Uncle J 13
By Kulsoom Ismail Idris
Page 13
Rufaida ce ta kawo mata duka ke har kin isa yangida suna magana kidinga sa baki kina musu rashin kunya,Mtswww to ke kuma awa agola kawai kibar yayan gidan suyi magana bake ba danna tabbatar kudai bajinin
Gidannan bane.Mom ce ta fashe da Kuka yanzu abun haryakai yar aiki ta dunga cin mutuncina wllh na tabbatar Rukayya kece kika gaya mata Allah ya isa tsakanina dake.Dad ne ya dagawa Mom hannu kinga Saratu sarai kinsan wacece Rukayya bazata saka wannan yarinyar agaba tadinga yimata zancan ki ba karki sake zagarmin mata nagaya miki,au ni ba Matar kabace, ko da kike matata ban lamunta ki wulakanta min Rukayya ba ita kikazo kika samu dan haka karna sake jin haka daga gareki.
Jalila ya kalla karna sake jin kinfadi wata magana akan Saratu da yayanta itama kamar Amma take dole kiyi mata biyayya kinjini ai to kawai tace amma badan zatai abunda yake so ba dan bazata taba zama Mom da yaranta su maida ita jaka ba.
Mom kamar zuciyarta zata babbake tsabar yadda zuciyarta ke tafasa dole ne ma tadauki mataki akan Dady da Amma tana zaune baza ta taba yadda tazama boraba indai shigowar ta gidan bemata wahala ba to juya megidan ma bazai mata wahala ba,dole ne komai ya dawo karkashin ikonta tazama itace me fada aji da ita suke zancan.
Cikin Kissa Mom ta karkace kai aikomai ya wuce Dady kasan sharrin shedan za a kiyaye gaba,kuma itama dan yarinya ce shiyasa nan gaba kocewa akai tayi aibazata yiba Amma ta kalla yar uwata kiyi hakuri hakan bazata sake faruwa ba.
Kar Amma take kallon ta tadade dagane wacece Sarah wajan iya makirci da tuggu wannan abunda ta fadama ta tabbatar akwai wani abu datake kullawa aranta,murmushi tai babu komai Allah ya kara hada kammu ameen Mom tace amma a zuciyarta fadi take tare dawa Allah ya kiya sheni da hadakai da kishiya ai tsakanina da kishiya yaki ne babu ragayya ko kadan.
Amma afuskarta bazaka taba gane hakan ba.
Dad ta kalla am dama nace meze hana mudawo wannan part din kaga Zumuncin mu saiya sake kulluwa ba kamar ana nesa ba,tofa abinda Amma ta fada kenan a zuciyarta fadada fara'a Dad yayi hakane Sarah kin kawo shawara mekyau babban burina dama naga kun hade kanku waje daya.
Wani farin ciki ne ya mamaye zuciyar Mom kamar ta tatashi tataka rawa intana nan aikinta zaifi tafiya yadda ya kamata,kallon Amma tai koba haka ba yar uwata sakin murmushi Amma tayi cike da basarwa hakan yayi kinyi tunani mekyau yawwa to Allah ya yi muku albarka ameen suka amsa.
Rufaida kamar ta zuba ruwa akasa tasha dan murna gata ga abun sonta haka Jalila take ayyanawa Alhmdlh ta kwana gidan sauki zako kuci ubanku saikin gwammace baki dawo dan ki takura mana ba munafukar mata,murmushin mugunta ta saki duk abinda takeyi Jalal na kallon ta ya tabbata yarinyar nan tana da aljanu zai fita daga harkarta gaba daya.
Tsam yatashi daga dining din yuuuu suka bishi da kallo Rufaida har hadiyar yawu take kamar mayyya sosai guy dinnan yake tafiya da imanin ta,haka Salima kejin wani abu akansa amma bazata taba nuna zalamar ta afili ba ita tasan ta wace hanya zatabi tasame shi cikin sauki bata da burin Auran sa amma ko yayane ta dan dani zumarsa koda saudaya ne wannan ya wadatar.
Haka suka bar dining din kowa da abunda ya kudurta a zuciyar sa.
Aranar Mom suka kwaso kayan sawar su komai akwai acikin part din part hudine a maine parlon na Amma saina Dad dana Jalal tunda Mom taga wannan part din taka zilamar sa tasawa zuciyarta saita shigo shi to yaudai burinta ya cika ta dawo kusa da Amma sosai tatsayawa Mom akahon zuciya da za'a bata dama babu Abinda zai hana takashe Amma murus kuwa har Lahira.
Kwana biyu da dawowar su part din wata haya niya bata taba tashi ba dan sosai Amma ke kawar da kanta akan dukkan abunda zata gani aiki fa yasake kacamewa Iya da Jalila data gama moping zasu bata kamar wasu yara ita kanta Amma ta dura da mugunta suke hakan kala batace musu ba.
Jalal da suke burin gani koda yaushe inya ga dama sai su kwana biyu ma basu ganshiba sai ya tabbatar da bakowa a parlon yake saukowa lambu shine wajan zaman sa dan fita sam bata dame shi ba yafi ganewa yayi zaman sa agida.
Mrs Baba Bello Abubakar
No comments