Recent Updates

Uncle J 25

 


Page 25


Maza kizo ki gaida su da baya ta dawo harda su sun kuyar da kai ganin Dad awajan ina kwana mun tashi lafiya,da fara'a Dad ya amsa kin tashi lafiya lafiya kalau na tashi,dai dai kunnan Jalal ta matso da bakinta dan India ina biri ina akuya fatan katashi ba

wuya tanayi tana murmushi saika dauka gaisuwar arziki take masa duka ya kawo mata tai saurin yin baya kingani ba Ammah ina gaida shi yana kokarin dukana bansan menai masa ba ya tsaneni.


Ammah ce ta harare shi wai meyasa bakasan abun arziki ba yanzu yarinya tana gaida kai baka amsa ba saika kawo mata duka harara yake wurga mata kamar idanun sa zasu fado,kwàfa yayi lamar zasu hadu awaje Dad bece komai ba kallon su kawai yake ya tabbatar Jalila ba abun arziki ta gayawa Jalal ba sai kunshe baki take tana Dariya Girgiza kai kawai yayi ganin wadda zatasa Jalal magana ko badan Allah ba.


Tashi kiyi tafiyar ki Jalila aike kingama aikinki tunda Allah yaga niyyarki ta alkhairi ce kin gaidashi shine be amsa ba kije wajan iya tabaki breakfast dinsa kikai masa dakin,zako kici ubanki haka ya ayyana aransa wayar sace ta fara ringing dama abinda yake so kenan yasamu hanyar fita Jalila kuwa tuni takai kasa da fatan Allah yasa yauma yace saita cinye itako da gaba takaita gobarar titi a jos.


Har Allah Allah take takai dakin nasa addu'a take alasa bedawo ba tabude ko yayane tadan ci tasan bazai iya cinyewa ba wata kilama yaga tasa hannu yace ya koshi ta cinye dariya tayi hakama zaice.Tana shiga ta ajiye basket din gaba daya bata lura da shi adakin ba yana lafe akan sofa yana kallonta yaga abunda zatayi ganin tana ta kokawa da basket lallai saita fito da kayan ciki,keee da sauri ta mike tana muzurai ashe dama barauniya ce ke bansani ba bayan rashin kunya harda sata.


Tuni ta hade fuskarta jin ya kirata da barauniya oya kneel down tsaye tayi tana kallon sa dan batagane meyake nufi Mtswww stupid girl ki tsugunna nace kidaga hannayan ki sama rike kugu tai tana kallon sa akan wane dalili menaima da zanyi hakan gaskiya ba wahala ta kawoni zaman duniya ba zaki da maiko nazo ci,ni kike cewa bazaki ba zumburo baki tai to da dawa nake.


"Juya masa keya tai gaba daya bataji lokacin daya taso ba kawai jin wani shegen rankwashi tayi aka,ash ta dafe kan bakaramar shigarta yayi ba tuni Hawaye ya fara tsere a face dinta kazama kawai,oya yi abunda nasaki durkusawa tai kamar yadda yasata akalla saidatakai 30mnt tuni idanunta sun raina fata tayi kuka harta gaji"


Mike da kyar tasamu ta mike guiwowinta jinsu take kamar ba nata ba sunyi matukar sanyi sai jamai Allah ya isa take azuciyarta dan babu halin furtawa yanzu jikinta zai karayin tsami,tafiya tafarayi da nufin fita adakin na sallameki ne dawowa tai kamar zata fashe da kyka tsallan kwado ware idanu tayi ni ban iya wani tsallan kwado ba to banazo na koya miki,da sauri ta tsugunna tafara tsallan kwado tanayi tana kuka face tayi jage jage da Hawaye amma tsabar taurin kai Irin na Jalila taki tabashi hakuri.


Hawan babur kai ranar Jalila babu kalar punishment din da Jalal be bata ba har tsotsar alawa saida yasata,daga karshe saida ta gagara tashi da kafafuwan ta tuni kanta ya fara tsananin ciwo ba ataba bata wahala irin yau kaf cikin rayuwar ta ba,zubewa tai a parlon tana numfarfashin wahala,shiko hamshakin yana zaune yana danne dannen waya saidai ya tabbatar ta dawo cikin hankalin ta,harshi zata cewa ina biri ina akuya aiko taga akuya ajikinta tashi ki ficemin adaki.


Da kyar tasamu tatashi zaune da rarrafe ta fara tafiya har takai dakinta bata hadu da kowa ba tana shiga dakinta ta baje Fashewa tai da kuka jin yadda gabobinta kamar an sassara mata su ko ina ciwo yake yimata zazzabi ne ya rufe ta sai rawar sanyi take haka ta wuni akwance sam Ammah bata san abinda ke faruwa ba,ta dauka tana can tana bacci dan yanzu Jalila ansamu hutu bata da aiki sai bacci.


Ga yunwa ta addabeta sai bayan la'asar ta samu da kyar tatashi tai alwala tai sallah,kamar me koyan tafiya haka ta fara taking steps tana saukowa ta tarar dasu Salima azaune an bararraje suna karta ita da Rufaida,kallon sutai da mamaki caca sukeyi wa Mutane agida danta san menene wannan tana gani a garin su anayi shima sai tantiran yan Iska sunayi suna busa hayaki lallai wadannan ba kananan marasa mutunci bane.


Ke dan Ubanki mu sa anninkine da zamuzo mu zauna kema kizo ki zauna kamar gidan Ubanki,dadinta ni daku duk daya muke kunga babu me yiwa wani gori babu sisin ubana aka gina gidan kuma babu sisin ubanku aka gina kunga kowa aimaganar ma tada jiniyar wuya bata tasoba.Gwarama ni nawa uban yana da Gida wayasani ko su o'o a gidan haya ake rayuwa.


Afusace Salima ta taso daga hannu tai zata dauketa da mari daidai lokacin Jalal ya sauko daga sama kallo daya yayi mata tagano mugun gargadi acikin idanun sa,sauke hannun tai sosai Jalal yake musu kwarjini barin inya hade rai kamar be taba Dariya ba,biyoni abunda yace kenan yayi gaba kallon kallo akafara to dawa yake wace zata biyo shi,harya kai bakin kofa ya juyo zubawa Jalila harara yayi sainazo na tattaka ki zaki taso.


Zumbura baki tai toni mezamma aina dauka da wadannan samudawan kake tashitai tabi bayan sa harlokacin jikinta ciwo yakeyi Rufaida da Salima har turereniya suke wajan lekawa ta window parking space suka ga ya nufa Jalila na biye dashi a baya kamar bindi,saimita take azuciyar ta ina zai kaita tuni zuciyarta ta bata kauye zai maida ita ai wllh babu inda zataje.


Durkushewa tai awajan tafashe da kuka juyowa yayi da sauri da tunanin ko wanine ya daketa ita kadai ya gane sai baba direba dame gadi da suke zaune sun zuba mata idanu suma da tunanin wacece wannan kamar wata me tabin hankali kinfito Lafiya amma haka kawai kizube kifara kuka kamar wata me iskokai.


Ubamme akai miki zakisa mutane agaba kidinga wannan kukan kamar wadda aka aikowa da sakon mutuwa,ai wllh gwara sakon mutuwa tunda ubana ya mutu uban kowama ya mutu bani da asara dadai wannan hukuncin da kake so ka yanke min namaidani kauye,ni dan India narasa mena tsarema acikin rayuwa ka takuramin duk wata hanyar jindadi na so kake ka toshemin ita kayiwa ALLAH kayi hakuri karka fitar dani daga Gidannan


Duk yadda yaso gimtse face dinsa saidai yayi murmushi sai shegen tsoro ga shegiyar tsokana,aiko yau dole kikwana akauye kije can kici gaba da cin tuwon masara da koriyar miya tundake baki da kunya,wllh wannan ma sharrin shedanne kasan shedan la'ananne shiyake kara zugani akowane lokaci amma daga yanzu naima alkawarin zanyi yaki dashi bazai sakecin galaba akaina ba wllh dagaske nake dan India kayimin rai.


Kuka ta sake fashewa dashi,su Rufaida dake hangen komai dadi kamar ya kashe su yau zasu rabu da kaya Jalal yayi musu daidai dazai fita da wannan tinkiyar suma sa wataya sukadai suyi abunda suke so babu me samu su idanu,baba me gadi sai tikar dariya suke ganin bilhakki Jalila take Kuka tana bashi hakuri kamar wadda yace zai maida ita gidan kurkuku.


Zaki taso kosai nazo dakai na dauko ki nidai kaimin rai karka maidani kauye Wayyo na shiga uku Ammah kizo ki ceceni kihanashi ya maidani kauye sake rushewa tai da kuka tayi jage jage da ita tattare hannun rigarsa yayi ganin ya nufita wuff ta mike da nufin guduwa taku biyu yayi yakamota cak ya dagata tana Kuka tana dukansa da yakushi saida ya danna ta amota ya rufe.


🤣🤣🤣Jalila har shidewa take tsabar yadda take gursheken Kuka aitanaganin sunfita daga gidan ta kwalla wata kara hannunta aka ta sake fashewa da Kuka ta tabbata tafita daga jindadi ita yanzu sam bazata iya rayuwar kauyeba wllh ina bazaima yiwuba,tsawa ya daka mata kokimin shiru kona wullaki ta glass dinnan motoci su take miki wuya kimutu kowa ma ya huta.


Shiru tai ina zata so ta mutu bata dauki fansa akansa ba wllh saiya san ya fitar da ita daga daula dajin dadi,fatarta ta kalla babu cizon sauro ko daya ajikinta yanzu zata koma kauye sauro ya samu nama,ranta ne ya sake baci gaskiya Jalal ya zalinceta har Lokacin matsar kwallah takeyi.


Jalal be tsaya ko ina ba sai wani katon super market manyan motoci ne kawai ke layin shiga kaida ganin wajan kasan na manyane in baka da yan canji bazaka doshi hanyar wajan baka tuni Jalila ta hadiye kukanta ganin wata aljannar Duniya daya kawo ta har sauke numfashi take tuni tamnta da batun wani kauye.

   Mrs Baba Bello Abubakar

       ........✍️✍️✍️✍️

No comments