Uncle J 12
By Kulsoom Ismail Idris
Page 12
Washe gari Jalila tatashi fresh da ita kamar babu wani abu dayake damunta amma fa yana cikin zuciyarta ta basar ne kawai tasha kwalliyar ta yaudai hoda kawai ta bamgaza bata sa jambaki da gazar dinba,sotake ta gane a ina dakin dan rainin hankalin can yake saita gano hakan zatai tunani akan aika aikar da zatai masa.
Amma ce tafito daga dakin ta sam batama lura da Jalila ba ganin ta mike hanyar dakinta yasa tabita da kallo da tunanin ina Amma zataje wani hadaddan part da take yawan ganin sa akullum saitayi tunanin na wanene nan taga Amma tashige batafi 3mnt da shiga ba taji karar bude kofa kir idanunta nakan kofar Jalal ne agaba Amma na bayansa.
Wani shegen murmushi ta saki ganin tasamu abunda take nema Farin ciki ya mamaye zuciyar ta zaka gane Allah da girma yake ga mata nan bisa kanka saika gwammace da namiji dan uwanka zaku fatata danni Jalila fada dani ba riba abinda take Ayyanawa aranta kenan.
Taku daya yayi a stairs zuwa biyu yayi arba da ita tuni yaji ransa ya kara baci ganin wani shegen murmushi da take saki kamar kyanwa kallo daya yayi mata besake marmarin hakan ba kallon tama baya kaunar yi.
Amma ina kwana yaji muryarta ta doki kunnan sa kamar ba muryar ta ba haka ya ayyana azuciyar sa haukan da yake hangowa afuskarta bejishi acikin muryar taba.
Dan India ina kwana ya jiki kuma cike da tsokana take gaida shi in yayi mata magana to kasar wajan tayi mata murmushi Amma kawai tayi dan sarai yanzu tagane halayyar Jalila saidai tabaiwa wani labarin ta Amma ce ta harare ta tare da jamata kunne dining table suka nufa saida ya jawa Amma kujera ta zauna tukunna shima ya zauna.
Kamar wani mace haka yakecin abincin kamar baya so Dad ne ya sauko Jalila har kasa ta tsugunna tana gaidasa da Fara'a ya amsa sannu da aiki yawwa ALLAH ya yimiki Albarka Ameen Jalila ta amsa da alamar taji dadin addu'ar.
Wani bacin raine ya sake sauko wa Jalal ganin tun kafin Dad yayi masa magana yayi wa wannan snake din,kara tamke fuska yai.
Wani kishine yake kara shiga zuciyar sa arayuwar sa ya tsani yaga iyayansa sun hadashi da kowa saiga wata kucaka suna bude mata hakwara suna magana da ita, ko su Salima bakauna yake yaga Dad yana musu magana ba balle wannna yar kauyan.
Mom ce ta shigo yaranta na biye da ita har awannan lokacin Salima bata dawo daidai ba yawon club din da sukeyi sà idai taga Rufaida tafice yawonta amma ita ba dama dan haryanzu jifan da tasha bata gama warkewa ba,idanunta ne ya fada kan Jalila da ta kunshe baki wata dariya kecinta makamata harara tai tare da jan kwafa.
Sannu maman luku juyowa sukai gaba dayan su suna kallonta mazewa tai kamar ba ita tai maganar ba,Dad ne ya kallo Jalila data juya taci gaba da aikinta Jalila ya ambaci sunan ta tare zuciyoyin su suka buga Jalila wannan tsinanniyar dama sunan ta Jalila haka Jalal yakarajin tsanar sunan meyasa sunan su zaizo daya.
Kamar Mutuniyar Arziki haka ta tsugunna gani Alhaji murmushi Dad yayi aah Alhaji kamar wani tsoho kidinga cemin Dad kamar yadda yarana suke gayamin kema yata ce ai,washe baki Jalila tai tsabar dauda har wani gansa kuka hakwaran keyi nagode Dad Allah ya kara girma Ameen suka amsa shida Amma sauran kuwa ai sungama kulewa.
Wace maman luku cewar Dad dago idanu Jalila tai tare da gyara Fuskarta tadawo kalar tausayi Salima da Rufaida ta nuna gasu dan wadannan a kauyammu sun Aurar da yaya kai har jikoki zasu iyayi yanzu haka koda yake addinin mune ba daya ba shiyasa babu ruwan su kamar al amara Jalila ta barke da Kuka.
Baki bude suke kallonta to me akai mata Fyace hanci tai wllh duk inda naga arne tausaya masa nake sabida amakarantar allo yadda malam lawi yake mana wa'azin yadda walakiri zaita gididdibar yan wuta,to kunsan zuciyar musulci tausayi suke ban tundana gansu da su nake kwana nake tashi azuciyata amma nadauki alkawarin bazan gajiya ba harse sun musulunta.
Duk yadda Jalal yaso gimtse face dinsa saidaya murmusa ya tabbatar wannan yarinyar bata da hankali amma daya karkata yakalli su Rufaida bega lefin Jalila ba dan yadda kasan inyamurai haka suke shigar su ga su abubuwa ba fasaliba dirka dirka gasu da uban tumbi kai gaba daya dai basu da fasali.
Mom kuwa taje iya wuya cike da bacin rai ta kalli Amma waini Rukayya wannann tsintacciyar kin kawota Gidannan ne dan ta hana yarana sukuni ko kuma Alhajin kika kawowa ya Aura narasa wannan jaraba haka danna lura kece kike daure mata kugu amma zanyi maganinta bazan lamunta wata can tazo ta hana yan gida walwala ba da sake wllh kodai ki sallameta ko kuma ni nadauki mataki akanta.
Ai wllh inkinga nafita daga Gidannan da sunan komawa kauye saidai gawata amma nazo kenan ta Allah ba taki ba bazakimin bakin cikin jar miya ba haka kawai nakoma na kamacin miyar kuka baki isa ba.
To ALLAH na tuba ko Amma ce ai yanzu banga abinda zatamin da zanyi zuciya natafi ba inza afitar dani sau goma saina dawo sau goma.
Mrs Baba Bello Abubakar
........✍️✍️✍️
[7/28, 9:35 AM] +234 903 511 7917: UNCLE J
No comments