Recent Updates

Uncle J 49

 


Page 49


Har sukaje suka dawo tana zaune,kallon Abincin hannun su tai wani dan mitsitsi bamai ba kayan miyar arziki sai nama yanka biyu.


Ku yanzu wannan abincin koni aka hadewa shi ai saina cinye batare dana koshi ba,baki bude suke kallon ta wannan abincin zaki iya hadawa ki cinye tas ma kuwa wllh to mukuwa indai kincinye abincinnan zamu baki lambar yabo hade mata abincin sukai waje daya saukowa Jalila tai daga gadonta.


Dirshan ta zauna kankace me ta lakume abinci tsuru sukai suna kallonta anya Jalila ke mutum ce kuwa me kuka gani aini wllh inba wukar yanka nagani ba bazan iya cin rabin abincinnan ba to sai gashi ni babu abunda nagani kuma na cinya.


Amma kina da aljanu Dariya tasa nini kadaice aini aljanu ma basu isa sun rabo inda nake ba saboda masifata ku nifa bana barin ta kwana balle tai tsami.


Uhm kina wasa da bording kiyi Addu'a kawai Allah ya rabaki da mugayan makarantar nan dan wllh daukar Amarya za'a zo ayi miki kinaji kina gani za'ai miki shegen duka babu kuma yadda zakiyi,ai matukar wata shegiya ta daken amakaran tar nan ranar zataga tashin hankalin da tunda gyatumarta ta haifota bata taba gani ba wllh,to mudai duk randa kikayo tsokana bamu da karfin tare miki.


Harara ta galla musu mari ma kun kasa ramawa aidama ni bana son kowa yashigar min fada ni zan tare muku amma guguwar da zan tsokano bazaku iya tare taba saini dakai na zan tare kayata, gaskiya ina so naga wane irin kwarin guiwa kike dashi ko waje fa baki fitaba tunda kikazo kifita waje kiga manyan yammata wadanda zasu goyaki suzagaye schl dinnan basusan kina bayan suba,aini nasaba fada da irin su dama agidammu akwai samudawa kunga karo da wa 'yannan bazai min wahala ba dariya suka sa.


Kwarin guiwarki ya bala'in birgeni zamiyi tafiya tare Ablah ta miko mata hannu suka tafa dan daman tafi Nasmah da Ismah zafi da rawar kai jiki magayi cewar Nasmah kudai ku zuba ido kusha kallo dama namu idone inji Ismah,hirar su suka ci gaba dayi Lokacin Islamiyya nayi suka shirya kowacce tasa uniform dinta na Islamiyya blue din riga da wando sai fararan hijabai har guiwa muje.


Suna tafe Jalila tana ta kalle kalle kowacce zaka ganta da Alkur'anin ta ahannu da sauran litattafan da ake musu kai tsaye class din su suka nufa har amfara taruwa suna shiga akayo musu caaaa da idanu ganin su da sabuwar daliba,duk shan kunu sukai dan yaran badai jan aji ba tsaki Ablah tai nifa natsani kallo wllh kunyo mana har da idanu to li'ilafi kuraishin.


Babu wanda ya tanka mata dan sun san masifar Ablah su Nasmah basu ce komai ba waje suka samu suka zauna muraji'a suka farayi Jalila dai tayi zugudi iyakacin izu biyu ta iya,agida sai allonta ya fita daga hayyacinsa take wankewa asakeyi mata wani rubutun gaba daya tasa wasa a dukkan al-amuran ta akallah sun wuce ta da kusan izu goma sha uku tirkashi.


Gadai Alkur'anin a hannunta amma ta bude wajan da suke biyawa ma bata sani ba, Nasmah ce ta dubeta kibude mana Jalila Malama zai miki bulala inyazo yaga bakya karatu,zumbura baki tai ke nifa bantaba jin wajannan da kuke biyawa ba kallonta ta sakeyi sosai kamarya baki taba jiba kamar yadda kika ji,kina nufin mun wuceki akaratu eh to aiba damuwa zamu dinga koya miki to kawai tace karba tai ta bude mata inda ake biyawa haka ta kurawa rubutun ido saitaji babu dadi dama ace itama ta iya gwanin birgewa take kallon yan ajin sun hada baki sai raira karatu sukeyi gwanin sha'awa.


Kari Malam yayi gobe kuma za'a kawo masa hadda sai karfe 5:30 suka fito daga class din dakin kwanan su suka nufa,tundaga nesa ta hango yaya Hauwa ras gabanta ya fadi tuno abunda ta gaya mata dazu tuni idanunta suka ciko da hawaye agaban su taja tinga ta tsaya ke mena gaya miki dazu,yanzu zanje na debo makaranta mukaje Allah yasa dawafi kikaje wannan bedaman ba nabaki mintuna biyar na ganki da ruwan wankana,kallon su tayi daya bayan daya kowacce kanta asunkuye amma Jalila kir take kallon ta.


Ke ni sa'ar wasan kice dazaki tsaya kizuba min idanu kina kallon cikin idanuna ko kala batace ba still bata daina kallon nata ba,Jalila mekikeyi anan juyawa sukai suna kallon Sauda da zuwan ta kenan ga wadda ta tsayar damu nan.


Hauwa me sukai miki kika tare su ahanya shiru tai dan ba karamin shakkar Sauda takeji ba kutafi daki gaba sukai suna sauke ajiyar zuciya gaba tai tabar Hauwa da dacin zuciya kwafatai tarasa meyasa Sauda take shigar mata hanci da kudun dune.


Ita kadai tasan wacece ita amakarantar nan sirrinta atafin hannunta yake shiyasa bataso wata doguwar hira ta hada su gudun tonuwar asirinta kwafa tai yan kanzaginta suka take mata baya kana kallon idanun su kasan ba kananan fitsararru bane idanun su asoye yake da tantiranci da rashin kunya.

             Mrs Baba Bello Abubakar

No comments