabon yanayi da Bilal ya dawo min dashi ba. Domin ko sannu da zuwa da nai masa furtawa kawai nayi ba tare da na dube fuskarshi ba.
   Hakan da tayi ba ƙaramin hamdalla ya yi ba da sauri ya wuce bedroom ya watsa ruwa duk da ya yi wanka a maimakon ya ji natsuwa sai ma ya ji zazzaɓi yana ƙoƙarin rufe shi, jallabiya ya zura gudun kada ta tuhumi shi yasa ya dawo parlour ya wuce dining room ya tsakura abinci kaɗan, cikin sanɗa ya wuce ta ya koma ɗaki ya kwata yayin da zazzaɓin da yake ji sai daɗa ƙaruwa yake yi, ya kashe wuta da Ac ya shige cikin duvert fuskarsa kawai ya bari a waje.
   Sai around 10 na gama kallo gani Love bai fito parlour ba sai nayi tunani ko ya ɗebo gajiya ne, shiyasa ma ana kammala drama ɗin na kashe kayan kallo na nufi ɗaki wurinsa. Ganinsa kwance ya tattake cikin bargo ya haifa min da faɗuwar gaba. Da sauri na nufi wurinsa a daidai side ɗin da kansa yake na zauna ina faɗin "Love lafiya na ganka lulluɓe da bargo?"
Sai da ya ɗan ya motsa fuskarshi kafin yace dani "Zazzaɓi ke damuna Love.
    "Subhanalillah... Sannu kasha magani ko na dauko maka Panadol?
Na ƙarashe magana tare da tattaɓa goshinsa zuwa ga wuyansa na ji jikinsa ya yi zafi sosai, sai kawai na miƙe da sauri na buɗe bedside drawer na ɗauko kwalin Panadol, na ajiye kusa dashi kana na fita da sauri naje kitchen na ɗauko mishi ruwa hankalina bai kwanta ba har sai da naga ya yi bacci sannan na nemi gefensa na kwanta tare da shigewa jikinsa daga haka bacci ya ɗauke ni.
Can cikin bacci yai mummunan mafalki wai Jeeddah ta daɓa masa wuƙa a ciki wani irin ihun ya kurma a gigice ya tashi zaune gaba ɗaya ya fita hayyacinsa.
Kamar daga sama naji ihun Love ya cika min dodon kunne, na tashi zaune a firgici na yada ganina akanshi ya dafe kanshi da dukkan hannuwanshi, da sauri na matso jikinshi ina ɗora hannuna akan hannunshi da ya dafe kanshi dashi ya zabura da ƙarfi ni kaina sai da na tsorata da yanda ya zubara ya wani kakkafe ni da idanuwa, jikinshi sai rawa yake yi kamar mai jin sanyi cikin rawar murya na ce "Sannu Love halan mummunan mafalki ka yi?"
  Ya gyaɗa kai gami da goge zufa da ya karyo masa a gefen kunnenshi.
  "Subhanalillah! Wannan wane iri mafalki ne da zai sa ka ihu cikin tsakiyar dare kalle jikinka sai rawa yake yi kamar mai jin sanyi?"
Shiru ya yi yana mai ci-gaba da zarar ido. Gani haka yasa na sake cewa "watakila zazzaɓi da ke damunka ne ya janyo maka mugaye mafalkai ka yi addu'a ka koma ka kwanta ALLAH ya sauƙawa.
Nan ma shiru ya yi bai amsa min ba can kuma naga ya dira ƙasa da gudu ya shiga bathroom, kafin ya kai ga sink ya shiga kelaya amai a ƙasan tiles sai kakari yake yi, nima da gudu na isa bathroom ɗin na dafa kafaɗarsa sai faman sannu nake masa. Yana gama aman na miƙa masa ruwa ya kus-kure bakinsa, na taimaka masa ya dawo bisa gado ya zauna kana na koma bathroom na wanke gun da ya ɓata.
   "Love ko za mu tafi asibiti ne?"
   "A'ah zan iya jurewa zuwa safe sai mu je.
Ya faɗa cikin dusasshewar murya.
   "Shikenan ALLAH ya ba ka lafiya bara na haɗo maka tea kada ka kwanta ba komai a cikinka.
   "Banaso madara coffee za ki haɗa min.
    "Tam!
Na faɗa da sauri gami da ficewa jim kaɗan na dawo ɗauke da mug din coffee na miƙa masa ya sha sosai tun kafin ya ƙarasa shanye wa gumi ya fara karyo masa na tashi na kunna masa Ac na dawo na zauna kusa dashi ya ajiye mug din akan bedside drawer ya matso ni jikinshi ya ƙamƙame ni da ƙarfin gaske kamar wanda zai mayar dani cikin sa, a sanyaye ya shiga faɗin "Love ina sonki ina miki son da bana yi wa kaina shi, ke ce bugun numfashina Dan ALLAH ki yi min alƙawari komai girman laifi da nai miki ba za ki taɓa barina ba.
Ya ƙarashe magana tare da tsare ni da idanuwanshi da suka canza launi, ƙayatatcen murmushi na saki mishi na ƙara shigewa jikinsa, sai da na sumbace ƙaton hancinsa kafin na ce "Love kenan a duniya nan ba wani laifi da za ka yi min da zai sa na guje ka, Dan ALLAH ka kwanta ka yi baccinka ka kuma sa a ranka Jeeddah taka ce har abada. Doguwar ajiyar zuciya ya sauke gami da sake matse ni.
Har bacci ya sake ɗauke shi ina manne da ƙirjinsa, sai da baccinsa ya yi nisa sannan na runtsi idanuwana daga haka nima nai bacci.
  Washegari tun da ya yi sallar asuba ya koma bacci ni kuma na fito zuwa 'yan aikace-aikace na around 11:30am na ji ana mana knocking on na taso na buɗe ƙofa sai kawai nai arba da A'isha Shattima idanuwanta su yi zuru-zuru kamar dai tana cikin tashin hankali.
   "Sannu A'isha Shattima ke ce tafe a gidan na mu ALLAH yasa dai lafiya domin na ganki a hargitse?"
Dogon numfashi ta ja gami da saukewa ta kalle ni a sanyaye ta ce "Jeeddah mu shiga daga ciki domin maganar nan ba za ta yiyuwa a tsaye ba.
   "Okay! Bismillah.
Na bata hanya ta wuce kana na maida ƙofar na rufe koda na shigo cikin parlour tana zaune ta rafka tagumi, kusa da ita naje na zauna tare da dafa ƙafaɗarta gaba ɗaya sai na ji zuciyata tana wani irin bugawa, da kyar na buɗe baki na ce "A'isha meke faruwa ne ba dai matsala ki ka samu da al'ameen ba?"
Ta girgiza kai tare da sauke tagumi da tayi sai kawai naga ta tsura min idanu ba ko kyaftawa alamar da ke nuni da cewa abinda za ta faɗa min yana da girman gaske. Cike da ƙosawa na ce "A'isha Shattima don ALLAH ki yi magana wallahi shiru nan naki yana ɗaga min hankali taɓa ma ki ji yanda zuciyata ke mugun bugawa.
Na ƙarashe magana gami da kama hannunta na ɗora a ƙirjina.
   "Jeeddah ki yi haƙuri maganar da zan faɗa miki yana da girman gaske kuma ba shi da daɗi sai dai banaso ko a gaba ki zarge ni da cin amanar a bisa ɓoye miki da nayi. Jeeddah ke ƙawata ce tun ta yarinta ba ki taɓa kama ni da cin amanar ki ba, kin yarda dani kamar yanda nima na ba ki yarda saboda haka ba zan taɓa bari a ɓoye miki wani abu ni kuma na ƙasa bayyana miki shi.
   Tun lokaci da A'isha Shattima ta shiga wannan dogon sarhi faɗuwar gabana ya tsananta, jikina ya ɗauki rawa koma menene za ta faɗa min tabbas yana tattare da tashin hankali saboda haka, nai ta maza ta hanyar sake matse hannunta a ƙirjina.
    "Jeeddah jiya da yamma aka ɗaurawa Ya Bilal aure a asirce da Nusaiba 'yar gidan Baffa Salisu, nasan ba ki sa ni ba shiyasa na zo na sanarda ke domin na tabbata Ya Bilal ba shi da kwari guiwar tunƙarar ki da wannan maganar ni kuma ba zan iya barin ki a ciki duhu ba. Domin duk ranar da ki ka sani sai kin tuhume ni da cin amana..
   Duk ƙoƙarina na gani na saita numfashina domin na ƙara bitar kalamanta abin ya ci turo domin kuwa numfashinta sai sama da ƙasa yake yi, da sauri A'isha Shattima ta danne ƙirjin Jeeddah da hannunta da ke ƙirjin Jeeddah sakamakon yadda ta ji zuciyata tana wani irin harbawa da mugun sauri. Da wata irin murya mai cike da zallar firgici A'isha Shattima take furta "innalillahi wa'inna illahim raji'un! Jeeddah Jeeddah miye haka Dan ALLAH kada ki yi min haka?"
Falkawar Bilal Shattima kenan sai ya ci karo da muryar A'isha daga parlour tana ihu kiran sunan Jeeddah, da mugun sauri ya ye duvet cover ya diro ƙasa ya kwasa da gudu ya nufo parlour tun kafin ya iso wajensu ya hango yanda Jeeddah ke fizgar numfashi kamar mai cutar Asthma. Yana zuwa ya ture A'isha cikin bala'in tashin hankali ya shiga girgiza Jeeddah gami da kira sunanta "Love.... Love Dan ALLAH kada ki mutu ki barni wallahi ina bala'in sonki ki ɗauki aure nan a matsayin ƙaddara. Jeeddah don na ƙara aure ba yana nufi na daina sonki ba.
Sai lokaci Jeeddah ta ciro kanta cikin wani mugun yana yi take ƙare masa kallo, shima cikin idanuwanta yake kallo nan take ya hango tashin hankali da take ciki lokaci ɗaya ta kwalla gigitatciyar ƙara numfashinta ya tsaya cak gangar jikinta ta saki ta sulale a jikinsa a some.....
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*IDAN KAJI GUƊA DA LABARI...!!!*

_INA MASOYAN ASMY B ALIYU? ALBISHIRIN KU? KUCE GORO....! OHO... HO.. HO... KO KUNSAN A SABUWAR SHEKARAR NAN TA SHIRYA KAWO MUKU DADDAƊAN LABARI MAI SUNA Muhabbatil Qalb? TAFIYAR TA FARA NISA, WASAN KUMA YANA TA DAƊI._

_*SHIN KINSAN YADDA AKE SHIGA CIKIN RAYUWAR ƊIYA MACE A LALATA MATA MUTUNCI, A TARWATSA DUK WANI KYAWU NA TA? KUNSAN YADDA ZAMANI YA CANZA? KI SHIGO CIKIN TAFIYAR DAN KISHA ROMAN ILIMI DA KUMA HANYOYIN DA ZAKI SAN ANA BI DAN SHIGARKI CIKIN WANNAN HATSARIN.*_

ASMY B ALIYU KUNSAN BATA WASA A CIKIN TAFIYAR TA. KARKI BARI AYI TAFIYAR BABU KE. SAMUN ILIMIN KADAI ABIN ALFAHARINKI NE MAI SIYA.

*MUHABBATIL QALB*🔥
*MUHABBATIL QALB*🔥
*MUHABBATIL QALB*🔥

AKAN  NAIRA 300 Kacal ne.

0004157137
Asma'u Buhari Aliyu
Jaiz bank

Ko katin waya ta 07043079282
Shaidar biya ta 07065283730 view WhatsApp

039...

"Gaskiya Aunty Farida da Khairat ba su kyauta min ba akan me za su tilasta miki abinda ranki bayaso amma ba komai zan dawo miki da tarkace ki. Dama can basu da wani amfani agareni.
Da sauri na ce "So what don ka dawo min dashi.
   "Babu! Miye ma abin burge wa a kyautar jallabiya, boxer briefs da underwear vest, sai wani mugun turare mai kama da na 'yan bori duk kyaututtukan da aka bani nake ne very disgusting but don't worry zan dawo miki da tarkace ki.
Ya faɗa cikin izza da taƙama.
   "Kam bala'in nan.
Na faɗa a hasale ina mai tsare shi da idanuwana da suka fara canza launi, saboda ba ƙaramin yarfa min magana ya yi ba. Sosai na harzuƙa na miƙe tsaye ina ta banbami faɗa ko kallona bai sake yi ba. Daga ƙarshe na juya fusace na nufi ƙofar fita har na kai bakin kofa na juyo a hasale muryarta tana rawa anytime from now zan iya fashe da kuka nace "Ka tabbatar ka dawo min da kayana domin shine kwanciyar hankalinka.
Kulawa ma yabawa ce domin ko ɗago kanshi bai yi ba balle nasa ran zai bani amsa, har na fita sai kuma na sake dawowa na ɗauki handbag ɗina a fusace ko sallama ban yiwa Mama ba nai tafiyata da zan yi reverse da gangan na yi baya sai da na zo daff da motarsa na buge bayan ta na sake ja baya a karo na biyu na sake bugunta, fitila ce kaɗai ta fashe sai kuma painting ta da ya goge kaɗan ni kuma tawa gabanta ya ɗan lotsa ko ba komai na rage haushinsa dake damƙare a zuciyata ga motarsa har na dawo gida ina jin haushi da takaicinsa.
Da Mama ta dawo parlour ta tambaye Jeeddah Ya Haidar ya ce shi dai ya ga sanda ta fita amma bai san inda tayi ba.
Daga haka suka rufe chapter Jeeddah tare da ɗauko wata.
Nusaiba tana gani Jeeddah ta fice jikinta ya ɗauki rawa babu shiri ta dire shopping bags ɗinta ƙasa tsoro ya kamata ko gaba da gabanta Aljani ya taka wuta.😂
A lokaci da ta shigo bata ga Jeeddah ba idanuwanta sun ri ga sun rufe ruff da so bada labari, sai kwatsam ta ji saukar muryar Jeeddah a dodon kunnenta "Na shiga uku Aunty Bahijja saura kiris nayi subul da baka sam ban lura da matar nan ba.
Nusaiba ta faɗa da raguwar tsoro har yanzu a tattare da ita.
   "Ai ni tun shigowar ki na fahimci hakan.
Cewar Aunty Bahijja tana taɓe baki.
"Amma Aunty Bahijja da kin ankarar dani.
   "Akan wane dalili ai gara ta ji da kunnenta balle ma shi sha'ani na aure ai baya ɓoyuwa koda kuwa an so a ɓoye shi, komai daren daɗewa dole taji ke ce wacce mijinta zai aura.
   "To miye ma a ciki da za a ɓoye mata, da ba a aure ita ma ba za a auro ta ba. Matuƙar Nusaiba ki ka ga ba ki aure Bilal ba mutuwa ce tai min sauri. jiya ina masa ƙarya hawan jinina ya tashi a dalili ƙin amincewa da aure ki da ya yi sai gashi yau da sassafe ya zo min da zance amincewa har gashi ya fita dake kasuwa saboda haka ki kwantar da hankalinki Jeeddah bata isa ta hana  faruwar wannan aure ba domin nayi mata tanadi ba kaɗan ba.
Hajja ta ƙarashe magana gami da yin ƙwafa tabbas lokaci ya yi da za su nuna wa Jeeddah ƙarfin iko akan Bilal.
Sosai daɗi haɗe da farin ciki ya lulluɓe Aunty Bahijja, dama ita ce ke ƙara cusawa Hajja ƙiyayyar Jeeddah.
Lokaci da Haidar Ka'oje ya zo tafiya ya ga irin ɓarna da Jeeddah tai mishi ga mota, sai kawai ya yi murmushi domin yasan da gangan tayi don ta ɓata mishi rai kamar yanda ya ɓata mata.
Da dare da Bilal Shattima ya dawo ya ga yanda Jeeddah ta kwaɗe gaban mota da ya tambaye ta sai shara masa ƙarya tayi ta hanyar cewa ta je reverse by mistake ta bugi katanga. Sosai ya yi mamaki domin yasan hannunta yafaɗa sosai, daga baya kuma sai yai tunani mota bata da gwaninta sai kawai ya bar zance.
Har nayi shirin kwanciya bacci na hau gado na kwanta sai kawai na buɗe Data na shiga WhatsApp a dalili bana jin bacci na dai yi shirin kwanciya ne koda zai zo daga baya ya sace ni tun da dama shi gwanin sata ne.
A cikin family group naga Aunty Farida da Ya Kabeer da Ya Haidar da wasu tsirarun mutane dake group ɗin suna fira, ban tofa albarkacin bakina ba kawai dai ina bi messages ɗinsu ina karantawa can Kuma na bi Ya Haidar a private na aika masa da saƙo kamar haka "Malam yaushe za ka dawo min da kayana?"
Shiru-shiru bai bani amsa ba na duba info ya buɗe message ɗina amsa ce kawai ba zai bani ba. Hakan da ya yi min yai masifar tunzira ni na sake rubuta masa "Da kai nake magana fa.
Tsawon ten minutes da tura masa saƙon ya buɗe amma ya ƙi responding, sai kawai na shiga typing long message "Wannan wane iri wulaƙanci ne ina ma magana ka yi banza dani?" Ka sani Jeeddah tafi ƙarfi wulaƙanci ga kowa balle irinka karan kaɗa miya, wallahi idan ba ka dawo min da kayana ba sai mu yi ɓatatciya ni da kai.
Na tura masa shima ya karanta yai biris dani wannan hali ƙyaluwa da yake nuna min ba ƙaramin ƙara tunzira ni yake yi ba. Nai ƙwafa tare da kashe data ranar da mugun takaici Ya Haidar na kwana duk fira da Love yake min sama-sama nake amsa masa.
Washegari ina office sai nayi sha'awar shiga WhatsApp saboda tun dare jiya da Ya Haidar ya ɓata min rai ban sake buɗe Data ba. Ina buɗe wa sai ga message ɗinshi kamar haka "Idan kina buƙatar tarkace ki ki aiko wada mijinki yasan sabon kamfanina ya karɓa miki.
Wada da ya kira Bilal dashi ya ƙara linka min ɓaci rai, a hasale na yi dialling number shi tare da ficewa daga office ɗin kasancewar ba ni kaɗai bace sai da nayi nisa kaɗan da office ɗin sa'annan na tsaya, har kiran ya tsinke bai ɗaga ba a fusace na ci-gaba da maimaita kira aƙalla  nai masa seven missed call sai ana takwas yai picking a fusace ya ce "wai waye ne yake so taƙura wa rayuwata?"
   "Banaso wulaƙanci banza Ya Haidar ka duk san ni ce...
  "Ta ya zan san cewa ke ce alhali ni banida numberki a wayana.
Ya katse ni da sauri.
Sai da na haɗiye wani kololo bakin ciki kafin na ce "Wannan kuma matsalarka ce na kira ne domin na kashe ma gargaɗi karka sake kira mijina da wada.
   "Mtsssss! Na fahimci cewa kema kin bi sahun mijin naki na rashin aiki yi saboda haka karki kuskura ki sake kiran layina domin ni ba irinku bane marasa aiki yi ina da tarin ayyukan masu matuƙar muhimmanci a gabana.
Kafin na sake furta wata magana har ya datse kira, na bi wayar da kallo baki buɗe lallai ma Ya Haidar ya taro match don wallahi ba zan kyaleshi ba ya faɗa min magana mai zafi irin wannan. saboda haka na sake kiranshi sai kawai naga number busy da na sake kira sai na fahimci ya yi blocking ɗina dole na shafawa kaina lafiya.
Tun daga lokaci ban sake kula shi ba idan za mu haɗu sau ɗari ba zan ɗaga kai na kalle shi ba. Hakazalika shi ma ya fita sabgata.
Soyayya tsakani Bilal Shattima da Nusaiba tayi ƙarfi da fari ya amince da aurenta ne a dalilin Hajja naso abinka da zuciya ba ta da ƙashi kuma ba a yi mata shamaki Bilal bai san lokaci da zuciyarsa ta fara son Nusaiba ba. Sai dai yana bala'in jin tsoron Jeeddah tasan da wannan labari, shiyasa ya ƙara linka kulawa da tattali da yake mata kullum cikin kashe mata kuɗi yake ta hanyar siye banza siye wofi. Har da mota ya canza mata a lokaci da labari canza mata motar ya zo kunne Hajja da Aunty Bahijja ba ƙaramin tashin hankali suka shiga ba kamar za su cinye Bilal ƙiri-ƙiri suka nuna baƙin cikinsu a fili, Hajja har cewa tayi sai ya karɓe motar sai da Bilal ya fito musu a mutum ta hanyar cewa idan har ta kafe lallai-lallai sai ya karɓe mota daga hannun Jeeddah shi kuma ya fasa aure Nusaiba, dole suka shafa masa lafiya. Sai dai ƙiyayya da suke wa Jeeddah ta ƙara ƙaruwa.
   Hajja ta bi ta azalzale Bilal akan za ta yi wa Baffa mahaifin Nusaiba magana ranar juma'a a yi musu baiko amma a zahiri ba baiko kaɗai za a yi ba hadda ɗaurin aure wanda Bilal Shattima bai san dashi ba. A cewar Hajja idan har ya sani ba zai amince cikin sauƙi ba gara ayi ta ta ƙara don ta gaji da gani yanda Jeeddah take more shi ita kaɗai domin duk abinda yake musu ita da Aunty Bahijja ba su gani sai wanda yake yiwa Jeeddah ne ya tsone musu ido. Baffa ta kira ta sanarda shi ƙudurinta kasancewar mahaifin Nusaiba sannan kuma ƙanin mahaifin Bilal shiyasa abin ya zo mata da sauki domin kuwa nan take ya yi na'am da shawarar ta ta.
Jeeddah batasan waina da ake toyawa ba sannan kuma A'isha Shattima bata sani ba balle ta tsegunta mata. Ana gobe ɗaurin aure Bilal Shattima yana bathroom yana wanka Nusaiba ta kira shi a waya dama duk lokaci da zai shigo gida kashe wayarsa yake yi gudun kada tsautsayi ya gitta Nusaiba ta kira shi, a gaban Jeeddah duk da taka tsantsan da yake yi yau sai da dara taci gida ya manta bai kashe wayar ba.
Jeeddah da ke tsaye a gaban closet tana arranging kayan Bilal da ya karɓo daga wajen wanki, ta juya ta kalle wayar dake ajiye akan bedside drawer ta kauda fuska gami da ci-gaba da aikinta sake kira aka yi sai kawai ta ƙarasa saka shirt din da ta ɗauko cikin closet ta nufo wajen wayar car service shine sunan da ta gani yana yawo akan screen, ta taɓe baki dama ba da sunan Nusaiba ya yi saving contact ɗinta ba. Car service shine suna da ya yi saving numberta dashi, Jeeddah tana kai hannunta akan wayar Bilal Shattima yana fitowa daga bathroom a ruɗe ya iso wajenta jikinsa ko ina rawa yake yi, ya dafe hannunta akan wayar kana ya ciro wayar ta kasan tafin hannunta, ko kaɗan Jeeddah bata kawo komai a ranta ba sai ma cewa tayi "Amma wannan bakanike akwai shi da rashin haƙuri ya kira ba ka ɗauka ba sai maimaita kira yake yi shi ne na ce bara nayi kauɗi na faɗa masa kana wanka sai gashi ka fito.
Ta ƙarashe magana ba tare da ta kalle shi ba ballantana ta gano hali da yake ciki ta juya abinta ta ci-gaba da aikinta yayin da Bilal Shattima ya saki ɓoyayyiyar ajiyar zuciya.....*[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

ASSALAMU ALAIKUM SISTERS,

abun da mamaki Ta yanda watan axumi yake ta qaratowa cikin Dan taqin lokaci,
Me kika tanadarwa kanki dama yaranmu yar uwa?
Munada kyawawan kayan Yara na dinki masu kyau sosai da bama zakice dinkawa akayiba yaro/yarinya sufito gwanin burgewa kowa yanasan barka,07046881166

Kayanmu sauqinsu yyi har kamar kyautane,zaki iya samunsu dga 2k harzuwa abunda yyi Sama,kizo kiyi sarin kayanmu kisamu alkhairi me tarin yawa,07046881166

Akway takalma Suma kyawawa daga kan 1k zuwa sama,07046881166

Sannan munada tsala tsalan frames da madubai na gyaran gida masu kyau d arha sosai,07046881166

Akway leshina d atamfofi,abayas sewanda kikazaba duk a farashi mesauki,07046881166

Karna cikaku d surutu ku kira:07046881166 domin qarin bayani,karku manta alkhairin Tari maganin mantuwa zaku iyashiga Instagram handle namu don ganin kayayyakinmu: everythng_handmade,

Sai mun ji ku 07046881166

041...

"Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Love.... Love! Dan ALLAH ki tashi  wallahi A'isha munafuka ce so take ta rabani da ke. Love am begging you please wake up, Love please don't do this to me...I love you I really do wallahi ba a son raina aka ɗaura aure nan ba asalima ba a sanar da ni ba kafin a ɗaura wallahi-tallahi rufa-rufa aka yi min.
Wata ƙatuwar harara A'isha Shattima ta watsa masa kafin a fusace ta ce "Wai kai Ya Bilal ba ka san ta suma bane da ka wani taƙarƙare kana zuba mata ƙaryayyaki.
   "Rufa min baki don ubanki tsohuwar munafuka, ke dai kin yi asara ace ɗan uwanki za ki haddasa wa fitina, ban ga amfani ƙawance ki da Jeeddah ba tun da har za ki yi aikata abinda zai jefa rayuwar ta a hatsari.
   "Dallah! ya isa haka Ya Bilal. Za ka ɗauke ta mu kaita asibiti tun da saura numfashinta ko kuma za ka tsaya kana ɗora min laifi.
  Wani wawan bugu ya kai ma A'isha Shattima tai sauri kaucewa ya sami ta a shoulder a hasale ya kyasta yatsun shi gami da cewa "Idan wani abu ya sami matata na rantse A'isha ba zan taɓa yafe miki ba munafuka haddasana kawai.
   Sosai A'isha Shattima ta ji zafin dukan da ya yi mata domin sai shafar gun da ya daka take yi, kafin ta galla masa baƙar harara tare da kauda fuska wani mugun haushinsa take ji ba don da tana matsayin ƙanwar sa ba da ba abinda zai hana ta rufe shi da duka har sai ya daina motsi. Ƙoƙari sungumar Jeeddah ya yi A'isha tai sauri dakatar da shi ta hanyar cewa "Ba dai daga kai sai gajeren wando da singlet za ka fita ba a tunanina gantallewar taka ba ta kai har haka ba?"
  Wani mugun kallo ya wulgawa A'isha gami da yin ƙwafa muddin ya ci-gaba da musanya yawu da ita ba abinda zai hana shi rufe ta da mugun duka, shiyasa ya juya kawai da sauri ya koma ɗaki ya sako jallabiya da key ɗin mota, har suka iso wani private hospital dake nearby dasu yana zagin A'isha Shattima gami da ɗora mata laifi, yau ba kalar zagin da bai yi mata ba. Tun tana tanka masa har ta gaji ta zuba mishi ido cikin hukunci Ubangiji da taimakon likitoci biyu da ke bisa kan Jeeddah suka samu numfashinta ya daidaita sai dai fizge-fizge da take yi haɗe da sambatu yasa dole sai da aka yi mata allurar bacci, kana aka mayar mata da drip ɗin da ta tuzge gari fizge-fizgenta. Bayan likitoci sun fita daga ɗakin Bilal da A'isha suka shiga Bilal ya ja kujera ya kai kusa da gadon da take kwance zauna tare da ya kura mata ido yana kallon hawa da saukar numfashinta a ɓangare guda kuma yana zullumin idan ta falka irin bala'i da masifar da zai fuskanta. A'isha Shattima da ke jingine da bango ta fiddo wayarta daga aljihun kaftan gown ɗin da ke jikinta, tai dialling number Khairat ringing biyu zuwa uku Khairat tai picking kamar daga sama Bilal Shattima ya ji A'isha Shattima tana faɗawa Khairat Jeeddah tana asibiti an yi admitting ɗinta, kana ta gayamata sunan asibitin da room number. Kafin ta ƙarashe wayar Bilal Shattima ya zubura ya tashi tsaye gami da nufo ta yana wani zare ido a mugun fusace yake nuna ta da yatsa tai sauri katse kira cikin tsawa yake faɗin "You're very stupid A'isha why don't you ask me first before ki kira wani daga cikin family matata wai miyasa kike min shisshigi ne?"
   "Fahimtar nayi son kai ba zai bar ka ka faɗawa family nata ba shiyasa ni na faɗa musu saboda suma suna da hakki sani hali da 'yarsu take ciki. Don ka sani ba shisshigi nake maka ba abinda ya wajaba ne na sauke.
   "Da kyau munafuka ba wani abu da ya wajaba kawai dai kina ƙoƙari ƙarawa wuta fetur ne.
     "Whatever!
A'isha Shattima ta faɗa gami da taɓe baki ta kauda fuskarta da bari kallonshi, ya yi ƙwafa tare da komawa wajen zamanshi kafin ka ce kwabo asibiti ya cika da Iyaye da 'yan uwan Jeeddah Bilal Shattima yana gani haka ya sace jiki ya fece daga asibiti yayin da A'isha Shattima ta ja Khairat gefe ta feɗe mata daga biri har wutsiya don ita a ganinta aiki gama ya ri ga da ya gama gwada kowa ya sani domin babu sauran ɓoye-ɓoye. Duk wanda ya ji zance aure Bilal Shattima sai mamaki ya kama shi sai misali ƙarfe 1:30pm Jeeddah ta tashi daga dogon bacci da  ɗauke ta, da tana tozali da Mama, Aunty Farida, Khairat tai sauri wartsake wa gami da fashewa da wani irin kuka, har shiɗewa take yi daga jin yanda sautin kukanta ke fita za ka fahimci har can ƙasan zuciyarta kukan ke fita irin mai masifar cin rai. Aunty Farida tai sauri zuwa gare ta ta rungume ta tana bubbuga bayanta,  gami da bata baki "Ki yi haƙuri Jeeddah wannan kukan da kike yi ba zai taimake ki da komai ba, kukanki bai isa ya sauya miki ƙadddarar ki ba. Kishiya dai ba a kanki farau ba. Gani nan har guda biyu Abban Siyama ya yi min kuma wallahi ba abinda ya sauya na daga ƙauna da kulawar da yake min ba sai ma abinda ya ƙaru. Haka suka taru gaba ɗaya har Mama suka dinga rarrashinta amma kamar suna zugata ne. Don sai ci-gaba da rare kuka take yi tamkar wacce ta rasa uwa da ubanta a lokaci guda. Har kowa ya gaji ya zuba mata ido tun tana kuka da hawaye har ta dawo kukan zuci. Zuwan Ya Kabeer ne yasa ta yin shiru don sosai ya ci-ci mata mutunci saura kiriss ya dake ta dole ta haɗiye kukanta. Rana ɗaya tak amma har ta fita hayyacinta idanuwanta duk sun bi sun kode, kafin yamma Jeeddah har tayi wata irin rama ta ban mamaki.
   Sai misali ƙarfe shidda na yamma Bilal Shattima tare da abokinsa Abbas suka zo asibiti, cikin sanyi jiki ya gaida Mama tare da tambayarta mai jiki a tunanin shi zai ga sauyin fuska daga Mama da Aunty Farida sai ya ga saɓani hakan. Domin Mama nasiha ta dinga yi masa tare da nuna masa kuskure shi na ɓoye wa Jeeddah, Khairat ce kawai ta kalle shi ta watsar daga ƙarshe ma ta fice daga ɗakin saboda ita mugun haushinsa take ji tana taya Jeeddah kishi.
  Yayin da na runtsi Idanuwana gam! Bana so gani Bilal ko muryarsa da nake ji a dodo kunnena zuciyata kamar ta kama da wuta saboda tsabagen tuƙuƙi da takaicinsa da nake ji. Na tsani Bilal Shattima yanda kasan wani baƙin dodo mai mummunan halitta haka nake jin sa a raina. Duk sannu da suke min ko ɗan yatsana ban motsa ba balle su sa ran zan amsa musu, gani haka yasa Mama da Aunty Farida suka fi ce daga ɗakin. Hakan ne ya ba Bilal Shattima damar furta mata kalmomi ban haƙuri ta hanyar tausassa murya ya shiga faɗin
    "I'm so sorry Love I don't mean to hurt you al'amari ne ya zo min very complicated bani da yanda zan yi ALLAH shi ne shaida ta akan hakan. Ga Abbas nan ki tambaye shi Wallahi-azim ban san da zance ɗauri aure nan ba.
A mugun fusace ta tashi zaune sai wani Irin fizgar numfashi take yi kamar mai ɗauke da cutar Asthma al'hali masifaffen kishi ne kawai ke ɗawainiya da ita, daga gani yadda take fizgar numfashinta kaɗai kasan na wahala ne, yayin da idanuwanta suka firfito sun kaɗa su yi jajir zuciyarta sai bugawa take da ƙarfi. gaske tamkar za ta faso ƙirjinta ta faɗo ƙasa.
     Cikin tsakani jigata gami da masifa ta shiga ƙare masa kallo mai cike da gundarin tsana, kafin ta furta "Ni! ni Bilal ni za ki yiwa kishiya?" Tana Magana tare da nuna ƙirjinta da ɗan yatsanta kana ta zarce da faɗin    "Na rantse da ALLAH Bilal ka ɗebowa kanka bala'i da masifa a gidanka, ina mai tabbatar maka da cewa da ka ya min kishiya gara ka haƙa kabari ka binne kanka yafi maka sauki bisa ga mummunan tanadin da zuciyata ta tanadar maka kai da ɗiyar shegiyar da ka aura, kuma maza ka ja munafiki abokinka ku ɓace min da gani.
    "Jeeddah Dan ALLAH kada ki bari fushin zuciya ya ɗebe ki  ki aikata abinda zai sa ki dawo daga baya kina danasani.
Bilal ya faɗa cikin kwantar da murya.
   "Dallah rufe min baki! Baƙin munafuki algungumi mai baki biyu, wallahi-tallahi Bilal na tsane ka na tsani ganinka banaso gani duk wani abu da ya shafe ka.
    "Kin ga Jeeddah ki yi haƙuri mana ki tuna kowanne ɗan adam da tashi ƙaddara, kamar yanda kika ji Shattima ya faɗa miki haƙiƙani gaskiyar kenan wallahi bai san da zance aure nan ba. Shiyasa nake riƙon ki da ki ɗauke shi a matsayin ƙaddara...
    "Kai Abbas!
Ta kwatsama masa tsawa mai cike da barazanar fasa musu dodon kunne don har sai da Abbas ya ja da baya domin yanda ta zuburo ya yi zato za ta rufe shi da duka ne, tamkar wata mai iskokai haka ta dawo musu.
   "Karka sake na ƙara jin bakinka a cikin wannan magana ba ruwanka in Kuma kaine baƙin munafiki da ya ingiza shi yai min kishiya ka fito ka faɗa min domin idan nai bincike na gano da kaina, na rantse da ALLAH Abbas har kai ba zan bari ba. Kai duk ubanda da yake da sa hannu a wannan aure sai naci b* ubansa gara ka faɗa min tun da wuri idan da akwai sa hannu ka.
    "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Shattima ina waje ina jiranka wannan al'amari yafi ƙarfina.
Abbas ya faɗa gami da ficewa daga ɗakin da sauri gaske. Bilal ya bishi da kallo kafin ya dawo da ganinshi kan fuskar Jeeddah wacce ke huci kamar zakanya tana jin yunwa.
    "Amma gaskiya Love ba ki kyauta ba shin miye laifi Abbas da za ki zage sa?"
   "Laifinsa da ya kasance abokinka.
Ta faɗa cikin shouting gami da zazzaro idanuwa.
  Ƙoƙarin kama hannunta ya ke yi kafin hannunshi ya sauka akan nata tasa ƙafarta ta dama ta kai masa mugun shuri a ciki, ihun azaba ya saki tare da durƙushewa ƙasa yayin da ta ci-gaba da zurfa masa zagi kala-kala sai jifar shi take da duk abinda yake kusa da ita shi kuma yana durƙushe sai ƙoƙarin kare jifar yake da hannunshi, can ta rarumi flask ɗin ruwan zafi ta jefa masa kasancewar flask ɗin na silver ne shiyasa da ya tare shi da hannunshi ya ji masa ciwo, don jin ya yi hannunshi ya dauke wuta inda ALLAH ya taimake shi flask din bai buɗe ba da gaba ɗaya sai ruwan sun ƙona shi. Da Abbas ya fita bai rufe ƙofa ba hakan ne ya ba su mama da ke waje damar ji irin kaloli zagi da jifar da Jeeddah take masa, da gudu suka shigo rai ɓace Mama tayi kanta ta ɗauke ta da gigitatcen mari a kumatunta na hagu da dama kana ta rufe ta da duka a rikice Bilal Shattima ya miƙe tsaye duk ƙoƙarinsu shi da Aunty Farida na gani sun kwace Jeeddah daga hannu Mama abin ya faskara sai da Mama tai mata duka sosai kafin Aunty Farida tai nasarar janye ta Mama tana huci ta nuna Jeeddah da yatsa tana faɗin "Na fahimci so kike ki ja min abin faɗa da gori a gari kafin kin cimma manufar ki jikinki ne zai gayamaki. Shashasha banza da wofi kanki aka fara kishiya da za ki bi ki fitine mutane kin bi kin hana mu sakatt! Da koke-koke mu yi rarrashi mu yi nasiha amma duk a banza yanzu kuma ƙoƙari illata mijin ki ke yi shikenan mu shiga bakin duniya. Kai kuma maza fice ka ba ni wuri ai duk kaine Ummul-habasi haddasa wannan fitina banda tsokaci iri naka taya za a ɗaura maka aure ba tare da ka sanar da iyalinka ba?"
   "Mama Dan ALLAH....
"Kar ka ce komai Bilal Dan ALLAH ka fita kawai daga Mama har Jeeddah kowane su a yanzu hasale yake da kai idan so samu ne ka daina zuwa har sai Jeeddah ta sauko.
Aunty Farida ta katse mishi hanzari.
Ba don ranshi ya so ba ya juya jikinshi a sanyaye ya fice har suka ɗauki hanya yana dafe da kai gaba ɗaya duniya tayi masa juyi ɗan mangwaro.
   Yayin da Mama ta ci-gaba da ɓalɓale Jeeddah da faɗa, Jeeddah kuma sai rusar kuka take yi.
    "Saboda kishiyar banza kishiyar wofi Jeeddah kalle yanda kika dawo me aka yi kishiya da har za ta yi silar kwanciyar ki akan gadon asibiti?"
Mama ta faɗa a hasale ita ma Jeeddah cikin sautin kuka ta ɗago tare da jefa idanuwanta akan fuskar Mama ta ce "Ai dole ki faɗa haka Mama saboda Baba ko da wasa bai taɓa gwada yi miki ita, ba kuma ba za ki fahimci tsananin zafi da ciwo da kishiya take dashi ba, har sai ranar da Baba ya ce zai ƙara aure wallahi Mama ranar mutuwa kawai za ki yi..
   "La'illaha inlallahu Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam!
Mama ta faɗa riƙe da baki yayin da Aunty Farida ta kwashe da dariya har tana dafe ciki domin furuncin Jeeddah ba ƙaramin dariya ya bata ba, harara Mama ta galla mata gami da faɗin...
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

042..

"Ke yanzu Farida har kin ga abin dariya anan wuri ina kallo yarinya ta koma mahaukaciyar ƙarfi da yaji?"
   Sai da Farida ta tsagaita da dariya kafin ta ce "ALLAH Mama furucinta dariya ya bani.
"Mtsssss!
Mama ta ja guntun tsaki gami da shigewa bathroom Aunty Farida kuma ta ci-gaba da dariyarta yayin da Jeeddah ke ci-gaba da rera kuka.
Bayan sallar isha'i sai ga Baba ya zo asibiti ya duba ta anan yake ji labari abinda ya faru, zaunawa ya yi ya dinga yi mata nasiha duk abinda Baba yake faɗa jin sa kawai take yi don ba lallai bane tai amfani da nasiharsa ba.
Washegari da safe sai ga Bilal Shattima ya sake zuwa duk da kashedi da Aunty Farida tai masa gani ya yi ba zai iya haƙuri rashin sani hali da matarsa take ciki ba. Shiyasa ya kamo hanya ya zo asibitin. Kamar dai yadda tai masa jiya yau ma haka tai masa zan ma iya cewa na yau yafi muni domin sheƙe masa kwalar riga tayi, tana faɗin sai ya sake ta. Gaba ɗaya ta yakushe masa wuya, hargagin ta ya janyo hankalin Mama dake bathroom, ta fito da gudu tana zuwa ta shiga ɓamɓare hannuwan Jeeddah daga jikin wuyan Bilal da kyar Mama tai nasarar raba hannuwanta ga wuyan Bilal Shattima zuwa lokaci Mama ta harzuƙa matuƙa sai kawai ta kashe ta da ɗan bala'in mari wanda ya dawo mata da ainihin natsuwarta. Gani yanda Mama take ta zuba mata faɗa ita kuma sai kuka take yi yasa Bilal ya fice daga ɗakin ranshi a jagule.
Sosai Mama ta dinga ɓalɓale Jeeddah da faɗa ita kuma sai kuka take yi yanzu ba wanda ta ƙula alaƙa mai kyau dashi irin kuka, sai da yamma Mama ta kira Mommy Turai ta sanar mata da abinda ke faruwa, ta ɓangaren Mommy kuwa tana zaune ne a parlournta tana gama waya da Mama ta tashi da sauri ta shiga bedroom ta ɗauko mayafi da handbag ɗinta sai da ta fito compound ta tuna da direbanta ya tafi gani gida, da sauri ta juya ta nufi apartment ɗin Haidar Ka'oje a parlour shi ta tadda shi ya saka laptop a gaba yana fitar da wani zane mota yanda Mommy ta tura ƙofa da yanayi da ta shigo dashi yasa shi ture laptop gefe ɗaya yana tambayarta "Mommy Lafiya dai?"
Sai da Mommy ta zauna akan hannu kujerar da Haidar yake zaune akai kafin ta ce "Ina fa Lafiya Aliyu yanzu nan na gama waya da Hajiya Fatee tun jiya Jeeddah tana asibiti.
     Taɓe baki ya yi kafin ya kalli mommy ya ce "Subhanalillah! Wacce Jeeddah?"
Harara Mommy ta galla masa gami da faɗin "Banaso tambayar wofi Aliyu duk faɗin garin Sakkwato wacce Jeeddah nake da ita?"
   Ɗan guntun murmushi ya yi tare da faɗin "ALLAH ya ba ki haƙuri Mommy ita kuma ALLAH ya bata lafiya. Halan haihuwa ce?"
  "Mtsssss! Wacce irin haihuwa kuma Aliyu ana haihuwa ne babu ciki ko ka ganta ɗauke da ciki ne?"
   "Taya zan san tana da ciki ko bata dashi Mommy tun da ba wani abu da yake haɗa ni da ita ba.
   "Saboda har yanzu kana fushi da ita ko?"
   "Haba Mommy fushi me? Ni fa tuni na daɗe da goge shafinta a rayuwata ke ma shaida ce akan hakan.
   "Huhmm! To naji tashi ka shirya ka kaini asibiti kasan jiya Audu direba ya yi tafiya.
Ɓata fuska ya yi mommy ta ce "Ko ba za ka je bane naga sai ya motsa fuska ka ke yi?"
   "Ni na isa nace ba zan je ba kawai dai ina kan wani aiki ne mai matuƙar muhimmanci zuwa dare nake so na kammala shi shiyasa throughout ban fita ba.
  "Duk muhimmancin sa na tabbata bai kai lafiyar 'yar uwarka ba, saboda haka jingine sa za ka yi ka tashi mu tafi.
  Bai ce komai ba ya miƙe ya shiga bedroom ɗinshi ya canza kayan jikinshi zuwa ash colour shadda bai sanya hula ba gashin kansa a gyare yake tsaf sai kyali yake gwani sha'awa, yana riƙe da key ɗin mota ya fito parlour take ƙamshin turarensa ya gauraye parlour Mommy ta ɗago ta kalleshi da murmushi akan fuskarta ta ce "Ko kai fa.
  Yai gaba tare da yin gunguni ƙasa-ƙasa ta yanda mommy ba za ta ji abinda yake faɗa ba. Kafin Mommy ta ƙaraso parking lot ya jawo mota ya iso wajenta da sauri ya fito ya buɗe mata backseat ta shiga ya maida ƙofa ya rufe maigadi ya buɗe musu gate sai da suka ɗauki hanya mommy ta ce "Ban taɓa gani ɗan banza yaro butulu irin mummunan miji nan na Jeeddah ba, in banda butulci iri na ɗa namiji yaushe Bilal ya yi arziki da zai ƙaro aure. Don yana munafuki ya je ya ɗaura auren sa a ɓoye. Kuma wani abin takaici bai faɗawa Jeeddah ba  sai da taji a bakin shanu talla, kai ALLAH ya wadaran namiji mai hali iri na Bilal.
   Da sauri Haidar ya furta "mijin Jeeddah ya ƙara aure which means an yi mata kishiya unbelievable Mommy taya haka ta kasance,?"
Ya ƙarashe magana ɗauke ɗimbin Mamaki shimfiɗe akan fuskar sa.
   "Uhmm! Bari kawai Aliyu butulci ne irin na Bilal ɗan banza yaro mummunan tsiya.
Mommy ta ci-gaba da kwashe wa Bilal Shattima albarka yayin da Haidar Ka'oje ya lula a duniyar tunani.
Akwai wata rana da Jeeddah ta zo gidansu zai maida ta gida suna kan hanya idanuwanshi suka sauka akan zoben hannunta wanda shi ne ya bata, yanda zoben ya yi matuƙar kyau ga yatsanta yasa shi kamo hannunta ya matse cikin nashi yana murza zoben a hankali ƙoƙari fizge hannunta ta shiga yi gani haka yasa ya sumbace yatsunta kafin ya saki hannun nata ya kalleta da murmushi akan fuskarshi yana faɗin "A duk lokaci da na kalle zobe nan na yatsanki Jeeddah sai na tuna da girman alƙawari da nai miki wanda daga ni sai mahalicci na muka san dashi, a koda yaushe addu'a ta ALLAH ya bani ikon riƙe wannan alƙawari.
  Runtse idanunta tayi cike da takaici ta sake buɗe su akan fuskarshi tsananin takaicinsa ya lulluɓeta, cikin fusata ta ce "Duk wani alƙawari da za ka ɗaukar min a gareni na banza ne Ya Haidar domin ka kasa ɗaukar min alƙawari da idan mun yi aure ba za ka yi min kishiya ba. Shiyasa har gobe na kasa alfahari da soyayyarka na wofitar da ita kana kuma na karɓi Bilal Shattima da hannu bibbiyu domin shi ne mutumin da yai min wannan alƙawari da kai ka kasa yi min. Saboda haka ka manta da wani alƙawarinka akaina domin ni ba zan taɓa aurenka ba. Na sha faɗa maka ba zan iya aure kyakkyawan namiji ba baya cikin tsarina dama za ka yi min alƙawari ba za ka yi min kishiya ba da na ɗaure na aure ka ko don wannan mugun naci naka amma ina ka kasa yi min yanda nake so kai ma ba za ka sami yanda ka ke so ba, don haka ba zan aura ba ka je can ka nemi matarka ni dai na gama zaɓina Bilal Shattima shi ne namiji da ya dace dani.
   A lokaci ba ƙaramin zafin maganganunta ya ji ba amma kuma sai yai ƙoƙarin danne wa ta hanyar cewa "Karki ce haka Jeeddah ina da yaƙini koda ALLAH ya ƙaddare ni da aure mace fiye da ɗaya ba abinda zai canza soyayyar da nake miki domin ƙaunarki daban take a cikin jinina. Kuma Inaso ki sani da kyakkyawa da mummuna duk ALLAH ne ya halicci su. Kada kishi ya rufe miki ido ki zama jahila al'hali kina da iliminki, namiji da kike gani duk muninsa ba zai rasa wacce za ta so shi ba.
  "Whatever!
Ta faɗa tare da taɓe baki ya girgiza kai gami da cewa "Shi kanshi Bilal ɗin wanne tabbaci kike dashi akanshi da ba zai miki kishiya ba?
   "Ya Haidar Please mu bar wannan magana na fahimci koda za mu kwana anan ba za ka taɓa fahimta ta ba. Amma inaso ka sani na fidda hakkin ka ba zan aure ka ba Bilal Shattima shi nakeso kuma shi zan aura.
   Runtse idanuwa ya yi tunawa kaɗai da ya yi da maganganunta sai da yaji wani abu mai kama da mashi ya soke ƙahon zuciyarsa, hakan yasa ya manta da driving yake yi kuma yana tafiya ne akan babban titi muryar mommy da ya tsinkaya tana salati yasa shi dawowa cikin natsuwarshi ashe ya saki hannunshi saura kiriss ya buge motar da ke gefensa.
   "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Aliyu kanka ɗaya kuwa tunani me ka ke yi da zai ɗauke maka hankali har ka manta da tuƙi ka ke yi?"
  Ajiyar zuciya ya sauke gami da saukar da glass din mota ya leƙar da kanshi ya ba wa mai motar da yai kusa bugu haƙuri kana ya maida glass ɗin.
  "Wai Aliyu ba magana nake da kai ba za ka faɗa min abinda ke damunka ko kuwa sai na fusata?"
Mommy ta faɗa a tsawa ce.
   Sai da Haidar ya sake sauke numfashi kafin cikin sanyi murya ya ce "Ki yi haƙuri Mommy domin ni kaina basan takamaiman abinda ke damuna ba.
   "ALLAH ya kyauta amma ka dinga kula sosai domin wannan kasada ce da sai da rai kana tuƙi kana tunani.
   "in-sha-Allah zan kiyaye.
Daga haka suka iso asibiti gun da aka tanada domin parking motoci ya nufa ya yi parking kana ya fito Ya buɗe wa Mommy ƙofa ta fito karɓa handbag ɗinta ya yi ya riƙe mata, suka jero zuwa cikin reception duk wanda ya kalle su sai sun burge shi duk da kasantuwar su na uwa da ɗa ba sai an faɗa maka ba kasan akwai shaƙuwa mai tsanani a tsakaninsu. A ƙofar shiga ɗakin da Jeeddah take suka tarar da Mama da Aunty Farida zaune akan farare kujeru rubber, bayan gaisuwa da ta shiga tsakaninsu kana mommy ta tambaye jikin Jeeddah Mama ta ce "jiki da sauƙi za a ce amma yanzu nan ba daɗewa ba likita ya gama gwada Bp ɗinta ya tabbatar mana jininta ya hau sosai idan har bata cire damuwar da ta ɗorawa kanta ba, da wuya bai zama mata hawan jini ba.
   "Subhanalillah! Kai ALLAH ya wadaran Bilal sam bai yi wa Jeeddah hallaci ba.
   Mommy tayi magana cike da takaici.
   "Ni fa banga laifi Bilal ba hakan ma da ya yi ya min dai-dai ba taƙamar take yi yai mata alƙawari ba zai mata kishiya ba, kin ga yanzu dole ta rage wa kanta wannan zazzafan kishin nata.
   Haidar Ka'oje ya yi magana yana taɓe baki.
A masifance Mommy ta ce "Kar na sake jin bakinka a cikin zance nan Aliyu dama ku maza duk halinku ɗaya.
  Dariya Mama da Aunty Farida suka sa gani yanda mommy ta hayyaƙo wa Haidar. Cikin dariya Mama take faɗin
  "Yi shiru abinka Aliyu kada a sauke haushi  akanka kishiya dai ce da 'yarta bata so an kuma ri ga da an yi mata ita.
   "Daɗi abin kishiya ba a kanta farau ba kuma kanta ƙarau ba.
Mommy ta faɗa gami da nufar ƙofar shiga ɗakin gaba ɗayansu suka biyo bayanta yayin da Mama take faɗin "Ko dai ba a kanta farau ba an dai yi muku zuwan bazata  kuma ba yanda za ku yi gara tun wuri ku sawa zuciyarku salama.
  Mommy ba ta sami damar bata amsa ba a dalili ta iso cikin ɗakin ta hango Jeeddah kwance ta ba wa ƙofa baya da sassarfa mommy ta nufe ta "Sannu Jeeddah!
Mommy ta faɗa gami da shafa kitso kan Jeeddah jin muryar mommy Turai da nayi yasa ni tashi zubur na fashe mata da kuka ina faɗin "Mommy Dan ALLAH ki taimake ni ki sa Bilal ya sake ni wallahi ba zan iya ci-gaba da zama dashi ba tun da ya zama munafiki mai ƙarya alƙawari.
  Kafin Mommy tai magana Ya Haidar ya daka min gigitatciyar tsawa wacce sai da hanjin cikina ya kaɗa "Ke dallah yiwa mutane shiru! In banda sakarci saboda auren wata za ki kashe naki a dalili wannan banzar kishi naki yasa mijin naki yai aurensa ba tare da ya faɗa miki ba. Alƙawari da kike cewa ya ƙarya dama na banza ne ya ɗaukar miki iya na fatar bakinsa ne.
   Ya ƙarashe magana yana min wani mugun kallo ji nai ba zan iya jure kallo da yake min ba nai sauri sadda kaina ƙasa yayin da na shiga rera kuka ƙasa-ƙasa. Ina jin lokaci da mommy ta rufe shi da faɗa yayin da Mama da Aunty Farida suke goyon bayansa. Kyale su mommy tayi ta dawo kaina ta zauna kusa dani gami da sanya ni cikin jikinta tana bubbuga bayana, kana ta shiga gayamin maganganu na kwantar da hankali da haifar da natsuwa tsawon lokaci ta share kafin ta samu ta ciyo kaina na daina kuka na dawo ajiyar zuciya. Ina ji Mama tana ba wa Ya Haidar labari haukar da na dinga yi sosai naji zafi labari da Mama ta bashi domin kuwa girke min dariya ya yi zan iya cewa tsawon zamana dashi ban taɓa gani ya yi dariya irin wannan ba. Wato ya yi farin ciki da kishiya da aka yi min ban ƙara tabbatar da hakan ba sai da na saci kallonshi da zarar mun haɗa ido sai ya saki min wani arne murmushi wanda ke nuni da yana cikin zallar farin ciki. Hakan kuwa ba ƙaramin ƙona min rai ya yi ba fushina yaƙara ɗaɗuwa har na kagara ya tafi, sai da aka yi kira sallar magariba sannan ya fita inda ALLAH ya taimake ni sanda ya dawo daukar mommy bai shigo ɗakin ba a waya ya kira ta.
Kwana na biyar a asibiti Sa'annan aka yi discharge ɗina, kuma har aka sallame ni ba wanda na ya zo duba ni daga gidansu Bilal idan aka cire A'isha Shattima domin ita kusan kullum da yamma sai ta zo kuma sai dare take tafiya.
Lokaci da aka sallame ni banso na koma gidana ba a cewa ta na gama zaman aure da Bilal Shattima amma Baba yana ji wannan furuncin nawa saura kiriss ya lakkaɗa min duka faɗa kuma ba kalar wanda bai min ba daga ƙarshe da kanshi ya dawo dani ɗakina, a cikin kwanaki biyar duk na bi na rame na fita hayyacina.
   Bayan sallar isha'i Bilal Shattima ya dawo gida a lokaci na shiga wanka koda na fito ɗaure da towel yana zaune a gefen gado tallaɓe da kumatunsa, kallo guda nai masa na ja guntun tsaki a duk lokaci da idanuwana suka sauka akan fuskar shi sai naji kamar na shaƙe masa wuya har sai ya daina motsi. Ya bi ta da kallo yanda yaga tayi baƙar rama ba ƙaramin tausayinta ya darsu a zuciyarshi ba, ya tabbata shi ne silar wannan ramar ta ta. Shi kansa yasan bai kyauta mata ba tun da yasan duk duniya ba abinda ta tsana irin kishiya kuma ya yi mata.
  A dare ranar parlour na kwana duk yanda ya kai da son rarrashina ya kasa domin kuwa dawowa masa nayi tamkar wata 'yar kwaya sai zafafan maganganu nake ta gaggaya masa. Tun daga ranar da na dawo ban sake kwana ɗaki ɗaya dashi ba, abinci ma na daina girkawa sai yunwa ta ci ni sosai nake iya haɗa ruwan tea nasha ko kuma nasha farau-farau fura, shiyasa na kara lalace fiye da tunani mai karatu ba ma zan iya misalta muku yanda na dawo ba. Hatta da office na daina zuwa ko wanka nayi iyakacina na nemi riga na saka I can't even remember when last da na shafa mai balle aje da zance kwalliya, yau ma Kamar kullum ina zaune a parlour abin duniya ya taro ya min yawa sai ga Aunty Farida ta zo direbanta ya dinga shigowa da boxes kusan set biyu amma different colors the same design, bayan ta zauna ko gaisawa ban bari mu yi ba nace da ita "Aunty Farida waɗanan akwatuna na menene?"

*Ku yi haƙuri kwana biyu kun daina ji na kusan jiki da jini*
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

043..

"Matsalata kenan dake Jeeddah gaggawa tun da ki ka ganni da akwatuna ko ba ki tambaye ni ba ai dole nai miki gamsasshe bayani.
   Taɓe baki nayi gami da kallo boxes ɗin na kauda fuska kafin na ce "Karki ga laifina Aunty Farida lamari ne da ɗaure kai.
  "Kin ga zo ki zauna mu yi magana a natse kin min tsaye kerere aka.
Ban ce komai ba na zauna kusa da ita cikin kwantar da murya ta ce "Kayanki ne na faɗar kishiya tare da lefen amarya, Bilal ne ya bani contract na haɗa muku, wadancan pink colors ɗin sune naki saboda pink yana ɗaya daga cikin favorite color ɗinki shiyasa na zaɓar miki su blue ɗin sune na amarya, gaskiya Bilal yana ji dake Jeeddah cewa ya yi fa duk abinda na saka wa amarya a lefenta kema irinsa za a sa miki ba abinda na bambanta sai colours...
  "Dallah dakata Aunty Farida!
Na katseta a mugun fusace cikin ɓaci rai na ci-gaba da faɗin "Yanzu fissibilillahi! Aunty Farida a matsayina na ƙanwarki wacce muka fito ciki ɗaya kin min adalci kenan? Duk faɗin garin Sakkwato Bilal ya rasa wacce za ta haɗa masa lefe sai ke ai wannan cin fuska ne da so gani an ƙara ƙuntata min.
Na ƙarashe magana ina sauke wani irin numfashi, kallona kawai Aunty Farida ke yi riƙe da haɓa can ta sauke ajiyar zuciya, gami da furta "iyee! Lallai ba shakka Jeeddah haukar kishinki yau akaina ya sauka to ki buɗe kunnenki da kyau ki saurareni ina shawartaki da ki yi gaggawa ki jinginar da wannan baƙin kishi naki a gefe, domin yanzu kai ya waye an daina wannan kishi na hauka, ki ɗauki misali daga kaina mana kishiya har guda biyu aka yi min kalle ni da kyau kinga na ragu da wani abu? Duk soyayyar da Abba Siyama yake min ba abinda ya ragu sai ma abinda ya ƙaru har gobe a gaban matansa zai buɗe baki ya ce bashida kamata ba kuma don baya sona ya auro su ba. Saboda haka duk wacce ta nemi taci zarafina za ta bar mishi gidanshi kin ga da na nuna mishi kwatankwacin irin wannan haukar da ki ke yi da ba zai nuna musu ina da matuƙar muhimmanci a gare shi ba. Jeeddah ki sani ba gazawa bace ko kasawa ke sa namiji ya ƙaro aure sai don yana da buƙatar hakan shin ke ba ki san cewa akwai namiji da mace ɗaya bata gamsar dashi ba?"
   "Amma kuma Aunty Farida sai ya rasa wacce za ta haɗa masa lefe sai k...
  "Dallah dakata Jeeddah!
Tai sauri tarar numfashinta "Ke wacce irin mace ce wai kam ko babu ƙwaƙwalwa a kokon kanki ne? Sai nayi gabas ke kuma ki yi yamma wallahi ki natsu ki san abinda ki ke yi kada ki yi wasa da damarki ta zo ta subuce miki daga baya ki dawo kina danasani.
   "Idan akan Bilal Shattima ne wallahi Aunty Farida ba zan yi danasani ba sai dai shi ya yi domin shi ne yaci amanata ya ha'ince ni kuma wallahi sai ALLAH ya saka min. Wacce irin ƙauna ce ban nuna masa ba tun bai shi da komai na aureshi a lokaci da kowa haushina yake ji a dalili zaɓar sa da nayi, ke kanki kina ɗaya daga cikin mutane da basu so aurena dashi ba. Shine yanzu don ya sami kuɗi zai min kishiya miyasa lokaci da yake matsiyaci sa Nusaiba bata aure shi ba sai yanzu da suka ga ya yi arziki?"
Riƙe baki Aunty Farida tayi tana kallona cike da al'ajabi yayin da ni kam ko a jikina sai ma ƙaimi na ƙara wuri antayawa Bilal zagi gami da ALLAH ya isa.
"Lallai Jeeddah sai yau na tabbatar da cewa ba iya zafin kishi ke damunki ba hadda iskanci da reni wayau, shikenan tun da kin aure shi ba shi da kuɗi yanzu kuma ALLAH ya azurta shi sai kawai ya cuce kanshi ya ƙi raya sunnah saboda ke.
Lallai kuwa kin tafka babban kuskure, domin namiji ba ruwanshi da wannan. Yanzu kalle yanda ki ka maida kanki duk kin rame kin fita hayyaci ki a takaice ma Bilal ya kawo min ƙarar ki ya ce gaba ki ke yi dashi kin daina haɗa shimfiɗa dashi, hatta da girki kin daina yi wallahi Jeeddah ki ji tsoron ALLAH kada garin mugun kishinki ki kai kanki wuta.
  Gani yanda Aunty Farida ta ɗauke laifi kacokan ta ɗora min yai masifar tunzira ni na fashe da matsanancin kuka ko kaɗan ba ta nuna damuwarta akan kukan da nake yi ba, sai ma gyara zamanta da tayi ta ci-gaba da faɗar "Ke kin isa ki hana abinda ALLAH ya ƙaddara ne?" Ko kuma kanki aka fara kishiya ne da za ki bi ki ɗagawa kanki da mijinki hankali ina tabbatar miki idan ki ka ci-gaba da haka kwaɓar ki za tayi ruwa duk so da kulawar da yake miki zai daina tun da yanzu ba ke kaɗai gareshi ba. Balle ya ci-gaba da wahalar da kanshi akanki. To bari ki ji kodai ki gyara halinki ko na faɗawa Baba hali da kike ciki domin na fahimci so ki ke ki kashe kanki saboda zafin kishi. Kalle kitson kanki yanda ya cukurkuɗe kamar kan mahaukaciya kin bi ki lalace anya kuwa kina wanka da sabulu naga duk ki yi wani iri mugun baƙi?"
Ta ƙarashe magana tare da sa hannunta ta murza gefen wuyana sai ga dauɗa, salati ta shiga yi tana tafa hannuwa. Dama ba wani wanka kirki nake yi ba iyakacina na watsa ruwa na nemi doguwar riga na saka. Bansan sanda na ƙarawa kukana sauti ba yayin da Aunty Farida ta ci-gaba da zazzaga min faɗa sai da tayi mai isarta kafin ta dawo rarrashina, tana ɗaura ni a hanya bata bar gidana ba sai da ta tsife min kitso kaina ta wanke min gashina, akan idonta na ɗora girki sannan tai min sallama ta tafi da nufi gobe za ta dawo idan bata ga canji ba tai rantsuwa sai ta faɗawa Baba ambatar suna Baba da tayi cikin zance yasa na tsorota duk da matuƙar wahala nayi iya dukkan abinda ta umarce ni ba. Amma na ƙudurta a raina zan kwatata ko da kaɗan ne.
Bilal Shattima ya kalle Nusaiba ranshi a ɓace ya ce "Ke mahaukaciyar wane gari ce Nusaiba akan wane dalili za ki kai ƙara ta wajen Hajja don kawai nace ban amince da dinner da ki ka ce za ki yi ba?"
  Cikin sanyi murya gami da kissa da kisisina Nusaiba ta ce "ALLAH ya huci zuciyarka jan gwarzo ban yi nufi na ɓata maka rai ba nayi hakan ne a dalili na sa raina ga dinner ɗin. Saboda a yanzu ne nake ji zan yi aure na nunawa tsara yanzu ne na aure mijin da ya dace da muradina. Amma tun da bakaso shikenan na haƙura domin duk abinda nakeso idan ya zo da akasin ra'ayin ka duk sona dashi zan haƙura dashi har abada.
   Ta ƙarashe magana tana wani kwantar da kai.
Ajiyar zuciya ya sauke sosai ya ji kalamanta sun ratsa jini da bargo jikinshi, har bai san sanda ya saki ƙayatatce murmushi ba ya ce "Ban ji daɗi yanda katsaye ki ka kai ƙara ta a waje Hajja ba, da tun farko kin nuna min ƙaunarki ga dinner ɗin tun da kina so dole na amince amma sai kawai ki ka kai ƙara ta a gun Hajja domin ni banga abin kai ƙara ba shiyasa raina ya ɓace.
   "To dan girman ALLAH ka yi haƙuri na karɓi laifina in-sha-Allah hakan ba za ta sake faruwa ba ka ji my Nurul-qalbi?"
Bilal Shattima ya ɗage girar ido gaba ɗaya jin kanshi yake yi cikin nishaɗi, saɓani ɗazu kafin ya fito daga gida irin tijarar da Jeeddah tai mishi yana zuwa gidansu Hajja ita ma tai mishi nata yanzu kuma Nusaiba ta wanke mishi duk wani ɓacin ranshi da daɗaɗɗa kalamanta musu sanyaya zuciya da gangar jiki. Ya yi nisa a tunani sai kawai ya ji ta cikin jikinshi dama suna zaune a ɗakin Yayanta Sageer dake soro, a hankali take shafar saje gami da geminshi yanda take yawo da hannunta akan fuskarshi yasa ya ji wani irin yanayi dama ya daɗe rabonshi da Jeeddah a matse yake ɗaurewa kawai yake yi, amma yanzu da ya ji Nusaiba cikin jikinshi ga kuma salonta da yafara awon gaba dashi bai san sanda ya ƙara matsota jikinshi ba, sannu-sannu ya fara shafar ta kafin ya rabata da hijabin jikinta wata munafukar riga ce a jikinta ita da babu duk ɗaya, shafo nonuwanta ya yi dake cikin rigar kusan a tare suka sauke ajiyar zuciya a rikice ya yi connecting bakinsu kiss ɗinta yake yi da zafi-zafi ba ka ji komai sai sautin fitar numfashinsu. Gaba ɗaya Nusaiba ta gigice ta fita hayyacinta dama ta dirke kayan mata har na fita hankali. Cire mata riga ya yi tare da kwantar da ita akan 'yar yalolowar katifar Ya Sageer ya yi mata rumfa da ƙirjinshi nonuwanta ya ƙura wa ido duk da sun sha bala'i gyara sai dai ko kusa ba za a haɗu su da na Jeeddah ba duk da kuwa ita Jeeddah ɗin ta taɓa haihuwa shiyasa duk cikin halittar jikin Jeeddah yafi so nonuwanta saboda tsaye suke cakk bulbul dasu.
Bai an kara ba yaji hannun Nusaiba cikin wandonshi nan take ta ƙara kunna shi, a hauka ce ya cire kayan jikinshi, da kyar ya samu ya ratsa ta a dalili matsi da tai amfani dashi, wani irin ihu Nusaiba ta saki tare da ƙanƙame shi sai wasu irin dirty talks take zuba mishi wanda tsawon zaman shi da Jeeddah bai taɓa jin ta furta masa irin su ba, nan ya sake rikicewa sai haƙarta yake yi bai dawo hayyacinshi ba sai da ya sami natsuwa da ita.
   Rungume ta ya yi yana lasar fatar kunnenta duk da ta zo mishi da sabon samfuri amma sai yake ji daɗin Jeeddah da ni'imarta dabam ne sai yau ya ƙara yarda da karin maganar nan da ake cewa mata suna suka tara, tabbas Jeeddarshi dabam ce ko a cikin mata ga dai daɗi an bashi hadda gudunmuwa kalaman batsa amma ni'imar Jeeddah yake tunawa gami da mararin ta.
Har ya maida kayan jikinshi Nusaiba tana kwance tana lasar lips kamar tsohuwar mayya ko kaɗan bata ƙoshi ba da son samu ne ya ƙara mata second round.
Abinda Bilal Shattima bai sani ba Nusaiba harija ce shine ma dalili mutuwar aurenta saboda tsohon mijinta bai iya gamsar da ita yana sonta amma haka ya haƙura ya sake ta, a bisa rashin sani Bilal Shattima ya kwaso wa kanshi jangwa.
    "Ki tashi ki sa kayanki mu ƙarasa magana banaso lokaci sallar ya yi ban koma gida nai wanka ba.
Nan take daɗi ya kashe Nusaiba ko ba komai Jeeddah za ta fahimci Bilal ya sadu da ita tun kafin su tare ta tabbata hakan ba ƙaramin ƙara hura wutar kishinta zai yi. Saboda haka ta tashi da sauri ta maida tambaɗaɗɗiyar rigarta, ta dawo kusa dashi ta zauna cike da kissa ta riƙo hannunshi tai ƙasa da murya ta ce "Thank you so much Baby for having you in my life you're so sweet daɗinka ya zarce 'yar ƙaramar ƙwaƙwalwata ta misalta shi, ka shayar dani zumar da ɗanɗano ta ba zai taɓa gushewa daga bakina ba. Ina sonka Ya Bilal kaine rayuwata, ba za ka tabbatar da hakan ba har sai na tare a gidanka.
  Shiru Bilal Shattima ya yi yana kallonta kafin ya yi murmushi gami da faɗin "Ni ke da godiya Nusaiba domin tabbatar da hakan na amince da dinner ɗin yanzu ki turo min da account details ɗinki zan yi miki transfer ɗin kuɗaɗen da za ki yi amfani dasu.
Da sauri ta rungume shi tana dariya sai ruwan kisses take mishi a sassan jikinshi sai faɗin take "thank you! Thank you Nurul-qalbi I love you I really loves you ALLAH yabar mana kai ni da Auntyna Jeeddah.
  Ambatar sunan Jeeddah da tayi ya ƙara jin wani irin ɗan bala'i daɗi ya shiga washe baki, ya kai bakinshi dai-dai kunnenta ya yi mata raɗa gaba ɗayansu suka sa dariya ta kai hannu ta ja mishi gemi tare da furta "Uhmm Nurul-qalbi gaskiya ji nake kamar mu koma ruwa wallahi ban ƙoshi ba.
Zaro idanuwa ya yi tare da furta "iyee....halan tuwo ne balle ki ce ba ki ƙoshi ba?"
    "Ba za ka gane bane Nurul-qalbi wallahi kafi tuwo daɗi kai har ma da zuma...
  "Ke dallah mu ajiye zance nan a gefe mu yi wanda ke gaban mu.
Ya yi magana a fusace don har ta fara bashi haushi ya tsani mace da batada aji.
  Murmushi tayi tare da gyara zamanta ta kalleshi gami da cewa.
   "Shikenan ina jinka.
  "Gobe in-sha-Allah za a kawo miki kayan lefenki ɗazu nayi waya da Aunty Farida ta ce ta kammala haɗa muku lefenku ke da Jeeddah, na ce ta kai ma Jeeddah kafin in dawo saboda haka kuɗi da zan tura miki hadda na ɗinki a ciki sai ki yi maneji kinsan gini nan da na ƙarasa wuta-wuta shi ya cinye min kuɗi.
   Har ya ƙarashe magana tana kallonshi yayin da annuri dake kan fuskarta ya gushe, wani irin mugun haushi ta ji ya turnuƙe ta lallai Bilal ya gama da ita hatta da kayan lefe 'yar uwar Jeeddah ce za ta haɗa mata wani ƙarin wulaƙanci kuma a kai gidanta. Cike da kissa ta shiga yi mishi godiya ko kaɗan bata bari ya fahimci cewa ranta ya ɓaci ba. Kaitsaye gida ya nufo yana tura ƙofar parlour ƙamshin girkin Jeeddah ya cika mishi hanci, direct kitchen ɗin ya nufa, tana tsaye tana haɗa coconut juice saboda shi ne favorite ɗin shi a hankali yake yawo da idanuwanshi akan tufafin jikinta half gown ce da kaɗan ta wuce gwuiwayinta, mai ɗauke da spaghetti hands sosai rigar ta bayyanar da surar jikinta ba ƙaramin burge shi tayi ba. Jin motsin mutum a bayana yasa ni juyowa a tsorace sai kawai nai arba da Love tsaye yana kallona da munafukai idanuwanshi, can ƙasan maƙoshi na ce dashi "Sannu da zuwa.
   "Yawwa Love ya gida?"
Ya amsa min cike da zumuɗi ban amsa mishi ba, na ci-gaba da aikina gani bai ga fuska ba yasa shi juyawa ya nufi bedroom kamar an ce na juya sai kawai idanuwana suka sauka akan kafaɗar rigarsa shatin jan baki na gani kasancewar kayan jikinshi shadda ce milk colour gaba ɗaya tayi wani irin mugun squeezing shiyasa ta bayyana da komai a fili, ni ba ƙaramar yarinya bace da zan kasa fahimtar hali da yake ciki gabana yai mugun bugawa da ƙarfi har sai da kaina ya sara a lokaci ɗaya nai wulgi da wuƙa da albasar da ke hannuna na bi bayanshi ji nayi raina na mugun tafarfasa har wani dishi-dishi nake gani ban taɓa jin bala'in kishi na fitar hankali iri yau. Da ƙarfi na banki ƙofa ta buɗe a tsorace ya juya saboda unexpected ya ji ta buge ƙofar, a hankali na bi tun daga kan fuskarsa da kallo har izuwa ga wandon jikinshi wanda ya ƙara gushe min da tantama ta tabbas Bilal Shattima ya yi having sex sama-sama nake jan numfashina yayin da nake kallonshi da idanuwana masu cike da zallar tashin hankali shima idanuwanshi suna kaina "Bilal!
Na kira sunanshi cikin wata irin murya.
   Bai amsa ba sai kawai ya tako da nufi kama ni kafin hannunshi ya sauka a jikina nasa hannuwana biyu na daki ƙirjinshi kana na ingiza shi baya saura kiris ya faɗi don sai da ƙafarshi ta hagu ta bugi gefen gado, ya yi ƙoƙari dafa bango cikin ihu na ce "Shikenan Bilal ka gama dani tabbas ka yi min tabo da ba zai taɓa warkewa a zuciyata ba...
  Na kasa ƙarasawa a dalili wani irin kuka da ya kubce min na durƙushe ƙasa da rarrafe ya iso gabana "Jeeddah Dan ALLAH ki saurareni...
  "Na saurare ka fa kace Bilal me zan saurara ka sani ci-gaba da kasantuwar mu a tare ya dogara ne da amsar da nake buƙatar ji daga bakinka shin ka yi having sex da Nusaiba ko ba ka yi ba?"
Bilal Shattima ya haɗiye wasu busassu miyau kafin ya ce "wannan wacce irin tambaya ce Love?"
   "Karka rena min hankali ka amsa min kawai.
   "Kin fi kowa sani Nusaiba ba ta tare ba taya zan kwanta da ita al'hali tana gidansu ko ɗakin uwarta kike so naje na haƙe mata saboda gani Bilal ɗin marasa kunya na duk duniya ko?"
   "Ƙarya ka ke yi Bilal wallahi-tallahi ka kwanta da mace koda ba Nusaiba bace amma tabbas hasashena gaskiya ne. Infact ga alamomi nan bayyane ga jikinka ga shatin bakin mace nan a ƙafaɗar rigarka tufafin jikinka sun yi squeezing alamar mace ta murje ka, iya son ranta ga kuma dry sperm nan a jikin wandonka dukka waɗannan alamomin za ka iya ƙaryata su?"
   Dafe kanshi ya yi ya rasa ta cewa yayin da na ci-gaba da wani irin gunji kuka mai cin rai "ka cuce ni Bilal ka ci amanata kai mugu ne azzalumi maha'inci wallahi ba zan zauna da kai ba ƙarshen zamana da kai ya zo.
   Na ƙarashe magana tare da miƙewa a fusace jiri yana ɗibata, na nufi ƙofar fita da sauri ya sha gabana idanuwanshi sun yi jajir "Ki yi haƙuri Love nasan ban kyauta miki ba amma inaso ki sani yanda ki ke matsayin matata haka ita ma Nusaiba, da ba ki hanani kanki ba da ba zan nemi ta ba har ta tare. Ta ya ina gani halak ɗina na ci-gaba da azabtar da kaina don kawai na faranta miki al'hali ke ɗin ba damuwa ki ka yi dani ba...
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*Assalamu alaikum*
*Shin 'yar uwa kinada labarin shararriyar Mai sayar da kayan gyaran Nan wato hjy*
*Madina Beauty Ventures** Hmmm *matso kusa Kisha labari ,wannan kamfani ya tanadar wa Mata Kayan gyara na* *musamman Wanda suka hada da kayan Mata masu kyu da inganci , Ƙarin Ni'ima, Ƙarin sha'awa,matsi da sauran su,akwai kuma* *supplements na gyaran jiki kama daga Ƙarin hips, Ƙarin kiba,gyaran skin sa haske da sheƙin fata duka Kuma Kayan su akan farashi ne Mai sauki ku tuntubemu a* *WhatsApp direct ta wannan link wa.me/2348037444722 or Call 08037444722*
*Ig_madina_beauty_ventures*
*Location _Birnin* *Kebbi,kebbi state*🤝

044..

Har ya dasa aya a zance shi ina aikin kallonshi idanuwana ne kawai ke yawo akan fuskarshi, amma a zahiri tuni na daina fahimtar abinda yake faɗa kawai dai naga bakinshi yana motsi muryarta a dusashe na ce "Tabbas Nusaiba matarka ce Bilal halali ka ce kana da damar da za ka sadu da ita a duk lokaci da ka so, to amma abin tambaya ana miyasa ka yi min alƙawari da kasan ba za ka iya cikawa ba miyasa Bilal ka yi min alƙawarin ba za ka yi min kishiya ba?"
Kai tsaye ya kalle cikin idanuwana ya bani amsa da cewa "Saboda Ina sonki ina kuma ƙaunar duk wani abu da zai sanya ki farin ciki, amma har ga ALLAH a can ƙasan zuciyata na ɗauki alƙawari ne ba don na cika ba nayi ne domin farin cikinki.
    Girgiza kai na shiga yi ina ja da baya gami da gunji kuka jin zuciyata nake yi tamkar za ta tarwatse kafin na ce "Idan nace da kai na tsane ka Bilal Shattima babu saura digon soyayyarka a zuciyata za ka yarda?"
Murmushin gefen baki ya yi gami da maƙe ƙafaɗa ya ɗage girar ido kafin ya ce "Zan iya yarda saboda azababben kishinki zai nuna miki hakan amma a can ƙasan zuciyarki ba haka bane.
   "Wallahi da gaske nake Bilal na tsane ka banaso ko kaɗan na buɗe idanuwana naga wannan mummunar fuskar taka ka cutar dani ka ɗora ni akan hanyar da ba za ta ɓulle dani ba. Na yarda da kai a makance ashe kai ba abin yarda bane, amma ba komai nima ka saurare abinda zai biyo baya don wallahi-tallahi ba kyale ka zan yi ba. Don sai na haddasa maka bala'i da masifa sai na hana ka jin daɗi rayuwa, in-sha-Allah ba za ka more amarci nan cikin daɗin rai da kwanciyar hankali ba.  Sai ka yi danasani cin amanata.
Ta ƙarashe magana gami da yi ƙwafa daga haka ta juya ta bar mishi ɗaki kitchen ta shiga duk abinci da ta ɓata lokaci ta girka masa sai da ta zubar da su duka cikin  dusbin, tana yi tana gunji kuka ta dawo tamkar mai taɓin hankali ko aljannu. Daga bisani ta faɗin zaune akan tiles ɗin kitchen ta haɗa kai da guiwa tana risgar kuka, bayan Bilal ya fito daga wanka ya sake shirya wa cikin blue color shadda ya fito riƙe da hularsa, kitchen ya leƙa ya ga hali da Jeeddah take ciki ga kuma yadda ta zubar da abinci shiru ya yi yana kallonta wani mugun haushinta ya kama shi can kuma ya yi gyaran murya gami da cewa "Jeeddah me kika aikata haka saboda zafin kishi za ki almubbazarar da abinci, kin kuwa san irin baƙar wahala da ake sha kafin a nemo shi?"
A mugun fusace na ɗago jajaye idanuwana na kalleshi dasu cikin hargowa na ce dashi "Ni kuwa nasan wahala da ake sha kafin a nemo abinci Bilal domin shekara ta uku ina ci da ƙartin banza wanda basu da halaccin zuri'ar butulci, ka ga kuwa na fi ka sani wahala da ake sha....
    "Jeeddah!
Ya kira sunana cikin kakkausar murya jikinsa har wani rawa yake yi nima na miƙe a fusace domin na ma fi shi hasala "Ko ƙarya nai muku ne Bilal Shattima gaba ɗayanku idan aka cire A'isha Shattima raguwarku kaji ne ku ci ku goge bakinku, ina mai tabbatar maka da cewa wallahi ba ku ci banza ba duk abinda ku ka ci nawa na rantse da girman ALLAH sai kun amayar dashi guntu ba zai zauna a cikinku ba.
  Murmushin gefen baki ya yi yana kallona da girar ido ɗage kafin ya ce "Ta nan kuma kika ɓullo to shikenan ba komai ai kina da damar yi duk abinda ranki yake so ba zan hana ki ba. Amma inaso ki sani ba zan lamunci faɗar maganganu banza akan ahalina ba. Gara tun wuri ki yiwa bakinki linzami.
   "Duk tsiyarka Bilal bai wuce ka sake ni ba abinda ba kasani ba a halin yanzu na fi ƙaunar saki da zama da munafiki wanda baisan darajar alƙawari ba. Sai yanzu na fahimci abinda Ya Haidar ya daɗe yana ankarar dani na kasa ganewa.
Ban yi tsammanin sako Ya Haidar a zancena zai harzuƙa Bilal ba ashe kishi ba ni kaɗai bace shima yana taɓawa domin kuwa wani irin taso min ya yi kamar zai rufe ni da duka sai faɗar yake "Ashe ba ki da mutunci Jeeddah da aurena akanki kina kira sunan tsohon saurayinki? To wallahi ba zan lamunci wannan iskanci ba.
   Duk da ina cikin tsanani ɓacin rai hakan bai hanani fahimtar kishi ne ya lulluɓe shi saboda haka nima na ƙudurta a raina sai na ƙunsa masa bakin ciki, don haka na kalleshi a ɗage na ce "ambatar sunan Ya Haidar yanzu na fara domin shi ɗin cikakken mutum ne yasan girman alƙawari shiyasa, lokaci da na nemi yai miki alƙawari ba zai min kishiya ba yaƙi a dalili yasan irin illar da ke tattare da ƙarya alkawari, saboda haka a gaban kowa zan faɗa da babbar murya Ya Haidar ya fi ka Bilal Shattima.
   Har na dasa aya Bilal Shattima yana kallona daga yanayi da yake kallona dashi na fahimci yanda ranshi ya kai ƙololuwa wajen ɓaci. Bai taɓa jin azababben kishi akan Jeeddah irin yau saboda haka ya haɗiye ɓacin rai nashi ta hanyar cewa da ita "Ki ci-gaba da ambatar sunanshi ba zai hana ki ba domin bakinki ne amma ki sani kina ambatawa kanki wutar jahannama ne. Ni ban yi aure don na ƙuntata miki ba na karo aure ne a dalili na gaji da cin tuwo ɗaya ina da buƙatar canji kuma ni ba pastor bane da zan ƙare rayuwa ta da mace guda. Gara ma ki shafawa kanki lafiya ki raba kanki da tunani wani Haidar domin har abada daga ke har shi ɗin ba za ku taɓa mallakar juna ba. Ni kuma ko yanzu ina da chance ɗin karo wasu biyu, na haɗa ki dasu dole kuma ki zauna dasu.
Yana ƙarashe magana yai tafiyarshi ya barni da dafin maganganu shi a kahon zuciya. Tabbas Bilal Shattima ya nuna min shi ɗin cikakken namiji ne to amma nima idan na kyale shi ban yiwa kaina adalci ba. Bedroom na shige na kulle kaina na dinga bitar kalamanshi ɗaya bayan ɗaya yayin da kowacce kalma tashi nake jinta tamkar ana yayyafa min tafasasshen ruwan zafi a zuciyata, kiran sallah magariba ne yasa ni tashi daga kwance da nake na shiga bathroom nayi alwala na fito, sai da na sallace sallar isha'i sannan na koma kan gado na kwanta.
Ta ɓangare Bilal Shattima da wani irin mugun haushin Jeeddah ya fita, a duk lokaci da ya tuna da ambatar suna Haidar Ka'oje da tayi sai yaji wani sabon haushinta ya lulluɓe shi. Kira Aunty Bahijja ya yi ya ce da ita gobe ta zo gidanshi ta ɗauki kayan lefen Nusaiba ta kai mata sosai Aunty Bahijja tai farin ciki da hakan domin tun lokaci da ta ji labarin Jeeddah har asibiti ta kwanta a dalili zancen auren Bilal take neman hanya da za ta haɗa su ta mayar mata da tsohon martani dake zuciyarta.
   Kwance nake sai tufka da warwara nake yi hanyoyin da zan ƙuntata wa Bilal nake nema, can kuma wani tunani ya faɗo min na tashi zubur, daga zaune da nake na buɗe bedside drawer na ɗauko zungurarriyar farar takarda da biro na shiga rubutu tun around 9 o'clock na fara rubutu sai 10:30pm na kammala na kalle rubutu da nayi na cika back and front na takarda sai kawai na saki murmushin mugunta, na linke takarda gami da ajiye ta akan drawer ɗin sai lokaci naji ƙarfi jikina har na fahimci ina jin yunwa na tashi da ɗan kuzarina na shiga kitchen na haɗa tea mai kauri ana cikin kitchen na tsaya na shanye tea ɗin, kana na koma ɗaki nayi wanka na shirya cikin sleeping dress na cotton gown, na sake bin gado nai kwanciyar ta misali ƙarfe 11:08pm daidai Bilal ya dawo, hatta da sallamar da ya yi ban amsa mishi ba shima daga haka bai ce min uffan ba har ya yi wanka ya shirya cikin kayan baccinsa ina kallonshi a ɗage, ya zauna daidai kusa da ƙafafuwana, sai da ya fesar da iska daga bakinsa kafin ya kira sunana "Jeeddah! Ki tashi zaune za mu yi magana.
Naƙi amsawa kuma ban tashi ba ya sake maimaitawa nan ma nayi biris dashi gani haka yasa ya tafi kai tsaye ga gundarin maganar da yake so ya yi min "Ki sami lokaci zuwa gobe ki yi min List na abubuwan da kike da buƙata  in-sha-Allah next week za mu tare a sabon gida, amma banda furniture saboda Aunty Farida zan turawa kudi ta zaɓar miki a plaza ɗinsu. Zan kuma turo miki da kuɗi ta account ɗinki sai ki yi amfani dasu ki kai ɗinki.
  Taɓe baki nayi gami da kallonshi na watsar, kafin na yunƙura na tashi zaune na miƙa hannu na ɗauko takarda da na rubuta domin shi na miƙa masa a wulaƙance.
  "Takarda mecece wannan?
   "Halan ba ka yi karatu bane da ba za ka buɗe ka gani ba?"
Na faɗa a yatsine sai da ya kalle ni kafin ya warware takarda ya shiga karantawa a natse can kuma ya ɗago idanuwanshi a razane ya kalle ni sai da ya ɗauki lokaci mai tsawo yana kallona kafin cikin harɗewar lafazi ya ce "Jeeddah me kike nufi da wannan dogon List ɗin naki?"
Danƙarerriyar harara na galla masa kafin na ce "ALLAH ya wadaran degree da ka yi Bilal Shattima tun da har ka kasa fahimtar wannan 'yar ƙaramar takarda...
   "Dallah dakata Jeeddah!
Ya katse ni a fusace kana ya zarce da faɗin "lissafi fa kika buga na duk wani abu da kika taɓa yi min tun daga farkon haɗuwar mu har kawo yau, aƙalla zan biya ki Naira miliyan goma Jeeddah yaushe kika kashi min maƙudan kuɗi har haka? Dan ALLAH ki dinga aiki da hankali banaso tadda zaune tsaye.
   Har ya kammala faɗar albarkaci bakinshi ina mishi kallon haɗari kaji, kafin na ce "Wallahi-tallahi Bilal muddin kana so zaman lafiya da kwanciyar hankali sai ka biya kudin nan idan ba ka biya su ta daɗin rai ba to za ka biya ta hanyar da ba ka yi tsammanin ba domin kuwa kotu zan maka ka.
   "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Jeeddah ba ki taɓa bani rance kuɗi ba ballantana ki kai ni kotu ko kin taɓa bani aro Kudi ne?"
   "Amma ai ka taɓa yi min sata ko ka biya ni wannan satar da ka yi min?"
Kalmar sata da ta ambata ta dake shi sosai don har sai da ya runtse idanuwanshi.
   "Karka manta ko machine ɗin da ka sayar a can baya ka biyawa Aunty Bahijja kuɗin surgery, bana ka bane bakada ko kwadala a ciki saboda haka a yanzu ina da bukatar a dawo min da dukiya ta kar fa ka manta kai yanzu mai arziki ne miliyan goma ba wata tsiya bace a wurinka.
  Zazzafar iska ya fesar yayin da gumi ya karyo masa ya shiga murza goshinsa kafin ya ɗago ya ce "Jeeddah ba ki taɓa ce min duk wahalhalu da ki ka dinga yi akaina zan biya ki ba?"
   "Kamar yadda ka faɗa alƙawari da ka yi min ba ka yi shi don ka cika ba nima kyautar ba da zuciya ɗaya na yi ta ba da manufar ba za ka yi min kishiya ba tun da haƙa ta bata cimma ruwa ba, kenan babu amfani na bar maka dukiya ta, idan ba a yi gwaɗo da yaro gara a bashi 'yar daddawar sa ya ƙara gaba. Da fatar ka fahimce inda zaurance nawa ya dosa?"
Shiru Bilal ya yi ga baki ɗaya ya zama speechless, ya ja gwaron numfashi gami da cewa "Ban taɓa gani mace mai azababben kishi irin ki ba Jeeddah amma ba komai zan biya ki kudinki sai dai yanzu banida su a dalili abubuwan da ke gabana amma in-sha-Allah idan nayi settled ba Miliyan goma ba ko duk abinda na mallaka kike so zan ba ki.
    "Mtsssss!
Na ja dogon tsaki tare da yi mishi kallo sama da ƙasa kana na taɓe baki kafin na ce "Yaushe ka yi arziki da za ka mallaka kawai ka turo min da kuɗi na shine kwanciyar hankali da zaman lafiyarka?"
     "Love ban ce ba zan ba ki kuɗinki ba amma a yanzu bani da su saboda tariya nan da za mu yi dole muna bukatar sababbin abubuwa....
   "Dallah saurara malam ni bana bukatar ko komai daga gareka kudina kawai nake so period!
"Shikenan zan ba ki.
Ya faɗa kai tsaye gami da miƙewa ya bar min ɗaki.
A washegari da sassafe ya fita don koda na falka daga bacci ya daɗe da fita, misali ƙarfe 11:00am ina kwance a parlour har zuwa lokaci zuciyata a cukushe take, na rasa abinda ke min daɗi a duniya wani irin ƙunci nake ji kamar daga sama naji ana bugun ƙofa da ƙarfi jiki ba ƙwari na miƙe na nufi ƙofar ina buɗewa nai tozali da Aunty Bahijja fuskarta cike da annuri sai fara'a take ban ce da ita uffan ba na juya na koma ciki parlour na zauna biyo ni tayi daga sama har ƙasa ta shiga ƙare min kallo kafin ta kece da dariyar mugunta. Sai da tayi mai isarta kafin ta ce "Daɗina da gobe sauri zuwa Hajiya Jeeddah sai kuma kika ji abin alkhairi da ya same mu ko?"
Ban ce da ita komai ba sai wasa nake da yatsuna yayin da zuciyata tai nisa wajen tunani wanne irin kalar rashin mutunci zan tata mata, sai kawai na tsikayi muryarta tana faɗin "Lefen Nusaiba na zo ɗauka duk nasan ba banza aka barshi ba shiyasa ya ba wa 'yar uwarki contract ɗin haɗawa Nusaiba lefe, sai dai duk tsaface-tsaface ku sun tafi a banza domin hakan bai hanawa Bilal ƙara aure ba.
    Da kyar na ɗago yayin da zuciyata ke tuƙuƙi na kalle ta da idanuwana da suka yi jajir, na miƙe tsaye jikina yana rawa cikin wata irin murya na ce "Aunty Bahijja ga lefen can ki ɗauka yanda akawo su ko kallon kirki ban mu su ba, ki yi gaggawa ki ɗauka ki barmin gidana idan ki ka sake ki ka kaini bango na rantse da ALLAH sai na sauya miki kamanu.
Na ƙarashe magana ina huci kamar zakanya da ke jin yunwa.
    Dariya reni wayau ta kwashe da ita ta kalle ni ta tofar da yawu tana faɗin "Duk abin da za ki yi min Hajiya Jeeddah ba za kai koda kwatankwacin rabin wanda ni nayi miki ba, ni fa na ri ga naci ki da yaƙi sai haƙuri ina fatar kina da labari jiya mijinki ya angwace da Nusaiba ya kwashi gara da garɗi da ba ki da irin shi...
Tun kafin ta ƙarasa rufe bakinta na miƙe tsaye a mugun fusace na ɗauke ta da gigitatcen mari, kafin ta dawo hayyacinta na rufe ta da bugu ta ko ina duka nake kai mata ina kuka irin mai masifar cin rai daga ƙarshe na falla da gudu na shiga kitchen na ɗauka wuƙa tana gani na dunfaro ta gadan-gadan da wuƙa tsirara a hannu ta kwasa da gudu ta nufi ƙofar fita....

*Dan ALLAH ku taimaka ku dinga taya ni sharing novel ɗinan, saboda ba kowanne group nake turawa ba kusan abin da yawa mutum ɗaya ba zai iya shi kaɗai ba*

Thanks one love#
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

💃🏻🔥 *INA MASOYA LITTAFIN RUD'ANI?*

*SHIN KUNADA LABARIN FREE PAGES SUN KARE NA LITTAFIN*
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
💥💧 *DA MA ACE...*

*SHIN KUNADA LABARIN HAZIK'AN MARUBUTAN NAN BIYU DA SUKAIWA KANSU LAK'ABI DA TAGWAYE BIYU SUNA NAN SUN YUNKURO DOMIN NISHADANTAR DAKU DA ZAZZAFAN LABARIN SU MAI SUNA👉🏼 DA MA ACE?.....LABARIN DAYA KUNSHI RAYUWAR MU TA YAU DA KULLUM LABARI MAI CIKE DA SOYAYYA DA NISHADANTARWA?LABARI MAI CIKE DA CAKWAKIYA DA SARK'AK'IYAR SOYAYYA AKAN MUTUM UKU DIK AKAN MACE D'AYA?LABARIN DA ZAI TAB'O MUKU SHARI'AR MUSULUNCI?SHIN KIN SHIRYA?KINSAN SUWAYE WAD'ANAN TAGWAYE BIYU?*

*TAGWAYE BIYU 2023*

*SLIMZY* Marubuciyar *RUD'ANI*

*FEEDHOM* marubuciyar  *ISHARA*

*MAZA HANZARTA KI SHIGA GANGAMI DA TAWAGAR WAD'ANAN HAZIKAN MARUBUTAN WAD'ANDA SUKE NISHADANTAR DAKU YANZUN HAKA DA ZAFAFAN LABARANSU MASU DADI FADAKARWA DA ILIMANTARWA DA NISHADANTARWA WATO  RUD'ANI DA KUSKUREN SO WAD'ANDA KE ZUWA MUKU A KYAUTA YANZUN HAKA*

MAZA KI HANZARTA KI BIYA KUDIN WANAN LITTAFI MAI SUNA *DA MA ACE* AKAN FARASHI 500 KACAL KISHA MADARAR SOYAYYA MAI RATSA ZUKATAN MASOYA....

DOMIN BIYAN KUDIN WANAN LITTAFIN KITURA TA WANAN ASUSUN BANKIN
👇🏻👇🏻👇🏻
9994468172
fiddausi musa
Access Bank

DOMIN TURA SHAIDAR BIYA TA WANAN NUMBER 08036953516 KO 07042276401

DOMIN TURA KATI TA WANAN NUMBER 08036953516

*TAGWAYE BIYU 2023*📢📢🔥

045..

Kafin hannunta ya sauka akan handle na danƙo wuyanta, ta baya na jawo ta da ƙarfi ina jan ta tana tirjewa, ni kuma ban fasa jan nata ba. Har mu ka dawo cikin parlour sannan na ingiza ta tai baya kamar za ta faɗi ƙafarta ta buge center table ta kwalla ihu. Dama Aunty Bahijja ba wani jikin kirki ne da ita ba irin su ne bahaushe ke ma laƙabi da ɓarna kiwo domin kuwa a bushe take jikin nan nata ƙamass yake, sai kace ƙamboli fara 'yar ƙarama da ita sai babbar azaba domin duk yanda ake azabtar da mutum matar nan ta azabtar dani ta hanani sukuni gaba ɗaya ta dungule min lissafi gami da harsuna min zaman lafiya. Saboda haka yau ALLAH ne kaɗai ya isa ya kwace ta daga hannuna batare da wani dogon tunani ba nayi kanta da wuƙa dake hannuna gani haka yasa ta shiga ja da baya wani irin mashahurin tsoro ya lulluɓe ta taga mutuwa ido biyu muraran, miyau bakinta ya kafe duk yanda ta so ta ba Jeeddah haƙuri bakinta yaƙi buɗewa balle har kalmar ban haƙuri ta fito daga cikinsa.
Sai kawai ta shiga dakatar dani ta hanyar buɗe tafukan hannuwanta, ban yi wata-wata ba na yanki tafi hannunta na dama ta kwalla mahaukaci ihu tana kururuwa neman agaji ban bari ta ƙarasa ihu da karuruwa nata ba, na sake yankar ta a damtse hannu, da ta fahimci da gaske rai da numfashinta nake farauta sai kawai ta zabura a karo na biyu ta kwasa da mugun gudu nima na dafe bayan ta, tana zuwa ta bugi ƙofar bedroom ɗina da dukkan ƙarfinta tana daff da shigewa ciki na sake yankar ta a gadon baya, duk da haka sai da ta rufa kofar inda ALLAH ya taimake ta akwai key saƙale a jikin ƙofar, sai kawai ta datse ƙofar zubewa ƙasa Aunty Bahijja tayi sai faman sauke numfashi wahala take yi kafin ta kai duba ga hannunta da ke tsiyayar jini ta ko ina raɗaɗi take ji yana ratsa ta, musanman gadon bayanta. Maraya kukan ta saki bata taɓa tsammani rashin hankali Jeeddah ya kai har haka ba.
Ina gani Aunty Bahijja ta rufu ƙofa har da murza key raina ya ƙara ɓaci na saƙale wuƙa a tsakani haƙorana na sama da ƙasa kana na shiga dukan ƙofar da dukkan ƙarfina da ALLAH subhanahu wata'ala ya albarkaci dashi, daga bisani na saki wuƙar tayi tsalle akan tiles ta bada wani irin sauti. Kafin na shiga faɗin "Aunty Bahijja ki buɗe ƙofar nan cikin lalama don ba abinda zai hanani aika ki gari da ba a dawowa kar fa ki bari na balla ƙofar nan na shigo na rantse yanda kika fitine rayuwata nima sai na datse miki taki.
   "ALLAH tsine miki albarka Jeeddah muguwa kawai baƙar 'yar ta'adda.
Cewar Aunty Bahijja cikin muryar kuka, yayin da hannunta da gadon bayanta ke fitar da jini ba na wasa ba.
   "Shikenan tun da ba za ki buɗe ba da kin buɗe da na rangwata miki kalar azabar da zan shayar dake amma yanzu nan zan nemo spare key na buɗe da kaina ina tabbatar miki a cikin ɗaki nan zan binne gawarki ko sallah ba za ki samu ba.
   Kowanne furunci da ke fitowa daga bakin Jeeddah Aunty Bahijja jin sa take ji tamkar ana ƙididdiga numfashinta ne, daga nan zaune ta saki fitsari gani ruwa yana fita daga ƙasanta yasa ta matsawa sai kawai taji ta zaune wayarta dake cikin aljihun gown ɗin ta. Hannunta yana makyarkyata ta ciro ta sau biyu tana zame wa daga hannunta tana faɗuwa kafin tai nasarar danno number Bilal inda ALLAH ya taimake ta shine last person da tayi waya dashi saboda haka kiransa ya zo mata a sauƙaƙe, tana ringing amma ba a ɗaga ba gashi Jeeddah sai bugu kofa take yi gami da furta mata razanannu kalamai.
   "Bilal Dan ALLAH ka dauka wallahi banaso na mutu a hannu wannan zautatciya matar taka.
Aunty Bahijja ta faɗa cikin sarƙewa numfashi, ci-gaba da kira Bilal tayi kusan kira haɗu tai mishi bai ɗauka ba. Ta kira wayar Hajja a kashe sai kawai ta sunne kanta tsakanin gwuiwayinta biyu ta saki kuka gaba ɗaya ta fidda rai ga rayuwa sai kawai ta ji wayar tai ringing a gigice ta ciro kanta ta kalle sensor din wayar tai tozali da suna Bilal ta rarumi wayar hannunta yana rawa ta danna kore madanni, kana takai wayar kunneta cikin fitar hayyaci take faɗin "Bilal Dan ALLAH ka zo ka taimake ni Jeeddah za ta kashe ni gaba ɗaya ta yayyanke min jiki da wuƙa jinin jikina zai iya ƙarewa a kowanne lokaci.
  Sosai Bilal ya tsorata a rikice ya baro Company ya nufo gida, tun a bakin Gate ya fara jin dukan ƙofar da Jeeddah take yi, saboda haka ya kwasa da mugun gudu ya tura ƙofar parlour. Jeeddah ya hango tsaye tana bugun ƙofa kamar zararriya sai faɗin take "Na gayamiki yau ni ce aljalinki a gidanan sai na faɗe ki da ranki ba dai kin ce Bilal ya kwashe gara da garɗi da ni ɗinan banida irinsa to kuwa in-sha-Allahu ba za ki sake ba wa wani mahaluki wannan labari ba don sai nayi gunduwa-gunduwa da naman jikinki....
  "Subhanalillah! Jeeddah kanki ɗaya kuwa kisan kai za ki yi?"
Bilal Shattima ya faɗa sa'ili da ya ƙaraso kusa dani, juyowa nayi na watsa masa idanuwana da suka yi jajir kamar mai cutar Apollo.
  "Idan har hauka ce ke saka mutum ya yi kisan kai tabbas na yarda na amince ni mahaukaciya ce, domin kuwa babu abinda nake da buri da ya wuce naga gawar Aunty Bahijja kwance cikin jini. Bilal banida maƙiyiya irin Aunty Bahijja wallahi ta zame min karan tsaye ta zama silar jefa ni cikin hali ƙaƙanikayi.
   Na faɗa a kausashe gami firfitowa da idanuwana waje.
Aunty Bahijja dake ƙargame a ɗaki jin murya Bilal yasa ta cewa "Bilal ka kira jami'an tsaro wallahi da gaske matar nan farautar raina take yi, ba ka yanda ta yayyanka ni ba sai rasa jini nake yi kira su Dan ALLAH kada jini jikina ya ƙarasa tsiyayewa.
Aunty Bahijja ta ƙarasa magana gami da ƙara rushewa da kuka.
Yanda Jeeddah ta ƙarashe magana tana zarar ido yasa Bilal Shattima birkicewa domin kuwa ba ƙaramin jefa shi cikin tsoro tayi ba. Har ya shiga wasi-wasi kodai tana da mutane ɓoye ne ko kuma da gaske ta haukace to kuwa ya zame masa dole ya lallaɓa ta don ya tsiratar da rayuwar Aunty Bahijja saboda haka ya kwantar da muryarshi a hankali kamar mai raɗa ya ce "Ki yi haƙuri Love ki yafe mata ko a haka ki ka barta taji jiki kuma na tabbata ko da kuɗi ba za ta sake shiga hurumin ki ba...
  "Ba zan haƙura ba Bilal har sai naga bayanta burina shi ne naga numfashinta ya fita daga gangar jikinta daga nan iyaso a rataye ni.
Jeeddah ta faɗa cikin hargowa a hankali Bilal ya shiga takowa har ya iso gabanta bata ankara ba yai mata kamun kazar kuku, ya cicciɓe ta da dukkan ƙarfi shi sai ihu take yi tana shusshura ƙafafuwanta "Ka sauke ni Bilal nace ka sauke ni to shikenan tun da ba za ka sauke ni ba na rantse kanka zan huce haushina.
Banza ya yi da ita sai da ya kai ta ɗayan bedroom ɗinsu ya sauke ta akan gado kafin tai wani yunkuri ya falla da gudu ya ciro key ya fita tare da saka key ɗin ya rufe ƙofar ta waje kana ya nufi ɗakin da Aunty Bahijja take wacce har ta fara gani dishi-dishi a dalili jini da ta zubar da kyar ta iya miƙewa tsaye ta buɗe ƙofa tana buɗewa ta faɗi ƙasa sumammiya. A rikice Bilal ya cicciɓe ta ya fita da ita da gudu yasa ta cikin mota ya ja ta da ƙarfi ya nufi asibiti mafi kusa, sai da aka yi mata ƙari jini a dalili ta zubar da jini ba kaɗan.
Sai da aka kammala treatment ɗinta ta sha ɗinkin kamar kwarya, kana ya nufo gida yana buɗe ƙofa Jeeddah tana zabura ta tashi da azamar ta, duk bala'i da masifa da take mishi bai kula ta ba sai da ya yi wanka ya ji shi cikin natsuwa kana ya shiga sauke mata nashi kalar rashin mutunci ya faɗi ta faɗi Saboda haka tai masifar ƙular dashi suka rabo baram-baram don har tabbatar mata ya yi da cewa idan wani abu ya sami Aunty Bahijja sai ya ɗauki mummunan mataki akanta. Yana fita kaitsaye gidan Aunty Farida ya je ya zayyane mata hali da ake ciki  lokaci da Aunty Farida ta ji iri ta'asar da Jeeddah ta aikata ba ƙaramin  gigicewa tayi ba. Saboda haka ta yanke shawara gara taje gida ta sanar da Baba abinda yake faruwa gudun kada al'amari ya yi ƙamari gara tun wuri yai wa tufkar hanci.
Har sha ɗaya dare ta gota Bilal bai dawo gida ba duk sai naji ba daɗi don na tabbata ni ce silar rashin dawowar tashi, sai kawai na shiga saƙe-saƙe idan har ba wani mummunan abu bane ya sami Aunty Bahijja, nan take na wani irin mashahurin tsoro ya lulluɓe ni, naji nadama haɗe da danasani abinda na aikata, duk da haka bana jin zan iya ɗaga waya na kira shi. Sha ɗaya da rabi tana bugawa na kashe kayan kallo na wuce bedroom na kwanta amma na ƙasa bacci.
Ta ɓangaren Bilal Shattima kuwa ƙarfe tara ya baro asibiti yayin da Hajja taci masa mutunci faɗa ta dinga yi ba na wasa ba don har cewa tayi sai ya saki Jeeddah, Bilal yana gani al'amari yana so ya ƙazanta ya baro asibiti. Kaitsaye gidan su Nusaiba ya nufa kamar dai wancan lokaci da suka sha shagalinsu a ɗakin Yayanta Sageer yau ma hakan ce ta faru a tsakaninsu, sun murji juna iya son ransu domin a wannan karo Bilal biye mata ya yi domin kafin ya taho sai da ya siye magani ƙari ƙarfi ya sha, sai da suka yi fourth round duk da haka Nusaiba bata gamsu ba so take ya ƙara mata shi kuma a lokaci ƙarfinsa ya gama ƙarewa hatta da abin nashi ya yi laushi, magani ya gama aiki duk jarabarta ba zai sake aikatuwa ba. Sai da ta jira gaba.
In takaice muku labari ranar sai ƙarfe ɗaya dare ya dawo gida, kuma har zuwa lokaci idanuwana biyu domin na kasa bacci. Yana switch on ɗin bulb haske ya gauraye ɗakin karaf idanuwanmu suka sarƙe, a hankali na bi shi da kallo yanda ya shigo min da tufafi duk squeezing a wancan rana yau ma haka ya dawo min, zan ma iya cewa na yau sun fi muni wallahi za ku zaci da kura ya yi dambe domin hatta da tazuge wandonshi ja take a ƙasa idanuwanshi sun yi masifar ja ko kaɗan ban yi tunani zai tarar dani a falke ba. Yadda ya ga ina ƙare masa kallo daga sama har ƙasa yasa shi jin wani iri ga baki ɗaya ya dabirce sai kuma ya tuna da irin ta'asar da tayi sai kawai ya haɗe rai ko kallonta bai sake yi ba
Nima tun da daga sau ɗaya da na kalleshi na kauda fuska ban kuma ce dashi uffan ba tsakanin da ALLAH ba zan ɓoye muku ba nagaji da musanya yawu da Bilal, na tabbata idan na ce zan kula shi da matuƙar wahala idan ban ɗuɗɗura masa ashar ba. Saboda haka na runtse idanuwana gam ban sake marmari kallonshi ba. Ban ma san lokaci da ya gama tsayuwar sa ya shiga bathroom sai saukar ruwa naji, don na gushewa kaina tantama abinda nake zargi sai kawai na sauko na nufi ƙofar bathroom ɗin cikin sa'a na tarar da bai rufe kofar ruff ba, na ɗan ƙara buɗe ta na leƙa ina kallonshi har ya kammala wanka sabulu kana ya fara na janaba, da sauri na baro jikin ƙofar na koma kan gado na kwanta na ja duvert na tattake cikinsa hatta da fuska ta ban barta a waje ba. Kana na shiga furzar da iska mai zafi gaske.
Bilal ya fito ɗaure da towel yayin da yake riƙe ɗan ƙaramin towel ɗin yana goge sumar kanshi, gani yanda ta lulluɓe cikin duvert yasa shi jan guntun tsaki, cikin rashin damuwa da hali da ya ganta ciki ya shirya cikin kayan baccinsa ya ɗauki pillow ya fito parlour.
Yanda naga rana haka naga dare ban runtse ba ko kaɗan, ina kammala sallar asuba har na kwanta sai naji ƙarar shigowar message a wayarshi da ya bari akan mirror, banaso duk abinda zai taƙura ni ko ya hanani bacci saboda haka na sauko na ɗauki wayar da nufi nasata silent sai idanuwana suka sauka akan message ɗin "Good morning Baby da fatar ka waye gari cikin ƙoshin lafiya ya gajiya daren jiya?" Duk da ina da tabbaci gajiya tabi jiki domin kai jarumi ne. ALLAH Baby jiya ka shayar dani daɗi marar misaltuwa ka buɗe data na turo maka da good morning pics I hope I'll enjoy it...
Kasa ƙarasa karantar message ɗin nayi a dalili wani ɗan uban jiri da ya kwashe ni, da baya-baya na dinga tafiya har sai da na kai ga gado na faɗin zaune dabass! A maimakon na ajiye baƙar waya nan sai kawai na tsinci kaina da son gani wane iri pics ne ake wa laƙabi da Good morning, already nasan code ɗin shi shiyasa kaitsaye na shiga WhatsApp ɗin shi. Bayan messages sun ta shigowa sai na ga na Nusaiba, ashe nudes pics ne ta turo mishi hannuna har wani rawa yake yi wajen buɗe hotunan na farko boobs ɗinta ne sai na biyu mai ɗauke da private parts ɗinta bansan lokaci da bakina ya furta "Wa'iyazubillah! Ashe da gaske ne akwai matan aure da ke turawa mazajensu hotunan tsiraicin su?"
Na faɗa cike da mamaki, rubutu da ke kasan video na karanta "Baby styles ɗinan irinsu nakeso mu yi anjima please don't say no.
Jikina ya yi bala'in sanyi wani irin tsoron mahalicci sammai bakwai ya shige ni, sannu a hankali na maida wayar inda na dauko ta ashe ko Baba da Babansa {lol}
Ina maida kaina jikin pillow yana shigowa abu na farko da ya fara yi shi ne daukar wayarshi, already ya shirya tsaf cikin English wears da alamu ɗayan bedroom ya shiga ya yi wanka, dama kuma muna da kayan sawa a ciki, ci kanki bai ce dani ba yana ɗaukar tsananniyar wayarshi ya fice abinsa. Zuciyata ta shiga kimtsa min yanzu can ya nufa wurinta su gwada styles ɗin da ta turo mishi, take naji wani zazzafan kishi ya lulluɓe ni, kuka nakeso yi amma na nemi hawaye na rasa ashe ko kuka rahama ne.
Zuwa yanzu gaba ɗaya naji Bilal Shattima da aurensa sun fita a kaina a yanzu banida buri da ya wuce ya rabani da ƙaddararre aurensa, domin wallahi ba zan iya zaman kishi da karuwa ba. Yoo! ALLAH na tuba miye banbamci Nusaiba da tamtagarya karuwa mai license a hannu.
Waya ta da ke karkashin pillow ringing ɗinta ya datse min tunani ni kaɗai nasan irin mugun raɗaɗi da nake ji a zuciyata shiyasa ban yi sauri ɗaukar wayar ba har ta tsinke aka sake kira jikina a mace na janye pillow na ɗauki wayar Baba ne mai kira nawa sai da gabana yai mummunar faɗuwa ina daga kira ko sallama da gaisuwata Baba bai amsa ba naji muryarshi a fusace ya ce dani "Duk abinda kike yi ki ajiye shi ki zo yanzu-yanzu nan Inaso gani ki.
Kafin nai wani yunkuri har ya katse kiran. Da na tuna danye aiki da na aikata jiya sai jikina ya ɗauki rawa, a tsorace na shiga bathroom nayi wanka wanda ba zan iya tantance ko na saka sabulu ko ban saka ba.
Ina tsoro karo da Baba domin na tabbata da wahala mu wanye lafiya, duk iskaci da iya shegena ina tsoro Babanmu tsoro kuwa ba na wasa ba.
Wallahi ko mai kasa shafawa nayi kawai dai na dauko Turkish Abaya mint green color na saka ba ko bra na yane kaina da mayafi mahadin rigar.
Tsabagen hankalina ya rabu kashi-kashi na manta inda na ajiye car key ɗina, har na haƙura da nema nayi deciding na hau adaidaita sai kawai na ganshi a parlour ajiye akan centre table, sai da na sauke zazzafar ajiyar zuciya kafin na ɗauki key ɗin. Da za ku tambaye ni yanda nayi tuƙi da wuya na iya faɗa domin kuwa ikon Rabbi ne kaɗai ya kawo ni ƙofar gidanmu.
   Ina fitowa daga mota tun kafin na maida murfi na rufe idanuwana suka yi tozali da motar Aunty Farida, nan fa na ƙara ruɗewa cikin sauri na maida murfi na rufe ashe na haɗa da rigata bansani ba, sai da na tunƙari kofar shiga gida naji anyi baya dani. A mugun tsorace na juya sam ban kawowa raina cewa rigata ce na dantse ba, sai naji kamar an shaƙe ni ne, na sake unlock ɗin motar na ciro rigar inda ALLAH ya taimake ni bata yage ba. Na sake kwasawa da sauri na shiga gida, kaitsaye parlour Babanmu nai yiwa tsinke,  turus nayi na kasa shiga parlour a dalili hango fuskar Babamu a mugun ɗaure iya sani na da Baba ban taɓa gani ya yi fuskar shanu kamar wannan ba, cikina ya yi bala'i murɗawa dama na kwana biyu ban sa mishi abinci kirki ba.
   "Shigo don ubanki ko ni na taso da kaina!
Furunci da Babanmu ya fara jifa ta dashi kenan,  ba yanda na iya dole na fara tattaki har na iso gabanshi na zube gwuiwayina ƙasa, da durƙusawa ta da saukar tafin hannun Baba akan kumatuna kusan a tare suka faru....

*Mu haɗu a shafi na gaba*

_please don't forget to share and comments on_

#Jeeddah Aliyu
#Team Zazzafan kishi.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*Assalamu alaikum barkanmu da warhaka*

*Ina masoyana wanda suka karanta littafin BIBIYATA AKEYI 🤝 WANNAN SALON SHEKARAR 2017 NE, YA KUKAJIN LABARIN? NASAN DA YAWANKU BAKU MANTASHI BA!*

    *TO MASOYA GANI NAN NA KAWO MUKU WANI ZAZZAFAN LABARI MAI CIKE DA SALO KALA KALA!!! WANNAN SABON LABARI SHINE BIBIYATA YAKEYI(WAYESHI).*

   *WANNAN SALON 2023 NE! SABON LABARI SABON SALON LITTAFI DABAN YAKE DANA BAYA BIBIYATA AKEYI!*

  *BIBIYATA YAKEYI(WAYESHI) PAID BOOK NE BA FREE BA.🤝*

*TURA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT D'IN.*

*ACCOUNT NUMBER:-0003075326 ZAINAB M BAWA*
*Jaiz bank SHAIDAR BIYA TA 08161146563.*

*KO KATIN MTN TA WANNAN LAMBAR 08161146563 TARE DA SHAIDAR BIYA.*

*SANNAN NAYI ADDING D'INKI A GROUP.. GA WACCE BATADA BUKATAR SANYATA A GROUP 400 ZAKI BIYA KULLUM ZAKINA SAMUNSA DA PC DA ZARAR ANSAKE.*

047..

Cikin tsanani tashin hankali na yada ganina akan Hajja yadda ta taƙarƙare tana rantsuwa sai Bilal ya sake ni ko ta tsine masa. Ba ƙaramin kaɗawa hanta cikina tayi ba. A kiɗime Bilal ya zo gaban Hajja ya zube gwuiwayinsa kana ya haɗe hannuwanshi yana faɗin "Ki dubi girman ALLAH Hajja ki janye wannan furunci naki Inaso matata ita ma tana sona na roƙe ki kada ki cilastani na aikata abinda zai wargaza min rayuwa...
   "Rufe min baki sakarai kawai!
Hajja ta daka mishi rikitatciyar tsawa kana ta ci-gaba da faɗin "A yanda na sha alwashi sai ka saki tsananniyar yarinya nan magiyarka ba za ta canza min ƙudirina ba. kwata-kwata ma banga amfani zamanka da ita ba. Kai har yau ka kasan fahimtar ba son tsakani da ALLAH take maka ba. Tun daga ɗa ɗaya cal! Da ta haifa maka ta zarge bakin mahaifarta kuma tsabagen mugunta irin na iyayenta ƙiri-ƙiri suka raba ka da ɗanka kai dashi sai hange daga nesa.
  "Hajja wannan hujjar bata kai matsayi da za ki dogara da ita ki cilastani na saki matata ba.
   "Wallahi-azim sai ka sake ta matuƙar ni ce na tsuguna na haife ka sai ka saki Jeeddah a yau ɗinan.
Hajja ta katse shi cikin tsawa da hargowa gani yadda take ta shan rantsuwa yasa Bilal Shattima fashewa da kuka duk jarumta irin ta ɗa namiji da aka san shi da ita Bilal ya nemi ta shi ya rasa a hankali na dinga tafiya da baya-baya har na ƙure a jikin bango na jingina bayana domin ƙafafuwana ba zai su iya ci-gaba da ɗauka ta ba. Tsawon rayuwata ban taɓa shiga tashin hankali ba irin wannan, na dawo tamkar gumki gani dai a tsaye amma na kasa tantance wacce duniya nake ciki sai rarraba idanuwana nake yi daga kan love zuwa ga Hajja kana na dawo kan Aunty Bahijja tun ina fahimtar zantuka da suke musanya a tsakaninsu har na dawo sai dai naga bakunansu na motsi.
  Duk roƙon da Bilal yake yiwa Hajja sai dawo tamkar yana ƙara zuga ta ne don sai rantsuwa take yi maimaita wa idan har bai sake ni ba za ta kwashe masa albarka, kuka Bilal Shattima yake yi haiƙan gani hali da ya shiga yasa nima durƙusawa na shiga bata haƙuri "Dan ALLAH Hajja ki yi haƙuri kada ki tarwatsa mana rayuwar aurenmu...
   Tun kafin na ƙarasa magana ta katse ni ta hanyar daka min tsawa "Yi min shiru munafuka mai baƙar anniya yau ƙarshen zamanki da ɗana ya zo tsinaniya kawai.
  Ba zan iya jure jin waɗannan kalamai ɓatatci ba zuciyata ba za ta iya ɗauka ba saboda haka na tashi daga durƙuso da nayi yayin da Aunty Bahijja ta bini da zagi, ban kulata ba na koma jikin bango na lafe Bilal ya daka mata tsawa yana faɗin "Ya isheki haka Aunty Bahijja karki sake na daina gani girmanki kwata-kwata.
  "Bahijja sa'arka ce da za ka dinga yi mata barazana to bari ka ji matuƙar kana so albarkata ta ci-gaba da bibbiyarka ka bi umarnina.
  "Hajja Dan ALLAH ki yi haƙuri wallahi ba zan iya sakin Jeeddah ba....
   "Ka sake ta Bilal ko na tsine maka.
Hajja ta katse shi a fusace domin ya kai ta bango.
  "Ba zan iya ba Hajja wallahi inaso matata.
"Na ce ka sake ta Bilal wannan shi ne kashedina na ƙarshe idan ba ka sake ta ba Wallahi-azim zan tsine maka.
  "Hajja Dan ALLAH kada ki tsine min...
"To ka sake ta idan ba ka so tsinuwata.
Sunkuyar da kai Bilal Shattima ya yi, yayin da yake wani irin gunji kuka irin mai azabar cin rai ɗinan kafin ya ɗago idanuwanshi ya kalle Jeeddah da ke lafe ga bango tana shasshekar kuka, wani irin mugun sonta ya ji ya mamaye ciki da waje zuciyarshi, kana ya dawo da ganinshi akan Hajja ya ce "shikenan Hajja zan sake ta amma kafin sannan ina neman alfarmar da ki janye zance saki uku ɗinan domin gujewa faɗawa fushin ubangiji..
   "Karka sake ka yi min wa'azi anan wuri ka bi umarnina shi ne zaman lafiyarka.
  "Hajja saki uku ya yi yawa ko a addinan ce ba a so kada ki yi min umarni da abinda zan dawo ina danasani akansa. Idan na sake ta saki ɗaya daga baya idan kin huce Hajja sai in dawo da matata domin ina sonta.
   "Wato ba za ka bi umarni nawa ba kou? To shikenan tun da ka zaɓi tsinuwata dama can ba kai kaɗai na haifa ba saboda haka Bilal ALLAH ya ts....
Kafin Hajja ta ƙarasa tsine masa yai sauri furta.
   "Jeeddah na sake ki saki ɗaya saki biyu...
kasa ƙarasawa ya yi kuka ya ci ƙarfinsa cikin ɓacin rai Hajja ta kalle shi tare da faɗin "ka ƙarasa saki ɗayan mana na fa rantse saki uku za ka yi mata kuma a rubuce na ke buƙata ba a baki ba domin za ka iya dawowa daga baya ka ƙaryata ita kuma ba cikekken imani ne da ita ba za ta goyi bayanka ku dawo kuna zaman dadiro saboda haka rubuta mata a takarda ta kai ma iyayenta shaida.
   Sulelewa nayi ƙasa na runtse idanuwana yayin da nake ji wani irin tuƙuƙin baƙin ciki yana bin zuciyata, can sama-sama nake tsikayar murya Bilal yana faɗin "Hajja banida takarda balle biro biyu ma da nayi mata ya wadatar.
  "A gareka ya wadatar amma a gareni tamkar na kashe maciji ne ban sare kai ba saboda haka a shirye na zo Bahijja bashi biro da takarda da na riƙo masa.
Aunty Bahijja ta zuge jakkata tana murmushi mai cike da zallar farin ciki ta fiddo da biro da takarda ta miƙawa Hajja kana Hajja ta miƙawa Bilal, tana faɗin "Ai saboda gudun irin haka yasa na zo da shirina maza rantaɓa mata uku cur! Ka yadda kwallo mangwaro mu ma mu huta da kuda kafin ya karɓa sai da ya kalle ni  zuciyarsa tana bugawa da mugun ƙarfi ya shiga rubutu yana kammalawa ya mike ya shige bedroom da sauri. Aunty Bahijja ta zo da sauri jikinta har rawa yake yi ta ɗauki takardar ta shiga karanta wa tana kammala wa ta saki ihu da shewa kana ta zarce da rangaɗa guɗa "Hajja yau ALLAH ya raba mu da alaƙaƙƙai aje can a bi wani sarki ba dai na garin mu ba karɓi nan annoba Bilal dai ya cika aiki ya rangaɗa miki saki uku, daga yau kin bi sahun zawarawa Sakkwato.
Ta ƙarashe magana tare da jefa min takardar akan fuskata.
   "Aiki ya kammala zo mu tafi Bahijja.
Hajja ta faɗa tana kamo hannun Aunty Bahijja.
  "A'ah! Hajja da saura dai gara mu tusa ƙeyar Bilal gaba tun da nan gidan ba nashi bane gara ya tattara abinda yake mallakinsa mu tafi gudun kada 'yan uwanta su zo su yi masa tozarci kinsan shi ɗin ba zuciya ce dashi ba.
  "En! Kuma kina da gaskiya zo mu je ɗakin gara ya bar mata tsinane gidanta da take yiwa mutane gaddara akansa.
Daga haka suka nufi cikin ɗakin baccinmu bansan ya aka yi ba sai ga su sun fito tare da Bilal ko tsinke bai ɗauka ba Bilal ya nufi gun da nake a zaune ya durƙusa a gabana cikin muryar kuka ya ce "Ba don bana sonki ba na sake ki ba na saki ne a bisa cilastawar mahaifiyata, na bi umarninta ne domin gujewa tsinuwarta ina kuma ƙaunar na ci-gaba da kasancewa ɗa mai biyayya a gare ta, ina kuma son ki sa aranki sonki yanzu na fara idan mutum ya cika ya zo ya cire min. Raba aurenmu ba shi bane datse soyayyar dake tsakaninmu, lallai zan tabbatar miki da cewa ni Bilal Shattima mai ƙaunarki ne na haƙiƙa.
Daga haka ya juya ya nufi ƙofa fita da kyar na yunƙura na tashi tsaye domin gaba ɗaya jikina jin sa nake yi kamar bani da lakka, Aunty Bahijja ta kalle ni ta kwashe da dariya tana faɗin "ai na gayamiki Jeeddah ki bi ni a sannu domin ni kwalki ce daidai ƙugun kowa. Kin ga dai yanda na gama da babinki cikin sauƙi da sauƙaƙawa da fari sai da nasa mijinki ya yi miki kishiya a maimakon ki fahimci girman izzata gami da ƙarfin ikona da yake ke daƙiƙƙiya ce sai ki ka sake yi min abinda ya uzirani har sai da na daddatsa igiyar aurenki ba fa guda ɗaya ba duka uku na tsitsika su kamar ana tsika igiyar shanya.
Ta ƙarashe magana gami da yi min kallon sama da ƙasa ta watsar duk da ina cikin yanayi marar daɗi amma hakan ba yana nufi ba zan iya mayar mata da martani ba, saboda haka cikin dusashewar murya na ce "Tabbas kin zama silar rusa tubalin rayuwar aurena amma ina so ki sani Aunty Bahijja lallai sai na zame muku karan tsaye a rayuwarku muddin ina nunfashi rabani da Bilal sai ya zame muku bala'i da masifa ba kun kirani da annoba ba tabbas za ku ga annoba gani idonku, domin daga ke har wannan tsohuwar banzar sai na saka ku kuka da hawayenku.
   A Hajja ta yo kaina da nufi rufe ni da duka domin ita Aunty Bahijja ta gama sani hatsari dake tattare da tunƙaro ni gaba gaɗi shiyasa ko kusa ba ta gwada yi wannan ganganci ba. A fusace kuma ciki ɗaga murya na ce "Kul! Karki soma gwada wannan ganganci idan ki ka sake hannunki ya sauka a jikina na rantse sai na nuna miki tsagoro jahilci, dama can ina girmama ki ne a dalili auren ɗa ki da yake kaina kin kuma ri ga da kin datse shi a yanzu babu komai a tsakanina dake kina gwada dukana sai na ƙarya miki hannu kuma maza ku tattara ku fi ce min daga gida tun kafin na nuna muku nawa kalar iskanci shegu matsiyata wanɗada basu gadi arziki ba. Idan har kun cika 'ya'yan shegu a ɗaurawa ɗaya daga cikinku aure da Bilal.
   "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Jeeddah ni fa mahaifiyar Bilal ce wannan kuma yayarsa uwa ɗaya uba ɗaya don tsabar ɗibar albarka ki ke danganta mu da aurensa  lallai Jeeddah ke ɗin ba ɗiyar arziki bace.
Hajja ta faɗa tana matsar idanuwa Aunty Bahijja ta kama hannu Hajja tana faɗin "rabuda ita Hajja zo mu tafi kinsan zafi da muka haɗa mata ba na wasa bane da alama nan gaba kaɗan haukacewa za tayi.
   "Uwarki ga ta nan gabanki tsaye ita ce za ta haukace.
Na faɗa ina sauke numfashi da kyar ba su ƙara kula ni ba suka fi ce abinsu, ban tabbatar da ingancin maganar Aunty Bahijja ba sai da suka tafi na zube ƙasa na rushe da wani irin kuka ina yi ina duka fuskata don gani nake yi kamar a mafalki ne abubuwa nan suka wakana dukan da nake yiwa kaina ina yi ne domin na falka sai da naji zafin dukan ya ratsa fuskata sai na fahimci duk abinda ya faru a zahiri ne ba a mafalki ba. Na yi kuka tamkar hawaye idanuwana za su kafe babban tashin hankalina bai wuce furuncin Baba akaina ba. A duk lokaci da na tuna sai na ƙara gigicewa na rasa tudun dafawa har aka yi sallar Azhar ina kwance akan tiles idanuwana sun yi luhu-luhu ga baki ɗaya na fita hayyacina, da kyar na tashi na shiga bathroom na watsa ruwa kana nayi sallah nan take zazzaɓi mai zafi ya rufe ni. Na tashi na hau gado na kwanta na lulluɓe jikina da duvert fuskata kaɗai na bari a waje daga nan bacci wahala ya ɗauke ni.
Ta ɓangaren Bilal yana fita ya shiga motarsa da mugun speed ya bar unguwar kaitsaye gidan abokinsa Abbas ya nufa, a lokaci da ya yi arba da Abbas zubewa ya yi a gabansa ya fashe masa da kuka kamar ƙaramin yaro, sosai hankali Abbas ya tashi gaba ɗaya ya bi ya ruɗe shi ma durƙusawa ya yi ya riƙo kafanɗun Bilal yana girgiza shi "Subhanalillah! Shattima kuka me ka ke yi rasuwa aka yi ne waye ya mutu Please Shattima ka yi magana mana?"
Kusan a jere Abbas ya watsawa Bilal waɗannan jeri tambayoyi.
   "Shikenan na rasata na rasa Jeeddah Abbas Hajja ta cilastani na saki Jeeddah saki har uku.
Ya ƙarashe magana tare da sake rushewa da sabon kuka har yana haɗawa da shassheka.
   "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Hasbunallahu wal-imaal wakeel! Amma kuwa Hajja bata kyauta ba me ya yi zafi da za ta yanke hukunci irin wannan?"
   "Bari kawai Abbas Hajja ta gama da rayuwata ta rabani da matata adaidai lokaci da nake da burin kyautata mata. yanzu wani irin kallo take so mutane su dinga yi min? Na tabbata da yawa sai sun zarge ni da rashin yiwa Jeeddah adalci mace da ta zauna dani banida ko kwabo ta dinga faɗi tashi akaina, yanzu da ALLAH ya azurta ni a maimakon na saka mata sai kawai aji na ƙara aure baya nan kuma na sake ta saki har uku, wallahi Abbas duk wanda ya ji wannan labari dole ya tsine min.
   Hannunshi Abbas ya riƙo ya miƙar dashi tsaye kana ya nufi cushion ya zaunar dashi, sa'anan shima ya zauna ya dafa ƙafadarshi "Ka yi haƙuri Shattima ka ɗauki wannan al'amari a matsayin ƙaddara iya adadin zaman da ALLAH ya tsara a tsakaninku kenan. Sai dai kai ma Bilal ka yi ganganci da ta kafe lallai sai ka saki Jeeddah sai ka yi saki ɗaya mana amma saki uku sai ka ce jahili ka sani babu biyayya ga Iyaye wurin saɓawa Ubangiji. Duk da ALLAH ne ya halatta saki amma ba irin wannan ba. Yanzu gashi tun ba a je ko ina ba ka fara kuka ba mu san abinda zai faru anan gaba ba. Iya abinda zan ce da kai ka yi haƙuri kuka ba zai dawo da aurenku ba. Ka rungume ƙaddara da ta Kunno muku. Jiya-jiya nan fa ka biya mata makka sai ga wannan al'amari ya faru.
  "Uhmm!
Bilal ya faɗa yana mai dafe goshinsa.
Sai bayan sallar la'asar ya nufo gida ban yi tsammanin zan tarar da Jeeddah a gidan ba. Yana shiga bedroom ya yi tozali da ita tana sharar bacci daga yanayi da ya ga numfashinta yana sauka ya fahimci bacci wahala ne take yi, ƙura wa fuskarta idanuwanshi ya yi yana kallonta, tsanani tausayinta gami da soyayyarta suka lulluɓe shi kusa da ita ya nema ya zauna ya ciro hannunta daga cikin duvert ya matse cikin nashi ya ɗauki dogon lokaci yana aiki kallo hawa da saukar numfashinta kafin ya miƙe ya shiga bathroom ya yi wanka yasaka jallabiya ya fice zuwa parlour, ya kira royal cuisine restaurant ya yi mata order abinci saboda yasan throughout ba abinda taci.
Kiran wayata ya falkar dani daga bacci da ya dauke ni wani irin sarawa kaina ya yi na sauko daga gado dafe da goshi na ɗauki wayata dake aje akan mirror, wani irin mugun faɗuwa gabana ya yi a dalili Aunty Farida ce mai kiran nawa, har kira ya tsinke ban iya ɗagawa ba. Na bi agogon wayar da kallo ashe na ɗauki lokaci kwance ina bacci domin ƙarfe 5:40pm da sauri na ajiye wayar na nufi bathroom na sake watsa wa jikina ruwa ko zan ji kuzari, har na kammala sallah Aunty Farida tana kirana cike da ƙarfin hali na ɗauki kiran nata "Wai ke ina kika shiga ne ina ta kira ba ki ɗaga ba?"
  "Ki yi haƙuri Aunty koda ki ka kira ina bacci bari nayi sai nayi sallah na bi kiran naki sai gashi kin sake kira ya gida da yarana?"
   "Lafiya qalau suke naso ki zo yanzu mu je ki zaɓi  furnitures ɗin da ki ke so.
Jin abinda ta faɗa ya ƙarya min da zuciya na fashe da kuka mai sautin gaske duk tambayar da ta ke yi min kasa faɗa mata dalili kukan nawa nayi, daga ƙarshe ma sai dantse kira nayi na kifa kaina a gefen gado na ci-gaba da kuka na. Sautin kukanta da Bilal Shattima ya ji daga parlour yasa shi nufo cikin bedroom ɗin.
   "Love ki yi haƙuri ni kaina nayi kuka nan har na gaji dole na rungume ƙaddara.
  Jin muryar Bilal a bayana yasani ɗagowa da sauri domin bansan cewa yana cikin gidanan ba. Aunty Farida bata haƙura ba ta sake kiran wayata ina kallo Bilal ya ɗauki wayar ya gayamata ga mu nan tafe gidanta.
  "Love tashi ki shirya na kai ki gidan Aunty Farida domin hatsari da ke tattare da ci-gaba da zamanmu a gidanan.
Ban ce da shi uffan ba na miƙe tare da sake zura hijabina na sallah na fice ina mai ci-gaba da rera kuka.
  Har muka iso gidan Aunty Farida Bilal yana aiki rarrashina amma kamar ƙara ingiza ni yake yi, da sauri na ɓalle murfi mota na fita na kwasa da gudu na shiga entrance ɗin gidan a parlour na tadda aunty Farida ina zuwa na faɗa bisa jikinta ina gunji kuka Bilal Shattima ya shigo da sallama yayin da hankali Aunty Farida yana kaina shiyasa bata sami damar amsa mishi ba ya nemi cushion ya zauna shi ma ya saki nashi kuka, ai kuwa hankali Aunty Farida ya ƙara tashi domin ƙato majiyi ƙarfi iri Bilal Shattima ace yana kuka har dasu shassheka lallai al'amari babba ne.
  Da kyar da shudin goshi Bilal ya yi mata bayani abinda ya faru, ai kuwa ba ƙaramin kaɗuwa tayi ba cikin tashin hankali take kallonshi da Jeeddah ce ta faɗa mata Bilal ya sake ta saki har uku ba za ta yarda ba amma da yake maganar ta fito daga bakinsa ko kwakwaran motsi ta kasa yi ta ɗauki dogon lokaci a haka kafin ta ce "Shikenan Bilal ba komai su kuma iyayenka nasu hallaci kenan tun da yanzu sun ga ka yi kuɗi ka sami ƙazantar duniya shine za su sakawa Jeeddah da butulci ko butulci irin wannan mai matuƙar muni. Tashi ka tafi kawai da sannu za ku ga sakayya.
   "Aunty Farida ki fahimce ni wall..
"Dan ALLAH Dan Annabi Bilal ka tashi ka fice min daga gida banaso ƙara jin wata kalma daga bakinka.
Aunty Farida ta katseshi cikin tsawa da hargowa saukowa ya yi daga kan kujera ya zube gwuiwayinsa kan tiles ya shiga roƙon Aunty Farida,  gani yanda yake mata magiya yasa ta fizge hannuna muka shige bedroom ɗinta, Bilal ya gaji da zama kana miƙe ya bar gida zuciyarshi kamar za ta yi bindiga ga Nusaiba sai faman kiran wayarshi take yi shi kuma yaƙi picking tuni Aunty Bahijja ta fesa mata kyakkyawan labari ya saki Jeeddah...

*Ina daɗa ba wa makarantar wannan littafi haƙuri a bisa rashin update akai-akai Dan ALLAH ayi haƙuri dani*
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

💧💥 *DA MA ACE.....!*

*TAGWAYE BIYU 2023*🔥🔥🔥

*SLIMZY*
*FEEDHOM*

*DAGA HAZIK'AN MARUBUTANKU WADANDA KE NISHADANTAR DAKU DA KAYATATTUN LABARANSU DA KUKE MARARI WATO RUD'ANI DA KUSKUREN SO*

*DAMA ACE....*

Labarin Nadiya! Nadiya...... Labari ne da aka gina bisa halin mu na yau da kullun, ba kuma gama garin labari ba! NADIYA, matar aure, yayin da ƙaddara ta afka mata to soma soyayya da wani mutun daban, wanda ta ke jin inda babu shi, ba zata taɓa rayuwa ba, gefe guda kuma Sadeek, wanda ya mutu a kan ƙaunar ta kuma ƙani ga Alaji....!
Bai taɓa haihuwa ba! Hasali ba zai haihu ba! Kwatsam sai ga ciki daga matar shi? Shin ɗan waye? Hmmm m... Soyayya, tausayi, cin amana, duka a littafin DAMA ACE..... 🔥🔥🔥🔥

Kin shirya?
Ki biya kuɗin ki domin tafiyar da ke, tafiya ce da zata jijjiga zukatan makaranta, Naira 500 ne  9994468172 Access bank fiddausi musa tare da shaidar biya ta 08036953516 ko 07042277401.

*AKWAI SPECIAL DISCOUNT DA MUKAYI DAGA YAU ZUWA RANAN DA FREE PAGES ZASU KARE GAREKU MASOYANMU DIK WANDA YAKESON SHIGA WANAN TAFIYA TO YA BIYA 400 DAN SAMUN DAMAR DA ZAA DAMA DAKU A LABARIN *DAMA ACE ....*

Kuma kin san wani abin ɗaɗin, ba zamu dakata da posting RUƊANI da KUSKUREN SO ba, ko da ace saura basu samu ba, ina tabbatar maku da waɗanda suka biya zasu samesa maza ku hanzarta

*SLIMZY*
*FEEDHOM*

*TAGWAYE BIYU 2023*🔥🔥🔥🔥🔥

046..

Kafin nai wani yunkuri Baba ya fito da bulala da ya sakade a cikin hannu kujerar da yake zaune, ko su mama basu san da zaman bulalar ba irin mai baki biyu ɗinan ce, tun lokaci da Aunty Farida ta faɗa mishi irin ta'asar da na aikata ya tanadi abarsa domin saita ni a cewar sa banida saiti. Dukkan hannuwana ya damƙe da hannunshi guda yayin da ɗayan hannunshi ke riƙe da dorina ya shiga zabga min ita da ƙarfin gaske, sai ihu da Karuruwar neman agaji nake yi ina bashi haƙuri amma wallahi kamar ina zuga shi ne da na fahimce da gaske Baba illata ni zai yi sai na koma kira suna Mama da Aunty Farida su zo su ceci ni, daga ƙarshe kowanne miƙewa ya yi ya bar mana parlour sai da Baba ya gaji don kanshi ya sake ni. Kana ya daka min tsawa tare da umartata da nayi mishi shiru babu shiri na haɗiye kukana, Baba ya koma akan kujera da yake zaune tun asali ya wani tamke fuska cikin hargowa ya shiga yi min faɗa in da yake shiga ba na yake fita ba. Tsawon lokaci ya ɗauka yana min faɗa gami da jan kunne kala-kala yana cikin faɗa nasa sai ga Mama da Aunty Farida sun dawo cikin parlour nan take zuciyata ta shiga kimtsa min su ma sun tsaneni kamar yadda Babanmu ya tsaneni domin da yana ƙaunata da ba zai min duka irin wannan ba. "Tashi ki zauna da kyau ina magana ki yi wani banza zama.
Babamu ya faɗa cikin tsawa domin tun lokaci da ya gama dukana na saki cinyoyina da suka yi raɗau-raɗau da shatin bulala, da kyar na ja rigar jikina na rufe cinyoyina kana Baba ya zarce da faɗin "Duk tarbiyya da gatan da nayi miki Jeeddah ba ki gani ba sai da ki ka aikata abinda zai taɓa ƙima da darajata saboda haka ina mai tabbatar miki da cewa muddin kika yi sanadi da aure ki ya sami tangarɗa ba zan taɓa yafe miki ba Fatee da Farida ku shaida idan har ba za ta bi umarnina ta zauna Lafiya da mijinta da 'yan uwansa ba ni ba ita kuma ki sani dangane da lissafi da kika buga wa mijinki daga yau banaso ko tashe batun nan na sake ji ki yi idan kuma naji sai ranki ya yi mummunan ɓaci. Kana kuma ki sa aranki ba ki da uba domin daga wannan ranar na tashi daga muhalli na mahaifinki sai ki je can ki nemi wani uba ba dai ni ba.
  Furunci Babamu ba ƙaramin gigita duniyata ya yi ba, na ƙara saki kuka jaye da ɗuwawu na isa gabanshi na kama ƙafafuwan shi sai kawai fatali ya yi da hannuwana ya tashi ya shige ɗakin baccinsa. Mama da Aunty Farida suka ɗora nasu faɗa daga inda Baba ya tsaya domin kuwa Mama har cewa tayi daga yau kar na sake zuwa mata gida kuma na tashi na ɓace mata da gani, dube-dube na shiga yi ina neman gun da na jefar da key ɗin mota ta, sai can na ganshi ƙarƙashin kujera da Aunty Farida take zaune ashe tsabar raɗaɗi bulalar Baba yasa na cilla key ɗin. Ko kallon gefen dasu mama suke yi ban yi ba na fita a fusace, domin har ga ALLAH na ga laifinsu matuƙa ai ko za a yi min faɗa da duka ya dace aji daga bakina a tambaye ni girman laifi da Aunty Bahijja tai min da yasa nai mata irin wannan hukunci amma haka kawai sun yi min rudugu sai kace wata marar gata. Ina tuƙi ina sharar hawaye tsabagen hankalina baya tare dani shiyasa ban fahimci hanyar fita gari na biyo ba ashe duk tafiya nan da nake yi nayi faci kasantuwar natsuwa da hankalina sun kaurace min sai da wani bawan ALLAH ya ankarar dani ta hanyar dinga yi min horn da na fahimce dani yake na sauke glass "Hajiya kin yi faci!
Abinda ya faɗa min kenan cikin ɗaga murya kafin ya ƙarawa motarsa gudu ya ƙara gaba, cikin sauri na gangara gefen titi nayi parking kana na kifa kaina ga steering, bansan adadin lokaci da na share a zaune ba kafin na fara tunani mafita domin tafiya kaɗan ya rage na shiga garin Bodinga. Koda na duba agogo jikin mota naga sha ɗaya da rabi ta gota da kyar na yunƙura na fito daga cikin mota gaba ɗaya jikina ya yi min tsami tsabar duka da nasha hannu Babanmu. Tsaye nayi gami da jinginawa ga mota na shiga rarraba idanuwa akan ababen hawa da ke wucewa cikin bala'in gudu duk motar da za ta wuce da mugun speed take wucewa bana tsammani na sami taimako su. Gashi inda nake babu mutane da ke tafiya a ƙafa ballantana na roƙi arziki ko take me home ce a saka min tun da ina da ita a boot. Da na ga tsayuwa nan ba za ta fidda ni ba na shiga tsayar da duk motar da ta zo wucewa amma kamar su ma suna goyon bayan Babanmu domin kuwa ko arziki kallo ban samu daga gare su ba.
Ga rana sai ƙara zafi take har sha biyu rana ta buga ina tsaye yayin da abubuwa masu tari yawa suka taru suka yi min yawa ga ciwo jiki da Headache dake barazana tarwatsa kokon kaina, ga rashin natsuwar zuciya uwa-uba yunwa da nake yi kamar ana yashe min hanjin cikina, ga kuma zafi rana da ke kuɗata ga rashin mataimaki da zai ɗora min taya in takaice muku abubuwa goma da ashirin kuma wai duk ni kaɗai. Gaskiya Bilal Shattima ya cuce ni domin shi ne ummul-aba'isi jefa ni cikin wannan bala'in. Nayi nisa a tunani shiyasa ban lura da wata mota baƙa wulik kirar Mercedes Benz 2020 ta da ta wuce ni da gudu baya wasu 'yan mintuna kuma sai ga ta dawo ta hanyar reverse, ma mallaki motar bai tsaya a ko ina ba sai kusa dani tsayuwar motar shi ya ankarar dani nai sauri ɗago Idanuwana na yada su akan motar, a hankali ya ziro ƙafafuwanshi farare tass! Da ke cikin black sandal kafin ya yunƙura ya fiddo da gangar jikinshi yana sanye da farar shadda ɗinki babbar riga yayin da ya kafa hular tangaran da ta dace da kayan jikinsa tun kafin ya ƙaraso guna na fara shaƙar haɗaɗɗen ƙamshi turarensa, walking majestically yake dunfaro ni duk tako sa ɗaya sai gaba na ya yanke ya faɗi.
  Idan har lissafi bai ɓace masa ba kusan shekaru bakwai kenan haɗuwar shi da ita amma daidai da second ɗaya bai taɓa gushewa a gareshi ba. Ba tare da ya tuno da kyakkyawar fuskarta ba. Duk da a wasu lokuta yana haɗuwa da ita a mabanbanta wurare sai dai tun lokaci da ya gano matar aure ce yake ƙoƙarin yakiceta daga zuciyarshi amma hakan ya gagara samuwa kullum soyayyar ta ƙara kanainaye masa zuciya take yi Engineer Ameer Bello Sardauna kenan{idan mai karatu ban manta ba shi ne mutumin da ya taɓa taimakawa Jeeddah har ya kai ta asibiti a lokaci da tana laulayi cikin Aiman}.
Sa'ili da ya iso daff dani sai ya yi min sallama
   "Assalamu alaikum!
zazzaƙar muryarshi ma'abociya sanyi da kammala ta ratsa dodon kunnena, sai da na sauke zazzafan numfashi kafin na buɗe bakina da ya yi min mugun nauyi na amsa da "Wa'alaikum Salaam!
   "Sannu maijiddah! Me ya sami motar ne?"
Suna da ya kira ni dashi ba ƙaramin girgiza min ƙwaƙwalwa ya yi ba yayin da ya jefa ni a duniyar tunani. Babanmu da Ya Haidar kaɗai ke kira na da suna maijiddah su ma ɗin sai tai yi musu daɗi, ko nayi musu abin kirki.
He looks so familiar but na kasa tuna inda nasan shi amma tabbas fuskarsa tayi min kama da wanda na taɓa sani "to amma a ina?"
Tambayar na kasa lalluɓo amsarta "Subhanalillah! Ashe faci ne ki ka yi ALLAH yasa kina da spare tire na canza miki domin nan wuri babu masu faci.
Can sama-sama na tsikayi muryarshi hakan yasa na tattara hankalina zuwa gareshi cikin mutuwar jiki da dusashewar murya na ce "Eh! Ina da take me home a boot.
   "Okay buɗe boot ɗin na canza miki.
  Haka na juya kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki na buɗe boot sai kawai naji numfashi mutum kusa dani da sauri na juyo na sauke mishi jajjayen kumburarri idanuwana da suka sha kuka har suka gode ALLAH, shi ma kafe ni ya yi da nashi idanuwana masu girma da jan hankali mai kallonsu gyaran murya da ya yi yasa ni sauri kauda fuskata "Ina tire ɗin yake?
Ya faɗa tare da kallon cikin boot ɗin "gashi nan a cik...
Sauran kalamai na suka ƙargame a maƙoshina a dalili ba wata tire a boot ɗin jack ne kawai a ciki tamkar zan fashe da kuka na kalleshi ina cewa "Babu tire maybe maigidana ya cire ta.
Wani irin faɗaɗɗa fuskarshi ya yi da sanyayyaye murmushi har sai da sautin murmushi nasa ya fito fili Yayin na kauda fuskata daga kanshi na mayar akan titi ina kallon motoci da ke ta faman kai da komo.
   "Tun da ba ki tire ni Kuma nayi niyar taimakawa bara na ara miki tawa amma make sure kin dawo min da abata domin aro zan ba ki ba kyauta ba.
   Da sauri na dawo da ganina akanshi still da murmushi akan fuskarshi cikin sanyi murya na ce "ALLAH zan dawo maka da abarka ni dai ka taimaka min naga kaina gida.
Na ƙarashe magana kamar zan yi kuka.
  Ba tare da ya sake magana ba ya nufi motarshi ya ɗauko take me home {irin ƙaramar taya nan} sai da ya fara cire babbar rigarsa yana dube-dube inda ya dace ya ajiye rigar karaf na miƙa masa hannuna gami da faɗin "Kawo rigar na riƙe maka"
Sai da ya ƙare min kallo yana shegen murmushi nan nasa da na rasa gane na menene, kafin ya ɗora rigar akan tafin hannuna ya sunkuya ya shiga kwance tire can Kuma ya miƙo min sifana yana faɗin "Maijiddah ungo riƙe min wannan.
Gudun kada na miƙa masa hannu hagu nayi rashin ɗa'a sai kawai na rataya rigarshi a shoulder na kana na karɓi sifana ɗin.
Sai kawai naga ya sake sakin ƙayatatcen murmushi wanda yafi duk waɗanda ya yi min a baya, kana ya dukufa canza tire ɗin cikin ƙanƙani lokaci ya canza min ya miƙe tsaye tare da ɗaukar tawa wacce ya cire ya buɗe boot ɗin motata ya saka min, ya dawo inda nake tsaye rataye da babbar rigarsa a ƙafaɗa hannuwanshi naga yana kallo sun yi dirty da sauri na buɗe mota na ɗauko robar ruwa na ɓalle murfi tare da kallonshi, shi ma kallo nawa yake yi kafin ya tara hannuwanshi na zuba mishi ruwan. Bayan ya kammala wanke hannuwan nashi na miƙa mishi rigar shi ya karɓa ba tare da yasaka ba ya ci-gaba da riƙe ta a hannu "Nagode sosai ALLAH yasaka maka da gidan aljanna firdausi.
Na faɗa ina ɗan murmushi.
  "Amin thumma Amin maijiddah!
So nake na tambaye shi a ina yasani domin daga jin yanda yake ambatar sunana gaba gaɗi, tabbas ba ƙaramin sani ya yi min ba. Sai dai kunya ba za ta barni nai masa wannan tambayar sai kawai na tsinci kaina da faɗar "Idan inaso na mayar maka da tayarka a ina zamu haɗu?"
    "Duk inda ALLAH ya sake haɗa mu sai ki bani.
Ya faɗa yana murmushi.
  "Uhmm!
Na furta kafin na sake yi masa godiya na raɓa gefenshi na buɗe ƙofa na shiga, har na yiwa mota key ya kwakwasa glass na sauke tare da jefa idanuwana cikin nashi "Maijiddah ki zama mai juriya yawan kuka baya magance matsala sai ma yaƙara liƙa damuwa na barki lafiya sai ALLAH ya sake haɗa mu amma bana fatar na sake gani idanuwanki a haka.
Daga haka ya juya ya tafi har ya ja motarsa ya ƙara gaba na kasa kwakwaran motsi sai naji kamar ya ɗaure ni da igiyoyi, jikina a sanyayye na ja mota na nufi gida ina zuwa gida kaitsaye kitchen na shiga  na dafa noodless naci kana na wuce bedroom na faɗa bisa gado na lumshe idanuwana, yayin da duk motsi da nayi sai na shaƙi ƙamshi turaren shi da ya gama bin rigar jikina, duk yanda naso na tuna da inda nasan bawan ALLAH nan ƙwaƙwalwata ta ƙasa tunowa dole na haƙura.
   AFTER SOME MINUTES
Na sauko daga saman gado na cire rigar jikina na maye ta da half gown wacce ta sauka iya gwuiwayina, tunawa da nayi da furucin Babanmu akaina yasa ni shiga kitchen na girkawa Bilal lunch irin abinci da yafi so, ta ƙarfi da yaji nakeso na gyara abinda na ɓata ba don komai ba sai don tsoron hukunci Baba. Ina kammala girki na zuba a warmers na kai dining room kana na wuce bathroom nayi wanka, duk da ban yi wata kwalliyar kirki ba domin kuwa har yanzu ina jin  takaici gami da ɓaci rai cin amanata da Bilal Shattima ya yi duk da inaso na cilaswa kaina na ci-gaba da yi masa biyayyar aure amma wallahi a can ƙasan zuciyata haushinsa yana nan damƙare.
Na dawo parlour na kunna kayan kallo ina kallo Indian movie amma hankalina yana can ga mutumin da muka haɗu ɗazu na kasa bari tunaninshi. Ƙarar rufe ƙofa ya dawo dani natsuwata na juya na kalle mai shigowa Bilal ne muna haɗa idanuwa na shiga ayyanawa yanzu haka daga wurin Nusaiba yake, nan take naji wani irin mugun kishi, nai sauri kauda fuskata ko kusa ban kawowa raina zai kula ni ba sai naga saɓani tunanina domin kuwa sallama ya yi min "Assalamu alaikum!
Jin haka yasa na amsa mishi cikin dusasshiyar murya "wa'alaikum Salaam!
Daga haka na sadda kaina ƙasa na shiga wasa da zoben yatsana wanda Ya Haidar ne ya bani shi har kawo yau na kasa cire shi a dalili ƙaunar da nake yiwa zoben.
   Kusa dani ya zo ya zauna ya leƙa fuskata yana murmushi, hakan da naga ya yi yasa ni ɗagowa tare da cuno baki "What!
Na faɗa ina hararashi ya saki murmushi mai sauti kafin ya rungume ni cikin jikinshi yana faɗin "Fushi ya isa haka matata kuma uwargidana abin alfarina, farin cikin rayuwata.
   Ture shi na shiga ina faɗin "Da ba amma banda yanzu ai ni tuni na yafewa Nusaiba kai.
Matse min baki ya yi na saki ƙara "Miye haka cire min lips za ka yi saboda ko ka rasa wannan kana da na Nusaiba ko?"
"Omg! Wai ke ba ki da zance ne sai na Nusaiba?"
Ya faɗa yana kallon cikin idanuwana. Na yatsine fuska gami da faɗin "Duk duniya ita da Aunty Bahijja ne matsalata ka ga kuwa bakina ba zai gaji wajen ambato sunan ta ba.
   "To naji mu ajiye wannan zance mu yi magana ta fahimta.
"Ba wata maganar fahimta da za mu yi da kana so maganar fahimta a tsakanimu da ba za ka kai ƙara ta wajen Babanmu ba kalle jikina ka ga irin duka da ya yi min duk jikina shatin bulalarsa ne.
Na ƙarashe magana gami da ya ye rigar jikina Bilal Shattima ya kalle yanda gadon bayanta ya yi jajir raɗau-raɗau da shatin bulala sosai ta bashi tausayi har bai san sanda ya rungumo ta ya shiga bata haƙuri tare da neman afuwarta a bisa dukkan laifukan da ya yi mata ya ci-gaba da yi mata daɗi baki tsakani mata da miji sai ALLAH sai ga Jeeddah ta sauko tare ma suka ci abinci sai nishaɗi gami annushuwa suke yi. Ta shiga kitchen ta wanke plates ɗin da suka yi amfani ta ji ringing ɗin wayarsa Nusaiba ce ta kira shi da sauri ta zo jikin ƙofa ta leɓe tana saurare magana da yake yi, tana ji lokaci da ya ɓalɓale Nusaiba da masifa har yana cewa karta sake kiranshi idan yana da ra'ayi magana da ita shi zai kira ta Raina ya ƙara yi fari tass! Saboda haka ban barshi ya fita ba sai da yamma liss! kuma ana gama sallah isha ya dawo sai da muka yi shirin kwanciya bacci ya riƙo hannuwana tare da furta "Albishinki love!
Sai da na ɗan taɓe baki kafin na ce "Goro!
Turo min kumatunsa ya yi yana faɗin sai kin fara bani hot kiss kafin na faɗa miki ina dariya na sumbace kumatunsa dama da hagu.
   "Cikin hukunci Ubangiji ya nufi ni da biya mana Makkah in-sha-Allah Hajji bana da mu za a tafi.
  "Are you serious?"
Na faɗa cikin zazzare idanuwana miƙewa ya yi ya dauko min shaidar biya gudu biyu ya miƙo min na karanta nasaki ihun fari cikin da murna kana nayi tsalle na rungume shi, sai kisses nake zuba mishi a kamatunsa da gefen wuyanshi sai dariya yake min daga bisani na shiga yi mishi godiya. Ɗauka ta ya yi cak ya ɗora akan gado kana ya zauna kusa dani gami da riƙe hannuwana ya kwantar da murya yana faɗin "Babu godiya a tsakanimu love duk abinda nai miki ban biya kwatankwacin rabi sadaukarwa da ki ka yi min ba. Kuma in-sha-Allah zan biya ki adadin kuɗaɗen da kika ce kina b....
Kafin ya ƙarasa magana nai sauri rufe mishi baki da tafin hannuna domin na tuna da kyakkyawan kashedi da Babanmu ya yi min akan zance kuɗaɗen da nace ina bin shi Baba ya ce muddin na sake cewa da Bilal ina bin shi bashi kuɗi bai yafe min ba. Shiyasa ina ji ya sako zance kuɗi na rufe mishi baki cikin sanyi murya nace "Love ka manta da zance kuɗi nan dama nayi ne domin na ɓata maka rai kuma a yanzu komai ya wuce ni na ma yafe maka kuɗin.
  Zaro idanuwa ya yi kana kuma yasa dariya tare da cewa "Eh! Lallai bulalar Baba ba ƙaramin shigar ki tayi ba.
Kuka shagwaɓa nasa mishi da sauri ya rungumeni in takaice muku labari dare ranar mun raya shi cike da so da ƙaunar juna har mantawa nayi da akwai wata aba wai ita Nusaiba. Washegari tun da muka yi sallar asuba muka koma bacci muna manne da juna tamkar an ce mana wani zai raba mu. Can cikin bacci muka ji ana mana heavy knock tamkar za a ƙarya mana ƙofa, daga ni har shi a firgici muka tashi ya kalle ni na kalle shi kowanne mu yana mamaki waye ke mana wannan mugun knocking sai ka ce mu ci bashi wani, daga shi sai boxer briefs da white vest ya sauko daga gado zai fita nayi sauri hana shi ta hanyar cewa "Love dawo ka kwanta abinka bara naje na duba waye?
Da sauri ya ce "a'ah yi zamanki bara na dubo da kaina.
  "Okay!
Na faɗa tare da maƙe ƙafaɗa ya fice ni kuma na sauko na shiga bathroom nayi brush kana na cire sleeping dress na maye gurbin su da boomshort da vest.
Rai ɓace Bilal Shattima ya buɗe ƙofa sai kawai ya yi arba da Hajja tare da Aunty Bahijja a bayanta da ɗan uban bandage ɗinta a damtse hannu, kallon mamaki yake musu yayin da zuciyarshi ta cika da tarin tambayoyi me suka zo yi mishi a gida a daidai wannan lokaci kasa haƙuri ya yi har sai da ya furta a fili "Hajja lafiya ku ke tafe yanzu?"
Ya ƙarashe magana fuskarshi tana ƙara bayyanar da mamakinsa a fili.
  "Ubanka na zo yi ɗan iska yaro shanyayye banza da wofi bani hanya na wuce yau dai zan kawo ƙarshen iskanci taƙadariyyar matarka.
Ta ƙarasa magana tare da ingije shi ta shiga cikin parlour yayin da Aunty Bahijja ta biyo ta a baya da sauri Bilal ya sha gaban Aunty Bahijja ya watsa mata mugun kallo kafin cikin ɓaci rai da fusata ya ce "Aunty Bahijja me nayi miki ne a duniya da bakyaso na zauna lafiya da iyalina wai me Jeeddah ta tare miki ne?"
  "Mtsssss! Duk ubanda ta tare min yau za ka gani don kuturun wulaƙanci matarka ta yayyaka min wuƙa a matsayina na wacce mu ka fito ciki ɗaya da kai ka kasa daukar mataki wallahi Bilal cka ji kunya.
Tana ƙarasa magana ta bi ta gefenshi ta nufi gun Hajja, ina fitowa daga bedroom nayi kicibus! Da Hajja ta nufo ɗakin baccinmu sai da ƙare min kallon sama da ƙasa kafin tace "Da kyau karuwa dama da wannan shigar ta karuwai ki ka mallake min ɗa ko?
   Wasu miyau na haɗiye domin ba ƙaramin zafin kalmar karuwa ta yi min ba, sai kawai na kafe ta da idanuwana "Shegiya tsinaniya baƙar karuwa yau ƙarshen ki ya zo la'ananniya kawai.
  Aunty Bahijja ta faɗa tana wani tadda murya sosai raina ya ɓaci zan iya haƙura Hajja ta kira ni da kowacce irin kalma da taga dama domin ɗanta nake aure kuma mahaifiyar ƙawata ce amma ba zan jure Aunty Bahijja ta ci-gaba da danganta ni da mummunar kalma ba. Saboda haka na tunkare ta a fusace ina faɗin "Ina gargaɗinki Aunty Bahijja da kada ki kuskura ki koma kirana da suna karuwa?"
    "Na faɗa karuwa, karuwa, Jeeddah ke karuw....
Kafin ta ƙarasa na ɗauke ta da mari ina faɗi "Ba dai ni ba wallahi sai dai in uwarki ce karuwa.
   "Jeeddah ni ki ke kira da karuwa?"
Hajja ta faɗa tana zarar ido cikin kaɗuwa Bilal ya ƙaraso yana faɗin "Jeeddah ki natsuwa ki san abinda daga yake fitowa daga bakinki Hajja fa mahaifiyarta ce?
   "Yadda take uwa nima haka nake uwa yadda za ka ji zafi idan an kira ta da wannan kalmar nima hakazalika ɗana zai ji zafi saboda haka muddin Aunty Bahijja ba za ta daina danganta ni da wannan suna ba nima ba zan daina cewa uwarta ce karuwa.
   "Wayyo ALLAH na shiga uku na lalace kaicona ni Hajja ashe na haifi ɗa da za a kirani da karuwa a gabanshi ya kasa daukar mataki.
Hajja ta ƙarashe magana tana gunji kukan munafuci yayin da Aunty Bahijja ke tayata.
   "Dan ALLAH Hajja ki yi haƙuri Jeeddah ba da ke ta ke ba, Aunty Bahijja ce ta ba wa amsa da za ta kira ki da wannan suna da tun farko da ki ka kira ta dashi da ta rama..
Cikin daka tsawa Hajja ta ce "Rufe min baki ɗan iska yaro wanda baisan darajar uwa ba to wallahi-azim yau sai ka zaba tsakani ni da ita.
   "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Hajja me ya kawo zance zaɓi anan ke fa mahaifiya ta ce ita kuma matata ki sani kowanne ku matsayinsa daban?"
   "Wallahi-tallahi! Na rantse da Ubangiji sammai bakwai yau sai ka saki Jeeddah ba saki ɗaya ba saki uku za ka yi mata ko na tsine maka albarka.....
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

Taɓa ka lashe..

   *ZAMANIN MU AYAU*

NA
  JEEDDAH ALIYU
      & NANA DISO

A Wannan zamanin namu ku yaran nan baku ɗauki ruwan ɗumi da mahimmaci ba, saboda Allah maryama ke ba yarinya ba da shekarunki kidinga shan ƙanƙara haka? Ki duba fa kiga babu ruwanki da tsarkin nan da ruwan dumi, wai kuma ƙin babbake ɗuk Duniya Abah ke yafiso yafi kyau na! " Wani ƙallo tayiwa mahaifiyarta tace "Anty wa zai so idan bani ba? Duk cikin family ɗin ƙinga mai kyau na? Nifa a duniya zan iya rantse miki abah yafi sona akan mahaifiyar nan tasa!  Banida diri ne ko kuma ni mummuna ce? Kuma ƙanƙara anty me zatayi min, hmm bari dai nayi shiru Amma idan kinga yadda abah yake bina a daƙi wallahi ko maye sai haka! "Lallai maryama zamani kenan ni mahaifiyarki kike gayawa wannan ƙalmar? To bazan miki baki ba Amma ina tabbatar miki ranar da abah yaga mata zakisan ke bakomai bace ba!  Kuma banda abunki ai ita macce ƴar dumi ce, wannan shanyin illa zaiyi miki acancikin ki, ai ita macce da ɗumi aka santa, ai ballagaza ita ke illata ƙanta da ƙanta sai sanyi ya kamaki kizo kisani agaba, haka naje na haɗomiki sassaken nan na ɓaure da ƙanin fari da minnas da zuma da citta da kirfa, nazauna nadafa miki amma kika kalleni kikace ƙwayoyin cutane wai ke ƴar boko nima mahaifiyar taki ƙallon baƙauyiya kikemin maryama kibi duniyar nan a sannu!" Hajiya anty Kenan! Basai nayi miki wani dogon bayani ba Amma nice zuciyar aba babu wata macce bayana!!!....

https://t.me/+RDbX-vD-HWdlNWE0

048..

Bilal Shattima yana fitowa daga gidan Aunty Farida kaitsaye gida ya wuce ya tattara  kayayyaki shi ko allura bai bari ba, ya rurrufe ƙofofi kasa tafiya ya yi yai tsaye yana yiwa gidan kallo na ƙarshe yana tuna irin rayuwa da suka yi shi da Jeeddah. Ji yake kamar ya dawo da baya sai dai abinda ya wuce ba zai taɓa dawowa ba. Wasu hawaye masu mugun zafi suka zubo masa a kumatu bai damu da ya goge su ba ya juya da sassarfa ya shiga motarsa kana ya yi reverse ya nufi gidan Hajja a tsohon ɗakinshi dake BQ ya saka kayanshi duk ƙura da ke ciki bai dame shi ba ya zauna gefen tsohuwar katifarsa gani komai yake yi tamkar al-mara.
Sosai Jeeddah ke ta rusar kuka Aunty Farida ke rarrashinta "Aunty ki barni nayi kuka abin kuka ne ya sami ni adaidai lokaci da muka sami daidaito tsakanina da Bilal muka fahimci junanmu kana muka tsara rayuwarmu ta gaba sai gashi kwatsam! An raba mu Aunty na kasa yarda Love ne ya saki ni kuma wai har saki uku da wane ido zan kalle Babanmu na gayamishi Love ya sake ni bayan na kwana da sani furuncinsa akaina.
   "Jeeddah Baba ba zai ga laifin ki ba domin ba ke kika ce ya sake ki ba shi kanshi Bilal cilasta shi aka yi amma duk da haka bai dace ace lokaci ɗaya ya yi miki saki har uku ba saki irin na jahilai farko, sai kace ba shi da ilimin addini.
   Girgiza kai nayi ina faɗin "Aunty titse shi tayi har ma da guzuri biro da takarda ta taho dasu, ba shi da yanda zai yi domin  tayi rantsuwa ta sake maida rantsuwa idan har bai sake ni ba tsine mishi za tayi.
Tsaki Aunty Farida ta ja gami da cewa "Mtsssss! Tsinannu mutane kawai butulu. Tun da ya yi kuɗi ai yanzu dole su tsane ki sun manta da lokaci da ɗansu yake taka rawa da bazarki. in-sha-Allahu sai sun girbi abinda suka shuka. Tun farko abinda muka yi miki gudu kenan ga ɗan uwanki me sonki tsakani da ALLAH domin tun kafin ki zama cikakkiyar mace Haidar yake danko sonki amma ki ka daka tsalle ki ka ce sai ɗan gidan gantalallu mutane wanda basu gadi mutumci ba. To ai ga irin sakayya da suka yi miki nan yanzu kan ai dole ki ɗauki darasi ki gano cewa ba inda kafuwa da naci zai kai mutum face ga wahala.
Duk abinda Aunty Farida take faɗin nasan gaskiya ne amma abu ɗaya na kasa gasganta wa shine laifin Bilal da take gani domin ni ko kaɗan ban ga laifinsa ba. Ni dai na dogara ne da cewa Hajja da Aunty Bahijja ne suka raba mana aure.
   Sai bayan sallar isha'i Aunty Farida ta tattara ni muka yo gida har Aunty Farida ta gama yiwa Baba jawabi ba abinda nake yi sai shasshekar kuka da alama ba ƙaramin girgiza Babanmu ya yi ba. Domin tallaɓe kumatu ya yi sai "innalillahi wa'inna illahim raji'un! Yake ta maimaita wa daga bisani ya yi shiru sai Mama ce ke ta zuba faɗa inda take shiga ba ta nan take fita ba domin kuwa har cewa tayi duk kudaden da na lissafa sai Bilal ya biya ni abina domin kuwa bai yi min adalci ba. Sai da Baba ya taka mata birki ya ce ko cikin fira bayaso ya sake ji wani daga cikinmu ya tadda zance kuɗi nan. "Duk abinda suka yi mata su da ALLAH ai Ubangiji baya bacci saboda haka na kai ƙarar su wurinsa matuƙar Jeeddah tana da hakki akansu sai ALLAH ya saka mata. Ki yi haƙuri Jeeddah nasani saki yana da matuƙar ciwo wanda misalta zafinsa sai wanda aka yi wa amma duk da haka ki ɗaure ki ɗauke shi a matsayin ƙaddararre al'amari ALLAH ya zaɓa miki abinda yafi zama alkhairi a rayuwarki. Ku tashi ku tafi zan yi magana da Mamanku. Ni da Aunty Farida muka tashi ina mai ci-gaba da sharar hawaye. Parlour Mama muka shiga yayin da muka baro Mama a can parlour Baba.
Sai misali ƙarfe 10:00pm Aunty Farida tai mana sallama da zimmar za ta dawo gobe. Mama sai lallaɓa ni take yi hatta da Aiman da ya dame ni da surutu wai na duba masa homework ɗinsa. Tsawa ta daka mishi gami da cewa ya kyaleni naji da baƙin ciki da ubansa ya ƙunsa min. Ranar a ɗakin Mama na kwana akan gadonta wani irin masifaffen ciwo kai ya saƙo ni a gaba yadda naga rana haka naga dare sai da asuba ya gabato sannan bacci ya ɗauke ni.
Tun da nayi sallar asuba Mama ta ce na koma na kwanta ina buƙatar hutu. Na koma na bi lafiyar gado yayin da ciwo kai da nake ji sai ƙara hauhawa yake yi, sai lumshe idanuwana nayi kamar mai bacci al'hali idona biyu ina jin lokaci da Mama ta shirya Aiman ya tafi school dama Abdul yaron Baba na shago ke kai shi ya ɗauko shi.
A cikin ƙura da yana Bilal Shattima ya kwana domin baya cikin natsuwar da zai nemi kyakyawan wurin kwana. Da asuban fari ya baro gidan nasu wanda har a washegari Hajja batasan cewa anan ya kwana ba. Kaitsaye hotel ya nema ya kama ɗaki sai a lokaci ya sami damar yin bacci kirki mai cike da mafalki an maida aurenshi da Jeeddah saboda haka da ya falka mafalki kawai ke mishi kai kamo a cikin ƙwaƙwalwa, har yai nasarar fara kimtsa mishi wani bakon al'amari.
Tun cikin dare Mama ta kira mommy Turai ta fesa mata mummunan labari Bilal ya sake ni saki uku, shiyasa da sassafe Mommy ta shirya tana isa parking lot Haidar Ka'oje yana fitowa daga apartment ɗinshi jikinshi sanye da sport wears white in colour da ɗan gudun shi ya nufo wajen mommy "Mommy lafiya za ki fita da sassafe nan?
Haidar ya faɗa sa'ili da ya ƙaraso gunta. Sai da mommy ta saukar da numfashi mai ƙarfi kafin ta ce "ina fa lafiya Aliyu ɗan shegiya nan tsinane mummuna tsiya mijin Jeeddah ya sake ta don yana ɗan jahila saki har uku.
   Wani irin mugun bugawa ƙirjin Haidar ya yi don sai da jiri ya kwashe shi ALLAH ya taimake shi akwai mota a gefensa yai sauri jingina jikinshi. Da ba abinda zai hana mishi faɗuwa "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Ita kuwa me tayi mishi da zai mata wannan sakin wulaƙanci?"
Haidar ya yi magana cikin sanyi murya.
  "Butulci ne kawai irin na ɗan Adam tun da yanzu yana gani ya yi kuɗi ya kuma auro 'yar uwarshi ai dole ya wulaƙanta ta.
"Uhmm! Mommy kada ki yi sauri yanke hukunci domin wannan bai isa ya zama gamsasshiyar hujja da zai sa ya yi mata irin wannan saki na jahilci ba.
   "To shikenan tun da ba ka yarda ba ai kai dama gaddamamme ne duk abinda aka faɗa sai ka yi gardama da kwaskwarima akanshi.
   "ALLAH ya ba ki haƙuri Mommy ni ba gardama nake miki ba kawai dai Inaso ki bari sai kin ji sahihin labari kafin ki zartar da hukunci.
  "Mtsssss! Bani wuri na wuce kada ka ɓata min lokaci da iya yinka na wofi.
Mommy ta faɗa tare da ture Haidar a fusace ta shiga ƙoƙarin shiga mota da sauri Haidar ya ce "Mommy bani key na kai ki saboda direbanki bai ƙaraso ba kuma kin daɗe ba ki yi driving da kanki ba kada ki je ki jawo mana aiki da sanyi safiya.
Ba tare da tayi magana ba ta cilla masa key ya cafe har suka iso ƙofar gidansu Jeeddah Mommy tana kwashewa Bilal da Hajja albarka.
A parlour Baba ta tadda Mama anan suka sake maimaita zance yayin da Mommy sai ɓaɓatun faɗa take ita ma ta goyi bayan mama gara Bilal ya biya ni kudina har cewa tayi idan ya yi gardama a maka shi kotu sai da Baba ya nuna mata ɓacin ranshi a fili kafin ta bar maganar amma kama daga kan Bilal, Hajja kai har ma da Aunty Bahijja sun sha zagi da tsinuwa yafi kala ɗari.
  Wani irin amai ne ya taso min a dalili mugun zazzaɓi da ya rufeni, da gudu na diro daga kan gado kafin na kai bathroom, amai ya kubce min na durƙusa ƙasan tiles na shiga kelaya shi sai kakari nake yi kamar zan amayar da hanji cikina.
  "Mama ina Jeeddah take?"
Haidar ya faɗa sai lokaci ya yi magana duk taƙaddama da ake yi bai furta uffan ya dai tallaɓe da kamatunsa, sai rarraba idanuwa yake yi shi kaɗai yasan irin yanayi da yake ciki.
Mama ta amsa mishi da cewa "Tana can ɗakina tana bacci je ka dubo ta ko ta tashi domin da zazzaɓi ta kwana shiyasa ma nace ta kwanta ta sami isasshen bacci gaba ɗaya sun hargitsa min 'ya shegu mutane kawai.
Ɗan guntun murmushi Haidar ya yi domin ya kwana da sani dama can Jeeddah hargitsatsiya ce.
Yana shiga parlourn Mama ya fara jiyo kakari amanta da sauri ya nufi ɗakin yana tura ƙofa ya hango ta durƙusawa ya yi a bayana ba tare da kyakyami ba ya rungume ni yana faɗin "Subhanalillah! Jeeddah ashe zazzaɓin ya yi tsanani har haka? Tashi na taimaka miki ki shiga bathroom ki tsaftace jikinki mu tafi asibiti.
  Da taimakon Ya Haidar na kai kaina bathroom kafin ya fita sai da ya haɗa min ruwan wanka masu zafi sosai. Da kanshi ya gyara gun da na ɓata ya fesa room freshener sannan ya fita ya faɗawa su Mama hali da ya tadda ni ciki, koda na fito su Mama na ɗakin Mommy ce ta taimaka min na shirya cikin doguwar rigar Mama saboda ban zo da kaya ko ɗaya ba. Yau na ji Mama ta kira Aunty Farida a waya ta ce da yamma ta je a kwaso kayana. Ya Haidar ya shiga kitchen ya haɗa min tea yatsine fuska nayi saboda banaso ƙarni madara cikin dusashewar murya na ce "Ya Haidar da black tea ka haɗa min.
Da sauri ya juyo ya fice da mug ɗin tea a hannu jin kaɗan ya dawo da black tea ɗin, ya miƙo min mommy ta karɓa ta dinga bani a baki nasha fiye da rabi mug kafib na ce da Mommy na ƙoshi. Tare da mommy muka fito zuwa asibiti yayin da Mama ta zauna gida.
  Nan take aka karɓe mu babu ɓata lokaci aka shiga treatment ɗina, da yake private hospital ne  kuma shine hospital ɗin family doctor ɗin su Ya Haidar. Bayan gwaje-gwaje da aka yi min bincike lafiyata ya nuna jini na ne ya ƙara hawa fiye da farkon kwanciya na asibiti. Hakan ba ƙaramin ɗagawa Ya Haidar hankali ya yi ba sai misali ƙarfe ɗaya ya baro asibiti ya zo gida ya yi wanka. Kana ya ɗauki abinci ya dawo tare da direban Mommy hakan ya ba wa mommy damar komawa gida, da yake Aunty Farida da Khairat duk sun zo.
  Sai kai da kawowa Engineer Ameer Bello Sardauna yake yi a harabar hospital ɗin da aka yi admitting ummarsa, tun safe da ya yi tozali da Haidar Ka'oje ɗauke da Jeeddah cikin halin rashin lafiya ya kasa samun kwanciyar hankali ƙarfin hali kawai yake yi domin zuciyarsa sai azalzalarsa take yi da  ya je room ɗin da take d ya ga hali da take ciki  koda zai sami natsuwa. Tun safe da ya ganta ya kasa gusawa ko nan da can sai zayar yake yi tsakani bakin ƙofar ɗakin da take zuwa wanda umma take kana kuma ya dawo harabar asibiti. Shi kanshi ya rasa gane wannan masifar da ta Kunno wa rayuwarshi na son matar aure.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

https://chat.whatsapp.com/IQnEzmrT2LOBqbo9lOW5WX

*ZAMANIN MU A YAU*

       Na

Jeeddah Aliyu
           &
Nana Diso

*TAƁA KA LASHE*

Ya kasa gasganta abinda idanuwanshi suka gane mishi sai faman mutsu-tsuka idanuwan nashi yake yi, domin ƙara tabbatarwa a karo na biyu sake yada ganinshi akansu duk da yana cike da kyamar abinda suke aikatawa, haka nan ya ɗore ya ci-gaba da ƙare musu kallo tabbas Ummul-Salma ce ƙanwa matarsa Surayya ke rungume a jikin Yazeed Talba sai tsotsar bakin junansu suke yi tamkar za su cinye bakunansu. Yayin da hannuwan Yazeed Talba ke ya mutsa boobs ɗinta da ke cikin doguwar rigar jikinta, tsanani takaici da tsanar Ummul-Salma suka yiwa Barrister Suleiman Abba Garkuwa  dirar mikiya bai taɓa tsammanin iskaci da tantiranci Salma har sun girmama har haka ba.
Yana kallon sanda Yazeed ya buɗe mata murfi mota ta shiga ya rufe sa'anan ya zagaya ya zauna a driving seat ya ja motar da ƙarfin gaske suka bar wajen. Wani irin tuƙuƙi baƙi ciki yake ji ba don komai ba sai don kasantuwar Salma ƙanwar matarsa da yafi ƙauna a duniya.
  "Abinda nake so da kai Mustafa ka fitar da yarinya nan daga zuciyarka domin ko bayan raina ban amince da ka aureta ba. Saboda haka ka tun wuri manta da ita ka goge shafinta a rayuwarka domin aure tsakaninku ba mai yiwuwa bane.
Cewar Former Minister of Finance kuma ɗan takarar Gwamna jiha Alhaji Ali Matawalle.
   Idanuwan Mustafa Ali Matawalle suka cicciko da hawaye domin shi kaɗai yasan irin raɗaɗi da ƙunci da yake ji a duk lokaci da Abbu da Addah Sa'adah suka yi mishi gargaɗi akan ya rabuwa da Leemart.
Har yau sun kasa gane cewa a matsayin shi na ɗa mai matuƙar biyayya a gare su da zai iya da tuni ya bi umarninsu sai dai kashhh! Soyayyar Leemart ta ri ga ta yiwa ruhi da gangar jikinshi babbar illa rabuwa da ita yana nufi rasa rayuwarshi.
   "Lallai Yusufa rashin kunyar ka ya kai maƙura ya kai matakin da zan iya yekuwa jama'ar duniya su taro na fesa musu labari na son zuciya da mugun hali irin naka. Kai yanzu banda lalacewa irin taka har kana da kwari gwiwa zuwa gidana ka dubi tsabar idanuwana Yusufa babu kunya balle tsoron ALLAH ka ce wai ka yiwa Mahanoor miji.
   Murmushi Alhaji Yusuf Ibrahim Zanna ya yi wanda bai wuce iya fatar bakinsa ba, ya kalli Hajjo wacce ta kasance suruka a gare shi ciki isa da taƙama ya ce "Hajjo! Hajjo!
Ya kira sunanta sau biyu cikin alamar rashin ɗa'a ya ci-gaba da faɗin
"Ni fa a rayuwa nan kina bani mamaki shin ke bakinsan cewa da Uba ake ado ba da rigar aro ba? Karki manta surukuta ke ɗin tamkar rigar aro ce a wurin Mahanoor kada ki yi amfani da wata ƙanƙanuwa rawa da kika taka a rayuwar 'yata ki nemi ki wuce makadi da rawa ni dai na fidda hakkin ki a matsayin ki na wacce ta reni Mahanoor.
   Kallon haɗarin kaji Hajjo tayi mishi kafin cike da takaici mai haɗe da tsanar Alhaji Yusuf Zanna ta ce "Ai tuni wannan damar ta kasancewar uba ga Mahanoor ta subuce maka Yusufa za ka iya nuna isa da tunkaho akan 'ya'yan matarka 'yar so ba dai akan 'yar da ka wofitar ba, wacce bakasan cinta ba, bakasan shanta ba, ciwonta lafiyarta duk ba ka san su ba, hatta da hakken ilminta na arabi da boko ba wanda ka sauke nauyinsa shi ne yanzu don kawai kana da muradin cikar wani burinka na son zuciya za ka kwaso jiki ka zo min da labarin ƙanzo kurege....

049..

Haidar ya ɗebo abinci da spoon ya nufi bakina da sauri na kauda fuskata, kana na shiga yatsinar fuska cikin muryata da ba ta fita sosai na ce "Ya Haidar ko kaɗan banaso ƙamshi abinci nan  yana ɗaga min hankali. Ji nake tamkar zan yi amai.
Zaro idanuwa Haidar ya yi tsawo lokaci ya share yana kallonta kafin ya yi ƙasa da murya ta yadda su Aunty Farida dake zaune kusa dasu ba za su ji shi ba ya ce "Jeed kaɗai mutumi nan sai da ɗirka miki ciki sannan ya sako mana ke idan kuwa hakan ta kasance gaskiya Bilal ya gama dani. Wallahi ya cuce ni.
Ya ƙarashe magana kaman zai rushe da kuka  ban tsan lokaci da na falla mishi kafira harara tare da jan guntun tsaki, furuncinsa ba ƙaramin ƙona min rai ya yi ba.
  Yayin da Haidar bai ma san tana yi ba domin gaba ɗaya hankali da tunaninsa sun kaurace masa, da sauri ya ajiye plate ɗin abinci ya miƙe jikinsa yana rawa ya fita da mugun sauri, na bishi da kallon takaici jimm! kaɗan ya dawo tare da nurse cikin faɗuwar gaba ya ce "Sister kamar yadda na faɗa miki tun farko PT nake so ki yi mata.
Raina ne ya ƙara ɓaci sai dai ba ni da yanda za yi domin banida kuzari faɗa dashi ina ji ina gani ba bakin gardama ko musu nurse ta ɗibi jinina, tare da bani small container nayi fitsari na kawo mata haka na tashi jiki ba kwari jiri yana ɗibata na shiga bathroom nayo fitsari na kawo mata.
Yayin da Aunty Farida da Khairat ke ta yi mana dariya ni kam sam banga abin dariya ba asalima haushinsa nake ji to ina ruwansa dani da har zai damu da ciki ne dani balle har ya tashi hankalinsa har haka. Tsabagen takaicinsa da nake ji yasa na kwanta tare da juya musu baya, kamar daga sama na tsikayi muryashi yana faɗin "Aunty Farida gabana sai faɗuwa yake banaso pt result ɗinan ya bada positive ni da nake so tana kammala iddarta ku sha biki sai ga wannan al'amari yana so ya rusa min budget.
A tunanina Aunty Farida za tayi sauri taka masa birki ta hanyar ankarar dashi illar dake tattare da abunda yake faɗa duka yaushe aure nawa ya mutu da zai fara kawo zance aure a tsakanimu sai kawai naji Aunty Farida tana cewa dashi "Ka kwantar da hankalinka Haidar saboda bana tunani ciki ne da ita da ciki ne da yanzu zaman nan da muka yi tayi amai yafi a kirga.
   "A'ah Aunty ki ka sani ko wannan ya bambanta da cikin Aiman ai da yawan mata yanda suka yi ciki fari ba lallai bane na biyu ya zo musu  kamar wancan na fari ba.
Khairat ta faɗa tana ƙunshe dariya gami da kallon Ya Haidar taga yanda fuskarshi ta sauya kamar zai rushe da kuka ta kwashe da dariya kafin ta taso ta dafa shoulder ɗin shi tana faɗin "Calm down bros wasa nake maka in-sha-Allahu ba ciki bane to amma abin tambaya ana ya za ka yi da Zarah?"
Ta ƙarashe magana tana sakin dariya domin tasan yana shirin ɗaukar dala ba ganwo ne, kasa kunne nayi naji wacce amsa zai ba ta domin kuwa duka saura one month bikinshi da Zarah.
  Sai da Haidar Ka'oje ya shafa lallausar sumar kanshi kafin ya ce "Haba lil sis kin manta da cewa ni ɗin mijin mace huɗu ne duka zan haɗe abina tun farko wancan mai ƙaton hanci shigo-shigo ba zurfi yai min yanzu kuma cikin hukunci Ubangiji ya dawo min da kayana this time ba zan yi wasa da dama ta ba.
"Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Na furta can cikin zuciyata. Duk cikin maganganu shi ba wacce tafi ɓata min gami da haddasa min soyar Zuciya irin cewar da ya yi zai haɗe mu ni da Zarah, lallai tsugunne bata ƙara min ba.
  Ƙara runtse idanuwana nayi yayin da Ya Haidar ya cigaba da yiwa su Aunty Farida sambatu akaina su kuma da rashin tunani irin nasu sai ƙara encourage ɗin shi suke yi, gaba ɗayansu haushi da takaicinsu ya taro ya yi min yawa ji nake kamar na tashi na rufe su da mugun bugu.
Wayar Bilal Shattima ce ke ruri gata aje a gabanshi amma yaƙi ɗaga kira gaba ɗaya haushin wacce take kira shi yake ji ya rasa me kuma Hajja take nema a wurinsa, kira nan da take mishi yafi komai ƙona masa rai ya rasa kira me take masa, tun da ya ri ga kawar mata da matsalar ta domin a cewar ta Jeeddah ce babbar matsalata a rayuwa. Da son samu ne ta barshi ya ji da hali da yake ciki wanda ita ce ta jagoranci shigarsa ciki ɗan guntun tsaki ya ja kafin ya ɗauki wayar adakile ya ce "Hajja!
Tun daga yadda ya kira sunanta tasan yana jin haushinta ne duk da ta fahimci baya ciki yanayi mai daɗi hakan bai hanata faɗar abinda ke ranta ba "Duk abinda ka ke yi ka bar shi ka zo yanzu-yanzu nan Inaso ganinka.
Daga haka ta kashe wayarta jifa ya yi da wayar bisa gado kana ya dafe kanshi da dukkan hannuwanshi, jiki ba lakka ya tashi ya shiga bathroom ya yi wanka kayan da ya cire su ya sake maida wa jikinshi duk sun yi squeezing yana baro hotel ɗin a maimakon ya tafi kiran da Hajja take masa sai kawai ya yi shagon abokinsa Abbas dama ya yi magana dashi a waya za su je su ba wa Iyayen Jeeddah haƙuri, dole sai kasuwa suka nufa domin a daidai wannan lokaci Baba yana kasuwa. Kasancewar Baba mutum ne mai sauƙi kai da haƙuri ko kusa bai nuna wa Bilal Shattima ya ji zafi abinda ya faru ba sai ma ya ɗauki al'amari ya ɗora a mizanin ƙaddara.
   Abbas ya ƙara gyara zama gami da faɗin "Baba sai magana ta gaba cikin hukunci Ubangiji ya nufi Bilal da biyawa Jeeddah Makkah, sai kuma ga wannan ƙaddara ta kunno kai shine ya ce na ari bakinsa naci masa albasa na faɗa maka,  idan ALLAH ya nuna mana lokaci aiki hajji za ta tafi domin ya ri ga da ya biya da sunanta sai kuma motarta ta hawa zai aiko mata da abarta domin ita ma halak-malak ya mallaka mata ita don girman ALLAH da Manzonsa Baba kada ka ce mana a'ah. Domin Jeeddah ta cancanci Bilal ya yi mata abinda yafi wannan musamman idan aka yi la'akari iri sadaukarwa da tai mishi.
  Har Abbas ya dasa aya a zance shi Baba yana kallonshi gani shiru na Baba yana neman ya yi yawa yasa Bilal Shattima ya fara sharar hawaye gami da marairaicewa cikin karyar da murya mai ɗauke da shasshekar kuka ya ce "Na haɗa ka da girman ALLAH Baba kabar Jeeddah ta more kaɗan daga cikin arziki na domin tasha gwagwarmaya rayuwa yayin zamanta dani, duk abinda nai mata wallahi Baba ban biya rabin kwatankwacin abinda tai min ba.
   Ci-gaba da roƙon Baba suka yi gaba ɗaya suka ɗaure masa jijiyoyin jiki da kalaman bakinsu, kasancewar a kasuwa suke duk da sai da suka keɓancewa gun da babu yalwar mutane sosai, shiyasa Baba ya amsa musu da su tafi zai nemi su daga baya idan ya yi shawara ba yanda suka iya haka suka baro kasuwa jikinsu a sanyayye duk da haka ba su haƙura ba kaitsaye gidansu Jeeddah suka nufa kasancewar gidan ba bakonsu bane shiyasa kai tsaye suka shiga, mama tana parlourn ta ta ji sallamar su ta fito tana arba dasu tai ɓata fuska gami da yi musu dubi ɗaya ta watsar tana ƙoƙarin komawa cikin parlour Abbas ya yi sauri gaidata "Mama ina wuni?
  "Lafiya qalau ku kuma daga ina kun wani faɗo min ciki gida ba ko neman izini?"
"Mama mun zo ne mu ba ki haƙuri a bisa al-amari da ya faru.
"To! Haƙuri kuma?"
Mama ta faɗa cikin sigar mamaki gami da dafe da baki.
"Kwarai kuwa Mama Bilal ya saki Jeeddah ne ba a son ranshi ba shine ya ga dacewar mu zo mu ba ki haƙuri a matsayin ki na mahaifiyarmu. Mama ki yi haƙuri mu ɗauki wannan lamari a matsayin ƙaddara dukkansu su na son junansu sai dai iya wa'adin da ALLAH ya tsarawa rayuwar auren su kenan.
Nasani mutuwar aure ba shi daɗi Mama musamman irin wannan na Jeeddah, amma idan aka yi hakuri kana aka bar wa Ubangiji ikonsa sai ki ga al'amurra sun tafi ta yanda ba a yi zato ba.
Har Abbas ya kammala zancenshi Mama bata katse shi bata kuma furta uffan ba, kana kuma bata basu izinin shigar mata parlour ba, ta ƙara gyara tsayuwar ta ta shiga wankewa Bilal Shattima allonsa tass! Daga shi har mahaifiyarsa ba wanda ta ragawa sai tai musu wankin babban bargon mashaya, kafin ta gangaro da faɗin "jiraye nake da Hajja ALLAH ya haɗa mu ko akan hanyar ne sai na faɗa mata maganar da har ta komawa Ubangijinta ba za ta manta ba. Ita kuma Bahijja ta jira Ubangiji ne zai yiwa Jeeddah sakayya in-sha-Allahu ko akanta ko akan 'ya'yanta. Maza ku fice min daga gida bana ƙaunar ganinka Bilal ko a yanzu wani mugun haushinka nake ji sai ALLAH ya sakawa Jeeddah akanku baƙaƙen azzalumai.
  Gani yanda Mama ta taƙarƙare tana ta faɗin maganganu masu ɗan karan zafi yasa Bilal Shattima zube gwuiwayinsa akan floor, ya fashewa Mama da wani irin kuka yana faɗin "Dan ALLAH Mama ki yi haƙuri ki yafe min wallahi ba laifina bane ALLAH shaidata ne akan irin matsanancin son da nake wa Jeeddah, Mama rabuwa ta da Jeeddah na ɗauki shi a matsayin rubutacciyar ƙaddara domin ko mafalki ban taɓa kawowa raina cewa zan iya sakinta ba. Sai gashi ƙaddara ta riga fata.
   Sosai ya ba wa Mama tausayi taga ingarman namiji ƙato majiyi ƙarfi irin Bilal Shattima yana riskar kuka, kamar ɗan shayi "Tashi Bilal miƙe dan Allah!
Mama ta faɗa cikin sanyi murya sai kace ba ita bace few moments ago take zabga faɗa ba, ta juya tare da faɗin "Ku shigo daga ciki.
A ƙasan rugs suka zauna yayin da Mama ke kan cushion cikin sunkuyar da kai Abbas ya shiga faɗin "Mama muna neman alfarma da ki yiwa Baba magana dangane da Hajji da Bilal ya biyawa Jeeddah, ya barta taje duk da mu je kasuwa mun sami shi da Maganar sai dai yanayi da ya amsa mana muke gani Kamar ba zai amince ba. Mama ni aganina tun da ya ri ga da ya biya da sunanta kuma tun kafin su rabu ne ya biya mata dama ace bayan sun rabu ne kin ga zai iya zama wani issue na daban Dan ALLAH Mama ku barta ta je ta sauke farali.
Abbas ya ƙarashe magana yana ƙara sadda kai ƙasa, Mama tai jimm! Kafin ta ce "Ni ban isa na zartar hukunci akan wannan al'amari ba amma in-sha-Allahu zan yi iya ƙoƙarina wajen lurar da mahaifinta.
  "Shikenan Mama mun gode sosai da kika saurare mu ALLAH ya ƙara miki lafiya da nisan kwana mai amfani mun gode, mun gode Mama ALLAH ya jiƙan Iyaye.
  "Amin thumma Amin!
Mama ta amsa da murmushi akan fuskarta.
Sai lokaci Bilal Shattima ya ji wata 'yar gajeriyar natsuwa ta zo masa, ya ɗago rinani idanuwanshi ya ce "Mama ban ji motsi ƙaramin maigida ba ko ba a dawo daga makaranta bane?"
Mama ta ƙara faɗaɗɗa murmushinta gami da cewa "Ai sai ƙarfe uku yake dawowa saboda yana tsayawa lesson.
"Ayya shiyasa kam don naga har ƙarfe biyu ta gota ashe lesson yake tsayawa.
"Humm!
Cewar Mama kafin Bilal Shattima ya maida ganinshi akan Abbas ya yi mishi alama da ido nan take Abbas ya fahimci abinda yake nufi cike da jin kunya Abbas ya ce "Mama ban ji motsin Jeeddah ba ko tana gidan Aunty Farida ne gashi za mu tafi ba mu gaisa da ita ba.
   "Ai Jeeddah tana asibiti yau da safe aka yi admitting ɗin ta ni kaina ina jira Aiman ya dawo na tafi asibiti ɗin.
  "Subhanalillah! Kusan a tare Abbas da Bilal suka furta nan take hankali Bilal ya yi mugun tashi cikin sarƙewa lafazi ya ce "Mama tana wane asibiti ne?"
Mama ta faɗa musu hadda room number a  gigice Bilal ya yi sallama da ita suna fitowa suka sake ɗaukar hanyar zuwa asibitin da Jeeddah take.
A karo na ba a adadi da Engineer Ameer B. Sardauna ke kai hannunshi akan handle ɗin ƙofar ɗakin da Jeeddah take sai kuma ya tsinci kanshi da kasa buɗe wa ga zuciyarsa sai azalzalarsa take yi da son ganinta duk bayan wucewar daƙiƙa guda sai ya ji bugawar zuciyarsa na canzawa rashin Kwari gwiwa da ya samu daga zuciyarshi ya hana shi shiga ɗakin yana tsoron ya haɗuwa da mijinta, tun da ya ga shigarsa ɗakin kuma har kawo yanzu bai fito ba.
Parking space ya nufa ya shiga motarsa ya kifa kanshi a steering addu'a ya shiga yi akan sabon al'amari da ya kunnowa rayuwarsa domin yasan illar dake tattare da son matar wani.
Daidai kusa da motar Engineer Ameer su Bilal suka yi parking ya ɗago idanuwanshi ya kalle sau ɗaya ya kauda fuska ya fito daga motarsa ya sake nufar cikin asibiti duk wannan jiran da yake yi so yake mijin Jeeddah ya fita ya shiga ya ga hali da take ciki koda zai sami natsuwar zuciya, shi fa duk tunaninshi Haidar Ka'oje shi ne mijin Jeeddah, yana zuwa bakin ƙofar ɗakin ya kasa shiga ya juyo da sauri ya shiga wanda ummarsa take ciki,  kaitsaye ɗakin da Jeeddah take Abbas da Bilal suka dosa Abbas yana gaba Bilal Shattima yana biye dashi, tura ƙofa Abbas ya yi tare da sallama Aunty Farida ta amsa yayin da Haidar dake zaune daff da Jeeddah duk motsin da tayi sai ya yi mata sannu  kallo ɗaya Haidar Ka'oje yai wa su Bilal ya kauda fuska, Bilal Shattima ya yada ganinshi akan Haidar Ka'oje yana kallon yadda yake zaune kusa da Jeeddarsa har ƙugunshi yana manne da cinyoyinta domin yanzu ta juya ne tana kallon su Aunty Farida duk da ba kasafai take saka musu baki a firar da suke yi ba. Sai jifi-jifi take tankawa shima a takaice.
Wani irin mugun kishi ne ya kama Bilal da kyar ya iya buɗe bakinsa ya gaida Aunty Farida kana ya tamabaye jikin Jeeddah.
Ranshi ɓace ya taka zuwa kusa da gadonta, ina arba da Bilal naga yanda ya fita hayyacinshi duk sai naji wani irin mugun tausayinshi ya yi min dirar mikiya a ƙahon zuciya, sai na tsinci kaina da kasa haɗa idanuwa dashi na shiga ƙoƙari tashi zaune sai kawai naji saukar hannuwan Ya  Haidar a kafanɗuna ya tashe ni zaune gami da jingina min pillow a bayana hadda wani tattaɓa gefen wuyana, duk sai naji ba daɗi musamman da na saci kallon Bilal naga idanuwanshi suna kanmu.
Ɗauke da murmushi Haidar Ka'oje ya miƙawa Bilal hannu su yi musabaha Bilal ya maƙale hannunshi sai kawai ya wani ce dashi "Sannu.
Ni kaina yadda ya yi ban yi min daɗi ba, shiyasa nai sauri ɗauke fuskata akanshi, cike da rashin damuwa Haidar ya dawo kusa dani ya zauna.
   Cikin dakiya irin wacce aka san ɗa namiji da ita Engineer Ameer B. Sardauna ya tura ƙofar ɗakin cike da taurin zuciya ya yi sallama kusan duk wanda ke ɗakin sai da ya waigo yayin da zuciyar Jeeddah ta shiga luguden aradu idanuwanta cike da mamaki take kallonshi....

#Jeeddah Aliyu
#Zazzafan kishi
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*ZAMANIN MU A YAU*
           Na
Jeeddah Aliyu
          &
Nana Diso

_*ƊÁÑƊAÑO*_

Kallon tsana Leemart take aikawa mahaifiyarta ji take kamar ta tashi ta rufe ta da shegen duka, duk duniya in da akwai wacce ta tsana bai wuce mahaifiyar ta ba. Domin duk ita ce silar hana ta mallakar abinda take so Mustafa Ali Matawalle shine cikon farin cikinta sai dai kashhh! Ba za ta taɓa mallakar shi a matsayin mijin aurenta ta cikin ruwan sanyi ba, a dalili baƙin painting da mahaifiyarta tayi mata, saboda haka tasha alwashi ta ko wanne hali sai ta cika burinta koda hakan yana nufi za ta rasa abubuwa masu matuƙar muhimmanci a rayuwarta lallai sai ta mallaki Mustafa Ali Matawalle.
Cikin ƙonar zuciya haɗe da zallar ɓacin rai Barrister Suleiman Abba Garkuwa ya dakawa Surayya tsawa abinda tun aurensu bai taɓa yi mata ba. "Ya isa haka Surayya sau nawa kike so nai ta maimaita miki cewa gantalalliyar ƙanwarki bata da masauki a gidana. Tattara Kayanta yanzu nan ta bar min gidana tun muna sheda juna dake in banda sakarci irin naki surry yarinyar da ta gaggari iyayenku shine ni za ki kwaso min ita to wallahi ba a gidana ba.
   Ringing ɗin waya ne ya katse wa mahanoor Yusuf Zanna baccinta mai shegen daɗi a fusace ta tashi ta ɗauki wayar gani suna manager gidan television ɗin da take aiki ya saka ta wartsakewa, sai da ta gallawa wayar harara Kafin tai receiving ta kara a kunne adakile ta furta "Hello Sir!
   "Zanna kina da hankali kuwa?"
Turo baki tayi kafin ta ce "Sir da bana da hankali na tabbata gidan telebijin ɗinku ba zai ɗauke ni aiki ba.
  "To ni gaskiya ina tantama akan hankalinki lallai kina da buƙatar gani likitan ƙwaƙwalwa saboda haka duk abinda kike yi ki jinginar dashi I want to see you in the next 20 minutes in my office.
  "Sir 20 minutes fa? gaskiya sir hakan ba dai-dai bane yaushe nayi wanka har na shirya naci abinci duk a 20 minutes.
  "Umarni ne idan ba ki zo ba nan da 20 minutes zan yi replace ɗin Nancy a show ɗinki.
Daga haka ya kashe wayarsa dafe kai Mahanoor tayi duk duniya manager shine matsalarta a rayuwa kwata-kwata batasan wani abu wai shi ɓacin rai ba sai ta fara aiki a gidan Tv Haske television.

*Kar ku bari a ba ku labari wannan tafiyar ta musamman ce domin cike take ta cakwakiya, cin amana, nadama, uba-uwa zazzafar soyayya mai ratsa jini da bargo*
  

050..

Ƙoƙarin saita natsuwata wuri ɗaya nayi yayin da a can ƙasan zuciyata cike take da tarin tambayoyi akanshi. Kasa haƙuri nayi har sai da nayi magana da zuciyata "Shi kuma wannan daga ina ya ɓullo?"
Yayin da ɗayan sashe zuciyata ya ce da ɗayan sashe, "To ko kuma tare dasu Bilal yake?"
Ɗayan sashe ya mayarwa ɗayan sashe da tambaya a maimakon amsa.
Kamar daga sama naji sautin muryarsa yana faɗin "Sannunku jama'a ya mai jiki?"
  "Al-hamdulillah! Jiki da sauƙi sosai.
Cewar Aunty Farida wacce ta tashi daga kan kujera da take ta ce dashi ya zauna "No ki yi zamanki kawai tafiya zan yi ba zan daɗe ba.
Yayin da Aunty Farida ta koma ta zauna abinta, walking majestically ya tunƙaro gadona a can ƙasan zuciyarshi yana tuna girman abinda ya aikata yana isowa kusa da gadona Bilal Shattima yana cewa "Love ya ƙarfin jiki?"
Kasa amsawa nayi sai kawai na sadda kaina ƙasa.
Cike da gundarin mamaki Engineer ya kalle Bilal kana ya sake maida ganinshi akan fuskar Haidar Ka'oje ƙoƙari yake ya gano shin ya ji kalmar da ɗa baƙi mutuminan ya kira matarsa dashi ko kuwa shi kaɗai ne kunnensa ya ji, ga ƙarin mamakinsa sai ya ga Haidar ya miƙe tsaye gami da faɗin "Jeeddah zan fita amma ba zan daɗe ba idan kina buƙatar wani abu Aunty Farida ko Khairat su kira ni.
Daga haka yasa kai ya nufi ƙofar fita daga ɗakin Aunty Farida tana mishi fatar adawo lafiya.
Haidar Ka'oje ya fita ne a dalili zuciyarshi ba za ta iya jure ci-gaba da kallon fuskar Bilal Shattima ba domin tun aurenshi da Jeeddah bai taɓa haɗuwa dashi face-to-face ba. Sai dai ya hango shi daga nesa shiyasa ko yanzu ya bar mishi ɗakin gudun kada wani abu marar daɗi ya faru a tsakaninsu musamman shi da bayaso hayaniya ko kaɗan.
Da kallon mamaki Engineer Ameer ya bi bayan Haidar dashi shi kam bai taɓa gani nusari irin Haidar ba taya wani ƙaton banza zai kira matarka da suna Love kuma a gabanka ka kasa tabuƙa komai ƙarashenta ma ka bar mishi wuri wato ya yi wadaƙarsa iya wayi sa lallai Haidar wawa ne baya kishin matarsa tun da haka ne ashe ta zo mishi gidan sauƙi kwace ta daga hannunshi ba zai min wuya ba. Da ya zo karshen wannan zanci zuci nashi bai san sanda ya saki ɗan guntun murmushinsa ba.
Abbas ya kalle ni tare da cewa
"Jeeddah ya ƙarfin jiki?"
   Na amsa mishi cikin ƙaramin sauti ta hanyar furta
    "Al-hamdulillah!
"ALLAH ya ba ki lafiya yasa kaffara ne.
Na sake amsa mishi da
    "Amin Nagode Abbas.
Kana Abbas ya juya wurin su Aunty Farida ya ce "Aunty sai anjima ALLAH ya bata lafiya.
  "Amin Abbas sannu da ƙoƙari mun gode a gaida gida.
  "Gida zai ji Aunty.
"Shattima sai ka fito ina mota.
  "Okay bani five minutes.
"Ba damuwa abokina take your time!.
Abbas ya ƙarashe magana tare da yi min sallama gami da sake yi min fatan samun lafiya.
Bayan fitar sa ne Engineer ya kalleta da fuska a sake cikin dakewa ya ce "Maijiddah ashe ba ki ji daɗi ba?"
Cikin sanyi murya na amsa mishi da "Eh! Amma na ji sauƙi sosai.
   Idanuwanshi suna yawo akaina kafin ya ce "ALLAH ya ƙara sauƙi nima ummana ce ba lafiya ɗakinta yana facing naki ɗazu da safe naga an kawo ki shine nace bara na shigo nai miki sannu.
    "Subhanalillah! ALLAH ya bata lafiya.
     "Amin maijiddah kema ina miki fatan samun sauƙi. Ni zan tafi sai na sake shigowa.
      "Nagode sosai da kulawa ka gaida umma.
  "Za ta ji Aunty sai anjima.
Ya ƙarashe magana gami da kallon gun da Aunty Farida take zaune cike da fara'a Aunty ta amsa mishi, kafin ya fita sai da sake kallon Bilal Shattima dake rakuɓe a jikin ƙarfen gado da nake sai rarraba idanuwa yake yi tare da mamaki waye wannan mutumin da ya zo duba ni.
Bayan Engineer ya fita Bilal ya yi gyara murya ya sake tambayata ya jikina na amsa mishi kafin ya shiga bani labari daga wuri Mama suke ita ce ta basu labari ina asibiti. Sai da ya saci kallo su Aunty Farida ya ga hankalinsu baya kanmu sai ya yi ƙasa da murya ta yanda ni kaɗai nake ji abinda yake faɗa sai ya ce "Love i really, really miss you ban taɓa shiga ƙunci iri na dare jiya ba. Har ji nayi kamar zan yi hauka ban ƙara tabbatar wa da kece bugun zuciyata sai a jiya da na kwana babu ke a kusa dani wallahi love ina bala'in sonki ke ce farin ciki rayuwata na tabbata rabuwa mu ita ce za ta kassara min rayuwa.
Ya ƙarashe magana yana sharar hawaye wani iri mugun tausayinshi ya kama ni. Nayi ƙasa da murya na ce "Ka yi haƙuri Love haka ALLAH ya tsara mana ba mu isa mu gujewa ƙaddarar mu ba. Dan ALLAH ka daina kuka idan ina gani hawaye akan fuskarka hakan zai iya ƙara linka min damuwar da nake ciki, kayi ƙoƙari ka cire duk wata damuwa a ranka gudun kada ya taɓa lafiyar jikinka.
Wani irin dogon numfashi ya ja gami da goge hawaye fuskarshi da tafin hannunshi kafin cikin rauni murya da karaya zuciya ya ce "Damuwa kam dole na shige ta tun da na rasa danƙarerriyar mace kamarki a kuma dai-dai lokaci da nake tsanani son kasancewa dake.
  "Humm! Na faɗa tare da sadda kai ƙasa kana na numfasa na ci-gaba da faɗin "Love kenan karka manta da kana da wata mata duk wannan damuwar na ɗan lokaci ne da zarar kun tare a sabon gidanku, za ku buɗe sabon shafi na soyayya tun kana tunawa dani wata rana za a waye gari ka manta dani abu ɗaya ne zai sa ka tuno dani idan ka yi marmari gani Aiman shi ma idan ta haifa maka wasu 'ya'ya mantawa za ka yi dashi. Bilal a duk lokaci da na tuna cewa shikenan na zama bazawara sai naji wani iri ƙunci ya ziyarci ni ban taɓa kawowa rayuwata zan rabu da kai ba sai gashi kwatsam! Alƙalami ƙaddarar mu ya zo da hakan.
Na dasa aya gami da rushewa da wani iri kuka mai azababben cin rai da taɓa zuciyar mai karatu.
   "Subhanalillah....kai Bilal! Mi ka faɗa mata ne take kuka?
Cewar Aunty Farida ta Kuma taso a mugun fusace taho kusa dani ta zauna tare da rungumeni Khairat ma ta taso ita ma cikin fusata ta shiga faɗi maganganu masu zafi dama tafi Aunty Farida ɗaukar zafi kasancewar tun farko ba ƙaunar Bilal Shattima take yi ba sai faɗin take yi "Ka ga malam kama hanya ka tafi ba ma buƙatar ka anan banda reni wayau ka saki mace saki har uku sannan don kuturun wulaƙanci babu Kunya balle tsoron mahalicci ka ɗebo ƙafafuwa kamar sanda kada shanu ka zo gun ta ka sani yanzu babu burbushi wata alaƙa tsakaninku, saboda haka mun sallame ka maza ɓace mana da gani. Ko don kaga mu zuba maka ido ka shigo ɗakinan karka zaci cewa kana da sauran daraja da ƙima a idanuwanmu. To ba haka bane mu kyale ka ne kawai don mu a gidanmu ba a yi mana tarbiyyar wulaƙanta mutane ba, da tun shigowar ka zan kaɗa ƙeyar ka waje saboda haka cikin girma da arziki ka fita tun kafin na tara maka jama'a munafuk....
    "Khairattttt!
Bansan lokaci da na raba jikina da na Aunty Farida ba har na sami ƙarfi daka mata irin wannan rikitatciyar tsawa, na yunƙura na tashi tsaye wani irin jiri ya kwashe ni da sauri Aunty Farida ta taro ni kasancewar jikina har yanzu bai yi wani kwari kirki ba. Ta zaunar dani da sauri Bilal ya ce dani "Sannu Love kwanta abinki karki damu da abinda Khairat take faɗa dama tun fil'azal ba ƙaunar aurenmu take yi ba shikenan yanzu sai ta zuba ruwa a ƙasa ta sha.
   "Fiye da abinda yafi ruwa sai na zuba nasha Bilal idan ma ka ce bana ƙaunarka ba ka yi ƙarya ba domin tun farko Jeeddah bata dace da mutum irinka ba.
   "Khairat ya isa haka Dan ALLAH.
Aunty Farida ta katseta yayin da na runtse idanuwana domin ba ƙaramin zafi maganganu Khairat suka haifar min dashi ba. Ban taɓa jin takaici Khairat irin yau duk da ba yau ne rana ta farko ba da ta saɓa faɗa maganganu marasa daɗi akan Bilal ba.
   "Ka ga Bilal ka tafi abinka mun gode ALLAH ya bada lada dubiya amma Dan ALLAH karka sake zuwa domin yanzu an daina kiwon dabbobin an koma na mutane. Ba ma so abin magana.
   Duk sai Bilal ya ji wani ban-barankwai ya juya jiki a mace ya buɗe ƙofa kafin ya ƙarashe fita ya juyo ya kalli Jeeddah da ke ta faman gunshaki kuka yasa kai da sauri ƙarasa fita.
Ta ɓangaren Haidar Ka'oje kuwa a dalili baya so gani Bilal Shattima shiyasa ya ƙiƙƙiro fita tsanar da yake ji yana yiwa Bilal ko lokaci da  aure Jeeddah bai ji irinta ba, domin ba ƙaramin haushin saki da ya yi mata ya ji ba musamman idan ya tuna irin sadaukarwa da tai masa duk da ya kasance ba shi da aiki yi a haka ta amince ta aureshi shi ne  don tsabagen butulci zai mata kishiya daga ƙarshe kuma ya sake ta. Shiyasa tun farko yaƙi amincewa da buƙatar Jeeddah ta alƙawanta mata ba zai taɓa yi mata kishiya ba domin bai san ya gobensa za ta zo masa ba. Baya so ya ɗauki alƙawari ya zo daga baya ya karya shi domin yasan muhimmanci alƙawari. shiyasa ya ƙudurta wa zuciyarshi da zarar ta kammala iddarta zai aure ta domin shi kaɗai ya cancanta ya kasance tare da ita a dalili tsanani tausayinta da yake ji. Da wannan zance zuci ya isa kamfanin shi.
  Engineer Ameer B. Sardauna yana fitawo daga ɗakin da Jeeddah take ya ji tamkar an zare mishi ƙaya wani irin farin ciki yake ji sai uban murmushi yake zabgawa tsabar farin ciki ya rasa inda zai jefa kanshi, cike da walwala ya tura ƙofar ɗakin da ummarsa take, tana zaune tare da aminiyarta Hajiya Tambai suna fira yanda ya shigo fuskarsa shimfiɗe da murmushi ya katse wa umma zance da take yi cike da mamaki take kalloshi, shi ɗin ma ya kafe ta da nashi idanuwa rabon umma da ta ganshi cikin farin ciki irin wannan har ta manta shiyasa cikin rawar murya ta ce.....

*Just to manage kar ku damu gobe in-sha-Allah  zan yi update kuma long page😄*

#Jeeddah Aliyu
#Zazzafan kishi
#Sabon Salo.[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

051..

"Ameer meke faruwa ne naga ka shigo kana zabga fara'a sai kace wanda aka yiwa bushara da gidan aljanna?"
   Kusa da ita ya nema ya zauna ya kama hannunta ya haɗe da nashi zuciyarshi fess! Ya shiga faɗin "Umma na ganta duk da tana cikin yanayi na jinya hakan bai dusashe farin ciki da nake ji na gami da ganinta da nayi ba.  Umma soyayyar maijiddah dabam ce a cikin zuciyata, a wasu lokuta har na kan ji tamkar ban taɓa so wata 'ya mace ba sai akanta. Dan ALLAH ummata ki tayani da addu'a na mallaketa domin ita ce muradina abinci ruhina.
   Har ya kawo ƙarshen zance shi umma da ƙawarta Hajiya Tambai suna kallo shi, yayin da umma ita kaɗai tasan hali da zantuka shi suka jefa ta ciki, daidaita natsuwa umma tayi gami da sauke gwaron numfashi kafin cikin fargaba ta furta "Ameer wacece Maijiddah waye ita shin yaushe ka ƙula alaƙa mai ƙarfi irin wannan da ita ni da nake matsayin mahaifiya a gareka ba ka taɓa faɗa min ba?"
   Sadda kanshi ƙasa ya yi zuciyarshi tana wani irin bugawa da ƙarfin gaske wato yana dubin ta ina zai fara sanarda umma wacece Maijiddah.
   "Ameer ka buɗe baki ka bani amsa shiru ka yana nufi abubuwa da dama banaso zuciyata ta dasa min zargi akanka.
  Cike da kunya abinda zai fito bakinsa ya ɗago idanuwanshi ya kafe umma dasu, kafin ya ce "Maijiddah ita ce yarinya da na taɓa ba ki labarinta  almost seven years ago, umma cikin hukunci Ubangiji har na fitar da rai da ƙara haɗuwa da ita sai gashi kwatsam! Kwanaki uku da suka wuce na haɗu da ita, yanzu haka tana asibiti nan a ɗakin da ke facing naki bata da lafiya a iya bincike da nayi domin ji irin ciwo da ke damunta abin mamaki umma Maijiddah tana fama da cutar hawan jini which means mijinta yana ƙuntata mata bata jin daɗi zama dashi, saboda haka na ɗaura ɗamarar kwace ta daga gare shi walau ta sauƙaƙƙiya hanya ko kuma akasin hakan. Ni dai muradina guda ɗaya ne na kasance Inuwa ɗaya da ita.
    Ya ƙarashe magana yana wani irin huci ƙofufin hancinshi yana fitar da iska mai zafi wata irin fargaba gami da tsanani tsoro suka lulluɓe umma, tasan wanene ɗanta ta kwana da sani hali naci da kafuwar sa bai iya son abu ba musamman akan soyayyar mace ta wannan fanni bashi da kyau ko kaɗan, komai zai iya aikata wa domin ya mallake abinda yake so.
  "Umma zan tafi gida nayi wanka ba zan jima ba zan dawo idan da akwai abinda kike da buƙata na taho miki dashi?
Sautin muryarshi ce ta fargar da umma daga duniyar tunanin da ta faɗa cikin sauri ta dakatar dashi domin har ya kai ƙofar fita "Ameer idan har ni na haifeka, ka sha daga gareni to ka fita sabgar matar mutane, ka yaƙi shaiɗaniyar zuciyarka da take kwaɗaita maka soyayyarta da ta haƙura da ita domin koda ta kasance batada igiyar aure wani akanta ba zan taɓa amincewa da ka ƙara yi aure a rayuwarka ba. Ina so ka gaggauta goge babinta a zuciyarka ka manta da ita koda hakan zai cutar da kai.
  Cike da zallar tashin hankali Engineer Ameer Bello Sardauna yake kallon ummarsa da ta koma ta kwanta gami da juya masa baya, da sauri ya ƙarasa buɗe ƙofa ya fita yana tafe yana haɗa hanya da kyar ya isa parking lot ya buɗe mota ya shiga yana maida numfashi wani iri yake ji a jikinsa ba ko tantama yasan ciwonshi ne yake so tashi, da sauri ya tashi mota da mugun gudu ya fita daga asibiti.
   Abbas ya juya ya kalle Bilal Shattima da ya buɗe mota ya shigo ranshi a ɓace sai sauke numfashi yake yi akai-akai sai da Abbas ya ɗauki hanya kafin ya ce "Ya aka yi ne abokina naga ka fito rai ɓace ba dai wulaƙanta ka Jeeddah ta yi ba ko?
"Huhmm! Abbas ba Jeeddah bace asalima ba taji daɗi abinda Khairat tayi min ba. Abbas wallahi na tsani Khairat da ɗan iska nan Haidar Ka'oje kana gani yadda muka tarar dashi manne da Jeeddah, Abbas idan har Haidar Ka'oje ya ci-gaba da bibbiyar matata tabbas ba zan iya sarrafa fushina ba, zai kai matakin da zan ɗauki mummunan mataki akan guy nan. A matsayin ka na abokina kuma amintatce na ka dubi hali da nake ciki ka nemo min mafita Abbas ban taɓa sani ina tsanani ƙaunar Jeeddah har ka ba sai da na rasa ta. Ka tausaya wa rayuwata abokina ka nemo min hanya da Jeeddah za ta sake kasancewa matata a karo na biyu.
  Bilal Shattima ya ƙarashe magana yana hawaye, da gaske yake yi wata irin masifaffiyar soyayyar Jeeddah yake ji tana bin jini da ɓargon jikinsa.
   Shiru Abbas ya yi na ɗan wani lokaci kafin ya riƙo hannun Bilal ya haɗe da nashi cikin kwantar da murya ya ce "Calm down abokina ka sassauta wa zuciyarka mana kalli yanda ka bi ka ɗagawa kanka hankali yau kaɗai duk ka fita hayyacinka, ka ɗaure ka bani ɗan wani lokaci ƙalilan na zauna nayi nazari ta ina za mu fara.
   "Shikenan Abbas na yarda da kai domin ba ka taɓa bani shawarar banza ba. Ka yi nazari mai kyau ni kawai so nake matata ta dawo gareni ko nawa ne zan iya kashewa domin buƙatata ta biya.
  Nusaiba tana zaune a gaban Hajja tana rera kuka kwata-kwata ta kasa gane idan Bilal Shattima ya dosa, ta kira wayarshi kira yafi a kirga bai ɗauka ba. Ta rubuta mishi messages babu adadi nan ma yaƙi responding daga ƙarshe ma sai ya dannawa numberta blacklist yanzu ko ta kira shi sai dai taga user busy, a takaice zuciyarta ta kasa ɗaukar wannan baƙon al'amari shi ne ta zo da kanta wajen Hajja domin ta ji musabbabi wannan sabon sauyi saboda bahaushe yana cewa zuwa da kai yafi saƙo gara ta zo da kanta ayi ta, ta ƙare ina amfani baɗi babu rai. Sai da ya fara lasa mata zuma a baki sai kawai ya guje ta.
Hajja tayi rarrashinta har ta gaji ta zuba mata idanu da ta ga kukan nata ba mai ƙare wa bane, babu shiri Hajja ta ɗauki wayarta ta kira Aunty Bahijja ta zo domin ita ce jagaban haɗa wannan aure. Gara ta zo watakila tana da magani magance wannan kukan na Nusaiba.
   Sosai na ji raina ya yi mugun ɓaci akan irin wulaƙanci da Khairat ta yiwa Bilal ko kaɗan ban ji daɗin hakan ba, asalima haushinta naji shiyasa ina gani ya fita rai ɓace na hayyaƙo wa Khairat cikin kakkausar murya nake faɗin "Wannan wane irin kuturun wulaƙanci ne Khairat akan wane dalili za ki faɗawa Love irin waɗannan maganganu?"
   "Excuse me! Me naji kin kira shi dashi anya kuwa Jeeddah kina da hankali?"
Khairat ta tambaya cikin kaɗuwa da al'ajabi, a fusace na ce "abinda duk kunne ki ya ji dashi na kira shi ko za ki hana ne?
   "Kai dallah ya isa haka!  Nan fa asibiti ne ba gida ba.
Aunty Farida ta faɗa cikin daka mana tsawa, yayin da Khairat ta ce "Aunty ita za ki yiwa faɗa ya kamata ta yiwa kanta karatun ta natsuwa ta fahimci yanzu babu wani abu da yai saura tsakaninta da Bilal Shattima, zance ta cigaba da kiranshi da Love gara tun wuri ta jingina shi a gefe.
   "Ina ruwanki da duk abinda zan kira dashi ni naji zan iya ke miye naki a ciki 'yar baƙin ciki kawai.
    Na faɗa ina mai galla mata harara Aunty Farida ta ƙarbe zance tana faɗin "gaskiya ne abinda Khairat ta faɗa Jeeddah inaso ki sani ci-gaba da kira Bilal da Love zai iya haifar miki da matsala domin a yanzu babu wata alaƙa da za ta sa ki kira da suna Love saboda haka wannan ya zama na farko kuma na ƙarshe da zan sake jin wannan suna ya fito daga bakinki.
   Kauda kaina gefe nayi zuciyata tana tafarfasa ji nake kamar na fashe da kuka. Domin ba su san irin mugun tausayi Bilal da ya darsu a zuciyata ba.
  Abbas ya ce da Bilal  "Shattima ka yi haƙuri mu je ka ji kira da Hajja ta ke maka.
   "Ko na je babu abinda zan yi mata Abbas saboda haka ba inda zan je duk bala'i da nake ciki duk ba ita ba ce silar jefa ni cikinsa ba. Jiya-jiya da rabuwa ta da Jeeddah Abbas dube ni da kyau ka  ga yadda na dawo, tamkar wanda ya shekara yana jinya ni dai wannan biyayyar da na yiwa Hajja ta cutar dani matuƙa.
  "Ka daina faɗar haka Shattima su Iyaye ba abin wasa bane muddin muna so mu ga dai-dai a rayuwarmu dole mu bi su sau da ƙafa mu yi musu biyayya, su kuma kada su yi amfani da biyayya da muke so musu su cutar da mu kamar dai yadda Hajja tai maka ta raba ka da matarka alhali kuna son junanku amma duk da haka ka yi haƙuri ka miƙawa Ubangiji lamurran ka in-sha-Allahu za ka ga haske. Yanzu ka yi haƙuri mu je duk abinda za ta faɗa ka zauna saurare ta.
   "Shikenan mu je ɗin na ji me kuma take so nayi mata.
Haidar Ka'oje ya dawo niƙe-niƙe da manya ledoji  yana miƙawa Khairat ya sake fita ya karɓo sakamakon gwaji da aka yi min yana gani negative ya saki doguwar ajiyar zuciya, gami da yin hamdallah! Fuskarshi cike da murmushi ya shigo yana zuwa ya miƙawa Aunty Farida result ɗin, dariya Aunty Farida da Khairat suka dinga yi masa yayin da ni kuma su duka suka yi bala'in bani haushi ji nake kamar na tashi na rufe su da duka.
Duk abinda suke faɗa ina jin su nai banza dasu sai da yamma Mama da Mommy Turai suka zo duk wanda ya zo duba ni yaga yanda Ya Haidar yake kula dani haɗe da tarairaya ta sai ya yaba mishi saɓani ni da yake bani haushi.
   "Hajja gaskiya Bilal ya yi mugun rena ki in banda reni tun yaushe ya ce gashi nan zuwa har yanzu bai ƙaraso ba ya wani shanya mutane sai kace kayan wanki.
   Aunty Bahijja ta faɗa tana yatsine fuska.
Kafin Hajja ta bata amsa ta ji murya Bilal ya bankaɗo curtain yana faɗin....

#Jeeddah Aliyu
#Team Haidar Ka'oje
#Team Bilal Shattima
#Team Engineer Ameer
#Zazzafan kishi.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*_Assalamu Alaikum ina mai ba ku haƙuri dangane da rashin samu ci-gaban labari Zazzafan kishi, ina mai muku albishir da na dawo za mu ɗora daga inda muka tsaya sai dai ba za ku dinga samu update kullum ba a dalili ina typing paid book da fatan za ku ci-gaba da kasancewa tare dani_*

052..

"Da kyau baƙar munafuka almura wacce bata da aiki sai haddasa fitina.
  Daga Aunty Bahijja har Hajja kallonshi suke yi baki buɗe domin maganarshi ta zo musu a bazata cike da mamaki Aunty Bahijja tai pointing ƙirjinta tana faɗin "Ni Bilal ni ka kira da munafuka almura?"
   "Ke ɗin ko kina da wani suna ne da ya fi wannan?" Ai Aunty Bahijja matuƙar ba ki tubarwa ALLAH ba ki ka nemi yafiyarmu ni da Jeeddah to kisani hakkin mu zai ta bin ki ne har izuwa cikin kabarinki da matuƙar wahala wutar jahannama bata ƙona ki ba saboda sunnah ma'aiki Sallallahu alaihi Wasallam! Ki ka raba.
Bilal Shattima ya faɗa yana huci yayin da yake ji wani irin takaici da tsanar Aunty Bahijja domin duk ita ce silar ruguza masa farin ciki.
  Da sauri Abbas ya ƙarasa kusa dashi ya ja hannunshi suka nufi three seater ya zaunar da Bilal yana faɗin "Calm down abokina Dan ALLAH ka danne zuciyarka yanzu ba lokaci musanya yawu bane saboda mai aukuwa ta ri ga da ta auku....
   "Daina bashi baki Abbas bar shi ya yi min rashin Kunya iya son ranshi, da gani yadda yake wannan haukar kasan ba yin kasa bane, har yanzu da raguwar asiri wancan 'yar matsiyatan a jikinshi.
  Wani irin zabura Bilal ya yi ya hayyaƙo wa Aunty Bahijja kamar zai rufe ta da duka sai faɗin maganganu marasa daɗi yake yi, sai da Hajja tai masa rantsuwa idan ban yi shiru ba ranshi zai ɓaci sannan ya koma akan kujera ya zauna sai ƙwafa yake yi akai-akai gami da girgiza ƙafa, yana sauke zazzafan numfashi Hajja ta dube shi cikin kakkausar murya ta ce "Ban kira ba don ka zo ka shukka min rashin ɗa'a anan ba. Na kira ne domin naji dalili da yasa ba ka ɗaga kiran matarka?"
A hasale ya ciro kanshi ya dubi Hajja adakile ya furta
  "Wacce daga cikin matan nawa?
Bilal ya faɗa yana shan ƙamshi tamkar ba da  Hajja da yake magana ba, sam babu girmamawa sai kace ba Bilal ɗin da yake daraja duk wani furuci da zai fito daga bakin Hajja ba. Amma sai gashi yau yana mata magana cikin gatsali.
   Sosai hanta cikin Hajja ta kaɗa domin ba ta taɓa tsammani fitar wannan tambayar daga bakin ɗa nan ta ba. Za ta iya cewa duk a cikin 'ya'ya da ta haifa Bilal yafi su yi mata biyayya tun shi na yaro ƙarami bata taɓa faɗa ya musanta mata ba. Sai gashi yau yana amsa mata magana gatsal-gatsal kamar yana magana da sa'an shi sani da tai wa Bilal ko Aunty Bahijja dake matsayin yayarshi yana girmama ta matuƙa balle ita da take mahaifiyar shi. Lallai biri ya yi kama da mutum maganar Bahijja akwai ƙamshin gaskiya a cikinta, in banda aiki asiri ta ya Bilal zai mata irin wannan tambaya. Danne mamakinta tayi ta ce dashi "wannan wacce irin tambayar banza ce ka ke min Bilal kana da wata mata ne da ta wuce Nusaiba?"
  "Ohhhh! Nusaiba wai.
Ya faɗa cikin sigar kamar idan mutum ya tunowa da wani abu da ake so ya tuna.
Nusaiba wacce take rakuɓe a jikin bango ta rushe da kuka domin tun shigowar Bilal taga yana yi da ya shigo dashi ta sha jini jikinta, yanzu kuma da ta ji abinda ya faɗa yasata fashewa da kuka domin har ga ALLAH tana son Bilal Shattima ba ta da buri da ya wuce ta shiga tanfatsetse gidan da ya gina musamman yanzu da ta ji labari ya saki Jeeddah har tana murna za ta ci karenta babu babbaka sai gashi tun ba a je ko ina ba murnarta tana ƙoƙari komawa ciki domin uban gayya ya zo mata da wani sabon samfuri wanda zuciya da gangar jikinta ba za su jure ɗaukar shi ba.
   "Ke dallah! Rufewa mutane ƙaton bakinki.
Bilal ya dakawa Nusaiba rikitatciyar tsawa wacce ta gigita ta babu shiri ta haɗiye kukanta, gami da dafe bakinta da ya kira da suna ƙato. Hajja ta kalle shi ranta ya kai ƙololowa wajen ɓaci, ta ce "Daina yiwa 'yar mutane tsawa ni ya dace kayiwa tsawa ba ita ba.
   "Ko kuma ya zo ya rufe ki da duka ba don naga wani rashin mutunci yake taƙama dashi.
Aunty ta faɗa tana danna mishi ƙatuwar harara.
Zuciyar Bilal tana tafarfasa ya kalle gun da Aunty Bahijja take cikin kakkausar murya mai cike da alamar gargadi ya ce
   "Aunty Bahijja ki fita sabgata ko na ta-ta miki rashin mutunci tun daga ranar da kika zama silar rabani da matata farin cikina na daina gani ƙima da darajarki Wallahi-azim idan ki ka kaini bango ko dukanki zan iya gara ki rufawa kanki asiri ki raba kanki dani.
    "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Bilal Bahijja ce za ka daka yayar taka ce za ka daka? Lallai Bilal ba ka hayyacinka ALLAH ya isa tsakanina da Jeeddah da zuri'arta.
Hajja ta faɗa tare da rushe wa da kuka Aunty Bahijja tana tayata, duk yadda Abbas yaso ya yi sulhu a tsakaninsu ya kasa a fusace Bilal Shattima ya miƙe tare da kakkaɓe rigarshi yabar musu gida. Abbas ya tsaya yana rarrashinsu domin gaba ɗaya sun cika falon da koke-koke sai kace gidan mutuwa da yaga lamarin nasu ba mai ƙare wa bane ya bi baya Bilal har suka iso gidanshi yana yiwa Bilal nasiha da yabi komai a hankali.
   Tun lokaci da Engineer Ameer ya iso gidanshi yake kwance akan sofa dake girke a falonshi furuncin ummarshi ke mishi kai komo a ƙwaƙwalwarshi idan har ummarshi ta kafe lallai sai ya rabuda Jeeddah ba shakka za su yi baƙin arbo domin gani da ya yi mata a yau ɗinan ya ƙara linka mishi zazzafar soyayya da yake mata a shirye yake da ya yi fito-na-fito da duk wanda ya nemi ya yi mishi katanga da ruhinshi domin Jeeddah ita ce rayuwarshi ba ya jin akwai wani mahaluki a doron kasa da ya isa ya yi mishi shamaki da cikar burin shi.
   "Jiddoh ki tashi ki ci shawarma saboda ke na siyo kin ga Khairat tana ƙoƙarin cinye wa ki tashi Dan ALLAH ki ci ko kaɗan ne kada ta cinye.
   Ya Haidar ya yi min magana cikin sigar rarrashi domin tun yamma da muka yi hatsaniya da Khairat nake shan ƙamshi na kasa bari jin haushinta, gani yadda Ya Haidar yake ta faman yi min magiya yasa na tashi zaune ina yatsine fuska Khairat dake zaune akan plastic chair tana cin shawarma ta waigo ta kalleni ta taɓe baki kana ta ɗauke kai. Yanayi kallo da tai min ba ƙaramin sosa min rai ya yi ba, amma shiyasa ba kwafa gami da kwaɗa wa ƙeyarta harara duk abinda nake yi Ya Haidar yana tallaɓe da kumatunsa yana kallona yana sakin murmushi duk yadda naso ya bani shawarma naci da kaina yaƙi dole sai ya yi feeding ɗina ba yadda na iya dole na buɗe baki ya dinga bani.
A takaice kwana uku a asibiti aka sallame ni duka cikin kwanaki uku ɗinan Ya Haidar yana tare dani duk wasu ayyukan shi masu muhimmanci ya jinginar dasu, ta ɓangare Engineer Ameer shima har aka sallame ni yana shigowa ya duba ni wani sa'in har sau biyu yana shigowa a rana Bilal ne dai bai ƙara zuwa ba sai a ranar da za a sallame ni ya shigo da safe yayin da aka sallame ni da yamma. A maimakon Ya Haidar ya kaini gidanmu sai ya wuce dani gidansu kasancewar shi da Aunty Farida ne sa'ili da aka yi discharge ɗina Kuma dama can bakinsu ɗaya shiyasa koda na nuna na fiso ya kaini gidanmu Aunty Farida taƙi goyon bayana cewar ta gara na zauna gidansu domin gudun gulmar 'yan unguwarmu. Koda muka iso har Mommy tasa musu aiki sun gyara min ɗaki da zan zauna ba abinda babu na dangin kayan more rayuwa a ɗakin ƙiri-ƙiri aka cilasta min zama gun da bani da ra'ayi zama. A tunanina Ya Haidar ya yi haka ne domin ya sauƙaƙawa kanshi cimma manufar shi akaina sai naga saɓani tunanina domin tun ranar da na zo gidansu ban sake sanya shi a Idanuwana ba. Sai dai ya kira wayar Mommy ya ce abani ya tambaye ni ya jikina daga haka zai kashe wayarshi. Sosai Mommy take kula dani gami da tattalina ko kaɗan bata bari na cikin kadaici koda yaushe tana tare dani idan ka ga ta gusa daga guna Daddy ne ya dawo. Ta ɓangare Bilal raba dare muke yi muna waya a sati na biyu da rabuwar mu yake bani labari wai ya siyar da gidan da ya gina a cewar shi tun ALLAH bai nufa na tare a cikinsa ba. Saboda haka bai ga amfaninsa sai wani ƙarami ya siya wanda ko kwata kyau da haɗuwar wancan bai yi ba domin wancan upstairs ne wannan kuma flat ne three bedrooms and two parlours lokaci da labari ya je kunne Nusaiba kamar za tai hauka sai dai bata da yadda za ta yi  tsabar baƙin ciki ko walima da tai niyar yi fasawa tayi a haka ta tare, a dare da ta tare sai around 11 o'clock Bilal Shattima ya shigo ko kallon arziki bai haɗa shi da ita ba ya ajiye mata kaji da ya siyo akan bedside ya wuce bathroom ya yi wanka koda ya fito daga wanka ya tarar da ita jingine da bango bathroom, kallo ɗaya yai mata ya ɗauke kai wani kafiri haushinta yake ji yana kammala shiryawa cikin kayan baccinsa ya ɗauki wayarsa ya dawo parlour.
   Yayin da ni kuma yini ranar cikin baƙin ciki nake domin Bilal ya sanarda ni ranar Nusaiba za ta tare har kuka sai da nayi da mommy ta ga idanuwana sun yi jajir da ta tambaye ni sai ƙarya na shara mata ta hanyar cewa kaina ne ke min ciwo hankalinta duk ya bi ya tashi ta ɗaga waya ta kira family doctor ɗin su ya zo gida ya duba ni.
Bilal Shattima yana fitowa parlour ya nemi three seater ya kwanta ya yi dialling number Jeeddah yini yau gaba ɗaya ya kasa gane kanta, lokaci da kiran Bilal ya shigo wayata ina kwance  a ɗakin da ya kasance nawa a gidan a duk lokaci da na tuna cewa yau Bilal zai kwana da Nusaiba a gida ɗaya a ɗaki ɗaya, akan gado ɗaya sai na ji zuciyata tamkar za ta tarwatse.

#Jeeddah Aliyu
#Team Bilal Shattima
#Team Haidar Ka'oje
#Team Engineer Ameer
#Zazzafan kishi
#Sabon Salo
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

053..

Baƙar harara na bankawa wayata ina kallo har kira ya tsinke ya sake kira shima ya tsinke ban ɗaga ba. Sai harara nake zubawa wayar sai kace ita ce tai min laifi sai da Bilal Shettima ya jera min 21 missed call kafin na ɗauki wayar a mugun fusace nai switch off ɗin ta. Knocking ɗin ƙofa aka yi sai da na kalli wall clock naga 10:10pm kafin nai wani yunkuri naji an turo ƙofa an shigo jajaye idanuwana na sauke akan kyakkyawar fuskarshi ma'abuciya kyau da kwarjini jikinshi sanye da pyjamas sky blue in colour ba ƙaramin kyau yai cikin kayan "Ya Haidar kenan ba dai kyau ba.
Na faɗa cikin zuciyata "Assalamu alaikum!
Ya furta cikin zazzaƙar muryarsa mai daɗi da gardi ga kunne ma'abuci sauraren ta.
   Cikin sanyi murya na amsa mishi da "Wa'alaikum Salaam! Ya Haidar ashe kana ganowa?
Kyakkyawan murmushi ya saki min wanda yai bala'i ƙara masa kyau tsanani kyau da yai min har ban san lokaci da na mayar mishi da martani murmushinsa ba.
   "Jiddoh kenan ai ko zan yi wuyar gani ga kowa ban dake kawai dai na ba ki space ne banaso taƙura miki amma ba don haka ba kema kinsan ni mugun mayyenki ne. Ban ƙi na zauna a gabanki na share wuni guda daga safe har faɗuwar rana ina kallon wannan kyakkyawar fuskar taki mai daɗa ƙara jefa ni a kogin sonki.
  Ya ƙarashe magana tare da kai hannunshi kan kumatuna ya shafa da sauri na buge mishi hannu na yunƙura na tashi zaune kusa da ƙafafuwana ya zauna.
  "Ya ciwon kan naki ya daina ko za mu tafi asibiti ne?"
Ya tambaya with so much care na kauda fuskata domin a dalili tunawa da nayi da Bilal Shettima yana can yana more darenshi tare da amaryarsa ni kuma yabar ni cikin ƙunci da suyar zuciya, kafin na dawo daga zance zuci da nake yi Ya Haidar ya dafa kafanɗuna ya dawo da fuskata izuwa kallonshi "menene hakikanin abinda yake damunki jikina ya bani ba Headache kadai bane akwai wani abu na dabam faɗa min menene shi?"
Ƙoƙari janye fuska ta nake yi amma ya hanani cikin rawar murya nace "Ba komai Ya Haidar zan kwanta bacci nake ji.
  "Ban yarda dake ba jiddoh domin a duk lokaci da ki ke cikin damuwa koda ba ki kusa dani zuciyata tana bayyana min, saboda haka ki faɗa min damuwarki a matsayina na yayanki wanda ya damu da damuwarki.
   Maganganu shi suka ƙara karye min zuciya dama mai neman kuka an jefe shi da kashin awakai sai kawai na fashe mishi da matsanancin kuka cikin shasshekar kuka nake faɗin "Ya Haidar yau amaryar Bilal Shettima ta tare gaba ɗaya wani irin zafi zuciyata take min na rasa me yake min daɗi, ji nake kamar na haɗiye zuciya.
Na ƙarashe magana ina mai sake rushewa da kuka.
  Shiru ya yi yana kallonta ya fahimci from the bottom of her heart take kukan nan kafin ya matsa kusa da ita ya riƙo hannunta na dama ya haɗe da nashi cikin kwantar da harshe ya shiga faɗin "Ni banga abin kuka da ɗaga hankali ba Jeeddah! Ki ɗaure ki ɗauki rabuwarku a matsayin rubutacciyar ƙaddara, ki yi ƙoƙari ki fitar dashi daga zuciyarki domin tun da ki ka ga ya tare da amaryarsa to alama ce da ke nuni da cewa shi ɗin ya fara taka matakin farko na goge babinki daga rayuwarsa.
  Kalaman Ya Haidar suka ƙara dagule min lissafi sai kawai na sake rushewa da wani sabon kuka, da kyar ya rarrashe ni nayi shiru da ya tambaye ni naci abinci na girgiza kai ya tashi da sauri ya fita sai gashi ya dawo yana gaba mai aiki Mommy Turai tana biye dashi ɗauke da ƙaton tray da warmers a sama ya nuna mata bedside drawer ta ajiye kana ta fice da kanshi yai min sarving ya tsare ni sai da naci abinci nan sosai raguwar wanda na rage ya ci sannan ya fita da kwanuka koda ya dawo na shiga bathroom nayi fitsari haɗe da brush. Na fito tare da komawa wajen zamana na zauna ya shiga yi min hira mai daɗi cikin ƙanƙani lokaci na nemi damuwa ta na rasa ni ce har da su dariya sai da ya ga ina hamma akai-akai sannan yai min sai da safe ya fice. Nayi addu'a gami da kwantawa sai dai na ƙasa bacci na lula tunani rayuwata ta nan gaba. Ni kaina nasan Ya Haidar yana matuƙar ƙaunata, ƙauna irin wacce babu algusu a cikinta zan iya cewa Ya Haidar yafi Bilal Shettima ƙaunata sai dai duk da irin tsanani ƙaunar da yake min har yanzu zuciyata ta kasa bashi matsayi masoyi. Na ɗauki dogon lokaci ina tufka da warwara kafin na samu bacci ya ɗauke ni.
Washegari da wuri na tashi domin na taimakawa mommy ta ayyukan gida duk tana da masu aiki har guda biyu yarinya da dattiju wa, na sanya doguwar rigar material marar nauyi kaina ɗauke da hula ina fitowa kaitsaye bedroom ɗin Mommy na shiga saboda ina da tabbacin bata isa fitowa main parlour ba. Gaidata nayi ta amsa min cike da sakin fuska kana ta tambaye kaina na ce na ji sauƙi kafin na ce "Mommy yau me za ki karya dashi domin ni zan haɗa miki breakfast na hutar da Baaba karime?"
   Yalwatatce murmushi ta saki har haƙorin makkahn ta ya fito ta ce "Lallai yau jiddoh na ta kammala takaba tun da har tai sha'awar shiga kitchen.
Dariya nayi ina sunne kai cikin tafukan hannuwana ina mai faɗin "kai! Mommy wane irin takaba kuma?
      "Takabar rabuwa da wancan butulu yaro da ya tsotsi butulci a nono uwarsa.
Kafin nayi magana ta ɗora da cewa "ki kwatar da hankali ki ko kya dawo da jikinki in-sha-Allahu sai kin aure miji wanda yafi shi komai na rayuwa kin ji Koh?
  "Tohm! Mommy na faɗa idanuwana suna cicciko wa da hawaye domin Mommy ta tuna min da shikenan yanzu na bi ayari zaurawa, masu neman mijin aure ban kuma san gidan wa zan faɗa ba. Tuni Mommy ta halbo jirgina saboda haka ta shiga kwatar min da hankali ta hanyar daɗaɗɗa maganganu masu saka natsuwa kafin ta ce ta faɗa wa Baaba karime ta soya mata doya da sauce ɗin cabbage sai ta dama kunu gyaɗa. Yanzu haka tana kitchen na je na ƙarbe ta amma ta tayani da wasu 'yan aikace-aikace. Na amsa mata da to! tare da baro bedroom ɗin kaitsaye kitchen na shiga na tadda Baaba karime tana fera doya na gaidata ta amsa min da fara'a kafin na karɓi wuƙar hannunta da kyar ta yarda ta bani shima sai da na faɗa mata da sani Mommy zan yi aiki. Na dukufa fera doya muna ɗan taɓa hira da Baaba bayan ta kammala jajjaga min kayan miya da zan yi sauce na je ta tafi kawai zan ƙara sa raguwar aikin da kaina nan ma da kyar ta yarda ta tafi cikin natsuwa na ci-gaba da soya doya cikin ƙanƙani lokaci har sauce ɗin na kammala na zuba ciki casserole dish masu kyau da tsada. Ina cikin zuba ruwan zafi a kettle a tap domin su ƙara tafa na dama kunu na ji muryar Ya Haidar yana faɗin "Kai! kai! Me nake shiri gani haka? Me  jiddoh take yi a kitchen?"
Ban amsa mishi ba sai da na jona kettle kana na juyo da murmushi akan fuskata sai da na fara ƙare wa kayan jikinsa kallo sanye yake ciki black suit rigar ciki sky blue in colour ya ɗora necktie shima sky blue ya yi mishi half windsor knot style, ba ƙaramin karɓar jikinsa suit ɗin suka yi kamar ɗan shi kaɗai aka yi su ya yi kyau marar misaltuwa. Da sauri na ɗauke idanuwana daga kanshi ina faɗin "ka ji min Ya Haidar da wata tambaya to duk abunda ake yi a kitchen shine nake yi kuma kwalele ka sai da ka haɗiye yawunka domin babu rabonka a ciki.
    "Really?"
Ya faɗa yana ɗage girar ido. Ban amsa mishi ba sai kawai na zabga mishi harara ya tako cikin tafiyarsa ta ƙasaita ga wani kwarjini na musamman da ya yi min ya iso kusa dani ya jingina jikinshi ga kitchen cabinet ya yi ƙasa-ƙasa da murya ya ce "kinsan wani abu kuwa jiddoh?"
Na girgiza kai saboda yadda ya haɗe tazarar da ke tsakaninmu yasa nake shaƙar haɗaɗɗen ƙamshi turarensa mai haifar da natsuwa "wallahi gani da bai miki da sassafe a kitchen ya haifar min da wani irin shauki, a sanda na shigo kitchen ɗinan nai tsaye a jikin ƙofa har imagination nayi mu yi aure kin tashi da sassafe kina haɗa min breakfast ALLAH ban ɗan da na kai zuciyata nesa ba da ji kawai za ki yi nayi hugging ɗinki tightly dan ba zan miki da wasa ba, yanzu kuma da ki ke kallona da farare idanuwanki sai naji kamar na sumbace ki wallahi jiddoh ina masifar kwaɗaituwa da son na tsotsi tattausan lips ɗinki sai dai wannan burin nawa zai cika ne kaɗai idan muka zama ɗaya dan ALLAH Jeeddah Usman maishadda ki bani dama na mallake ki a matsayin mata ta ta sunnah....

#Jeeddah Aliyu
#Haidar Ka'oje
#Bilal shettima
#jeeddah Usman maishadda
#Team zazzafan kishi.

   
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

055

Wata ƙarfaffiyar ajiyar zuciya na sauke na kasa samun natsu lokaci zuwa lokaci sai na waiga na kalle corridor shiga part ɗin Ya Haidar, tsinta kaina nayi da miƙewa tsaye cikin sanɗa kamar wata ɓarauniya na nufi corridor ɗin. Ina zuwa sai kuma na kasa ci-gaba da tafiya na dawo baya da sauri na laɓe ina laiƙasu, ko za su fito yanzu shiru-shiru ba su fito ba kuma na kasa komawa cikin parlour na ƙarasa cire farce na.
Haidar Ka'oje ya kalle Zarah da murmushi akan fuskarshi ya nuna mata resting chair da yatsan shi yana faɗin "Have a seat dear!
Ta zauna tare da faɗin "ina abunda ka ce za ka nuna min?"
   "Oh! My Zarah ke dai kin cika gaggawa bara nasa aka miki abinci yawan abinci da ki ka ci yawan abunda zan nuna miki.
Dariya tayi gami da fari da idanuwanta tana faɗin "wannan ai wayau ne Aliyu.
  "En! Mana!
Ya faɗa yana 'yar dariya sai da ya cire rigar suit ɗin sa tare da necktie ya ɓalle two bottoms na gaban shirt ɗin sa kana ya nanaɗe hannuwan rigar, kana ya nufi ƙofar fita duk abunda yake yi idanuwan Zarah Malik suna kanshi yana jin yadda idanuwanta ke yawo a jikinshi amma ya yi kamar bai ganta ba.
Sake laiƙasu su nayi sam bai lura da zuwan Ya Haidar ba sai karo naji nayi dashi kaina da na zuro ya buge jikinshi "ouchhhhh! Ya faɗa yana dafe gefen jikinshi "OMG!
Ya sake faɗa yana kallona sai wani fiƙi-fiƙi da idanuwa nake yi kamar an tsoma kaza cikin ruwan zafi da kalle ni za ka gano bani da gaskiya, a yatsine na kalleshi tare da turo baki gami da juyawa na nufi cikin parlour ina gunguni ƙasa-ƙasa "A dai ji tsoron ALLAH a dinga tunawa da mutuwa.
  Da sauri ya biyo ni a baya yana faɗin "Me kika ce?
"Abunda kunne ka ya ji.
"Idan ba tsoro ki sake maimaita wa.
Cakk! Na tsaya gami da juyawa na kalle shi a fusace na ce "Kai zan ji tsoro ko kuma wancan figaggiya da ka kawo?"
"Wacece figaggiya?
    "Ka fi ni saninta tun da ko yaushe kana manne da ita ko kunya bakyaji.
"Kin ga baiwar ALLAH gara ki fito fili ki amaryar da abunda yake cikinki ki daina wani luge-luge.
Ya ƙarashe magana yana ƙunshe dariya ya nufi kitchen yana kwallawa Labiba kira mai aikin Mommy.
   "Labiba! Zo ki haɗawa Zarah abinci.
Jin abunda ya faɗa yasa na rugu da gudu na tare ƙofar shiga kitchen da dukkan hannuwana ina faɗin "Camdijam! Wallahi ba za ta ci abinci nan ba domin ni na girka kuma ban girka da ita ba.
Da girar ido ɗage Ya Haidar yake ƙare min kallo sai wani galla masa harara nake yi gami da murguɗa masa baki.
   "Ikon ALLAH! Ni da gidanmu a nuna min fin ƙarfi?"
"En! Na ji ɗin gidanku ne amma Wallahi ba ka isa ka ba wata abinci da nasha wahala na girka, ka je ka siya mata na kasuwa mana.
"Kyakkyawar shawara nagode da wannan shawarar taki, yanzu-yanzu nan za ki ga an kawo mata abinci mai kyau da tsada mai irin naki jagwalwale ba.
"Wannan kuma matsalar kace ni ba ma za ka burge ni ba har sai ka tattaro dukka Restaurant dake cikin garin Sokoto ka kawo mata.
"Ke ma kinsan hakan ba zai yu ba da ba abinda zai hana ni kawo mata ai Zarah ta musamman ce komai zan iya yi mata.
   "Mtsssss! Ni ban ga alama ba domin duk mace da ta amsa suna ta musamman ba za ta ɗebo ƙafa tun daga Kebbi ta zo Sokoto wajen saurayi ba.
Taɓe baki ya yi tare da yi ƙasa da murya ya ce "Wai duk wannan kishi na menene bayan an ce ba a sona amma kuma ana tsanani kishina wannan wane irin salon SOYAYYA ne?"
Yadda ya tsare ni da idanuwanshi yana wani shegen murmushi yasa na ruɗe na rasa abun faɗa sai kawai na watsa masa harara, na shige kitchen.
Ya kira wani Restaurant mai kyau ya yi wa Zarah order abinci, tsabar ɗaukar magana sai da ya laiƙo ni kitchen ya ce "jiddoh za ki ci shawarma a haɗo dake ki ci alfarmar Zarah?"
A fusace na kalle shi cikin ɓaci rai na furta "ALLAH ya kiyaye naci alfarma koɗaɗɗiyar budurwarka.
Dariya ya yi tare da bari wuri yana cewa "idan delivery ya kawo abinci ki karɓa ki kawo min kin ji 'yar ƙanwata mai hankali.
Cikin ɗaga murya na ce "Ashe kuwa za ta mutu da yunwa.
Bai tanka min ba ya wuce ɓangare sa, tsabar takaici kasa zaman parlour nayi na koma ɗaki, wayata na ɗauko ko za ta rage min raɗaɗi da nake ji bai fi five minutes da nayi switch on ɗin ta sai ga kiran Bilal Shattima, sai da kira yana daff! Da tsinkewa nai picking a fusace na ce "Malam lafiya?
  Sai da ja dogon numfashi kafin cikin ƙaramin sauti ya kira sunana "Jeeddah!
Banza nai mishi dan ba ƙaramin haushinsa nake ji ba "Dan ALLAH Jeeddah ki yi min magana mana wallahi ba zan iya jure fushinki ba.
   Sai da na gama shan ƙamshi kafin cikin ɗaurarriyar murya na ce "Ka ga Bilal Shattima banaso yaudara ka faɗi dalili kira da ka yi min ba wai ka ka tsaya gayamin kalamanka da babu komai a cikin su sai zallar yaudara ni yanzu na dawo daga rakiyar kalaman bakinka.
   "Innalillahi! Dan ALLAH kada ki ce haka Jeeddah Wallahi-azim a hali yanzu babu wata 'yar mace da nake gani da ta wuce ki. Jeeddah ina jin sonki da ƙaunar ki suna huda sassa jikina, akanki da uban kowa zan iya ɓatawa daga ciki kuwa har da Hajja. A dalilinki na kori Nusaiba nace ta tafi gidansu idan ma cewa ki ka yi na sake ta da gudu zan aikata.
Shiru Jeeddah tayi tare da nazari maganganun sa bi da bi "idan har abunda Bilal Shattima yake faɗa gaskiya ne tabbas zan yi amfani da wannan damar na ɗauki fasar wulaƙanci da cin kashi da mahaifiyasa da 'yar uwarsa suka yi min zan dinga juya steering rayuwar Bilal iya son raina sai na nuna wa su Hajja sun kashe maciji ne ba su sare kai ba.
    "Hello Love!! Dan ALLAH ba dan ni ba ki yi min magana ko zan ji sanyi shiru ki zai iya shafar lafiyar jikina.
   "Hmm! To me kake so nace Bilal? Bayan duk irin ƙaunar da na nuna maka daga ƙarshe sai da ka wulaƙanta ni ka yi min sakin wulaƙanci, bayan ka kwana da sani rabuwa da kai zai iya jefa ni a mummuna yanayi.
   "Ki yi haƙuri Love na sake ki ne a bisa tursasawar mahaifiyata ba dan bana sonki ba. rabuwar rubutacciyar ƙaddara ce shiyasa nake so ki bani dama na gyara duk abunda na ɓata hope za ki bani second chance?"
   "Love ko na ba ka second chance ba abinda za ka yi domin bakin alkalami ya riga da ya bushe ka tuna saki uku ka yi min.
   "Na sani Love shiyasa nake so ki yi min alfarma albarkacin soyayyar da muke wa junan mu, ki karbi shawara da na zo mana da ita wacce za ta sake ba mu damar Mallakar juna ta hanyar aure.
  Cikin kaɗuwa na zaro idanuwa kafin cikin rawar murya na ce "ka kuwa san abunda ka ke faɗa love wacce hanya ce za ta sa mu sake zama a karkashin Inuwa aure alhali ka sake ni saki har uku?
    "Love auren kisan wuta za ki yi aure da ba zai wuce one to two months ba, muddin soyayya da muke wa junan mu gaskiya ce ta wannan hanya kaɗai za mu bi mu sake zama ma'aurata dan ALLAH kada ki ce min a'ah!
       "Amma Bilal ALLAH subhanahu wata'ala ya yi hani da wannan aure sai nake g......
   "Amma Jeeddah Idan ki yi duba da rabuwar mu ba a ran mu bane kuma za ki yi wannan aure ne a bisa ƙaunar da muke yiwa juna mu, idan ke za ki iya rayuwa da wani namiji ba ni ba to ki sani ni ba zan iya ba. A bisa wannan dalili yasa na yanke shawara muddin kika amince za ki yi auren kisan wuta ni kuma zan saki Nusaiba, kuma zan yi rantsuwa da al-qur'ani ba zan taɓa yi miki kishiya ba.
   "Bilal al-qur'ani ba abin wasa bane.
Na faɗa cikin rawar murya domin lamarinsa ya fara wuce hankali da tunanina.
"Na sani Jeeddah shiyasa ma nace zan rantse dashi.
Shiru nayi na kasa cewa komai hakan ya ba shi dama ci-gaba da kanainaye ni da daɗin bakinsa. Na sauke gwaron numfashi gami da cewa "Na ji buƙatar ka love amma ina so ka bani lokaci nayi nazari....
   "Haba Jeeddah wane Irin nazari za ki a kai na wanda tun can farkon zaman mu ba ki yi ba? kodai zuciyarki ta fara karkata akan Haidar Ka'oje ne wato shiyasa ya hana ki zama gidanku ya kawo ki gidansu domin ya mallake zuciyarki ta ruwan sanyi ko?"
Ya ƙarashe magana yana sauke zazzafan numfashi.
Ɗan bazawari murmushi nayi tare da faɗin "Koma haka ɗin ne miye laifin sa?
"Kin ga Jeeddah kada ki ɓata min rai akan wani banza wanda nake da yaƙini na fi shi matsayi a cikin zuciyarki.
  Karo na farko da na ji wani ya faɗin mummunan kalami akan Ya Haidar na ji zafi rai ɓace nace "A'ah! dakata Bilal banaso cin fuska bai kamata ka dinga jifar Ya Haidar da mummunan lafazi irin wannan ba.
   Cike da zallar mamaki Bilal Shattima ya ciro wayar daga kunnen shi ya duba sensor wayar ya ƙara confirming da Jeeddah ne yake waya ba wata sannan muryar ta ce ke fita daga cikin wayar, tabbas ita ce babu tantama cikin rauni zuciya ya maida wayar kunne shi ya kira sunanta cikin ƙaramin sauti kamar zai fashe da kuka "Jeeddah!!
   "Bilal!
Na faɗa kai tsaye domin har lokaci ina jin zafin zagi da ya yiwa Ya Haidar ni ganina duk wanda ya zagi Ya Haidar dole na ji zafi ko ba komai shi ɗin ɗan uwana ne jini jikina ina ma damar da zan yi fushi dashi kamar yadda shi ma Bilal Shattima a can lokuta baya nake nuna fushi akan duk wanda ya faɗin maganar banza akansa.
     "Jeeddah ina sonki ina miki so da baya misaltuwa idan ki ka juya min baya wallahi-tallahi zan iya mutuwa domin ke ce ruhina, bugun zuciyata Dan ALLAH Jeeddah kada ki bari Haidar Ka'oje ya yi nasarar dakile mana soyayya. A hali yanzu Jeeddah na fi shi sonki na fi shi tsanani buƙatar ki domin shi bai zauna dake a karkashin inuwar aure ba ballantana yasan irin daraja ni'imar da ki ke da ita ni kuma na ɗandana na lasa idan har aka ce za a rabani dake tamkar za a rabani da numfashina ne.
  Ya ƙarashe magana cikin sanyi murya, numfashi na sauke domin maganganu shi ba ƙaramin tasiri suka yi min ba.
  "Ka ga Bilal abunda ka ke zargi babu shi a tsakanina da Ya Haidar saboda haka ka kwantar da hankalinka, sai dai buƙatar da ka zo min da ita haƙuri za ka yi ka bani lokaci nayi tunani komai na duniya yana buƙatar tunani kafin yanke hukunci.
    "Shi kenan Love na ba ki daga yau zuwa gobe ina gani zai wadace ki ki yi duk wani tunani da za ki yi amma ina so ki tuna yayi da ki ke tunani ni Bilal Shattima ina mugun sonki zan kuma iya aikata koma menene domin na sake mallakar ki a karo na biyu.
Yana gama magana ya dantse kira, na bi wayar da kallo kafin na taɓe baki yayin da zuciyata take kallon maganar shi ta ƙarshe a matsayin barazana.
Ban san sanda Ya Haidar da Zarah Malik suka bar gidan ba domin tun da na shige ɗaki ban ƙara fitowa ba har sai da mommy ta dawo, muna zaune a falo hadda Ya Haidar mommy take ba mu labari Mama ta kira ta ta faɗa mata irin kalar haukar da Hajja da su Aunty Bahijja suka yi mata, sosai na ji raina ya ɓaci na kudurta a raina zan amince da buƙatar Bilal Shattima ko dan na wulaƙanta mahaifiyarsa da 'yar uwarsa. Yayin da Ya Haidar baya ga ALLAH ya kyauta ba abinda ya ce.
   ************
Engr Ameer B Sardauna ya je unguwar da Jeeddah take ya fi a kirga ya nemi nesa da gate ɗin gidan ya zauna har ya ƙarashe zaman shi, ko mai kama da ita bai gani. Duk ya bi ya rame ya susuce ya fita hayyacinshi, wani irin azababben ciwon so ke ɗawaniyya dashi abinka da mai cutar mental disorder sai yake gani ko ta ƙarfin tuwo ne sai ya mallake ta. Duk ƙoƙari mahaifiyasa na gani cutar tashi bata motsa ba abin ya ci tura ranar da ciwo ya tashi sosai ya ji wa kanshi ciwo sai kuka yake yi yana kiran sunan Jeeddah. Ba ƙaramin tashin hankali ya haifar wa ummarsa dashi ba dole sai amininsa Dr Abubakar ta kira wanda shi kaɗai ne yasan da wannan boyayyiyar lalura tashi ya yi mishi allura da aka saba yi mishi a duk lokaci da ciwon nashi ya tashi. Dr Abubakar kwararre likitan mahaukata ne.
Sai da ya gyara zaman farin gilashi dake lulluɓe da kwayar idonshi kafin ya tattare hankali da natsuwar sa akan umma ya ce "Umma ya aka yi Ameer ya tadda zance maijiddah a tunanina tuni ya goge shafinta a rayuwarsa domin duk wanda ya mutu baya dawowa?"
  Sai da Umma ta ja numfashi gami da sauke wa ta ce "Abubakar wannan wata Maijiddah ce ta dabam ba wancan bace da ka ke tunani.
"Wata kuma Umma? Yaushe hakan ta faru miyasa ki ka bari Ameer ya sake faɗawa SOYAYYA bayan kin kwana da sani irin salo da yake gudanar da tashi SOYAYYA ya sha bambam da na saura mutane?
   "Na iya ƙoƙarina domin na hana  faruwar hakan sai dai na gaza Abubakar domin Ameer ya yi nisa a son yarinya nan, babban tashin hankalina bai wuce kasantuwar matar wani ba. Da ace babu igiyoyin aure wani akanta koda raina bayaso dole na amince ya aureta domin kwanciyar hankalinsa, sai dai kashhh!  Maijiddah tana da aure ta ya ka ke tunani Ameer zai mallake ta?"
   "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Matar aure fa ki ka ce Umma?
"Kwarai kuwa matar aure ce Abubakar domin shi da kanshi ya tabbatar min da hakan.
Gaba ɗaya gaɓo bin jikin Dr Abubakar suka yi sanyi rasa abun cewa zuciyarsa ta shiga bugawa domin yasan akwai badakala.
*********
A kwana a tashi asarar mai rai har nayi wata ɗaya da kammala iddata kafin lokaci abubuwa da dama sun faru daga cikinsu akwai amincewa da nayi da buƙatar Bilal Shattima ta yi aure kisan wuta sai kuma dawowa da nayi gaba baki ɗaya gidan Iyayena. Zuwa lokaci mutane da dama sun sami labari mutuwar aure na. Yayin da ni kam ko a jikina sai ma shirye-shirye tafiya aikin hajji nake yi wanda tare za mu tafi da Aunty Farida da Mommy Turai Aunty Farida mijinta ya biya mata, Mommy Kuma ya Haidar ne yana samun labarin tafiya ta ya biyawa mommy a cewar sa ban taɓa zuwa ba bai dace na tafi ni kaɗai ba. Dole ina buƙatar su a kusa dani kasancewar Aunty Farida ita ma shi ne farko zuwan ta kuma jirgin yawo za su bi. Ni kuma nasan ya yi hakan ne domin ya dakile hanyar da zan haɗu da Bilal Shattima.
Cikin hukunci Ubangiji da iyawarsa muka kammala aikin Hajji sai dai fatar ALLAH ya karɓi ibadun mu. Bayan dawowar mu da sati biyu Bilal Shattima ya kira ni mu haɗu a wani keɓantatce wuri zai gabatar min da wanda yake so na aure sunyi yarjejeniya da zarar mun cika watanni biyu da aure zai sake ni. Cike zumuɗi na shirya kaina cikin black blue colour Abaya tayi matuƙar karɓar jikina, ni kaina sa'ili da na dubi mirror sai da na yabawa kyau da nayi key ɗin motata na ɗauka haɗe da handbag na fito sai da na fara leƙawa falon Mama na sharara mata karya da tun farko na shiryo da za ta bar ni na fita saboda ba kasafai take bari na ina fita daga wuri aiki sai gidan Mommy Turai "Mama na tafi gidan Mommy zan taya ta aiki kinsan yau ne Ya Haidar zai dawo.
Mama ta ri ga tasan da zance dawowar Ya Haidar daga Cyprus kusan watan sa ɗaya da tafiya ya je gudanar da wani contract shiyasa nan take tai min fatar a dawo lafiya. Kai tsaye wuri motata na nufa wacce tun safe na saka musa almajiri ya wanke min ita tass! Lokaci da na tafi Makkah koda na dawo Ya Haidar ya ɗauke motar da Bilal Shattima ya siya min ya kawo min wannan a cewar sa bayaso ganina tare da duk wani abu da ya shafi Bilal Shattima wancan motar ma kyautar da ita ya yi. A lokaci da naga yana nuna izza da ƙarfi ikonsa akaina dariya yake bani domin kuwa kallon mahaukaci nake masa saboda nasan irin kulli da nake kulla wa.
A hankali nake murza steering motata akan titi gani wani irin nishaɗi da nake ji, waya ta na haɗa da Aux ɗin mota na saki ɗaya daga cikin wakokin Hamisu breaker, Ina bin wakar tare da gyaɗa kai.
Kai tsaye sabon gidan da Bilal Shattima ya siya mana na nufa kasancewar ya taɓa kaini naga gidan, horn nayi maigadi ya zo ya buɗe min gate tun da na danno hanci motata na hango shi tsaye a compound yana jiran isowa ta. Sai da na isa daff dashi nayi packing kafin na fito har ya buɗe min ƙofar mota, murmushi muka sakarwa junanmu "Barka da zuwa rabin raina!
Bilal Shattima ya faɗa tare da maida kofar mota ya rufe.
   Sai da na kare wa kayan jikinsa kallo black jeans da red colour t-shirt ya yi stocking da belt ɗin Company D&G ƙaton tumbinsa ya fito, sai kawai na ji wani irin ɓaci rai ya ziyarce ni na tsani namiji mai tarin teɓa, ko ba ka tambaya ba, kasan kitse ne ya yi masa yawa a dalili kafiri ci nama da yake yi ya mayar da nama abincinsa. Gashi kuma bayaso motsa jiki.
   Cikin yatsine na ce "Gaskiya Love ka rage wannan ƙiba da ka narka kalli yadda cikinka ya yi girma nama fuskarka duk ya cicciko kumatunka sun cika sun yi suntun-suntun, ba zan ɓoye maka ba wannan ƙibar duk ta rikita min kai.
   Dariya ya kwashe da ita gami da faɗin "Naira na shigo ni ta ko'ina Love ba dole na aje tumbin ba. Duk mutumin da ki ka ga cikinsa a shafe bai da ko kwabo, ko kuma matsolo ne baya ci kuɗinsa.
Turo baki nayi tare da faɗin "Ni dai banaso ganinka haka gara tun wuri ka fara tunani yadda za ka rage weight.
   "Shi kenan na ji zan rage ɗin mu shiga daga ciki kafin Khamis ya iso.
Muka jera side by side tare da nufar entrance ɗin gidan. A main parlour muka zauna already ya zuba furnitures a gidan sai dai ɗan abinda ba a rasa ba. Shi ma yana jiran sai in za mu yi aure ya saka.
Ban wuce Ten minutes da zuwa ba sai gashi Khamis ya kira sa a waya ya iso ya ce dashi ya shigo ciki sai lokaci yake ƙara yi min bayani akan khamis "khamis yana da kirki sosai shiyasa na zaɓe shi a matsayin wanda zai aure ki yana ɗaya daga cikin yaran kamfanin mu da suke kawo mana motoci daga c'otonou bana tunani za a samu matsala saboda kammala da mutuncin sa ni kaina nasha baƙar wahala kafin ya amince da manufa ta.
   "Hmm! Ka ce ya taɓa yi aure ko?"
"En! Amma matarsa ta rasu a guri haihuwa shekaru biyu da suka gabata.
Kafin na sake yi magana na tsikaye sallamar khamis, na ɗago da sauri na yada idanuwana akan fuskarshi, fari ne tass! Yana da saje baƙi wulik kwance akan fuskarsa, gami da ɗan gajeren gemu shi ba dogo ba kuma ba za a saka shi a layi gajeru ba. Khamis yana da matuƙar kyau sai dai duk wannan kyau nashi ba za a taɓa haɗa shi da Ya Haidar ba domin Ya Haidar maƙura ne kyau.
Sai da ya fara miƙawa Bilal hannu suka yi musabaha kafin ya nemi kujera da ke facing ɗinmu ya zauna, bai tanka min ba nima ban ce dashi uffan ba. Tun sanda ya shigo na kalle shi sau ɗaya na kauda fuska jikina ne ya bani ana kallona hakan yasa na ɗago na saci kallonshi idanuwanshi kyam! Akaina gani bashi da niyar janye ganinshi yasa ni na janye nawa idanuwana zuciyata cike da gundarin mamaki irin wannan kallo da yake min.....

#Jeeddah Aliyu
#Haidar Ka'oje
#khamis
#Engr Ameer B Sardauna
#Jeeddah Usman maishadda
#Bilal Shattima
#Team zazzafan kishi {sabon salo}

 
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA  waaBA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

054..

Ya Haidar ya ci-gaba da kora min sirri zuciyarsa sosai jikina ya yi sanyi gaɓɓan jikina suka saki domin ba ƙaramin tasiri kalamansa suka yi akaina ba. Tun ba yau ba nasani Ya Haidar masoyina ne na gaske sai dai ina gani a yanzu da nake Matsayin bazawara ko kaɗan ba mu dace da juna ba. Abin kunya ne babba na karɓi tayin soyayyarsa alhali a can baya na guje sa cikin sanyi murya nace "Ya Haidar aure a tsakanin mu ba zai yu ba ko ka manta an yi maka Engagement da Zarah Malik 'yar aminin Daddy?"
  "Ban manta ba Jeeddah ban Kuma ce dake ba zan aureta ba. Yadda aurenki ba zai hanani aure Zarah ba hakazalika aure Zarah Malik ba zai hanani aurenki ba.
Ya faɗa fuskarshi a haɗe wani irin bugawa zuciyarta tayi wato nufinsa mu biyu zai haɗe ya aura gaskiya ba zan iya ba wani irin fushi na ji ya taso min ɗan kuwa numfashina har wani sarƙewa yake yi rai ɓace nace dashi "To gaskiya ba zan ɓoye maka ba ba zan iya aure ka ba kwata-kwata ni aure baya gabana gara tun wuri ka fitar dani daga ranka.
Na ƙarashe magana gami da nufar wuri kettle a mugun fusace na ciro kettle na dama kunu gyaɗa ɗin duk abunda nake yi cikin ɓaci rai nake aiwatar dashi yayin da Ya Haidar yake bina da idanuwanshi da suka fara canza launi. Maganganuna ba ƙaramin ƙona masa rai suka yi ba. Na ɗauke flask ɗin da na juye kunu a ciki na bi ta gefen shi na fice daga kitchen ɗin ina jin tako tafiyarshi a bayana juyowar da zan yi naga ya ɗauki briefcase ɗinshi da ke aje akan kujera a parlour a mugun fusace ya fice na bishi da kallo kafin na taɓe baki.
***********
"Wai Ya Bilal me kake nufi dani ne? Duk lokaci da na zo kusa da kai sai ka canza wuri zama haka jiya ka kaurace min alhali ka kwana da sani yadda muke doki zuwan daren jiya da kuma irin tanadi da muka yi masa amma duk suka tafi a banza jiya ko kaɗan ban runtse ba saboda azababbiyar sha'awarka da kyar naga wayewar safiya. Yanzu kam gaskiya ba zan iya jurewa ba dole ka bani hakkina.
Ta ƙarashe magana hawaye na bin kumatunta.
Bilal Shattima ya ɗago idanuwanshi ya kalle ta sau ɗaya ya kauda fuska ya ci-gaba da ɗora agogon shi, wata irin tsanar Nusaiba yake ji ciki da waje zuciyarshi yana gama saka agogon ya saka ɗaya daga cikin jeri takalma sa ya nufi ƙofar fita daga bedroom ɗin da sauri ta bishi a baya har suka iso falo tana mishi magiya haɗe da kuka.
  "Ya Bilal Dan ALLAH ka tsaya ka ji da buƙata ta idan kuma laifi nai maka a bisa rashin sani ka yi haƙuri ka yafe min Wallahi zuciya da gangar jikina ba za su iya jure rashin ka ba.
"Mtsssss!
Bilal ya ja guntun tsaki gaba ɗaya haushinta ya ƙara lulluɓe shi a kufule ya ce "Ai kuwa gara ki jure domin ko kaɗan bakya gabana idan kuma fyaɗe za ki yi min to Bismillah! Tun da ke harija ce nasan za ki iya.
Sosai maganganu sa suka yi mata zafi cikin muryar kuka ta ce "Duk wannan wulaƙanci da cin kashi da ka ke min nasani duk akan wancan banzar ne wacce har ka koma ga mahalicci ka ba za ta sake zama matarka ba....
Wawan mari ya dauke ta dashi sai wani irin huci yake yi gami da faɗin "Jeeddah ki ka kira da banza?
"Eh ita ɗin mecece ita idan ba banza ba.
Sake wanka mata maruka har guda biyu ya yi gami da cewa "uwarki ce banza 'yar Iska jarababbiyar wofi kuma wallahi-tallahi idan bakinki ya sake kiran Jeeddah da banza sai kin bar min gidana kin dai ji na gayamiki akan Jeeddah da uban kowa zan iya ɓatawa.
Ya ƙarashe magana tare da ƙyasta mata yatsu sa biyu akan fuskarta, ya fice rai ɓacewa. Da baya-baya Nusaiba ta dinga tafiya har ta kai ga cushion tai zaman 'yan bori, ta fashe da kuka mai matuƙar cin rai ta ɗauki lokaci tana kuka babu mai rarrashinta sai da tagaji dan kanta tai shiru kamar wacce aka mintsina ta tashi da sauri ta nufi tv stand ta ɗauki wayarta sai idanuwana suka sauka akan passport ɗin zuwa Makkah guda biyu gami da wasu farare takardu da an haɗe su guri ɗaya, haka kawai ta tsince kanta daso gani passport ɗin waye na farko tana buɗewa ta ci karo da fuskar Bilal mamaki ne ya lulluɓe ta dama Bilal ya biya Makkah shi ne dan kuturun wulaƙanci bai gayamata ba. Ta ja tsaki mtssss! Tare da buɗe guda ɗayan saura kiriss! Numfashinta ya fita da gangar jikinta sakamakon abinda idanuwanta suka gane mata "Kutumar ubanan! Tashin hankali wanda ba a sa masa rana lallai za a yi babbar b****uba.
Ta ƙarashe magana tare da lallaiyo uwar ashar, yayin da jikinta ta ko'ina rawa yake yi. Da kyar ta iya lallabo number aunty Bahijja ringing ɗaya zuwa na biyu Aunty Bahijja ta ɗauka "Wayyo ALLAH mun shiga uku mun lallace Aunty Bahijja Jeeddah ta cuce mu Jeeddah ta gama da Bilal!
Abinda Nusaiba ta faɗa cikin gunji kuka.
  "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Me kuma shegiya yarinya nan ta sake aikatawa me ta yiwa Bilal, ki daina kuka nan ki natsu ki faɗa min abunda tayi?"
Kusan a lokaci ɗaya Aunty Bahijja tayi waɗannan maganganu ba ko numfasawa.
   "Aunty Bilal ne ya biya wa Jeeddah Makkah!
"Me ki ka ce Nusaiba Makkah fa?"
"Kwarai kuwa Aunty Bahijja Makkah.
Nusaiba ta ƙara tabbatar mata.
"Anya kuwa Nusaiba wanda ya kawo miki wannan zance ba ƙarya ya sharara miki ba?"
"Wacce irin ƙarya Aunty? Ga shaida nan a hannuna.
"Camdijam! Lallai kuwa idan abinda ki ke faɗa gaskiya ne Nusaiba a wannan karo Jeeddah Usman maishadda ta ɗebo ruwan dafa kanta bata isa ta je Makkah da kuɗi ɗan uwana ba. Zan bi kowacce irin hanya ne dan gani na hana hakan faruwa. Ki zo yanzu-yanzu nan mu haɗu gidan Hajja kuma ki zo tare da shaidu da ki ka ce domin dasu za mu kafa hujja.
"Gara dai ku yi wani abu akai domin kuwa ga dukkan alama shahararren boka ta samu wanda aikinsa yake ci ba iri-iri naku makaryata ba.
Nusaiba ta faɗa gami da kashe wayarta a gaggauce ta shirya ta zuba passport ɗin da takardun ciki handbag ɗinta ta rufe gida, cikin sauri ta nufi titi domin ta sami abu hawa, adaidaita ta hau gani take yi tamkar baya tafiya sai cewa take yi ya ƙara gudu, suna iso ta bashi five hundred ko canjin ta bata tsaya karba ba ta nufi guri Aunty Bahijja da tun ɗazu ta iso ta kasa shiga cikin gida tai tsaye tana jiran isowar Nusaiba, duk kira da mai adaidaita yake yiwa Nusaiba ta tsaya ta karɓi canjin ta ko waigo wa bata yi ba suka nufi cikin gida. Kamar wanɗada aka jefo haka suka shiga falon Hajja tana zaune sai ganinsu tayi wujuga-wujuga, cikin tsantsan tashin hankali Aunty Bahijja ta shiga ba wa Hajja labari, tana dasa aya Hajja tai wani irin zabura ta miƙe tsaye har zanin jikinta yana faɗowa, Aunty Bahijja tai sauri taro mata shi tana faɗin "Hajja zaninki!
Sai lokaci Hajja ta gano zaninta yabar jikinta inda ALLAH ya taimake ta tana da underwear skirt.
  "Wallahi-azim ba za ta sabu ba wai bindiga a ruwa ban da aikin asiri ta ya matar da ka saka saki har uku za ka biyawa kujerar Makkah, wallahi asiri Jeeddah da iyayenta suka yiwa Bilal.
Hajja ta faɗa jikinta yana rawa "mataki ya kamata ki ɗauka Hajja muddin ke ki ka haifi Bilal ki nuna masa ƙarfin ikonki kada ki bari Jeeddah ta je Makkah nan.
Aunty Bahijja ta faɗa tana zaro tula-tula idanuwanta.
Nusaiba ta karɓe zance da faɗin
"Wannan shine magana Hajja ki tursasa shi ya barmin domin ni ce matarsa ni na fi cancanta na je ba wata 'yar iska ba.
Nusaiba sam bata lura da mugun kallo da Aunty Bahijja tai mata sa'ili da ke magana domin ita ma Aunty Bahijja abinda yake ranta kenan sai gashi Nusaiba ta ri ga ta furta wa saboda haka cikin fushi ta furta "Haba Nusaiba dukka yaushe ki ka aure Bilal da har zai kai ki Makkah? Ya dai kamata ki dinga adana kwaɗayinki ki daina bayyana shi a fili hakan zai iya zubar miki daraja da ƙima musamman ga mu ahalinsa sai wani ya zaci saboda kuɗinsa ki ka aure shi.
Sosai mamakin maganganu Aunty Bahijja suka lulluɓe Nusaiba har ta kasa magana sai bin ta da kallon mai cike da mamaki take yi, Hajja ta taɓe gami da kallon Nusaiba ta ce "wannan haka yake Bahijja zance ki dutse ne ke Nusaiba ki daina saka dogon buri a rayuwarki gudun kada ya shafi lafiyar aurenki gani ga wane ya ishe wane tsoron ALLAH.
Hajja ta ƙarashe magana gami da nufar bedroom ɗin ta ta dauko hijab ɗin ta, yayin da Nusaiba ta bi bayan ta da kallo kafin ta sauke doguwar ajiyar zuciya a cikin zuciyarta take cewa "Hmm! Ɗan adam butulu lallai mutane nan ba kusan wacece ni ba shiyasa ku ke son ku yi wasa da hankalina amma mu tafi a haka nan da ɗan wani lokaci kaɗan zan bayyanar muku da ainihin kalata.
Ta ƙarashe zance zucin nata tare da yin ƙwafa.
Kaitsaye gidansu Jeeddah suka yiwa tsike Mama tana kitchen ta ji muryoyi daban-daban suna kwaɗa sallama ba kakkautawa, cikin sauri Mama ta fito sai kawai taci karo da mutane da ɓata taɓa expecting ganinsu gidanta da sassafe.
   "Malamai lafiya irin wannan sammako da kwaɗa sallama duk na menene?"
Mama ta tambaya sa'ili da ta ƙaraso kusa dasu.
Cike da masifa da bala'i Hajja ta hayyaƙo wa Mama tana faɗin
     "Ina fa lafiya Fatee ke da 'yarki saboda tsabar rashin imani kun asirce min ɗa to wallahi-azim ba ku isa ba matuƙar ina numfashi a doron duniya duk tsafin ku Jeeddah bata isa ta je Makkah da kuɗin ɗana ba.
"Mtsssss! Mama ta ja dogon tsaki wanda ke bayyanar da takaicinta a fili kafin ta ce "Ke kam Hajja kin yi asara  a haka za ki ƙare kullum shekaru ki daɗa tafiya suke yi kina maida kanki baya, yanzu ke ko kunya bakyaji ki ɗebo jiki da tarkace marasa tarbiyya 'ya da surukarki ku zo mana gida da sanyi safiya kuna mana haushi sai kace karnuka. Idan har kin isa da Bilal shi ya dace ki tara da wannan zance ba mu ba, kuma da kike zance tsafi me zai hana kema ki je gun matsafi da yai mana tsafi akan ɗanki kema ya yi miki.
    "Fatee ni ki ke gayawa Magana?
"An gayamiki Hajja ki ɗauki mataki tsohuwar banza da wofi.
Bahijja tai karaf ta karɓe zance cikin fitsara da rashin kunya take cewa
"Kema tsohuwar banzar ce rashin tarbiyya kuma akanku ya ƙare an saki 'yarki saki uku amma tana bibbiyar ƙanina to wallahi idan kuna ci ƙasa ku kiyaye ta shur.....
Kafin Aunty Bahijja ta ƙarasa Mama ta tsinke da kafiri mari.
Dai-dai Baba ya fito daga ɓangare sa da farko da yake ji hayaniya bai zaci cikin gidansa ne ba ya zaci maƙota ne da ya kasa kunnensa sai ya fara jiyo muryar Mama sama-sama shi ne ya fito dan ya tabbatar da abinda kunnensa ke ji gaskiya ne.
   "Kai! Subhanalillah! Meke faruwa su waye waɗannan matan me suke yi min a gida?
Baba ya faɗa tare da tunƙaro wajen Mama ta ce "Zo ka ganewa idonka Alhaji mahaifiyar Bilal ce tare da 'yarta da surukarta suke mana halin dabbobi.
Bahijja dake dafe da kunce ta ta ce "Wallahi ba ki mare banza ba akan wannan mari da ki ka yi min sai ya yi sanadi rusa tubalin rayuwar 'yarki.
Kafin Mama ta bata amsa Baba ya ƙaraso cikin ɓacin rai ya ce "Yarinya kin kuwa san abunda ki ke faɗa? To bari ki ji daga nan har izuwa numfashinki na ƙarshe idan wani abu ya sami 'yarta ke ce kuma ina tabbatar miki Shari'a ce za ta raba ni dake. Ban da jahilci da rashin sani hakkin ɗan adam ku zo har cikin gidana kuna yiwa rayuwar 'yarta barazana. Naga abunda ya haɗa su{aure} kin raba to neman fitina na me?"
   "Ai dole ka faɗi haka Alhaji Usman maishadda saboda ba banza ku ka bar shi ba. Ya saki 'yar saki uku sannan kuma ya biya mata Makkah wannan magana hankali ba zai ɗauke ta ba. Matuƙar kuna so 'yar da lafiya ku hana ta zuwa Makkah da kuɗi ɗana.
Mamaki ne ya rufe Baba duk akan Makkah ne take wannan masifa da bala'in take neman ta tara masa maƙota a fusace Baba ya ce "Idan akan wannan ne gara tun wuri ki ba kanki lafiya domin ba abinda zai hana wa Jeeddah tafiya Makkah da kuɗin da kike kirari na ɗanki. Idan kin manta ni ban manta ba tsawon shekaru Jeeddah tana yi muku hidima ke da ɗan naki kisani Bilal ya biyawa Jeeddah Makkah tun tana da igiyar aurensa akanta da yake shi ɗan halak ne ba irin uwarsa ba yasan ta cancanci fiye da hakan a wurinsa shiyasa bai janye tafiyarta ta ba. Saboda gudun magana iri-iri ku jahilai yasa nace ban aminta ba amma a dalili wannan ɗibar albarka da ki ka yi min a gida na amince ɗari-bisa-ɗari Jeeddah za ta tafi Makkah da kuɗin ɗanki ina jiran sammaci daga kotu.
Baba ya juya wuri Mama yace "Fatee koma ki ci-gaba da aikinki duk wanda bai ƙaunar ALLAH daga cikinsu ya ƙare second biyar a gidanan ya ga irin mataki da zan ɗauka.
Daga haka Baba ya koma ɓangaren sa Mama ta dube su ta ja tsaki tare da tofar da yawu ta juya ta shige kitchen ta barsu tsaye suna muzurai, Nusaiba dake tsaye tun zuwansu bata furta uffan ba. Ta saki ƙayatatcen murmushi ranta ya yi farin tass! Dama haka take so kowa ya rasa suka ja ƙafafuwansu jiki a mace suke fice suna zuwa gida Hajja bata haƙura ba sai da ta kira Bilal Shattima, dama yana fita ya tuna da ya manta bai fito da passport ɗin Jeeddah da yake so ya kai mata, dole ya juyo gida ya sha matuƙar mamaki da ya dawo ya tarar da gida a rufe ya yi using keys ɗinshi ya buɗe gidan. Ba ƙaramin daɗi ya ji da ya tarar da Nusaiba bata a tunaninsa yaji tayi, duk inda yake tunani ya ajiye passport ɗin ya nema amma bai ganshi ba, yana ciki neman sa sai ga kira Hajja ya shigo wayarsa kamar ba zai ɗauka ba sai kuma ya tuna da matsayinta na mahaifiya a garesa, ranshi a dagule ya yi picking up sosai ya ranshi ya ƙara ɓaci a dalili furunci da yaji yana fitowa daga bakin Hajja. Kashe wayarsa ya yi ya juya a fusace koda ya iso cikin falon Hajja ya cika ya dam! Da zuwansa ya miƙawa Nusaiba hannu cikin dakakkiyar muryarsa mai cike da fusata ya ce "Bani passport ɗina da ki ka dauko kuma daga nan ki wuce gidan ubanki, su koya miki tarbiyya bari shiga abunda bai shafe ki ba.
  Yadda Nusaiba taga fuskarsa babu alamar rahama ya haifar wa jikinta  rawa mugun tsoron sa ya lulluɓe ta da sauri tai zipping handbag ɗinta ta ciro su ta miƙa masa ya fincike shi da ƙarfi har yana haɗawa da ɗan yatsanta.
Kana ya juya kan Hajja wacce ke kallonshi da baki buɗe domin ba ƙaramin firgita tayi da jin furuncin shi akan Nusaiba "Hajja Dan ALLAH ki fita sabgar Jeeddah babu ruwanki da ita kuɗi dai nawa ne gumin jikina ba na wani ba saboda haka ita naga damar biyawa Makkah, ku sani ni ba kaza bane ci ki goge bakinki ban manta da irin halacci da Jeeddah tai min ba. Ya sake komawa kan Aunty Bahijja ya ce "ke kuma tsohuwar munafuka, mutaƙƙabira wacce babu ALLAH a ranta duk ranar da ƙafarki ta sake takawa gidansu Jeeddah da nufi cin zarafin ta na rantse da ALLAH sai na ƙarya miki ita.
Yana ƙarashe magana ya juya a mugun fusace ya fita gami da bugu ƙofa da ƙarfi, cikin zallar tashin hankali Hajja ta bishi da kallo ta kasa furta koda kalmar sunansa ne kamar haɗin baki suka sauke wata kafirar ajiyar zuciya a tare.
*************
Engineer Ameer B Sardauna ya fito cikin shirinsa na farar shadda ɗinki kaftan kansa babu hula gashi kansa ya kwanta luf-luf gwani ban sha'awa, kallo ɗaya za ka yi masa idan kasan shi a baya za ka gano ya yi muguwar rama, fuskar nan tasa a murtuƙe kamar bai taɓa dariya ba. Parking lot ya nufa ya shiga motarsa ya fige ta da mugun gudu maigadi ya taso da gudu ya buɗe masa gate. Kaitsaye asibitin da Jeeddah ta kwanta a kwanaki baya nufa wanda hakan ya zame masa jiki kullum sai ya zo ya bincika ko ta zo check up, duk zuwan da yake yi har yau bai haɗu da ita ba. Yau kam yanke shawarar neman address ɗin ta ya yi ta folder ɗin ta dake asibiti bai wani sha wahala ba ta hanyar ba da cin hanci. Cike da farin ciki ya baro asibiti sai dai farin ciki nashi ya koma ciki da ya tuno cewa matar aure ce. Kasa nufar gidan nata ya yi dole ya nufi wani gun daban. Shi kaɗai yasan yadda sonta ke azabtar dashi za bi ko ta wacce irin hanya ce domin ya mallake ta. Walau hanya mai sauƙi ko kuma akasin hakan shi dai bashi da buri da ya wuce ya rayu da ita bai damu da kasantuwar matar wani ba. Dole ta zama tashi shi kaɗai.
*************
Haidar Ka'oje yana tsaye gaban architect board a katafaren office ɗinsa yana ƙara kallon zane wani gida da ya kammala zanawa, ji ya yi an turo ƙofa yana jiran ya ji muryar saktariyarsa sai kawai yaji shiru kuma wanda ya turo ƙofar ya gama shigowa tsakiyar office ɗin nasa. A fusace ya juyo domin ya tsani a shigo masa babu sallama idanuwanshi suka sauka akan fuskarta da take a murtuƙe can ƙasan maƙonshinsa ya ce "Zarah Malik!
Ya furta full name ɗin ta with so much surprise, kafin ya tako izuwa gabanta da murmushi akan fuskarsa "Camdijam! Yarinya nan kin fara zama abin tsoro how many hours ago da muka yi waya dake ba ki ce min za ki zo Sokoto ba?"
   Sai da ta galla masa harara da manyan idanuwanta kafin ta turo baki gaba tana faɗin "Aliyu kishiya fa kace za ka yi min abin takaici ma wacce na kwana da sani irin azababben so da ka ke mata Aliyu zuciyata ba za ta iya jure wa ba, Dan ALLAH ka haƙura da Jeeddah nan na rasa min ka gani a jikinta da ka nace mata wanda babu shi a jikina. Ka kalle ni daga sama har ƙasa wallahi ba yabon kai ba na fi Jeeddah kyau na fita wayewa na fi t........
    "Ya isa Zarah!
Ya sauri katse ta domin ya fahimci kishi ne ke ɗawaniyya da ita. Ya fridge ya nufa ya dauko mata ruwa mai sanyi da drinks, ya zuba ruwan a handle cup ya miƙa mata kauda fuska tayi cikin sanyi murya ya ce "Please Zarah kar ki ƙara ɗaga min hankali kinsan ko kaɗan banaso ɓacin ranki.
Da sauri ta shiga rarraba idanuwa cikin office ɗin kamar tana neman wani abu Kafin ta ce "Ai na zaci ko Jeeddah tana cikin office ɗinan domin waɗannan kalaman nata ne aka ara min dan kawai a kwantar min da hankali.
  Ɗan bazawari murmushi ya yi gami da maƙe ƙafaɗa ya ce "whatever! Za ki sha ruwan ko na mayar da kayana?"
Da ƙarfi ta fizgo cup ɗin har ruwan yana zube mata a jiki ta kafa kai ta shanye duka kafin ta dire cup ɗin akan centre table dake girke a gabanta, kafin ta kalle shi cikin rauni zuciya ta ce "Wallahi Aliyu na kasa ɗaurewa tun lokaci da ka sanar dani burinka naso auren Jeeddah kafin ni hankalina ya yi mugun tashi naji gaba ɗaya na tsani karatuna domin duk shine sanadi da tun-tuni ya hana mu mallakar juna da mu yi aure wallahi Jeeddah bata isa ta sake shigowa rayuwarka ba ballantana har ta saka min shakku akan soyayyata.
Ta ƙarashe magana tana sharar hawaye da gefen mayafinta.
  "Kin ga Zarah banaso mu dinga maimaita magana ɗaya tun farko haɗuwata dake ban ɓoye miki ba sanarda ke koda mu yi tsufan kwado ALLAH ya kawo sanadi da Jeeddah bata igiyar aure wani akanta tabbas zan cika muradin zuciyata ta hanyar mallakar ta saboda haka ki daina ɗaga hankalinki domin kin daɗe da sani matsayi da wanzuwar ta a gareni. Ina sonki Zarah Malik da bana jin sonki a zuciyata ba. Da ba zan taɓa bari alƙawari aure ya shiga a tsakanin mu. Saboda haka ki tashi mu tafi gida gobe da sassafe zan mayar dake Kebbi banaso ki yi missing exams ɗinki. Hope kin zana ta yau da kyau?"
  "Na kammala amma bana cikin yanayi da zan rubuta ta da kyau da matuƙar wahala idan ban yi Carry over ɗin ta ba.
Ta faɗa cikin sanyi murya.
  "ALLAH ya kyauta!
Ya faɗa yana harara ta saboda laifinta yake gani domin bai ga abin tada hankali ba. Kafin su iso gida har sun shirya tamkar ba some minutes ago Zarah Malik ta gama kuka ba. Sai nishaɗi suke yi abinsu yana ɗaya daga cikin dalillai da yasa Zarah Malik ta sami matsuguni a zuciyar Haidar saboda haƙurinta da sauri yafiya.
Zaune nake a main parlour ina gyara farce gidan ya yi tsit saboda Mommy ta fita unguwa kaɗaici ya dame ni shiyasa na fito main parlour na kunna kayan kallo, tun jiya da na kashe wayata ban ƙara marmari kuna ta ba.
Na shagala sosai da yake farce na na ƙafa naji ƙarar buɗe ƙofa kafin na ɗago hancina ya shaƙi ƙamshi turarensa, sai kuma na ji sautin dariyarsa da na mace a matuƙar razane na ɗago Idanuwana yayin da zuciyata take wani irin bugawa, wanda na rasa na menene wani irin kallo na bi su dashi zuciyata sai fattt-fattt! Take yi kamar za ta tsinke ta faɗo ƙasa muryar Zarah Malik na tsikaya tana min sallama har da wani cewa "Jiddoh sannu da gida!
   "Sannu da gidan ubanki.
Abinda ya dace nace da ita kenan amma kuma sai na tsinci kaina da faɗin "yawwa! Daga haka na maida ganina akan yatsun ƙafa ta.
  "Zarah zo tafi ɓangare na akwai abunda zan nuna miki kafin Mommy ta dawo ku gaisa.
Ya Haidar ya faɗa tare da nufar part ɗin sa ita kuma kamar raguma ta bishi a baya tana faɗin "Sweetheart kada ka yi min wayau irin na ranar kadai gane?
A mugun razane na bisu da kallo baki buɗe har suka ɓacewa ganina ban ɗauke idanuwana ba akan corridor da suka bi......

#jeeddah Aliyu
#Egineer Ameer B Sardauna
#Bilal shettima
#Jeeddah Usman maishadda
#Zarah Malik
#Haidar Ka'oje
#Team zazzafan kishi
#sabon salo.
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

*Assalamu alaikum*
Ina miƙa sauƙin gaisuwa ga masoyana mabiye wannan littafin nawa. Bayan dogon lokaci da ku ka ɗauka kuna jiran ci-gaban wannan labari sai yau ALLAH ya nufe ni da ci-gaba da kawo musu shi a dalili wasu abubuwa da suka faru dani wasu masu daɗi wasu akasin haka cikin amincewar Ubangiji da iyawarsa gashi na sake dawo muku da ƙarfina in-sha-ALLAHU babu tsayawa har sai na kai muku ƙarshen wannan labari mai ɗauke da cakwakiyya, al-ajabi, butulci, cin amana. Ku dai ku ci-gaba da haƙuri tare da jimirin bibbiya ta.
___________________________________

056.

Muryar Bilal Shattima na tsikaya yana cewa "Khamis ga Jeeddah. Kana ya juyo gare ni ya ƙara cewa "Jeeddah ga Khamis duk wani bayani da ya danganci nai masa akanki already nayi masa tun kafin haɗuwar ku. Hakazalika ke ma na faɗa miki takaitaccen tarihin sa.
   Duk maganganu da Bilal yake yi ba wanda na fahimta a dalili wani irin bugawa da ƙirjina ke yi na kuma rasa dalili faruwar hakan. Sai da khamis ya sauke boyayyen numfashi yayin da fuskarsa ke ɗauke da miskilin murmushi, ya ce "Ka yi haƙuri maigida Bilal akan tambayar da zan maka watakila ta ɓata ma rai miyasa ka ke so tayi auren kisan wuta alhali kasan ALLAH ya yi hani da yin sa?"
Tamke fuska Bilal Shattima ya yi saboda duk mutumin da ya ce zai kawo masa illar dake tattare da muradin sa haushinsa yake ji cikin daurarriyar murya ya ce "wannan ba matsalar ka bace khamis asalima wannan aiki ba kyauta za ka yi min ba biyan ka zan yi ba kuma ƙaramin amfana za ka yi da kuɗin ba musamman da za su zo ma a daidai Lokaci da ka ke da tsananin buƙatar su.
   "Haka ne Maigida Bilal tabbas ina tsanani buƙatar kuɗi shi ne ma dalili da yasa na amince da buƙatar ka saboda haka ta ɓangare na babu Matsala sai ka tambaye ita uwar gayyar idan nayi mata?"
Da sauri na ɗago da nufi na ce ba ka yi min ba sai kawai na tsikayi muryar Bilal yana faɗin babu buƙatar domin aure wuci gadi za ku yi saboda haka ba sai ka yi mata ba asalima bana buƙatar ka yi mata. Saboda haka ka shirya daga gobe za ka fara zuwa zance gidansu daga nan za tai ma iso gun mahaifinta kai kuma sai kayi gaggawar tura magabatan ka banaso a ɗauki dogon lokaci na fi so ayi komai agaugauce a wuce wurin.
   Cike da zallar mamaki Khamis yake kallon fuskar Bilal Shattima wato komai shi zai shirya masa azahirin gaskiya Jeeddah yake tausayi in ban da kwaɗayi na mata ALLAH ya raba ki da wannan mummuna mai kama da gwaggo biri, da wani burtomi hancinsa kamar ƙofar kasuwa miye na wani aure kisan wuta ki koma masa ai kamata ma yi ta haɗa gaggarumin party a tayata murna rabuwa dashi.
   "Khamis ya naji ka yi shiru ba ka ce komai ba kodai tsari nawa ne bai maka ba?"
   "Hmmm! Ba ko ɗaya maigidan Bilal ai ni banida zaɓi sai abunda ka ce.
   Murmushi Bilal Shattima ya yi tare da faɗin "shikenan za ka iya tafiya zan nemi ka daga baya sannan ka duba ta WhatsApp na tura maka number Jeeddah koda za ka je gidansu sai ku yi waya.
  "Okay maigida.
Khamis ya faɗa gami da miƙewa ya kalli Jeeddah ya ce "Ranki shida de sai anjima.
  "Humm! Ka gaida gida.
Na faɗa a sanyayye bayan tafiyar khamis na gyara zama tare da fuskantar Bilal na ce "Ni fa Love kwata-kwata ban yarda da wannan mutumin ba wallahi bai kwata min a rai ba.
   "Haba! Love don ALLAH kada ki kawo mana cikass! A cikin tafiyar nan. Da ace Khamis yana da wata matsala da ko kusa ba zan kawo miki shi ba.
"Duk da haka Love ka ƙara zurfafa bincike akan sa ruwan munafukai ne dashi.
   Dariya yasa kamar wani wawa ni kaina naji haushi dariya da yake yi ba kasafai nake so dariya ba a wasu lokuta ina sauri harzuƙa idan ana min dariya a fusace na ce "Banaso dariya love ka daina da wannan dariyar ta rashin dalili da ka ke yi dama ka natsu ka yi nazari abunda na hango a tattare da wannan mutumin mai zubin munafukai.
Ya tsagaita dariyarsa kana ya ce "Jeeddah ki yarda dani Wallahi-azim khamis bashida matsala nan da ki ke ganinsa mutumin kirki ne mai matuƙar tsoron ALLAH.
    "Mtsss! Mai tsoro ALLAH ne zai yarda ya yi auren kisan wuta ko kuma shi nashi kalar tsoron ALLAH ne haka.
"Kin ga Hajiya Jeeddah mu jingine wannan zance a gefe mu ɗauko wani.
Kafin na bashi amsa waya ta tai ringing nai sauri zuge jakkata na ɗauko sunan Mommy na gani da sauri nai picking "Assalamu alaikum Mommy Ina wuni?"
  "Wa'alaikum Salaam lafiya qalau Jeeddah na kira Mamanku a waya ta gayamin kina hanya zuwa gidana idan da akwai kuɗi hannunki ki biyo min da cabbage sai da na zo aiki dashi na tarar babu gashi kuma direba ya tafi Airport ɗaukar Haidar.
   "En! Mommy ina da kuɗi shi kaɗai ne kike da buƙata?"
"En!
Mommy ta faɗa tare da jaddada min da nayi sauri ni kaɗai take jira.
Shiyasa ina maida wayana jakka na miƙe cikin sauri Bilal Shattima ya kalle ni tare da faɗin "Ya naga kin miƙe ba dai tafiya za ki yi ba?"
  "Tafiya zan yi Love Mommy tana jira na.
   "Haba! Love bai kamata ki tafi tun yanzu ba musamman idan ki ka yi duba da tsawon lokaci da muka ɗauka ba mu haɗu ba.
  "Ni ma ba a son raina zan tafi ba na gayamaka tun farko karya na yiwa Mama na ce gidan mommy zan tafi to shine ta kira ni yanzu ta ce na siyo mata cabbage na taho mata dashi ka ga bai dace na zauna ba.
   Ambatar mommy da nayi yasa annuri kan fuskarshi ya ɓace batt! Ya yi kici-kici da wannan fuskar tashi kafin cikin muryar dake bayyanar da ɓacin ransa a fili ya ce "Ni fa Jeeddah banaso kina zuwa gidan Turai domin tuni-tuni zuciyata take kimtsa min so take ta sake cusa miki ɗanta a karo na biyu, dama can tana cikin mutane da suka tsani tarayya ta dake, shiyasa duk duniya idan da akwai mahaluki da na tsana bai wuce Haidar Ka'oje ba. Domin shi kaɗai ne mutumin da nake da yaƙini zai iya rabani dake rabuwa ta har abada.
   Yadda Bilal Shattima ya kira sunan Mommy gatsal ya yi masifar ƙona min rai ko babu komai Mommy ta cancanci girmamawa a gare shi kasancewarta ƙanwar mahaifina uwa ɗaya uba ɗaya yadda Mommy take nuna min ƙauna zan iya cewa ko 'ya'ya da ta haifa albarka. Idan har aka faɗin maganar banza akanta dole na ji ciwo saboda haka cikin ɓacin rai na kalle shi gami da faɗin "A'ah dakata malam banaso rashin kirki sunan mommy fa ka kira gatsal ba ko sakayawa kada kaga na amince da buƙatar ka, ka nemi wuce makadi da rawa muddin za ka ci-gaba da nuna rashin ɗa'a akan Mommy wallahi za mu iya ɓatawa domin Mommy Turai mahaifiya ce a gurina ba wai ƙanwa mahaifi kaɗai ba. Tun da nake da Mommy bata taɓa cusa min ra'ayi na so Ya Haidar ba saboda haka wannan ya zama karo na karshe da za ka furta mummunar kalma akanta.
    Yadda Jeeddah ta zage tana ta faɗar maganganu hakan ba ƙaramin ƙonawa Bilal Shattima rai ya yi ba dama kusan mutane naku da baƙar zuciya babu mai haƙuri a cikinsu kowanne su zuciyarsa a baki take saboda haka a hasale ya kalleta yana wani ƙanƙantar da idanuwa na tijara ya ce "Yanzu na gano ki Jeeddah idan har kin fara son Haidar Ka'oje ki fito fili ki faɗa min na daina wahalar da kaina a banza akanki.
   Nima a fusace na kalle shi from head to toe gaba ɗaya zufa ya jiƙa shaddar jikinsa kamar an masa wanka da ruwa, naman fuskarsa sai rawa yake yi kamar abinda ake girgizawa nan take haushinsa ya ƙara kama ni na ce "idan har haka zuciyarka ta kimtsa ma to ka ɗauka haka ɗin ne dama za ka ɗauki shawara ta ka je ka rage wannan uban ƙiba da ka ke kaya yafi ma wannan zargi da ka ke min.
Daga haka na juya rai ɓace na buɗe ƙofa na fice abina ina jiyo shi sai ihu da ɓamɓatu yake yi ko waigo wa ban yi ba. Bayan na siyawa Mommy aike ta akan hanyata na zuwa gidanta traffic ya tsayar dani sai na hango mai siyar da turare mota dama nawa ya ƙare na sauke gilashi mota na kira shi na siye guda biyu bayan traffic ya sake mu horn na ji ana min a bayana ni dai nasan akan hannuna nake saboda haka banga dalili a dinga yi min wannan ɗibar albarka ba. Ci-gaba da tafiya nayi ba tare da kaucewa ba ko kuma na ƙara speed kamar daga sama naga wata black Benz ta zo daff dani mamallaki motar ya zuge gilashi ya leƙo da kanshi, ta window ya kwalla min kira "Maijiddah Dan ALLAH ki tsaya ki bani taya ta.
  Lokaci da nayi arba dashi zaro idanuwa nayi a zuciyata na ce "Amma wannan mutumin an yi wawa duk don saboda taya ko taya ma take me home ba wata taya kirki ba zai nemi ya tashi hankalina akan titi mtsssss! Sabon yankar rake kawai.
Na faɗa a bayyane tare da gangara wa gefen titi nayi parking zuciyata cike da zallar haushinsa, tsabar takaici dake cina yasa na kifa kaina akan steering. Fuskarshi ɗauke da shu'umin murmushi ya ƙaraso yana zuwa babu wani excuse ya buɗe front door ya zauna kallon amma ba kada hankali nai masa kafin na taɓe baki leiƙa fuskata ya yi tamkar zai sumbace bakina nai sauri ɗauke kaina daga steering ina hararashi ƙasa-ƙasa "Maijiddah manya ganinki sai mai sa'a kullum ina sintiri haɗe da gararranba neman ki sai yau ALLAH ya haɗa ni dake.
   Har ya dasa aya ina kallonsa da baki buɗe yanzu saboda ALLAH akan wata tsinaniya taya take me home yake nema na a kufule na ce "Yallabai halan taya taka ta gold ce domin kasantuwar ta gold kaɗai zai sa ka dinga gantalli nema na?
Na ƙarashe magana ina wani yatsine fuska.
Wani irin azababben sonta ke ratsa jini jikinsa duk abinda take yi mugun burge sa take yi ji yake kamar ya jawo ta jikinsa ya yi mata kyakkyawar runguma, ya tsotse ɗan ƙaramin bakinta.
"Da alama na ɓata miki rai ko?"
    Sai da na sake galla masa harara kafin na ce "Ba iya ɓaci rai ba har haushi da takaici ka bani.
Sai kawai yasa 'yar ƙaramar dariya yana kallona yana wani lumshe idanuwa "ALLAH ya huci zuciyarki gimbiyar matan dukka duniya nayi haka ne domin shi kaɗai ne uzuri da zan kawo da zai sa ki tsaya mu gaisa.
   "Gaskiya Yallabai kai ɗin na musamman ne yanzu saboda mu gaisa zai sa ka dinga kwaɗa min kira akan titi, gaskiya banaso kar ka sake yi min haka.
Murmushi ya yi tare da faɗin "Tuba nake ranki yadade da girman kujerar ki in-sha-Allahu hakan ba zai sake faruwa ba.
  Sai lokaci na saki fuskata na ce "Ka yi haƙuri Yallabai ban san inda zan ganka ba shiyasa ban kawo maka taya ka ba. Kuma koda na dawo daga Saudiya na tarar da Yayana ya canza min mota gashi taya ɗinka yana ciki wancan mota.
   Duk abunda take faɗa daidai da second ɗaya bai ɗauke idanuwanshi daga fuskarta ba. Baisan haka yake mahaukaci sonta ba sai da yau ya haɗu da ita sai da ya saki kyakkyawar ajiyar zuciya kafin ya ɗage girar ido guda ya ce "Karki damu Maijiddah ni tuni na manta da zance wata aba taya burina shine ta wacce hanya zan bi da zan ci-gaba da gani wannan kyakkyawar fuskar taki mai hanani bacci.
    Taɓe baki nayi gami da faɗin "miyasa za ka saka wa ranka ci-gaba da son ganina alhali ka kwana da sani hakan ba daidai bane ko manta ni matar aure ce?"

#Bilal Shattima
#Egnr Ameer
#Haidar ka'oje
#Jeeddah maishadda
#team zazzafan kishi
[8/20, 6:42 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

057

Kalma tana da aure da ta ambata ba ƙaramin girgiza duniyar sa ya yi ba. wani irin mashahurin kishi ya lulluɓe shi ya haɗiye wasu yawu adams apple ɗin shi suka yi wani kalar motsawa da ƙarfi. Ina gani ya nusa a duniyar tunani na ce "Yallabai ni zan wuce sai gani na gaba ka gaida Umma.
Na faɗa tare da yiwa motata, key a manufa ta taso ya fita min daga mota nasan inda dare ya yi min amma sai yai wani ƙara gyara zamanshi cikin sanyi murya ya furta "Sauri me ki ke yi haka?"
   "Gida ake jira na Yallabai.
Na faɗa cike da ƙosawa a zahiri gaskiya ya gundare ni na matso ya fita min daga mota.
  "Shikenan Maijiddah sai yaushe za mu sake haɗuwa?"
Yatsine fuska nayi gami da furta "Duk sanda ALLAH ya sake haɗa mu.
   "Haka ne amma ki taimake ni da number wayarki.
"Yallabai number wayana fa?"
Na tambaya cike da maɗaukakiyar mamaki.
"En! Ko ba za ki bani bane?"
"En! To ba wai ba zan ba ka bane ba kawai ina tunani amfani me za tai maka.
    "Idan za ki bani Maijiddah ki ba ni kawai duk amfani da za tai min wannan ba damuwarki bane.
"Hmm!
Na faɗa gami da miƙa masa tafin hannuna karaf na ji ya riƙe min hannu har yana haɗawa da wata irin shassheka kamar wanda ya yi tserar gudu ya zo na ɗaya, cikin sauri na fincike hannuna ina faɗin "Yallabai wayarka za ka bani ba hannuna za ka riƙe ba.
   "Oh! I'm sorry.
Ya yi magana tare da ciro wayarshi daga gaban aljihun rigar jikinsa ya miƙo min na saka mishi numberna tsabagen rashin yarda sai da ya kira wayana ya ji ya yi ringing kana ya buɗe ƙofa ya fita ya dafa ƙofar mota gami da tura kanshi cikin motar cikin wani irin salo ya ce "haƙorin makkahn nan ya yi miki kyau ban taɓa gani mace da haƙorin makkahn ya yiwa kyau kamar ke ba, komai na ki na musamman ne Maijiddah.
Yana ƙarashe magana ya juya da sauri ya nufi gun da ya yi parking motarsa na bishi da kallo baki buɗe kafin na taɓe baki na ja motana na halba kan titi da high speed na iso gidan Mommy domin nasan na ɓata mata lokaci sosai ina zuwa na tarar da ita a kitchen tare muka ƙarasa aiki. Muna kammala wa ta bar min arranging dining table ita kuma ta wuce bedroom tai wanka.
   Ina tsaye a dinning room Ina ƙara ƙarewa table ɗin kallo koda da akwai abunda ban ɗauko ba. Na ji sallamar direban da yaje ɗaukar Ya Haidar ya shigo janye da luggage ɗin shi yayin da Ya Haidar yake biye dashi a baya cikin salon tafiyar nan tashi ta izza da ƙasaita tsintar kaina nayi da wani irin faɗuwar gaba bansan miyasa a yanzu ko muryar Ya Haidar na ji sai gabana ya faɗi ba, alhali ada can baya bana ji hakan akansa. Na shaƙi sanyayye ƙamshi turarensa mai haifar min da natsuwa a hankali na fara tafiya na nufo cikin falon cikin wata kalar kasalalliyar murya na ce "Ya Haidar oyoyo!
Saukar muryata a dodon kunne shi yasa shi tsayawa kana ya dawo da ganinshi ta inda nake ya wani zuba min manyan farare idanuwanshi masu kama da na mai jin bacci, ya wani ɗage girar ido fuskarshi a haɗe ya ce "Ke me ki ke yi a gidanmu?"
Murmushi ne mai ɗan karan sauti ya sumbace min domin idan ban manta ba dare da zai yi wannan tafiya muka yi faɗa har na ce dashi idan har yana da zuciya a ƙirjin shi kar ya sake zuwa mana gida wato bai manta da abunda ya faru ba shi ne ya rama.
Rausayar da kai gefe ɗaya nayi tare da faɗin "Ranka ya dade abinda ka ke zuwa yi a gidanmu nima shi na zo yi a  gidanku.
  "Oh really?"
Ya faɗa yana ƙara ɗage gira jinjina masa kai nayi tare da nufar gun da direban yake tsaye na karbi luggage ɗin ina faɗin "Malam Rabi'u kawo na kai mishi ciki.
  "Tohm! Ranki yadade.
Cewar malam Rabi'u yana mai hanita min luggage ɗin. Ya Haidar yana gani Malam Rabi'u ya fice ya kai hannunshi zai karɓe akwatin sa nai sauri janye wa ina dariya ɗan guntun tsaki ya ja gami da nufar bedroom ɗin Mommy ni Kuma na ja akwatin na nufi corridor da zai sada ni da part ɗin sa.
Har bedroom ɗinsa na kai masa akwati ina buɗe ƙofa zan fito yana sako kai muka tsaya cirko-cirko! Gaba ɗaya ya zuba min narkakkun idanuwanshi numfashi da yake saukewa akai-akai iskar tana sauka akan fuska ta hakan ya haifar min da  shiga wani sabon yanayi mai wuyar fassara wa, gashi ya tare ƙofar fita ballantana na fice da kyar na iya buɗe bakina na ce "Aliyu lazy ka bani hanya na wuce ko duk laziness ɗin ne yasa ba ka san ka tare ƙofa ba?"
  Dan kawai na harzuƙa shi na kira shi da wannan sunan tun yana primary school wani schoolteacher ɗin shi ya sa mishi wannan sunan a dalili ciwo zuciyar da yake ɗauke dashi yasa a class ba shi da kama jiki duk lokaci da aka yi musu note sai kowa ya ri ga shi gamawa sai teacher ɗin yake kira shi da Aliyu lazy sam bayaso sunan ni kuma a duk lokaci da nake so ɓata mishi rai nake kiran shi dashi. a maimakon ya ɓata rai kamar yadda ya saba sai kawai ya saki shaƙiyi murmushi tuni nayi observing ɗin Ya Haidar muddin ya yi irin wannan miskilin murmushi zai furta maganar da ta girmi tunanina saboda haka nai sauri toshe kunnuwana ina faɗin "Dan ALLAH ka rufa min asiri ka haɗiye maganarka ta koma cikin ka.
Dariya mai ƙaramin sauti ya yi tare da sa hannunsa ya ture ni ya wuce cikin ɗakinsa, yana faɗin "Da ki bari na faɗa miki hakikanin gaskiya amma duk da haka ina fatar ALLAH ya kai damo ga harawa a lokaci za ki fahimci koda ni lazy ne amma ban da wannan fanni ba.
   "Mtsssss! Ɗan iska kawai dama ba abunda ka kware dashi da ya wuce wannan.
Na faɗa ƙasa-ƙasa ina gani ya juyo na kwasa da gudu na fice.
Jim kaɗan sai gashi ya dawo sanye da farar armless da black colour three quarter crazy jeans farare ƙafafuwan shi ɗauke da flip flops, sai uban ƙamshi yake zuba wa na ɗago daga danna wayata da nake yi na sauke idanuwana akan fuskarshi ba ƙaramin kyau ya yi min ba har sai da na yaba kyau nashi a zuciyata.
Yana zuwa ya saki min ɗan ƙaramin rankwashi aka yana faɗin "Daina kallona karki cinye ni mayya.
   Dafe kaina nayi tare da furta "Ouchhhhh! Wannan zalunci fa?"
"In kin girma ki rama.
Ya faɗa yana murmushi nai sauri ajiye wayana na tashi zubur ina faɗin
"Tun da ka faɗi haka zan nuna maka na girma dan wallahi sai na rama.
Na ƙarashe magana tare da yin tsalle da nufi na rankwashi kansa kafin hannuna ya sauka akanshi ya riƙe ni kasancewar yafi ni tsayi nesa ba kusa ba.
   "Daga dawowarka ko hutawa ba ka yi ba za ku fara hali naku.
Mu ka ji muryar mommy daga bayan mu duk da yaga mommy bai sake min hannuwana ba yasa dariya ya ce "ALLAH mommy ba laifina bane ita ce ta fara gaba ɗaya yarinya nan ta gama rena ni idan har ba aura min ita ku ka yi ba reni da take min ba zai kau ba.
Jin abunda ya faɗa yasa naji Kunya ta lulluɓe ni nai sauri sadda kaina ƙasa mommy ta ƙaraso tare da zare min hannuwana daga cikin nashi tana faɗin "To naji cikamin yarinyata kar ka ji mata ciwo sarkin marasa kunya duk duniya.
Yana dariya ya sake ni Mommy ta ja ni zuwa dining room shi ma ya biyo mu a baya tare muka ci abinci, daidai da second ɗaya bai ɗauke idanuwanshi daga kaina ba. Sai dare na baro gidan shi ma da kyar Ya Haidar ya bar ni dan har rokata ya yi na kwana na ƙi saboda gobe ranar aiki ce zan je office.
Washegari sai around 11:30am na iso office yau nayi latti sosai, tun kafin na ƙarasa parking space da aka tana da domin ma'aikata, na hango shi tsaye jikin motarsa fuskarshi a haɗe babu annuri ko kaɗan akanta sai faman danna wayarsa yake yi, ko ban tambaya ba ina da tabbaci ni ce yake kira domin tun rabuwar ta dashi jiya na danna numbershi a blacklist, nima na ɗaure tawa fuska na fito daga mota ina ƙoƙari rufe ƙofa ya hango ni cikin zafin nama ya iso wurina yana zuwa ya damƙe damtse hannuna da ƙarfin gaske sam bai yi la'akari da public place muke ba ya manna ni jikin mota yana wani irin huci kafin ya ce dani "Miyasa ki ka yi blocking ɗina?"
Sosai na tsorata dashi domin yanayi sa kwata-kwata bai yi min kama da na mai cikakken hankali ba jikina ya ɗauki mugun rawa dama can bakin ne kawai dani amma tsoro kamar farar kura, cikin rawar murya na ce "Dan ALLAH ka sake ni mutane su na kallon mu zan gayamaka dalili.
   "Ba zan sake ba har sai kin gayamin.
Yayi magana cikin loud voice na ja dogon numfashi cikin sarƙewa lafazi na ce "Banaso ka kira mijina ya ji wallahi zan iya shiga matsala.
    "Mijinki.....mijinki I hate this name I absolutely hate this name idan bakinki ya sake furta wannan suna a gabana komai zai iya faruwa idan na ce komai Maijiddah ina nufi komai ma.
   Wani irin mugun tsoro shi ya ƙara lulluɓe ni da kyar na aro jarumta na yafawa kaina cikin dakakkiyar Zuciya nace "waye kai me ka ke nema a gurina don na gaji da bibbiya ta da ka ke yi?
     "Waye ni me nake nema a gurin ki wannan duk ba damuwarki bane tun da ni nasan wacece ke na kuma san abunda nake nema a gurinki abu guda nake so a gare ki if I call your phone just pick up koda ba za ki yi min magana ba ki ɗauki kiran kawai.
   "Innalillahi wa'inna illahim raji'un! Wannan wane irin hauka ne?" Haba bawan ALLAH yanzu da aure nawa zan dinga picking call ɗinka hakikanin gaskiya ba ka yiwa rayuwata adalci ba da kuma nasan za ka zame wa rayuwata matsala da a wancan ranar ban amince da taimakon ka ba.
   Sai kuma naga jikinshi ya yi sanyi har ya sassauta riƙo da ya yi min cikin sanyayya murya ya ce "Ba za ki iya gane irin muhimmanci da ki ke dashi a gareni ba Maijiddah koda zan iya cutar da kowa ke ba zan cutar dake ba. Ki yi haƙuri da abunda nai miki ina da wani hali idan raina ya ɓaci hankalina gushewa yake yi amma ni ba mugun bane ki yafe min kin ji?"
Ɓoyayyiyar ajiyar zuciya na sauke har zuwa lokaci tsoro shi bai gama saki jikina ba.
   "Shikenan.
Na faɗa a takaice.
  "Ke haƙura kenan za ki cire ni a blacklist?"
Na gyaɗa kai.
"To ki cire a gabana shi ne zai bani tabbaci kin yafe min.
Ba tare da nace komai ba na ciro wayana a handbag na cire security code na miƙa mishi da sauri ya karɓa ya cire da kanshi kana dawo min da ita yana mai ƙara bani haƙuri ban ce dashi uffan ba nai tafiyata ko juyowa ban yi ba. a can ƙasan zuciyata fargaba nake kada ya gano cewa bani da aure saboda wannan mahaukaci muddin yasan cewa bani da aure na shiga uku lallai dole na gaggauta sanar da khamis ya turo magabata sa domin ban ga dalili ɓata lokaci ba tun da aure wuci gadi ne za mu yi ba na soyayya ba ballantana a ce ana bukatar fahimtar juna. Ban san adadin lokaci da ya ɗauka tsaye a guri ba kamar an dasa shi kafin ya yi ƙwafa gami da shiga motarsa ya bar wuri yayin da zuciyarsa cike da muradin mallakarta ko ta hali ya ya
********
"Ban taɓa sani ke mutuniyar banza bace ba marar wayau sai yau Nusaiba. ke kenan kullum cikin yaji sai kace kanki aka fara aure.
  Cewar Baffa mahaifin Nusaiba wacce yau da sassafe ta dako yaji kullum bata da korafi da wuce Bilal yana tare da Jeeddah burinta su rabu har abada sun yi yawon gidan je bokaye da na tsibu ita da Aunty Bahijja har sun gaji sun ka sa nasarar raba tsakanin su.
Kuka Nusaiba ta fashe dashi tana faɗin "wallahi Baffa na gaji da aure nan gara araba shi kowa ya huta, tun da muka yi aure nan ban san mijina ya zauna tare dani ko na hour ɗaya ba. Hatta da hakkina na aure sai in na saka mishi magani tadda sha'awa a cikin abin sha zai nemi ni...
   "Innalillahi wai'inna illahim raji'un! Nusaiba yaushe ki ka lalace har haka? Yanzu ke ko kunya bakyaji da ki ka kalli tsabar idona ina matsayin mahaifinki ki ka dinga zaro min waɗannan manya-manyan maganganu.

#Haidar ka'oje
#Bilal Shattima
#Egnr Ameer
#Jeeddah maishadda
#Team zazzafan kishi
  [8/20, 7:36 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

059.

Bahijja tana ƙyala ido ta ga mijinta har wani washe baki take yi gaba ɗaya haushinta gami da takaici ta suka lulluɓe Hajja ta maka mata uwar harara kafin ta dawo da ganinta akan malam Haruna dake tsaye ƙi ƙam yana wani muzurai nan take haushinsa ya ƙara turnuƙe ta. Domin bata ga amfani wannan zuwa da ya yi ba. Ko bai musu sallama ba, bai kuma gaidata ba. A matsayin ta na uwar matarsa balle har ya bata haƙuri akan mummunan duka da yai wa 'yarta. Bata taɓa sani malam Haruna tsinanne ne marar albarka ba sai yau. Ita kuma ba abinda zai hanata nuna mishi ita ma tsohuwar banza ce don haka ta miƙe a fusace ta ce "Haruna uban me ka zo ɗauka asibiti nan ko ka zo ne ka inda ƙarasa ta?" domin duk wanda yaga wannan kafiri dukan da ka yiwa Bahijja yasan rayuwarta kaso ɗauka ALLAH ne bai ƙare mata kwana ba da yanzu ta daɗe a kushewa.
Duk maganganu da Hajja take yi Malam Haruna yana tsaye yana mata kallon wulaƙanci, yayin da Bahijja take ƙoƙari kama hannun Hajja da ɗayan hannunta mai lafiya so take ta taka wa Hajja birki, tun da har ya zo duba ta bai kamata tai masa irin waɗannan maganganu ba. In fact ita bata ga laifinsa ba tasan magauta ne suke so ɓata tsakanin su in-sha-ALLAHU ba za ta taɓa bari su yi nasara ba. Domin har ta ƙudurta a ranta tana tashi daga jinya dole ta koma wajen boka ya yi mata aiki da irin makamancin wannan abin ba zai sake faruwa ba.
   "Haba miye haka don ALLAH Hajja sai ka ce ba ki san ƙaddara da sharrin magauta ba? Ni dai ya daka ba wani ba, kuma tun-tuni nace na yafe masa domin ba hali malam bane dukan macce kuma ma ai tsakani mata da miji sai ALLAH duk wanda ya shiga tsakaninsu rabonsa kunya saboda haka ki kyale min mijina.
   "Innalillahi wai'inna illahim raji'un!
Anya kuwa Bahijja Haruna bai asirce ki ba kamar yadda kema ki ka asirce shi?"
Hajja tai subul da baka domin tsabar mamakin furuncin Bahijja da ya lulluɓeta bata masan takamaiman abunda take faɗa ba.
Ƙoƙari tashi zaune Bahijja take yi duk da ƙafarta guda tana sakale a jikin ƙarfe an yi mata pop ga Kuma hannunta tun daga tsitsiyar hannunta har izuwa ga shoulder ta shima lulluɓe yake da pop amma gani Hajja tana so ta ɓallo mata ruwa ta ɓata tsakaninta da mijinta, yasa ta yunƙuri tashi zaune, sai da duk iya yunƙuri da take yi ta kasa koda ɗago kanta daga pillow balle har ta iya tashi zaune.
Malam Haruna ya zura hannunshi cikin aljihun babbar rigarsa ya ciro farar takarda ya kalli Hajja da Bahijja a wulaƙancce ya shiga faɗin
"Kin ga Hajja ba zuwa nayi don ki shuka min rashin mutunci da ki ka saba shuka wa surukanki ba. zuwa nayi na kawo wa tsananniya 'yarki takarda saki domin ba zan iya ci-gaba da zama da ita ba.
Ya ƙarashe magana tare da cilla wa Hajja takarda akan fuskarta "gashi nan na saki Bahijja saki uku, tun jiya na kwashe kayan ta na aika mata dasu can gidan ubanta, a yanzu ko tsike bata dashi a gidana. Kuma yayana dukka na karɓe abina har wacce take wurinki na karɓe abata.
Yana ƙarashe magana ya nufi ƙofar fita ya buɗe ya fita abinsa yana ji Bahijja na ihu haɗe da kwalla masa kira, wani irin gunji kuka Bahijja take yi ashe haka saki yake da ciwo ashe irin wannan raɗaɗi da zafi ake ji a yayin da aka ce an sake macce, nan take ta tuna da Jeeddah ashe lokaci da suka sa aka sake Jeeddah saki uku irin wannan baƙin ciki ta ji. Jikin Hajja ya yi sanyi ta duƙa ta ɗauki takardar tana jujjuya ta kafin ta koma ta zauna, cike da baƙin ciki take kallon Bahijja dake zabga kuka tana sambatu marasa kan gado "Hajja kin cuce ni kin rabani da mijina Wallahi-azim ko da bala'i sai na koma gidansa na rantse da ALLAH ban saku ba.
Haka dai Aunty Bahijja ta ci-gaba da koke-kokenta tana haɗawa da sambatu tare da durawa Hajja laifi.
*****************
Ban yi ƙasa da guiwa ba na kira khamis na ce ya zo yau-yau ɗinan ya gabatar da kanshi ga Baba lokaci da na faɗa masa wannan magana ina ji sanda ya saki murmushi mai sauti gaske wanda na rasa na mene ne nan take na ji ya bani mugun haushi sai kawai na datse kiran ina mai jan dogon tsaki. Ban don inaso komawa gidan Bilal Shattima ba da ba abunda zai kaini da aure wannan ɗan iskan.
Da yamma sakaliya na fito cikin shirina riga da skirt na lace ne a jikina, ban ɗura ɗan ƙwali ba sai kawai na yane kaina da ɗan ƙaramin veil, ban yi makeup ba domin ni ba ma'abociya so kwalliya bace kawai dai na gogawa fuskata powder kana na zizzarawa idanuwana kwalli, na shafawa laɓɓana man leɓe, sai wani walkiya suke yi jikina na ƙamshin designer perfume wanda yana ɗaya daga cikin tsaraba da Ya Haidar ya kawo min. Na saka flat shoes a ƙafafuwana hannuna riƙe da handbag da car key kitchen na nufa wurin Mama na tsaya a bakin ƙofa na ce "Mama na tafi saloon a wanke min kaina daga can zan biya gidan khairat na duba Airah.
Mama ta dakatar da aiki da take yi ta juyo ta kalle ni tare da faɗin "wai Jeeddah miyasa ki ke so fitar yamma?" Yanzu ke da gidanan sai isha kin kuma san Babanku bayaso yawan fita nan naki.
  Cuno baki nayi ina faɗin "Mama yau dai ba zan kai isha'i ba anan magariba za tai min.
"Shikenan a dawo lafiya ki gaida min da takwara ta.
"Tohm! Amma ba za ki ba da komai akai wa takwara taki ba Mama?"
Na faɗa ina dariya.
Murmushi Mama tayi gami da faɗin "Ai nayi ƙoƙari tun da har nace ina gaidata in Kuma kun rena gaisuwa tawa sai na fasa.
Da sauri na ce "a'ah mun gode ba sai kin fasa ba.
Na ƙarashe magana tare da juya wa ina kwallawa Musa almajiri kira dake falon Mama yana yiwa Aiman gugar kayanshi, ya amsa tare da fitowa Aiman yana biye dashi a baya "Musa mu je ka buɗe min gate zan fita.
Na faɗa tare da yin gaba da gudu Aiman ya sako takalmin shi ya biyo ni yana faɗin "Mommy zan bi ki.
Ba tare da na juyo na kalle shi ba na fara korafi "kai da kace ba ka da lafiya Mama ta goyi bayan ka, ka ƙi zuwa islamiyya shi ne yanzu kana ji zance yawo ka warke ko?"
  Ya ƙaraso kusa dani yana dariya cikin sangartatciyar muryarsa ya ce dani "ALLAH Mommy da gaske bani da lafiya taɓa jikina ki ji har yanzu da raguwar zafi.
"Kai rufe min baki kafin na doke ka.
Nayi magana ina maka masa harara musa ya buɗe min gate ina unlock ɗin kofufin mota, har Aiman ya ri gani shiga na kalle shi kawai na girgiza kai nayi reverse na fita da motar yayin da Musa ya rufe gate yana min fatan a dawo lafiya.
Kaitsaye Ahmadu Bello way na nufa shagon Vicky wacce ta kasance classmate ɗina dama a gun ta nake wanke kai bayan ta kammala wanke min kai, na wuce gidan khairat anan nayi sallar magarib kafin na nufo gida akan hanyar mu na zuwa gida Aiman ya adabe ni sai na siya mishi ice cream dole na tsaya a Seven stars mall ina riƙe da hannunshi muka shiga mall ɗin kaitsaye gun da ake sayar da ice cream na nufa roba biyu ƙanana na siya ni da shi ina ƙoƙari fiddo kuɗi a jakkana, na ji murya Engr Ameer dab dani yana faɗin "Hajiya Maijiddah ice cream guda biyu bai yi muku kaɗan ba?" Ai ko yarona kaɗai zan iya shanye su a ƙara musu manyan guda biyar.
Ya ƙarashe magana yana kallona kafin nai magana har an ƙara ice cream ɗin ya kama hannu Aiman dole na saki dayan hannunshi dake ciki nawa, ya ja shi suka nusa cikin mall ɗin na bishi da wani irin kallon mamaki, sai kawai nayi zugun ina tambayar kaina "miyasa wannan ɗan taliki ke so takurawa rayuwata ne?"
Da nagaji da tsayuwa na juya har ice cream ɗin anan na barshi nai tafiya ta ina ji ma'aikatan wuri suna min magana nai banza dasu, na bude mota na shiga na zauna, lokaci zuwa lokaci nake kallon agogon mota na tabbata yau faɗa a wurin Mama sai na toshe kunnuwana.
Na ƙudurta a raina sai nai masa tijara domin banga dalili da zai sa yi min irin wannan shisshigi ba. Tsabar takaici ji nake kamar na tafi na barshi da Aiman ɗagowa da zan yi sai na hango su tafe yana riƙe da hannu Aiman yayin da ma'aikatan wurin ke biye dashi da 'yan uban shopping bags niƙi-niƙi har dasu keke yara wanda ko ban tambaya ba nasan Aiman ya siyawa, sai kawai na ji raina ya ƙara ɓaci ko uba wa ya gayamishi Aiman yana bukatar keke, bayan ko wannan tafiya da Ya Haidar ya yi sai da ya siyo mishi wani keke mai charging da wutar lantarki shi ma sai nayi faɗa don banga abunda zai yi dashi ba, baya kusan keke huɗu yake da dukka uku Ya Haidar ne ya siya mishi guda ɗaya ne Ya Kabeer ya kawo mishi fisibilillahi idan ba dafa masa keke zan yi ya ci ba, me zai yi dashi.
Knocking ɗin gilashi motar da ya yi yasa ni dawowa daga duniyar tunani da na lula cikin fusata na sauke gilashi kana na buɗe ƙofar front seat na kalli Aiman da ke ta faman haɗiyar chocolate yadda yake ci choco ɗin tsakani da ALLAH sai ka ce bai taɓa ci ba, wani mugun haushi ya ƙara turnuƙe ni, a hasale na daka mishi rikitatciyar tsawa "Aiman shiga mota mu tafi kuma kafin ka shigar min mota ka tabbatar ka jefar da wannan Choco dake hannunka. Idan muka je gida wallahi sai naci ubanka ba dai na sha faɗa maka ka daina karɓa abu a hannu strangers ba? amma da yake kai ɗin kwaɗayayye ne, shi ne ka karɓi Choco a hannu wannan mutumin mai siffar mugaye.
Da sauri Aiman ya jefar da chocolate ɗin tare da furzar da na bakinshi, yana goge bakinshi da bayan hannunshi, tuni idanuwanshi suka fara tara kwalla domin yasan halina mugun duka nake masa kuskure kaɗan zai yi min na kama shi nai ta duka cikin ma Mama tana tsawata min, kwata-kwata bani da haƙuri da yara. Mama na yawan faɗar da Aiman a hannuna ya taso da tuni duka ya kashe shi. Shiyasa babu wata shaƙuwa a tsakanin mu.
Jikin Aiman yana rawa ya kama murfi mota zai shiga karaf ya riƙe mishi hannu kana ya watsa min jajaye idanuwanshi, da babu komai cikinsu sai zallar ɓaci rai nima nawa ran a ɓaci yake na kalle shi a mugun fusace ciki tsawa na ce "Dallah malam! Cika min yarona mu tafi nagaji da wannan wulaƙanci naka.
  "Idan kina da ƙarfi ki zo ki karɓi shi a hannuna.
Yana ƙarashe magana ya ɗauki Aiman ya nufi motarshi dashi, yayin da na bishi da kallo baki buɗe akan idanuwana, aka saka mishi shopping bags ɗin shi har ma da keke da nake zaton na Aiman ne a motarsa.
Cikin wani irin fushi na ɓalle murfin mota na fita, tsabar raina a ɓace yake ko gabana bana gani, ina zuwa na buge gilashi motarsa da ƙarfi.
Engr Ameer ya saki murmushi dama yasan dole ta biyo ɗanta ya saukar da glass ɗin ya wani zuba min idanuwanshi, a fusace na ce "Wannan wane irin kalar hauka ne ya za ka ɗauke min yaro baya ka gama ɓata min lokaci?
"Idan kina so na ba ki yaronki ki shigo mota mu yi magana just five minutes.
"Idan naƙi fa?
"Ba zan ba ki shi ba.
"Shikenan na bar maka shi kai ta riƙo.
"Wasa ki ke yi Habibty nasan ba za ki iya tafiya ki bar shi ba yadda ki ka tafi a fusace nan haka za ki dawo.
Ya yi magana yana dariya, na juyo a wani kalar hasale na ce "Za ka ga wasa gani idonka.
Daga haka na juya na shiga motata a harzuƙe na yi reverse na halba ta kan titi da sauri shi ma ya tashe mota ya bi ta a baya, ta mirror na hango yana bina, na ƙudurta da na fita round zan tsaya na karbi yarona. Sai dai abinda yai mugun ɗaure min kai ya kusa ya sumar dani bai wuce rashin gani Engr Ameer ba. Kusan five minutes Ina zaune a mota babu shi babu labarin sa, kafin nagama mamaki ina ya tafi min da yaro wayana ya yi ringing, na buɗe jakka na ɗauka Mama ce ke kirana kasa ɗauka nayi har sai da kiran ya tsinke. Nai maza na dannawa numbershi call sai dai har wayar ta ƙarashe ringing bai ɗaga ba. A takaice sai da na jera masa kira goma jere da juna amma ɗan taliki nan yaƙi picking up. Abu kamar wasa ƙaramar magana ta zama babba. Cikin mutuwar jiki na buɗe mota na fito na gani koda ya yi parking nesa dani, kiran khamis ne ya shigo wayata tsaki na ja tare da yi disconnected duk da haka sai da ya sake kira, kusan kira biyar khamis yai min ina disconnected can kuma sai ga Baba ya kira ni anan kam ido ya rena fata don ban san sanda na fashe da kuka ba. Kira uku Baba ya yi min amma ban ɗauka ba. Na ƙudurta a raina muddin na haɗu da Ameer ya bani yarona wallahi sai nayi masa wulaƙanci da kaff a tarihin zamansa na duniya ba a taɓa yi masa makamancin sa ba. Sai naci zarafinsa sai na zagi ta uwa da ubansa. Zagin ƙare dangi zan masa.
Haka na shiga mota na sake komawa Seven stars mall, har ciki na koma na tambaye ma'aikatan wuri koda sun ga ya sake dawowa nemana, amsar da suka bani saura kaɗan zuciyata, ta buga a haka na fito na sake shiga mota sai gani na buge da bin titunan ina neman Ameer ina rera kuka ga baki ɗaya dabara ta ɓace min. Har na nufi hanyar gida sai ga Ya Haidar ya kira ni, ai kuwa da mugun sauri na saka signal na gangara gefen titi nayi parking, da azama nayi picking "Hello....Honeypie!
Ya Haidar ya faɗa cike da shaukin son sa'ili da ya ji nayi picking up, sai kawai ya ji na fashe mishi da matsanancin kuka, a firgici ya tashi tsaye daga zaune da yake "Subhanalillah! Jeeddah mene ne me ki ke yiwa kuka?"
Jin muryarsa kaɗai da nayi na ƙara ji wani irin mugun rauni a zuciyata domin shi kaɗai ne mutumin da a koda yaushe yake taimakona a duk sanda na shiga matsala ko damuwa ba tare da yaga laifina ba koda ya kasance ina da laifi ɗin.
   "Ya....Hai....dar.....Ai....man...
Na faɗa cikin sarƙewar murya domin kuka da nake yi bana wasa bane ambatar sunan Aiman ya ƙara masa tashin hankali "me ya sami Aiman?
"Ya ɓata Ya Haidar wani mutum ya tafi dashi bansan inda zan ganshi ba.
"Innalillahi wai'inna illahim raji'un! Hasbunallahu wal-imal wakil! Jeeddah a gari ya ya Aiman ya ɓata?
"A Seven stars na je siya mishi ice cream shine ya ɗauke shi ya tafi dashi.
"Ke kuma kina aiki me har ya tafi dashi?"
Ya Haidar ya faɗa a tsawace alamar na bashi haushi ba kaɗan ba, gani haka sai kawai na ƙara wa kukana sauti, dama nasan abunda ya tsana kenan cikin sauri ya ce "Ya isa ki daina kuka ganina zuwa kina ina yanzu?"
"Ina kan titi sama Road.
"Okay ki jira ni anan kada ki ɗaga ko ina kina cikin wannan hali ba za ki iya driving cikin natsuwa ba.
"Uhmm!
Na faɗa tare da hanging up sai lokaci na ji zuciyata ta ɗan yi sanyi ko ba komai zan sami mai taimaka min.
Cike da tashin hankali Ya Haidar ya fito farfajiyar gidansu yana kwallawa direban Mommy kira da gudu ya zo "Rabi'u mu je ka kaini sama Road.
Haidar ya faɗa yana miƙa mishi key ɗin mota da high speed suka iso yana shiri kirana sai kawai ya hango ni tsaye jikin motata, ina juyawa naga Ya Haidar ya nufo ni da saurinsa, kasa jira nayi ya ƙaraso na kwasa da gudu na isa gare shi ina zuwa na faɗa jikinshi na ƙanƙame shi ina wani irin gunji kuka na fitar hankali. Bubbuga bayana ya shiga yi tare da faɗin "Banaso kuka nan Jeeddah ya isa in-sha-ALLAHU za a ganshi ina ji a jikina Aiman bai ɓata ba.
Sai gyaɗa kai nake yi kusan three minutes muna tsaye yana aikin rarrashina da kyar nai shiru ya cire ni daga ƙirjinshi ya riƙe min hannu muka nufi motata, sai da ya zaunar dani kana ya zauna a driving seat ba tare da ya tashi mota ba, ya kalle ni gaba ɗaya nayi wani irin zuru-zuru, idanuwana sun kumbura sutum. Cikin sanyi murya yake tambayana yadda Aiman ɗin ya ɓata gani hali da nake ciki babu saura wani ɓoye-ɓoye da zan masa, ciki sadda kai na bashi labari tun daga farko haɗuwa ta da Engr Ameer har kawo yau da zafin kai ya ɗebe ni na bar mishi Aiman tun sanda na fara magana Ya Haidar ya kafe ni da idanuwanshi bai taɓa ji haushi da takaicina irin yau ba. har baisan sanda ya finciko ƙafaɗata ya juyo dani na fuskance shi ya kifa min wani mugun mari zan iya cewa yau ne rana ta farko da hannu Ya Haidar ya sauka a jikina da sunan duka.

#Haidar Ka'oje
#Engr Ameer
#Jeeddah maishadda
#Aunty Bahijja
#Malam Haruna
#Hajja
#Team zazzafan kishi.
[8/22, 10:48 PM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

060

Ina dafe da kuncena nake kallonshi fuskarshi cike da wani irin kalar fushi wanda tsawon zamana dashi ban taɓa gani ya yi makamancin irinsa ba. Ya sake fizgo ni da ƙarfi tamkar zai ƙarya min kafaɗa cikin kakkausar murya yake faɗin. "Ashe ba ki da hankali Jeeddah?" ashe haukar naki har kai, ki saka rayuwar yaro ƙaramin cikin hatsari. Wannan wane irin daƙiƙanci ne? Halan babu ƙwaƙwalwa a kokon kanki ne Jeeddah?" Da za ki tafi ki bar ɗa da ki ka haifa da cikinki a hannu mutumin da ba ki sani ba.
Sake fashewa da kuka nayi cikin muryar kuka na ce "Wallahi Ya Haidar a lokaci raina ne yai mugun ɓaci shiyasa amma na rantse da ALLAH bana nufi....
"Rufe min baki sakarya uwa kawai. Na rasa laifin me Aiman ya yi miki da ya cancanci wannan kiyaya daga gare ki. Watakila mutumin nan ko mai garkuwa da mutane ne ko kuma mai satar yara. Kawai dai zafin kanki ya ba ki, ki tafi ki bar mishi yaronki.
"Ya Hai.....
"Nace ki rufe min shiru banaso ji kalma ko ɗaya tak! Ta sake fitowa daga bakinki.
Dole na haɗiye kalamaina sai na ci-gaba da rera kukana yayin da Ya Haidar ya ci-gaba da babbaka min faɗa abunda ba halinsa ba. "Da kinsan bakyaso Aiman salwantar da shi za ki yi ta wannan hanyar dani kin bar min shi, saboda ina sonshi tamkar yadda nake so numfashina ban taɓa kallo Aiman a matsayin ɗa Bilal Shattima ba. Face ɗan da na haifa da jinin jikina, Jeeddah Aiman yaro ne mai shiga rai, yaro ne mai wata irin bawa wacce rashin kulawar ku daga ke har wancan nusari uban nashi ku ka kasa ganewa. Ga shi nan sanadi sakarcin ki, kin jefa rayuwarsa a hatsari.
Tsabar tashin hankali da Haidar ya shiga gaba ɗaya rigar jikinsa ta jiƙe da zufa ga wani irin hawa da sauka da numfashinsa ke yi a dalili faɗa da yake yi ciwon sa na ƙoƙari tashi da sauri ya ɓalle murfin mota ya fita, yadda yake dambe da numfashinsa ya ƙara linka tashin hankali da nake ciki da sauri na fito, na tsaya gabanshi tare da ƙoƙari riƙe mishi hannu da wani irin zafin nama ya janye hannunsa gami da nuna ni da yatsa yana sauke numfashi ɗaɗɗaya ya ce "Kar kuskura ki sake yunƙuri taɓa ni.
Wannan kashedi da yai min yasa ni dole matsawa nesa dashi ina shasshekar kuka. Mun ɗauki lokaci a tsaye kafin ya samu daidaituwar numfashinsa. Ba tare da ya kalli gun da nake ba ya ce "Shiga mota mu tafi police station gara mu yi gaggawa kai musu report.
Da sauri na zagaya na shiga domin ni yanzu Ya Haidar ya dasa min tsoronsa. Mun kusa isa police station sai ga Engr Ameer ya kira wayana, jikina yana rawa gami da wani irin bugawar zuciya na kalli Ya Haidar muryarta yana cracking na ce "Ya Haidar shi ne yake kira. Da sauri ya ce "Yi maza ki yi picking kuma ki saka wayar a handsfree. Da kuwa sauri na bi umarninsa gaba ɗaya muryar Ameer ta karade cikin motar "Hello....My Habibty nasan zuwa yanzu nayi magani wannan tsiwar taki, ko ba haka ba Habibtynaaaa?"
Ya wani ƙarashe magana yana jan sabon sunan da ya laƙa min.
Wani irin kuka ya subuce min cikin muryar kuka na ce "Don  girman ALLAH Ameer kada ka cutar min da yaro ka faɗa min me ka ke buƙata gare ni amma don ALLAH ka dawo min da Aiman ɗina.
Haidar ji yake kamar ya finciko wayar ya ɗuɗɗura mishi ashar amma kuma sai yake gani da zarar ya yi magana watakila zai katse kiran, shikenan sun rasa Aiman shiyasa ya shiga kokari danne fushinsa, saboda haka sai wani irin huci yake yi tare da fesar da zazzafar iskar daga bakinshi.
   "Ni fa Habibty ba wani abu nake buƙata mai yawa daga gare ki ba kuma ni ban yi garkuwa da yaronki ba asalima kece ki ka yi fushi, ki ka bar min shi ni kuma tun daga kallo ɗaya da nai masa ALLAH ya dasa min ƙaunarsa a zuciyata, wallahi-azim Maijiddah ko akuya ce ta kasance mallakin ki ba zan iya cutar da ita ba balle ɗan da ki ka haifa da cikinki. Ashe idan na cutar da Aiman soyayyar da nake miki ba ta gaskiya bace.
Ɗagowa nai na kalli Ya Haidar ya maka min wata kafira harara, da sauri na kauda fuska na sake cewa "To idan abunda ka faɗa gaskiya ne Ameer ka faɗa min inda ka ke na zo na karɓe shi wallahi ina cikin tsanani tashin hankali.
   'yar dariya ya yi tare da faɗin "Ai nasani dole ki shiga tashin hankali Maijiddah da gangan na tafi domin na hora ki koda gobe kin yi fushi ba za ki sake yunƙuri bari yaronki a hannun stranger. Ko ba haka ki ka kira ni dashi ba?"
Ban sanda na sake fashewa da kuka ba ina faɗin "Na tuba ba zan sake ba Ameer ka rufa min asiri ka faɗa min inda ka ke kada ka zama silar bugawar zuciyata.
"Okay...naji zan faɗa miki amma banaso na sake ji ki ambaci bugawar zuciyarki. Ki duba inbox ɗin wayarki tun ɗazu na turo miki da address ɗin gidana.
Ya ƙarashe magana yana dariya ƙasa-ƙasa da sauri na yanke kira na duba naga one new message almost one hour ago da ya turo shi, da ƙarfi Ya Haidar ya fincike wayar ya karanta address ɗin, rai ɓace ya ƙara taka mota, a maimakon mu nufi police station kamar yadda ya ƙudurta tun farko sai naga ya sauya hanya. A rikice na kalle shi da firgitattu idanuwana masu cike da zallar tsoro muryata tana rawa na ce "Ya Haidar akwai hatsari mu tunƙare shi, mu kaɗai Why not mu fara zuwa police station?"
Kafin ya amsa min sai da ya zuzzuba min harara kana cikin zallar takaicina ya ce "Ke wacce irin mahaukaciya ce? Wato kanki kawai ki ka sani bakya tunani wane irin hali Aiman yake ciki. Idan muka je police station kafin su gama daukar statement, wani ɓata lokaci ne. A shirye nake da na tunƙare wannan mutumin komai hatsari sa muradina nai ido huɗu dashi.
Gaba ɗaya jikina ya yi mugun sanyi nasani Ya Haidar yana ƙaunar Aiman sosai yana bashi kulawa ta musamman fiye da mahaifinsa Bilal Shattima da yake Bilal irin mutane nan ne da ba su damu da 'ya'ya ba. amma ban taɓa tsammani ƙaunar da yake masa tayi zurfi har haka ba.
Ikon ALLAH ne ya kawo mu ƙofar gidan da Ameer ya turo min da address sabuwar unguwa ce da babu mutane sosai, amma duk da haka Ya Haidar bai karaya ba. Kanshi tsaye ya danna horn maigadi ya buɗe mana gate Ya Haidar yana danna hanci mota a farfajiyar gidan muna hango Engr Ameer tsaye jingine jikin motarsa ga Aiman sabe a ƙafaɗarsa yana bacci. Ya Haidar ya taka wani mahaukaci brake cikin zafin nama gami da tafarfasa zuciya ya ɓalle murfin mota ya fito, kaitsaye ya dumfari Engr Ameer nima da sauri na fito na bi bayan shi, wani irin zubawa Haidar Ka'oje idanuwa Engr Ameer ya yi yayin da wani irin ƙololon takaicinsa mai haɗe da kishi suka ya tsaya masa a maƙoshi. Haidar yana zuwa abu na farko da ya fara yi, finciko Aiman da ƙarfi daga ƙafadarsa, juyowar da Engr Ameer ya yi cikin fusata Haidar bai tsaya wata-wata ba ya ɗauke fuskarshi da matsiyacin mari, har sai da ya dafe kumatunsa na hagu da ya mara yana ɗagowa a mugun fusace nima ina ɗauke shi da mari a ɓari kunce sa na dama sai kawai ya dawo da ganinshi kaina ya zuba min rinannu idanuwanshi yai wani kalar ɗage gira ni kuma ina masa kallo mai ɗauke da gundari tsana kafin na ƙyasta mishi yatsuna akan fuskarshi na shiga kashe mishi gargaɗi "Ina gargaɗinka da kakkausar murya daga yau daga rana mai kama da yau kada ka kuskure ka sake zuwa inda nake na tsaneka wallahi. Kai mugu ne baƙin azzalumi...
Kafin na ƙarashe magana Ya Haidar ya jawo ni ya miƙa min Aiman wanda tuni ya falka daga bacci da yake yi, sai rarraba idanuwa yake, kana ya maye gurbina ya tsaya gaban Ameer, ba za ka iya tantance tsakanin su biyu wanne yafi harzuƙa ba. Cikin matsanancin fushi Haidar ya kai wa Ameer nushi cikin sa'a ya same shi a hanci da yake Haidar ya fi shi tsayi wani irin mahaukaci zafi Ameer ya ji ya ziyarci shi a hanci, bai bari ya wartseke ba ya rama nushin sa, shi ma ya sami ya Haidar a chest, haba nan take ƙazamin dambe ya barke a tsakaninsu maigadin Engr Ameer ya iso da gudu ya dinga ƙoƙari raba su yayin da Jeeddah ta fashe da ihun kuka domin duk abunda yake faruwa ita ce sila, kururuwar da Jeeddah ke yi yasa mahaifiyar Ameer fitowa "subhanalillah! Waye kai da za ka shigo har cikin gidana ka kama yarona da kokawa?"
In ji Umma sa'ili da ta ƙaraso tare da ƙoƙari ɓamɓare Haidar daga jikin Ameer da kyar Umma da maigadi suka yi nasara raba su Umma ta fashe da kuka tare da ƙanƙame Ameer tasan halinsa da baƙar zuciya, zai iya aikata mummunan abu akan Haidar yayin da Haidar ya nuna shi da yatsa yana huci alamar gargaɗi "Wannan shi ne kashedi na farko kuma na ƙarshe da zan maka ka fita harka iyalina idan ba haka ba na rantse da ALLAH kotu ce za ta raba mu. Banza baƙin jahili.
Ameer ya yada ganinshi akan fuskar Haidar ga mamaki Haidar sai yaga ya sakar mishi wani ƙazamin murmushi ya ce "Sai dai ka yi haƙuri domin zuciyata ta riga ta nutse a kogin son matarka, idan duk mutane duniya za su taru akaina ba zan daina sonta ba. Ina mai tabbatar maka komai dare daɗewa sai na cika burina akan Maijiddah idan Ameer ya ce yana son abu kasani duka da zagi ba sa tasiri akansa ko na juya baya sai dai ma su daɗa ƙara min ƙaimi. Wannan duka da ka yi min ba abunda ya rage min daga cikin soyayyar da nake wa matarka, sai ma ƙara min sonta da ya yi.
Wani irin ture Ameer ummanshi tayi tare da kifa mishi mari, tsabar takaicinsa da gama lulluɓe ta kasa magana sai kawai ta zuba mishi idanuwanta da suka take fidda kwalla.
   Wani irin zubura Haidar ya yi da nufi sake tunƙarar shi da sauri Jeeddah ta sauke Aiman ƙasa ta riƙe shi "Don ALLAH Ya Haidar ka yi haƙuri ka zo mu tafi in yaso gobe mu kai wa 'yan sanda report gwada ka bari hukuma ta ɗauki mataki akanshi, domin wannan da ganinsa mugun criminal ne.
Ba don Haidar yaso ba ya kyale shi sai don kukan da Aiman ya fara yana rirriƙe shi kamar yadda yaga Jeeddah tayi, duk da haka sai da ya nuna Ameer da yatsa cikin kakkausar martini ya ce "To shikenan idan har ka cika cikakken ɗan iska ka bari na sake ganinka kusa da matata na rantse da ALLAH sai dai uwarka ta sake haifar wani ba kai ba. Ya ƙarashe magana a matuƙar fusace kana ya sunkuce Aiman ya nufi mota da gudu Jeeddah ta bi su a baya da ƙarfi ya ja mota yayin da maigadi ya danna da gudunsa ya buɗe masa gate. Ameer yana cika yana batsewa ya nufi entrance ɗin gida yana wani kalar sauri kamar zai tashi sama, umma ta bishi tana kira sunan shi "Ameer! Ameer! Ameer na ce ka tsaya ka saurareni ko kuma ranka ya ɓaci.
Ameer ko waigo wa bai yi ba ballantana Umma tasa ran zai saurare ta. Yana isa cikin parlor Umma tana kama rigarsa ta baya ta jawo shi da karfi, cikin wani irin mugun fushi ya juyo tamkar zai kai mata bugu kana cikin tsawa da hargowa ya ce "Ki rabuda ni Umma ki tafi ki bani wuri bana so gani kowa kusa dani Maijiddah kaɗai nake so, dole na mallaki Maijiddah Umma koda hakan yana nufi zan kawo ƙarshen numfashin wancan ɗan iskan mijin nata.
Yana dasa aya a zance sa Umma tana sake ɗauke shi da tagwaye maruka. Sannan kuma ta fashe da matsanancin kuka, cikin sauti kuka take faɗin "Ameer ka natsu kasan irin maganganu da suke fitowa daga bakinka. Kada ka jefa rayuwarka a hatsari, wannan wane irin toshewar basira ne ya same ka na son matar aure? Haba Ameer wannan wane irin son zuciya ne? Ka bar yarinya nan ta zauna lafiya da mijinta Idan har ni na haife ka Ameer a karo na biyu ina ƙara gargaɗinka ka fita sabgar Maijiddah. Ka yi gaggawar cire ta daga zuciyarka.
Umma tana ƙarashe magana ta juya ta nufi ɗakin bacci ta zuciyarta na mata wani irin zogi, tasan duk wannan abu da Ameer yake yi ba yin kansa bane ciwo da yake ɗauke dashi ne ke sa shi aikata abubuwa da hankali ba zai ɗauka ba.
Yadda Haidar ke sharara gudu akan titi za ka zaci cewa don shi kaɗai aka shimfiɗa shi. Inaso nai masa magana nace ya rage gudu amma ina jin tsoro saboda haka sai ƙara ƙanƙame Aiman nayi koda muka iso ƙofar gidanmu 10:33pm daidai sai wani irin bugawa ƙirjina ke yi ina cike da fargaba haɗuwar da Mama da Baba baisan irin amsar da zan basu ba ina nan ina tunani har Ya Haidar ya fita ya buɗe gate ya dawo ya shigar min da motata ciki, kana ya fito ya buɗe side ɗin da nake zaune nayi zugun gaba ɗaya na dawo kalar tausayi, ya ɗauki Aiman daga jikina ya nufi cikin gida na bishi da kallo kafin na sauke naunanye numfashi, kana na fito tare da kule mota Cikin mutuwar jiki na bishi a baya kamar kazar da kwai ya fashewa a ciki ina zuwa tsakar gida na tsaya cak! Sakamakon muryar Mama da naji tana sallati gami da tafa hannuwa "To wai a gari ya ya Aiman ya ɓata?
Sai kawai na ƙara baza kunnuwana na ji wacce amsa Ya Haidar zai bata kusan gogan naku miskili ne maganarsa can ƙasan maƙoshi yake yi ta dole sai da na cire ƙafafuwana na nufi baƙin ƙofar shiga parlorn Mama na rakube, kana na ji abunda ya faɗa "A Seven stars mall ne ta je siya mishi ice cream Mama kinsan hali Aiman da ƙiriniya sai da ya bari hankalin Jeeddah ya dauku ya sace jiki ya fita daga cikin mall ɗin.
  "A'ah! Aliyu kawai dai kana ƙoƙari kare Jeeddah ne kawai amma kowa yasan halinta na sakaci da sakaryaci.
  "Mama ba kare ta nake yi ba hakikanin abinda ya faru ne, na faɗa miki.
"Ni fa Aliyu duk abinda za ka faɗa ba zai sa na daina ganin laifinta ba. Babban takaicina da Jeeddah bata tsira shegen yawonta na tsiya sai taga yamma tayi liss! Sai ka gannta tafe da jakka sai kace jikar wanzamai tana wani maƙe murya tai min daɗi baki ta fita. To wallahi bari ta shigo daga yau na soke fitar yamma, ba don da ALLAH ya takaita mana wahala ba aka ga yaro nan ciki sauki da yanzu ta haifar min da hawan jini.
"Kin ga Fatee kada ki bi ki daurawa yarinya nan laifi shi fa tsautsayi idan ALLAH ya kawo shi ba wanda ya isa ya hana, kamata ya yi ki godewa ALLAH da yasa aka ganshi.
Baba ya faɗa cike da so kawo ƙarshen mita Mama.
Ƙarfaffiyar ajiyar zuciya na sauke ina ƙara godewa ALLAH tare da Ya Haidar da ya kare ni da bai faɗi takamaiman abunda ya faru ba da yau na shiga uku don mai hana Mama ta ci ƙaniyata sai ALLAH.
Ina ji Ya Haidar yai musu sallama zai wuce gida sai na ji Mama ta ce "To wai ita Jeeddah ina ta tsaya ne?
Kafin Ya Haidar ya bata amsa nai wuff na faɗa ciki parlor, ina faɗin "Gani Mama.
  "Auu.... laɓe ki ka yi mana.
Na kasa magana sai kawai na sadda kai ƙasa Ya Haidar ya miƙe yana faɗin "Ni zan wuce sai da safen ku Baba.
"Sai da safe Aliyu ALLAH ya tsare ya kai ka gida lafiya.
Baba ya faɗa ina gani ya fita nai wuff na bi shi ina faɗin "Mama bari na bashi key ɗin motata saboda bai zo da mota ba.
Gudu-gudu na bishi a baya gami da kwalla masa kira "Ya Haidar! Ya Haidar tsaya ka karɓi key.
Ya tsaya ba tare da ya juyo ba na ƙaraso kusa dashi sai ina kallonsa  naga yadda ya murtuƙe fuska babu annuri ko misƙara zarrati akanta, nai sauri miƙa masa key ɗin ya fizge shi da ƙarfi ni na buɗe masa gate ya fita ina kokari yi masa godiya ya ja motar da kafiri gudu ya barni tsaye da baki buɗe. Can kuma na taɓe baki a fili na furta "Can ta matse ma mai baƙar zuciya.
Na maida gate na rufe kana na wuce cikin gida kaitsaye ɗakina, na shige na cire kayan jikina nayi wanka har bacci ya fara fizgata na ji ringing ɗin wayata ina jin ringintone ɗin nasan Bilal Shattima ne mai kirana saboda special ringintone nasa masa. Cikin kasalalliyar murya nai mishi sallama a maimakon ya amsa min sallama da nai masa sai kawai na ji ya rufe ni da faɗa "wannan wane irin wulaƙanci ne Jeeddah? Ya za ki ce khamis ya zo sai da yazo kofar gidanku ya kira wayarki ki ka ƙi picking ya aika yaro a kira ki aka ce kin fita.
"Uhm! Wallahi Love kana da muguwar matsala da kasan abinda ya faru dani a yau ɗinan da sai ka tausaya min.
Jin abunda ta faɗa yasa shi sassauto wa daga fushi da ya hau ya ce "Subhanalillah! Me ya faru dake love wallahi ba ki ji yadda gabana ya yi mummunan faɗuwa ba?
Na kwashe irin karya da Ya Haidar ya shimfiɗa wa su Mama na faɗa masa ya nuna alhininsa a fili sai kuma ya sake dauko min zance khamis.
   "Jeeddah ni fa so nake Baba yasan da zaman khamis kafin ya turo da iyayensa.
"Wannan ba abin damuwa bane Love zan kira shi gobe ya zo, kafin ma ya zo zan faɗawa Baba yasan da zuwan nasa.
  "Shikenan Love ALLAH ya kai mu gobe.
"Amin!
"Love!
"Na'am Love!
Na amsa mishi ina narkar da murya.
Haka da tayi ya ƙara rura wutar abunda Bilal Shattima ya ke ji akanta.
  "Love Please ki kunna Data mu yi video call kinsan kwana biyu nan bana gane kanki ba ki ga yadda nayi rama ba duk tumbin nan nawa da ki ke complain ya ɓace fatt!
Yana ƙarashe magana na kwashe da dariya cikin shagwaɓe murya na ce "Kai love anya kuwa wannan maganar taka gaskiya ce?
  "To ki buɗe Data ki gani da idanuwanki.
Ina dariya na katse kira kana na kunna data jim kaɗan kiran shi ya shigo da alama already yana online, sai da na ƙara gyara kwanciyata kana nai picking up, idanuwana suka sauka akan mummuna fuskar nan tasa daga shi sai farar vest a jikinshi. Wani irin mushriki kallo yake min ni kuma na ɗage girar ido ina wanke shi da ƙayatatce murmushi.
   "Love a kullum ƙara kyau ki ke yi kalli yadda ƙirjinki ya ƙara ci-cikowa kamar balan-balan fatar jikinki sai glowing take yi, wallahi har tsikar jikina ya fara zuba Love kin yi bala'i tayar min da hankali fa.
Bilal Shattima ya faɗa cikin wata 'yar iskar murya yana kashe min farara idanuwanshi. Ƙara faɗaɗɗa murmushin kan fuskata nayi tare da yi fari da idanuwa ina faɗin "Ba wani nan koda ma na tayar maka da hankali kana da wurin zuwa da ka ci-gaba da jin sauyi a jikin ka kashe min waya za ka yi ka je ɗakin matarka ku kashe fitila.
Na ƙarashe magana cikin azababben kishi.
  "Mtssss! Don ALLAH Love idan ina maganar akanki ki daina sako min zance wancan sokuwa mata, abunda ba ki sani ba wallahi Nusaiba bata da ni'ima ko kaɗan gaban nan nata a bushe yake ƙamass! Ga ɗan banza abun nata a wage kamar ƙofar kasuwa duk da fa kullum cikin shan kayan mata take ta sha wannan ta cusa wancan, ta lashe wannan amma duk a banza, kana jefa guga sai da ka ji zudum!
  Ai bansan sanda na fasa wata uwar dariya ba yana tayani sai babbaka dariya muke yi sai kace waɗanda suka shuka abin arziki.
Daga nan muka buɗe shafi hira duk rabin hirar ta mu zagin Nusaiba ne yake yi, musamman da ya fahimci hakan yana sa Jeeddah nishaɗi sai ƙara aibanta Nusaiba yake yi.
Su Bilal Shattima an shagala sosai sai suburbuɗo zance yake yi, ga wani shaƙiyi murmushi shimfiɗe akan munafukar fuskarsa.
Abunda bai sani ba tun lokaci da ya fara waya da Jeeddah Nusaiba take tsaye jingine da ƙofa kasancewar kofar a buɗe take shiyasa bai ji shigowarta ba.

#Bilal Shattima
#Haidar Ka'oje
#Jeeddah maishadda
#Nusaiba
#Aiman Shattima
#Team zazzafan kishi.
[8/24, 9:19 AM] My Number: *💥ZAZZAFAN KISHI....!*         _{Sabon Salo}_

*FREE BOOK.*

Na Jeeddah Aliyu

Wattpad-jeedddahaliyu

©HWA

*Ga masu buƙatar a tallata musu hajar su cikin farashi mai sauƙi kindly contact me on my cell phone number 07032566172*

_*Gare ku masoyana ma'abuta karantar litattafai na ga wata dama ta same ku da za ku karanta littafai na complete documents har guda uku a cikin farashi mai sauƙi gaske dukka littattafai na guda uku akan ₦700 littafan sune kamar haka*_
*AZAAD JUNAID*
*GIDAN RINA*
*DA BANSAN ASALINTA BA*

_Ga masu buƙatar guda ɗaya tak_

Azaad junaid ₦300
Gidan Rina ₦300
Da bansan asalinta ba ₦250

061.

Wasu zafafan hawaye suka fara bin kumatun Nusaiba. Jeeddah ta zame mata masifa da bala'i tayi danasani fitarta daga gidan Bilal Shattima da tasan rabuwar ta da Bilal masifa zai zame mata da bata goyi bayan Hajja da Aunty Bahijja suka fitar da ita ba.  Ita kam bata taɓa gani masifa irin wannan ba, ka saki macce saki har uku kuma ka dawo kana bibbiyar ta. Ta kai ta kawo yanzu ko kallon arziki bata ishe Bilal ba. Da ya dawo daga aiki zai shige ɗakinsa yana waya da Jeeddah idan tayi magana ya rufe ta da zagi. Magani da suka karɓo wurin bokansu bata ga amfaninsa ba. Gani ma take yi kamar ƙara rura wutar soyayyar Jeeddah ya yi a zuciyar Bilal. Duk yadda Nusaiba taso ta juya ta bar ɗaki ba tare da ta tankawa Bilal ba zuciyarta taƙi bata haɗin kai, wani irin masifaffen kishi take ji yana taso mata musamman da ta tsikayi muryar Jeeddah tana faɗin "Ni dai gaskiya Love koda ALLAH ya ƙaddara dawowa ta gidanka ba zan zauna da wannan shegiyar matar taka ba. Gara tun da wuri ka sani don kar sai na dawo ka, kawo min ƙamli da ba'adi.
   "Haba Love yaushe zan bari haka ta faru to uban me take tsinana min da zan ci-gaba da zama da ita? Kina gani macce da zubin taɓarya babu shape ba gaba ba baya. Wallahi Love idan ki ga nonuwan Nusaiba sai ki yi amai gaba ɗaya sun yamushe sun yi wani laga-laga sai azabar tsawo kamar igiyar shanya za ki zaci yara goma ta shayar alhali ko ɓatan wata bata taɓa yi ba.
   Na kwashe da wata irin mahaukaciyar dariya har ina dafe ciki, tsabar dariya ƙeta da nake yi har hawaye ke fita daga idanuwana.
Yayin da gogan naku ke taya ni kamar daga sama ya ji kukan Nusaiba daga bayan shi ya juya da sauri, nan take na haɗiye raguwar dariyata nai wani kici-kici da fuska a matuƙar fusace Nusaiba ta ƙaraso ta shammace Bilal ta fizge wayar hannunsa sai da ta yada ganinta akan screen ɗin wayar muka haɗa ido tai min wani baƙi kallo kana ta dubi jikin bangon ɗaki ta maka wayar nan take wayar tayi tararratse kana dawo da ganinta kan fuskar Bilal ya saki baki da hanci yana kallonta "Kai wane irin jahilin mutum ne Ya Bilal? Ina matsayin matarka ta sunnar ma'aiki za ka dinga aibanta ni tare da karuwa wac.....
Saura kalaman ta suka ƙargame a maƙoshinta sakamakon kafiri mari da Bilal ya ɗauke ta dashi, kafin ka ce kwabo ya rufe Nusaiba da ɗan banzan duka sai da ya yi mata liga-liga ya ja ta tamkar kayan wanki ya watsa ta waje ya maida ƙofar ɗakinsa ya rufe sai wani uban haki yake yi uban tumbin sa yana sama da ƙasa sai kace mai ciki wata tara.
Ta ɓangare Jeeddah tana gani vid call ɗin ya yi disconnected ta kuma san aikin Nusaiba ne sai kawai ta kece da dariya sai da tayi mai isarta kafin ta gyara kwanciyarta. Duk duniya ba abinda yake min daɗi ya saka ni nishaɗi irin naga Bilal Shattima da matarsa Nusaiba, suna rikici. Na sha alwashi ba zan taɓa bari Bilal ya zauna da wata 'ya macce ba ni ba. Tun da mahaifiyarsa da 'yar uwarsa suka haram ta min zama dashi shi ma ya haramta da zama da kowacce macce da suna zaman aure.
Washegari da wuri na tashi ni na yiwa Aiman wanka na saka mishi uniform kasancewar motata tana wurin Ya Haidar, dole sai adaidaita na hau na kai shi school ina dawowa na shiga wanka nai shiri tafiya office. Sai da na biya parlorn Baba na gaida shi anan ma na tarar da Mama nai musu sallama, ina fitowa gate Ya Haidar yana tsayawa da motata ko kaɗan banso haduwa dashi ba. Saboda abinda ya faru jiya, na kasa ƙarasa wa wajensa sai da ya yi min horn jikina a sanyayye na nufi motar na buɗe front seat na zauna daddaɗa ƙamshin turarensa ya bugi hancina, cikin sanyi murya na ce dashi "Ina kwana Ya Haidar?"
   "Lafiya!
Amsa min a gajarce yana wani tamke fuska, ya ja mota tafiyar kurame muka yi tun daga gaisuwa daga ni har shi ba wanda ya ƙara furta uffan. Gara ma ni ina satar kallonshi, shi kam ko sau ɗaya bai kalle ni ba har muka iso wurin aikina ya yi parking a maimakon na fita sai na gyara zama da nufi na bashi haƙuri sai kawai ya daka min wata irin gigitatciyar tsawa "Fita!.
Unexpected na ji saukar tsawar a kunnena shiyasa nai bala'i razana jikina ya ɗauki rawa hannuna yana kakkarwa na buɗe murfin mota na fita, ya wani fizgi motar da ƙarfi ya nufi gate ɗin fita, na bishi da kallo. Na taɓe baki na wuce office ɗin mu kasancewar mu haɗu ne a office ɗin mutum biyu na tarar a ciki muka gaisa. Na nufi desk ɗina na zauna kana na buɗe computer dake sama, na fara gudunar da aikina. Misali ƙarfe 12:00pm sai ga kiran Bilal Shattima ya shigo wayana bayan nayi picking up yake gayamin yana waje yana jira na, ban yi mamaki zuwansa  ba saboda ya saba zuwa ofishin nawa, sai da na rufe computer ɗin na ɗauki handbag ɗina, na fito wajensa na buɗe mota na shiga muna haɗa idanuwa na shiga ƙunshe dariya harara ya watsa min yana faɗin "Wato kin ma mayar dani madari ko Love?
     "Ai dole nayi dariya Love don na tabbata jiya gimbiya Nusaiba bata barka ka runtse ba.
Na ƙarasa magana ina sakin dariya da nake ƙunshe wa. Taɓe baki ya yi yana murmushi ya ce "Wace ce ita da har za ta hana ni bacci? Ta dai fasa min waya na kuma yiwa shegiya dukan tsiya da sassafe ta daka yaji yanzu haka tana gidansu Baffa da Hajja sai kirana suke yi yanzu ma can na nufa, na ce bara na biyo na fara gani sanyin idaniyata.
  Nan take na ɓata rai don na tsani tarayya shi da Nusaiba ba kaɗan ba ni fa na matso ya kawo ƙarshen aurensa da ita. Yana gani yadda na ɓata fuska ya bi ya ruɗe "love lafiya naga mood ɗin ki ya canza? Dan ALLAH ki faɗa min mene ne kinsan ba abunda na tsana sama da ɓacin ranki?.
   "Love na gaji da zamanka da Nusaiba idan har da gaske kana sona kana so farin cikina Love ka kawo ƙarshen zamanka da ita.
Murmushi ya sakar min tare da kama hannuna ya haɗe da nashi "Haba love idan wannan ne ki daina bata ranki nima na gaji da zama da ita gara mu rabu kowa ya kama gabansa dama can ba mu dace da juna ba. Hajja da Aunty Bahijja ne suka matsa min har na aureta.
   "To Dan ALLAH Love zama me take da igiyoyin aurenka?"
Sai da ya sumbace hannuna kafin ya ɗauko jotter da biro yaga falle ɗaya ya ɗura akan jotter ɗin ya damƙa min, yana kallon ciki idanuwana ya ce "Duk abunda na faɗa ki rubuta min a takarda nan.
Zaro idanuwa nayi ina shirin buɗe baki nai magana ya ɗura yatsanshi akan lips ɗina gami da ɗaga min gira ya ce "shhhhhh! Don't ask just write what I'm saying. Ni Bilal Ibrahim Shattima na saki matata Nusaiba
Sai kuma ya tsaya tare da kallona kamar mai tunani kafin ya ce "Love ai saki uku ne Hajja tasa nai miki ko?"
To ita ma saki uku za mu yi mata ko ya ki ka gani?
Ina wani shegen blushing tamkar wacce aka yiwa bushara da gidan aljanna, cikin shagwaɓa na langwaɓar  da kai na ce "Love ayi haka kuwa kodai mu yi mata biyu?
   "No...No...uku za mu yi mata idan muka yi mata biyu akwai raguwar guda ɗaya Baffa zai iya cilasta ni na dawo da ita, kuma kinsan an ce igiya ɗaya tsawon rai ne da ita.
  "En! Kuma fa haka ne gaskiya gara mu yada kwallon mangwaro mu huta da ƙuda.
  "Tsitsika su duka Love.
Bilal Shattima ya faɗa cike da shaƙiyanci yana wani ƙazamin murmushi.
Cike da zallar nishaɗi Jeeddah ta ƙarashe rubutun ta like takarda Bilal ya ciro white envelope daga gaban aljihun blue colour shadda dake jikinsa ya miƙawa Jeeddah yana faɗin "love saka mata anan mu ƙara karrama ta domin ba kowacce macce ce take da arzikin takardar saki a envelope ba.
Yana ƙarashe magana muka tintsire da dariya zuciyoyin mu wasai sai zuba fira muke yi muna kwasar dariya sabuwar wayarsa da ya siya da safiyar yau tai ringing sai da ɗago wayar ya nuna mi Hajja ce ke kiran shi kafin yai picking up sai da ya ɓata fuska cikin daurarriyar murya ce "Hajja na ce gani nan zuwa.  "To amma Hajja nima ba ki san irin muhimman ayyuka da ke gabana ba amma haka na jinginar dasu na taho.
"Tohm! Na ji.
Ya kashe wayar tare da jan siriri tsaki "Love bari na tafi muddin ba ganina Hajja tayi ba, ba za ta barni na huta ba kinsan tana jinyar Aunty Bahijja a asibiti mijinta ya lakada mata mugun duka har sai da ya kakkarya mata hannu da ƙafa sannan kuma ya damƙara mata saki uku. Shikenan Aunty Bahijja da Nusaiba sun yi anko Hajja kuma hawan jininta zai tashi.
Bilal ya faɗa yana murmushi abinsa
Cikin kaɗuwa na zaro idanuwa na ce "mijin Aunty Bahijja ya sake ta saki uku Dan ALLAH Love da gaske ka ke yi ko kuwa wasa ka ke min?
"Wallahi kuwa ya sake ta tun jiya na manta ne ban gayamiki bane satin ta ɗaya a kwace gadon asibiti sai jiya ya je, ya kai mata takardar saki.
Basan sanda na kurma ihun farin ciki ina faɗin "Wayyo ALLAH! Daɗi kashe ni aure Aunty Bahijja ya mutu ita ma ta zama bazawara kamar dai ni.
Dariya Bilal ya dinga yi min ya ce "Hakke ki ne yake bibbiyarta Love kaɗan ma ta fara gani.
Tsanani farin ciki da nake ji bakina ya kasa rufuwa. Sake kiran shi da Hajja tayi yasa muka yi sallama dole ba don ran mu yaso ba. Na fito daga motar har na fara tafiya da nufi komawa office na ji Bilal yana min horn na juya daidai ya fito daga mota na koma wurinsa ya miƙo min wayata da tsanani farin ciki da nake ciki yasa na mantawa da ita. Ina shirin juyawa Bilal ya shammace ni ya sakar min sumba a kamatuna, na dama. Hararashi nayi gami da nuna shi da yatsa ina murmushi kana na juya shi kuma ya ja motarsa ya tafi. Kamar an ce na juya hagu na, naga Engr Ameer tsaye a jikin motarsa ya kafe ni da masifaffun idanuwansa saura kiriss numfashina ya bar gangar jikina, ba ƙaramin kaɗawa hantar cikina tayi ba duk ƙoƙarina naso gani na, arce na kare sai da ya cimmin da wani irin ƙarfi ya damƙe damtse hannuna ya ja ni yana zuwa ya buɗe motarsa ya cilla ni ya rufe da wani mahaukacin gudu ya ja motar sai uban gudu yake sharara wa akan kwalta sai ka ce wanda zai bar gari motar har wani tsalle take tana tashi sama wani irin mugu tsoro ne ya lulluɓe ni domin gani nake yi kamar so yake ya wutsilar damu da alama zafin kanshi yasa ya manta da cewa rai ɗaya ne tak! Da an rasa shi, shikenan tunawa da hakan da nayi yasa na ankarar dashi cikin rawar murya "Ka ga  Ameer wannan haukar ya isa haka ka tsayar da motar nan na fita na fahimci baka so rayuwarka, to ni inaso tawa ka tsaya na sauka naceee!
Na ƙarashe magana cikin shouting.
Ko kaɗan bai saurareni ba. Ya ɗauki hanyar fita gari sai da ya shiga garin sifawa kana ya gangara gefen titi ya taka wawan brake har sai da na faɗo daga kan seat goshina ya buge dashboard. Ya kifa kanshi a steering Yana sauke zazzafan numfashi, yayin da ni kuma sai faman sassauke ajiyar zuciya nake yi tsawon five minutes muka ɗauka a haka kafin ya ɗago mahaukatan idanuwanshi masu masifar tsorata ni, ya watsa su akan fuskata nima tsare shi nayi da nawa idanuwa da babu komai a cikinsu sai tsoro da razanarwa. Cikin wata kalar murya ya furta "Wace ce ke?"
Zaro idanuwa nayi bansan sanda kalmar "What? Ta fito daga bakina saboda ba ƙaramin mamaki tambayar tasa ta haifar min dashi.
   "Yes! I want to know who you're.
"Mtss! Na ja guntun tsaki cike da takaici na kauda fuskata da bari kallonshi na fahimci ba ƙaramin ɗan reni wayau bane. Ni a tunanina ya daɗe da sani wace ce ni to da bai san ni wace ce ba miyasa yake bibbiya ta?
"Please tell me who are you?
Na tsikayi muryarshi dab da kunnena nai wani irin zabura na buɗe mota na fita, cikin wani irin sauri na fara tafiya ban wuce tako biyu zuwa uku ba ya sha gabana tare da ɗura min wata ƙaramar a gefen wuyana, cikin zare idanuwa ya daka min tsawa "Koma ciki mota ko yanzu nan na fizge jijjiyar wuyanki, ki mutu kowa ya huta.
Kalma nan da ya ambata yasa jikina ya shiga kakkarwa yawun bakina suka ƙafe ƙam! Gashi wurin da muke babu mutane masu wucewa da ƙafa sai dai motoci suma rabi duk matafiya ne domin da wani irin gudun tsiya suke wuce mu. Cikin harɗewar harshe na ce "Do....n...All...ah...Am...eer..ka....d..
  "Na ce ki wuce mu tafi.
Jikina yana rawa na juya yayin da bai ɗauke wuƙar daga wuyana ba. Ya buɗe ƙofa da hannunsa guda na shiga kana ya maida ƙofa ya rufe ya zagaye ya shigo, sake nuna min wuƙar ya yi ya ce "Ki yi magana Maijiddah ki fidda ni duhu ki dawo dani haske. Bansan wace ce ke bani da wata masaniya akanki, a makace na kamu da sonki. A farko haɗuwa ta dake nasani ke matar aure ce amma duk da kasantuwar ki matar wani na kuma san illar dake tattara da sonki da nake yi, amma a haka na rufe idanuwana na cigaba da sonki. A ranar da na ganki asibiti har na shiga ɗaki da ki ke na duba ki na tara da waɗannan maza guda biyu a tare dake wanɗada na kasa tantance miye alaƙarki dasu. Maijiddah kodai kina ci amanar mijinki da wasu maza ne?
Da sauri na girgiza kai hawaye na bin kumatuna domin asiri na yana dab da tonuwa.
"Ki buɗe bakinki ki yi min magana ai ke ba kurma bace balle ki dinga girgiza min kai. Ki faɗa min hakikanin gaskiya Maijiddah tsakani wannan dogo fari kyakkyawa da kuma gajere nan mummunan waye mijinki a cikinsu kowanne su na hango, matsananciyar soyayyarki a ƙwayar idanuwansa?" Wallahi idan ki ka yi min ƙarya na rantse da Ubangiji sammai bakwai ba za ki taɓa komawa gida ba.
   Wani irin bugawa zuciyata tayi kafin cikin rawar murya na shiga bashi tarihin rayuwata babu abunda na ɓoye masa gaba ɗaya na juye masa.
  "Auren kisan wuta! Maijiddah kin kuwa san miye hukunci auren kisan wuta a addini musulunci?
Harara na sakar masa da idanuwana dake tsiyaya hawaye na ce "wannan kuma matsalata ce nasani bansani ba wannan bai shafe ka ba. Ka dai yi min titse na faɗa maka abunda ka ke so ji dangane dani saboda haka ka tada mota ka mayar dani inda ka ɗauko ni.
   "Tsawon rayuwata ban taɓa ci karo da macce mai azababben so zuciya irinki Maijiddah. Wato daga ni har Haidar haukar banza mu ke yi akanki.
"Kwarai kuwa domin daga kai har shi ba wanda na taɓa furta wa kalmar ina sonshi ba. Gara ma shi Ya Haidar na taɓa sonshi. Shi yasa tun farko na ɓoye maka cewa bani da aure saboda nima ina da nawa muradi a ƙasan zuciyata, don haka ka fita sabgata ka je nemi mai sonka tun kafin dare ya yi maka.
  Wata ƙarfaffiyar ajiyar zuciya ya sauke yana kallona yana cizo lower lips ɗin sa, yai wani kalar girgiza kai ba tare da ya sake furta wata kalma ba kawai dai ya yi ƙwafa ya tadda mota. Kai tsaye ma'aikatar mu ya nufa dani tun daga nesa na hango Ya Haidar jingine jikin motata, yana dannar wayarsa wani irin mahaukacin bugawa zuciyata tayi, har bansan sanda na furta "Na shiga uku!
   "A'ah! Maijiddah ba ki gama shiga uku ba sai anan gaba idan ALLAH ya ɗura miki cutar son wani wanda babu ke a zuciyarsa a lokaci za ki shiga uku za ki ɗanɗani raɗaɗin azabar da muka ɗanɗana akanki. Abunda na fahimta a tattare dake kwata-kwata ba ki taɓa sani mene ne so ba. Kin aure Bilal Shattima on your own selfishness ba don kina masa cikkaken so na gaskiya ba. Komai naki cike da son zuciya ki ke aiwatar dashi karo na farko a rayuwata da naso abun da yake wahalar da ruhina. Amma hakan ba zai sa na haƙuri dake ba Maijiddah. Tun sanda ki ka faɗa min wacece ke na gama fahimtar tsagoro son zuciyarki ya zarce tunanina, sai kawai na ji a zuciyata ba zan taɓa iya haƙura dake ba. Saboda haka daga yau ni Ameer Bello Sardaunan na ɗaure damarar yaƙi neman aurenki har sai na mallake ki ko ta hali yaya. Na kuma godewa ALLAH da yasa sa'ili da nake neman kusanci dake ba ki da aure akanki.
Yana ƙarashe magana daidai ya iso kusa da Ya Haidar ya yi parking ya buɗe mota ya fito ya zo ya buɗe min ƙofa domin ga baki ɗaya jikina ya gama mutuwa kalaman sa sun ratsa jini da bargon jikina suka haifar min da wani kalar tsoro.
Kallo ɗaya Haidar Ka'oje yai musu ya ɗauke kai zuciyarsa na wani irin tafarfasa wani irin kishi mai haɗe da tsanar Jeeddah ya ji yana kokari mamaye masa zuciya.
  "Maijiddah ki fito mana don banga amfani zama da ki ke min a mota ba gara shi ma ki fuskance shi, ki faɗa masa farar gaskiya da ki ka faɗa min ki tsamo sa daga cikin duhu da ki ka tsamo ni. Ki faɗa masa cewa ya haƙura dake domin mallaki na ce ke.
Karo na farko a rayuwata da naji kunyar haɗa ido da Ya Haidar. Ko fahimtar hakan Ameer ya yi ne sai kawai ya saki murfin motar ya soma tattaki cikin wata irin tafiyar izza da taƙama ya nufi wurin Ya Haidar, yana zuwa ya miƙa masa hannu alamar su yi musabaha, sai da Haidar Ka'oje ya fesar da zazzafar iska daga bakinsa kafin ya miƙawa Ameer hannunshi "Ka yi haƙuri abokina ba wai ina ba ka haƙuri ne a bisa wani laifi da nai maka ba. Na baka haƙuri ne a bisa hali da ka tsinci kanka a ciki, na soyayyar Maijiddah gashi kuma a karo na biyu za ka sake rasa ta. Dukkan mu jirgi ɗaya ne ya ɗebo mu, muna hasashe ne ciki duhu amma ni Al-hamdulillah! Ta haska min haske na fita daga baƙin duhu da na daɗe ciki yanzu saura kai ya rage. Na barka lafiya Aliyu Haidar.
Daga haka Ameer ya saki hannu Haidar ya juya ya yi haka ne ya haddasa fitina a tsakaninsu, saboda ya fahimci irin tsanani soyayyar Jeeddah da kishinta a ƙwayar idon Haidar. Sai da ya dawo cikin motar sannan na sami kwarin gwiwa fitowa.
Tun sanda Ameer ya juya Haidar Ka'oje ya kasa ɗauke ƙwayar idanuwansa daga kansa yana auna maganganun sa a mizanin hankali har sai ya shiga motarsa ya kasa fahimtar inda maganganun sa suka dosa. Engr Ameer ya ja motarsa ya ƙara gaba kana Haidar Ka'oje ya dawo da ganinsa akan Jeeddah wacce ke tsaye ta sadda kanta ƙasa ji take kamar ƙasa ta tsage ta shige. A kallo ɗaya ba za ka iya tantance wane irin hali Haidar Ka'oje ya shiga ba kawai dai za ka ga idanuwanshi sun sauya daga farare zuwa jajaye.
      "Idan kin tashi tafiya gida ki zo mu tafi in kuma nai tafiyata ga key ɗin motarki.
Cikin wata irin murya mai cike da rauni Ya Haidar ya yi magana gami da miƙo min key kaina yana kasa na iso na buɗe front door na zauna tun daga yanayi kallo da Ya Haidar yake min hantar cikina ta kada, har muka iso gida bai ce min uffan ba. Yana yi parking ya fi ce da sauri daga motar nima da sauri na fito ina kwalla mishi kira "Ya Haidar Ya Haidar! Dan ALLAH ka tsaya ka saurareni abunda ka ke tunani ba haka bane wallahi babu komai a tsakanina dashi.
Ko waigo wa bai yi ba ballantana nasa  ran zai tsaya, jikina a sanyayye na shiga gida.
****************
Bilal Shattima yana zuwa gidan Baffa ya tarar da Hajja da Baffa haɗe da Umma mariya sai kuma Nusaiba dake fama da kumburarriyar fuskarta. Cike da wata irin izza ya zauna ya yi crossing legs ɗin shi, cikin rashin mutunci yake girgiza su, ba tare da ya gaida duk wanda ke cikin parlorn ba, ya yada ganinsa akan fuskar Baffa ya ce "Baffa ni fa bana buƙatar wani sulhu tsakanina da 'yarka saboda bata da tarbiyya ko kaɗan kuma ni ba zan iya ci-gaba da zama da macce da bata wadatu da tarbiyya ba. Don haka na gaji da zama da ita na sauƙe mata. Ba ma shi ba ai ban manta da kalar wulaƙanci da ku ka yi mana kai da 'yarka da matarka sanda na nuna ina so Nusaiba Hajja ta zo wurinka da suna a haɗa zumunci da budar bakinka ka ce ba za ka ba marar aiki yi 'yarka ba. Babu irin ci kashi da Nusaiba bata yi min ba sai gashi ALLAH ya haɗa ni da Jeeddah ta aureni duk da banida aiki yi. Sai yanzu da kaga ALLAH ya daukaka ni, ka shiga ka fita kai da 'yarka da matarka ku ka yi min asiri na aureta kasani yanzu na dawo hayyacina ka ga wannan envelope ɗin takardar saki 'yarka ce a ciki Baffa. Jeeddar nan da bakwaso ita nasa ta rubuta mata saki har uku, yana ƙarashe magana ya cilla wa Nusaiba envelope ɗin akan fuska ya fice abinsa. Yayin da a lokaci ɗaya Hajja da Nusaiba suka rushe da kuka Baffa ya dafe kanshi ba a taɓa ci masa mutunci iri yau ba. Umma mariya sai tsinewa Bilal Shattima take babu kalar zagi da ALLAH isa da ba ta yi masa ba.
**************
DA DARE.
Tun dawowar ta daga office da na shige ɗaki na kwanta ban ƙara fitowa ba. Wani iri nake ji kaina amma ko kaɗan ban ji zan iya fasa kudurina naso aure kisan wuta ba, zuciyata gaba ɗaya ta fi karkata akan Bilal Shattima fiye da Haidar Ka'oje ko Engr Ameer duk da shi Ameer ɗin ban saka shi a jerin masu lafiyar ƙwaƙwalwa ba. Lamarin sa ya fi kama da na mahaukata tuburan! Misali ƙarfe 8:40pm khamis ya kira ni yana ƙofar gidanmu, cike da kwari gwiwa na tashi daga kan pryamat ɗin na gama sallar isha'i na linke ta na mayar da ita mazaunin ta. Kana na fito kai tsaye parlorn Baba na nufa anan na tarar da Mama na runsuna tare da gaida su na nemi kusa da Mama na zauna yayin da zuciyata ke wani irin luguden aradu ina cike da fargaban abunda zai fito bakina na sadda kai ƙasa, duk irin faɗuwar da gabana ke yi bai sa na karaya ba cikin sanyi murya na ce "Uhm!.... Baba!Uhm.... Baba.
Gani yadda suka zuba min idanuwa yasa gaba ɗaya na daburce na rasa ta ina zan fara sai ambata sunan Baba nake yi.
   "Ya aka yi ne Jeeddah? Naga sai kiran sunana ki ke yi kuma kin kasa magana.
In ji Baba yana ƙara tattara hankalinsa akaina. Ta ƙasan ido na saci kallon gefen da mama take naga tana min kallo mai kama da na tuhuma. Sai da na haɗiye wasu tsikakku yawu masu ɗauke da sinadarin tsoro kafin na ce "Dama Khamis ne ya zo ku gaisa kafin ya turo da iyayensa.
   "Khamis kuma?
Mama ta faɗa daga gani yanayi da tai magana kasan a harzuƙe take, kana ta zarce da faɗin
"Shin ba tun ranar farko da ya fara zuwa gidanan nace ki sallame shi ba?" Ashe har yanzu kina tare dashi wai Jeeddah sai yaushe za ki yiwa kanki karatun ta natsu? Na fahimci soki ke ki sake kunyata mu a karo na biyu ko? To wallahi ba ki isa ba tun wuri ki faɗa masa kina da wanda za ki aura.
Kasa magana nayi sai musu-musu nake yi da baki. Baba ya gyara zamanshi sai dai shi ba za ka iya tantance yanayi sa ba a farat ɗaya ba. Domin shi mutum ne da ba kasafai yake bayyanar da ɓacin ransa a fili ba.
   "Jeeddah ki bi maganar mahaifiyarki, ki amince da Aliyu ko ba komai ya nuna miki ƙauna irin wacce babu algusu a cikinta.
Baba ya faɗa yana ƙara zuba idanuwansa akaina cikin sanyi murya na ce "Ni gaskiya Baba ba zan iya aure saurayi ba ina matsayin bazawara. Kuma fa akwai sa ranar wata akanshi idan na amince dashi tamkar ban yiwa wac....
Wawan bugu Mama ta kai min a baki babu shiri na haɗiye raguwar kalamai na, na dafe bakina da har ya feshe yana fidda jini ga wani irin zogi da raɗaɗi da yake min. Cikin tsanani fusata Mama ta fara zuba min faɗa "Ke har kin isa muna faɗa kina faɗa. Amma ba laifin ki bane Babanki ne yake goya miki a duk sanda ki ka yi yunkuri bijere mana. To amma ki sani muddin a karo na biyu ki ka bijirewa auren Aliyu wallahi Jeeddah babu ni babu ke har duniya ta naɗe ki a ranki ni ba mahaifiyarki bace na cire a jerin 'ya'ya da na haifa.

#Haidar Ka'oje
#Egnr Ameer
#Bilal Shattima
#Jeeddah maishadda
#Nusaiba
#Hajja
#Baba
#mama
#Team zazzafan kishi.
  

No comments