Uncle J 40
Page 40
Kunshe dariya Jalila keyi Allah sarki hajja daga gani kinsha wahala ba kdan ba,ai bazata kayyadu ba da rarrafe tafito daga bayan gadon jikinta har diga yakeyi saboda fitsari,hajja fitsari kikai ne shiru tayi ahaka takoma gadonta ta shige bargo bakinta cike da addu'a Kala kala.
Kwanciya Jalila tai ranta fes ko banza tayi maganin hajja ga kuma dadin da zata kwasa gobe aita komai zam zam.
Sam hajja kasa runtsawa tai gaba daya gani rai daran yayi mata tsayi kiran sallar farko akunnan ta tashitai cikin tsoro take dube dube ganin babu komai adakin sai Jalila dake sharar bacci hankalinta kwance, toilet ta fada saidatai wanka sannan ta dauro alwala ana idar da sallah tanufi part din Anty Zainab kwankwasa tai yar aikinta ce tazo ta bude ganin hajja yanzu tasan akwai Abunda ya kawo ta yanzu haka tijarar tatace ta motsa ta gaza hakuri har gari ya waye
Ina kwana hajja lafiya kalau cikin sanyin murya kamar wadda tai cutar shekara tayi zuru zuru samun waje tayi ta zauna tana jan cazbahar ta,zaman minti 5 tayi mijin Anty Zainab ya dawo daga masjid,ganin hajja saidai kirjinsa ya bada ras da sauri ya karaso gabanta har kasa ya duka yana gaisa ita antashi lpy lafiya lau amma hajja lafiya kuwa kika fito da asubar nan.
Kakalo murmushin dole tai lafiya lau dama. Maganar taron suna ce na janye magana ta kowa agayyato shi ai abun murnane da farin ciki jiyayi kamar beji daidai ba ai hajja maganar ce ban ganeta ba,ba matarka ta haihu ba kuma yau ne suna hakane hajja to shine nace agayyato yan uwa da abokan arziki ayi suna.
Kuma lafiyarki kalau hajja harara ta zabgamai aah ciwon hauka nakeyi ba haka nake nufi ba,karkacewa tai ta zaro kudi acikin sket dinta yawwa ga wannan sai ahada ayi hidimar suna,jujjuya kudin yake al,ajabi ya kamashi lallai Allah me iko addu'ar daya dade yanayi yau Allah y amsa masa hajja tagane gaskiya,tunda Matarsa take haihuwa haihuwar fari itace kawai tayi rawar gani daga wannan haihuwar bata sake nuna murnar taba.
Angode Allah ya kara girma Ameen ina Zainab din bari na kirawo miki ita to,minti biyu suka fito tare adarere tagaida hajja cikin sakin fuska take amsawa wai rabon dataga fara'ar hajja tun tana Amarya.Ina jaririyar wane suna aka saka mata Rukayya sunan yayar Zainab Allah sarki to Allah ya raya ameen suka amsa gaba dayansu.
Kowa da Abunda yake sakawa acikin zuciyar sa musamman Anty Zainab datake ganin abun kamar amafarki ikon ALLAH yafi ga haka,sai kuma maganar taron suna kigayyato duka yan uwanki ayi taro ai abun murnane nima yanzu zan kira yan kauye suzo ayi Dasu,lallai hajja ba ita kadai bace Mummunan gamo tayi kuma gata dai acikin hayyacinta to hajja Allah ya kara girma Ameen bari natashi natafi sai anjima.
Har bakin kofa suka raka hajja nanfa akafara kallon kallo wai anya ba mafarki nakeba abban sajida ido biyu kike Zainab ALLAH ne ya amshi addu'ar mu Allah ya ganar da hajja hanyar gaskiya Alhmdlh lallai wannan haihuwar tazo mana da Alkhairi me girman gaske.
Sosai kuwa ALLAH mun gode maka.
Daki hajja ta koma yan uwa da abokan arziki ta dinga kira runi yan kauye aka ciko mota dama tsoron hajja ke hana su gidan,gida ya cika dankam da bil adama kowa warkajimin sa yake Jalila taci nama haryayi mata yawa data tsaya daci hajja zatace yata kici iya cinki duk kwadayin Jalila ayaudai saidata kai ta kawo ko kamshin Nama bata sonji ansha shagalin suna kowa ya watse karfe 8 dai dai akofar gidan Anty Zainab taiwa Jalal jiyayi kamar sun shekara basa gidan ransa abace yake tunda suka tafi gidan bayayi masa dadi sam.
To mudai zamu tafi Allah y raya Ameen yaya Jalila sai yaushe kenan sai ankwana biyu zance dan India ya kawo ni wane kuma dan India ni abu dariya Ammah tai Jalal mana shine dan India dariya tai kai Jalila zan so agidannan kike wllh babu ruwana da bacin rai kullum cikin sani Nishadi zaki kasance dariya kawai tayi.
Mrs Baba Bello Abubakar
......✍️✍️✍️
No comments