Recent Updates

Uncle J 44

 


Page 44


Kowa mamaki yake yadda megari ya tashi ya fita salin alin sabida sannin halayyar sa matukar yace yana sanki to ko zaki mutu saiya Aure ki ta karfin tsiya kuma dole ki zauna babu yadda zakiyi daya gano wata zai sakeki ya aurota.Ajiyar zuciya suka sauke ganin yafice shida ta wagar sa kallon ta sukai da tunanin dariyar me take tabbas akwai abundata kulla.

Wai dariyar me kike haka babu komai Inna kawai na tuno da wani abune amma kinsan bazamu taba yadda ba babu ta yadda za'ai megari ya tashi ya futa daga gidan nan salin alin dole da wata akasa,tabe baki gwaggo tai kinga barta tunda Allah dai ya tsallakar damu daga sharrin sa ai shikenan.


Kai Allah y kiyaye mu da mugunji da mugun gani amen gwaggo sakin hirar sukai suka fada wata,sosai Jalila taji dadin zuwa kauye duk da tayi missing din abubuwa da dama amma yanayin garin yayi mata dadi sosai.Inna ta hada mata tsarabar su kuku kubewa daddawa zobo duk takaiwa Ammah haka gwaggo ma ba'abarta abaya ba ta hado tata tsarabar kaya rigijif suka hada mata sosai sukai mata nasiha da fada tayi abunda ya kaita.


Gidan su yanxu Alhmdlh ba rashin ci ba rashin sha komai saidai ma sha Allah suna cinna kansu daidai gwargwado.

Tun sassafe Indo ta doka Sallama motar safe take so subi bata so suyi rarnar tafiya tsaf Jalila ashirye take dama rungume su tai gaba dayan su kewar suce ta mamayeta fashewa tai da kukan rabuwa dasu kamar karta barsu haka take ji inna ma goge hawayan ta takeyi saboda kewar yar tata tana matukar son Jalila,dakyar suka rabu suna dagawa juna hannu tasha sabuwar atamfarta riga da zani wanda Innah ta dinka mata kala uku masu kyau.


Wannan karon babu dage dagen hannu da yiwa yan kauye bye bye anutse suke tafiya kamar ba Jalila samarin da suka nuna suna sannta sai cizon yatsa suke ganin zata koma basu samu shiga ba.

Kai tsaye tasha suka nufa basu wani jima ba Motar su tatashi saidai fatan sauka Lafiya.Lissafi yake tundaga Kwana daya har kwana ki bakwai ayau da zata dawo wani madaukakin Farin ciki yakeji yarasa meyasa ya damu da ita meyasa ma zai dunga tunanin ta ya wahala ba kadan ba tashin jinta surutunta duk yayi missing din su.

Jamal kansa yasan ya sauya tambayar duniyar nan yace masa babu komai baya jin dadine kawai dan dole yagaji ya kyalesa sake juyi yayi abed din karo na barkatai ko sun taho ko basu taho ba bashi da tabbaci murmushi yadan saki me kayatarwa tare da lumshe idanun sa.


Karfe 10:30 suka shugo gidan Ammah tundaga bakin get take gaggaisawa dasu baba direba yanxu sun saba sosai sai sannu da zuwa sukeyi mata,tundaga kofar parlour take zabgawa Ammah kira Mom ce agaba su rufaida abayanta,to! mayya saida kika dawo mutum kamar gidan tsohon sa bashi da ko gashi agidan amma saikin kara dawowa.


Salima ce tasaka dariya kokuwa yaushe za'a iya zama gidan inna da baba baki ya saba da dandanar Abin Arziki ku baku ga harta rame tayi duhu sai Yanzu na lura salima bakiyi karya ba anje anbigi mugun boss acan,mene kuma mugun boss dariya suka saka gaba dayan su af tuwo mana shi nake nufi,magana take sonyi Indo ta toshe mata baki muje karkice komai tamace wllh daga ke har ita zamu hada miyi muku shegen duka.

          Mrs Baba Bello Abubakar

No comments