Recent Updates

Uncle J 8


 Page 8

Kai tsaye part din su Rufaida ta nufa duk suna zaune aparlo sunyi jugum jugum Salima na kwance har Lokacin rike da kirji tana matsar kwallah damai da numfashin azaba.

Asslamu Alaikum ta rangada sallama kamar mutuniyar arziki haka ta sunkuyar dakai,ina wuni yame jiki ashe haka wannan abu ya faru to ALLAH ya kiyaye gaba kallon Salima tai sannu wai jikinne har yanzu kinga da akauye muke akwai masu kamun kirji aida ankaiki to Allah na tuba abune ma kamar jela taya za ai masa kamun fashewa tai da dariya.

Rufaida ce tamike afusa ce to dan ubanki komadai kece kika jajjefe su ba asani ba,wa ni karki dauramin jakar tsaba kaji su bini nida sai yanzu ma ake gayamin ga tsautsayin daya afkawa maman luku ke uban wace maman luku gatanan kuwa wannan aisedai akirata da maman luku na tabbatar wannan ta haifeni yasin nidaga yanzu ma Mama zan dinga ce muku.

Cikin fusata Rufaida ta biyo ta da gudu tai hanyar kofa tsayawa tai tana haki tana murguda musu duwawu tana musu gwalo harda su tafi tafara raira mata waka.

Maman luku me rababe rababe wacece me rababe rababe maman luku me rababe rababe,gaba daya mahaukata ta maida su, Mom kamar zata fashe tsabar tsanar da taiwa Jalila,saida Jalila tagama yi musu rashin kunya tsaf tukunna ta falfala da gudu ta koma part din su cikin nishadi da farin ciki.

Yau take Monday kuma ayau megidan zai duro kasa Nigeria kasarmu ta gado tare da babban dansa daya kammala karatun sa a America yau Gidan ba zama ko ina gyarashi akeyi girki kuwa kala kala haka aka shirya su.

Daga Amma har Mom kowa so take ta burge megidan nasu gyara akeyi tako ina yau Dad zai dawo su kansu su Iya ba abar su abaya ba dan sosai Dad yake musu alheri dole ne suyi farin ciki da dawowar sa.

Rufaida tarasa inda zata tsoma ranta yau sahibinta zai dawo agoge cen a mulke can wasu riga da wando ta saka wandon crazy ne sai riga body hop attached din kanta yasha gyara farata zako zako haka taje aka saka mata.

Mom sai kara gyare Rufaida takeyi dan dai kawaii yagani ya yaba takuma samu shiga duk wannan gyaran da sukeyi wanda akeyi bemasan da zaman suba sukadai suke haukan su.

Amma murna take kamar zata taka rawa sosai take mararin ganin tilon dan nata shi kadai ALLAH ya basu daga shi bata sake haihuwa ba.

Shiyasa Dad ba karamin ji yakeyi da shiba babu abunda zai nuna ya naso besa meshi ba matukar kudi yana siyan abun tofa zai narka ko nawane wajan siya masa.

Waini Iya suwane zasu dawo aketa wannan hada hada haka kamar wanda megari zaizo Dariya Iya tayi yo Allah natuba megari aikaramin alhakine keyanzu agarin ku inme gari yace zaizo gidan ku haka ake zama anata shiri,hmm tab to ai nagaya miki agarimmu ai saime matsayi megari zaije gidan sa har fadawa ne dashifa nasha yin lefi azo ace za'a tafi dani kafin azo nagudu.

Tab kice Jalila kin zuba fitina agarinku kibari kawai Iya kema karki mamakin kika shigo gonata na hukun taki nifa bana barin kota kwana har so nake atakale ni wllh jikina har kaikayi yake in nakwana biyu ba airigima dani ba,au harni ma bazaki kyale ba Jalila, kedai kawai kiyi Addu'a kar ALLAH yasa muyi arangama fada dani ba riba tasheke da Dariya tunawa da abunda taiwa Salima.

Dariyar me kike kuma uhm abardai kaza cikin gashinta kawai dan in aka figeta bazatai kyan gani ba,adai fige tan kowa ya ganta dan ubanta cewar Iya cike da san gulma dan arayuwar Iya akwaita dason tsogwami.Zan gaya miki amma bakin ki kisamai linzami inba haka ba zan dauki fansa akanki ato.

Cikin zakuwa Iya kefadin kinji nace zan fadawa wani kawai kifadamin kidaina jamin rai naimiki alkawarain babu wanda zan gayawa kima fada,saidata leka ta tabbatar Amma bata kusa sannan tajuyo yawwa ina rannan da wancan rindinar tai gamo da aljanu a wancan dajin, inane daji kuma inda wadan can bishiyun suke af lambu zaki ce to naji lambu to aini ce babbar aljanar zare idanu Iya tayi bangane ba yarnan ganar dani.

Karkace kai Jalila tai tafara bawa Iya labari tsuru Iya tai tana kallonta kai wannan yarinyar badai shedanci ba,yanzu dama kece kikai wannan aika aikar bayan tagama tikar Dariya amma kuma fa kin birgeni kinyi maganin yan iska bammu kashe Iya zamiyi tafiya tare dake a'ah Allah ya tsare ni da wannan iblishin naki zanci gaba da yamiki addu'ar fatan shiriya.

Koda daima ai dan megidannan tsaf zai dawo dake cikin hankalin ki imma ya gudu to zainemo miki shi wllh dan baya daukar wargi ko kadan kinga wadan can shirga shirgan su kan su tsoransa suke ji balle ke aba kamar abusheki kifadi,aini Iya wllh babu wanda nake jin tsoronsa da kowama zan iya karawa nan da kika ganni tokidai kama kanki wllh ina fada mikine karki jawo sanadiyyar da zaisa akaiki gadon asibiti.

Fashewa tai da Dariya ina tabbatar miki matsawar za akaini gadon Asibitin akan wani to kisa aranki tare za a kamu dan saidai muyi mutuwar kasko.

      Hmmm wannan cin alwashi haka Kubiyo ni Fans dan jin yadda za afara wasan yanzuma aka fara muje zuwa.

      Mrs Baba Bello ABUBAKAR

[7/28, 9:35 AM] +234 903 511 7917: UNCLE J

No comments