Recent Updates

Uncle J 18

 


Written and Narrated

By Kulsoom Ismail Idris

Page 18


Ranar dai adakin Ammah Jalila ta kwana ta bararra je iska tako ina batsamin dauda babu hamamin da yake tashi daga jikinta ita kanta taji dadin jikinta amma wankanne fa gsky bazata taba jurar sa kullum ba,washe gari tana yin sallar asuba dakinta ta wuce kaya ta canza acikin yamu tsatstsun kayan ta yaudai bata shafa komai ba sosai taji dadin jikinta kamar batai wani ciwo ba.


Kasa ta sauko Iya naduke tana moping taga saukowar Jalila baki sake tabita da kallo ganin goshinta akumbure bata rai Jalila tayi wannan kallon fa iya kamar kinga sabuwar halitta,yo badole na kalleki ba jiya yarinyar nan kika tashi hankalin mutanan gidanan babu inda ba adubaba amma bake babu alamarki,kin bamu wahala wallahi.


Tabe baki tai kun sodai ku wahalar da kanku kunsan ko amafarki bazan gudu daga gidannan ba duk ranar da ku kaga haka koda amafarkine da kunfarka kuyi sadaka dan bani Jalila kuka ganiba saidai shafar aljanu,au damma mun miki abun arziki mun damu dake shine bamuyi miki gwananin ta ba aishikenan za akuma,babu abunda za akuma Iya kidaina min mugun fata dan bansan irin bakinki ba haka kawai kijamin salalar tsiya.


Naji bazan sake fada ba yanzu dai kifadamin meya faru kinsan nidake bata baci,murmushi Jalila ta saki gaskya Iya da agidan sarauta kike daba karamar munafuka za aiba kuma al gunguma hade rai Iya tayi nice zan zamo munafukar Jalila tabe baki tayi ke nifa ALLAH kawai nake jin tsoro da kika ganni ko innata tai lefi saina fada mata bare ke damukai haduwar kan titi.


Yau na tabbatar Jalila baki da mutunci ni kike gayawa haka,haba iyalliya ta wajena mene kuma abun hawa sama salan na kulaki miyi fada kiragemin zubin abinci tonidai bazaki fada daniba aminiyas,harara Iya ta galla mata da kika gama zagina yanzu ba aidole ki doje saboda tunawa da abinci,to kiyi hakuri tunda dai nabaki hakuri komai ya wuce subutal kalam nai dayake wani zubin kamar ba agasan baki ba haka nake saikinyi hakuri dani Iya.


To shikenan komai ya wuce yanzu dai kifadamin ina kika shiga jiya akaita nemanki,anya Iya ba mayya bace ta ayyana hakan azuciyar ta,hmmm kibari iya ainake fada miki jiyannan gamo nai da manya manyan ifiritai ba karamin artabu mukai dasu ba dayake nima kinsan badaga baya ba wajan jarumta,saboda kakana na bakwai yayi yaki da aljanu guda dubu 70 dafe kirji Iya tai kakan naki.


Kwarai kuwa cewar Jalila ganin yadda ta fara rufta Iya harta hau kan layi kuwa,to kinsan tsakanina dake akwai zama na amana ina saukowa naga wani shirgegen aljani ya durfafi dakinki  waishi aljani dan kundale kuuuuu cikin Iya ya murda idanu awaje take kallon Jalila maganar gaskiya kike fadamin kota wasa,bata rai tayi kintaba ganin nayi miki karya girgiza kai tayi alamun aah jikin Iya sai karkarwa yakeyi saboda tsoro.


Tom shine fa nasha gabansa da tambayarsa mezaiyi adakinki Iya baiwar ALLAH da kullum kaganta da carbi ahannu,kada baki yayi tare da fadin kullum kinamai fitsari aka haka ankawo masa abinci merai da lafiya kinshiga toilet ba addu'a ba Bismillah kika fitsare mai abinci shine ya fusata yazo daukar fansa.


Tuna irin alkhirin da kikeyimin in kin bani abinci ban koshib haka bakya gajiya zaki karomin wani ga nama akai ga ruwa mesanyi bana manta Alkhairi ko kadan shiyasa nai kunar bakin wake natare shi muka dinga fafatawa, parlon nan yayi mana kadan har duniyar su na bishi mukai kaca kaca acan dakyar ya samu yagudu amma shine Iya duk baki ganiba akankifa nayi wannan kasadar na saida rayuwata saboda ke aiya kamata kijin jinamin tunda kinji dalilin dayasa kukaita nemana gwara ku iya nan kuka neme ni nikuma dana tafi Duniyar aljanu fa.


Fashewa Iya tai da kuka ashe Jalila haka kike kaunata agidannan ban saniba bani da wani masoyi bayan ke Jalila,aini yanzu ko sau goma zakici abinci nadaina jin haushin ki zoma ki zauna aidole kihuta nizanyi miki aiki yau taho taho kawar arziki,gintse dariyar dake cinta tayi wani munafukin hawaye ta kakalo Allahu akhbar kaji masu yi dan ALLAH kin cika yar Adam tagari in akaima alkhairi karka saka da sharri,aibazan taba saka miki da sharri ba nagode miki bazan taba iya biyanki ba.


Harkan sofa ta zaunar da ita tanai mata sannu feee Iya ta bude bridge wani sumamman drink ta dauko mata me shegen dadi makwat Jalila ta hadiye yawu,kai Iya na Dady ne fa ke toko Hajiya Ammah taji wannan aikin saida rai da kikayi abinda yafi wannan ma zata baki babu Abinda zata ce,kumafa hakane bana sha ko zanji sanyi araina.


🤣🤣🤣 Ina zuwa wani shegen zawo ne ya tasowa Iya gaba daya ta kasa sukuni tana barin wajan Jalila ta fashe da dariya saukowa tai daga kan sofa tai birgima harda hawayan mugunta gaskiya ta yadda Iya bata da wayo gaba daya zatayi amfani da ita taitacin dadi abinta sai inda manta ya tsaya yatsa ta ciza woni Jalilan Inna da Malam,tunda ya fito daga daki yake jiyo sautin driyar ta kobe ganta ba yasan wace mahaukaciyar ce ke wannan dariyar ilaikuwa itance tana kwance akasa tai shame shame cikinta harya kulle dan dariya.


Hade face dinsa yayi tsaf yana sane saidaya daidaici yan yatsun kafarta ya take su da takalmi dan mugunta harda murza kafar karar azaba ta saki gaba yayi kamar be aikata komai ba da sauri tatashi ta zauna tana kallon kafar tata dan yatsanta harya fara jini dan ba karamar mutstsuka yayi musu ba,idanun tane suka ciko da hawaye waime tayi masa hakane meta tsare masa kosan ganinta ne ba yayi agidan su kome zaiyi bazata fitaba tana nan daram saidai shi ya fita ya bar mata gidan amma itadai nan gani nan bari sadakin agalawa.

Da kyar tatashi ta komai dakinta ga azabar zugin da kafar ke mata ga takaicin drink dinta ya bare garin birgimar da tasha.

     Mrs Baba Bello Abubakar

No comments