Uncle J 39
Page 39
Wannan kayan na wanene nawa ne uniform din Islamiyya tane kuma da fararan kaya kuke zuwa eh,shikenan anan suka sha shance har kusan karfe 2 harabar gidan suka fito sudan zazzagaya motar da suka zo aciki ta hango da Mamaki take kallon motar tabbas acikinta suka zo da gudu ta ruga gidan gaba ta fara lekawa yana cike akwance kamar me bacci amma ba bacci yake ba shikadai yasan abunda yake tunani.
Dan India dama baka tafi ba tome kakeyi anan,ahankali ya bude idanun sa akanta daga ita sai vest harararta yayi ina kayanki suna gida zafi nakeji kuma wasa zamiyi Sajida ya kalla da take washe mai wawulanta ke kuma fa nima wasan zanyi ke bakiji kunya ba godai godai dake kirasa da wadda zaki wasa saida Sajida mene dannayi wasa da ita tazama kawata ai saikije kitayi kukoma gida kuyi wasan acan.
To kaima anan zaka kwana Jalila ki kyaleni karna fasa miki baki hannun Sajida ta kama sukai gaba cikin jin haushin Jalal yayi mata tsawa,futowa yayi daga motar ya nufi cikin gidan lallai idanunka kenan Jalal saiyau zaka zo min barka bana bukata Murmusawa kawai yayi ayi hakuri Anty Zee kinsan yanayin aikimmu,dama kana nan tun sanda mukazo mekakeyi to da baka tafiba.
Dariya Anty Zainab tai kema kinjiki Anty zamanne Inaga yayi masa dadi ko kuma akwai ajiyarsa atare damu babu wata ajiyarsa a hannuna kawai binbinine irin nashi kamar yaron goye, Ammah ya kalla kai Ammah meyasa wai kika rage ji dani sabida na samu mace mezan tsaya ina yi awajanka zauna yarona ka kyale yaya zama yayi tamiko masa babyn no Anty bana daukar baby iyee iyayi iya reto tom Idan matarka ta haifa zamuga yadda za ai sai kace bazaka dauka ba.
Iyayine kawai ba wani abuba zai dauka ne Allah ya nuna mana matar tasa ta haihu naga ya dauki dan da aka haifa,shidai yanajin su Murmusawa kawai yayi mikewa yayi Ammah zan wuce yaushe zanzo na daukeki sai gobe in angama suna sai darema zamu dawo,Allah ya kaimu ameen.
Ranar Jalila wuni tayi tare da yayan Anty Zainab suna wasa da tsalle tsalle Ammah har tayi magana ta gaji,bayan sallar isha'i suna zaune suna kallo hajja ta doka sallama saida gaban Anty Zainab ya fadi sannu hajja face ahade ta amsa yawwa kece da sannu ai ke za ayiwa ita shiru tayi dan tasan yanzu neman abunda zai hada su fada takeyi sabida danta ya kusa shigowa.
I lai kuwa tana zama yanayin sallama sai Lokacin ta saki fuskarta shigo dan Albarka kadawo eh hajja mun sameku lafiya lafiya lau hajja kusa da ita yazo ya zauna in dai yanasan zaman lafiya aiko hakan ba karamin dadi yayi mata ba kayan hannun sa ta karba tana budewa kayan Baby ne cikin wata katuwar leda ahaka dai zaka kare kullum kana yawo da kayan jarirai ahannu kullum matar ka biri biri ta haihu har nagaji da gayawa mutanan kauye naja bakina nayi shiru kai tir wllh.
Adaiyi hakuri hajja kyautar Allah ce bamu san wanda zasuji kammu ba kai tafican sauna sha sha sha ana nuna maka gabas kanayin yamma sai kaje can ka karata tunda ni bazaka taba goyon baya naba sai matar ka kardai ka manta nice na kawo ka duniya ahto.Shiru yayi yarasa wai hajja wace irin macece bata kaunar zaman lafiya ko kadan burinta kullum aita cece kuce akan magana guda daya.
Zo mutafi mukwanta yarinyar arziki kedai Uwarki ta iya farar haihuwa, Ammah Jalila ta kalla acan zaki kwana eh Ammah Jalilah shishshigi Amma ta ayyana hakan to tashi ki bita Allah y tashemu lafiya Ameen,tare suka fita har sunfara tafiya ta tsaya nayi mantuwa hajja kije kawai zan taho,to zadai kizo dinko eh zanzo to ina jiranki gaba tai tabar Jalila tsaye awajan.
Dakin su sajida ta nufa wasu kaya ta harhada aleda cikin hijab dinta ta boyo ledar tazo ta fice sanda ta shiga har hajja ta fara bacci samun waje tai ta ajiye ledar hannun ta tanemi waje ta kwanta.Karfe biyun dare ta farka saidata jima a zaune ledar data shigo da ita ta dauka kayan ciki ta zazzage fararan kayane aciki sai farar hoda da bkin kwalli.
Tsam tamike ta cire kayanta fararan kayan ta saka tasamu hodar nan ta babbur suna kanta dama atsefe yake ribom din ta cire ta barbaza gashin kwallin tasamu ta zazzane face dinta dashi saidata tabbatar komai yayi yadda take bukata, kiching din hajja ta nufa wata shegiyar wuka ta dauko me shegen kaifi da tsini duk shekara hajja ke amfani da ita saboda aikin sallah.
Dauko ta tayi tareke ahannu kafar hajja taxo ta faraja Atine!!! taji wata shegiyar murya tana kiran sunan ta afirgece tamike shekaru nawa rabon da taji wani ya ambaci sunanta,bayan gado tai aguje sabida abunda tai arba dashi bayan tafarka tacikin hasken farin watan daya haske dakin.
Wa innahu sulaimanu wa innahu Bismillah hasbunallahu lakadi ja'akum nashiga Uku ni hajja nayi gamo dan Allah dan Annabi kuyi hakuri kukyale marainiyar Allah,shiru!!! Aka daka mata tsawa tsit tai zaro mata idanu tai kin sannu wllh bansan kiba ko me kama dake ban taba gani ba zaro mata idanu tai wato ke muniyar banza ce kin takurawa surukarki akan tana haihuwa kin manta Allah ne ya bata kyautar Allah ba ta mutum ba,wllh na daina sharrin shedanne dama amma yanzu na gane gaskiya ban shirya mutuwa ba yanzu.
Wukar hannun ta taga kamar zata sara mata ki tabbata ni aljana hari ina sane dake duk iskancin da kike na kyaleki ne ina bibiyar ki,mema kika ce baza aiba gobe cikin rawar murya take fadin taron suna to ya zama wajibi ayi aci asha ayi wadaka daga rana me Irin tayau nasake ganin ko afuska kin nunawa jikokinki kiyayya ki tabbatar zakisha wannan wukar can Duniyar mu zaki koma sai kin dandana kudarki.
Nagode Allah ya saka da Alkhairi bazan kuma ba kiyimin rai ki rabu dani,sannan wani abu guda daya ina bakuwar da kikayi gatanan akwance to ya zama dole gobe suna kisamu katon kwano ki cika matashi da nama har saitaci ta barshi sannan kidamo mata fura me shegen sanyi wllh zan bata kuyi hakuri kindauki Alkawarin na dauka nadauka wayyo ni Atine!!! barkewa da Kuka hajja tayi.
Rufe idanun ki zamu tafi rufe idanu tai jikinta sai rawa yake tuni ta tsula fitsari yakai sau uku,da gudu Jalila ta ruga parlo kayan jikinta ta cire tamaida nata wukar data dauko ta mayar Inda ta ganta toilat ta wuce ta wanke Fuskarta da sabulu tas sannan tafito har Lokacin jikin hajja rawa yake idanu arufe.
Hajja lafiya kiketa hada gumi sai Lokacin tabude idanu fashewa hajja tai da kuka Allah natuba kayafin matsowatai kusa da ita wai lafiya,ina kuwa lafiya wllh gamo nayi yarnan gamo kuma acikin dakinnan ehman to wane irin gamo,aini bazakiji abakina ba tunda Allah yasa Mutuniyar arziki ce ta gafar ceni.
Mrs Baba Bello Abubakar
No comments