Recent Updates

Uncle J 16


Written and Narrated

By Kulsoom Ismail Idris

Page 16


Kiran sallar magariba yasa Ammah tashi alwala ta daura bayan ta idar da sallah tajima tana addu'a kafinta shafa tafita daga bedroom din gaba daya,kasa ta sauka tuni su Mom anhallara gara sarakan ci tafada aranta da alama ko sallah basiyi ba amma sun

rankayo cin abinci,cikin kisisina Mom ta rike haba ohni Saratu wai ina yarinyar nan tashiga ALLAH yasadai ba guduwa taiba dama tsiyar dan kauye kenan waya sanima ko sata tayi ta gudu.


Hmm kamar kin shiga zuciyata Mom nima abunda nake tunani kenan dama kina ganin idanun wannan yarinya ai kinsan barauniya ce,sam Amma bataji dadin abunda suke fada akan Jalila ba ai Jalila dai nariga naganta toilet dina tashiga ya kulle takasa fitowa sak sukai suna rarraba idanu gaba daya abun be musu dadiba sun so ace shegiya sace ta akai sa huta suma.


Rufaida ce tatabe baki kunji kauyancin ba taya zaka shiga toilet karufe kanka kakasa fitowa tur wllh jahilar banza kan yadade da dafewa da miyar kuka dariya suka saka tare da tafawa kamar wasu kawaye.


Banza Ammah tai musu danta lura so suke ta kula su ayi sa insa ita kuwa bata da lokacin su gaba daya,wai ina yaya Jalal yana sama Ammah ta bata amsa tsugul ta mike bari na hada masa Abinci nakai masa yawwa yar Albarka maza kikai cewai Mom data kiftawa Rufaida idanu,azuciyar Amma kuwa dariya takeyi gaki gashinan indai Jalal ne saikin gwammace bakije kai masa ba.


Saidata zuba masa komai dayake kan dining din tadauka tai sama har gyara tafiya ta sake ita alallai zataje wajan masoyin ta,tura kofar dakin tai wani sanyi ne da kamshi ya bugi face dinta lumshe idanu tai tana ayyana Jalal badai tsafta ba komai nashi fes fes.


Sallama tayi shiru da alama baya parlon abincin ta ajuye maimako ta fita tsabar naci kin fita tayi kai tsaye hanyar bedroom dinsa ta nufa kanta ta zura tare da lekawa.


Farka warsa kenan daga baccin daya kwashe shi yana niyar tashi yaji alamun anshigo masa room shiru yayi yana jiran yaga wanane ya shigo masa har uwar daki ya tabbatar ba Ammah bace da itace da yanzu tayi magana,gaba dayanta ta shigo dakin hangoshi datai akwan ce rabin jikin sane kawai arufe da blanket.


Gashin kirjinsa data hango a waje taji tana marmarin tabawa ahankali tafara sanda har bakin bed din ta isa zama tai dirim saida gadon yayi kasa a hankali tadauki hannun ta tare da dorawa akan kirjinsa kamar ta dora masa garwashin wuta haka yaji hannun nata ransa yayi masifar baci har shi zata zo tataba da wannan qazamin hannun nata.


Shiru yayi yaga iyakarta su Hajiya Rufaida fa tuni ta manta a inda take sunkoyo da face dinta tayi daidai tasa bakinta ta miko da nufin kissing dinsa dunkule hannu yayi saidaya daidaici ta kawo bakinta daidai nasa ya takarkare ya zabga mata wani uban naushi abaki tuni bakin ya fashe kanta dawo daga azabar da take fuskanta abakinta ya sake zabgama mata wani wawan mari.

Tare dasa dukkan kafafunsa ya harbota daga kan bed din kuka Rufaida ta fashe dashi gaba daya jikinta yayi mata wani uban nauyi lebanta kuwa ya haye kamar ganda da rarrafe take neman hanyar futa daga dakin amma gaba daya ta kasa gani tsabar gigi cewar da tayi hanyar toilet ta nufa tsawa ya daka mata karki kuskura kishigar min toilet da kazamin jikinnan naki.

Juyowa tai gaba daya taga ma gigicewa har wani dishi dishi take gani na azaba.

Da rarrafan tafita daga room din baki daya tuni ta mance da abunda ya kawo ta.


Da kyar ta samu ta tsaya da kafafunta daidaita nutsuwar ta tayi tare da jan vail din kanta ta rufe fuskarta dashi tun data fara taking steps suka zuba mata idanu musamman Mom dataji ta shiru har dadi ya mamaye zuciyarta suna can suna hirar soyayya🤣🤣🤣batasan wal mukalafatu take sha ba,Ammah kallo daya tai mata tagano halin da take ciki wata dariya ce take son kufce mata Allah ya kara take maimaitawa a zuciyarta ko barin da suke bata kalla ba tawuce part din su.


Gaban mirror ta tsaya tukunna ta bude fuskarta sai data runtse idanu ganin yadda tayi wani uban muni ga bakinta ya hadu yayi zungurere babu kyan gani ita kanta bata son kallon fuskarta bare kuma wani sai lokacin taji wasu hawaye na tsiyaya daga idanun ta menene laifinta dan ta so shi ta kauna ce shi duk wayewar ta ace akwai Namijin da zai dinga gudunta haka.


Yadda maza suke binta tanai musu wulakanci amma shi ya samuma tana binshi yake wofantar da ita, Mom ce tashigo danjin yadda suka kwashe da Jalal turus tayi ganin yadda fuskar Rufaida ta hadu takara wani uban muni kumatu yakara subu subu baki ya zama zungurere,wata ashar ta mulmulo wane dan iskanne yayi miki haka dakyar ta bude bakinta dayake azabar zafi Jalal eh lallai nayadda wannan dan iskan yaro ne.


Kamar ya samu jaka ya zauna yayi miki wannann mahan gurbar toke kina ubamme kika zauna ya dakeki daga abun Arziki kin kai masa Abinci samJalal badan arziki bane amma zanyi maganin sa ko zanyi yawo tsirara saikin Aure shi kinjuya shi kamar waina ni Saratu bantaba faduwa akan abunda nasa gaba ba.


Salima ce ta shigo jin hayagagar Mom tunga parlo karewa Rufaida kallo take tun daga sama har kasa fashewa tai da wata shegiyar dariya ke kinga yadda kika dawo kuwa kamar wata gwagwgwan biri waima garinya haka tafaru Jalal dinne yayi miki haka ko hatsari kikai a hanyar zuwa,harara ta maka mata Uban hatsarin nai ba hatsari ba dirshan Salima ta zauna tana tikar Dariya dan itafa wannan abu yayi mata dadi gwara su hadu su rasa gaba dayan su.


Ala baki hakuri daga tambaya dama ganinai abokin kuka shi ake gayawa mutuwa, Mom ce ta wurgamata harara wane irin rashin mutuncine zaisa kitisamu gaba kina tikar dariya kamar kina farin ciki da abunda ya faru aah Mom ni karki dauramin sharri aidama na lura kinfi son Rufaida akaina shiyasa kome kika samu saikin fara bata sannan kiban.


Banda abinki ba ita ce babba ba niba ruwana da girmanta wllh kowa ma babban kan sane,kinga Salima karkimin rashin kunya yanxu zan tashi mufidda rainin wllh,to mu fidda man daka musu tsawa Mom tai mene kuke haka ko sokuke magauta suyi mana dariya kushiga hankalin ku.

     TAKU koda yaushe.

Mrs Baba Bello Abubakar

No comments