Uncle J 38
Page 38
Tunda suka fara tafiya shiru sukai babu wanda yake magana bakin Jalilah dai kaikayi yakeyi tana son magana da sun hada ido da Ammah zata wurga mata harara don dole tai shiru badan taso ba,hayin Malam bello suka nufa hon yayi akofar gidan get man ya wangale masa kofa saidaya daidaira parking tukunna Ammah ta bude tafito Jalilah ta biyo bayanta.
Kallon Jalal tai da ya gyara kwanciyar sa bashi da niyyar fitowa,dan India kafito mana jagora zakimin kuje kawai jan hannunta Ammah tai suka wuce tunda suka doshi parlourn suka fara jiyo hayagagar wata tsohuwa,iyee nifa wllh nagaji haihuwa biri biri kamar mage yaushema Kuka yaye wannan Yaron kalle shifa amma harkin sake haihuwa sakan duk dukiyar dana takoma hannunki to wllh bazata yiwuba ni intashi atutar babu.
Sallama sukai a parlon amma wannan tsohuwar bata daina masifar da takeyi ba,yawwa me Rukayya shigo kisamu waje ki zauna zama Ammah tai tana kallon hajjah ina wuni hajja ba gaisuwarki nake bukata ba haihuwar ki nawa daya hajja to Alhmdlh akamme ita zata saki takashi taita haihuwa ke da yake kinsan abunda ya kamata aigashinan haihuwa daya kikai.
Shikadai na haifa amma Sure shekara 7 ta haifi yara bakwai wace irin masifa ce wannan ninasha gumin dana da wahalar da harya kawo haka haka Kawai kuma saitazo tacika mana gida da yara to bazan lamunta ba ehe.Ayi hakuri hajjah ai haihuwa nufin ALLAH ce ke yimin shiru kekiyi mana in haihuwar dadi ce dole taje asibiti Adam yadda zaai da ita haba wannan jaraba haka.
Kalli yara kamar Yayan kiyasai duk inda na juya yara nake gani duuu kamar kudaje.Anty Zainab ta kalla datake kukan bakin cikin wannan suruka da Allah y hadata da ita ai ba Kuka zakiyi ba kiyi abunda nasaki shine kawai zaman lafiyarki agidannan wallahi,Fuuu hajjah tatashi tai part dinta tana sababi da masifar za acinye dukiyar danta.
Kiyi hakuri Zainab komai me wucewa ne haka Allah ya yota saidai kiyi hakuri kawai,wllh Ammah nagaji bakiga yadda a kullum take in mutunci na na na safe daban na rana daban yanzu da ban haihun bama haka fa zata dinga cin mutuncina kuma ko agaban wane bata ragamin kullum acikin kunci da bakin ciki nake haba dan ALLAH yaya ya ake so nayi.
Haka zaki daure kicinye jarrabawar da Allah yayi miki komai me wucewa ne hawayanta goge,sai Lokacin ta lura da Jalilah datai tsuru tana kallonta bataso taga mutum yana kuka fadi take amma wannan hajjar anyi shedaniyar mata, murmushi Anty Zainab ta sakar mata itace Jalilan taki murmusawa tai eh itace yaudai nace bana zo da ita banta ba zuwa unguwa da ita bag sai yau.
Ina wuni anwuni lafiya lafiya lau Jalila kai Ammah dama zaki barmin ita wah so kike hajja tacinna mata wuta jikokinta ma tana neman kai dasu bare ita bare,ai batayiwa bare tunda tasan tafiya zasi aa kafata kafarta babu wani dadin baki dazakiyi min,Uhm ai shikenan zo kidauki kanwar taki Jalila tasowa tai aka bata babyn kyakykyawa da ita Ammah mutafi da ita,rufan asiri inkaita ina aini yanzu na manta yadda ake raino danna na sameki nadan fara tunawa.
Kawota Jalilah maza kije wajan kannan ki kuyi wasa to ta mikawa Ammah babyn tashitai ta nufi inda yaga yaran zama tai akusa dasu,lah kema Agidan Ammah kike ya akai bamu sanki ba anan nake bakwa zuwa ne shiyasa baku sanni ba zamuzo in akai hutun school menene hakan toke bakisan schl ba daga kai tayi alamun eh to makaranta nake nufi.
Shiru tai dan batasan komai a harkar karatu ba waccan tsohuwar wacece,bata rai yarinyar tai kakar muce amma bata sanmu kai haba har kuma bataso na dauka babyn can cance kawai bata so harda mu,to ita kuma inane dakinta zo muje na rakaki to tashi tai suka rankaya gidan babbane sosai amma gidan Amma ya ninkasha a kyau da tsari har part din hajja ta rakata kinga part dinta zo mushiga mana make kafada tai nidai bazani ba duka na zatai,me kikai mata tace karmu sake matsawa inda take tunda mu yayan jarabane sai haifomu ake kamar qwari ita bata son yara shikenan bari ni na shiga mugaisa to anan zan tsaya
Dan madai daicin parlon take karewa kallo komai tsaf tsaf dan hajja badai tsafta ba,kai wanake ji anan nice kewa bakuwar da mukazo da Ammah to to aimata wadan can fitsararrun ne zauna ganinan fitowa zamatai akan sofa tana sake kallon ko ina,bayan mintuna uku hajja tafito hakora ta washe Allah sarki zauna yar nan.
Ina wuni ta gaida hajja lafiya lau yar nan kina lpy lafiya lau ina mamarki tana gida ku nawane agidanku nikadai aka haifa sake fadada fara'arta hajjo tai kaga irin albarka zauna sosai kinji tashi tai ta bude fridge damammiyar fura ta dauko mata sai tashin kamshi take ungo maza kisha aini akwaini da son yara amma kar su wuce daya zuwa biyu,makwat Jalila ta hadiye yawu.
Saukowa tai dirshan tafara shan furar me shegen dadi tana sha hajja na janta da hira sai data shanye tas sannan ta ajiye robar,duk dadinnan da kika ban bazai hana naci Ubanki anjima ba to bana tafi hajjah haba kekuwa jikata kiyi zaman ki mana ai karki damu zanzo na tayaki kwana anjima to! Aiko dakin kyauta zan gyara miki shimfida kuwa kiyi bacci ki more.
Zanzo kuwa karki damu tana fita taga yarinyar da suka zo tare zaune abaranda taso mutafi,naga kindade hajjan ce tace ki zauna ehman harta bani fura nasha ma me shegen dadi tab lallai kinyi sa'a tunda har hajja ta sakar miki fuska tabaki abunta uhm wai ya sunan ki Sajida sunana oh yayi dadi zo muje dakimmu.
Mrs Baba Bello Abubakar
No comments