Recent Updates

Uncle J 50

 


Page 50


Kowa Zuciya ba dadi suka koma daki,Jalilah ce ta dube ta kuma ke yanzu Nasmah ruwan zakije ki debo mata? gyada kai tayi tsabar takaici ma ta kasa magana tabe baki Jalilah tai to saikije kitayi kidinga yiwa wata banza bauta wllh dani tasa dataga yadda ake iya iskanci da daga yau bazata sake sa kowa yade bomata ruwan wanka ba.


Yanzumma bazan kyaleta ba zamu gauraya wataran,shiru sukai dan aganin su Jalilah cika baki kawai takeyi suma sun sha wannan alwashin abaya kafin su zubda makaman yakin su.


Uniform suka cire tare suka sake fita Ismah ce ta rike boket din,duk inda sukaje uban layine wanda kafin azo kansu magariba zata iya yi yammata ne kala kala manya da madai daita wasu da riga da zani wasu sket kai watama daga ita sai daurin kirji warkajamin su suke kamar agida suke ammafa inkema jan wuya ce inko baki kaiba saidai ki koma gefe.


Sun zagaye kaf makarantar basu samu ruwa ba tuni Nasmah tafara kuka kashirfan dan Allah kadai yasan irin dukan da yaya Hauwa zatai mata,kowaccen su face dinta dauke da damuwa suke rarrashin ta,wai babu rafi acikin makarantar nan akwai mana amma wa zaiyi wanka da ruwan rafi kinji sanyin sa kuwa.


Tabe baki Jalilah tai to ina ruwan mu da sanyin sa mudai ba mukai mata ruwa ba ita tasani kuzo muje,tsayawa sukai babu fa wanda yake zuwa wajan kuma ga nisa ni kubani sai naje mene abunni sa,bayadda zasiyi haka suka bita.


Dan danan sukaje wajan nanne me nisa kuban nashiga na debo mika mata sukai babu tsoro ba komai tashiga ruwan saidata cika shi taf da ruwa sannan ta fito ji take ma kamar tai wanka aciki,kallonta kawai suke koda kudi baza su iya shiga wannan ruwan ba muje bayan ta dora bokitin aka.


Har kofar toilet ta kaishi sannan ta sauke ko minti biyu ba'aiba yaya Hauwa tataho sai hura hanci take yi masu tsoronta tuni suka sunkuyar dakai.


Ruwan ta kalla fari tas tas dashi harara ta wurga musu Allah ya temakeki da kika kawo akan lokacin dana kayyade miki dana zo naijiranki awajan nan saidai buzunki ku ware ni kubani waje,da sauri suka bar wajan amma banda Jalilah data tsaya rike da kugu.


Nan fa hankalin daliban yayi kansu ke da kika tsayamin aka uwar me kike jira bokitimmu zaki bamu tunda badaga gidan tsohuwa kikazo dashiba,dif wuta ta dauke wa hauwa tana maimaita kalaman Jalilah idanun ta kamar zasu fado take nuna kanta jikinta har tsuma yake ni ni kike gayawa haka.


Jujjuyawa Jalilah tai au da dawa nake ko akwai wasu awajannan kedin din dai dake nake koki juye ko wllh na barar dashi akasa kowa ma yara sa,tuni wajan ya kaure da hayaniya masujin haushin Hauwa sai hamdala suke da Allah ya kawo merama musu,da masu ALLAH ya kara azuci saboda tsoron furtawa azo asamu matsala.


Daga hannu tai zata kashe fuskar Jalilah da mari caraf ta rike hannun karki fara wllh marin fuskar nan daidai yake da tsokanowa kanki bala'in duniya wanda bazaki iya tare shiba,yarfe hannun Hauwa tai tuni aka dauki sowa da tafi saiga Hauwa tayi tsamo tsamo kamar wadda aka tsoma aruwan zafi.


Akaf Rayuwar datai a makarantar babu wanda yataba daga mata murya balle hartace zata mareshi ya rike mata hannu ita Hauwa ta samu wadda zata kalu balance ta inah hakan bazai taba faruwa ba har abadah.


Hankadar da ruwan Jalilah tai kif kuwa ya sheke akasa daukar bokitin tai tai gaba,su Ablah kansu abun ya girgiza su ido bude suke kallon Jalilah mamaki ya hana su magana.


Har sukaje daki babu wadda ta iya magana acikin su sun zama kuraman karfi dayaji,banko kofar akai kamar za aballe musu kofar wata shirgegiyar matace ta shigo sai huci take tana hura hanci kare musu kallo take daya bayan daya tuni su Ismah sun dade da gurfana akasa jikin su na kakkar wa Jalilah kuwa ko motsawa batai daga inda take ba karewa matar kallo take da tunanin ita kuma wannan wacece.


Eh koda ban tambaya ba nasan kece kika aikata wannan mummunan lefin Hauwa dake gefanta tana huci gyada kai tayi kwarai ita ce,dan jim tayi na wani lokaci muje kamarya muje baki dauki mataki akanta ba,wani kallo matar ta wurgawa Hauwa kofa ta nuna mata dole tafita daga dakin zuciyar ta cike da sake saken meyasa takasa daukar mataki akanta kamar yadda ya saba.


Wani makirin murmushi ta saki tana karewa Jalilah kallo wanda ita kadai tasan ma'nar sa,juyawa tai tafi ta Jalilah tabita da kallo baki bude.


Numfashi suka dinga saki wanda ya tsaya amakoshin su sai yanxu suka samu damar fesar dashi.Kallon Jalilah suke kamar tibi wai wannan kallon na meye.


Ablah ce ta magantu dole mukalleki gaskiya ke yar baiwa ce tunda har Anty Zarifa ta kyaleki bata dauki mataki akanki ba.


Wacece ita Jalilah ta tambaye su.


To fans kubiyoni danjin wacece ita kamar yadda Jalilah take bukatar amsa haka nima nke bukata.

Kubiyo ni danjin yadda zata kaya.

Taku har Kullum.

Mrs Baba Bello ABUBAKAR

No comments