Uncle J 43
Page 43
Gidan Maman Ladi ya shiga da sallamar ta mijin ta na zaune adaki kuri yayi yana kallonta saidaga baya ya gano wacece hade face yayi jaraba kin dawo kennan to inma kallo kikazo yi ba akunna ba,harara ta maka mai tv dinka din banza ni yanzu wannan abar kamar kiyashi ma ai bazan iya kallo acikin ta nake birni naga yadda ake harkar arziki bata tsiya ba.
Ni ba kallo nazo yiba wajan Maman Ladi nazo to batanan saikiyi waje karyar banza babu wata tv datafi wannan duk Nigeria dariya ta sheke da ita hakane awajan ka ki haryanzu kanka abakar leda yake amma ni da naje na wataya abirni nasan Abun ba haka yake ba karike kwaranabbiyar TV dinka Jalila tafi karfinta.
Ficewa tai tana dariya wai TV dinsa kaf Nigeria babu kamarta,bala metsire ta hango tundaga nesa yake washe mata baki hade face tai Jalilah Jalila yan mata yatsina fuska tai ya akai Bala me tsire,washe hakwara ya sakeyi tunda na hango ki kindawo nake ta alla alla kifito na baki tsire.Allah sarki bala nagode kabar abunka yanzu ba da bace ni yanzu wannan naman naka da kudaje kebi bazan iya cinsa ba.
Zuru yayi yana kallon ta meyasa ai wannan tsiran naka yanzu kwayoyin cuta sun gama baibaye shi Iska ta gabas da yamma kudu da arewa duk ta hau kansa,da kuma da kike cifa to bakaji da kace ba kuma tana baya gaba tai ta barshi shanye da baki yana jimamin anya wannan Jalilah ce kuwa ba canjata akai ba.
Nan fa samarin kauye akaita layi akofar gidan su Jalilah gaba daya sun rikice ganin yadda tadawo fresh babu kazanta babu warin dake tashi daga jikinta ga suturar da take sawa Irin ta yan birni amasu zuwa neman Aure harda me gari yasha rawanin sa harda masu take masa baya.
Jikin Inna na rawa ta shimfida katuwar ta barma atsakar gida har cikin gida aka shigo dashi gwaggo ma sai yashe hakora take megari yau agidan su lallai sun duro Duniya a sa'a,cikin girmamawa suka gaida me gari gyaran murya yayi ya fara da Fadin.
Allah y jikan Malam mutumin kirki tun yana raye naso akulla wannan Abun alkairin amma yanzu duk da baya nan nasan zaiyi Alfahari da haka,wato abunda ke tafe dani shine Magana akan Jalila shekara kusan daya naso nazo da batun neman Auran ta saina samu labarin tatafi birni shiyasa na dan dakata tunda yanzu Allah y nufa ta dawo sai ayi komai agama tatare adakinta.
Gwaggo ce ta gaza hakuri Allah ya kara lpy bamu game inda kasa gaba ba,abunda megari yake nufi yaga iri yana so abashi Auran Jalila nan da sati biyu masu zuwa,shida kansa ko dansa nida kaina yafada yana gyara rawanin kansa.
Kallon kallo ake tsakanin gwaggo da Innah sake kallon sa sukai akalla yaba shekaru saba'in baya kodai ita kanta batajin zata Aure shi balle Jalila da take jikar jikar sa,burum Jalila ta fito daga daki duk tattaunawar da ake tana jin su karewa jama'ar kallo tai sannan ta dawo da kallonta kan gwaggo.
Wai gwaggo kasuwa kikai ne naji ana batun Auranki juyawa tai ta Kalli megari Allah yaja zamanin ka megari Indai gwaggo ce ambaka ita baka da wata matsala ina ce shikenan,gyaran murya megari yayi nkusa da shine ya ari bakin sa Allah ya temakeki ba gwaggo yake bidar Auranta ba ke yake bida saboda sanin kyawawan hayanki da nagar tarki.
Kujera ta jawo ta zauna ni kake nufi zaka Aura kare masa kallo takeyi daga sama har kasa to ngd da kauna Allah yasa ka da Alkhairi zaku Iya tashi sawunku a likkafa kufita Idan kuma kanaso na maimaita abunda naima abaya to kaci gaba da zama,makwat megari ya hadiye wani mugun yawu tuno tsiyar da Jalilah ta shuka mai.
🤣🤣🤣Akwai wani lokaci da Jalila tai lefi cak aka dauketa har gaban megari sai muzurai yake yana zare idanu,ke kina wasa da maganar muko zuwanki na 10 kenan gabana yau da kaina zan hukuntaki lawwali asamin ita adaki angama ranka ya dade daukarta aka sakeyi har dakin horo inda ake kai masu lefi a tsulale su.
Tashi yayi tsam daga wajan zaman sa saidaya tanadi zukekiyar dorinar sa ta dukan Jalila,tana rike da kugu ya daga bulalar ya zabga mata kirmi sisi tai kamar bataji dukan ba karka sake dukana ina ganin mutuncin ka sake daga bulalar yayi fit tashige babbbar rigarsa gasa mata mintsini ya kushi babu abunda bata yi masa jin azaba ta ishishe ya murde mata kunne jin yana barazanar tsige mata kunne caraf ta damke wandon megari.
Duk wasu ma'adar sirri dake kai kawo ajinkinsa saidata dena aiki tsabar Mugunta irin ta Jalila murdeta take kokarinyi tuni megari ya hada Uban gumi kiyi hakuri nagama ki da Allah ki kyaleni wannan itace rayuwa ta kimin rai wllh bazan sake shiga harkar kiba.
Katabbata kwarai kuwa sakar masa wandon tai har tuntube yakeyi wajan fita daga dakin yanayiwa Allah godiya daya rabashi daga ta addancin Jalilah.🤣🤣🤣katuna ko kwafa tai tashi kufita tashi yayi kamar kazar sa kwai ya fashewa aciki.
Fashewa tai tai da wata muguwar Dariya buga cinya tai saini Jalila me makaman yaki.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️✍️
No comments