Uncle J 11
By Kulsoom Ismail Idris
Page 11
Tana tsaye tana tikar Dariya ganin Rufaida yashe akasa wani azababban mari ya tsinka mata saida Jalila tai wata katan tawa saigata dabar akasa gaba daya radadin har cikin kwakwalwarta take jinsa, Rufaida da farin ciki ya cikata atunanin ta ita yaramawa dukan harda sake fashewa da Kuka.
Kanta dawo daga hayyacinta ya rufeta da duka tako ina azabace ta ishi Jalila caraf ta kankame shi cizo daya kushi ta dinga kai masa sosai yakeji ajikinsa dan tuni fatarsa tafara fashewa Rufaida ce ta rusa ihu kufito za ai kisan kai zata kashe shi Amma Dad aguje suka fito har suna neman kayar da juna dakyar Amma da Dad suka banbaro Jalila daga jikinsa sai kuka take da tunanin metai masa yake jibgarta haka kamar jaka.
Cikin tsana yake kallon Jalila gaba daya ta yayyage masa fata sai azabar radadi yakeji daya san zaizo yasamu wannan yar daban dabe dawo ba kamar yadda yaji ya tsaneta itama haka taji ta tsaneshi kuma taci alwashin saita rama dukan da yayi mata bedaki banza ba.
Kala bece da kowa ba duk ko da tambayar da suke jera masa balle kuma Jalila dake rusar Kuka babu wanda yataba yimata wannan Uban dukun sai dan India kai ita ayanzu gaba daya yan Indian suma ta tsane su bama shiba.
Rufaida ce tafadi karya da gaskiya cikin jin zafinta Jalila tamike to almunafunfun saiki bari se antambaye ki kiyi karya medalili,Amma ta kalla wllh Amma saina dauki fansa akan abunda wancan dan Indian yaimin banmai komaiba zai mayar dani kamar wata jakar sa bashi ya dauka Fuuu tatafi daga wajan tana gursheken Kuka Dad Jijjiga kai kawai yayi kai ni nama rasa mezance wllh kome ya hadashi da wannan Yarinyar oho.
Amma data san halin Jalila inbaka tabata ba bata tabaka ta Tabbatar Jalal ne ya fara takalar ta itakuma bata barin kota kwana tamaida martani Allah ya kyauta.
Cikin tsananin bacin rai ya fada bedroom dinsa hargitsa gashin kansa yakeyi wace mara mutuncin yarinya aka kawo musu gida dole nema saita bar gidannan dan wllh saiya hanata sukuni matukar zaina ganin wannan halittar zai iya yimata mummunar illah.
Fatar sa yakalla da tasha ya kushi tako ina tayage masa fata kamar wata kura kwafa yayi zamu sake haduwa shikadai yasan abunda zaimata.
Kamar yadda ya kudurta aransa haka Jalila ta kudurta tana dakinta tana safa da marwa dukkan wata muguntarta saidata tattaro ta waje daya saita rama dukan dayayi mata atarihin rayuwar ta ba atabayi mata bata rama ba haka wannan shima bazata taba barin ya tashi abanza ba dolene tadau fansa babu ruwanta da wanene shi agidan koshi ne megidan saita rama balle ma bashi din bane.
Tofa Jalila tadau alwashi haka Jalal ya dauka wazaici nasara atsakanin su Kubiyo ni yanzu ma aka fara.
Amma ganin har magariba Jalal be fito ba dakanta ta hadamai abinci da sallama tashiga dakin nasa yana kishin gide har lokacin ransa amugun bace yake fuska ahade yake amsa sallamar murmushi kawai tayi indai Jalila ce kayi kagama dan kunta karawa kenan.
Son meyasa baka fito kaci Abinci ba cikin kara jin tsanar Jalila yake fadin banaci meyasa shiru yayi wai duk akan fadanka da Jalila kake wannan fushin Kanwar kace fa,da sauri ya dago yana kallon ta Jalila ransa ne ya sake baci ya zama dole acanza masa suna,hakan yake Ayyanawa a zuciyar sa.
Lallashin sa Amma ta somayi dan sosai take kaunar dannata da kyar ya sauku ya yadda zaici Abincin ganin yadda gaba daya ta damu da kincin abincin nasa dakanta tai feeding dinsa yana ci yana bata shagwaba ahaka ta samu yaci sosai sun dan taba hira lokacin sallar isha'i yayi tukunna ta fito daga dakin.
Taku har kullum.
Mrs Baba Bello Abubakar
........✍️✍️✍️✍️
No comments