Uncle J 48
Page 48
Har daki taraka ta gadaje hudune acikin dakin babu matsi babu takura kowa da jakarta akusa da gadonta sai lokar kayan Abincin ta wanda yake daga bakin taga shine babu kowa akai su uku ne acikin dakin,itace cikon ta hidun su akwatinta ta ajemata awajan sai lokar ta zuba mata kayan abincin ta,key din ta mika mata gashinan in kika yar babu ke babu cin abinci kikula dashi yadda ya kamata to ta amsa.
Ki zauna yanzu ankusa tashi in za'ai karatun Islamiyya saiki je kema ni zan koma class duk abinda kike so kine meni ina fatan kingane eh futa tai daga dakin tabar Jalilah tsuru azaune zafi harya fara damunta babu AC 🤣🤣lallai Jalila zakiyi medalilin.
Kusan zaman awa daya tayi kafin taga ana ta bullowa tawata hanya kamar kiyasai dan danan taga yammata da sa'anninta sun cika Makarantar ashe da akwai mutane da yawa ta ayyana hakan,su ukune kusan kansu daya dakin suka nufo suna tafiya suna hira gwanin ban sha'awa,wata Budurwa taga tasha gabansu babu wani bayani ta daga hannu takashe Fuskar daya daga cikin su da wani shegen mari saidata durkushe akan guiwowinta kafin ta saki wani marayan kuka.
Kyakykyawa ce Yarinyar dagani hutu da jindadi sun samu wajan zama ajikinta dafe kunci Jalila tai kan uba wace shegiyar ce wannan bala'i inni tamara aiyau saidai buzunta.
Dan uwarki harkin isa nasaki aiki kikiyi wai baki da lafiya Allah yasa suma kikeyi wllh daga yau wannan shine magana takarshe da zammiki bama keba duk wani mara kunya amakarantar nan zan gyara masa zama kuma anjima kifito kiyi noma tunda baki da mutunci kin shigo komata kenan sannan ruwan wankana na tsahon sati daya duk inda zakije kinemo ruwa nasameki a kokar toilet kina jirana inkunne yaji gangar jiki ta tsira.
Hankadeta tayi tai gaba kawayan nata ne suka sunkuya suka dago ta abunka da farar fata tuni fuskarta tai jajajir hawaye kawai ke shatata a kuncinta hannunta suka kamo basu ce komaiba face din su abace take dan babu yadda zasiyi ne dasai sun rama mata,dakin da Jalila take ciki suka shiga gaba daya basu lura da ita ba suna ta aikin rarrashi.
Dan Allah kiyi shiru Nasmah kibarta da Allah,yanzu Ablah menai mata ko zalinci ne kawai zata daken bansan me naiwa yan schl dinnan ba suka tsaneni haka kodan sunga bana ramawa nayi dana sanin zuwa Makarantar nan zance da Dadyna acire ni nakoma day,cikin zafin rai dayar dabatai magana tafara fadin itadin banza acikin kayan miya wane gwalagwajin ce da harzata hanamu sukuni babu inda zakije muna tare wllh.
Ismah bazaki taba ganewa ba ninasan zafin da nakeji acikin Zuciyata babu wanda yake dukana agidammu kowa sona yake da tattalina bazan zauna wata zindi kiya tadinga dukana ba.
Jalilah datai tsuru tana kallon su dan motsin datai ne ya sasu juyowa cikin mamaki suke kallonta sam basu san da za manta adakin ba.
Wow new student suka hada baki wajan fada tasowa sukai gaba dayan su suka zagaye Jalila datake binsu da kallo Nasmah ce ta miko mata hannu My Name is Nasmah Aliyu Sadauki,mika mata nata hannun tayi Jalilah Muhammad Uba dan sosai Jalil yai zaman koya mata full name dinta dukan su mika mata hannu sukai babu nuna kyama agare ta hakan yayi matukar yi mata dadi.
Fatan zamu zama kawayan juna murmushi ta sakar musu gyada musu kai kawai tayi,ko bakya magana um inayi mana ban saba daku bane aiko zaki saba damu yan ukune amma yanzu mun dawo yan hudu dariya sukai gaba dayan su sabanin Nasmah data dan mirmusa da alamun magana be wani dameta ba.
Nasmah take kallo da harlokacin fuskarta bata dawo daidai ba mekikai mata ta mare ki idanunta ne suka ciko da hawaye girgiza kai tayi alamar ba komai amma dai wllh muguwa ce kekuma zaman me kike dabaki rama ba,waro idanu sukai gaba daya akanta tarama fa kikace yau inta daki Anty Hauwa sai ankusa tsireta a tsakiyar Makarantar nan bakiga yadda malamai ke sonta ba saboda me saboda tana da kokari.
Mtswww ni ina ruwana wllh duk ranar data maran saina daga hannu na sama zan wanka mata mari dariya suka saka ammafa kina da cika baki Jalilah um kuna wasa dani ko kuzuba idanu duk zan kwato muku yan cinku sai andawo ana duka mana ahanya ana take mana baya,dariya suke sosai ko yanzu Jalila ta sasu farin ciki.
Ablah ce ta rungumeta munji dadin haduwa dake sister,hannu Nasmah ta miko alkawari dora hannayan su sukai akan nata munyi alkawari zamu zama kawaye na amana kawayan juna masu temakon juna bazamu taba juyawa juna baya ba zamu tsaya tsayin daka domin temakon junan mu, Jalilah dai kallon su take bazata iya jera wannan maganar ba suna sakin hannu taga sunnufi lokar abuncin su.
Roba kowa waccan su ta dauko kema kidauko taki ina zamuje abincin rana zamu karbo abincin da nazo dashi fa ai zamuci amma saimun karbo na namakaran ta inba haka ba kafin azo mana visiting mun tagayyara a school dinnan tab kamar wata almajira kuje ni ina nan ai yayana yace za akawon inya kare ba yadda basi da Jalilah ba taki haka suka tafi suka kyaleta zata dawo kan hanya ne.
Mrs Baba Bello Abubakar
No comments