Recent Updates

Uncle J 21



Written and Narrated

By Kulsoom Ismail Idris

Page 21


Ammah zama tai akusa dashi ta rafka uban tagumi da tunanin meyasa meshi haka kamar me shafar aljanu hawayan fuskarta ta share ganin yadda lokaci daya ya hautsine kamar bashi ba duk ya kakkar ce fatar sa saboda susa yayi jajawur dashi.

Bude kofar akai aka shigo Jamal ne fuskarsa dauke da damuwar halin da abonkin nasa yake ciki,meyake da munsa ne Jamal me binciken ya bayar,Numfashi ya sauke gsky Ammah duk wani binciken da akai musu haryanzu ankasa gano musabbabin Abunda ya kawo musu kaikayin da suka fuskanta musamman na Jalal haryafi na Mom hatsari zai iya tabawa mutum kwakwalwa saboda yadda kaikayin yake zautar da mutum yarasa inda zaisa kansa.


Jinjina kai Ammah tai to muma munrasa wace masifa ce wannan ta kunno kai cikin gidan saboda abin shida Sarah kawai ya taba mugamu lafiyar mu kalau nafi tunanin ko a iska suka shaka,dan murmushi ya saki baza su shaka a iska ba saidai sunyi tarayya wajan amfani da abinda ajikinsa suka sami wannan cutar,gaskiya Jamal banajin akwai wani abu da Jalal zai yadda suyi tarayya dashi saboda ninasan wanene Jalal baya amfani da kayan kowa sai nasa.


Kuma sanda abin ya faru gaba dayammu muna daki bazamu tantance akan tata taya hakan ta faru ba amma yanzu alhmdlh tunda ansamo bakin zaran har sun sami bacci fatammu dai ALLAH ya kiyaye gaba za asanya ido ko za agano inda matsalar take,hakan yayi Allah ya kiyaye gaba Ameen cewar Ammah da haryanzu abun daure mata kai yakeyi.


Sake duba Jalal yayi ganin babu wata matsala yayiwa Ammah sallama ya fita.


Su Rufaida ma suna can suna tattauna yadda wannan lamarin ya kasan ce lokaci daya Mom ta birkice haka,anya Mom ba gamo tayi a toilet dinnan ba Salima tafadi haka tare da kallon Rufaida nima abinda nake tunani kenan tabbas aljanu ne suka shiga jikin Mom ba ita kadaiba har Jalal tunda bantaba ganin makamancin hakan koda wasa atare dasu ba,cigaba sukai da tattaunawa atsakanin su.


Jalal dai saida ya wuni a asibiti yasha allurai da karin ruwa kamar yadda Jalila tai alkawari saiya kaishi Gadon asibiti,bayan Magariba ya matsawa Ammah su dawo gida ya samu sauki babu yadda Dad beyi dashi ba akan ya bari ya sake kwana yace aah sutafi gida haka babu yadda suka iya haka suka taho gida Mom harwata rama tayi yini daya kawai sai idanu awaje har Lokacin afirgice take Jalal din ya fita karfin hali kansa har wannan lokaci azabar ciwo yakeyi.


Yana shiga part dinsa kan sofa ya lafe dan bayajin yau zai kwana akan bed din dan be manta akansa yafarajin wannan Mahaukacin kaikayin ba,ya zaka kwanta anan Jalal anan zan kwana Ammah kaida baka da lafiya kace anan zaka kwanta aikasan zaka Wahala ka koma kan bed din fir yaki yadda kuma yaki gaya mata dalilin da zaisa yaki kwana akai dakin yashiga ta dudduba bataga komai ma bedsheet din ta cire ta canza masa wani sannan ta fito.


To na canzama bedsheet jin hakan yasashi mikewa adarare yahau bed din jin babu Abinda yaji ya gyara kwanciyar sa sosai blanket Ammah ta jamasa ta jima adakin kafin taimasa Addu'a tafita duk yana jinta ya lumshe idanu ne kamar me bacci,shiru yayi ya zurfafa cikin tunanin Abunda ya sameshi ayau ta ina garin yaya wane ibtila'i ne ya fado musu haka towa zai aikata musu hakan.


Jalilah zuciyar sa tafada masa haka kawar da wannan tunanin yayi duba da yadda bashi kadai abun ya samu ba dashi kadai ne saiyace ita ce kuma aina ma zataje ta samo wannan abun me uban kaikayi bazama ta iya hakan ba haka ya karaci tunanin sa har bacci ya dauke shi.


Jalilah baccinta take kashirban ranta fes yau makiyinta ya hau gadon asibiti kai ita wace irin babbar rana ce agareta taga faduwar sa ko banza tafara huce haushin dukan da yayi mata ba wai tagama bane somin tabine wannan sainan gaba zata san abinda zata kara masa dashi dan ita bata yafiya ba kuma ta mantuwa.

Ita ce ta fara fitowa daga dakinta taci kwalliya riga da sket ne ajikinta yau shaawar kwalliya take ta zane fuskarta sosai da baki tasha jambaki da farin ciki tafito cikin Nishadi take aikinta.Mom ce agaba sai Rufaida abayanta kowaccen su ta dauki wanka ko ina zasuje da sassafen nan take ayyanawa aranta.


Ina kwana Mom ya jiki kuma ashe jiya hauka kikai gaskiya madai aljanun bada karfi suka shigeki ba tunda baki fara duka ba kuma gakinan ras kamar bake ba ina zakuje haka kukaci kwalliya gidan Ubanki zamuje ah daga tambaya zaki zagi ubana yana kabarin sa dannayi yakana saboda zaman tare naimiki ya jiki mene lefi anan.


Duka Mom ta kawo mata shegiyar Yarinya mekama da ifiritai ni kikewa rashin kunya zanyi maganin ki acikin gidannan nan kusa sai kin hada kayanki kin koma kauye badai agidannan ba banza taimata taci gaba da raira wakokinta abun ya sake kular da Mom zata sake magana Rufaida ta rikota ki kyaleta Mom ai ita bakomai bace kibari mugama da manyan tukunna wannan karamar alhaki ce koni zan gama da ita bama saikin sa min hannu ba.

Kwafa Mom tai aini shegiyar yarinyar ce haka kawai naji na tsaneta wallahi ko ganinta bana sonyi,aibaki fini tsanar taba da za aban wuka tsaf zan yankata wallahi,bangaje ta Rufaida tai saida Jalila takai kasa to dama abace kamar abushe ta tafadi shiyasa duka daya zata baje akasa babu karfi sai tsabar tsokana fita sukai daga parlon binsu tai da harara aikin banza kawai nidai ba yadda zakui dani.

No comments