Uncle J 37
Page 37
Parlo suka dawo kowa ya zabga ta gumi Iya dai ganin wannan zaman bana kare bane tashi tai tafara ayyukan ta.
Farka warta kenan daga bacci Ahankali ta sauko daga bed dinta kafarta ta kalla har Lokacin tanai mata zafi ya zama dole taje ta duba aikinta dan gaskiya matukar suna nan kalau dole ta rama abinda Jamal yayi mata dan akan murna taje ta taka kwalba wahalarta bazata tafi a banza ba.
Tana fitowa daga daki ta hango Ammah ta zuba tagumi cikin sanyin jiki tafara saukowa ahankali harta zauna Ammah bata san ta sauko ba, Ammah mene ya sameki sai Lokacin ta farga da sauko warta yadai Jalilah kafar tai sauki gyada kai tayi menene naga kin zabga tagumi kamar anyi mutuwa,uhm wllh su Saratu ne kwalara ta kama su abu kamar yaki suna can naga shiyan rai a hannun ALLAH.
Kamar ta taka rawa amma kawai sata kanne toh sukuma abinda ya same su kenan to ala Kyauta maganin masu shegen ciye ciye,au harke zakicewa wani me ciye ciye kidai yi ahankali kema karki jawo mana wahala muna zaman mu yanzu da kece ai Inaga sai qashi kawai zamu gani ajinki tsokar dai tagama karewa dariya ta saka ni Ammah ai ina da kiba eh gskiya fa naga alama sannu giwa.
Akallah su Mom basu suka farka ba sai kusan biyun rana Dad harya gaji dajira ya tafi meeting dinsa yayi muguwar makara,da kyar suka rarrafa suka shiga toilet kafafuwan suma bazasu iya daukar su ba.
Har daki Jalila tazo duba su sai kunshe Dariya takeyi bata tata suke ba yanzu shiyasa babu wadda ta amsa yajikin da take musu,ikon Allah waiku mena tsare muku agidannan baku da Lafiyar ma bazaku daina gaba dani ba gwarama ku sassautawa kanku nidai babu yadda zakui dani haka ta karaci neman tsokanar ta tafito ranta fes ganin kowaccen su sai Uban idanu awaje da goshi agaba.
Sunkai kusan 1 week kafin su dawo daidai ammafa ba karya sunji jiki awannan lokacin kuma Jalilah ta warke sarai tana ta warkajamin ta.
Gobe ne sunan kanwar Mom data haihu Jalilah sai murna take zasuje suna Ammah tace zataje da ita.
Jalilah koki tashi kishirya kona tafi asheke bacci ma kike tasha ban sani ba kafarta ta jawo azabure ta mike Ammah zanje karki tafi kibarni ke kika sani kuma nidai tafiya ta zanyi in har bakiyi sauri ba da gudu ta fada Toilat wanka ta burbura ta fito kayanta kawai ta dauka tasaka sababbine bata taba daka su sun mata kyau matuka,mayafinta ta dauka wanda Ammah ta siyo mata harda hijabai ta diddika mata.
Ammah na shirya to kin kyautawa kanki da kika shirya da wuri wane kayan zan saka ranar sunan basai kin dau kaya ba nayi miki anko rungume Ammah tai woo Ammata kina sona sosai kamar Innata murmushi kawai tayi naji dadi da dan India ba mace bane da yanzu harda shi zaki dinga siyawa,au ke kishi kike da dan Indian naki nikam eh bana so asiyamin abu asiyawa wani gaskiya wannan ma ai gasa ce bari ya jiki saiya daina siya miki kayan da kike sawa ainasan bazaki gayamai nafadi haka ba.
Muje ni kin tsaya shegen surutu dakin Jalal ta falla da gudu yana zaune yana danna laptop dinsa wani aiki yake ta sauri ya karasa ganinta kawai yayi kamar ancillota,sai haki take tana bude hanci,wash wallahi na gaji wai meyasa bakya abu na hankali kuma bana ce inkinzo kidinga tsayawa a parlo ba to dan India mene inna shigo dakinnan ban sani ba karki shiga hankalin ki zumburo baki tai ta juyamai keya.
Iyee ninake miki magana kike juyan keya to bakaine baka son ganina ba nibarama natafi,juyawa tai zata tafi cike dajin haushi ruko hannunta yayi ke baza ai miki fada ba sai kizo kinajin haushin mutum ko juyo da ita yayi hawaye ya gani shabe shabe a face dinta,me kuma akai miki bakai ne ba ok sorry me kikazo ki fadamin Unguwa zamu tafi da Ammah shine nazo yima sallama amma ka koreni,kallon ta yake komene abun Kuka anan oho.
To ya isa ina zakuje haka gidan suna kuma kwana zamiyi idanun sa ya waro kwana kuma har dake ehman bkaga na shirya ba,shine kika sha wannan kwalliyar banyi kwalliya ba,to ni kuma fa aina zaku barni kenan agida mana aikai kayi girma da zuwa Unguwa nidin eh kaifa uhm shikenan adawo lafiya.
Amma dan India bazaka rakamu ko bakin kofa ba tunda Saudiyya zaku tafi mezai hana ban raka kuba dariya tasaka yaushe zamuje Saudiyyar kefa babu mai akanki wllh fitani kin katsemun aikina,sai mun dawo zan kawoma tsara ba kaji to daga mata hannu yayi alamar byee,binta yayi da kallo harta fice dan murmusawa yayi yaci gaba da Aikin sa.
Kina can kina zuba kamar kanya ko,sallama naiwa dan India kin sanni Ammah duk me bani ina ganin mutuncin sa,af kenan ni bakya ganin mutunci na haba Iya aike ta daban ce keda kike bani abindadi ina zanki ganin mutun cinki,to yanzu naji magana har harabar gidan Iya ta taji su tanai musu adawo lafiya.
Baba direba ne zai kaisu har sun shiga mota ya fito face dinnan ahade baba kawai ya mikawa hannu alamun ya bashi key din bashi yayi,yana yi musu adawo lafiya Ammah ce take kallon sa baki bude kaida kace aiki zakai bazaka samu damar zuwa ba yanzu aikin ka gama kenan,um kawai yace dan India kaima kwana zakai banza yayi da ita zata sake magana Ammah ta maka mata harara komawa tai tazauna ta nutsu kamar ba ita ba.
Mrs Baba Bello Abubakar
........✍️✍️✍️✍️[7/30, 9:18 PM] AMINA KABIR CAPS: UNCLE J
No comments