Uncle J 33
Page 33
Ni kuke yiwa wannan rashin mutuncin Kamar ba Uwar ku ba,to Mom dan kin haifemu kuma shikenan sai akace mu bayinki ne nidai Allah saidai ki kwana anan,Kuka mom tasa sai kuma kiyi gaba Salima tai tabar Rufaida a tsaye to nima bazan iya wannan jegon jakar ba aisaima ki karyani sai kin taho,itama sauka tai suka bar Mom jabe akasa kamar kayan wanki takaicin duniya ya gama cika mata zuciya.
Duk abinda sukai mata bataji wani abuba Jalila kawai ta dorawa alhakin haka kuma dole tagirbe abunda ta shuka mata,dajan jiki ta samu tafito daga dakin dakyar kamar yadda suka cedin da rarrafe ta fara tafiya tuni ta hada gumi tai sharkaf sai haki takeyi kamar zata shide dan azaba.
Jalila ce ta futo tana shan chocolate hango Mom tana rarrafe yasata rugowa da gudu shekewa tai da dariya wai wayaga gwangwarasa wllh Mom ko fasali bakiyi da rarrafan ba na tabbatar koda kina yarinya bakyau kikai ba sanda kina rarrafe,dariya ta sake fashewa da ita,muje na take miki baya kinga ba abarki kekadai ba karkije kizame kifasa baki.
Duka ta kawo mata afusace wllh duk ranar da kika shigo hannun na saikin gane baki da wayo matukar ni Saratu na haifu saina baki mamaki Duk iskancin ki na dameki dani kike xancan zakiga abinda zai biyo baya,ah nisaidai naga alkhairi duk wani shige da fican mutum akan idanuna kuke namiki alkawarin matukar ina Numfashi bazaki taba cin nasara akan Ammah da dan India ba nasan dai waccan me zubin samudawar kike so ki manna masa to kwalelen kare da hantar kura.
Buga cinya tai tai gaba tabar Mom sake da baki kirjinta na dukan tara tara aina shegiyar yarinyar nan tajiyo zancan nan,anya mutum ce ba aljana ba metake nufi da bazata taba bari aci galaba akan Ammah ba kodai tasan kudurinta,kai bata sani ba wama zai gaya mata bata da wayon da zatace ta karanci abunda mutum yake kullawa,sainaga bayanki Mom ta fada cike da cin alwashi.
Dakyar Allah ya taimaketa ta sauka guiwowinta kamar zasu cire bajewa tai aparlo tana shan iska kafarta ba karamin ciwo take mataba harta fara kumbura daga gani targade ta samu.
Jamal ne yayi sallama akofar parlon hango Mom abaje akasa tana numfarfashi yasashi shigowa da sauri subahanallahi Mom menene ya sameki haka,cikin bakin ciki take dubansa tunda shima abokin Jalal ne yana cikin makiyanta,nafadi ko aka kayar dani,wa yakayar dake Mom ina wata matsiyaciyar yarinya yar aikin da uwar Jalal ta kawo itace taimin wannan aika aikar,tana fadin haka ya gano watake nufi.
Ayyah abu beyi dadi ba gaskiya bata kyauta ba kaida kasan ya kamata kenan tsugunnawa yayi yana kallon kafar gaskiya dole sai angyara miki kafarnan to indai zan iya takawa a gyaramin, gyara zama Jamal yayi yadda inya damki kafar Mom bazai sakiba saiya gama aikin sa.
Yana rike kafar tunkan ya fara gyaran Mom tafara wash wash gaskya da zafi hmm zaki bayani nan gaba,fara gyarawa yayi tun Mom na daurewa saiga mom tafara kwarara ihu tana dukan sa ya cikata kememe Jamal yaki cika mata kafa tsananin azaba ta ishi Mom tuni tayi cilli da dan kwalinta.Jalilah dake wasa adaki jin kukan Mom yasata fitowa asukwane haka Jalal har gware suke wajan saukowa suga meke faruwa.
Tsaki yaja hango Jamal azaune yawani gwagwgwafe yanai mata gyaran targade juyawa yayi ya koma inda yafito,jalila rike ciki tai tana tikar dariya mom shabe shabe take kuka tai wujiga wujiga,tashi tai tana rawa da tsalle me kuka tana dariya ai mata dan kwadan daddawa,rufaida da salima ne suka shugo asukwane suma turus sukai ganin yadda Mom take gursheken Kuka ga Jalila agefe tana rawa da waka.
Jamal gumtse dariyar sa yayi shikansa dariya cinsa takeyi bilhakki take kuka babu algus ba ha'inci,samun waje sukai suka zauna zubawa Mom ido sukai abunma ba karamin haushi ya basu ba dan wannan gyaran takewa kwaroro to,ko sannu babu wacce tai mata acikin su kan agama ai tuni Mom ta tsula fitsari zirrrr saiga fitsari yana gudu.
Mom fitsari fa kikai cewar Salima ah lallai Mom nayadda da irin azabar da kike sha,gaskiya Mom ke bakaramar raguwa bace Kuka fa kikeyi ni wllh kinma badani kizauna agaban dan cikin ki kidinga wannan kukan kin barar mana da mutunci wllh,to dama mutuncinne daku da harza abarar muku kungama zubdashi tun atiti,dawa kike ah da wanda ya tsargu zakici Ubanki.
Biyota da gudu Rufaida tai dan taci alwashin saita ragar gajewa Jalilah baki duk yadda taso kama Jalila kasawa tai sai wahala data ke sha sai haki take,nifa bazan taba gajiya ba dama na kwana biyu banyi wasa ba ga abokiyar wasa hargida dan kanta tagaji ta kyaleta ta lura ba kamuwa zataiba walahar dakanta kawaii take.
Mrs Baba Bello Abubakar.
........✍️✍️✍️✍️
No comments