Recent Updates

Uncle J 19

 


By Kulsoom Ismail Idris

Page 19


Ammah ce tafito daga part dinta kai tsaye dakin Jalila ta nufa dan sake duba jikin nata,tura kofar tai hade da sallama tana zaune rike da kafa dan abun bana wasa bane kamar yadda ta daukeshi ji take kamar yatsanta zai cire hawayene wani na kurar wani aface dinta,da sauri Ammah ta karasa shigowa Subahanallahi meya sameki Jalila Cikin sheshshekar kuka take fadin kafata ke cewo.


Wa yayi miki hakan shuru tai tana sharar hawaye da dan kwalin hannunta shuru tai bata bata amsa ba ko faduwa kika gyada mata kai tayi alamar eh,haba Jalila Meyasa kina girma kina kara tabar barewa akalla fa zakika 13years ya kamata kisan kin zamo budurwa kikame kanki garin wasan ki kikaje kika bazge kafa,bata ce komai ba dan ita kadai tasan yadda zuciyar ta take tafasa akan abunda Jalal yayi mata.


Wayarta ta daga kiran Jalal tayi baya kusa bedaga ba Jamal takira ringing daya ya dauka gaisheta yayi cikin girmamawa da fara'a ta amsa abokinna kafa bama tare Ammah to dama yarinyar wajena zai dubawa kafa tadan samu rauni ne,bagani ba Ammah bana zo na dubata anan din bama sai kun zoba to shikenan Allah ya yayi Albarka Ameen Ammah.


Kallon Jalila tayi to kidaina kukan haka ga abokina Jalal nan zaizo ya duba miki kafar tsuke Fuskatai ai ita duk wani abu daya danganci Jalal ta tsane shi Ammah ce Kawai sai Dad suke suka fita zakkah sudai bataji ta tsane suba,sannu Ammah taci gaba dayi mata 20mnt ya karaso gidan kiran Ammah ya sakeyi akan gashi yazo to tace masa tare da bashi Umarnin shigowa maine parlo.


Hannun Jalila ta riko sauko muje ya dubaki kamar ta rafsa ihu haka takeji kafar wani azababban zafi takeyi mata duk dauriya irinta Jalila saigashi tana hawaye wani nabin wani,ahankali ta dinga saukowa saboda kafarta tunda suka fara taking steps yake kallon su da tunanin a ina Ammah ta samo wannan yarinyar da ganinta dai daga kauye aka kawota.


Kallo daya ya yimata yakaranci zatai rawar kai da kuma tsiwa face dinta ya kalla tahadeta tamau kamar wata babbar mace Abin Dariya ya bashi itakadai sai hura hanci takeyi agabansa Ammah ta zaunar da ita kara bata face tai dan karma yaga hakoranta ya raunata,gaida Ammah ya sakeyi tare da kallon kafar ta ta garin ya hakan ta faru,kabari Jamal garin kiriniyar ta taje ta bige kafarta.


Kallon kafar yayi sosai amma kamar taka mata kafar akayi ba bigewa bace wannan,da sauri ta kalleshi taya akai yagane hakan kenan abokin nasa ne ya fada mai harara ta galla masa Murmushi kawai ya saki na canka dai dai kenan wa kika tsokana yayi miki wannan hukuncin haka.


Kamar ta fashe dan tsabar yadda ya kular da ita,kayi abunda ya kawo ka kabar shiga abunda babu ruwanka abunda be shafeka ba shi wanda ya gayama shiya takanin kuje kaida shi nabarku da Allah akwai ranar kin dillanci ni Jalila kabewar kan kabari ce bakin cikin me taushe beci banza ba Ina nan bisa kan sa,tana wannan bayanin tana hararar Jamal danji take kamar ta tashi ta rufeshi da shegen duka.


Ammah ce ta auna kalaman ta ama aunin hankali tsaf ta gane abunda take nufi kallon Jamal tai sukayi murmushi dasu kadai suka san ma anarsa,nidai bani nakar zoman ba ratayar ma ba abani ba babu wanda ya gayamin takaki akai kawai nayi duba da yadda dan yatsannaki yayi ne amma zakiji sauki kanwata,ni bani da ya bani da kanwa bazan taba zaman kanwar kaba har mahadi ya bayyana.


Dariya ya saka dan ya kasa daurewa sosai ta bashi Nishadi kaga ka kyaleta kayi mata taimakon gaggawa kar kafar tata ta rube,bare baki Jalila tai ta barke da Kuka jin ance kafarta zata rube har sheshsheka takeyi tana tsinewa Jalal a zuciyarta,kinga kiyi shiru matukar kikai shiru akai miki abunda ya kamata babu abunda zai samu kafarki shiru tayi.


Ina box din Jalal tana dakinsa bana dauko maka,yi zamnki Ammah mene amfanina bari na dauko miki,tashi yayi  ya haura sama kai tsaye bedroom dinsa ya nufa yasan tana ciki,yana shiga kuwa ya ganta a gefan bed dinsa harzai fito ya hango kayan daya dura awata bag dawowa yayi da baya ganin wasu sun leko a yayyage daga kayan yayi tare da zaro idanu kaya masu matukar tsada anya Jalal be fara sheye shaye ba mezaisa ya wulakanta kayansa haka kamar wani tababbe.


Aiko saiya tambayeshi yaji dalilin dayasa ya yiwa kayan haka in baya so yabawa mabukata mana,saiyaji duk ransa ya baci sarai yasan Jalal da zuciya zai iya yiwuwa wani abu ya bata masa rai ya huce akan kayan.

Asanyaye ya dawo ya zauna Ammah ta lura da yadda ya sauya amma batace komai ba, hydrogen yasaka ya wanke kafar duk wani taimako yayi mata magunguna ya ciro daga aljihunsa ya bata bewani jima ba yayiwa Ammah sallama ya fita,asibiti ya koma kai tsaye office din Jalal ya nufa shiga yayi tare da yin sallama akasan makoshi dan haushin Jalal ya cika masa zuciya.


Tana kishin gide ajikin kujerar sa kamar besan da shigowar sa Office din ba yatabbatar shine shikadai zai iya shigowa wajan sa batare da yabashi izini ba.


Jalal yaushe ka fara shaye shaye ban sani ba shan yayyun idanun sa ya bude masu cike da bacci da gajiya zuba masa su yayi,kawar da kansa yayi daga kallon sa shi kansa wani zubin Jalal yana yimasa matukar kwarjini shiyasa mata suka mato akansa kaf hospital dinnan matan su Dr Jalal Ma'aruf yayi wuff da su kai wasu ko magana cema ta hada su amma babu fuska kullum face dinsa adinke kamar wanda aka aikowa da sakon mutuwa.


Kamar besan abinda yake fade akan saba ganin bazai kulashi ba ya nisa meyahau kanka ka yayyanka kayanka kana da lafiya kuwa Jalal,ciwon hauka nake tsut ya tsuke bakinsa,in wannan maganar ta kawo ka zaka iya fitar mun daga office cikin barai yake nuna masa hanyar fita saboda duk wani bacin rai da Jalila ta kunsamai jinsa yayi ya dawo sabo kamar yanzune take yayyanka masa kayan.


Tuni idanun sa sun hadu sunyi jawur matukar be illata yarinyar nan ba bazai taba jindadi a rayuwar saba saiya hanata walwala dajindadi zai nemi kauyansu shida kansa zai dauketa ya maida ita ya yarda kwallan mangwaro ya huta da kuda.Yasan halin Jalal sarai inyayi fushi kabar shi kawai in ya sauko da kansa zai nemeka,bece komai ba ya tashi ya fita yana mamakin tomeya bata masa rai haka daga zancan kaya kodak bashine yayiwa kayan hakaba dage kadarsa yayi alamar shiya sani.

Mrs Baba Bello Abubakar

       ......✍️✍️✍️✍️

[7/28, 9:35 AM] +234 903 511 7917: UNCLE J


Written and Narrated

No comments