Uncle J 35
Page 35
Tun tana zaman jiran Jamal harta gaji harabar gidan takoma tazauna batafi 20mnt da zama ba taji andanna hon mikewa tai dan taga wanda zai shigo shidinne kuwa dadi kamar yayi mata me da gudu ta ruga tunkafin ya gama daidaita parking yana budewa zaifito da sauri tarike mufin motar haba abokin dan India aiba saika wahalar da kanka kafito ba kabani kawai la juya abunda za ayishi asirri kuma akaga ma dawo aise agane ma.
Au bazan ma huta ba,to wane hutu zakai dan Allah kabani kajuya,daban kawo miki bafa kinsan yanzuma zan iya juyawa da abuna,kai aina sanka da imani bazaka iya komawa dashi ba Murmushi kawai ya saki to naji cikamin murfin mota nafito nasha iska badan tasoba ta matsa ranta harya fara baci yaba ta abu amma sai faman bata mata lokaci yake.
Ungo hannun ta harrawa yake gashinan kina zuwa kisha yanxu guda daya da safe daya da rana daya da daddare hakama ya isheki basai kin kara shaba komai zai daidaita,washe baki tai amma allai maka albarka da gudu tajuya tabar shi anan binta yayi da kallo yana girgiza kai gaskiya suna aiki da suka iya zama da Jalilah.
Dakinta ta fada saidata adana maganin hankalinta ya kwanta,kwanciyatai tana wake waken ta ranta fes tasan abunda ta taka allah alla take kawai dare yayi ita tasan irin tsiyar da zata shuka yau acikin gidannan.
Mom sai bayan La'asar ta iya tashi dakyar tadan cangala tanufi part din su cike da sakejin tsanar Jalal da Jalilah itakadai tasan abunda take ayyanawa azuciyarta dole ne sushiga komar ta.Bayan sallar isha'i suka hallara dan cin abinci babu wadda taiwa Ammah magana acikin su balle suyi mata Allah ya raya itama bata kula suba.
Ke tsohuwa iya ce tafito daga daki tatsani irin wannan kiran da suke mata,kije ki dafo mana tea tunda bakisan aikin kiba komai sai angaya miki kina gab da barin gidannan Mtswww taja tsaki babu yadda iya zatai haka ta juya,wani mugun Murmushi Jalilah ta saki dama tasamu,bakar munafuka tashi kije kuyi tare kullum saidai ki kalmashe kafa kizauna babu aikin fari balle na baki,hmm aiko baku fadaba ma dama tashi zanyi kusha kurumin ku.
Mikewa tai tana sakin murmushin samun nasara dakinta tafara zuwa kai tsaye saida ta dauko ajiyarta,hajiya Iya kawo nadafa dan nasan ba karamar gajiya kikai ba kamar ko kinsani wllh nagaji harna fara bcci wa yancan marasa mutuncin suka taso ni,sai hakuri kije ki kwanta kawai aiko Allah yayi miki albarka bari naje na kwanta,kisha baccin ki hankali kwance Iyata to saida safe Allah ya kaimu.
Tana ganin Iya tafita ta dauko magninta akallah ta zuba kusan guda goma tuni magani yaji ruwan zafi ya narke tas citta da kamun fari ta zuga duk masifar su babu yadda za'ai su gane,tsaf tagama saida kowa tacika mai cup taf sannan ta dauka daya bayan daya takai musu Mom ce karsha kaiwa saidata zuba mata rankwashi aka shegiya ragowar yunwa kullum ci kike amma ba agani ajikin ki kin kusa hada kayanki akoma gidan Inna da baba aci gaba dacin gabza.
Ko kala bata ce musu ba komawa gefe tai tana kallon su,to koke mayyace bazakisha tea dinnan ba shiru tai itafa babban burinta taga sun fara sha,suna sha suna zafinta da tsine mata Albarka,dan dacifa sunajin daci a tea din kinga Mom tsabar muguntar yarinyar nan tatashi tacika citta da kanin fari shayin har daci yakeyi,nima naji tsabar Iskanci ne da samun waje dan mukasa shako dayake ba ubankine yake kawo kayanba to sai munsha saidai ki mutu.
To da mubata tasha ba Gwara mun zubdashi a rariya ba wllh kuwa,tas suka shanye tea saikizo kidebe cups din kuma kitanbatar kin wanke su shiru kake ji Jalila ko kanzil bata ceba abin fa ya basu mamaki yau yan rashin kunyar ne basa Kusa🤣🤣🤣basu san tsiyar data kulla musu ba,tana shiga Kichin din tai wulli da cups din biyu suka fadi suka tar watse rawa kawai tafara tika tsabar yadda farin ciki ya cika mata Zuciya.
Bata ankara ba kwalba ta shige mata kafa tsabar yadda take cikin farin ciki batasan ma cups din sun fashe ba kara ta kwalla tarike kafar ta tuni jini ya fara malala akwaita da tsoron taga jini kuka tafarayi tana yarfe hannu,wayyo ALLAH Ammah dan India kazo ka cecan jinina zai kare.
Dawowar sa kenan daga hospital ya bala'in gajiya tunda ya shigo yaga su Mom ya hade face kamar be taba Dariya ba harya taking steps yafara jin kamar kuka a kiching dan jim Yayi jin ana amtar dan India lokaci daya yagano ko wacece,hakiman suna zaune kuma sarai sunajin kukanta amma babu wadda ta nuna tajima koda wasa.
Da baya ya dawo hanyar kiching din yayi cikin sanyin jiki gaba daya yagaji da fitinar Jalila dole ne yasan yadda zaiyi da ita Bazata kashesa da ransa ba,tsayawa yai yana kallonta ganin yadda tai kaca kaca da kiching din ga glass din data tarwatsar akasa,kuka tasake fashewa dashi dan Allah takwarana kazo kasamin magani karjinina ya kare.
Ware idanun sa yayi akanta wai takwaranta lallai yarinyar nan tama raina shi,hade face yayi dawa yakawoki kiching din wllh tsautsayine nidai katemaken cike da takaici yake kallonta kafarsa daya yasa akiching din ya figota zaka karyan hannu dan India kasake ni banza yayi kamar be jita ba.
Saida yakaita har dakinta sannan ya dangwarar da ita bakaramin jin zafin yarda itan da yayi tajiba,kara tasaka Ammah dake shirin kwanciya a sukwane ta fito,ke meyake faruwa kike wannan karar ganin Jalal adakin yasa ta dakata tana kallon su Fuuu yazo ya wuce Ammah ko hutawa beba kansa yadau zafi tazo takara zafafa shi tsaki yake ja ajejjere.
Innalillahi Jalila garin ya kikaje kika taka wannan kwalbar,nima Amma a kiching na taka bansan wanda ya fasa ba dama ansane tunda ansan zan shiga naje na taka,dama kina shiga Kichin ne da har za'a ajiye kwalba saboda ke bana son karya kifadamin Abunda ya faru gaskiyar kenan Ammah,to aishikenan ni yanzu yaya zanyi dake saidai Jalal yazo ya cire miki.
Dakin Jalal Amma ta nufa yana tsaye gaban dressing mirror dinsa,Jalal kaifa nake jira ga Jalila can tana ta faman kuka kasan dai bazan iya cire mata ba kaine zakai wannan aikin wuce muje,rai bace yafita sai yayiwa Jalila mugun duka zata shiga hankalinta,har Lokacin kuka take tsugunnawa yayi agabanta ya rike kafar kwalbar tashiga sosai.
Da kyar ya samu ya zare ta zuwa lokacin hawayan Jalila sun kare sai ajiyar zuciya da takeyi wanke kafar yayi ya samata magani yana gamawa ya cika mata kafar yayi gaba,jarababbe tunda kayi mata aishikenan zama Ammah tai akusa da ita tanai mata sannu lamo tayi kamar me bacci wannan fa shine anyi ba aiba tunkafin abinda ta aiwatar ya fara aiki abu yana neman komawa kanta.
Mrs Baba Bello Abubakar
No comments