Recent Updates

Uncle J 46

 


Page 46


Washe hakora take tana kallon sa ahankali ya tako har gabanta kare mata kallo yake yar kauye yaushe kika dawo canake ammiki Aure acan,bata fuskatai fatan da kakemin kenan aini bayanzu za'aimin Aure ba amma kaga su talatuwa kawaye na duk ammu su Aure.

Kema kina kan hanya kizuba idanu kigani muna zaune zamuji ana guda andaurawa Jalilah Aure Dariya ta kyalkyale da ita kuma kasan meyafaru danaje kauye,aah saikin fada inazan sani kina katsina ina daura.Hmm,kafa yadda samari suka dinga layi akofar gidammu wai suna suna harfa dame gari Dariya ce ta kwacewa Jalal kice kinyi kasuwa to yanzu ansa rana dame garin ko kinga babu ke ba zuwa makaranta.


Wane megarin ka ganshi kuwa yafi baba megadi tsufa fa gaskiya kinyi babban kamu Jalila ashe haka kike da farin jini muma nan gaba kadan za'afara dambe akofar gidannan,fari tai da idanu dagaske kake dan India mataba yimiki karya ne a'ah ni dai kadaiba min zan can Aure ni karama ce,amma kike cewa da wasu samudawa kema saikin zama kamar su kenan.

Lah wanene ya fada maka wannan sunan ai zancan duniya baya buya agari naji gidammu akwa samudawa guzumaye dariya tasa to ai ba karya nayi ba kasan kaima hakane ah ni babu ruwana karkisa suji su taru siyi min duka in kuma zaki shigar min to,mezai hana ban shigar maba ai bazan taba yadda su dake kaba uhm naga alama,hakanan yakejin Nishadi aduk lokacin da ya biye mata suna shirman tare.


Har parlon sa ta rakashi ina tsara bata kaima da zanta fi mekaban kin manta kenan alawarma daka bani yar micililiya ko makogwaro na bata jeba aiko kinyiwa kanki zaki sake zuwa gida ne babu abinda zan baki,yi hakuri dan India kai bakasan wasa bane ni wasa nake ma bara naje nakawo ma goruba ce da taura.Rike kayanki bantaba ciba bazan kuma taba ciba wannan ai wahalar da rayuwa ne shikenan takara auki dama wllh addu'a nakeyi karka karba murmushi yayi to addu'ar ki ta karbu lallai ke yar baiwa ce sosai ma.


Yawwa Ammah tace zakui tafiya kaida wannan abokinna ka zaka tafi dani,aike batafi dake wannan kasar tsaf zan iya kare rayuwata adaure dan bansan aika aikar dazakije kiyi ba,kamar wata bera wai meyasa kake cewa ina da fitina nidai nasan banda ita.Nan gaba Ammah tace zan zama yan mata in zama yar gayu babu wanda zai rainani hakan nake fata ai amma haryanzu da sauranki baki zama big girl ba mene haka kuma babbar yarinya mana aiko yanxu nagirma,baki da girma zaina jikinki amma hankali dai da sauki.


Kije Nagode zanne miki anjima tun ana abu na marmari saikinsa mutum ya kosa da magana fita tai tana kunkuni Jalal yace mata mesurutu,bin bayanta yayi da kallo Girgiza kansa kawai yayi mikewa yayi ya shiga bedroom dinsa.

Tafiya makarantar Jalila babu abunda ba agama ba gobe ne tafiyar Ammah da kanta ta wanke mata kai har wannan lokaci Jalila bata daina kukan kitsoba sosai gashinta yayi yawa tana kuka da burburwa aka gama kitson saida Jalal ya dauko belt ya zuga mata daya tukunna ta daina tirje tirjan da takeyi tana ji tana gani akai mata kitson.

Dungure ta Ammah tai kedai wllh kinji kunya Jalila bansan randa zaki hankali ba kina girma kina kara tabar barewa Allah ya shiryeki,haka zakije makarantar kina kazanta bazasu kyaleki ba dakan gumba zasiyi miki sai kindawo cikin nutsuwar ki,kala batace ba sai kukanta take hankali kwance kamar kara zugata akeyi.

Ke!!! yiwa mutane shiru karna tattakaki wllh me akai miki zaki kamayiwa mutane kuka tsit tai dan in Jalal ya hade rai kokai babba kwarjini yake maka.Tashi kazama kije ki wanke fuskarki tashi tai da sauri ta shige dakinta Ammah binta tai da kallo tana ayyana abubuwa da dama a zuciyar ta nufashi tadan sauke.

Karfe Nawa zaka kaita karfe 7 zamu fita kinsan jirgin karfe 2 zamubi dole naje nakaita da wuri to Allah ya nuna mana amma ina tunanin tafiya kubarni nikadai bazanji dadi ba sam,ga iya aidama da ita kika saba zama ada ba aini yanzu jinake duk randa Jalila zata koma garin su bansan yadda zanyi da rayuwata ba wllh haka kawai nake sonta kodan sunan ku kusan daya ne.


Dariya ya saka kin yadda da zancan Jalila datace sunan mu iri dayane yarinyar nan tacini wasa.eh aida gaskiyar ta dayanne ma,wata hirar suka fada cikin kauna irin ta da da Mahaifi.

               Mrs Baba Bello Abubakar

                 ......✍️✍️✍️✍️

No comments