Uncle J 14
Page 14
Yau Jalila ta ware ranar fara duty dinta 6 na safe tagama dukkan shirye shiryen da ta tanada kai tsaye dakin Jalal ta nufa cikin sa a taganshi a bude murmushi tayi sadaf sadaf ta shiga parlon sa baya ciki bedroom ta wuce kamar wani dakinta duk da dakin ya burgeta amma tatabe baki ina ruwanta ma da kyan wani daki.
Karar ruwa taji alamun wanka ake a toilet bakaramin jin dadin hakan taiba yarfe hannu tayi yanzu ta ina zata fara aikin ta wardrobe ta hango ahankali take takawa budewa tai kayansa ne a jejjere abun sha awa sai tashin kamshi sukeyi almakashin ta data boyo azani shita futo dashi saida ta zabi wasu shaddodi masu shegen kyau da tsada yanka na rashin mutunci takama yi musu baji ba gani saida tai musu lahanin da ta tabbatar bazai taba mora ba.
Futowar sa kenan kamar ance ya daga kansa ya hango aika aikar da take yi masa harde hannayansa kawai yayi ajikin kofa saidata gama aikinta tsaf dadi kamar ya kasheta tana dago kai tai abar dashi duk rashin tsoro na Jalila saidata firgita bacin ransa ne ya kasa boyuwa mene ribarta inta bata masa kaya kayan ya kalla tuno uban kudadan daya batar kafin ya dinka su.
Afusa ce yayo kanta gadan gadan dolene yayi mata dukan mutuwa yau da hannu daya ya cafkota a kokarinta na fyallawa da gudu kafin ya kara so inda take wasu tagwayan maruka ya kashe face dinta da su wani dummm taji kunnuwanta sunyi kafin ta farfado ya rufeta da azababban duka tsabar yadda dukan yake shigarta kukan ma kasayi tayi.
Saidaya tabbatar jikinta ya gayama ta tukunna ya kyaleta dan kwalin kanta daya dade da sabulewa ya dauka tam ya daure mata baki Allah sarki Jalila idanunta ma kasa budewa tai tsanar Jalal kuwa tasake samun matsugunni a zuciyarta hawaye kawai ke kwarara a face dinta keeee haka yaja ta kamar kayan wanki ya watsata a toilet kamar shara gum kanta ya daki bathtub saiga kan ya fashe tuni jini ya soma zuba daga goshinta.
Hankalin sa kwance yayi shirin sa cikin kananan kaya sosai sukai masa kyau kayandata gama kacaccalawa ya tattare wata katuwar leda ya dauka saida ya dura su tas ya barsu awajan makulli yasaka a kofar toilet din ta yadda babu wanda zai iya kawo mata agaji.
Ko tsayawa Breakfast beba yayi ficewar sa bayan get man ya wangale masa get da mugun gudu ya fita har Lokacin ransa a matukar bace yake da abunda Jalila tayi masa.
Karfe 8 Amma taji shiru ba Jalila ba labarin ta karfe 9 ta tabbatar kodai bata da lpyane dakinta ta bude yagama cakubewa tai kaca kaca dashi ga wani tsamin dauda dayake tashi adakin,Jalila Jalila shiru har toilet ta leka babu Jalila ba labarin ta saukowa tai tana tambayar Iya kotaga Jalila girgiza kai Iya tai aini Amma yau kome kama da Jalila ban gani ba ko aiki batayi ba yau.
Lambun gidan suka rankaya ita da Iya ba Jalila kai hankalin Amma fa ya tashi karfa yarinyar mutane ta bata tashiga uku,baba buzu ta tambaya yace shibema santa ba babu wanda yazo ya fita sai yallabai daya fita tun sassafe.
Part din su Mom ta tura Iya tagano ko tana can suka bada tabbacin basu ganta ba Iya tana futa suka sa shewa in sha Allah baza'a gantaba shegiyar yarin mayya alasa ansaceta akaita can imma yankata za ai a yanka basu da asara.
Amma zama tai tare da zabga Uban tagumi ina Jalila tashiga kodai guduwa tai tome zaisa ta gudu gaba daya batai tunanin duba dakin Jalal ba tana da tabbacin babu Abinda zataje yi dakin sa shidama akace yafita sassafe.
Dad ne ya sauko ganin Amma ta zuba Uban tagumi meyake faruwa ne gaba daya Amma ta kasa magana dan tana bude bakinta to kuka zata fashe dashi Iya ce tai masa bayanin abunda yake faruwa sosai abun ya daure masa kai to ina zata shiga dama tana fita ne à ah Alhaji tunda tazo ko bakin Get banajin ta taba zuwa,dakan sa ya fita ya sake zazzaga gidan bega Jalila ba.
Allah sarki Amma ko ruwa kasa kurba tai saboda tashin hankali Jalal da yanacan wajan Abokin sa Jamal yama manta da wata Jalila sai karfe 2 ya nufo gida tunda yashigo parlon yasan ba Lafiya kusa da Amma ya zauna gaba daya ta firgice tai wujiga wujiga.
Taku har kullum.
Mrs Baba Bello Abubakar
........✍️✍️✍️
[7/28, 9:35 AM] +234 903 511 7917: UNCLE J
No comments