Recent Updates

Uncle J 28

 


Page 28


Ammah wata shawara na yanke mezai hana akai yarinyar can makaranta hakan zai taimaki rayuwarta sosai zata rage wannan rashin jin da takeyi da giggiwa da rawar kai,numfasawa tai to banki ta taka ba Jalal amma kana ganin iyayanta zasu amince kuwa zasu amince Ammah aiba daina biyanta albashi za aiba za aci gaba da bata kamar yadda aka saba.


Ni zan dauki nauyin komai na karatun ta uhm Murmusawa Ammah tai Allah yayi Albarka zan kira Indo nasanar da ita shikenan Ammah,wata hirar suka shiga ta daban ta tsakanin su.


Wankafa yau ansha shi fes ta tsaya tài wanka babu algus aciki ba ha inci,zaman dirshan tai agaban kayan sai canki cankar wanda zata saka aciki take karshe dai wasu riga da sket ta dauko peach color sosai sukayi kyau data sasu das sukai mata tartare gashin kanta tai ta daure shi da ribom kallan kanta tai amadubi kamar ba ita ba palet shoe ta dauko tasaka acikin kayan daya siyo mata tun adaki take gwada irin tafiyar da zatai da zarar tafita.


Tafiya take kamar me tatata ahakan wai tafiyar gayu takeyi,step biyu tataka Mom da suke zaune a dining suka zubo mata idanu da tunanin wacece wannan tazo gidan basu sani ba,danta kala kular dasu taku ta sake canzawa saidata sauko sannan suka shedata wayyo ina wuta sujefa Jalilah har wani daci mom takeji amakoshinta kasayin shiru tayi.


Janyo rigarta tayi ke dan Uwarki a ina jika samo waddan kayan ko yawan kwaruwanci kika fara bamu sani ba inba hakaba wazai baki wadannan kayan da sai yayan wane da wanene ke sasu ko kifadan inda kika samo ko nai miki mummunan dukan da babu wanda zai iya shaidaki,cikamin riga karki shafan datti kumani ba karuwa bace wllh yayanki ne karuwai tunda rannan agabana naga Namiji yana tabata kuma ance duk wanda Namiji ya tabashi dan iskane kuma karuwa ce.


Rankwashi ta sakar mata aka sosai ya shigeta Iya ce tafito daga Kichin cikin al ajabi take kallon su tika tika dasu amma sun kama karamar yarinya suna zalintar ta,haba Hajiya metayi muku kuke dukanta haka ke dallah gafara can tsohuwar munafuka kema baki wuce mudake ki ba bama ita ba karki sake shiga abunda babu ruwanki kisaka ido kisha kallo,shiru Iya tayi cike da bacin rai amma babu yadda zatai barin wajan tai indai Jalila ce kutabata kuna sani wllh.


To matukar ba yawon karuwanci kika fara ba wannan kayan satoshi kikai,niba barauniya bace saidai kune barayi Salima ce ta durka mata duka abaya shegiya medogon baki sosai taji zafi abakinta dama wannan gabjejen hannun ba dole taji zafiba,tuni hawaye sun fara malala akuncinta,duka dai Jalilah ta shashi sosai take kuka ai Mom Abinda za'ai kayannan najikinta acire su dan basu dace da ita ba.


Kici kicin cirewa Jalilah kaya suka hauyi cizo da yakushi sun shashi amma saida sukai wa Jalila tik daga ita sai panta suka barta hatta vest din da ta saka saida suka cire,gashinta Mom taja shima wannan tsinannan gashin sai munyanke shi damu kike zancan saikin bar gidannan tunda bana ubanki bane,kuka kawai Jalilah ke risga cike da takaici da bacin ran abunda sukai mata wani cizo ta gantsarawa cizo babu shiri ta saketa tare da sakin karar azaba kansu farga tuni ta falla da gudu harta kusa kaiwa karshan benan.


Sun jawa kansu masifa dan wllh sai sun gwammace kida da karatu saita gana musu azabar da basu taba dan danar kamarta ba,kai tsaye dakin Jalal ta nufa tana kuka bil hakki,yana kwance ya bararra je yaji kuka asaman kansa yayi zatan mafarki yake jin kukan yaki ci yaki cinyewa ya bude idanun sa arba yayi da Jalilah sintir daga ita sai pant,da sauri ya tashi zaune yana kare mata kallo ganin kukan nata bana kare bane,wai me akai miki kike wannan kukan kuma ina kayanki kike yawo haka.


Kuka ta sake fashewa dashi hannunsa ta ruko tanaja nikazo muje ka ramamin dukan da wadan can azzaluman sukai min,cikani zauna gefansa ya nuna mata zama tai har Lokacin hawaye bedena zubaba babban takaicinta sababbin kayanta da suka kwace,inajinki suwa ne suka dakeki duk abinda ya faru saidata zayyane masa tsai yayi yana kallonta lallai iskancin su Mom harya kai sukama yar mutane siyi mata sintir ya tabbata da katuwar budurwa ce tsaf zasu iya yimata haka.


Rasa mezai cemata yayi shidai ba iya rarrashi yayi ba bare ya rarrasheta,oya kibar kukan haka zan siya miki wasu sai lokacin tai shiru tanajan ajiyar zuciya,sauka yayi daga kan bed din hannunta yaja suka fice daga dakin dakinta ya wuce betaba shiga dakinba koda wasa sai yau babu laifi tunda ta rage kazanta amma haryanzu dai sai ahankali, wardrobe dinta ya bude riga da wando ya dauko mata rigar Iya guiwa sai dogon wando.


Bata yayi maza saka kikwanta kiyi bacci banason fitina kinjini ai ban kumace ki kara sauka ba,fita yayi adakin zuciyar sa sam ba dadi ya rasa meyasa yanzu bayaso yaga damuwar yarinyar kodan yana tunanin tayi nisa da iyayanta akan talauci ne oho,haka nan yakejin tausayinta dan akwai shi da san yara dan ita tafara takalar sa da fadane amma da babu abunda zai saka ya daketa mezai dakama awanann jikin abu duk kashi.


Gaba daya Ammah batasan abunda ya faruba sai wajan 11 tafito ranar itace da Dady al adarta ce dama saita tsaya ta kula da mijinta kafin ta sauko,dakin Jalila ta fara lekawa tana takure awaje daya tana bacci tab lallai Jalila manya haryanzu bcci kike tayi,kasa ta sauka dama tun dazu bakin Iya kaikayi yakeyi tundazu take duban hanya Ammah ta sauko sai yanzu.


Iya ce ta zabga tagumi oh ni jikar isyaku ana zalinci agidannan wllh har Ammah ta gotata ta dawo da baya waya zalinceki Iya,anzo wajan abunda take jira kenan dama hmm wllh Ammah wani abune ya faru agidannan mara dadinji dazu da safe meyafaru haka nan Iya ta zayyanewa Ammah duk abinda ya faru,Jalilan sukaiwa haka eh Hajiyar Amma bakiga ba danai musu magana babu kunya haka suka zageni tas basu dubi girmana ba.


Shikenan Iya nagode,ran Ammah sosai ya baci to ina ruwan su da kayan jikinta da zasiyi mata wannan wulakancin zata dau kwakwkwaran mataki kuwa akansu dan bazata lamunta ba tunda ba zaman su takeyi ba itace ta kawo ta gidan bataga wanda zai takura mata ba.

Dakin Jalila tajuya ta sake shiga sai yanzu ta kare mata kallo da alama har tai baccin kuka takeyi Girgiza kai kawai tai takoma dakinta cike da takaicin halo irin na Sarah da Yayanta na rashin tarbiyya da wulakanta duk wanda beyi musu ba.


Sai bayan azahar Jalila tafuto har Lokacin ranta ahade yake tunanin Abunda zatayiwa su Mom kawai takeyi sakowa tai suna zaune aparlon suna tikar dariyar sunyi maganin Jalila gashi ta kasa futowa saita koma taci gaba dasa tsummokaranta,tsabar kidima tsaye suka mike ganin kayan da tasa ayanzu yaci uwar wanda suka cire mata dazu kallon kallo suke atsakanin su da tambayar kansa wa yake siya mata wannan kayan.


Ko kallon su bataiba ta wuce kiching wajan Iya taje tabata abinci,kare mata kallo Iya tai oh ni wai Jalila waya siyamiki wannan kayan dan India ta bata amsa saboda ALLAH fa zan miki karya ne,kinga yadda kikai kyau kamar bake ba amma wadan can azzaluman sun cuceki bayan duka harda cire miki sutturar jikinki sudai kayan summu su kadan bare nace sakawa zasi babu daya balle Kanwar biyu,kibarsu da Allah kawai Uhm kawai Jalila tace tafita daga kiching din.

             Mrs Baba Bello Abubakar

              ........✍️✍️✍️✍️

No comments