Uncle J 20
Page 20
Jiyayi ransa yana kara baci akan Jalila harshi wannan yarinyar zatayiwa wannan gagarumar asarar ita awa dazata shigar masa rayuwa abarda befi ya mutstsike taba yazama dole ya dauki mataki akanta tsaki
yaja alamar Abun yana ci masa zuciya.Wuni tayi akwance aparlo duk yadda su Rufaida suka so takalarta dan su daketa kin tankasu tayi kamar batasan da zamansu a parlon ba duk zata waiwayo kansu baridai taji sauki,abunda yake sake bata musu rai yadda Ammah takeji da ita kamar wata yar uwarta kamar ba aiki tazo yiba sai wani lelenta Ammah keyi abun yana kona musu Zuciya.
Biris Ammah tayi dasu sai harare harare sukeyi babu wanda ya kula su Allah sarki Iya wuni tai tana gudawa saboda firgitar da tai wuni daya tai zuru zuru Addu'a kuwa inzata shigar toilet saitai mintuna biyar tana jero ta gaba daya jikinta yayi Laushi Jalila tuni ta manta da wani labarin kanzon kurege data fadawa Iya itama tana can tana fama da kafarta wannan fa shine kowa da abunda ya dame shi makocin me akuya yasai kura.
Saida Jalila tai sati sannan kafar tata tasaki gaba daya ciwonma saura kadan ya warke,kullin kayanta ta dauko saidata nemi wajan zama akasa dirshan ta zauna ta bararraje kayan tafito da su kaf wasu bakaken leda tadauko kowanne da abu acikin su leda daya ta daka ta maida sauran ta zuge jakar tamayar da ita a mazaunin samun wajan ajiyeta tai.
Sassafe ta fito daga dakin ta kai tsaye part din Mom tafara nufa ajiyar zuciya ta sauke jin komar abude ahankali tafara ta kawa lekawa tai bakowa a aparlo dukan su suna daki suna sharar bacci tunani ta tsaya yi tana canki cankar takan wa zata fara takan uwar yaka mata ta fara sannan ta gangaro kan yayan,saidata lalleka ta tabbatar da bedroom din Mom tukunna ta tura kanta tashige.
Tana bararraje ta hangame baki tana sharar bacci sai jan mumshari take kamar rago, toilat ta nufa babu tsoron komai atare da ita bathtub ta duba babu komai aciki bakalledar hannun ta ta bude wani gari ta dauko harda guzurin spoon dinta debo garin tai ta barbade cikin bathtub din babu ta yadda mutum zai gane ansaka wani abu Murmushi ta saki sadaf sadaf ta fice daga part din gaba daya.
Har wannan lokacin babu motsin kowa part din Jalal ta sake nufa ahankali ta tura kofar bedroom din yana kwance yana sharar bacci yarfe hannu tai saboda wani dadi daya ziyar ceta ahankali ta wuce toilet dinsa yadda taiwa bathtub din Mom haka taiwa Jalal fitowa tai tana ajiyar zuciya,lallabawa tai ta isa har bakin bed din debo garin Maganin tai ta barbade daidai inda tasan da yayi juyi zai hau kan sa.
Tana fitowa daga room din ta sauke ajiyar zuciyah dakinta ta wuce ranta fes kamar ta kadda tsalle tai ta haye kan gadonta cikin tsananin munna da jindadi.
Baccin yau ba karamin dadi yayi masa wani mafarkin yake me matukar kayatarwa agare shi juyi yayi da nufin sake bararrajewa kamar an tsikareshi yafara jin kaikayi yana dan damun sa basarwa yayi kamar bejiba kai abunfa na gaske ne adari da sittin ya mike jin wani irin mahaukacin kai kayi daya ziyarci dukkan sassan jikin sa, toilet ya fada aguje famfo ya kunna tunkafin bathtub din ya gama cika ya afka ciki.
Jiyayi kamar ya fada cikin tafasashshen ruwan zafigigi cewa yayi ya rasa ina zaisa kansa yaji dadi susa ya farayi kamar mahaukaci jikin gini ya juya bayan sa yana susa yaji ina hakamma baiyi ba kaf jikin sa babu Inda besamu rabon saba tuni fatar jikinsa tai jajawur ta tashi tai rudu rudu dagashi sai boxer yafita asukwane dai dai lokacin Mom ta fito daga part dinsu aguje tana kai kayi kai kayi Wayyo Allah zammu tu na shiga uku ni Saratu ihuntane ya tada mutanan gidan gaba daya sukayo waje.
Mom daga ita sai sket iya guiwa ba riga ba dan kwali itama fatarta tayi burdun burdun har fuska,wai ina Jalal tuni Jalal ya fice daga maine parlo sam besan inda yake jefa kafafun saba tsananin tashin hankalin da yakeji adukkan sassan jikinsa tuni kansa ya fara juyawa Baba Direba ne ya soma hangoshi ya dirfafo kofa gaba daya baya hayyacinsa Subahanallahi meyake faruwa da yallabai kokarin fita yake daga gidan gaba daya baba megadi suka rukoshi yana fizgewa yana yi yana susa kamar mahaukaci sak haka ya koma.
Meyi musu wanki ne ya ruga cikin gidan da gudu Alhaji ga yallabai can ana kokawa dashi zaifita ba kaya ajikin sa,da gudu Amma tayo waje dan babu wanda yasan Halin da yake ciki kallo daya Ammah tai masa ta fashe da Kuka dan azatanta gamo yayi ko kuma aljanu aka turo masa sam baya gane kowa baya gane kowa kai hatta kwayar idanun sa masifar kaikayi sukeyi masa.
Dad ne ya rukoshi cikin tashin hankali meyasamu tilon dan nasa Ammah ce ta sake rugawa ta dauko masa jallabiya dakyar aka saka masa ita aka sashi amota tare da Mom da take ihu dkyar aka samata kaya itama aka rankaya dasu asibiti duk wanda yaga Jalal saiya tausaya masa amma banda Jalila zuciyarta wasai dama tai alkawarin saita kaishi gadon asibiti,allaurai akai musu sai wani magani d aka shafa musu na kashe kaikayi ankai kusan away daya dayi masa allurar kafin ta fara aiki ajikin sa allaurar bacci aka zarkada musu lokaci kan kani suka hau baccin wahala da azaba musamman Jalal yafi Mom jin jiki.
No comments