Recent Updates

Uncle J 9

 


By Kulsoom Ismail Idris

Page 9


ALHAMDULILLAH komai ya kammala mata fiya ake jira kawai tuni an nufi airport dauko su karfe biyu dai dai na rana aka wangale musu makeken get ahankali motocin suka silalo cikin harabar Gidan.

Sannu da zuwa Alhaji Baba Megadi da Baba Direba suke sake maimaitawa murfin Motar suka bude masa fitowa yayi fuskar sa dauke da Fara'a yake amsa musu min sameku lafiya lafiya lau Alhaji.

Su Mom fitowa akai ana karairaya ita me Miji gaba daya bata ita yakeyi ba Amma kawai yake hange ina zai hangota,cikin takunta na nutsuwa tafito tasha lullubi cikin shigar kamala sabanin Mom da tafi to haka gandai gandai bataji kunyar mazan da suke wajan ba,tuni kwalliyar da Mom take ganin ta caba ta dusashe tunda Amma tafito washe baki yayi yana kallon ta sosai yake kaunar matar tasa.

Duk wani bacin rai ya hadu ya ruftowa Mom ita kanta tasani ko Amma batai kwalliya ba bazata taba hada kanta da itaba bare kuma tai kwalliya jibi tsabar tozarci itace tafara zuwa amma bemasan ALLAH yayi ajiyarta awajan ba shiyasa tasha alwashin saita tar watsawa Amma farin cikinta,kamar yadda take tar watsa mata nata ako yaushe.

Murmushi ta sakar mai itama cikin kaunar Mijin nata sannu da zuwa Dady haka take cemai kamar yadda dan su yake kiransa tun yana karami yauwwa Uwar Gida sarautar mata kum Mom tasake kumewa kamar ta rufeshi da kuka dakyar ta iya danne abunda yake zuciyar ta.

Cikin Kissa da kisisina take fadin nifa banga My Son din nawa ba Dariya Dad yayi kinsan halin miskilancin dan naki saiya gama shan kamshi tukunna zai fito,um ashe haryanzu halin be canba Mom ta fada cikin Dariyar yake saima abunda ya karu cewar Dad.

Amma da kanta ta karasa gaban Motar daya hakimce kamar wani sarki ja tai tabude kofar lumshe idanu yayi bakaramin missing din Amman tasa yayi ba sosai yake kaunarta jini da tsoka itace bugun numfashin sa akoda yaushe.

Kafafuwan sa ya fara zurowa kamar wanda baya taka kasa har wani jini jini kake ganin ya kwanta akafar luf ga gargasa data cikamai kafa tana kwance luf luf.

Jalila fa ana can ana caba kwalliya dan itama karfa arainata aimata kallon yar kauye yau har wanka tayi sabi biyu ahakan bakaramin kokari tayi ba aganinta dan dai kawai ta kashe kala itama.

Hhhh taba su runduna Mamaki kamar yadda ta saka musu suna zata tabbatar babu wanda bai gigice saboda ganin wankan data dauka ba tana gaban madubi an gambaza hoda ansha jam baki jagira akaja har kunne cunku tagano a Fuskar Rufaida tadau alwashin saita yita aiko tsaf tacike girar ta da uban baki.

Tsagun mage ta fara jerawa dan aruwarta tana son tsagun mage har tsakiyar kuncinta ta kaishi bayan dige digen da Fuskar tasha jujjuyawa tai komai yayi cikin jindadi ta zuge buhun kayanta doguwar rigar da Amma ta dinkamata tasaka wadda ta mayan cewa tsabar nacin satan da take yi harta fara tsofewa  ta tattare.

Gwada irin tafiyar da zatai inta fita tai silifas dinta ta dauko ta dora shi akafar nan wow kai sai wanda yaga irin haduwar da Jalila tai abunma ai ba amagana.

🤣🤣🤣Fans naso kunga wannan wanka amma ku hasaso shi aranku tabbas har liki zaku manna mata.

Harabar gidan ta fito tana taku dai dai gawani Uban dauri data dan kwama akanta,dai dai lokacin daya fito daga mota adai dai lokacin sukai arba da juna wani ihu Jalila ta kwalla tare da zurawa a guje gadan gadan tayo kansa tana ihu da murnar ga dan Indiya ga dan India ALLAH y cikan burina naga dan India tuni aka dare kowa yayi ta kansa dan bakaramin firgita su Jalila tai ba yadda kasan damisa haka takoma.

🤣🤣🤣Tuni ya saki murfin Motar ya bawa hammata Iska amma ina Jalila tana biye dashi abaya tana cin gudun san takamo shi karya gudu batare data tambaye shi acikin film din da take kallo shikuma ya sunan sa,hhh shi gaba daya zuciyar sa tatafi a gamo yayi wannan ba mutum bace yarasa ma gane halittar macece ko Namiji.

Wani sufa Jalila tai saigata daraf ajikin Jalal jiyayi kamar numfashin sa zai dauke Jalila fa ta makale masa kamar kaska da kyar ya samu ya banbare ta kamar takadda haka yayi wulli da ita jikake kum ta bugu da kasa sai Lokacin ta dawo hayya cinta zumbur tamike kan Lokacin tuni ya samu wajan buya tsit kake ji babu kowa, kowa yayi takansa dan ma'aikatan gida babu wanda ya taba ganinta bare ya shaidata.

Cike da takaicin ya kufce mata tashiga parlour babu kowa sai karar AC dake tashi a parlour dakinta ta wuce tana cizon yatsa.

Amma ce take maida numfashi dafe da kirji Dad na kusa da ita da tunin me suka gani haka suke cin wannan uban gudu dan shi firgita ce tasashi gudu sam bega abunda akewa gudun ba dandai kar agudu abarshi ne bayadda zaiyi haka ya ware kafa ya dafe hularsa akai gudun tare dashi.

Waini gudumme kuka samu haka mekuka gani wanda ya baku tsoro,sauke numfashi Amma tayi haba Dady yanzu kai bakaga abunda muka gani ba wllh nidai damisa kawai nagani ta tunkaro mu shiyasa nai takaina tunkafin ta waiwayo ta ganni.

Cikin Mamaki yake kallonta damisa kuma agidannan kai gaskiya bakiga dai daiba Rukayya,au haka kace aida ALLAH ya nunama ita bazaka fadi haka ba, kingani ba wannan ba kizo ki sallameni yunwa nakeji to waima ina Jalal nifa banganshi ba.

Dafe kirji tai tashi tasahi muje mu nemoshi,mikewa Dad yayi tare suka fito suna karewa parlourn kallo babu kowa hatta Iya tasa sakata adakint tsit kake jinta.

      🤣🤣🤣🤣Kubiyo ni danjin ina Jalal yaje ya buya.

Mrs Baba Bello Abubakar

.........✍️✍️✍️✍️

No comments