Recent Updates

Uncle J 3

 


Written and Narrated

By KULSOOM ISAMA'IL IDRIS

Page 3

Gidan Gwaggo suka shiga itama har Kuka tayi daga musu hannu sukai tayi har suka dena hango su tunda sukai nisa Jalila ta

manta da wani kewar gida duk wanda tagani dagamai hannu takeyi tatafi Birni sai alaraka taki gona akeyi sai murna jama,ar gari keyi yau dai sun rabu da alakakai.

   Ganin abun na Jalila bana kare bane Indo taja hannun ta tasha suka nufa suna zuwa mutum daya dama ake jira anata kaduna kaduna shiga sukai Indo tadora ta akan cinyarta dan danan direba yaja mota suka tafi tun Jalila na kalle kalle har bacci ya kwasheta.

11 dai dai suka sauka daga mota mashin ta tsare musu suna soma tafiya Uwar dakinta takirata akan ta wuce da Jalila gidan kawar tata,da yake tasan Gidan dan mashin din tafadawa inda zai kai su,wata hadaddiyar unguwa suka nufa shiru kamar ba mutam me numfashi a unguwar kowa na gidan sa.

Wani tan game man gida suka nufa tunkan kashige shi kasan an narka dukiya acikin sa,wasu fulawoyi ne masu gwanin birgewa suka zagaye katangar gidan tundaga waje.

Jalila dai kanta kamar zai tsinke sai mika wuya take tana kallon gidaje tsararru ba irin na kauyan su ba,kwankwasa get Indo tai wani buzu ne ya leko ta wata yar karamar kofa ganin ya santa karamar kofa ya bude musu suka shiga.makeken gida ne me girman gaske shuka ce kala kala kai zan iyacewa akayan fruit babu abunda babu.

Makwat Jalila tahadiyi miyau kai ashe zatasha gara ashe abirnima akwai bishiya bata sani ba,yan Aikin gidan gaba dayan su maza ne sai wata dattijuwa shine dalilin da yasa tanemi asamo mata yarinya mehankali wadda zata dinga taya Dattijuwar ayyuka,babban burin Jalila ta ganta akan bishiyar wani mangwaro data hango fes fes irin binta sugannan ne.

Kaida kaga Jalila basai angaya makaba kasan daga inda tafito,kofar parlon suka nufa itakanta kofar me azabar kyau ce da tsari.

Kinga Jalila muka shiga kikame kanki karki abunda zaija tace bakiyiba ajuya dake kauye,tab ni banda hankali zan shigo wannan gidan nafita ai nashigo kenan bafita karfin hali abunda Indo tace kenan to zako kiga ikon ALLAH karki nutsun in bata dauke kiba aidole kiyi waje.

Norking Indo tayi sunkai kusan mintuna biyu akazo akabude kofar wannan Dattijuwar ce da fara'a take kallon Indo danda akwai sanayya atsakanin su maraba kushigo mana cewar matar suna saka kafara su aparlon Jalila rai saurin da wowa baya danji tai wani suuuu wani abu me santsi taji tataka kamar zai kayadda ita

Taho mana Jalila so kike nafadi nakarye kina gani sun zuba mai adakin su salan haka kawai su cucan amaidani kauye nazo kenan harda su murguda baki aiko zan maidaki tunda baki da kunya.

Saida kyar tasamu Jalila tashigo makeken parlourn daya gaji da haduwa kamar me koyon tata haka Jalila tafara takawa daga karshe tsugunnawa tai takama rarrafe danji take kamar zata subale tafasa baki,cikin takaici Indo take kallonta ganin yadda take nema tabayar da ita tajawo Hajiyar ma tace tafasa,ita kanta Dattijuwar nan Dariya take sha ta tabbata wani babban comedy aka kawo musu.

Tsakiyar parlourn ta zauna tana zazzare ido gasanyin Ac yafara ratsa Jalila harwani lumshe ido take yi,ido hudu sukai da makekiyar plasma wayyo zokuga yadda Jalila tasa ihu saida suka razana gaba dayan su,adaidai lokacin wata hamshakiyar mata ta sauko kyakykya wace kamar balarabiya haka take fuskarta dauke da mirmushi akalla zatakai 50years amma jindadi ya boye shekarunta saika dauka batafi 40years ba.

Ganin su atsaye cirko cirko suna kallon ikon ALLAH dan Jalila fashewa tai da kuka baki bude suke kallon ta,ganin Hajiya ta sauko yasa Indo kama hannu Jalila datake gursheken kuka tazaunar da ita kan sofa Hajiya taiwa kanta matsaugunni.

Indo ta kalla kukan me takeyi haka Indo,wallahi Amma ban saniba kawai gani mukai ta fashe da kuka,kallon Jalila tayi ya akayine yammata saida Jalila aka fyace hanci tuni kwalliyar zuwa birni ta cakube fuska tai dama dama ga dauda ga uwar hoda data lancaba saita bada wata kala daban.

Wallahi Hajiya bakomai yasani kuka ba ashe kunanan cikin Aljannah muko mumacan cikin Jahannama to wallahi nazo kenan bazan koma ba ni ashe anjima ana cutata ban saniba ji wamcan katuwar TV ko rabi rabin tagidan Maman ladi batakai ba kai bama irinta bace kalli kan wani abu dakika zauna daganinsa zaiyi shegen laushi jiwani abu da kuka shimfede wannan uban wawakeken dakin.

Tunda nashigo banga kasaba muko munacan muna fama dajar kasa kema Hajiya dazakimin adalci nace zan koma kauye wallahi kyasa akaini gidan Mahaukata dan kinsan ba kalau nake ba.

Kalli fatarki subul subul inaga tunda aka haifeki a inji ake miki wanka.

Dariya suka fashe da ita har Hajiya jin shirman da Jalila takeyi to banda abinki waya gaya miki nance Aljannah aike Hajiya kingama shiga Aljannah tum tuni nice dai sai yanzu ALLAH ya kwatoni,àah Gwara dai nashiga ta gasken cewar Amma cikin zuciyar Jalila kuwa ayyana wa take amma wannan matar bata da godiyar ALLAH duk wannan dadin bemata ba wani take nema zata sake magana Indo ta rufe mata baki.

Waike Jalila wace irin yarinyace da bakin ki baya shiru wallahi matukar baki kama kanki ba zan maidakine ai miki Aure shiru tai dan Aduniya tatsani ayi mata zancan Aure badan taso ba tai shiru amma bawai dan tarasa abun fada bane.

Sai lokacin suka gaishe da Amma hakamma saida Indo ta kiftawa Jalila ido hankalinta yanacan wajan kallon plasma.Gatanan Amma inafatan tayi miki cikin murmushi take fadin tayimin sosaima kuwa gashi daga zuwanta tafara sani Nishadi kinga nasamu medebe min kewa tunda duk basa nan yaran.

Cikin jindadi Indo tace to Alhamdlh tafiya tayi kyau angode Hajiya Amma Dariya tayi babu komai Indo ina Hajiya Maimunan ai dawowata yanzu tace nafara kawo ta kunsake yin waya eh hakane kin kyauta ya sunan yar tawa Jalila kama baki tai kai suna medadi yanzu ki tashi kuhaura sama kinuna mata dakinta,koma dai barshi na kaita da kaina to Amma angode ALLAH ya saka miki da Alkhairi babu komai.

Bana tashi natafi kudi tadauko ajakarta gashi kyayi kudin mota ko amsa tai angod ALLAH ya kara arziki ameen,kallon Jalila tai bazaki rakani ko bakin Get ba kallon Indo tai lallai baki da hankali,um nagaji nibazan iya tashiba ma sarai Indo tagane manufarta karta futa kanta dawo arufe kor parlon dariya tai tana girgiza kai lallai jama'ar Gidan nan zasu sha fama sun hadu da daidai da su.

Dan tasan za asha gwagwar maya yi tafiyarki Indo tunda tace ta gaji sallama tai mata tare da sake jawa Jalila kunne akan ta kama kanta agidannan banda shiga abun da babu ruwanta to tace mata to wama zata takala fadan indai bada Hajiya zatai ba itadai bataga kowa ba sai Hajiyar zuwa bakin Get ma akwai tafiya medan nisa.

        TAKU MRS BABA BELLO ABUBAKAR.

[7/28, 9:35 AM] +234 903 511 7917: UNCLE J

Written and Narrated

By Kulsoom Ismail Idris


No comments