Recent Updates

Uncle J 31


 Page 31


Sai data idar yasake dagata tea yafara hada mata da kansa ya dinga bata saidata shanye tas,Lallai yarinyar nan badai ciba duk cutar da take kalli ta bude ciki tana dirkar abinci,abinci ya zuba mata dan kadan spoon ya dauka yana bata saiga Jalilah ta lamushe abinci wanda yadebo nashi da nata duk sai data hada ta cinye ya yadda ba ita kadai take cin Abincin nan ba harda aljanun ta.


Magani ya dauko zai bata nanfa Jalila tace batasan zan canba tuni ta fara Kuka,hade face yayi kodai kisha maganin nan wllh kona danneki na dura miki kememe kinsha tai gata da shegiyar kafiya da taurin kai bayadda beyi da ita tasha maganin fir taki,cup ya shiga Kichin dinsa ya dauko gaba daya maganin ya hade mata waje daya ya zuba ruwa a cup din saidaya tabbatar ya narke matsowa yayi kusa da ita babu damar tatashi tagudu matsa daya yayi mata ta kasa motsi yadda akewa yara dura haka ya dura mata tana kuka tana komai saida tasha.


Saidaya tabbatar yagama dira acikinta sannan ya saketa harara ya zabga mata kazama kawai yar kauye Kuka ta sake fashe dashi kamme zaice mata yar kauye Murmushi kawai yayi tunda bakya son sunan nan aiko na samu abinyi,malama yimin shiru ko yanzu nasake dura miki maganin shuru tai gaba daya bakinta ya kauraye da azabar daci ganin yadda take ta ya mutsa fuska durowar jikin gadon sa ya jawo saiga chocolate kala kala daukowa yayi ya bare ya samata abaki tuni Jalila tai shiru taji zaki sabanin dacin daya addabi rayuwar ta.


Ai tunda ka nunamin wajannan nasamu na zuwa nasha alawa saina shanye ta tas zakasan ka duramin magani mitar da takeyi kenan oho bemasan tanayi ba laptop dinsa ya dauko ya rage aiki sosai sai wajan 12 yagama kashe laptop din yayi sam ya manta da wata Jalilah adakin saidaya juyo ya ganta kwance a wajan datai sallah ta kudun dune a hijab din Ammah.


Hijab din ya cire mata ya kwantar da ita akan bed ya jamata blanket,parlo ya koma kan sofa ya kwanta yasan yau ba Lallai ya iya bacci ba besaba da kwanciya akan sofa ba to waccan magajiyar tazo ta gajemai shi kuma gaskya bazai iya kwana waje daya da ita ba duk da yarinya ce yana ganin hakan be dace ba.


Besan sanda bacci yayi awon gaba da shiba,kiran sallar farko a kunnan sa akayi shi mikewa yayi gaba daya jikinsa ciwo yake ga kwannan takura ga gajiyar da yayi ta dawainiya da Jalila kafadunsa wani shegen ciwo suke, toilet ya wuce yayo Alwala nafil fili yayi kafin yaji ana haramar tada sallah ya fita Masallaci,sai wajan 6am ya dawo har Lokacin Jalilah tana kwance tana sharar bacci.


Gsky Bazan iya sake kwanciya anan ba bedroom din ya wuce  bed din ya hau can nesa da Jalila ya kwanta dan danan bacci yayi awon gaba dashi.

Ta dade da farkawa amma gaba daya gabobinta har wannan Lokacin ciwo sukeyi ahankali tatashi zaune ba laifi ba kamar jiya ba juyawa tai tana kalle kalle da tunanin a ina ta kwana hango Jalal tai yana baccin sa hankali kwance,waro idanu tai tab dama adakin dan India na kwana gadon ta kalla shikansa bed din abun kallo ne ga shege laushi kai ita dai tasha dadin ta.


Ashe haka yake da mutunci data sani da batai masa wannan muguntar ba kalli yadda har abinci ya dinga bata abaki,sauko wa tai kamar me koyan tafiya dakinta tatafi saidatai wanka sannan tai Alwala sai Lokacin tai sallar asuba,awajan ta sake kwanciya har Lokacin batajin dadin jikinta.

Salamu alaikum iya ta rangada sallama adakin Jalila sannu yar nema kinanan kina bacci kin barni inata faman aiki to wllh tashi zakiyi yanzun nan kafar ta tafara ja ke Jalila tashi kitashi kikama aikin ki,tashitai cike da jin haushin iya haba iya saboda Allah yanzu bazaki barni nayi bacci ba,jakar Ubanki bacci kikazo yi nifa nalura Jalila bakisan abunda ya kawo ki gidannan ba,kawai kifito fili kice kinfara yimin hassada da bakin ciki to inba hakaba ina ruwanki dani.


Au nice ma nake miki hassada da bakin cikin masu gidan sukace nata soki kifara aiki bazaki dinga ci kina kashi ba, to kije ki gaya musu nace bazan zo ba duk shegiyar data isa tazo ta daukeni inanan ina jiranta,dafe kirji Iya tai to badani ba sai dai kije kifada musu da kanki amma baza aji mutuwar sarki abakina ba keta shafa amma nidai kigaya musu sakona bazan zoba uwar su tazo ta daukeni.


Harta kwanta ta mike saboda ma kina bakin ciki da rayuwa ta da yanzu andade dayin jana izata shine bakimin ya jiki ba kinkama fadin nafito nai aiki nifa innaga dama zan Iya cewa nadaina aikinnan tunda nazama yar gayu gaskiya zan fadawa Ammah asamo wata ni na yaye kaina,ashe koma warki kauye yayi babu inda zani ina gidannan kuma bazanyi aikin ba kizuba ido kiga ikon Allah saidai na hangoki kina ta aikin wahala inai miki gwalo.


Zangani kuwa dan kika daina aiki nima denawa zanyi dariya Jalila tasa to kidaina mana Iya wai Meyasa kike son gasa dani kefa kin kusa mutuwa niko yanzu nake karama keko kin fara jiyo kamshin mutuwa,Kuka Iya ta fashe dashi dan arayuwar ta tsani ayi mata zancan mutuwa,Allah ya isa tsakanina dake Jalila na tabbatar bakya kaunata tunda kikemin fatan mutuwa.


Nifa ba fata nake miki ba kawai duba nai da yadda kika fara tsufa nan da kowane lokaci zaki iya arangama da mutuwa duka ta kawo mata ta goce tana dariya dayi mata gwalo,ganin inta biye mata ita zata bata ranta abanza,daga murya tai kice musu bazan zoba din suzo sujani,karaf akunnan Mom data hawo taga ubanda Jalila takeyi Acikin dakin.

        Tofa kaka kara kaka ga Jalila ga Mom kubiyoni dan jin yadda zata kaya.

             .......✍️✍️✍️✍️[7/28, 2:13 PM] +234 903 511 7

No comments