Recent Updates

Uncle J 34

 


Page 34


Mom ba karamar wahala tasha ba kan agama gyaran ta tainewa Jalilah yafi akirga,haka kuma Jalilah bata fasa yi mata dariya da waka ba,yana kammalawa ya sakar mata kafa tabishi da harara dan acewar ta da mugunta ya dinga matsa mata kafa,su Rufaida ta kallah da suka kunshe dariya duk wanda zaiga Mom awannan halin dole ya dara ko yaya ne kuwa.


Dukan kafadar Jalal yayi mutumina baka da dama kana gani mamarka tana ihu da neman dauki kaki zuwa ka rarrashe ta,harara ya wurga masa karka sake hadani da ita ko ahanya wllh in wannan ce tahaifeni ai banzo duniya a sa'a ba Murmushi kawai Jamal yayi to shikenan tunda haka kace dadai yafi maka gwara kayi abunda ya kawo ka.


Gyara zaman sa yayi aikasan meya kawoni wai Jalal meyasa kake da taurin kai karatun da zamu karo na 2years amma ka gaddame baza muje ba mekake tunani,iska ya furzar me zafi bana sha'awar sakeyin nesa da gida gaskiya matukar saina karo karatu za'a karan matsayi na hakura kayadda ka hakura daci gabanka mene aciki biyammu fa zaadinga yi muna karatu muna daukan salary,uhmm zan duba sarkin naci bazan can naci bane gaskiya ce.


Zanzo na sanar da Ammah da kaina tunda ni ancema bani da baki ko,ah ainaga kanaso kai mana sakiyar daba ruwa ne,kuma nasan Dad yana sane yayi biris ya kyaleka nan gaba fa kai zai dorawa Alhakin kula da Asibitin nan shiyasa yake so ka karo karatu amma narasa menene yahau kanka kodai kafara soyayya ne ban saniba, àah soyewa na farayi kyalkyalewa da dariya Jamal yayi gwara dai ka fadi gaskiya mutumina dan murmusawa kawai Jalal yayi besake cemai komai ba.


Harya tashi tafiya bega Jalila ba yana fita ya hangota a harabar gidan tana tsalle tsalle kai wannan yarinya bata rabo da wasa,sai lokacin ya kare mata kallo saiyaga kamar ba itaba takara girma ta kara haske kayan jikinta ya kallah yana da tabbacin Ammah ce ta siya mata.


Ganin yafito ta rugo da gudu tana haki tsayawa tai agabansa tana haki yadai Jalilah gudun me kikeyi haka kamar wadda za'a kama,canza fuska tai tana yamutsa ta abokin dan India dama tambayarka zanyi to inajinki kaima kana allura da bada magani kamar yadda dan India yakeyi,cikin Dariya yake fadin Inayi mana aikinga aminan junane na amana washe baki tai yawwa ta kwana gidan sauki.


Dama magani nake so kabani,name kenan akalla nakai wata guda banyi bayan gidaba shine nake so kabani maganin da zanta tsuga gudawa saina yi biyan bashin na baya dan bakaji yadda ya dankare min acikiba,ke Jalila bana son karya yaushe bayan gida ke makalewa mutum aciki,to tsayama meya hana kitambayi dan India saini bakar fata dan Nigeria,to aikaga garinmu daya kenan nidakai shikenan saika bani basai wani dan gari daban yaji sirrimmu ba.


Kallonta kawai yake waishi zataiwa wayo kuma kinyi magan mekyau yanxu yaushe kike so,katemaka kawon yau saboda bana iya bacci yadda naga rana haka nake ganin dare ok shikenan zan kawo miki nan da anjima,dama nasan kanada mutunci amma karka bari kowa ya gani meyasa,matse kwallah tai saboda kar hankalin su ya tashi shiyasa gwara ayi komai cikin sirri.


Ok saina zo anjimar,ngd zanjiraka anan harka dawo girgiza kai kawai yayi wannan yarinyar badai drama ba,tsalle ta daka cike da farin ciki ta koma parlo dadi kamar ya kasheta, Rufaida da Salima basa parlourn sai Mom da take baccin wahala bararrajewa tai babu abinda ya dameta ranta fes.


Ammah oyoyo tatashi da gudu ta rungumeta oh Jalila danja fatan dai ba wanda kika tsokana fada,dawa zanyi fada ai babu sa'a na a gidannan kuma kin sanni da hakuri ko ammin saidai na kauda kai naji nasihar da kikaimin ta hakuri kuma nadauka,kai Alhmdlh haka nake so kizama ainama zama Ammah tun tuni,hannunta ta kalla mekika kawon mezan kawo miki kuwa daga Asibiti nke fa.

Au wai baki da lafiya kalau nake haihuwa akai kece kika haihu kai Jalila wllh kincika tambaya kibarni na huta haka ko kinganni da ciki bare na haihu,aini Ammah Innata nikadai ta haifa bantaba ganin cikin taba na sani ko ciki ne dake kikaje kika haihu.To! bani bace kanwa tace zaki dani suna zanje dake zata sake magana Amma tarufe mata baki kiyiwa Allah ki kyaleni inaga aikin Jarida zaki karanta kowa ma ya huta.


Gaba tai tabar Jalila sam bata gaji ba in zasu wuni atsaye bazata taba gajiya ba,kallon Mom tayi datai rashe rashe tana bacci ke lafiya kuwa saratu take wannan baccin kalau take cinnaka ya shige mata riga shine taita kuka harda fitsari ke kauce nan ban yadda da wannan zan can naki ba na kanzon kurege.

Sama tahau tabar Jalilah anan kamar megadin Mom kar wani abu yazo ya dameta nan ko dariya takesha yadda Mom ta hangame baki tana sharar baccin wahala.

             Mrs Baba Bello ABUBAKAR

No comments