Uncle J 32
Page 32
Wani ashar Mom ta lailayo ni kike fadawa haka cigaba tai da hawowa tanayi tana masifa saita zubarwa da Jalila hakwara inta shigo,karkashin gado Jalila ta leka tajawo bakar ledar data adana budewa tai aguje ta fada Toilat ruwa ta kam fato a cup ta zuba karkashin data dauko me uban yawa kofar dakinta ta kwara shi ta tura kofa ta yadda babu yadda za aita lura dashi.
Afusace Mom ta banko kofar ta fado dakin zuuuu tatafi santsin karkashin yajata ji kake kum ta buga kanta ajikin madubi sai jini tsananin azabar data ratsata tasata sakin kuka,dariya Jalila tasaka harda tafi wooni Jalila yanzu saiki tashi kidakenin ai gani anan indai zaki iya kitaso Mom,karar da mom tasaka itace ta tayar da Jalal daga bacci tsaki yaja wacece wannan zatazo tadinga yimusu ihu.
Futowa yayi rai bace bega kowa ba hango dakin Jalila da yayi abude yasashi nufar wajan Mom ya hango yashe akasa rike da kugu ga kafarta da takeji kamar ta karye,Jalila ya kalla wadda take tikar rawa gaba daya batasan da tsayuwar shiba girgiza kansa yayi ke yar kauye juyowa tai da sauri bata rai tayi,kallon Mom yayi data cika tai form kamar zata fashe tsabar takaici da bakin ciki.
Ko kallon ta bebe ya tsallaketa Jalila datai kalar tausayi matsawa baya take fuska amarairai ce kan yayi hakuri karya daketa,kunnanta ya kama ya jata dole tabiyo shi jin yana barazanar cizge mata kunne dan Allah dan India kacikamin kunne karkacire min ka tsaya nai maka bayani bani da hannu a faduwarta wayyo gwaggo zai cire min kunne tagaban Mom suka wuce anan suka barta sake da baki ta bisu da kallo.
Saida ya shiga part dinsa tukunna ya sakar mata kunne wash wllh kunnena kamar ya tsige rankwashi ya kaimata aka,meyasa kika kayar da ita ni babu ruwana tahowa tai zata daken akan banje nayi aiki ba shine Allah yasa kamin tunkafin takara so,karya kike wani abu kika samata ta fadi yanzu saikije kisan yadda zaki da ita,haba dan India nidakai fa bata baci bansan haka kake da mutunci ba sai jiya har abinci kadinga bani abaki.
Ashe dai kana sona harara ya wurga mata yimin shiru da bakinki awajan shiru tai dan yanzu kaf Gidannan tafi ganin mutuncin Jalal babu abunda zai sata bata aikata ba,tsaki yaja kansa harya fara ciwo saboda ya tashi baccin be gama sakin sa ba.
Kan sofa ya zauna TV ya kunna tuni Jalilah tai gaban plasma taiwa kanta matsugunni aduniya tana son kallo sai dariya ko take dama dan ita ya kunna kozata barshi ya huta.
Mom kuwa wani kululun bakin ciki yazo ya tokare mata a kahon zuciya har ita za aiwa wannan rashin mutuncin yakamata fa tafarka daga baccin daya fara daukarta itace fa Saratu wadda bata ragayya bata sanayya intasa kanta abu saita aiwatar kwafa tayi,Iya ta kwallawa kira da sauri Iya ta hauro harara ta wurga mata tsohuwar munafuka kema zan dawo kanki tare dake aka hada baki harna subale batare dana sani bako.
Wllh Hajiya banda masaniya ke dallah yimin shiru bakinki sai faman hamami yake wuce ni kikiramin su rufaida suzo su fitar dani daga dakinnan,juyawa tai cikin jin zafin abunda mom suke mata sanda taje part din suna bararraje a parlo kowacce daga ita sai vest da gajeran wando,Allah ya shirya Iya ta fada azuciyarta kuje Hajiya tana kiranku tafadi ta kasa tashi ne.
Kallon juna sukai tafadi kan sugama tan tancewa tayi juyawarta sunkai mintuna biyar kan Salima ta mike tanajan tsaki wai Mom meyasa zata dinga abu kamar yarinya bazata dinga kallon gabanta ba intana tafiya saita jawo mana wahala,nima abinda nagani kenan suna kumbura suna komai suka fita parlon kallon parlour sukai basu ga alamun wata Mom ba itako tana hango su kwala musu kira tai.
Kun ganni nan sai Lokacin suka hangota dabar azaune hawa sukai suna tunanin meyakaita dakin yar kauyan nan saura kadan Rufaida ta zame dakyar tasamu tarike kofa,haba Mom aisai kigaya mana Halin da dakin yake ciki ba kibarmu a duhu ba salan mufadi muzama daya mudake wannan dai ba rayuwa bace,ni sanda zan shigo dakin gayamun akai niba wani surutu ba kukamani ku saukar dani.
Me! mune zamu dauke ki tundaga sama har kasa gaskiya bazan iya ba bansani ba ko Salima zata iya wannan aikin,kema da kike yar gwal bakiba saini wllh bazan ba nima, wannan ai wahala ce ki sauko da rarrafe mana aizaki iya.
Mrs Baba Bello Abubakar
.......✍️✍️✍️
No comments