Recent Updates

Uncle J 41


 Page 41


Sanda suka shigo parlo su Mom suna baje suna shan iska har Lokacin idanun su bai dawo dai dai ba sannun ku da gida ya jiki kuma,naganku kowacce idanu awaje ko haryau zawon be tsaya ba zoki duba dan Ubanki nace zoki duba shegiyar Yarinya kai me kafirin surutu ina ruwanki da Lafiyar mu da zaki dinga shegiyar tambaya kamar makauniya.

Daga abun arziki tun baku son addu'ar Allah ya sake maimai tawa saidai kigani akan ki da uwar data daure miki kugu kike rashin mutunci,in sha Allah babu Abinda zamu gani dan mu bama hayam hayam kamar tinkiyoyi kullum baki abude, Ammah ce ta buge mata baki wuce muje bana son rashin kunya sama tahau tana juyowa suka hada idanu da Rufaida gwalo tayi mata ta karasa hayewa tana dariya.

Kiyi hakuri Saratu kinsan yarinya ce kinga Rukayya bana son wani gulma duk wa ya kitsa mata ta rainamu agidan Idan bake ba kiwuce kiyi Abunda yake gabanki kawai to alakara sauki inma baki fada ba zai bayar Mtswww suka ja tsaki,gaba tai cikin sanyin jiki bata son tashin hankali ko kadan a rayuwarta sukuma ta lura burin su kullum ayita hayagaga ana kumfar baki baza'ai wannan da itaba sam.


Dama ba yunwa suke jiba kowa neman waje yayi ya kwanta asuba tagari Jalil da Jalilah.


Haka rayuwa taci gaba da gangarawa ayi dadi ayi tsiya Jalila ta kara girma tarage fitina da tsokana zata iya sati ayanzu bata tsokani kowa ba ita da Jalal sosai ake dasawa.


Bording school ya samo mata daga primary two zata fara dan da aka kwankwasa kan Jalila babu wani labari in aka kaita js on za'a samu Babbar damuwa,ga Jalila tayi girma da primary akalla takai 14yers ayanzu haka wata malama ya samu a Makarantar yanemi alfarmar tadinga yimata lasson daya ke harka ce ta kudi da kauri ya biyata dan danan ta amince harda alkawarin zata kular masa da kanwar sa.

Tun daga kd ya sama mata makaranta mekyau da tsada amma suna da nisa sosai da gida   gwara tai nisa da gida zatafi maida hankali akan abunda za'a koya mata.

Jalila ya kamata kije gida kiyi kwana biyu kafin kitafi makaranta to nan fa keyin ta saidai muje tare Ammah dawa zakije kauyan aini da zuwa garinku sai antashi auranki bata rai tayi ni bazanyi Aure ba bige mata baki Ammah tai kul karna sakejin kin fadi haka kuma kinsan ALLAH saikinje gida ko mutuwa zakiyi saboda Kuka.

Ni wllh Ammah wayo kawai kike so kiyi min amaida ni kauye shikenan bazan dawo ba haka na gaya miki bazaki dawo ba kitashi kihada kayanki indo zata zo kutafi nan da anjima sake rushewa tai da kuka Ammah da kanta ta hada mata kayanta.

Tunkan yayi parking ya hango Jalila azaune dirshan tana gurzar Kuka hmm matsala kome akai mata kuma oho,harya tsaya agabanta batasan yazo ba zata daina cin shinkafa da nama gaba daya hankalinta ya gama tashi,ke kukan me kikeyi sai lokacin tasan da tsayuwar kuka ta sake fashewa dashi Ammah ce tace sai nakoma gida kiyi me wai nayi kwana biyu.


Shine kike wannan kukan kamar wadda ake duka toko dai kiyi shiru kokuma inkin tafi kintafi kenan tundake baki da saiti garin nakune bazaki jeba,aini bana so naci tuwo murmusawa kawai yayi to aishikenan saiki kulle shinkafa kije kita dafawa acan inadai shikenan naman fa wannan kuma saidai ki rungumi sorry gaba yayi yabarta anan yana mamakin halin Jalila shegen kwadayi acikinta harda na siyarwa.

Sai lokacin taji dan dama dama wanke fuskarta tai da tagama cabewa da hawaye,kin gama kukan shiru tai Allah ya shiryeki Jalilah ni bansan sanda zakiyi hankali ba inaga saikinje makarantar zakiyi hankali dan can kikai rawar kai shegen duka zakisha babu ruwan su.

Saisu daken kamar wata jaka wllh koda aranar bazasuyi baccin dare lafiya ba mezaki musu uhmm bakomai Ammah zadai kawai suji ajikin su ni bana sanayya bana ragayya aiko zakici wahala wllh dalibai ma saki aiki zasu dingayi kuma dole kiyi.

Ammah kamar kin mance ni nikam ya za'ai na mance ki zandai biki da Addu'a kar adawon dake akakkarye shekewa tai da Dariya aiko da ban cika sunana Jalila kanwar dan India ba,Dariya Ammah tai kin yadda yanzu kanwar tasa ce ba yar aikin Gidan su ba,tuni Ammah aisu kansu yan makarantar nace musu yaya nane zakiga suna girmamani naga alama kuwa ko kuma su sakoki agaba ba.


Indo ce ta rangada sallama amsawa Ammah tai to kinga tazo dauko jakarki ki fito da ita to Ammah,maimakon tai Abunda aka sakata dakin Jalal ta nufa yana zaune yana rubutu ta shigo zumbura baki tai wai baka fara kewata ba,tsayawa yayi da aikin da yakeyi kewarmi tame aini dadi nakeji ma zan rabu da ciwan kai nice ciwan kan ehman aini kika tafi har kiba zanyi kafin kidawo shikenan tunda abun haka nema.


Mezaka bani to natafi dashi tunda nace kidauki shinkafa aina gama miki komai ko, to shinkafar gaya zan dinga ci.

            Mrs Baba Bello Abubakar

No comments