Recent Updates

Kishiyar Kabila Complete Hausa Novel

 


*KISHIYAR ƘABILAH...*




 _BY SURAYYAHMS._ 

Wattpad@Surayyahms.



 _®Any resembelence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence._ 



Bi-ismillah..


Episode 1️⃣



A hankali yake kai desert din dake gabansa ixuwa bakinsa kansa a sunkuye yana dan murmushin nan nasa mai kyau da ya kai ga har ana iya ganin lotsawar dimples dinsa. 


Acikin sigar nitsuwa da kamala sosai yake xaune jikinshi sanye da wata petite cambridge grey colour zegner french suit dinsa datamai kyau ajikin shi bana wasa ba.


Sassanyar muryan mahaifyarsa ne yake ratsa shi,ahnkli ya dan girgixa kai snn ya dago lumsashun idanunwansa yana kallon dattijiyar matar dake Zaune akan kujerar dake kallon nasa fuskarta a daure takafa masa ido tana kallonsa, "murmushi yakuma yi mai sauti xai yi magana ta rigasayi a fusace tace "ohhhh,ni ce ma na xama abun dariyarka yau ko Ahmad? Maganan yarinyar nan kafayat fa nake maka but ure busy smilling at me kamar wani abun arxiki nace ka aikata mata..arent u ashame? Yadda ta karashe a fusace yasa shi kara sakin murmushi wanda ya dada tunxirata,

muryanta cike da fusata tace "ohhhhhh wato ga mahaukaciya nan na maka ihu ko,Ahmed are u out of ur mind?..


Babu shiri ya dan marairaice fuska snn ya ajiye fork din hannun sa da murynsa mai taushi da dadi kasa kasa yace pls calm down, i am really sorry maa, wallh ba haka bane Mamee,ni nama isa in maidaki mahaukaciya ne? ai naji me kikace akanta, toh ni wallh bansan ranta ya baci ba ma saida kika fada ynx,toh wai meye nata na yin fushi ne dan ban tsaya a wajen birthday partyn ta ba sai kace wani ni saurayinta ne? Wani ruwan Takaici ne taji ya shake mata makwogoro daya furta hakan.


tsimewa tay bata ko kulashi ba dan tasan ranta ne kawai xai kara baci inta tsaya yin masa wani bayani, baki bude take kallonsa acikin yanayin mmkin halin basarwa irin nasa yo ace duk wani walakanci da cin fuskan dayay ma yarinyar nan agidan nan shibaima san yana yi ba..


Kyabe bakinta tayi tanamai karkada kafafunta aranta tana jin tsananin takaicinshi ayayinda take tuno da irin baqar wahalar da kafayat din tasha agidan nasu kwana biun nan, wani irin sihirtaccyar ajiyar xuciya mai nauyi ta sauƙe cos Kafayat whud have been the perfect doter inlaw and a responsible wife for her son Ahmad domin yarinyar nan itace ta san shi tun suna yan kanana tun basu san kansu ba suke abota.


Gashi tun xuwanta Nysc take xama dasu agidan dan sabida tana kulawa da su na musmn sabida son Ahmed din datakeyi aranta duba da shine first love dinta, hatta mahaifin sa ya bala'in amincewa da kwaxo da kuma halayyar kirki irin na kafaya,gata nan masha Allah black beauty omo yoruba, gaba da baya full option,gata da tsafta, ga son shara, ga iya wanki da guga, ga iya wanke wanke,uwa uba ga iya girki,ga kuma ladabi da biyayya,duk tayi musu luguden hidima agidan sabida shi amma waishi baima gani ba.


Acikin sassauto da muryansa kasa kasa sigar lallami yana kallon yanayinta yace iyami",my mamee, harararsa tayi tun bai fara mata dadin bakin ba, yace "toh kiyi hakuri mana mama naa inadai kafayat buraimo ne?i promise i will apologise for ur sake! kikace wai dan naki attending birthday din da kuka hada ne yasa tayi fushi ta bar gidan nan ko? Lumshe ido tay dan harynxu mamki yake bata ganin cewa baima san lefin daya aikata ba, Girarsa ya dage sama ahankli, da har dai xaice "She is soo silly" sai kuma ya kumshe sauran maganan abakinsa yy shiru,dauke kan datayi yasa ya dan shafa kansa da yanayin damuwa a muryansa yace "mamee pls now, kidena fushin nan mana nide nasan damuwarki bai wuce kice xancen relashp dina da kafayat ba,i told u i need time..kuma aikinsan komai fa lkci ne, AUREN nan xanyishi in lkci na yayi,kawai su Dad sun kasa gane hkn ne kema kika bi bayan su,sun ki fahimtar abinda nake nufi batun auren nan,i swear im still searching for a good nd decent wife just for u,kuma nasan idan lkci na yy na aure xan kawo muku matar Aurena ko ba kafayat ba,am just bored of all dis match making da kuke min. Kubari mana uhmm iyami?..


Ta cigaba da kallonsa rai bace batace mai uffan ba,shafa kansa ya kuma yi har lkcn fuskar sa na dauke da damuwar yanayinta dan sosai ya tsani yanaganin bacin ranta,saidai shikansa baisan mesa suka saka kafayat aransu hr haka ba, sallamar da aka yi ne yasa duka suka maida hankalin su ixuwa ga bakin kofar tare da amsa sallamar baki daya.


Mikewa tayi ganin yan uwan mijinta ne suka shigo su subiyu, Anty temi (ramotou) da anty (moslimat) Mojushola,da wata kyakyayar budurwa mai suna maryam wacce kallo daya kamata ya ishi kasan bahaushiya ce,da fara'arta ta tarbesu tana masu sannu da zuwa basu wani tanka ta sosai ba suka karaso cikin falon aka shiga gaggaisawa sama sama dan duk hnklinsu da nitsuwarsu nakan dan saurayin ne.


A cikin nitsuwa ya rusuna ya gaishe su snn ya mike tsaye yanamai kallon mahaifyar tasa, adan gaggauce yace "mamee ni xan wuce sai na dawo ko xuwa gobe"..kafin ta amsashi har Anty Temin tay sauri ta amshe xancen cikin sautin babban muryanta na giant woman, fuskan ta babu alaman fara'a tace "oshey Damilare, wat do u mean by dat statement? _Ahhh dami, iwọ ko si oju iberu ti o ni ibanujẹ?_ (ahhh dami,u no dey fear face?)..Daga xuwan mu ne sai kace gobene xaka dawo? but Dats not fair oo,ta kalle babban dadan su da batace uffan ba cikin bambami ta karashe xancen fuskarta a daure "Ahhh see Shildren of now adays,kadai dawo xuwa anjima kar kakai daddare dan bamu gama magana dakei ba, tana maganan tana kallon  cikin kwayar idanunsa suna hade ido sai ta kalle budurwan data sunkuyar dakai kasa da alaman ta fahimtar dashi abunda suke nufi, ahnkli yyi murmushi yace its okay "toh in' sha Allah xan dawo anty rahama.


Shiru tayi batace mai uffan ba sabida she love them to be adressing each oda da sunayen yaren su amma sam shi bayaji, shiyasa ma ita sam bata kiransa da  Ahmad aganinta sunan hausawa ne irin na maman sa, sudei a fannin uba saidai sucemai "DAMILARE " ko "DAMI" KO "LANRE" sabida sunan nasa inkiyar sunan baban mamansu ne so they respect dat name alot.


duk maganan nan da ake Anty mojushola batace musu uffan ba banda cika iska da hura hanci da yatsine datake bin su dashi, dan itadin ta manyanta sosai dan itace first female child da  mahaifinsa yake bi,sai uncle dinsa bakare,anty temi (ramotou) kuma itace autarsu.


Bayan sunyi hakan sai yyi musu sallama ya fice daga falon yana kallon agogon hannunsa daga nan yanajin anties dinsan sunakan watsa habaici wa mahaifiyarsa na cewa tunda yaki auren mace daga kabilarsu aiga nan bahaushiya sun kawo masa daga nata irin kabilar, sam dangin mahaifinsa basa da sauki,they just love to be in control of evrthing. A farko ma sunedai suka soma cusawa kafayat ra'ayin xama agidan iyayensa dan tana musu bauta,so during her nysc session sai ta xo just to get his attention ayi aure, dukkan dangin ubanshi suna matukar son ace  kafayat ce ta auri Ahmed just for the simple fact that itama kabilar su ce na yoruba. 


gun motarsa ya nufa da sauri yana tafe yanamai kallon agogon hannunsa acikin gaggawa ya buɗe ya shiga ciki ya kunnata da sauri yabar harabar gidan nasu.


Ahankli yake tukin aransa yanata tunanin yadda xai kawo karshen wann matsalar data kunno masa kai acikin familyn sa musammn na yadda kowa yake son yaga lallai ya aurar dashi acikin gaggawa..



After some few hrs...



 _National communicable disease control Theathre hall maitama Abuja._ 

 _5.56PM_ 



Manyan likitoci da public health professors ma'abota ilimi da wayewa da kuma kwarewa a bangaren yaƙi da yaɗuwar cututtuka ke shige da fice a babban hall din NCDC dake garin Abuja kowa da alaman fara'a akan fuskan sa.


Lectures din da suka yi yau was very interesting Dan Sai yanzu duka suka fahimci abinda minister of health na kasa yake nufi a lokacin da yake 

ce musu the youngest professor dinsu AHMED BELLO JIMADA is the best and leading young epidemiologist da sukay employing acikin CCD project dinsu na wnn shekarar sabida yanada gwaxo sosai,snn yana bin komin sa ne a dalla-dalla cikin nuna ilimi da kamiya. And He makes sure He carries everybody along acikin kwarewarsa. Snn Yana making good references da abubuwan da yaje ya koyosu a kasashen waje yanamai kara budasu tareda yin gamsashen bayani akansu using simple terms wanda ko the most dummiest and stupidest person zai fahimce shi.


Yau yay musu electronic lectures ne akan manyan pandemic and prevalant diseases dake addaban iyakar boundaries na tsakanin kasa da kasa kamar su COVID19,i:e corona virus, Acquired immuno-deficiency syndrome(AIDS) da severe acute respiratory syndrome (SARS)da wasu ire iren viral flus.


Anan kowa ya kara fahimtar cewa shi mutum ne mai tsantsar nutsuwa da ilimi, komai nasa a hankali yake yinsa. He is very gentle bashi da hayaniya sam saidai daga ganinsa za ka iyasanin cewa yana mugun ji dakansa sabida wani irin tsantsar self assurance da kuma zazzafan self confidence dayake nunawa ayanayin sa musammn in yana fidda bayanansa acikin kwarewa da ilimi daya gama ratsashi.



Wajajen karfe biyar ya wuce suka kammala lectures din ya fito cikin takun nitsuwa jikinshi sanye da hadadden petite cambridge grey suit dinsa dayake wani irin fallasa tsantsar burgewan dake tafe da karancin shekarunsa dan matsakaicin 32-33yrs da haihuwa as one of the current youngest leading professors and doctor of  epidermiological science a Abuja.


Prof.Dr Ahmed bello jimada kyakkwa fari ne amma ba fari can ba dan za'a iya kasa shi acikin light skin yoruba demons mai yanayin tsiririn hanci da fuskar uwarsa ta asalin fulanin garin illori..


Saidai kuma da akwai wnn kamannin da kuma zubi na Jinin mahaifinsa na cikakken bayarben oyo state msmn ayanayin ginanne kuma tsayayyen siffar jikinsa da kuma yanayinsa mai tsananin burgewa,yana da cikakken saje da dan matsakaicin gashin gemu da kuma fasalin kamala ta kyawawan mazajen arewa daya debo acikin jinin xuriar mahaifyarsa.


A matsayinsa na matashi mai ji da ilimin zamani da kuma wayewa da daukaka yasaka yake da karancin lokacin yin sabbin abokai bare kuma ajega yan mata,daga scndry schl har izuwa jami'an dayay baida sabbin abokai duk abokansa na yanzu tun na childhood dinsa ne.


iyakan aikinsa da karatunsa sune kawai agabansa cos he alwys believe serious girl friends and new friends to be a distraction to his career and success, shiyasa ko wani soyayyar arziki bai taɓa tsayawa wajen yi arayuwarsa ba saidai yayi soyyaya ta sharholiya na lkci kalilan.


In his life dan yay keeping companyn mace na kwana biyu ko yay tarayyar sati daya ba wani abu bane sanin cewa lokcin aikin sa nayi to shikenan soyayyar ya kare,shiyasa shi bai taɓa cewa yana son kowacce mace dagaske ba,saidai duk wacce taƙuso masa kai ta kawo kanta wajen shi zai iya bata lkcin shi na kwana biyu ko sati guda da ita daga nan in aikinsa ya tashi bazata kara ganin idonsa ba.


Mata dayawa har sunyi sun gaji sun hkura sun dena sakashi aran su sanin cewa inya gama da mace xai iyayin ma kamar bai taɓa ganinta arayuwrsa ba, halin sa yasaka mata dayawa ke muradinsa a matsayin miji cos he is really hard to get type,yana da high taste wajen xabar macen da xaiyi tarayya da ita,shi irin kalar maza ne da mata ke mutuwar son kasancewa da su sabida yana da sakkaken hannu kudinshi bai dame sa ba, saidai shi namijine da bai da saukin kai,ba asaka shi ba kuma hana shi,he alwys need to be pleased gashi da tsinannen shiga rai da iya nuna ko in kula da komi musmmn ma in amfaninsa ya kare agaresa.


mata dayawa daga  nigeria har waje sunsha sako burin su akansa kodama zai tsaya ayi wata magana ta soyayya da aure amma haryau baida wann ranar bare kuma lokci,wasu sunyi sunyi tun yana 20s har sun gaji till he is 33yrs old now kuma babu abunda yanema ya rasa arayuwar sa, ilimi, kudi, kyau, gata, snn shine namiji daya talli kwal awajen mahaifyar sa mai suna hajiya khadijatu muhammad gidado wanda takasance cikakakkiyr bafulatana ce a garin kwara,jihar illori.


Ahmed yay karantunsa ne adan kankanin shakeru sabida irin kyakkyawan kulawar dayasamu arayuwarsa yayunsa uku da suke uba daya uwa daban daban duk sun girme shi nesa ba kusa ba kuma kowannen su yana kulawa dashi sosai.


mahaifinsa Alhaji Bello Ayodeji jimada,bayarbe ne daga garin oyo,jihar ibadan, shi kabilar yoruba ne da sukayi xaman cirani da lumana tare da fulanin garin illorin,a sanadiyar rasuwar matarsa na fari wato alhaja simiat laide ne ya auro matarsa na biyun bafulatana wato hajiya khadijatu muhammad gidado wanda itace ta rike masa sauran yayansa.


Babban dansa shine Kazeem wanda ake cewa Aremu (Qasimou) sai mabiyinsa hamzat Dimeji (hamusé) da kuma ta mace wato Zainab moturayo (senap) kafin nan Ahmed(Damilare)


Ahmed shine dan Autan gidan nasu,ya kammala first degree dinsa ne a can obafemi awolowo university ta ibadan oyo state garin mahaifinsa while he is 21yrs,yay masters dinsa a kasar waje acan United kingdom for 12month afannin CCD(control of communicable disease)

Sauran kuma ya karasa a university of manchester wanda sabida gwaxonsa ne yasa he became the youngest professor of comuncble disease at age of 31, bayan ya kammala karatunsa 2yrs ago ne yafarajin kamar is high time yafara enjoying life dinsa.


saidai wani hanxari ba gudu ba, his family only desperately wanted him to get married akan lokci sabida Xpectations dinsu kenan akan duk wanda ya kammala karatun sa ya kuma samu dukan wani achievement dinsa na rayuwa sabida su kare mutuncin yayansu dana xuriarsu daga haifo yayan shegu awaje.


saidai shi har yanzu shi bai da wata tsayayyar budurwa bare ajega matar aure dan baisan yama za'ayi ya fara soyayya ba bare aure snn har acikin xuciyrsa in akwai abunda ya rantse baxai amince ya yarje akansa ba shine auren hadi..


SHIN KO YA XA'AYI AHMED YA KAWO MUSU MATAR AURE? 


#SURAYYAHMS grp

08060712446 chat only no calls.*KISHIYAR ƘABILAH...*




 _BY SURAYYAHMS._ 



 _®Any resembelence of story or lifestyle shud be considered as a coincedence._ 


Daga cikin Littafan dana rubuta:

#Arne

#samarin shaho

#sakamako

#ajalinso

#Ahumaggah

#tuntuben harshe

#kudi kumbar susa

#takaicin wasu

#shade of rufaida

#fitar rana

#lamarin gobe.



Episode 2️⃣



Wajajen Shida da rabi saura na yamma Dr Ahmed bello jimada yabar headqtr nasu na nigerian disease control ya kama hanyar gidansu dake cikin jerin layin masu kudin anguwar Katampe extenstion dake abuja.


Ahnkli yake tuki yana jan tsaki har ya iso kofar gidan nasu yay horn a bakin gate mai gadinsu ne yazo agurguje ya buɗemai snn ya shigo ciki batare da ya kula shi ba.


Babban compound ne sosai dake dauke da shuke shuke da bishiyoyi masu daukar hankali, kai kana ganin tsakar gidan kasan kwanciyar hankli da wadata ta zauna.


mahaifinsa Alhaj Bello Ayodeji jimada also knwns as professor Bello jimada(prof BJ) babban manomin shinkafa ne kuma kwararren tsohon professor ne a fannin psychology, wanda ilimi da wayewa yagama ratsashi.


makeken tsakar gidan nasu na dauke da sassa har biyu masu design iri daya,snn ko wani sashe akwai tazara mai dan tsayi tsakaninsa da wani sashen, sashin farko wanda shi zaka ci karo dashi bayan shigowar ka cikin gidan shine mai bungalow dinsa yana da girma sosai don sashin ya fi dayan sashin girma.


Sashen da baida girman ya wuce kai tsaye snn ya haura sama yawuce side dinsa tun anan falonsa ya fara rage kayan dake jikinsa yana yardawa nan kasa while walking like a fierce model cos he have the perfect manly fitted shape and muscular figure.


Ann Cikin part din dake cikin na mahaifiyarsa nasa sashen yake dan kuwa na musamman aka sake gyara yanayin building din tun alokacin da aka haifesa,shiyasa he have his very own parlour da bed room da closet inda ke lode da kayan sawa kala kala masu tsada da kyau. Ya xabi xama a sashen mahaifyrsa ne sabida yafi sakewa sosai da ita. In ka shiga Bangarensa zaka san indeed shi dan gatane awajen mahaifiyarsan..


Bangarensa is well organised kamshi wajen yake kowani lokci sabida kulawa masa dashi datakeyi sosai,dan madaidaicin falonsa mai kyau na dauke da set of expensive and luxury sofas sai madaidacin tv plasma babu wani tarkace ,yana kaiwa tskiyar dakin nasa ya jefar da takalmansa snn ya wuce wajen wanka direct,.


Anan ma Sai da ya kusa hour guda acikin bathroom babu abinda yake sai shafawa kansa ruwa da sabulu ahankali kaman akansa aka fara sauke kalman lalaci da gajiya,sai can daga karshe snn ya fito daure da towel yana goge kansa da wani dan karami,soft palmers cocoa butter oil ya hau shafawa a jikinsa daga sama har zuwa kasa, sai da ya gama yadauko doguwar jallabia kalar toka ya saka ta with small tiny shorts daga ciki. Ya fetsa turare mai sanyi, da Har ya fito zashi masallaci sai ya tuno da mahaifinsa, sai kuma ya fasa ya kulle side din nasa da keys, Sallahn magrib da isha'i yay,snn ya nemi waje ya xauna akan sofa yay zugum harna dan wani lkci.


jin yunwa na neman damunsa yasa ya bude fridge dinsa ransa a harɗe da baiga wani abun kirki anan ba..


Da har xai rufe sai yaga wani shiny leather acan gefe, budewa yy batare da ya dago ba, Birthday cake din da chilhood friend dinsa kafayat buraimo ta aje masa ya gani a aje, gajiyayyen tsaki ya saki aransa yana jinjinawa kalar xubda aji irin nata,wasu dai haka Allah yayisu basu da aji sam sam, kyabe bakinsa yy tuna yadda yake mugun ja mata aji, birthday din da tayi tayi ya saka kanshi acikin hidiman amma yaki to me na aje mai cake duk da uban walakncin daya mata? Girarsa na sama a adage yasaka hannu ya dauki cake din yafaraci kamar dole, yana taunawa yana tunawa da wagagan lips dinta yana jan tsaki  dan aganinsa halittar labbarta daya danyi kato shine kawai ya ɓata ta, but after that she is clean gata da diri mai daukar hankli. Sede shi sam baisan mace mai katoton baki da girman nono. And kafayat can talk for africa kai kamar ma dan shegen son gulma da shishiginta yasa Allah ya bata kyautar katoton baki. Haka nan dai ya rinka debe mata albarka aransa yanayi yanacin cake din kamr ansaka shi ci dole.


Sai can ya koma kwanta ahankli ya fara resting mind dinshi for a while acikin yanayin lumshe ido iya abubuwan da iyayensa ke yawan gaya masa na batun kawo matar aure sune suka fara dawowa masa akansa daya bayan daya.


 Tare da sakin wata shakurarren tsaki yay kasalallen juyi tare da pillown dake manne akan kirjinsa jin kamr cake din ne ya tokarasa akirji. 


Shi Duk yan matan dake bibiyarsa haryau bai ga wacce ta masa daya aura ba,tashi zaune yy cikin damuwa, but how comes he does not have feelings for any girl even kafayat dat was his best friend tun na yaranta data san abubuwa dayawa game da rayuwarsa amma bai taɓajin tai masa aransa ba harynxu.


Dada taƙure kanshi yay cikin zurfin tunani tare da tunowa da maganan daya daga cikin babban yayansu wato brother dimeji a.k.a hamzat bello jimada da yake cemai hala shine dai bai nitsu ya gano tashar wacce zuciyarsa take so din ba.


But Ders are so many girls going after him taya ne ma zai gane wacece aciki yake so mtschew! a iya tunanin su ma kawai wani ciwon kai da wahala yake kawo masa,

Ynx bbn matsalar sa shine ya rasa gane  wacce ce special girl din acikin babes din daya taba sani arywrsa, ance dai ur special girl itace wacce tafi fadowa cikin ranka amma sai yay kwana fiye da talatin bai tuna kowace ya mace aransa ba,gara gara ma his childhood friend din kafayat obviously sabida tana yawan kiransa a waya, alwys acting like his wife, bayan ita then there is this innocent yarinyar data dan kula dashi sosai wani lokci dayaje research dinsa a garin cross river calabar wanda yasan dai sai yana cikin wani damuwa ne yake iya tunowa da ita cos she helped me more than anyoda girl can arayuwarsa.


Kuma harga Allah sukadai ne matan dayasan yake iya tunawa dasu aransa involuntary sabida koba komi yana dan iya sake jikinshi dasu sosai, but in his heart kafayat is just a friend and Adiaha was just a helper.


Altho ADIAHA, was just a coincedental friend baxai iya cewa budurwansa bace..


Wanda yasan hala da baije aikin research agarin su ba dabazai ma santa ba, but despite being a typical IGBO/EFIK girl itace dai ta taimakesa sosai,tana da sakin fuska tayi masa hidiman abinci,ga kulawa na musmmn data bashi dayaje aiki a garin calabar during his scientific research programe na lassa fever.


Life was indeed calm with her dan yarinyar sam bata da hayaniya.


Saidai ayanzu baisan ko inya koma wajen zaije ma ya sameta ba dan tun daya kammala damuwar sa a calabar yabar wajen baisake nemanta koda a waya ba. Yasan hakan dayay xai iya bata mata rayuwarta, He is sure hala ynxu har tay fushi ta mance da shi kamar yadda sauran yan matan dayake dumping dinsu a rana tsaka suke yi.



Wani gullutun Tsaki ya ja tare da sauke pillon daya rungumar akirjinshi yanamai jin haushi kansa a karo na farko dan baisan meyasa ya kasa neman yarinyar kodam yy mata godiya ba.She was nothing but good to him, innocent and care free, sau tarin yawa tayi ta kkri wajen nuna mai irin kaunarsa datake mutuwar yi aranta saidai bai taba nunawa cewa yasan da cewa tanayi ba cos dats was his habits alwys. Yana son yaga mace tana son shi yana nunawa kamr baisan tanayi ba. He love to ignore ppls feelings cos he is self obsessed kuma yana mugun ji dakansa bana wasa ba.


Ko aynxu Ya tabbata dan acikin matsi xcyrsa take da ko kadan baxai tuno da ita ba,Sassanya kuma nitsutsyar murmushin ta ya soma tunawa yanamai jin sauyin yanayi mai tafe da bugun zuciya atattare dashi. yasan dai yay kuskuren rashin yi ma zuciyarta adalci msmn daya guje mata batare da cemata komi ba,she is faultless saidai shi ba mutum bane mai son tunowa da kuskurensa dan haka sauri yay wajen kawar da wann feeling din aransa na jin cewa yay mata rashin adalci dan kar ya karaya sosai,Ransa a dan hargitse ya sauƙo kasa daga kan gadon kamr ana ingiza shi, yarasa meke masa dadi, ruwan sanyi yaso daukawa a fridge dinsa sai yaga babu mai sanyi sosai dan haka acan gefen gadonsa ya tsuguna tare da buɗe bedside drawer nashi da key,ya ciro wata kwali aciki ya fidda wata kwalban wine mai tsada dayazo da ita daga UK. 


Ya dade da dena shan giya amma ji yake yana bukatar sha sabida  yadan ciremai tunanin komi musmmn ma na auren nan dayake dagula mai kwakwalwa, nan ya buɗe kwalban yafara sha ahankli after a while ya yarda kwalban akasa ya kwanta batare da yin tunanin komi ba daga nan sai bacci.


 

Washe gari da safe

Farakal din Agogon dake manne jikin bango ne yayi ticking dot 6:30am dai dai na safiyar ranar friday tare da yin sautin alarm mai karar water ascent wanda tuni ya gauraye wajen da wani irin kara mai cikka kunne, 


tashi yayi firgit tare da miƙewa daga kan lallausan katafaren gadon da yake kwance akai,yana mai dafe kansa datake mai nauyi.


Dagowa yayi sann ya juya ya kalli agogon da ya farkar dashi daga bacci yaga har 6:35am tayi, da dan hanzari ya diro kasa daga nan baijira ba ya fada toilet din dake cikin dakin shi cikin hanzari ya saka toothpaste ajikin brush dinsa wanda yake fari kal da sauri da sauri yayi brushing teeth dinsa ya kunna warm shower yay wanka sannan ya fito daga toilet din daure da hadadden white body towel da kuma wani dan karamin towel din a hannunshi yana famar goge fuskarshi da ita har ya karaso gaban wani babban mirror da mutum kan iya kallon kanshi tun daga kai har kafa yana mai kare ma hadadden dirinsa takaitacen kallo tare da sakin nannauyr ajiyan zuciya, sake tunowa da lamarin Adiaha daya karayi aransa yasashi lumshe idanunsa tare da buɗewa ahankli cikin rasa dalilin dayasa ya fara sakata aranshi.



Dagata cikin mirror ya hango empty wine bottle dinsa akasa dayasha jiya yaja tsaki bai kara kallon wajen ba yafara goge kanshi cikin saiɓi.

Aransa yana mita yana cewa Inba irin wann damuwar auren ba maixai saka shi yasha giya dan ya samu nitsuwa?


yana cikin karasa goge kanshin kenan zai shafa mai yaji karar wayarshi na ringing,Dan daga girarsa sama yy da har yayi kaman bazai dauka ba sai kuma ya juya ya karasa inda wayar take yana ganin mai kiran da sauri yayi maza ya dauki kirar tare da neman wajen zama cikin risina kai mai nuna alamar tsantsar girmamawa tamkar mai Kiran na gabanshi zama yayi kamin ya kara wayar a kunnanshi tare da cewa 


"mamy na kin tashi lpya?


Daga daya bangaren aka amsa da murya kasa kasa da cewa lpya lau Alhamdulillah ,sannan ta sake ce mishi Ahamad harka shirya ka fita ne? 


Fuska ba yabo ba fallasa yace à ah mamy Amma saura kadan yanzu zan shirya in fito ina dan sauri ne yaudin.. 


Ajiyar zuciya ta sauke snn tace ok toh kadai sauko din, na shirya maka breakfast inajiranka akasa inason magana dakai. Take yaji walwalar fuskarsa ta dauke tuna cewa basuda wani maganan da suke masa a kullu yaumin face na AURE ita da mahaifinsa, da can dai yadauka wa yan mata kawai ake irin wnn takuwarar akan suyi aure subar gidan iyayen su amma sai gashi shima baida katabus agidansu sabida duk sauran yayunshi suna da aurensu shine kawai ya rage baiyi ba, adan gaggauce yace "toh" Yana fadan Hakan ya katse wayarsa batare daya jira Wani furucinta ba, da alamar ranshi bai wani so amsawar dayay ba.


Tsaye ya mike cikin sauke huci tare da yin wani ball da empty wine bottle din yanamai turasa cikin karkashin gadonsa.


Closet din kayanshi ya bude sannan ya dauko wani true blue men suit mai laushi da tsada ya saka ajikinshi,ya bude wata madaidaicyr transparent safe ya dauko nordstrom neck tie dinshi marching colour mai azaban kyau na kamfanin steve sannan ya sanya ya masa das,agogon shi na rolex submariner ya makala a hannunshi na dama sannan ya dauki 

Turaren paco rabane  dake gaban mirror dinshin yafesa a jikinshi Duk Inda ya juya kansa qamshin ne ke binshi.



gaban wata small coffee table ya Mika hannu ya dauki car key din motar sa dake ajiye akai da kuma wayarsa daya jefata acikin aljihun sa sannan ya jawo takalmin shi baqin cover shoes mai sheqi yasaka a kafarsa snn ya fito daga dakin yana saukowa yana dan kallon agogon hannun shi yaga wai har bakwai da rabi tayi.



Saukowa yake daga kan benen cikin kwanciyar hankali da natsuwa har ya karasa sauka ya isa katafaren parlourn su.


karasowa yayi cikin parlourn ya isa wajen mahaifyrsan dake tana da dan haske tasanya wani babban atamfa purple colour an mata dinkina alfarma sanye take da farin gilashi à idonta Gabanta kuma 10 inches dinning table ne dauke da hadadden royal flask din tea tazuba Kadan a dan karamin transparent kofi na shayi tana zuƙa ahankli, Nan ya karasa gaban ta tare da zama dab yana kalle kalle can snn yace mamy yana ganki ke kadai anan, DAD fa, kodai bai farka bane? 


Sauke cup tay agabansa ayayin da tadaga idanun ta sama tadan kallesa kadan tace badai bakaje sallahn asubah yau ba? 


Fuska ba yabo ba fallasa yace na makara, tace hmmm shiyasa, Baban ka tun a lokcin ya fita, Jiya ya tura da saƙo wajen ka an sanar maka? 


Dauke kanshi yy kmr Bai amsa ta ba ya girgiza kai. Bata kulashi ba tace malam liman yace min wai jiya ka dawo da wuri amma kuma ka rufe kofa kuma wayoyin ka ma duk a kashe. a kasale cikin rashin son jin maganan Yace mamy nagaji ne shiyasa nay bacci da wuri. Cup din data aje mishi ya dauke ya kai baki badon yay niyya ba 

Ya kurbi kadan snn ya sace kallonta yace Mamy Pls lest have our breakfast now in mungama mayi maganan later, batace mai uffan ba ta zauna tafara serving dinsa beans cake da wainar panke, har ya deba yafara kaiwa bakinsa kenan yana taunawa sai ya dago kansa sama caraf idanunsa suka fada kanta ganin yadda ta rabza wani irin tagumi tabi ta zubamai ido tanata kallon sa cikin yanayin matsanancin damuwa da zurfin tunani.

#surayyahms

08060712446

Follow wattpad @surayyahms.KISHIYAR KAƁILA....3



Sihirtaccyr Ajiyar xuciya mai nauyi ya sauke snn ya dauke kansa akanta jin har tafara fidda masa abubuwan dake wakana daga cikin zuciyarta na irin maganganunsa da sukayi jiya tare da su anty mojushola da dayan antynsa ramatou.


Cikin gyara zaman farin gilashin dake sakale a  idanunta ta karashe bambaminta da cewa Ahmed ai kasani sarai cewa Kafayat itace xabin su kuma sunsakata aransu sosai amma haka kaki kula yarinyar nan sam ka watsa ma kowa kasa a ido,let me inform u dat ur aunt ramatou is soo pained dataji wai baku fahimce juna da kafayat ba,and ur aunt moju is even worst, cos she is not even talking to ur father,ko gaisuwar sa ynxu bata son amsawa,ai kasanta yar debar xafine.

  she is just blaming me up and down dan haryau gani take kmr nice nake controling din rayuwarka kaida ubanka, tace komi dake faruwa ynxu lefina na ne, waini na mallake ubanka na rabasu da shi sai abunda nace masa kawai yakeyi.


"Ni har na rasa mema xance musu,iya Rashin dawowarka gidan nan jiya bakaramin jamin cin fuska yyi ba,Ahmed ure just too stubborn, kai dakanka u knw how ur anties behave with me, amma kodan ni baxaka iya behaving kanka na lkci guda ba?sai kasa surika maida duk wani abunda ka aikata akaina dan awajen su nice nake daure maka gindi a gidan nan?gaskiya baxata saɓu ba, Enough is enough Ahmed! Wallh ka shiga hanklinka dan ni nagaji da ku baki daynku baku kuka kawoni duniya ba.

  kadena kuma jin kanka kamr kafi karfina cos ure still my child,in har na isa dakai ina son ka tabbatar min da haka ta hanyar yin abunda nake so kawai, Ahmed for the last time yau ina gaya maka ka kawo mana matar aure, bana sonjin wani dogon bayani daga gareka anymore.


Dan ina daga maka kafa dole ne abun naka yafara wuce misali,km bawai dan duk wani abun dakake aikatawa da rayuwanka awaje ban sani bane wallh nasani sarai cewa kana tarayya da yan mata,i dont care how u wil do it..nide kaje ka kawo min mata acikin su kowace ce cos i am tired of cin fuskan da dangin ubanka suke min akanka, i ave heard enough, ka tsaida matar auren kawai kowa ma ya huta, dis is ur last chance with me inba haka ba saidai kaji ayyururi, dan duk wacce nakara jin labarin cewa kana kulawa awaje ita xamu aura maka koba ka sonta wallh!.


Tsaye ta mike tana huci

"Dake nice bare agidan nan aidolene ku hade min kai kuna nunamin warayya,kowani sharri sai ace ni,kwanan nan dangin ubanka xasu ce min hala ni na haɗiye destiny dinka na aure, "komi nice, amma kai da kake ɗana nake alfahari dakai duk duniya baka ganin kunci na bare kuma xubar hawaye na.


Hawaye ta farayi cikin sheshhkar kuka tace "toh shikenan, kaje Ahmed gaka ga dangin uban naka da suke nuna cewa sune kadai suka san xafin ka,sune masu sonka kuma sune da iko dakai,nikuma da ban da iko dakai ai Allah ne gata na. Tana fadin hakan ta fashe da kuka tare da barin wajen a gaggauce.


Jiki a mugun sanyaye ya sauke kofin shayin dayake kurba kasa bakinsa abude yana kallon yadda tahaura sama a fusace ta barshi wajen da alaman bacin rai sosai  ayayanin ta, ajiyar xcy mai tsananin nauyi ne ta kufce masa jin xuciyarsa na halbawa da wani irin tokararren damuwa, sai can snn ya girgixa kansa cikin sunkuyar dakansa kasa jin xuciyarsa na bugawa da bala'in sauri...aransa yace "this is really getting serious"...


Abincin dake gabansa ya kalla atake sai yaji komi ya sane masa, yafi minti talatin a xaune batare da yasan abun yi ba, tunani kala kala yaxo mind dinsa amma bai fahimce inda ya dosa ba, he just cant afford to make his mum cry bcos of all this dolene kawai ya nemi mafita saidai bayajin har abada xai iya kasancewa mijin kafayat. Shikan sa baisan dalilin sa najin hakan ba, haka kawai yaji aransa cewa baxai auri kafayat ba, and thinking about oda girls just make him sick sabida sunyi yawa,Adiahar can kuma tayi masa nisa,kai bama wai dan nisan kawai ba, tuna cewa sai yaje garin su ya lallabeta ya bata hakuri akan abunda yy mata yasaka yakejin  muguwar kasalar karfafa magananta aransa duk dama dai itace gwamma gwamma.


But He is just not feeling intrested in begging or petting anygirl at all, duk ya rasa ta ina ne xai fara warware wann tulin matsalar tasa ,yasan dai baxai iya yanke wani hukunci aynxu ba. 


Wayarsa yasaka hannu ya dauka ahankli ya bude call log ya fara scrolling Tunani kala kala yana yawo acikin kwakwalrsa.


Adede kan wata lamba da aka rubuta BANJI ya dakata, Da har xai dialling sai ya tuna yanayin abokin nasa dake son kasancewa da budurwansa hidaya a kusan kullum, karamin tsaki yaja sann ya shiga wajen text message ya rubuta sako "i need to talk to u banj! snn yatura masa baiyi ko minti biyu da turawa ba yaga reply an rubuta" is not safe,pls lets chat!.


Kai tsaye yafahimce cewa ba shikadai bane awajen dayake, dan haka babu bata lokaci ya hau rubuta masa damuwar san ta text msg din dake Banji din abokinsa ne na tun primary har sukakai secndry iya university ne kawai basuyi tare ba amma yana daya daga cikin aminansa na kud da kud.


Banji na xaune tare da babe dinsa hidaya yaga shigowar Sakon wanda ya shigo da wasu irin rikitattun bayanai na cewa Ahmed yana son yyi aure by all means xuwa next week but almost duka yan matan dake available bayason ya auresu.


Daga xaune abokin nasa yake amma saida ya miƙe xumbur yanamai duban text din da tunanin ko Ahmed ya samu tabun hankli ne for being dis confused, kallonsa budurwansa take har ta karaso gefensa ta tsaya ayayin da taga ya nitsu yana karanta sakon, ya memeta yakai sau biyu ita kuwa tsaki taja ta dauke kai dan ta tsani Ahmed din sosai sabida yadda yake bala'in rainawa mata hankli,bai kulata ba ya amsa shi..

Ya rubuta masa "Guy are u insane?..waime kake cewa ne.


Bai amsa shi ba ya rubuta.."Can we see now?Banj..i need to see u now..im desperate! Mamy is upset with me akan maganan auren nan.


Banji na daga ido yaga budurwansa ta tsume ta hada gabar da yamma tana watsa mai wasu uban harara masu xafi  girarsa na sama a dage ganin tayi masa alaman kar yace masa yaxo da alaman dai bata son xuwan nasa,hakan yasa yy shruging shouldern sa dan shikansa ya tsani draman su subiyun dan kullum acikin fada da juna suke. Bai turamai text ba sai kawai ya kirashi awaya, bayan kmr ringing biyu sai ya dauka suka fara magana sama sama dake budurwan tasa bata basu waje akan lkci ba har saida taji yace masa karyaxo gidan sabida yana tare da ita.


Duk da takaicin da banji ya bashi dayace masa hakan Baidamu ba sabida a matse yake yana neman koxai samu wani mafita na daban.  A wayar kawai suka soma yin maganan since its urgent.


Bayan kasancewarsu su biyunsu awajen nan Ahmed yafara gaya masa Abubuwanda ya faru da abunda yake ji aransa.


Bayan saurararsa na dan lkc wani Ajiyar xciya banjin ya sauke snn yace "guy calm down, indai na fahimce ka da kyau kana nufin sabida fushin mamy kake son kayi auren nan cikin gaggawa amma bawai dan kana son yi ba.. and then baka son ka aure best girl friend dinki kafayat buraimo not bcos batayi maka ba, but sabida dan kaidai baka son ita ta kasance matarka...snn sauran yan matan ma basu maka ba,and yet innocent babe dinka na can calabar itace gara gara amma baka son kaje ka bata hakuri right?..


Yace yeah..sumting like dat..


Girgixa kai banji yayy baice komi ba. Sai can snn yace okay..Ahmed, ka riga kasan cewa kai namiji ne wanda bakasan ina ka dosa akan mata ba,i mean guy, ure soo scruternixed wallhi baka da alqibla acikin burinka na aure..ure just lost.


Fusknsa a daure yace "yes am lost! thank u if dats a compliment. Since i am lost can you pls find me?see Guy Just tell me wat to do dan Allah. Wnn matsalar yafara samun damuwa. Wai ahaka bacin ran mamy fa kenan? Ran da na hadu dana baba na kam hala sai dai insha duka dan naji ance nema yake agidan kamar kudi.


Banji yana dariya Yace hmm aikai din ne bamai iyar maka sai Allah, jokes aside Lets think outside the box dan Ta hakane kawai xamu iya samun spec dinka tunda dukan wanda suke available din basune agabanka ba amma dai kasan in de kana son burinka dana mamy ya cika acikin gaggawa dole ne kayi hakuri da result dinko?


Nodding kansa kawai yy amma Baice komi ba.


Banji Yace okay i have an idea, Ahmed baice komi ba alaman yana sauraron shi,..dan shiru yy kafin nan yace "Ahmed,nace why not munemi wata babe na daban sai ayi arranging contract marriage tsakanin ku. After some months or years or so, saika saketa ta tafi basai wani abu ya shiga tsakaninku na aure ba,the marriage shud just be on paper like a name sabida kwanciyar hanklin famlynka,i am sure by then kafin contract din ya kare harka samu wata wacce kake asalin so din right?.


A mamakance sosai Ahmed yace " _kini? mi, adehun igbeyawo?_ 

(What? Me,contract marriage?)


Tun Kafin banji ya amsa a firgice cikin axalxala masa masifa da ihu yace "kamin shiru malam, _Ṣe o ya were? .. kini imọran aṣiwere ni banji yii?_  (kana hauka ne?..what stupid idea is this)


Murya kasa kasa banji yace. _Aaa kini, shebi dats kini o fẹ?_ (Aaa, Ba abunda kake so bakenan?) Yafada dramatically sounding irin shebi dats wat u want right?.


Ido a lumshe Ahmed yace but dats nonsense now...contract marriesh Ahhhh banjiiii _ure Egba asiwere mi ore_ (ure absolutely mad my friend)


daga kafadu sama Banji yy snn yace okay oo nide na gaya maka nawa iya naxarin,dan nasan hakan ne xaifi maka sauki nide aganina..Cos now idan ma aka samu matar auren bafa sonta kakeyi ba,Ba xaka kulata ba,toh ba gara kayi na contrct wanda xaka san yarjejeniya bane a tsakaninku tana rayuwarta kana naka?


"Yen yen yen yen malam kamin shiru kawai. Is marriage a joke to u?


Dariyar mamaki ne ya kufce wa banji Cikin dariyar yace hmmm says by the person who want to get married in two weeks amma baida tsayayyen budurwan ayanxu.


Tsaki mai tsayi Ahmed yaja cikin mita da bambami mai yawa kamar matar mamaci yanacewa _i'm daju dat gun ọfun ọrẹbinrin ti urs ti mu u_( I am sure dat  long throat girlfriend of urs has intoxicated u)..


Banji yace ahhhhhhhhh damilare Ahmed bello pls do not insult my swt girlfriend, errn aigara ni na ajiyeta kuma ina sonta snn auranta xanyi..


Cikin katsesa Ahmed yace shut up ure in lust jare, fuck u both. But Its okay sha ka aje wayarka kusa xan kiraka anjima idan nagama tunani And dont expect me to thank u for this stupid advice oo. _O ya were,look at u, Awon contract marriesh gang,mtsssss_ Har ya katse wayar banji bai dena dariyarsa ba.


Bayan nan ya dade a xaune akan chair na dinning table din yana juya maganan banji acikin ransa,saidai ta duk inda ya bi da maganan sai yaji hakan bai masa ba, duk ya rasa meke masa dadi, yasan kuma idan ya nemi wani extra shawara daga wajen dayan abokinsu bankole abu dayane kawai xai gaya masa cos he is a party boy,yasan cemasa xaiyi ya shirya suje club yy wa wata cikin shege su haifi dan sukawo gida cos aganinsa a grand child is wat our parents want,and he cant do that ko dan for the sake of his mamy, dan duk iskancin shi dai bai taba aikata xina ba sabida iyayensa sun bashi ilimin addini sosai, mikewa yy jikinshi duk babu kwari snn ya fice daga sashen yana tafiya ahankli yana kallon agogon hannunsa, gun motarsa kirar Lexus ya nufa cikin kankanin lkcin ya bar cikin gidan nasu.


tafiya yake ahankli akan titi har ya iso wani layi da ake saida manja,equshi, da busashen kifi wanda mafi akasarin mutanen wajen  inyamurai ne,rage tukin yy sabida cunkuson jama'a, ya shiga murxa stiring motarsa ahankli yana dan satan kallon wata poster da akasa abakin wani shago na ogoja market Festival in calabar. Lokaci guda mind dinsa ta daka tsalle kwakwalarsa ta hau tuno masa wann ranar being the first day daya soma cin karo da kyakkwan fuskar yarinyar nan ADIAHA agarin calabar.


Hanyar dake 61,Aguiyi ironsi street yabi ixuwa maitama district hospital inda yake da first casual appointment dinsa nayau  ahankli yake tuki danhar ya isa bakin gate din asibitin tunanin abunda ya faru a wann ranar festival din yakeyi aransa Da kwakwalrsa..


After some few minutes ya kammala aje motar sa acikin parking space na hospital din, sauke ajiyar xuciya yy kafin nan ya sauko dauke da jakar laptop dinsa yana tafiyar sa mai aji kowani step dinsa acikin nitsuwa wanda ko kallo daya kamasa baxakace yana cikin wani damuwa ba.


Direct ya haura sama private office dinsa dan shi babban consultant ne a asibitin yakan duba files din duk wani cases na marasa lpya daya shafi communicable diseases.


After 20 minutes.



Zaune yake akan kujeran haɗaɗɗen office ɗinsa wanda yake juyawa dashi ahankli ga wani sanyin a.c mai qauraye da qamshin turaren sa daake tashi ahankli yanamaai mamaye wajen, sosai office din nasa ya hadu, yana ɗauke da set ɗin 2 L shape cushions, table da kujerun xama na patient, sai gadon dubiya, fridge da doctors Cabinet. 


Daga gefensa kuma show glass shelf ne wanda yake shirye da Awards da frames ɗin hotuna insa da yake sanye da convocation gown as the best overall medical student in uni of ibadan,obafemi awolowo uni, ɗayan frame ɗin kuma duk honors dinsa na U.K da manchester ne he is also the best, sai ɗayan kuma da Labcoat da electronic microscope ayayin dayake gudanar da disease research a calabar national science laboratory..


Kallon hoton ya dinga yi yana tunowa da fuskar Adiaha tana masa murmushi..dafe kansa yy aransa yace ohh Allah!! Ni kode yarinyar nan ta mutu ne..haka kawai seta fadowa mutane arai?


Knocking ƙofar aka yi wanda ya sashi katse tunaninsa,nurse ce ta nemi ixini kanta a sunkuye a ƙasa, hade rai yy bai amsa ba ya bude wani file ya fara rubutu sai can kmr after 3 mins snm ya bata izinin shigowa ciki,Da sallama a bakinta ta shigo ta gaishe sa bai amsa ba yace "what?..bakinta na dan rawa ss..sir..you have a call from..tun bata karashe ba ya datse ta cikin ixxa yace "where?

Speak fast..kina wani abu kamar doluwa..


Da kyar ta hadiyi yawu cikin gaggawa snn tace "Dr hassan's hospital sir..its an emergency...

They..


Ya kara datse ta

"....Need my urgent attention?


Tace "ohhh, yes sir!..


Daga nan bai kara kulata ba ya cigaba da abunda ke gabansa harta gaji da tsayuwarta ta bar wajen.


Fitar ta keda wuya ya dau wayarsa ya wuce Dr hassan's private hospital dake iller cresent, no 5 katsina ala street cos is not far, duk dai acikin maitama din yake.


Yana isa ya ci karo da dayan abokin nasu Doctor ibrahim bankole suna cemai Banky anan shi yake aiki he is a correct sugeorn shiyasa idonsa idon mata lolz.


Ko wani gaisawa basuyi ba suka fara aikin daya ke gabansu, its a streanous job sai wajajen karfe biyu sann suka kammala suka fito yin sallah azahar suka ci abinci,dr banky yayi  ta tsokanansa akan batun auren nan da ake matsa masa yy agidan su, yana yi yana bashi shawarar cewa kawai yadawo  manemin mata kawai irinsa domin suji dadin rayuwar su regardless of the stress,yace masa with girls he wll enjoy his life better saidai ko kulashi ahmed din baiyi ba,dalilin hakan yasa ya karajin ma baxai taba iya gaya masa asalin damuwarsa akan maganan su kafayat ko Adiaha ba, haka nan yaja bakinsa yy shiru har suka koma bakin aikinsu..


As usual 5:30 na yamma suka kammala komi but by then Doc banky ya gama cika masa ciki da xancen yan mata, da abu dayane kawai xaice ya karu da shi,ganin doc banky dan shige shige ne kuma yasan kan yan mata yasaka acikin tadin nasu Ahmed yarinka kawo masa xancen contract marriage saidai da mamakinsa yaji banky na cewa ai babban kuskure ne yin contrct marriage yanxu sabida yawanci scammmer sunyi yawa aciki ba a samun mata masu cika alkwari,snn yace masa ba afiye cin sa'a akai ba, har yadan babbasa labarin yadda mata suke daukar advantage din auren suyi trapping din maxa su kwace arxikinsu da kwancyar hanklin famylin su,wasu kuwa har kashe maxan nasu suke dan su maye gurbin arxikinsu.


Anan ma kan Ahmed ya dada kullewa sai imagining din abubuwan yakeyi akansa, dan yasan mata dayawa sun saka shi a target dinsu, da yuwar in yy contract marrige din nan shima xai iya xamowa scape goat a hannun wata.


And his family too, ther are too desperate human beings,iya sukadai ma xasu iya sakawa yarinyar tayi betraying din contract dinsa tace tana son xama dashi na har abada And before he knows it saidai yaji anyi drugging dinsa har sunyi cikii an haihu bada son ransa ba, yasan daga xarar ya haihu da mace iyayensa baxasu taba amince mishi ya saketa na har abada ba....Ahhh another drama..tunda ya dau hanya babu abunda yakeyi sai calculations na rayuwarsa..dan daga yanayin bayanin Doc banky ya fahimce cewa yuwar contract marriage din nan agareshi akwai hatsari aciki sosai...



As usual karfe shida saura ya dawo cikin gidan su,bangaren su ya nufa jin ko ina shiru yasa ya wuce side din dakin mamansa,nan ma yaga ko ina a kulle alaman haryanxu dai bata sauko ba, yaiyita sallama tanaji amma bata amsa shi ba

Jikin shi a mugun sanyaye ya koma room dinsa. Tunda ya shiga dakin bai iya tabuka komi ba sai lissafe lissafe, washe gari da safe ma kusan the same thing me ya faru da shi, gashi yanata avoiding din mahaifin sa, ga nan mahaifiyarsa ma ta fara avoiding dinsa. Yaune ranar da ya soma fita aiki batare da yaji muryanta ba ko ta amsa gaisuwar sa ba, sai yaji kansa daban, baida sukuni a xucyrsa ko kadan.


Kusan kwanaki biyar ya dauka ahaka duk ya rasa nitsuwarsa, yy kkri sosai wajen shiryawa da mahaifyrsa amma taki sam ta kulashi kullum dai magana daya take gaya masa nacewa inhar yasan darajarta yakawo matar aure.


Gashi ya riga ya yanke aransa cewa baxai dau risk din yin auren contract din nan ba wanda hakan ne ya dawo masa da tsoffin options dinsa guda biyu dasuka rage masa wato chilhood gf dinsa kafayat buraimo da kuma wancan calabar girl din Adiaha.



Yau juma'a da wuri ya dawo daga office sabida yana mutuwar son ya samu isashen bacci dan gobe sartuday xaije yay spending wknds dinsa awajen abokinsa Banji..


Althouhg he knws his annoying girlfriend wud be der amma bai damu ba dan yasan banji ne kadai yake da matured sense din da xai iya bashi shawara mai kyau mai inganci akan kafayat da Adiaha duk dama yasan aransa bayajin xai iya amincewa da kafayat amma kuma aransa he is sumhow attached to her don sun mugun dadewa tare kuma babu wata ya macen data sanshi ciki da waje kamr ita,and dats why he feel she just "can't" be his wife. Acan kasar ransa sam sam Bayason macen data gama sanin press button dinshi da duk wani launi na weaknesses dinsa.


Shidai Yafison wanda tafi son shi,snn wanda xai iya controling dinta sosai both emotionally physically and mentally sabida sam baison wani rigima da rainin hankli daga wajen wata ya mace acikin hidiman rayuwarsa...


Tun dawowarsa yake dakinsa banda sallaah babu abunda yake tashi yyi, yauma da wuri ya kashe wayarsa yy bacci sabida yasan inbaiyi ba dan aikan mahaifinsa xa'axo yafara kwala masa kira bayan yasan bai shirya haduwa da baban nasa aynxu ba.


Surayyahms 08060712446*KISHIYAR KABILAH 4*


BY SURAYYAHMS.


....washe gari Karfe bakwai da rabi na safiya Ahmed ya gama parking din motarsa a parking space na gidansu bayan ya dawo daga mrning workout awani nearby gym dake cikin anguwar su.


Ahankli ya bude motar ya fito yanamai kallon motar dad dinsa dake parke a kofar babban sashen wanda ko ba a gaya masa ba yasan yana ciki, baibi tanan sashensa ba kawai ya nufi balconyn da xai sada sa da asalin kofar shiga babban falon gidan dan ya duba mahaifrysa dake kowani sartuday a main house take shan coffe,a can ciki yyi sallama ya shiga babban falon ya tarda Babban dadarsa wanda yake bi, wato sister xainab moturayo da danta sha'fiu dake bacci tana kwance akan doguwar cushion tana kan kallo,tana ganinsa ta mike xaune cikin mmkin ganinsa tace "Dami,.is dat u? Tun jiya naxo gidan nan da dare amma banganka ba i even tot ure out of town..Ba tare da ya kalleta sosai ba yabi ya share abunda take cewa din snn yace "sister senap..pls hv u seen mum?"tabishi da harara sama da kasa snn tace ohhh baxaka ma iya gaishe ni ba kana tambayar mum? _Dami se oya were?_ girarsa na sama a ɗage ciki ciki yace oya good morning toh"..mum fa? Tsaki tayi..tace Na hadiyeta, ko kulata ba baiyi ya daga kansa sama ya nufi stairs dan yayi sauri ya bar sashen, kallon sa ta dingayi tana dan karkada kai harya bace ma ganinta.


Ahmed ya kama hanya kenan xai haura suka kusan cin karo da Dad dinsa nan take ya ja baya da sauri tare da dan ritsinawa har kasa yahau gaishesa. _baba owurọ_


Babu yabo bbu fallasa mahaifin nasa ya amsa snn yace "ina nemanka a falona ynxu, kar ka bata min lokaci ,tun bai amsa ba ya dada memeta masa kalmomin da yare yace _Maṣe fi akoko mi ṣòfò_ a ladabce yace _yes sir_ dad din nasa bai kulasa ba ya juya ya koma ixuwa falon sa nacan sama inda babu mai shiga sai ya bada ixini.


Nan Atake Ahmed ya share wata irin xufa dake keto masa a goshinsa xirrrrrr yabi ya shafe kansa yana sauke ajiyan xuciya snn ya shiga haurawa saman a sanyaye kmr ba shi ba.


Jin baida karfin gwiwa yasa yayy kwana ixuwa dayan bangaren, Dakin mahaifiyarsa ya nufa cikin gaggawa lkcin tana xaune agefen gadonta tana waya sabuwar mai aikinsu ta kawo mata fruits a faranti ta aje kenan xata fita,nan ma ta gaishe sa ko amsawa baiyi ba tsabar yadda xucyrsa ke bugawa, a takure ya nemi gefenta ya xauna har ta gama amsa wayr tana kallonsa abunka da uwa data gansa a tsomare yana kame kame nan daman ta sauko tace "Ahmed lapya kuwa? Ya naganka haka, rusunawa yy har kasa ya dan marairaice mata yace "mammy don Allah na roke ki, nasan banaji, amma pls kiyi hakri ki raka ni gun Dad cewa yy wai yana kirana" 


tayi masa wani irin kallon takaici tace "saini ce xan raka ka kuma?tab Ashe ko baxa ka je  ba. Wani irin kasala yaji jikinshi ya dirar mai, nan danan ya ciro handky ya share xufar fuskarsa baice mata komai ba ya mike gwanin ban tausayi ya fita daga dakin har yafita bata dena kallonsa ba ya nufi falon dad dinsa...


Ajiyar xcya ya dinga saukewa taciki dan yasan halin baban sa da taurin kai inhar ya xantar da hukunci akan Abu toh ya xauna kenan, aransa yanata fargaban abunda xai je ya tarar, da kyar ya tattaro nitsuwarsa yy ta maxa ya fuske snn yy sallama, xaune ya tarda Dad din nasa yana shan black coffee dauke da remote din TV a hannun sa, yasan dad din nasa promax dinsa wajen nuna ixxa da kuma iya rashin mutunci dan haka a mugun ladabce ya xauna kasan carpet din dake tsakiyar falon ba tare da ya kallesa ba, sai can snm yace baba gani


Dad din nasa ya ajiye kofin coffee dake hannunsa yace "ka gama playing din hide nd seek din naka dani ? 

 Ahmed ya dan yi gyaran murya ba tare da ya shirya ba yace amm.. Dady wllh ba hka bane aiki ne daman yyi min yawa a hospital"..


Cikin datsar numfashin sa Mahaifin nasa yace shut up jare,ka rufemin baki, am i ur mate? kansa a kasa yace _Ma binu sir_ 

Ahankli yace" Aahhhm sorry sir, baban nasa nayi masa wani irin kallo yace "stupid".


Tura kofar da akai yasaka suka maida hanklinsu duka bakin kofar, Mahaifyrsa ce ta turo kofan falon ta shigo tana wani irin qamshin turare mai dadi saidai fuskanta duk ba asake ba da alamn takasa samun nitsuwa ne dan haka tabiyo sawun danta, sosai Ahmed yaji relieve dya ganinta ta,ko kallan sa batayi ba nemi gefen mai gidan nata ta xauna a cikin nitsuwa.



 A hankali Ahmed ya dan dago kai yana kallonsu ganin sun xubamai ido yyi yawa, wani irin hatsallen kallonsa ya ga babansa na yi, hkn yasa ya dukar da kansa sosai 


Prof bello ya girgixa kai ya sauke ajiyar xuciya mai sanyi snn yace my son,waime kake nufi da mu ne? Cos ive failed to understand u..


Yadda mahaifin nasa yy masa tambyar a nitse yasaka Ahmed shakewa taciki kasa cewa komai  yyi har lkcin kansa na kasa,prof bello ya maida kallonsa ga TVn dake ta aiki a falon, sai can snn yace "shknn, dat clearly shows dat raina mu kawai kayi dama,irin ure now a professor and a doctor, and then _o ti dagba awọn iyẹ ati iwo_ ya kyabe baki "Ahmed Uve really grown some wings and horns, ka kasa sanin cewa ka girma, ure now 32 abi na 33 amma babu aure, kuma ko kunya bakaji, Oshey ooo, shame on u! 


Wani irin shiru wajen ya dauka snn baban nasa ya dada cewa its okay ni dama na riga na yanke shawara,tunda babu wacce kake so din mu xamu hada ka aure Da KAFAYAT yar ALHAJA IMAM BURAIMO, her father is a good muslim masha Allah, so in two weeks time xan je ayi magana agama kome, saika je kayi shawara da mind dinka nd bet me,no one will ever change my mind, _oya jade_ ka tashi ka bamu waje yenxu yenxu..


kasa ko da kwakkwaran Motsi Ahmed yyi daga inda yake a durkushe kamr wanda baiji me aka cemai ba dan komai nasa ya tsaya masa cak, da kyar ya shiga share xufar dake keto masa a fuska ya daga kai adan birkice maganan na dawomai akai one by one


Muryansa na rawa rawa a dan rude yace Ahhhh baba,marriage ? kafayat ké? dad but dats too harsh now.. _pls baba ṣugbọn iyẹn jẹ lile, check it_.. Ayadda ahmed ya fidda maganan da dagon murya soo disrespecfully haka nan yaji Sauƙar wata mari akan fuskansa saida ilahirin wajen ya dada daukawa da wani irin shiru, rai abace baban nasa yace "shut up, niba shawara ko ra'ayinka naxo nema ba, _pa ẹnu rẹ_ see...the audacity!


Mun baka isashen lokaci iya lokaci amma me kayi da shi? Me kake nufi da cewa dats too harsh,oya _setumo_ harshness? C'mn go on define harshnesh leme hear, Abunda ka kasa ne dolene mu muyi maka. 


Ahmed ya sauke hannun sa daga kan face dinshi fuskarsa kamr na wanda xaisaka musu kuka,ransa a dagule yace but "kilode ti kifayat baba? Wai Meyasa sai ita ne dan Allah..i want to make my own choicess.


Mahaifiyarsa ce ta amshe maganan ta hanyar saka musu baki tanamai hararsa tace "and why not her, kowa de yasan kafayat buraimo budurwanka ce tun kuna yan kananan, Yarinyar nan tana matukar sonka, and she is ready to marry u at all cost amma haka nan kaki bada kai, Dago kai yy a mamaknce yana kallon Mum dinsa da ko kadan baiga alaman hkn ya wani dameta ba..


Baidai rusuna ba ya sauke muryansa kasa kasa yanamai cewa Dan Allah kuyi hakuri baba pls _laarin mi ati kafayat tun jẹ idiju_ in yafadi da yare saiya fadi da hausa dan gani yake kmr bajin shi ma sukeyi ba, yace na rantse btwn me and kafayat is still very complicated, haryau bamu dedeta kanmu akan maganan aure ba tukuna. Our relshp Is still very complicated.


Baban nasa ya bisa da wani irin kallo snn yaja tsaki muryansa kasa yana cewa "Oshey mr complicasion..Look at me young man, i dont care, u hear? I said _Emi ko bikita_ ...


Saukar dakansa yy sosai yafara rokonsa kamr ba shi ba,sai magiya yake da yaren su yana cewa Baba mi binu jọwọ dariji mi, mo mọ pe emi ko tọ,Baba dan Allah kayi hakuri kayafeni nasan inayi maka laifi. Baban nasa Bai ko kulashi ba kuwa sai can yace ka tashi ka bani waje. 


Ahmed ya dada susucewa  Dan Allah kayi hakuri.. kayafe min _pls mo bébé fun idariji baba_


Shiru duka suka masa shima sai yy shiru sai can yaa kara matsowa yace Toh Please can u consider me and give me dat 2wks sir, in sha Allahu xan kawo mata kafin nan i promise i wont fail at that. Baba pls and pls _jọwọ ro mi ki o fun ọsẹ meji sir Emi ko kuna ni iyẹn ṣe ileri u._ 



"See young man, i am not giving u any ultimatum, na riga na yanke hukunci akanka period, nace kaji me nace maka kam? i said _wo ọdọmọkunrin, emi ko fun ọ ni akoko akoko igbẹkẹle.._ 


Shiru ahmed yy jin kansa na juyawa sosai, Auren sa in 2weeks time kuma waida da kafaya?,iya hakan da ya bijiro masa a xcyrsa ne suka shiga yawo masa atsakar kansa, ji yyi kmr ya saka ma iyayen nasa ihu cikin kuka, Muryar mahaifin nasa ya ji a tsakiyar kansa yana cewa kaje kawai ka fara shiri and have it in ur mind dat ure getting weded, ka fahimta? Oya o kan lọ ki o mura ararẹ ni o ni ọkan ninu rẹ pe o ti fẹ, so i think we re done here,sai ka tashi ka bamu waje.


Dago kansa yyi da sauri ya kara marairaice murya yana kallon iyayen nasa yace mammy, dad,Dan Allah dan darajar Annabi muhammad S A W kuyi hakri, yabi baban shi da maraitaccen kallo dan yasan shine mai taurin kan,yau yare kawai yake son yin masa dan ma yanajin shi da kyau da kyau yace " _baba pls Mo bẹ ọ ni orukọ Allah ati ọlá ti woli muhammad S. A.W,_ don Allah kayi hkuri bba wllh ni duk ban shirya auranta ba,amma na maka alkawarin nn da sati biyun kacal xan gabato maku da matar da xan aura plss baba na consider me, nasan ina maku laifi" ya karashe mgnr kmr xai yi kuka.


a mugun tsawace baban nasa yace Damilare did u want me to slap u?.. ya yunkura cikin masifa da bori Damili ni o fẹ ki n lu ọ? Ahmed Ya girgixa kai, baban na masa mugun kallo yace "ka raina ma kan ka hankali ba mu ba. common get out my frnd.


Juyawa yyi da sauri yana kallon Mum dinsa da fuskar tausayi sosai, idonsa ya kada yyi jajur cikin rawan murya ya fara mata mgna mamy don Allah ki sa baki...." hararar dabai kai har ranta ba ta watsa masa tace "Da kenan amma ba ynxu ba,i have warned u several times Ahmed amma bakaji toh ni me xan maka ynxu? dafe kansa yyi xuciyarsa na tafarfasa,ya kasa cewa komi sai yy shiru, goge xufar Fuskarsa yyi da handky a nutse yana kallon babn nasa ya cigaba da magana  yanata neman a bashi sati biyun dai..karshe tsawa babn nasa ya daka masa yace "Enough Malam, tashi ka ban waje" daga nan Ahmed bai kuma cewa komai ba ya mike da kyar ya juya yanami cewa _ma binu sir_ i am really sorry sirr, daga nan ya fice daga falon yana tafiya kamr ruwa ya kwaso su dan duk duniya babu wanda yake iya ganin daman sa akansa kaman mahaifin sa..


Tun ficewarsa a falon Hjiya khadijatu cikin hikima da lallami ta rinƙa lallashin xuciyar mijinta akan maganan Ahmed dan sosai tasan yadda yake son yayan sa sosai, shikansa baida ra'ayin yin ma Ahmed auren da bai so amma ta fahimce kamar takurawar daga can family house dinsu dama su haka suke da son suga sune suke controlling rayuwar kowa. Sun dai tsayawa kowa a wuya sunce saidai a aurar da Ahmed kamar akwai wani abunda auren xai kara musu, itadai lallabar mijinta ta dingayi cikin nuna mishi ruwan madarar soyayya sai wani narke mata yake dan dama asalinshi dan son soyayya ne sosai, yanama daya daga cikin dalilin dayasaka ya aureto bayan mutuwar matarsa,Alhaj bello jimada yadan girma sosai dan akalla dai xai iya kaiwa 65yr ko abunda yafi haka,bayan mutuwar matarsa ta farko he felt he is timeless,sai ya farajin kamr yana bukatr a younger beautiful fulani woman wanda xata dai aure shi,wanda ta iya daukar wanka kuma kullum tana cikin qamshi mai dadi wanda xaina rage tsufarsa da ita.


After some hours


Karfe goma da rabi ya wuce hjya khadija ta shigo dakin Ahmed, lkcin yana kwance ya kafa ma bango ido da ganinsa kasan abun duniya ne ya ishesa, har ta karaso ta xauna gefensa tana kallonsa bai sani ba, sai can datay gyaran murya snn ya mike xaune fuskarsa a marairace sosai yace mamy na wai dan Allah Da ke ake shirin min auren dole ko? 


Ajiyr xcya tay snn tace "Toh ai kai ka ja ma kan ka Ahmed,tun yaushe nake binka ka kawo mata amma kana ta wasa kana kakkaucewa duk ka maida mu duka yan yara" 


komawa yyi ya kwanta baice mata komai ba


Sarai tasan halin dan nata da abun da ke iya faruwa in yafara yin shiru shiru musmmn in yana cikin tashin hankalin nan da yake ciki, hakn yasa tace "toh ai sai ka kwantar da hankalinka my son,na shawo mana kan Baban naka amma fa da kyar,  Nan da nan Ahmed ya miƙe xaune yana sauke ajiyar xucya xaiyi magana kenan ta tsare shi tanamai cewa

 Ka saurareni da kyau kaji yace min dai ya baka 2 weeks din da kace don haka kafin lkcn saikay kkri karkaban kunya ka gabato matar aure indai kana da niyya, kasan ni bana son abinda xai taba min kai ko? Pls Ahmed dont cause any trouble for me again..bana son na sake shiga damuwar dangin uban nan naka..

Kasani sarai baya tsallake maganan Elder sisternsa Anty mojushola she is very fragile in har xata girme baban ku ma baxai fi da shakaru uku xuwa hudu ba,amma kamar wata uwarsu data mutu haka dukansu suke daukarta kuma sukejin maganarta basa son bacin ranta sam.


mikewa Ahmed yyi ya rungume mahaifyr tasa cike da jin ddi ya shiga mata godiya sosai yana lallabata yanamai bata hkri akan fushin dayake sakata aciki,sosai zake son Ahmed dan shine mata danta kwalli daya a duniya tasan dai ba sake wani haihuwar xatayi da shekaruntan nan ba.


Ahankli sosai ta shiga shafa kansa tana dan masa murmushi har ta saka masa albarka snn ta mike yyi mata godiya ta fita xuwa falo wajen xainap da danta danta debe musu kewa wanda ajiya da darene sukaxo musu xiyara suka kwana tasan hala xuwa anjima xata wuce ta koma gidan mijinta.


 Kasa xama Ahmed yyi duk dama hankalinsa ya dan kwanta da aka bashi sati biyu sai dai yanxu damuwarsa dayace ta inda xai shiga ya fara nemo matar da xai gabato ma parent dinsa in 2 weeks witou a failure dan harga Allah aranshi baison ya kuma batawa mahaifyarsa ranta.


Xagaye yake ya kasa xama ya rasa ta ina xaifara wnn jan aikin wanda iya tunanin hkn na mugun tada masa hankali da kyar ya nitsu snn yay wanka ya shirya ya fito sanye casual wears wandonshi baki yasaka farar polo short akai da face cap ya wuce gidan banji domin ya samu cikakken nitsuwa.


Gudu sosai yake dan haka Tukin kamr minti 20 ne yakaisa har duplex flat din banji dake street din gwarimpa. Horn yy abakin gate mai gadi yaxo ya bude mai gate din ya shiga kai tsaye ya wuce cikin dan madaidaicin duplex flat din mai 3 bedroom dan dede haka dashi mai kyau sosai.


Sau biyu yy knck sai yaji alaman kofar kamar a bude da mamaki a fuskar sa ya tura kofar ya shigo ciki dan yasan mutumin nasa bai barin kofarsa a bude haka nan musammn ma idan budurwan sa tana tare da shi. Tun da ya shigo yy sallama ya tsaya shibai kara gaba ba baiyi baya ba, hadadden falo ne wanda yaji set of sleek sky blue sofas komina wajen dan dede a typical bachelors setting.


Banji yana kitchen yaji kamr motsin mutum saiya wanke hannun sa a sink ya goge da hand towl sann ya  fito Tun Daga can nesa wajen kofar kitchen ya hango sa a tsaye, Da murmushi akan fusknsa ya karaso sukayi musabaha..


Banji yahau tsokanarsa yana cewa Kaga Angon anytime...hmm ure actually looking like a groom..ko kulasa Ahmed baiyi ba yaja tsaki.."i quest ur girlfriend is not here right? Banji yace "yes, "sartuday is for wedings. Daxu ta shirya Taje bikin wata colleques dinta na office, tun ma bai karasa xancen ba Ahmed yy rau da ido yace "Ahh thank god dan bason shegen gulman ta nakeyi ba, finally der is space for some more fresh air abeg!..banji yy murmushi baice komi ba


Ahmed xai xauna kenan yace"guy muje kitchen mana Ina dan dafa abinci ne..i'am famished. Ko kai bakajin yunwa?


Ahmed ya kallesa sama da kasa cikin basarwa 

ni Nay maka kama Da wanda xai shiga kitchen ne?...


banji yace why not, ohh har wani kama muke dashi mudake muke shiga? 


Yace "Eh, man,nikam dai ina ɗa namiji lafiyayye kuma kyakkawa dani, nayi wanka na ina baxa  kamshin turare,Allah ya sawwake min in shiga cikin kitchen wann ai aikin mata ne..waima me kake kwabawa awajen ne?


Banji yana murmushi yace Toh ina ruwanka tunda kace aikin mata ne? See is not about a woman or man..learning how to enter kitchen to help clearly shows how responsble u can be to ur wife and future family.


Ahmed ya masa wani irin matsiyacin kallo yace toh naji..go and get someting for me to drink..amma nikam baxanci abincin namiji irinka ba.


Dariya sosai banji yayi yace makaryaci sau nawa kana ci? Sha u knw ur way, i am not going to serve u drinks..ka tashi kaje ka dauko drink din dakanka.


A kasale sosai ya mike yana mita..mutum ma yaxo gidanka baxai huta ba? sai shegen son saka mutum aiki..yana tafiya yana tsaki mtsss, ahaka dai yaje gaban fridge din ya bude yanata kalle kallen abubuwanda ke ciki yanadan kyabe baki gani yy kusan komi dake ciki ya kusa karewa can yasaka hannu ya dauki cold coffe drink, da har xai xauna a falon sai ya fasa yabi bayan abokin nasa kitchen din da drink dinsa a hannu.


Ahankli ya tura kofar ya shigo lokcin Banji yana kan gauraya wata arniyar greenish spagheti jollof dataji asalin manyan kifin sardines da vegies qamshin abinci ya game gauraye ko ina..


Kallonsa Ahmed yake yana ta shan mamakin yadda akayi banji ya mugun kwarewa a dafa abinci, bakaramin dadi qamshin abinci yy masa ba, take yaji cikinsa ta amsa, sai ynxu yake tuna cewa ashe shima baici komi agida ba. But he can neva cook like dat, dan Allah ma yasani wan aikin mata ne bana shi ba, Banji na famar gauraya abincin sa hadiyan yawun ahmed yasakashi ya juyo ta bakin kofa suna haɗe  ido waje guda Ahmed ya wani tsime kamr baisan me yakeyi ba, girgixa kai Banji yy yana murmushi.

"Mr Neat guy, How far? Meya kawoka kitchen kuma kohar ka dawo mace ne? Cikin shan qamshi mai ban dariya ya karaso da drink dinsa a hannu yace "nop..i need a fancy glass cup for my drink.."Banji ya fashe da dariya mai sanyi baice komi ba nan ya masa nuni da safe cupborad da hannu,a hakan ma saida yyita saibi kafin nan ya hkra ya saka hannu ya dauko wani glass cup mai shegen kyau wanda ko amfani dashi basu tabayi ba,yana cirowa kuwa karamin insect wanda ake cewa yan matan kaduna har guda biyu sukabiyo hannun sa a mugun firgice ya sake cup din akasa tay kara tassssss...Banji ya saka ihu "Ahhhhhhhhh Ahmed warris dis now? Kaxo ne dan ka fasa min komi da komi a gidana, dont u know dat this glass cup belong to my girlfriend hidaya..yanxu intaxo me xance mata. 


kirar sunan hidaya da banji yy sai ya mugun bawa Ahmed takaici a mugun masife yace "karka ce mata komi ka bata bayanka ta bugeka kawai, nonsense..toh saime dan ya fashe?arnt glasses meant to break?


Banji yace malam dakata

"Glasses can break mana amma ba ta hanyar ganganci ba, Ahmed da sannunka fa ka sake glass din nan a kasa...dats carelessness my friend


Yana rufe baki Ahmed Ya hararesa Yace "eh To na sake din..Next time bani xaka kira careless ba kafara ma budurwan ka lectures akan tsafta tukuna, toh in banda kaxanta kullum tana gidan nan amma sai insect suna yawo akan kofin shan ruwan mutane? No wonder ure alwys purging..kullum acikin toilet kana xuba kashi mai wari sabida virusses din dakake ci haaaaaaaaa what level of untidieness is dis 


Banji ya rasa me xaice masa ya tsaya yanata kallonsa. Sai can yace toh shikenan saika dauko tsintsiya da parker ka kwashe broken pieces din kakai dustbin tunda kai kana da tsafta..


Sadaf sadaf Ahmed ya tsallake kan glass din ya koma gefe snn yace no way. Ajirata dai ta dawo taxo ta kwashe takai bola..ni ban iya shara bama..wnn aikin mata ne nd since u have one agidanka ai sai ajira taxo tayi aikinta..nikam i cant.


Banji ya dafe kansa agajiye yace Ohhhh Allah na, Ahmed bello waime ka dauke mata ne?Marasa daraja, 'Bayi? 


Yace oh Ni bance maka haka ba.


Banji ya kashe gas snn ya juyo yanata kallonsa yace dami u really have to change ur mindset about women. yadda ka dauke mata ba haka suke ba, women are special human beings ka dai gyara tunaninka akansu.


Baikulashi ba ya bude drink dinsa yafara sha ahaka, saida yaji sanyi aransa snn yace Akan me? daga cewa budurwanka batada tsafta shikenan yadawo mindset issure.


Ahmed ba haka bane,

Ina magana ne akan aikin gida,dafa abinci, wanke wanke, gyaran gado, shirya yara ba aikin wani gender bane, is simply a shared responsibilty musammn ma awajen ma'aurata. Bana son kaje ka shiga hidiman aure kana cewa ehhh kayi wanka kay kyau baxaka shiga kitchen ba, or u cant sweep cos ure not a woman whats dat?


Ahmed yy rau rau da ido

Waidan naxo tayaka girkin shine xaka haumin wa'axi?  ..


Banji yace Amma ai cewa kayi kaxo daukar cup.. 


jokingly yace ohh did i said dat?


Dariya banji ya fashe dashi __ure egba asiewere ni ore_ mahaukaci kawai Allah dai ya shiryamin kai.


Ahmed yafara dariya yace ameen amma ba hakan ne yasaka ya share floor din ba, yana tsaye banji ya gama serving dinsu abincin,sai shi ya dauki plate din abincin da fork guda biyu yakai musu har falo Banji kuma ya share kitchen dinsa ya tattara ko ina yy tsaf snn ya fito ya same shi har ya dau fork yy bismillah yakai abincin bakinsa yana ci hankli kwance.



Murmushi kawai yy yaje ya dauko musu ruwan sanyi snn ya xauna shima suka cigaba da ci, can yaga Ahmed duk yafishi cin abincin.


Da kamar xai tsokane sa sai ya fasa yace guy ya ake cikine da maganan mu ka gama yin shawarar ne? Cos I have a girl on my mind wanda xata iya mana abunda muke so na contract marriage.


Fadan hakan da banji yy yasaka Ahmed aje fork  din nasa akan plate din ahankli sakamakon tunowa da yy da abunda ya faru da shi a gidansu daxu. Wani nannauyar ajiyar xuciya ya sauke ya dauke wipes ya goge gefen bakinsa snn ya sha ruwan sanyi ya dan samu nitsuwa kadan" ido kawai banji ya xuba masa ganin inda yanayinsa ya sauya gabaki daya atake..


Xai kara shan ruwan banji ya tsare sa da ido yace "Ahmed what is wrong?..wani abu ya faru dakaine?...


Ahnkli ya kurbi ruwa, snn ya lumshe idonsa ahanlki yace "baba yace in 2 weeks banji.


Baki bude Banji yace "2 weeks? Whats dat?


Lumshashun idanunsa ya buɗe yana kallon sa idanunsa sun sauya sunyi wani iri kalar tausaiy snn yace Dad yace na kawo mata in 2 weeks ko ya auramin kafayat.. im just sooo confused.


Kafadun sa banji ya dafa ahnkli snn yace cmon men, dont break down over dis small issure..toh meye ne abun damuwa aciki naga dai kafayat din nan tun muna kanana ake tare. And she loves u alot tun muna yara, kai kanka kasani..toh meyene matsalar Ahmed? Dama can ba itace matar naka ba? Kun dade fa kuna tare..


Agajiye ahmed Yace baxaka gane bane Banji, bawai bansan kafayat tana sona bane, and i liked her tooo, okay? A tunanin ka akwai wata ya mace dana sake mata fuska sosai kamar kafayar din ne?


Banji yace "Okay just say u love her, admit it...kafada mata mana Ahmed sai kowa ma ya huta.


Yace "In gaya mata me? Nine ma xance ina sonta ita meya hanata ta fito fili ta gayamin? Lallai kai mahaukaci ne..


Banji yace, Akan me?sau nawa kafayat tana fada maka? Wai shin mutuwa xakayi inka fada mata kaidin?..


Ahmed Yace baxan mutu ba, infact Ko ciwon kai baxanyi ba, I like her alot, she is fun, she is trustworthy, tana da dukan abunda mata ke tinkaho dashi amma gaskiya baxan iya ce mata i love her hakan nan kawai ba. I just like her, she is cool, and i think she knows dat.

 

Oh cmon Ahmed, haba!

Meyasa kake tsaurara wann lamarin? Kaine fa kasaka komi ya xamo a rikice..just u say u love her, u want to marry her, cos ders no perfect woman in this world 


Yace I know banji, nasani, but i hate alot of things about kafayat, xaman aure da ita inda ace xallan maganan in nuna mata kulawa itama ta nunamin ne baxai mana wahala ba,.amma ai xaman aure ya wuce haka banji, kafayat tana da baki sosai, gulma ajininta yake,and she sabi over do things yadda kasan mayya..

..wallh yadda take nunamin too much obsession shi yasaka na kasa iya jincewa ina sonta araina, haryau bana jin kmr ina sontan dagaske, cos she is stalking me..kullum acikin nuna kanta take a matsayin matata ta, and i haaaaattttte it..and not only dat kafayat tasan komi da komi akan rayuwa na dana iyaye na dana family na. Har can wajen su anty tems da anty moju take xuwa tana musu bauta..she is making her self too cheap for my liking...


 Wani ajiyar xucya ya sauke snn ya cigaba da cewa "Banji, bana son na xo na auri kafayat taxo gidana ta samu waje ta rinka kunna mana series of gulma da munafurci a gidan mu, wallh she knw all my weaknesses, she can easily blackmail me, kartaxo tana cutar dani, and mind u family na gabaki daya bayanta xasu bi sabida ta riga ta gama dasu tun ynxu.

Bansan ko kana fahintar mene ka fada ba, i dont knw but im so scared of maryying kafayat even thou i liked her..ynxu dan Allah mene laifi na aciki dan nayi wann tunanin banji? Banda ikon da xan protecting rayuwata na nan gaba ne?..i need a wife i can control and dat girl is not kafayat shiyasa bana son na aureta duk dama ita din daice nafi shakuwa da ita ..


Ahankli banji ya tayashi rike hannunsa suka sauke kasa atare Dan tunda ya soma wnn maganan hannunshi da jikin shi da muryanshi duk gabaki daya rawa sukeyi tsabar abun yana damunshi aranshi sosai .


sai yanxu banji yadan fara fahimtar nasa point of view din,even more than ever, Atleast yau Ahmed yy making small sense, all he said can be true duk dama babu wani dan adam wanda yasan gaibu sai Allah, Cikin muryan lallami yace "Damilare pls, calm down now Ahh ahhh. pls take a breath..aina fahimce ka ynxu..


Ahmed baice komi ba yadan jingina bayansa da kujera yay shiru sosai yanamai kame nunfashin sa...sai can cikin sanyin murya sosai yace "hmm nifa kowa laifi yaka kalla, and funy thing is dat no body want to understand me. Wallh aurena da kafayat din nan Da akwai matsala, gashi ko kunya bata da, badama taxo dakina tana son na taba mata nono, nifa baxan iya auren mace irin kafayat ba gani nake kamr ma tafi karfina.


Banji yace A'a kar kace haka mana. Lets just find a tangible solution bamu da lokci dan Sati biyu fa kamar yau da gobe ne kuma kasan halin baban ka sarai bayason rainin hankli.


Ahmed yace ni ai a shirye nake amma dai duk wani solution din da xamu nema kar asako kafayat cos she cannot be my option...


Banji yace "she have to be. Bari dai mu aje ta a last option din mu ynx muyi maganan contract marriage din, ina fatan ka kammala shawara akai.



Ahmed yace "nagama shawara na akai.. ina ga kawai abar maganan nan kawai. Kai tsaye yace "I am not intrested in it.


Ajyar xuciy banji ya sauke batare da wata jayayya ko musu ba yace its okay,dats fine nasan kana da dalilinka. So who do u have in mind now? 


Shiru Ahmed yy cikin naxari baice komi ba har na kusan na tsawon minti biyar daya sauke nannauyar ajiyar xuciya.


Banji ya kalle sa yace "ehen, ina jiranka, did u ave anyone in mind?


cikin Lumshe ido da budewa ahankli ahmed yace "Yes...


QUESTIONS

 OF THE DAY🔥 👉🏿 

*I WILL DEDICATE NEXT PAGE MA WANDA YA BADA AMSOSHI GAMSSASHU.08060712446 save my number and dm ur coments idan bana kusa dakai🔥* 


*Q1- SHIN KUNA GANIN DAIDAI NE IYAYE SU TAKURA WA YAYANSU SUYI AURE AT A CERTAIN AGE OR TIME KAMAR YADDA AKEYI WA AHMED?*


*SHIN RA'AYIN AHMED GAMEDA MATA DAYACE SHI YAFISON WANDA XATA SO SHI FIYEDA YADDA YAKE SON TA DAIDAI NE?*


*A MATSAYINKI NA ƳA MACE XAKI IYA AUREN NAMIJI MAI IRIN RA'AYIN AHMED?*


FOLLOW SURAYYAHMS ON WHATSAPP *08060712446* SAVE IT AND HI UR COMENTS, SHARE AND FOLLOW SURAYYAHMS ON WATTPAD.*KISHIYAR ƘABILAH..5*

By surayyahms.



*OYA SHOUT OUT TO THE  COMENTS/RESPONSE OF👇🏻 NAGODE🥰*

*Mrs beatrice, balkisu suleiman, zara gambo, Maryam umar matusgi, najiba ibrahim danjalele, mmn aysha,zahraAhmed, M2, Danzaki,oum noor, hadiza salmanu,nameske surayya,mum taheer,Dr halima maude,zahra, manyaro,mamn munirat, vivacious,khadijamalan,mamn arfat,aysha imran muhd,beenat,mom iyad, anty mimi, maymuna.*



murmushi mai sanyi Banji ya sakar masa snn yace wacece yarinyar?Ahmed ya dan bude lumsheshan idanunshi ahankli fuskarshi kamar na wanda yake cikin naxari da kokonto sai can kuma yace itace yarinyar Dana fada maka ranar..the girl i met in south east..


Baki bude Banji yace ohhhh ohhh so u mean yarinyar nan ce na can cross river i mean ur calabar tribe girl right? 


Yace eh ita.. 


Banji yace okay good, But are u sure about her? 


Babu tantama Ahmed Yace yeah am Sure. 100%.


"Kuma ka tabbata iyayenka da nata iyayen baxasu kawo muku wani matsala akan maganan auren naku ba, Kasan sometimes yoruba family basu fiye son hada xuria da tribes from igbo regions ba and like wise igbo.


Ahmed Yace Banji ka mance da duk wann shirmen tribalism din nifa nayi tunani sosai akai, and i know im soo desperate right now amma my decision about marrying her is not just out of a blue,nasan ita kadai ce dai xan iya aura naji kaina so safe and secured aynxu,besides the girl loves me more than anything, kuma nasan xata iyayin komi akai na,nide so kawai nake ka taimaka min, baxan iyayin abun nan nikadai ba, stay by my side har inje in sameta mudedeta,inyaso inta amince kawai itadin ce xan aura Ko da baxata canja addininta ba it wll be fine by me. And then na tabbata iyaye na xasu so ta even fiye da yadda suke son kafayat sabida sosai adiahar nan take da tarbiya da hankli, infact she is too sweet and good and she can cook very well too.


Banji yace hmmm u seems too sure akan babe din nan, to Allah sai yasa itace mafi alheri agare ka, is okay. i will alwys support u,yanxu menene plan dinka?


Gyara xama ahmed yy cikin nitsuwa yace ina tunanin na shirya naje garin sun ne in sameta  muyi magana mu fahimce juna shikenan..


cikin datsar numfashinsa Banji yace yanxu Xaka je kace mata kana sonta ke nan ko ya?...


A dakile Ahmed yace "what? So kuma? No pls cos Dats weird,ni baxan iya ce mata ina sonta ba dan bansan ko ina asalin son tan ba..kawai xanje ne in tambyeta ko xata aureni. U knw her consent is important for this union right?...


Banji yes, and love too, Aure fa xakuyi Ahmed, kai kanka baxaka so ace love and affection din ya tsaya ata bangare daya ba.


Ahmed yace karka damu dat wunt happen banji, i do care about her am sure shiyasa ma haryau kaga ban mance da ita ba. Nasan idan mukayi auren nan ma xata gode min,and she will be fine with me cos dats wat she alwys wanted. 


kallon sa banji yaketayi baice masa komi ba dan harga baisan mexai kara cewa ahmed akan yadda yake daukar mata aransa ba.


 Memeta maganan Ahmed din kawai yaketa yi a mind dinsa musammn ma inda yace wai "Inna aureta xata gode min cos dats what she alwys wanted? So Ahmed thinks he is doing her a favour by marrying her duk da shi din ma ya gudu ne wa trap din auren budurwansa kafayat dan sabida ya kare kanshi daga shiga taskon soyyarsu da yake tafiya a speed daban daban da kuma depressed marriage..


Yasan wann lamari dai nasa da akwai son kai da son xuciya aciki amma badai xai yanke hukunci ba tunda bai taɓa haduwa da adiaha din ba Karyaxo yay kkrin hana faruwar auren kuma ya cutar da ita batare da sanin sa ba,.


Tuna haka aransa yasa kawai ya share maganan suka cigaba da harhada plans din su na maganan tafiyar Ahmed cross river, calabar domin samu consent din Adiaha!.


Base on Poster din ogoja market festival dayagani ranan akan titi abakin shagon wani inyamuri suka shirya schedule na ranar tafiyar, sede Ahmed bai yarje ma Banji ya bishi har can ba, yace masa ya xauna kawai a Abuja sabida baison wani abu ya faru kuma iyayen sa suxo suyi suspecting na cewa tare suka hada plan din dan haka komin su a sirrance suke son suyi shi batare da sanin kowa ba. Yace In yaso in aka ci nasara akai toh shikenan sai a sako maganan auren nasu kowa yaji amma idan ba'aci nasara ba kuma shikenan bama sai kowa yasani ba.


Acikin kankanin lokaci suka hade good plan na yadda abun xai kasance.



Yau ranar sartuday snn kasuwar ogoja da ekpo festival xai fara ne on wednesday Dan haka xuwa monday wato jibi Ahmed xaibi jirgi yaje calabar yafara neman information akan Adiaha.


Bayan sun kallama tattaunawa akan hakan suka dan yi kallon ball kafin nan aka kira sallah xuhr sukayi alwala tare suka wuce masjid suka gabatar.


Dawowarsa keda wuya kowa ya nemi waje ya kwanta suka soma kwashar bacci, basuda farkawa ba sai wajajen 4 pm lokcin asr, atakaice dai yau gabaki daya agidan banji Ahmed ya wuni Sai can wajen after five snn yabar gidan lkcin daf lkcn budurwa banji xata dawo, tun da yabar gidan yake yawo acikin garin abuja shikadansa yanata tunani yanamai lissafin yadda komin shi xai kasance idan yaje calabar wajen Adiaha.



Washe gari da safe



Wata mata ce kalar fatar ta na wankan tarwada, gata nan a tsaye kuma doguwa, kibabbiya mai yelwataccen maxaunai ta sako babban leshi mai manyan holes dinkin riga da xani irin buban nan, matar tafi minti goma a bakin kofar yarta tana doka mata kira tana cewa "kafayat?,kafaya.. Kafayat..Kafayatiii,.tsabagen kiran datake yi sanda ta jawo hnkln duka masu aikin dake cikin babban gidan nasu. Haka Duk suka fito suna kallonta basu iyacewa komi saboda matar bata da dadi sam irin muguyen matan kabilan nan na gasken gaske.


Juyawa tayi tanamai binsu da wani irin tsinannen kallon kyamata dana ban haushi,A tsawace tace musu dont just stand der and be looking at me ,ina kafayat take wai bata farka bane? maganan take tana duban golden watch dinta lokacin ana neman wajen karfe sha daya da rabi saura daya daga cikin masu aikin namji yace "Tana ciki Ma daxu dai kwalliya takeyi.


Matar tana waigowa tace

"What? Kwalliya?



Nan Dukan su sukayi shiru suna ciccire idanu, kasa ce musu komai tayi takada kanta ta bar wajen within few minutes ta dawo da spare key ta bude kofar ta shigo ciki.


Wata hadaddiyar yarinyace full option ke xaune agaban mirror ta gama rabxa kwalliyarta tsaf tayi kyau ta xuba red wine a cup tana kan shan wine din abunta gabaki daya sai wani layi layi takeyi da alaman tasha giyar da yawa haryana dan bugar da ita sosai.


A mugun hargitse matar tayo kanta ta kwace kwalban nata da karfi cikin yanayin fada ta watsar akasa inda duk bacin ran yartan ya bayyana , she was wearing a green lace desire balconete fitted gown mai wani irin kyau saidai bakaramin matse surar jikinta yayi ba Inda kusan dukan kyaun surarta yake nunawa...


ACikin layi tamiƙa tsaye tasa hannu xata amshe giyar a hatsale matar tace Ke da Allah ya isa haka ode, olodo, You are too useless kafayat, sai akace miki in kika cigaba da lalata rayuwarki shixai saka Damilare yasan kinayi ne? Why wud u even tell evryone that shine xaki aura for god sake, ynxu Bagashi kowa sai ido yake xuba miki ba kinje kin baxa a gari wai shine mijinki and now u cant even move out peacefully sabida kowa sai ya tambayeki ranar aurenku,?uhmmmm  maganinki kenan ai tunda kece kika jawo mutane suke kan depressing dinki akan batun aurenki da damilare cos ure the one  acting desprate not him, ni dai baxan lamunci hauka ba _rara oti rara_ cmn get up and get back into ur senses we have some money making business to attend to.


Cikin wata malalacin qwuiya kafayat ta wulla kafarta kasa ta buga akan tiles dinsun tanata kukkuni, ohhhh mumy whats this now..shikenan 

Mutum bazai dan huta ba saidan akan maganan auren damilare? Yes he is the man of my dreams kuma inajin haushin shi saboda yaki ya kula da maganan auren mu amma badan shi nake shan giya yanxu ba,i jst want to forget about evrything..


A hatsale matar tace ohhhh now i seee, kina so ki mance komi da komi kamar irinsu yadda damilare yake kakkaucewa maganan aurenku ba? Lie on, cos u cant lie to me kafayat,u cant!!! Dat boy doesnt even see ur worth, dama ai wanda yake da jinin northener, jinin hausa ajikinshi kwata kwata baisan darajar mace ba, inba haka ba wani ɗa namiji ne xai dinga wasa da hanklin matar auren sa kamr shi? And dat his family members dat are the worst walking liers on earth,sukuma basuda wani aiki sai karya,kullum damwrsu su miki karyan cewa dansu xai aureki, xaki shiga famylinsu. Ke kuma yen yen yen har kinje musu aikin bauta, _oya were?_ .continue, nidai bana da lokcinki ynxu kawai ki tashi  ki wuce wajen business kiyi abunda ya kamata ki dubi agogo fa ynx is almost twelve noon wai dama yau bazakije shagonki bane? 



Kafayat ta mike da kyar tana mutsaka idanun ta tana turo baki "wai Yaushe aka fara gaya min abunda zanyi ne agidan nan?mumy dan Allah kibarni. 


Matar tayi shiru tana ta kallonta cikin rasa me zatace mata.


Sai Can ta tabe baki tace"hmm lallai kafayat ure so lost akan da namiji ahhhh Anyya kafayat, anya kuwa nice na haifeki?..nifa bansan ta ina kika dauko wann halin naki ba.



"Mummy im not lost,Im fine, just in an energy saving mood.



Daukar pillow tayi ta gwada mata akai,ni sa'arkice da zakice min haka,wani shegen enrgy saving mood ne wannan?rashin tunani da kasala dai dayayi miki yawa ajikinki, see making money shud come before any man, and not man before money, ke haryau bakiga abunda ya faru dani da ubanki ya rasu yabarni banda wani madogara ba? kullum senayi tunani ta yaya ne zaki iya rike kanki a gidan mijinki namijin ma wai Ahmed bello jimada, please tell me how..


Kafayat ta takune fuskar ta tana dada gyara tsayuwarta Haba mumy Ahmed din shi meye ne?maza fa in xaka basu good sex, kana da kyau ilmi, kuma ka iya kwaliya dan kisisinan sace xcyr familynsu ai shikenan ka gama dasu. My only issure now shine in samu hanklin damilare, and i am sure daga xarar ya yadda ya aureni randa muka hada gado shikann baxai iya cigaba da mun wann halayyar san ba,infact mumy xaki sha mamakin yadda ahmd xai dawo kamr kare awajena, sai abunda naga dama nayi dashi agidansu just wait and watch, As of now im calm cos i know i have his full family support



Matar tace hmmmmmm

Haka ne ko?oshey mrs family suport i greet u oloshi mumu girl, Wani irin banxan family support ne har ynxu sun kasa tsaida magana akanki bare akawo mana kayan aure? to tsaya kiji abunda xan yaga miki Nan ta same waje ta zauna turus tana kallon yartan data gama dora fuskar damuwa ayaynin ta,tsaki taja snn tace Kafayat, maganan gaskiya daci gareta amma dolene  a fada miki, nifa tuntuni araina bana jin mutanen da akwai damshin wani gaskiya alamarin su cos something is really fishy abot them, ni ban yarda da wann game din da suke playing akanki bafa.


Kafayat tace like how mummy wani irin game kuma kike nufi xaki fara irin abunkin nan ko?why are u negative mumy Wani irin game kuma 


Da harara mai xafi tabita tace the game ure too blind to see so just shut up,gyaran muryanta tay snn tace "so as i was saying, kinga wancan uwarsa bahaushiyar din can..? To bari na gaya maki walai Soyayyar munafurci take nuna miki tuntuni amma ke kinki fahimtarta she doesnt wnt u to marry her son att alll, kafayat cmon think about it,ke kin fini saninta da yadda take son danta,snn kinsan  waye Ahmed da yadda yakema uwarsa biyayya, he is a mama boy  evryone knws dat,duk abinda tace mishi yyi ko bayaso shiyake aikatawa, haka ma babansa itace take juyashi, duk tabi ta mallake su da sihirin su na hausawa da kayan mata,So now tell me, inhar dagske tana son aurenki da danta Ahmed meyasa haryau ba'ayi auren ba?both of them shida babansa acikin tafin hannun ta suke  wallai, Inda har tana sonkii da danta degeske da baxamu kai wann stage din ba...


wani irin bugawar xucyane ya xiyarce kafayat dan ko itama ta dade tana xantar da ire iren wann tunanin aranta, saidai bata taba daukar hakan aranta ba sabida yanayin yadda ta rike hajiya khadijatu da amana dan itace ta raineta tamkar yarta a lkcn da mamanta take gwargwarmayan kkrin daga business din nan nasu da tabi ta watsar da dukkan lamarinta taje kasar waje ta barta anan hnnun masu aiki ayyin datake karama,.


Shkarar kafayat biyar mahaifinta ya rasu,ita da mamanta sun sha baqar wahala da family crisis akan maganan raba gado awajen yan uwan mahaifin nata sabida kafayat itace kadai yarsa ta mace sauran yaran kishiyoyin mahaifiyarta sune masu yaya maxa dayawa snn kusan rabin arxikin mahaifin nasu duk wasu aka bayar saidai dake mahaifiyrtan tana bautawa spirit of fire and revenge goddess yasaka tayi tsayuwar daka harta samu musu babban mansion din mijinta a matsayin gadon yarta kafayat. Banda babban mansion din babu abunda aka basu na gado,Bakin cikin rabata da dumbin dukiyar mijinta yasaka ta  fanjama uwa duniya domin neman masu kudi. Saidai revenge, hatred da greed sune suka rufe mata ido sai bata damu da rayuwar yarta kafayat datake karama ba alkcin neman kudin kawai tasaka agaba.


Haka kafayat ta girma a hannun masu aiki da nannys dinta, when she was 7 she became so loney wanda shi yasaka ta xamo soo obsessed da abokinta Ahmed bello jimada,sun taso ne as grp of yoruba freinds.


omotola Kafayat buraimo,Ahmed damilare bello jimada,oyebanji Abdlsalami bakre sai na hudunsu shine ibrahim bankole Abdul fatahi, kafayar itakadai ce mace acikin abokan nata maxa su uku, saidai acikin sun nan duk tafi shakuwa da Ahmed damilare sabida jinin fulani ajikinshi dayasa yy dan fari da kyaun fuska saiya kasance he is very very intelligent and attractive to oda girls.


Kamr yadda kowa ke son rabarsa Hakanan kafayat itama ta taso da wann obsession din akansa har suka girma suka saba sosai tana binshi kullum har gidansu ko wani rana in suka tashi a makaranta.


Duba da yadda iyayensa suka fahimce halin da kafayat take ciki na kadaici da rashin kulawar mahaifyrta yasaka suka amshe ragamar kulawa da rayuwar kafayat hannu bibbiyu, musmmn ma mahaifyrsa hajya khadja,dan tamkar  yar cikinta haka ta dauki kafayat ta bata kulawa, komi na nuna gata da soyayya tana nuna mata daidai gwargwado har yakaiga kafayat ta fara samun daman cike gurbin rashin uwarta dake damunta a ranta ta itama sai fara rayuwarta kamr kowa acikin jin dadi. She loves Ahmed alot, sabida aganinta shine saviour dinta daga mental depression dashi da familynsa.


Tsawon Shekaru goman nan cass daga primary 3 xuwa sss3 kafayat tayi shine a karkashin kulawar hajiy khadijatu snn dukkan wani abu da ya mace take bukata na rayuwa itace ta koya mata ixuwa wnn lokci.


mahaifiyar kafayat mai suna hajiya Fatihat Adetunji balogun da farko dai dataxo taga kafayat na xama a hannu mai kyau ta nuna godiyarta amma daga baya ganin yadda kafayat din take mutuwar son hajya kahdija da danta ahmed yasaka tafara jin tsananin kishin matar aranta, tun alokcin kammala schl dinsu na scndry tafara jan yarta ajiki sosai tanamai kkrin cusa mata wasu ra'ayina cewa babu amana tsakanin kabila da bahaushiya, sai tana nuna mata cewa ai hjya kadijatu muguwa ce, burin ta shine kawai ta rabasu shiyasa taje wajen malamansu na hausawa suka bata asirin manta uwa.


Kafayat wll alwys rebuke her mother intana furta mata hakan dan tasan dik karyane, wanda ake ganin kamar dan sabida son datake ma Ahmed ne yasa bata son taji ana furta laifin mahaifyrsa agabanta. bayan sun kammala scndry schl din ne mahaifyrtan ta karbe ta mai gabaki daya suka koma yin xamansu tare a mansion dinsu cikin daula sabida wani irin bunkasa da businesss inta yy, kafayat tace ta karanta law university of nigeria nsukka, dake result dinta baiyi wani kyau ba yasa maman taki nema mata aiki sai kawai ta bude mata business din salon da boutique tukuna, daga nan kuma kowa ya shiga tsabgar rayuwansa har suka girma sosai. ko aynxu ma kafayat xata iya cewa mahaifiyar Ahmed din itace take kan rainonta, da can ma itace ta bata ci sha sutura da emotional support of a mother kai hatta yadda ake wanka,wanki, saka pant,saka brexiya, tsafta, wankan tsarki,da komi na rayuwar ya mace matar nan ce ta koya mata yadda akeyinsu. 


Idan tana da wani personal problem haryau bata iya kaiwa wajen mahaifyarta direct saidai taxo ta gayawa hajiya khadija dan itace kawai mai iya kwantar mata da hankli


Tun da take Bata taɓa samun shakku ko wani kokonto akan maganan matar nan ba har sai  akan batun xancen auren ta da Ahmed which is now getting out of control a xucryta dan kuwa babu wani abu da batayi na nuna biyayya da bautawa Ahmed da familynsa waidan yace yana sonta a fili ba.


Kai Hatta jikinta saida tayi masa tallarsa a free amma duk da haka yaki yabata hadinkai.


Babu kalar shirya masa da batayi ba amma a kowani rana dabiar Ahmed baya nuna mata komi face cewa da akwai wani boyayye kuma babban lamari da xai iya bullowa a tsakanin su wanda take ganin kamar shine xai rabasu na har Abada.


A kullum yaumin idan mahaifiyarta na mata tambaya akan rashin yuwar aurenta da ahmed bayan tasan baya tsallake maganan mahaifyrsa abun yakan dameta aranta bana wasa ba.


Ganin jikin kafayat yy sanyi nan Hajiya fatihat ta cigaba da xugata tana cewa "that woman is busy planning sumting againts u. Hala ma bata son ki aure mata danta ne sabida dantaga ke ba haushiya bace irinta


Magangunu kala kala babu wanda bata mata akan lamarin ba


Wani Tunani kafayat tayi aranta sai taji kmr tafara amincewa sa xancen mahaifyrta, karde maganan mahaiyrtan gaskiyane,karde hajiya khadijatu kabilanci xata nuna mata, ta hada Ahmed aure da wata bahaushiya ba ita ba?


Lumshe idonta tayi sosai tanajin fargaba mai karfi dan da alama Da damshi damshin gaskiya acikin wnn xancen dan tasan kowacce uwa burinta kenan rayuwar danta ya xamo yana under control dinta..


Ta bude baki xatayi magana kenan wayarta yafara ringing nan take sabuwar wakar davido na timeless album dinsa wato "unavailable" ya karade ilahirin cikin dakin.


Kusan atare suka dubi kan screen din suka kalli lambar mai kirar atare.


 Agaban screen an rubuta "Anty tems" yana yawo akai.  Adan mamakance Kafayat tace why is Anty ramouto calling me kode har Ahmed yace musu xai aure ni ne?


Wani Doguwar tsakin takaicin mahaifyrtan taja muryanta kasa kasa tanamai cewa oya keep dreaming .


Ko kulata batay ba da rawar jiki ta dau wayar tabi ta rusuna kasa cikin girmamawa kamr wanda ake kallonta.


Acikin harshen yarensu ta fara gaishe da Anty ramatou. Wadda take ce mata Anty tems sabida bakaramin sabawa da su tayi sosai ba. Ita kanta Bata san Suna janta ajikin su ne bane sabida suna son Ahmed lallai yay aure daga kabilar su na yoruba dan sam basa son uwarsa tace xata hadashi da wata yar bahaushiya.


Har kasa kafayat ta tsuguna da wayar a kunne tanamai cewa


"o dara irọlẹ

Gud evening ma

Anty tems whatsup kiloshele? Any latest


Daga ta dayan bangaren Anty temi tace "Der is alot oo, but first thing first,i wll like to see u today.. we have a big meeting with u _iyawo wa_ 


Tsaye kafayat ta mike kalman _iyawo wa_ yana ringing acikin brain dinta cos its means "our future bride" jikinta harna rawa kmr wacce xata tashi sama tace really?


Hararar da uwarta take binta dashi yasa ta dan nitsu Ahankli tace Ahhhh but i hope dai Akan batun aure na da Ahmed ne anty tems.


Daga ta dayan bangaren anty tems din tadan gutsira mata labari sama sama na abunda ake ciki na batun cewa sun saka ma baban Ahmed daci sun takura mashi har yaje ya bawa Ahmed sati biyu akan daya kawo musu dalili ko su Aura mata shi. Kafayat taji kamr xata fashe dan murna dan tasan Ahmed will neva escape marying her in two weeks time din nan dan tasan dai baida wata budurwan daya shaku da ita sosai sai ita, 


nan anty tems tace mata Kedai kawai kiyi kiyi marmaxa kixo family house kisamemu musan abinda muke ciki


Godiya ta mata snn ta katse wayar jikinta harna bari babu wani jira tafara shiri ta kwaso nan ta kamo nan kamar wata mahaukaciya, nan ta dauki karamin jaka tasaka hadaddun kaya guda biyar aciki da kayan kwalliyarta da su turare kala kala da jaka mai kyau da damin kudi dubu dari biyar  kusan rabin dan ribar kasuwancin ta na satin da sauran tarkacen jewrlies dinta


Mamaki da takaici yabi ya ishe mahaifiyarta amma bata ce mata uffan ba harsaida ta kammala shiryawan snn tace mata wai ina xakije  ne kafayat? Ke Daga kawai sun kiraki sun gaya miki magana saiki dibi jiki yuuuu xakije gidansu aikin shashanci da bauta.


Kafayat Tace Ahhh mumy nifa ba gidan su Ahmed xanje ba, Anty temi ne tace naje suna nema acan family house dinsu gidan Anty mojushola. Mum Wai bakiji me take cewa bane? She said in two weeks time xasu aura min Ahmed yeeeyyyy.. omo mi iyawo 


Tsawa matar ta dakata mata tace "Shut up jare

Ure a disgrace to woman race  _itiju lori rẹ_  awon desperate gang,omo busy body.. kafayat wai yaushe ne xaki san darajar kanki ne? Innice namiji yake having scnd tot akaina baxan jirashi ba, kafin ma yagama min yanga saidai yaga har na nemi wani wanda yake sona nayi aure na nabarshi. In Ahmed yana sonki why wud he take two weeks to decide. Ur just a desperate bitch girl.


A mugun masife kafayar ta kalleta tana huci da alaman maganan ya ci mata rai,a cikin yanayin tsawagoron rashin kunya tace mumy pleassse Abegggiiii. What is dis now, why are u alwys negative?


Mamar tata xatay magana tabi ta tsareta da tsefaffen ido tanamai cewa "i ave heard enough of u mum, me kika taɓamin arayuwata? U left me here to die  wadann mutanen ne suka rikeni yanxu kuma a memakon Kiyi supporting dina akan abunda nake so sai dai kokarin juyamin mind dina kikeyi akansa  ur evil plan againts me will not work witch.


Ta juya a xafafe xata tafi uwartata ta fixgota tare da daura mata mari akan fuskarta.


Kafayat is me ure calling a witch akan namiji? After all the insult i went trou in oda to secure ur future dan ubanki olodo shegiya,saketa tay tana mai cewa "Okay fine.. ga hanya nan jeki. Amma kisani, Idan har aurenki da damilare baiyu wann karon ba.


Cikin katseta kafayat tace are u going to trow me out of this house bcos this is my father house not urs...



A mamakance Fuska a matukar daure matar tace ohhh really? Ni ai baxan taba korarki nan gidan ba, akan me xan koreki acikin gidan danine na sha wahala wajen kwato miki shi?

Kafayat da kinki da kinso nine na tsuguna na haifeki snn nice agaba da kowa wajen son naga rayuwarki tayi dede.


Xatayi maganan ta tsareta da hannu tanamai cewa:


"listen and listen carefully kafayat, inhar maganan aurenki da Damilare baiyu ba wann karon kisaka aranki cewa nice xan xaba miki miji dakaina nan gaba.


Rai abace kafayat tace okay fine mum..nikuma nayi mikii alkwari baxan dawo gidan nan ba face saina auri Ahmed .


Tun bata karasa furta hakan ba mahaifyar taja doguwar tsaki ta fita tabarta awajen a tsaye.


Abun na mugun damun kafayat aranta amma hakanan ta basar da komi taja akwatinta ta wuce babban mansion din late Alhaji jimada dake anguwan gwarimpa inda family house dinsu Ahmed yake....

SURAYYAHMS. 08060712446 chat only..

" What did u guys think about this chapter? ....*KISHIYAR ƘABILAH 6..*



BY SURAYYAHMS.



Tunda kafayat ta dau motarta tahau kan titi tana tuki babu abunda yake dawo mata akanta sai maganan da sukayi da mahaifiyarta, tafiya take amma bakaramin bugawa kirjinta yakeyi ba, ta rasa da wanne xataji tasan dai inhar bata samu Ahmed ba babu Abunda xai hana mamanta yi mata auren dole, atake taji kasala na dirar mata akowani sassa na jikinta,da kyar da wuya ta kaucar da wnn fargaban tafara tunanin yadda xata yi tasamu cikar burinta akn Ahmed, musmmn aynxu data san da cewa xancen ya kwabe mata yaxamo mata tamkar kashin kifi a wuya, tasan dolene komin rintsi komin wuya tasan yadda xatayi su tsaida maganan auren nan nasu da Ahmed damilare kafinan tace xata shiryawa komawa gidansu taje ta gamu da bala'i da masifa irinna mamanta dayake jiranta.


wajajen karfe 1 dai dai na rana kafayat ta iso gaban babban gate na Jimada's family house dake cikin wani hadadden estate dake anguwar gwarimpa.



Duplex ne babban gaske sai parking space gari guda mai dauke da motoci kala kala da basufi guda takwas aciki ba. Kana ganin gidan xa kasan gidane daya kafa dumbin tarihi. 


Mai gadinsu bahaushe dan garin yobe yana bude mata gate kai tsaye ta shiga bata tsaya kulawa da gaisuwarsa ba. Tana fita ta wuce babban sashin su anty mojushola, Kayanta ma anan ta bar ma masu aiki su suka ciro a booth suka kai mata cikingidan.


Dan babban falone dake shimfide da turkish carpet brown mai gida gida, ga saitin kujeru manya na daidai rufin asiri masha Allah palon sai kamshin turare yake ko ina tsaf tsaf babu ko digon datti, Anty moju ne a tsakar falo tanakan dadduma tana sallan axhr, kana ganinta kasan tadan kwana biyu a duniya tanada jiki sosai da manyan maxaunai.


After some mints ta sallame sallan cikeda natsuwa sann ta daga kai ta kalli kafayat data kusan kwantawa kasa  agabanta sabida tsabar nuna girmamawa. 


A mugun ladabce ta shiga Gaishe ta  _o dara irọlẹ_ ma..


Anty mojushola dake murmushi sosai tace _irọlẹ mi darling, iyawo wa iwaju_ (Evening my darling our future bride) tana murmushi sosai tace "kafayat hows ur mother? Fatan tana lpya ?..


Wani irin murmushi kafayat tayi kanta na can kasa tace  Alhamdulillahi she is fine maaa _o ṣeun_ 


Anty moju tace its okay.

 _ọlọrun bukun fun ọmọ mi_ (God bless u my child) ure welconme


Tace Ameen oo _o ṣeun_

A dede nan Anty temi ta tarar dasu, nan kafayat ta miƙe tana murmushi sosai ta koma gefenta itama ta rusuna har kasa suka gaisa suka danyi hira awajen lunch kadan  kafin nan kafayat tayi xcusing dinsu taje quest room in da kayanta yake tayi sallahn axhr tayi wanka ta sake cancanda kwalliya snn ta sauya wani kayan mai kyau ta dawo kasa.


As usual bata xauna acikinsu ba direct kawai ta wuce kitchen ta shiga kkrin shirya musu wani irin hadadden dinner, she planned to cook igbin chops with yam wanda kafin ma ta fara hada girkin saida ta tsaya ta hada musu wani irin tasty mushy butter crumbs na taɓawa snn ta hado musu da cold and refreshing smoothie takawo musu har cikin falo inda suke xaune suna kallo, anan ma babu wanda bai saka mata Albarka ba, hirar lamarinta da Ahmed suketayi suna tabawa ita kuma tanacan kitchen tana shirya musu abincin dare. anty mojushola tayi tayi akan Ahmed yaxo gidan da daddare ayi dinnern tare dashi amma sunkira wayarsa sau babu adadi basu same sa ba,duka line dinsa a kashe suke tun da rana, kai Har gidansu sun kira amma duk ba a sameshi ba.


Kafayat kuwa tana kitchen tanakan aikinta happly da Farko ta tafasa doyarta ta xuba a wamer, sauran kuma tayi tuwon sakwara da shi shima tasaka shi a wamer na daban,for igbin dinta bata wani bata lokaci ba ta nemo shelled jumbo snails (dodon ƙodi) da scotch bonnet pper, tattasai da albasa da lemon tsami, bay leaf, manja, shrimp powder da seafood bouillon powder 

Nan danan Ta hada igbin chops into 2 difrent ways, daya tayi sauce daya tayi stew. Wanda xa'a iya serving dinsu duka da tuwon sakwarn da tafasashen doya.


Bayan ta kammala hada abincin ta hado musu da drinks masu dadi kala kala ta jera komi akan dinning table snn tahaura sama domin yin wanka.


Kafin kace wani abu gida ya cika da yan uwa da jikoki cos Anty ramatou bata tsaya nan ma saida ta gayyaci surkunayen su wanda suke nan a nigeria suka xo da yayansu yin dinner. Anty Nurat itace matar babban yayansu Ahmed, wato brother kaziim AREMU yana da yaransa uku duk maxa, "shehu", "sulu"da "femi". Saidai shi mijin nata yana kasar waje bai dawo ba tukuna.


Sai Anty Adizatu itace matar Brother Hamzat dimeji, yaranta biyu duka mata, medina bolanle da karimat omolara. Brother hamzat Shine mafi kusanci da Ahmed dan haka komi na shirin da akeyi na bikin Ahmed shine yake saka bakinsa aciki kai tsaye.


Sai sistersu xainab moturayo wanda daga ita sai Ahmed din, itama bata nan taje oshogbo inda gidan mijinta yake ita kuma danta dayane dan karami shine shafi'u dake tadan samu matsalar rashin haihuwa.


Anty nurat taxo da Autarta femi, sai Anty Adizat kuma taxo da duka yan matan nata wato Medina da karimat 10 and 13yrs old.


Around 7:30pm lokcin kowa yaci kwaras an hallaro kan dinning table


Kafayat was really feeling like a bride musammn ma dataga matan yayun Ahmed sunxo da yayansu anacin abincinta anata xuba santi already su medina da su femi da karimat sunata kiranta da sunan iyawon Uncle Dami.



Duk dama rashin halattar Ahmed ixuwa wajen dinnern yaso yadan dameta aranta amma soyayyar da familynsa sukata nuna mata awajen ne yyita sassaita mata xuciya.


Itakanta ta nemei shi awaya sau babu adadi amma duka layukansa a kashe. Around 10pm aka kammala hira kowa ya watse.


Nan Kafayat ta koma makwancinta da tunanin hirar tsokananta da sukayi a tsakanin Anty temi da su anty nurat na cewa yakamata su hada ma kafayat da Ahmed grand surprise engagemnt party a gidan. Acikin wasa da dariya sukayi hirar amma da mamakinta sai taji washe gari da safe Anty temi tana sake dago mata da maganan.


A bangaren Ahmed kuwa aikinsa kawai yake kkrin kammalawa da wuri domin ya samu isasshen daman yin tafiyarsa cikin kwnciyar hankli batare da tashin hankli ba. Jiya  monday din da sukata kiran layinsa akashe bai dawo gida ba ne, a office dinsa ya kwana yana aiki shiyasa bai kunna wayarsa ba.


Yau Tuesday morning da Asubah ya dawo gidan batare da sanin kowa ba yy wanka ya shirya kansa ya kara ficewa asibitin Dr hassan don ya kammala da can shima...


Gobe Wednesday by 9.am jirginsa xai tashi ixuwa calabar, and he want to beat it on time ixuwa lokacin daxa aci taron ogoja market festival dan anan ne kawai yasan xai iyacin karo da Adiaha.


Jimada family house

Tuesday morning 


wajajen karfe tara saura na safiya kafayat ta fito ta kammala musu komi tana kan Goge goge a kitchen sai ga Anty tem ta shigo,hira suka kamayi suna dan raha a tsakanin su, Anty ramatou tafara gaya mata Yadda suke son komi yayu sabida dama sunkirata ne dan su shirya tarban Ahmed a matsayin angonta na next week.


Anty ramotou ta bata 100% tabbaci na cewa komi xai tafi musu daidai sabida aganinsu sati biyun nan kamar gobe ne so babu amfanin jira shiyasa suka kirata kawai domin taxo afara dan shirye shirye...


Idan ana maganan auren nasu Kafayat will be blushing all the way like jinjirin biri. Sai kaga har tana kasa iya haɗe ido da su anty temi a tunaninta sun riga sun dawo surukunai.


Sukuwa abunda suke so kenan suga sun same total submission and biyayya daga wajenta, ta inda koda anyi Auren sune xasuyi controlling Rayuwar Ahmed tunda Hajy khadijatu uwarsa itace take juya musu kan dan uwansu Bello, But with kafayat by their side sunsan xasu same nasu daman suma ata wajen Ahmed.


Haka suka nitsar da kafayat suka nuna mata cewa babu wani abun kunya wajen ya mace idan tayi proposing ma namijin datake so dan ba haramun bane.


Tunda Ahmed yaki ya furta mata yana son ta kuma yana son suyi aure sukace toh ita saita shirya furta masa dakanta inhar Ahmed ya amsata toh basai ma anjira 2 weeeks din nn ba xa'a fara shirin aure .


Hakanan su anty nurat da anty najat suka taru suka cikama kafayat kasa aciki, aka fara shirya grand suprise proposal party wa Ahmed. Kasuwa suka baxama na musammn aka sissiyo kayan ado wanda xai saka Ahmed ya kasa iya rufe bakinsa inyagani. Wani hadadden backless red flowing gown kafayat ta siya mai tsada na dubu arba'in da biyar da takalmi mai tsini da head crown da flowers da rings dinta masu kyau.


Har dare sunakan yawon siyayya agari suna shiri ma suprise engagement party kafayat kuwa tasha hadadden gyaran gashi da attachement cos batada dogon suma sai tayi manicure da pedicure tasaka nails dinta masu shegen kyau da tsada she is ready shining like a bride kowa sai yabonta yakeyi ranar


Shiyana can yanata aiki baima san me sukeyi anan ba, Tun safiyan ranan tuesday din anty ramatou taxo gidansu ta same hajy khadijatu ta gaya mata abunda suke shiryawa, itama batayi kasa agwiwa ba tasaka albarka akan lamarin dan aganinta kafayat will make a good wife to her son ahmed inhar yana son auren ita bata da matsala sam.


Sunyita nemansa awaya still yauma tuesday din amma basu same shi ba,sai can da yamma lis kafin nan yabaro asibiti ya taho gidan agajiye da niyyar shiryawa tafiyarsa na gobe da sassafe.


Samu yy hanklin maman sa duk ya tashi dan ta nemesa awaya har ta gaji,tun bai Xauna ba tafara bashi labarin tafyar, haka tayi tayi dashi akan cewa ya shirya kawai gobe da safe karfe takwas suje gidan su anty mojushola tare amma haka nan yaki mata sam yace baxaije ba dan yasan baida wann lokcin domin kuwa karfe tara jirginsa xai tashi ixuwa garin calabar, toh gashi abun nasu suprise ne ba ason agaya masa harse yaje ya gani hjya khadija ta rasa ta yadda xata soma shawo kansa.


8:30 am na safiyar wednesday aka shirya masa suprise party din.


Kafayat is already feeling sooo excited dan gani take ko ba dan Allah ba idan Ahmed yaxo yaga idanun manya awajen kamar irinsu anty moju da mahaifyarsa da su Anty temi hala xai hkra ya amsa batun aurensun kawai even if its out of compulsion. Sosai ta saka ranta akan wann lamari shiyasa ko wani baccin arxiki bata samu tayi ba.



Batasan da cewa  shawo kansa dan yace xaixo wajen ma saida akata drama da shi agidansu sosai ba...


Karshenta ma Anty mojushola ne ta kirashi dakanta awaya ta dinga kuka tana kora masa ashariya ahakan ma saida ta hadashi da babansa kafin nan yace musu xaixo tare da mum dinsa Cos he is already very annoyed da yadda suka matsa masa akan saiyaje wajen musammn ma da basu gaya masa dalilin xuwan ba.


Cikin dare adakinsa yau ko runtsawa baiyi ba yahau kimtsa trolley na kayansa na yin tafiyarsa ixuwa calabar,sassafe karfe shida ya farka a bacci bayan yy sallah yy wanka yaxauna yana shiri at same time suna waya da abokinsa banji.


Bayan sun kammala maganan Adiaha Ahmed yafara bashi labarin irin matsa masa da akayi jiya akan wai yaje family house dinsu yau da safe, lokci guda banji ya soma dago kan xancen a mind dinsa. Ahmed yana kan mita banji ya datsi numfashinsa da cewa

Guy wait..amma kayi magana da kafayat awaya jiya kuwa?


Ahmed yace no, akan me ita uwata ce daxan mata magana..naga dai tulin miscalls dinta jiya ban bita kanta ba..


Banji yace hmm to mesa baka kirata ba.


Tsaki Ahmed yaja yanakan daura igiyan booth dinsa yana cewa 

"I cant oo,ina maka maganan family na meya kawo maganan kafayat anan kuma, dat one na normal thing now..ai dama ta saba min irin waynn miscalls din sabida bata da aikin yi a rayuwanta sai bina.


Banji yace hmm ba haka nake nufi ba,i just smell sumting fishy abt her cos she called me yestade tana tambaya na wasu abubuwa game dakai dana tambayeta tacemin wai gift take son siya maka, kuma naji surutun su Anty adizat anan gefenta sai nayi tunanin me sukeyi atare ahaka?


Da mamaki Ahmed yace  kafayat din ne take tare da sun anty adixat?? 


Banji yace yea i am sure naji muryansu sosai lkcin she was shouting at her doter medina, surutu awajen dai kmr suna kasuwa nace kodai wani abu suke shiryawa ne baka sani ba.


Ahmed ya kyabe bakinsa a yanayin ko inkula snn yace "Oho nide sunki sufada min komi kawai cemin akayi wai muje family house before 8 amma karka damu koma miyene ni nasan mexanyi dasu.


Banji yace toh shikenan dai inka sauka lpya dai ka kira take care bro.


Ahaka suka kammala wayar kowa ya cigaba da abunda ke gabansa.


After some few minutes saida ya lura kamr babu motsin kowa snn ya fito acikin sanda ya yaje ya bude bayan booth dinsa ya aje trolley dinsa aciki ya kulle snn ya dawo ciki


tsaye agaban mirror yy lkcin harya kammala shiri yana fetsa turare yanata tunanin abunda xai gayawa mum dinsa idan yaje mata sallama qamshin jikinshi gabaki daya ya gama cika dakin yanamai dada gyara gashin kansa da brush. 8 o clck na bugawa aka fara buga masa kofa akan ya fito, Baiyi wata wata ba ya sauko kasa dan ya nufi dakin mum dinsa dan shikansa yana son ya isa airpot by 8.30 kuma baifi saura 30 min ne 8:30 din yy ba.


Qamshin turaren jikinshi dayasaba sakawa ne ya dinga baxa ilahirin gidan ayayin daya sauko yana doka sallama a dakin mum dinsan ta juya tanamai tsaresa da idanuwanta da sukayi luhu luhu sabida kukan dataci. tun dagacan mahaifiyrsan ta xuba mai ido tana sauke sanyayyar murmushi datake fiddawa da kyar ganin irin mugun kyaun da yyi yau yasaka All black casuals ne na marks and spencer mai 3 qtr jacket, yasha booth dinsa ubansu da agogonsa na new police irin matte black din nan snn ya shafa mayukan gyaran gashi sai kyalli kansa yakeyi..


Yanayinta dayagani ne na ragwabewr jiki da jimami yaso yadan dagamai hankli nan take ya taho wajenta a gaggauce cikin tashin hankli, tambyarta yake amma bata amsashi ba har saida ya karaso ta wajenta tukuna ya lura da cewa video call takeyi da babban dadarta wato Anty hajiya maimunatu mohd gidado.


Su biyunsu mahaifinsu ya haifa amma suna da wata kanwarsu yar kanwar mahaifinsu da aka rainesu tare.


hjya maimunatu din itace Babbar yayansu, sai mahaifyrsa Hajiya Khadijatu,snn hajiya Aminatu wanda itace yar kawunsun snn itace karamarsu wanda bata wani jima da yin aure sosai ba ta rasu awajen haihuwa.


Yau shekara 18 kenan da rasuwarta amma haryau sunajin mutuwartan kamr sabuwa domin kuwa wann mutuwarta yar uwartasu aminatu ya musu ciwo musammn ma da hjya maimunatu take da tabbacin cewa *Kishiyar kabila* ce ta kashe musu yar uwansu aminatu akan batun haihuwa.


Mijin yar uwansu Aminatu Alhaj Amadu hussaini yy aure yakai sau goma amma bai taba samun haihuwa ba sai akan yar uwarsu aminatu wanda shiya jawo kishiyarta datake *kabila* ta hade baki da likitoci aka kasheta awajen haihuwa. 


Anyi case sosai bayan mutuwar aminatu saidai Kafin lkcin basu da wani kudi snn iyayensu kaf sun rigamu gidan gaskiya dan haka basu samu mai tsaya musu akan gaskiyarsu ba,snn alkcin shikansa mijin yar uwartasu yay gamone da wani irin kaddara na shanyewar rabin jiki sanadiyar hawan jinin daya turnukesa ayayin dayaji cewa matarsa Aminatou ta rasu awajen haihuwa dan bakaramin sonta yakeyi ba.


hjy maimunatu itace tamkr uwa kuma uba agare su dukansu dan haka lamarin sosai yay mata ciwo fiye da kowa wanda shine sanadiyar dayasata shiga harkan siyasa da neman kudi har Allah ya daukakata. Sosai take son taga ta raya xuriarta da kuma jininta, Shiyasa haryau take kaffa kaffa da rayuwar yar uwarta hajya Khadijatu agidan yarbawan nan dan yanxu ita kadaice ta rage mata a duniya bayan mutuwar aminatu, Basu da kowa a duniya sai yayansu, wato yarta nafisa da kaninta sadik,da shi Ahmed din da kuma yarinyar da aminatun ta haifa kafin rasu ta bar musu mai suna YASRAH AHMED HUSSAINI wanda a hannun hjya maimunatun ta girma.


Yau yasra take cika shekara 18 takwas a duniya wanda yy dede da ranar mutuwar mahaifyarta aminatu shiyasa duk suka taru sunata kuka suna masu tunawa da ita atare.


Ahmed yana isowa wajen ya fahimce abinda suke ciki, jikinshi a mugun sanyaye ya xauna akasa yanajin conversation dinsu mai saka tausayi da jimami dan mahaifyr sa tasha bashi labarin rayuwar hajy aminatu da yadda kishiyarta ta bala'in axabtr da ita dan ance har hauka saida tayi da ciki ajikinta. 


Shidai yasan shi bamai son xumunta bane dan haka baxai iya kirga sau nawa ma yajeshi katsina wajen hajy maimunatun ba dayake karami, xai dai iya tuna lkcin da akayi sharia a kotu aka kwato custodyn yasra daga hannun dangin ubanta da suke son riketa na dole dan sabida sunacin arzikin mahaifinta tunda shi baida lpya,da asirin su ya tonu kotu sai tabawa hjy maimunatu amananta na har izuwa lkcin da mahaifin nata zai samo sauki, amma bayan nan bai san komi ba saidai duk da haka yasan dacewa antynsan tana son famlynta sosai.


Xamansu A turkey na tsawon lkci a matsayin ambassada na kasa shiya dada sakawa xumuncinsu yyi nisa sosai wanda shiyasa ma kwata kwata bai taba sanin kamannin yan uwansa nacan turkey ba.


 yasan dai da akwai adda nafisa wanda take babban ƴa ga hajya maimunatu, dake ta girmeshi a shekaru ita a U.K ma take da aure, sai sadik wanda kusan ya girmesa da shekara guda ne,amma yasran kam baida tabbacin xai iya ganeta ynxu dan rabuwarsa da ganinta ido da ido tun tana yar shekara bakwai lokcin ma tana fama da ciwo sosai.


Saida suka dan samu nitsuwa snn ya rusuna kai ya gaishe da anty maimunatu wanda ganinsan ne yadada sanyaya mata xucyrta taji dama dama, albarka ta rika saka masa tanamai masa adduar samun lpya da kuma tsari tanamai nuna alfaharinta dashi dan tana son jininta sosai. 


Lokacin kan yasra na kallon kasa sama sama takejin su suna gaisawa saidai sam bata iya dagowa sama ta kalleshi ba duk dama tasha jin labarinshi awajen hjya maimunatu itama tana son taga kamannin dan uwantan amma sabida kukan tuna mahaifyrta dataci sai bata iyayin hakan ba.


Ahmed Yanata satar kallonta ashe itama satar kallonsan takeyi  da shanyayyun idanunta da suka gama canxa kala bai sani ba,a cikin wani irin bakon yanayi ya tsinci kanshi mai tafe da rashin samun nitsuwa, sai can data tamaida idonta ta rufe ruf snn ta dago akayi akayi ta gaishe sa amma sam taki cemai komi, shima sharr yy da ido yanabin ta da kallo kamar bai taba ganin kyakwar mace irinta ba musmmn ma dan karamin bakinta mai kyau irin wanda bai taba ganin irinsa ba .


Saida iyayen sukadan lallabeta snn Ahankli ta budi baki muryanta can kasa kasa kamr xatay magana, suka hade ido yarasa me xaiyi sai ya hade rai ya watsa mata harara, ta sake budan bakin ahankli suna kara hada ido taji wani irin kasala na dirar mata da yanayin irin kallon da yake jefo mata nan da nan ta girgixa kai yanayin ta cike da shan qamshi da shagwaba tayi masa shiru batace mai uffan ba sai shima ya basar. Cikinsu babu wanda yacema wani uffan.


Anty maimunatu tana Dan murmushi tace Ahmed pls understand her kaji?, duk ranar birthdaynta haka take rigima sam bata son yin magana bare murmushi.


Ta sake kallonta cikin lallami tace yasra, Ahmed fa babban yayanki ne kisaki jikin ki dashi kinji? Dan yauko da bana duniya sune jagora agareki da shi da sadeek, shine yau kuma baxaki iya cemai koda sannu ba?


Batace komi ba ta dada sauke kanta kasa alaman dai baxata cemai komi ba


Babu yabo ba fallasa Ahmed ya kyabe bakinsa snn yace its okay bakomi momy, ahnkli yana satar kallonta yace atleast muma ai baxamu ce mata happy birthday ba. 


Tashi tayi tabar gaban screen din tana tura baki ko irin murmushin nan batayi ba, atake sai yaji attitude dinta ya kuma shakesa a wuyarsa amma saiya ya basar cikin murmushi suka dan gaggaisa yanaji suna maganan shirye shiryen graduation party da xasuyi na gama scndry school din yasra idan suka dawo nigeria in few months time.


Bayan sun kammala wayar hjya khadijatu ta sauke nannauyar ajiyar xuciya tana cewa Oh Allah ka nunamin ranan dawowarsun nan lpya,sounding sooo happy tace i just cant wait..dan kuwa katsina xan koma wajen adda maimu nayi hutuna ko kunaso ko bakwaso.


Murmushi ahmed yy sigar tsokana yace Wann ai ma dad knan kike tura wnn sakon, nidai saidai na xama muku dan aika dan nasan shine baxai iya jure xama babu ke agidan nan ba..


Kunnensa taja tana dariya tace marar kunya kawai kaci kaniyarka kenan wato kai lkcin har kayi aurenka ko?


Kansa ya girgiya yace no binki can xanyi ai dama rabona daganinsu na dade kafarki kafata,..


Dariya kawai tayi yace

a babban gidanta na katsina xata xauna ko?


Tace eh,  kasan tunda tenure dinta ya kare acan turkey, already har president yay signing mata wani new political appointment anan senate house of assembly Abuja. Kaga ko da ban tare a katsina ba still xatana xuwa abuja akai akai sabida aikinta Yanxu haka ma maganan karatun yasra ne yake damunta tanata tunanin a nema mata university anan ne ko acan turkey ne xaifi, but i dont think  xata iya kyaleta a wani kasa da karancin shkaruntan nan u knw sumtimes she can be soo protective. Inde anan din yasra xatayi karatu i think nice xan dauki ragamarta kawai sai anemo mata spot a nile ko base university tafara karatun anan Abuja kusa dani tunda kaikam ma aurenka xakayi. 


Baice komi ba yay murmushi sai can snn yace toh Allah dai ya dawo da su din lpya.


 Tace Ameen


Agogonsa ya kalla ganin 8.15, yace mamy lets go mana akwai inda nake son xuwa and Its very important daman tun jiya naso na fada maki sai bansamu dama ba.


Tace 'a a ,abar wann maganan kawai tashi muje dan tun asubahi anty temi take min waya akan na make sure naxo tare dakai. Inyaso idan munje saika fadamin inda xakaje din


Yace mammy what is it dat ure not telling me?

Wai meyasa akace dolene sai munje family house by this time


Sharesa tayi ta dauki hadadden golden veil dinta ta yafa snn tace meet me outside my friend da  already ma munyi latti..


Baice komi ba ya miƙe yabita abaya suka fita kusan atare, tunda suka dau hanya yake takurata yyi yyi ta gaya masa menene amma sam haka taki har suka isa kofar mansion din jimada.


Ana bude musu gate yy ma mai gadi ido akan karya kulle kofa alaman yanxu xai juyo..


Lpya lpya ya sauke mamansa har kusan bakin main door,snn yace mata ta shiga daga ciki shi xai gyara parking din motarsa acan parking lot xai biyota abaya .


Batasaka komi aranta ba ta shige cikin gidan kai tsaye, ko minti biyu batayi da rufe kofar gidan ba yay kwana snn yaja motarsa cikin gaggawa ya bar gidan aguje ya wuce hanyar airpot abunsa....


COMENT AND SHARE FISABILLAH.


SURAYYAHMS WHATSAP ONLY 08060712446.

SAVE AND CHAT❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥*KISHIYAR ƘABILAH 7...*



BY SURAYYAHMS.



Tunda Ahmed ya kama hanya zuwa Airpot bai sake ya bar wayarsa a kunne ba acikin gaggawa kawai yake tuki dan already lokacin tafyr tasa baifi saura minti goma ba.


Daga ta cikin gidan kuwa Ko ina yy fess fess kowa yaji kyau andau qamshi kowa ya saka hadadden kayansa mai tsari duk anyi kyau musamn ma kafayat buraimo data sako backless red flowing gown dinta mai tsada.


Kowani lungu na cikin gidan anyi decorating dinsa ne da heart shape ballons da katoton red flyr an rubuta will u marry me ajiki mai ja da fari ana jiran shigowarsu Ahmad da mamansa ayi suprising dinsu.


8.40 am dot hajya khadijatu ta doka sassanyar sallama acikin gidan snn ta shigo ciki fuskarta dauke da fara'a tanamai furta wow wow masha Allahu ganin inda waje yy mugum kyau dn anka kashe kudine akayi romantic decorations da abubuwa masu ban sha'awa da burgewa sosai.


Dukan tara tara sau goma kirjin kafayat yy dataji sallaman hajya khadijatu,rashin jin muryan Ahmed bai dameta ba ,dan a tunaninta lokacin cikar babban burin xuciyarta ne yaxo.


She was soo nervous and excited to the wings tana jin kanta acan sama kamar wacce zata tashi sama dan murna.


Nan Kowa yaja ya tsaya in position aka rage hasken wajen ya dawo dim ana jiran Ahmed ya shigo sai ayi suprising dinsa. After some min saiga haj khadijatu ta bullo ita kadai ,tun kafin su fara gaisawa anty ramotou tajata gefe murya kasa kasa, tace iya dami shushhh, pls dont talk loudly u will ruin the suprise for the kids.


Tooh ina shi damilare din yake,ya baki shigo ciki tare da shi ba kuma? 


tun kafin hjy khadijatu ta amsata caraf kafayat ta juyo ta tsareta da ido da alaman tanajiran jin amsar itama


Hajiya khadijatu tay murmushi snn tace ku kwantar da hanklinku Ahmed yana waje dan tare dashi mukaxo shiya jawoni ni ma a motarsa.


Anty ramotou tay yake tana duban kafayat data sunkuyar dakanta kasa tana dan murmushi tace Alahamdulillahi rabboul Alameenà


"Why is he not here yet."

Anty moju ta katsesu


Acikin girmamawa hjy khadijatu tace "ohhh He said he wll be parking his car outside, Nasan ma hala harya kammala parking din. Wani irin sihirtacyar ajiyar zcya kafayat ta sauƙe snn ta dauke idanunta akansu jin ta samu wani nitsuwa ta cikin ranta.


Anty ramouto tace its okay, kowa yy shiru..any moment Ahmed will be in  and in sha ALLAH he wll love this .


Nan kowa yay shiru sunata murmushin jin dadi,after some few mins wajen kimanin 25mins ya tafi abanza anata jiran ganin Bullowar Ahmed sai shiru abun nashi har ya soma sakasu cikin suspense duk wani motsi ata bakin kofar sai sun leka amma sai shiru..


after like 20 more min Anty moju tafara mita kadan kadan da yaren su tana cewa wnn wani irin parking mota ne aiko kera sabuwar mota yakeyi albarka..anty ramatou ne ta dan fara calming dinta dan karta fara daga musu hnkli.


Sosai kirjin kafayat yake bugawa taciki sai tafara jin tsananin bugun zuciya da fargaba mai karfi na neman hadiyeta amma bata san na menene ba.


Da shirun yafarayin yawa Haka nan kawai sai ta soma tunanin ko Ahmed ya fasa zuwa ne dan tasan zai iya aikatawa, thinking of that make her soo weak tafarajin kmr ana suyar masa ne akan kaskon kirjinta. 


Gashi ta gama cika baki wa kawayenta na business cewarta ayau duk wani gulma da akeyi akan maganan jinkirin aurenta da Ahmed zai zamo tarihi, and she wll update them live dan suga engagement dinta da Ahmed. 


So One of her close business partners mrs Zikirat fasihu da gulma ya mata yawa, ta kasa hakuri tanajin labarin partyn already harta kira mahaifyar kafayat din awaya ta watsa mata labarin dan tasan me ake ciki,babu abunda zikirat bata sani akan rayuwar kafayat ba sabida yawanci idan kafayat tasha giya hakanan take zama ta juye mata dukkan wasu sirrinkan dake cikin cikinta.


Hajiya fatihat najin wann batu batay wata wata ba ta dau jakarta ta kamo hanya izuwa jimada family house dan goddess dinta riga ta gaya mata cewa akwai abunda zai faru da yarta ayau marar dadi.


9.30 oclock dede aka kunna wuta acikin falon, a cikin gajiya da rudani da tashin hankli hjya khadija da su anty tems suka fito har waje tsakar gida domin duba Ahmed dan shirun nasa yay yawa..



Sosai jikin Kafayat ya fara ragwabewa zucyarta yasoma bata wani abu marar kyau dan haka atake tafara hauhawan numfashi..


Anty nurat da anty moju sune suka rirriketa suna kwantar mata da hankli duk yanayinta saida ya canja a lokaci guda tafara hawaye mai sanyi


Sauran matan duk suna waje babu abunda sukeyi sai kwalawa Ahmad kira aduba nan aduba can 


Rashin ganin motarsa awajen parking yasaka anty temi ta tumu tafara mita tanamai kokarin lakawa mahaifyarsa sharri na cewa karya takeyi dama tuntuni bataxo da shi gidan ba.


Kusan cece kuce suka farayi awajen hjy khadijatu ta rantse musu da Allah cewa tare dashi suka shigo gidan amma anty ramouto sam taki  amincewa har saida mai gadi ya tabbatar masu cewa ficewa agidan Ahmed yay kamin nan hjy khadijatu ta samu sa'ida.


 anty adizat dake ita surkuwace acikinsu bata iyacewa komi sai binsu kawai takeyi tana kallon family dramarsu.


Jeka ka dawo anty ramotou take a tsakar gidan tsakanin parkimg space da bakin gate cikin yanayin masifa da tada gurmi tana bambami tanamai cewa _nibo ni ọmọkunrin yii le wa? kini o ro_ ( Ina yaron nan ya fita yaje?..tunanin meyakeyi)..why wud he even go out..kini rizin?Iya Dami Can u pls explain urself, tana maganan ne tana huci tana wani irin hararar hajya khadija kmr wanda zata hadiyeta dan takaici.



Sosai kan hjya khadija yay zafi ta rasa meke mata dadi Sai kirar layinsa takeyi babu kakkautawa amma abu daya ake cemusu switchd off.


Sai can bayan kamn minti 30 da fitowarsu waje da basuji shi ba anty ramoutou tasaka ihu ta dora hannu akai cikin yanayin masifa sosai tace "what sort of disgrace is dis..Damilare is soo fond of disgracing the whole family. Ahhh, Ahhhhhh,Ahhhhhhhhhh Dami..Dami..Damilare

 _iga ti embrassement_ Tafada tana huci kamar kanta zai tsage dan takaici, Toh Yanzu me zamuje mu fada aciki kenan, shud we tell dem he ran away? Cos im sure he ran away, ohhh ohh poor kafayat, Kafayat, i really pity dat girl,such an irresponsible shild.. Ahhh Damilare is really a disgrace..hmm..


Hjya khadijatu ta haɗa rai tace pls anty ramotou kidena cewa haka akan  Ahmed tunda dai bamusan abunda yasaka shi ya juya ya tafi ba, besides it might be an emergency..


Kamar jira anty ramouto take nan danan tayo kanta a masife tanamai cewa "wani shegen emergncy ne wnn? Hehehe awon emergency ehen...wato yanzu da aka sako maganan laifin danki kinyi caraf kin amsani zaki nema masa uzuri ko? Nasha fadawa anty mojushola cewa kece kike koyamasa wann halin na rashin respect, Ur son is a disgrace, just accept it iya Dami..


Tsaki hjy khadijatu taja ta dauke kanta batako amsata ba tahau neman layukan abokansa banji da bankole saidai a cikin su babu wanda yace mata yasan inda Ahmed yake ayanzu.



Anty adizat ta naɗe hannunta ta koma gefe ganin kowa ya birkice da wayarsa ahannu yana mai neman layin Ahmed.



Dagata bangaren Ahmed din kuwa 9:am sharp yayi hoarding kansa cikin flight din air peace dan shine mai zuwa straight to calabar in 1hr 3 mins time,earpice ya saka a kunnensa yanajin kida hnkli kwance batare da ya kawo tunanin kowa aransa ba.. 


Aransa yasan a yanayin yadda ya barsu stranded sunajiransa a gida hala inhar ya dawo abuja baizo musu da matar aurensa ba ya gama yawo awajen familynsa kenan, fargaba yakeji acan cikin ransa duk dama baisan laifin daya aikata musun ya wuce tunaninsa ba.


Dan Ko kodan acikiin ransa bai kawo cewa suprise engagment suka hadamai shida kafayat ba,shidai ya bari ne akan shirmene kawai na maganan memeta masa kirgen kwanakin daya rage masa na batun kawo musu matar auren sa da suka sabayi yasa suka kirasa family house.


Tun ahanya Ya tura ma babban yayansa hamzat sako akan cewa yana da wata maganan sirri dazaiyi dashi dan duk acikin familynsu jininsa yafi haduwa da brothersa na biyun, wato brother hamzat dimeji, cos he is a very calm and understanding person sabida yadanyi cudanya da garuruwan hausawa sosai..


Yanata son ya tura ma mahaifiyarsa tex ya fada mata cewa shi yy tafiya ne amma baisan ta ina zai soma fada mata ba dan ya tsani jin bacin ranta.



Kafayat kuwa tunda taga su hajya khadija sun dade awaje basu shigo ciki ba tasan sa cewa akwai matsala,nan da nan zube kasa tafara musu kuka sosai tana yarfa hannu gwanin ban tausayi.


kirjinta dake mata zafi ta dafe tana cewa noo noo noo this cannot happen to me, yau fa rana ne, im suppose to be engaged, tanata kuka Kowa nata jin tausayinta..


Daga waje kuwa dukansu sun kasa yanke hukuncin shigowa ciki sai musu akeyi akan Ahmed tsakanin anty ramotu da hajya khadija,ita dai tasan danta baijin magana amma aynzu so take tasan ko yana lpya dan hanklinta bai kwanta da fitar da yay acikin gaggawa kamar yadda mai gadi ya fada ba.


Kafayat na ciki tana mai tsananta kukan datakeyi duk ta birkito kasa ana rirriketa, jin karar horn din mota a bakin gate tin daga waje yasaka ta birkita ta miƙe tsaye tanamai cewa "is that Ahmed?..dat must be Ahmed..bari naje na duba shi..tin kafin su anty nurat su rikota a guje tayo wufff tayo waje da tunanin Ahmed zata gani nn su anty moju duk suka biyota abaya.


Tana isowa farfajiyan gida ta samu kowa hanklinsa ya koma ga bakin gate dan kaf tunani dayane ke yawo a mind dinsu kowa na fama da fargaba da bugun zuciya.


Mai gadi yaja gate tun bai gama budewa ba hajya fatihat adetunji ta waina babban jeep dinta na prado tayo cikin gidan a mugun zafafe kafin kace kobo harta kashe motar agabansu.


Evrything happen so sudenly dan A karkace ma tay parking motar tata tsabar dirin masifa ta sauko daga cikin jeep din babu ko talkami a kafarta a mugun masife ta taho tanamai cewa "kiloshele gon gon? Kini? What is happening here kafayat...?


Wani Turus kafayat din ta tsaya cak batako motsi a tsakiyar su hajiya khadija dan tun dataga motar mahaiyarta ne ya shigo gidan bana Ahmed ba sai tafarajin kanta na juyawa sosai tafarajin jiri jiri..


 "Are u ppl daft? Nace menene ya faru? Why is my doter in tears..


Anty ramotou da su anty mojushola sukai shiru kowa ya tsime yana kyabe bakinsa cikin rashin sanin abun cewa


Babu zato Ta wani finciko kafayat din tajawo ta tsakiyarsu snn ta matse mata hannunta sosai tanamai dubanta da fuskan rashin imani da tausayi,girarta na sama a dage tace" meye faru? Why are u in tears, _kini aṣiṣe? Kafayat kilode ti o fi wa ni omije?._ .answer me. What is it...


Kuka mai tsuma ne ya kufcewa kafayat din tausayi yasaka hajya khadija  karasowa wajenta tana isowa ta kwaco hannun kafayat din ana mahaifyarta tadan jawota jikinta sigar lallami snn ta rungumeta akafadunta ayayinda take kukan sosai.


Wani irin shewar baqar kishi dana kashe aure hjya fatihat tayi snn tace " i dont understand oo..inata magana anmin shiru.. Ahmed ya mutu ne? Is damilare dead..dat boy shud better be dead so that my doter will not be crying like this ....


A mugun tsawace Anty ramoutou tace  Ah, ah, how dare u fatihat... _oya werey?back to sender u evil woman.._ 


Hjya fatihat tabita da muguwar harara


Rai abace Anty moju tace..thunder fire dat your evil maught...idiot woman, shegiyar mata marar respect.


Ido bushe hjy fatihat ta hararesu snn tace And  who shud i respect here?ehhhh..kufadamin? Meya same yata take kuka shine kawai damuwa na ko acikinku babu isashen da zai iya min bayani ne.


Anty adizat ta harzuka harzata cakka mata baqar magana Cikin katseta Hajya khadija tace pls relax, ayi abu cikin hankli, hjy fatihat Duk da kika ganmu anan hanklimmu atashe yake cikin sanyin murya sosai tace "My son is missing" muma nemansa mukeyi bamu gansa ba, munxo tare dashi har nan amma kuma har yanzu bamu san inda yake ba.


Hjya fatihat taja tsaki adan kunyace alaman bataso jin haka ba dan a tunaninta Ahmed din ya walakanta mata yarta ne ko har ya furta cewa bazai aureta agaban familynsa ba..


Ta tura bakinta gaba tana kikkifta ido ahankli snn tace ohhhh,mtsss, ashe ma bacewa yay?arggh, Toh Shikenan kuma dan Dami ya bata sai akace ataru ayita kuka akansa kamar ana gidan mutuwa

..in mutuwan yay kuma yaya kenan..


Sosai ransu anty ramoutou yake harzuka da maganganun matar amma basuce mata komi ba sabida basa son su tada wani magana since hajy khadija tay kkrin sassaita maganan cikin hikima ta hanyar cewa bata Ahmed yay..


atleast sunsan ko itama kafayat din zataji dama dama aranta akan da ace guduwa yay.


A zafafe kafayat din ta dago kai tana kuka sosai ranta abace tace mum why now? Wai Meyasa kike kiran kalman mutuwa ne wa damilare and in front of his family too pls how is dis fair.


A masife cikin katseta tace "nothing is fair here musamn ma dakika maida kanki jaka marar kwakwala agaban wayn mutanen, Ni banma yadda dacewa bacewa dansu yay ba, arent u planning a suprise engagemnt for him? Toh Wayasan ma guduwa yay yabarki munafukan dake zagaye dake kuma sukace miki batawa yayi.


Cike da dakatarwa kafayat tace Mum pls, karki sake cewa familyna munafukai saidan kece babban munafuka if not a ina kikaji zancen engagemnt dina da damilare? 


Furucin sosai yaci ma hjy fatihat rai amma ta tsime tace "oh mamaki ma kike sha ? Toh Ai maganan duniya bata boyuwa..

hmmm okay ohhh, to barikiji The same way i heard it kidauka aranka cewa haka nan ma Damilare zaiji zancen cewa zakimasa surprise engagement and dats why he will run away and leave u..


Cikin karayar zuciya da kufcewar kuka kafayat tace mum ya isa haka

Ance miki bata yayi..we wll find him am sure 


Hajy khadija ta katse su da sauri tanamai cewa yes. Zamu nemoshi and Pls hajya fatihat leave evrything to us..zamu nemosa snn za'ayi engagement din nan ayau..in ma bamu same shi yau ba duk inda yaje ya dawo nayi alkwari he wll engage kafayat agabana.



Hjiya fatihata ta bushe da dariya snn tace "Iya dami? Ki tabbata geskiya kike fada min ooo cos if not..,if not...wallh, tallahi, kinji na rantse miki da Allah kece zaki fi kowa shiga uku awajena.. i wll make ur life soo terible and miserable the same way ur son is taking advantage of my doter.


Hajiya khadija batace mata komi ba tajanye hannun kafayat suka koma cikin gidan aka barta da su anty ramoutou suna cecekuce kamar zasu tada gidan haka suka kaure da masifa..


Da sauran dirin masifan suka dawo cikin gidan dukansu bayan tafiyar hajya fatihat, nan suka samu lokacin har hjya khadijat tay nasara wajen rarrashin xcyar kafayat da kalamai masu dadi da kwantar da hankali akan da cewa zasu hadakai ne sunemo Ahmed duk inda yake a afadin garin Abuja.


Anty mojushola da tsananin fushi ya rufe mata ido tana shigowa tahau dakawa hjya khdijatu tsawa tanamai dora mata laifin komi .


Kowa cewa yake laifinta ne da Ahmed ya zamo marar tarbiya wanda baijin maganan manya


Anty moju Sai diri take tana kumfar baki anty ramoutou na rirrikota at same time tana mai tayata. Surutu suke ma hjy khadijatu a masife suna hargagi tamkar zasu bugeta ..


Sai cewa suke ajininta na hausawa Ahmed ya debo rashin sanin darajar mace shiyasa ya iya walakanta matar da zai aura tun yanzu..


Sosai Kafayat ta rude a tsakaninsu duk sai tarasa maganan waye zata ji guda daya.


Su anty temi sunce da gangan Ahmed ya gudu bayan hjya khadija tace mata bacewa Ahmed yay


Anty ramoutu Tace iya dami kece xaki biya yarinyar nan kudinta data kashe, dan kece kika lalata yaronki ya zama wawa, Uve encourage your son to be soo irresponsible duk da kokrin da mukeyi akansa.


Anty moju ta dafe kirjinta tana sumbatu cikin jin takaici da yarensu tana cewa _gbogbo rẹ ni nitori ọmọ rẹ pe obinrin yii ṣe ẹlẹya idile mi?_(duk akan danki ne akazo har gidana aka cimin mutunci?) _Ọlọrun mi yoo ṣe idajọ rẹ_ (Allah ya isa..Allah zaimin sakayya *anyone)


Tun Bata kammala rufe bakinta sai wayar hjya khadijatun yay kara da alaman shigowar wata sako..


Anty moju ta dube hjya khadija snn tace mata" _tani iyẹn? Ṣe o jẹ ọmọ aṣiwere rẹ?_ kallonta kawai hjy khadija tayi, Sai can da ta tuna cewa bata jin yaren su snn tace "i said, Who is that? Is it your foolish son..)


Hajy khadijatu bata kulasu ba tsabar ranta ya baci sosai, tana dubawa kuwa taga sunan Ahmd saidai sakon nasa ta voicemail ne ya aiko, hamdala tay cikin ranta snn tace musu Its my son Ahmed, tana fadin hakan kowa ya miƙe tsaye, sauri take tana kkrin ta bude sakon taji meyene aciki nan taji an fauce wayar a hannunta tana daga ido taga wayar a hannun anty ramoutou tana mai kkrin budewa cikin sauri, galala da baki tay tana kallonsu.


Hannun Anty ramoutun har rawa yakeyi tanamai cewa "Bazamu yarda ki cigaba da yaudarar yar mutane ba, in ma hada baki kukayi da danki ai zan playing sakon kowa yajishi a fili..


Lokaci guda falon ya dau shiru kowa ya kasa kunne can saiga muryan Ahmed ya soma fitowa cikin nitsuwa.


Yace mammy Dan Allah kiyi hakuri kiyafeni, i wanted to tell u dat im out of town, zan danyi kwana biu awani waje. im really sory maaa, i just cant wait, sabida inda zanjen ne yanada mtkr muhimmanci agareni, And pls tell the rest of the family that im sorry, idan na dawo zanzo in kawo musu wanda zan aura din..am really sorry for dissapoiting evryone.


Anty moju ta saka ihu tanamai cewa Haaaaaaa so Damilare has dis bold guts? har nine zan kirashi gidana snn ya shareni yay tafyarsa wani waje? 

I swear to oludumare am going to deal with dami, ahhhhh..zan nuna masa cewa na riga ubansa bello zuwa duniyan nan.. how useless can he be, imagine the audacity!!!!! Da karfin huci ta furta maganan Out of strong frustration and anger dan ta tsani raini sosai anty ramoutu ne agabanta tanakan bata hakuri



Hajy khadija batace musu uffan ba ta amshe wayarta a hannun anty ramotun ta kara sauraran sakon ,jiki a ragwabe kafayat ta koma kasa a sulale tay zaman turus hawaye na sauka zurrrrr daga cikin idanunta.


Magangnun mahaifyarta sune suka shiga mata yawo a kwakwalarta musammn ma datake ce mata itace kadai ce take acting desperate akan batun auren ta da ahmd, itace kadai take son shi dayawa, itace kadai take wahalar, snn shi baisan darajarta ba.


Masifar da su anty sukeyi yasaka kafayat ta kara shigewa cikin rudani musmmn ganin yadda suka taru sukama Hjy khadijatu chaaaa akai sai duk ta dauka ko dagaske ne kawai dama deceiving dinta hajya khadijatun take sonyi shiyasa take son ta rudeta ta rufawa danta asiri akan laifin dayay. But she just cant forgive Ahmed soo easily a wann karon, taya ma zai gudu ranar engmnt dinsu witout consiidering her feelings, why? Tana cikin zantar da hakan aranta ta fashe da wani irin kuka mai kara. Atare duka suka taru sunata rarrashinta.



After a while kura ya lafa saidai kowa yanayinsa babu dadi dan kowa sai dirin masifa yakeyi ata cikin zuciyarsa sun zauna kowa ya daure fuskarsa yana diri. 


Hajya khadija ce kawai tare da kafayat a daki ta kwanta akan cinyarta tanata mata kuka sosai.


Babu kalar hakuri da lallamin da hajya khadijatu batay wa kafayat ba amma haryanzu zafin abun da rudanin sata shiga bai dena damunta aranta ba.


Daga yanayin tambayoyin da kafayat take mata acikin kuka yasa jikin hjya khadija ya soma bata cewa kafayat is already doubting her akan behvrs din Ahmed.


Tausayin yarinyar ya dameta duk sai Ta rasa yadda zatay ta fahimtar da kafayat din cewa ita bata san komi gameda tafiyarsan nan ba.


Tasan kuma inta kyaleta anan gidan su anty ramoutou zasu iya kara hura mata wutar shakku da rudani acikin zucyarta game dasu dan haka ta umarce kafayat din akan cewa ta shirya kayanta suje gidanta su jira dawowar Ahmed din acan atare.


Dake ita ta raine su tasan duk wani luggansu acikin sauki ta shawo kan kafayat din ta hanya nuna mata cewa tana tare da ita yau sosai.



Immidiety bayan sallahn zuhr suka bar gidan, ko wani sallaman kirki su anty moju basuyi mata ba dan ko kadan basuji dadin tafiya da kafayat gidanta da tay ba.



Koda suka isa gidan ma lallaminta ta dingayi tana mai shagwabata tamkar itace ta tsuguna ta haifeta, ganin kafayat din ta damu sosai yasa tay mata alkwarin cewa muddin Ahmed ya dawo zata sakashi ya bata hakuri with an engagement ring kmr yadda take so din.


Sosai kuwa duk wata lugga da salon rarrashin  hjya khadijatu yy tasiri acikin zucyar kafayat dan dama can bata taɓa furta mata hakan ba, she is sumhow realived dataji yau hajy khadijatu da bakinta tace zata tursasashi ya aureta inya dawo dan bata taba furta mata hakan ba sai yau.


Rarrashi da kalaman hjya kahdijatu shine ya dawo da kafayat daidai tadan sake jikinta kadan..



******


 *10.30 am*

 _margaret ekpo intnl Airpot calabar, cross rivers state nigeria._ 



A daidai wann lokacin jirginsu Ahmed ya kammala sauƙesu yana isowa arrivals already uber driver dinsa na nan jiransa agaban space na parking with a broad and warm welcoming smiles.


Gaishe sa yay baima amsa shi ba.


madaidaicin troley dinsa drivern ya amsa ya saka masa a booth sann  ya taho a guje ya bude masa murfin motar agidan baya ya zauna after some few min drive suka iso transcorps hotels dan shine convenient location din dake kurkusa da aiport din.


Tun akan hanyar yaketa nazari a brain dinsa na yadda zai bullowa dan uwansa brother hamzat dimeji da wann maganan cos he really need his support fiyeda da yadda ake tunani. Tunani yay Kodai ya aiki Banji ne tunda su suna abuja ynxu akanda yaje ya samesa ya masa bayanin komi kafin lkcin shi ya samu nitsuwa saisu tattauna? that seems like a prety good idea dan Yasan abokinsa banji duk ya fisu nitsuwa da iya magana cikin girmamawa da manya.


A hadadden suit din daya kama daki mai lamba 105 ya zauna ya soma hutawa kadan snn ya jawo system dinsa ya fara duba abubuwan dake gabansa dan karya manta da wasu.


Already shida abokinsa banji sunyi kyakkwan bincike game da festivals din da za'a gudanar a garin wanda anan ne yake saka ran zaigana da fuskar yarinyar dayazo nema, a cikin nitsuwa yake scrolling files dinsa da cursor har ya iso kan wani file da aka rubuta _leboku_ Wato festivals.


 Acikin wann document din ne aka turo masa dukkan wani bayani hade da locations na wajajen da zaije domin cimma abunda ya kawosa garin cikin sauki. Bude files din yay ya soma karantawa daga farko dan yay refeshing memorynsa.


 _Leboku_ kalma ne dake nufin festival da yare, awajen mutanen wann gari na calabar babban festival dinsu bai wuce annual new yam festivals da suka shafi shekaru aru aru sunayi ba, shi new yam festival din ansamo shine daga mutanen yankin _yakaa_ masu speaking yaren su na _yakuur_, ana taruwar gangamin celebrating wann gagarumin festival din ne a south south ko east region na cross rivers state, inda ya haɗa da dukan Comunities da yarukan dake karkashin mutanen _yakaa_ wato yankunan ugep, idomi, ekori,mkpani and nko.


sai kuma international celebration na new yam festival dake ayinsa ne sau daya a shekara acikin yankin ugep inda kasashen duniya daban daban suke tahowa domin halattar wann gagarumin festiva kamr irinsu jamaica, lebenon, sierreleone da kuma yan cameron. Shiyasa ake ambatar festival din a matsayin  the biggest african street party .


Musmn ma da garin calabar ya riga ya shahara da cinikayya na siye da siyarwan kaya tsakanin yan kasa da yan kasashen waje, duk wata harkan comercials  activites dinsu ya bunkasa ne tun acan zamanin slave trade a 18th century.


Cross river calabar wajene daya tara rabe raben harshuna kamr irin  Yaren dayafi yin karfi awajen wato yaren EFIK duk dama anfi regarding din region din as an IGBO LAND. Sakamakon transition din da aka samu na cigaba a duniya yasaka duk wani harkan kasuwancin dake yankin cross river suka bar zancen saida bayi suka dawo siyarda manja, da sauran ma'adanai kamr su ivory, red wood, rubber, barwood. Cinikayyar su tafi karfine da mutanem portugal, da kuma french,dutch da america. Yaren Efik ya kashune izuwa "seven sister clans" most of them suna tsakanin cross river ne da akwa ibom.


Yanki ne da gabaki dayanta take zama a karkashin _ibibio tribe_

Sabida ibibio tribe din dadaddiyar yare ce datake in existance tun kafin a samo kasa me suna nigeria, ibibio land is known as the mother eastern region of nigeria as a whole. Shine yankin da ya hada zuriarsa da yakunan mutanen Efik( sune northen ibibios) annang(sune westen ibibios), oron niger in niger delta state, eket(sune southen ibibioa), sai kuma ogoja disrict inda yawancin babban kasuwar su ta festival yake, Wanda ahalin ayanzu duka wayann yarukan sune aka fi saninsu da yankin _Biafra_ (bight of biafra)

East, and South eastern nigeria.


During civil war ne aka raba sashunan suka dawo  su uku ,wato south east,(cross river,calabar) south west(akwa ibom izuwa yankin boarder nigeria da cameron) sai northwest (adamawa, da taraba) some are in delta states some in abia, umahia and equtorial guinea.



Mutanen dake wayann yankunan sunfi ta allaka ne akan addinin su ta gargajiya gadon kaka da kakanni wato addinin nan bautar spirits din magabatansu. Shiyasa yankin easten nigeria gabaki dayansu suna under two dimensions ne wato suna kiran spirit din magabatansu da  Allolin su ta hanyar" offering din "secrifices,consultations na bokaye, chief priest incantations, worships of sprits, communicating with the death,da yin muamala da mutattu,


Sunada shahararrun Alloli kamar irinsu _God of nature_ (Wann din shine Allahn yanayi) wanda idan yace kai mai arzikine toh ta zauna akanka kenan, hakama idan yace kai din matsiyaci ne tsiya tazauna akanka kenan bamai iya zanca maka yanayinka._sai God of destiny_ Wann Allahn nasu shikuma shine wanda idan  wani abu mummuna na kaddara ya afku akan mutum akanje ne a rokesa akan yay reversing din abun ko kuma ya canza shi mai gabaki daya, misali"

kamr idan mutum mai kudi ko mai ilmi ya mutu accidently, toh familyn mamacin zasu iya  consulting diviners na Allolinsu sai agaya musu  abinda yasaka dan uwansu ya mutu,snn abasu sharudan da zasu bi suyi reversing destiny dinsa dan ya dawo rayayye, wann Allah nasu shine yake basu, snn inhar sukabi sharudansa strickly to tabbas komi zai kasance musu daidai. Akwai wasu ire iren su kamar God of heaven, god of earth snn kowa da aikinsa 


Sann akowani division na yarukan akwai sacred lands(akai) wato forest, _akai_ shine baqqar jejin da suke aikata duk wani tsafe tsafensu, ana kiran wajen _Akai_ ne sabida babu wani halittar da aka halatta masa yin noma ko yin gini ko kasuwanci aciki ajejin gabaki dayanta.


Wajene da ake binne gawawwaki, ake gina manyan shrines, da kuma hazikan secret societies masu tuamali da manyan Allolinsu, da cult grps kamr irinsu Akpo onyoho, ekpe, idiong, ekoong and obon da sauransu sune acikin jejin saboda they are consider as sacred.



Inhar kai baka kasance  member na wani cult  acikin wayn ba toh shiga cikin jejin ya haramce ka kenan har abada hakama bazaka dauki koda itace ko tsinke daga jejin ba, bare ajega deban ganye ko hunting animals, koko kace kaje debo dodon kodi ko kuma itacen girki. All these things are highly prohibted  in the sacared land or forest.


Snn dukan yankunan sunada wani al'ada da ake cewa _"the soul and life after death_ 



Duka yankunan earsten nigeria suna kasa rabe raben soul din mu a gidaje guda hudune 


..acewarsu soul dinmu na farkon shine "gangar jiki"wato (etherel body)

Na biyun kuma shine asalin "ruhi"(soul) na ukun shine fatalwa (spirit)na hudun shine suke cewa (over-soul).


Acewarsu shi Over-soul din ba ajikin dan adam yake ba dan ahade yake da spirit din jikinsu..they believe that over soul shine gangan jikin dan adam dayake zama acan duniyar mutattu.


A cikin wann sashen ne ake gane masu animal soul, water soul, ko shadow.


Misali akwai souls din su dayake rayuwa a matsayin maciji, ko kura ko zaki ko duji ko tsuntsu ko wani wild animal ko forest beast. saidai most time akan iya shiryawa mutum mugunta idan aka gano inda nashi over soul foarm din yake, misali in nashi soul din na water body ne, wani zai iya striking din ruwan daga inda yake sai kuma mutumun ya mutu a dik inda yake, hakama idan inuwa ne evil spirit zasuyi saurin kamawa su daureshi, in dabbane za'a iya harbesa da kifiya ko bindiga ya mutu.


Snn sun yarda da cewa idan mutum ya mutu a duniyan nan rayuwarsa ta duniyan shine zaije yay acan lahira.


Misali, idan ka mutu a matsayin manomi anasu tunanin a sama ma matsayin manomin zaka taso, hakama idan kamutu a mai arziki da arzikinka zaka tashi, snn inka mutu mashayin giya hakanam zaka tashi dashi kacigaba da rayuwarka bayan mutuwa. Shiyasa kafin nan akaika kabari sai an maka guzirin abubuwan amfani kamr su abinci tukunya, kayan sawa da abubuwan bukata dan a tunanin su ko daga wani irin yanki ka fito daga zarar ka mutu a cikin zuriarka ta duniya zaka tashi.



AHMED saida yaja wata iriyar doguwar numfashi mai tsayi bayan ya  kammala karance brief files na tarihin al'adan su na da can da yadda suke muamalarsu da mutane a al'adance yanzu har izuwa yadda suke yin al'adun su na aure da biyan sadakinsu.


Kafin nan ya kammala nazari akan komi har lokacin azhr ya tunkaro dan haka ya sauƙa daga kan gadon ya rage kayan jikinshi ya faɗa toilet yay wanka yay alwala snn ya taho yay sallah, bai iya shirin gaggawa ba dan haka ya fasa fita batare da yaci abinci ba.


Oder abincin kawai yay ta telephone din dake room din aka kawo masa hadadden rice and lamp stew with couslow ya zauna ya ci sosai ya koshi snn ya soma yin shirin zuwa filin da za'aci taron,nan ya bude trolly dinsa ya fidda wata  hadaddiyar casual wear  mai fitinannen kyau snn ya shiga shirya kansa acikin nitsuwa...

#surayyahms 08060712446 chats only*KISHIYAR ƘABILAH..8*



BY SURAYYAHMS.



CALABAR INT'L TRADE FAIR (C.I.T.F).


Wajajen karfe 2:00 na rana Ahmed ya kammala shirinsa izuwan wajen taron, yau yasaka wata hadaddiyar golden colour raymond shirt ne akan wata dark brown pants da cooperate duster coat mai open breast wanda kallo daya kamasa akaro na farko zakace shidin wani kazamin dan mai kudi ne dan gatan hajiya dan bakaramin kyau yay ba, kan nan tashi tasha gyara kamar a sace shi, duk inda ya ratsa sai an juya an kalleshi sabida banbancin yanayinsa da mutanen wajen gawata mayyar qamshin turaren regenedes dake bibiyar duk wata salon tafiya da kuma motsawar jikinshi mai tafiyarwa.


Kwanaki 32 ake deba na musmamn domin yin shahararren festival din wanda aynzu haka baifi saura kwanaki sha hudu a kammala festival din gabaki daya ba..


Shi damacan ba wai damuwarsa bane yazo yaga wasannin al'adansu yazone dan ya same abun daya kawo shi a garin. Dan zaman da yay a garin during disease reaseach dinsa yasaka yadan sassan wajaje da dan dama acikin gari shiyasa ma bai damu da neman location din hidiman awajen kowa ba.


Kai tsaye ya wuce wajen sanin cewa yana da valid i.d card dinsa ajikinshi wanda yasan duk inda yaje ya nuna zai zamu masa free pass tunda shaida ne nasanin cewa shima babban likitane.


Daga cikin hidimomin da suka rage baifi hidima hudu zuwa biyar bane akarkare dan duk sauran shirmen festivals dinsu sunyishi ne a baya tun kafin ya iso. Wanda suka ragen sune Hiv/aids walk and conference, sai canirval queen peagent (beauty contex), sai musical displays da ekpo session wanda shine akeyinshi karshe wanda ake yinshi tare da bokaye da dodonni.


Yaune za'ayi business and street walk tun daga hall din tinapa business resort, dats bayan an kammala yin taron da zasuyishi na HIV/AIDS conference sun danyi walk to honour the occasion,a daren yau dinne kuma za'ayi beauty contest at the same hall na hotel din for calabar carnival queen peagent.



Tun karfe 12.00 na rana aka fara taronsu na hiv/Aids conference inda likitocin turawa da kuma manyan masana kiwon lpya da wasu daga cikin ministers na kasa da sauran masu hannu da shuni aka taru aka tattauna akan wann cuta.


Ahmed bai wani jima acikin hall din ba aka kammala taron kowa ya fito waje domin yin street walk din, yana fitowa ya fara haduwa da mutanen da yadan sassani just few mutanen da suka sanshi sosai awajen sukayi recongnising dinsa suka tsaya suka dan gaggaisa dashi duk basu wani sha mamkin ganinsa anan ba sabida sunsan duk wani abunda ya shafi communcable disease ya shafe sa.


Bayan sun kammala gaisawar da can har zai musu sallama ya tafi saiya tuna cewa binsu izuwa street walk din zai bada ma'ana sosai wajen rufa masa asirinsa agida.


Yasan duk rintsi yau dai iyayensa zasungansa a TV yana hiv/aids street walk, snn duk zasuyi tunanin aikine kawai ya kawosa calabar ba shirme ba, hakan yasaka ya saki jikin shi sosai acikin yan uwansa likitoci anata raha da shi kmr bashi ba.


Tare suka dauki placards da poster ya shiga cikin su sukayi walk din ana debe ma juna kewa yana gaba gaba suna takawa akan titi har suka kai ga business center inda za'aci taron acikin market square.


Wajen bakaramin cikawa da jama'a yay ba, maza, yara da tsoffi da yan mata kyakwwa sosai kowa yasako kayansa mai azaban kyau ana kida ana rawa wasu suna waka da yarukansu.


This is exclty the point where he first met Adiaha, hanklinshi yaji ya koma wajajen rumfan da yan matan suka tattaru yanata satar kallon cikin rumfar wai koda ma zai ganta acikinsu amma harya gama dube dubensa awajen bai ganta banda tarin kyawana yan matan da suke masa kallon kurilla daga can nesa.


Calabar girls are mostly elegant and beautiful masha Allah, kusan da kyar ake cire mummunar mace acikin matasan su musammn ma matasan yan matansu dan Kusan kowacce zaka ganta da cikakken dirinta da kyan fuskarta gasu da kuzari.


Wani Waje mai kyau ya nema ya zauna kusa da wasu annang town ppl da few criers daga ogoja district musammn ma dayagan su duk sunsako kala da irin kalar kayan da adiahan ta saka ranar

Daya fara ganinta.


Har aka fara rububin hidindimu awajen amma hanklinshi baiya jikinshi sosai, he kept staring and staring at girls tun da aka haifeshi bai taba tsayawa yana kallon yan mata kamar nayau ba.


He desperatly want to see adiaha sabida Allah baiyishi mai yawan hakuri ba aransa bai ki ace yau ya sameta izuwa gobe ta amince agama komi ba. Baida wani burin daya wuce yaga ya tsallake family problems dinsa. Dan duk duniya babu mai bashi matsala arayuwarsa kamar familynsa musammn ma wayanda suka matsa masa wai saiyay aure alokcin da shi baima shirya yin auren ba.


Yan mata dayawa sai signal suka masa amma yaki ba da kai, wasu ma harsuzo su gaishe sa amma baiya kulasu.


Sai can kusan karfe hudu da rabi ya bar wajen ya nufi wani filling station inda akwai masjid ya gabatar da sallahn asr sann ya siya ruwan sanyi na gora da energy drink a super market dinsu yadan shashsha.


Bai kara dawowa cikin taron ba sai wajajen biyar da rabi saura ya zo ya tarar da wajen duk ya kacame an tattashi ana rawa ana tafi wa wasu yan mata dake rawa a tsakiyar filin kasuwan.


Ahankli ahankli ya kusa kai ya shigo ciki wajen zamansa ya fara kallo shima.


Group biyune na yan mata duk sun sako traditonal attires sun daura zani iya gwiwa da fararen riguna masu daukar hankli da waist and legs beads, suna murza rawan yarensu duk jikinsu sunyi ado da jigidan rawa.


Akaro na farkon ma bai ganeta ba saida town crier guy na gefensa ya soma mata ikirari da sunanta, a karo na farko da Ahmed ya kalleta da kyau saida yaji wani sanyi aransa jin kaman ya samu karensa ne daya bace masa ajeji, he was lost for a moment saboda sosai Adiaha ta canja ta kara girma sosai ta murje tayi kyau bana wasa ba. 


Itace farar yarinya yar kyakkwa natural beauty dake rawa agaba, tana da matsakaicin tsayi da tumin duwawu da wani irin kibabben jiki wanda tsayintan ne kawai yake dada rufa mata asiri da saidai ace ta girme shekarunta cos she is 27yrs old and looking 34, it seems like itace shugaban yan matan dake rawan dan itace agaba sauran yan matan kuma suna biye da ita abaya suna rawan suma.


Da Ahmed ya cigaba da kallonta kuma duk sai memories dinsu tare ya soma dawowa masa cikin brain dinshi daya bayan daya. 


Wani bin  inya tuna wani abu sai murmushinsa ya gushe masa sosai musammn ma inya tuna wahalar da Adiaha tasha akansa, itace masa girki wani bin ma da kudinta take siyen abincin snn ta dafa masa ta kawo masa ahakn ma sai ta rokesa kota lallabashi snn yake yarda ya ci, haka zata masa shara ta tsaftace masa ko ina agidan hayan daya zauna, intazo ko ruwan wankansa bata bari yakai bandaki, kai har wanki da guga tana masa alokcin amma ba hakan bane yasa yataba nuna mata alaman cewa yasan tanayi dan aganin shi easy going girls are cheap girls. Wani abun ma har baison tunawa, dan yasan inya sake ya cigaba da tuna wasu  basarwa da walakncin dayay mata abaya hala dan karfin gwiwar dayazo dashi duk zai kare awajen tunani.



Cheerful song da Town crier dake gefensa yakeyi ne ya dawo da shi hayyacin shi ganin inda ya zauce yanata kwadata sosai kamar yaga matar sarkin garin sun mai gabaki daya.


Wani tunani yy snn yasaka hannu ya ciro kudi dubu biyar sababbi a aljihunsa ya bawa mutumin kyautar kudi


Aikuwa nan da nan mutumin ya juyo kanshi da ikirari da godiya shikuma ahaka yasamu daman janshi cikin hirar Adiaha. Sai yay kamr baisanta ba, so he just asked him akan meyasa yake ta yabonta what is soo speacial about her


Acikin sauki mutumin ya soma zuba masa zance


Yace masa ai itace take cinye qasar crown canirval queen na beuty peagent contest da akeyi kusan kowani shekara amma wann shekarar zata aje gasar ma yan baya sabida anasone a aurar da ita. 


Da mamaki sosai Ahmed yace "a aurar da ita kuma?


Mutumin yace masa eh, amma batason auren, elders ne sukayi shawara akan haka and already a wann rububin bikin festival din an bada dama ga duk wani wanda yake son auranta dayaje Gidan sarki a tattauna da shi in akaga ya dace da ita sai ahadasu.


Ahnlki Ahmed ya gyada kansa snn yace "Hakan al'adanku ne ayi ma yarinya auren dole?..


Mutumin yace "mbaanu, no sir..gefe da gefe ya duba kamr munafuki sai yy wasu yan maganganu cikin harshen yarensu snn ya sasssauto da muryansa kasa kasa yace you seee,dat girl refused to date anyman duk da yawan maza dake layi akanta, see erhn even son of obong, our prince has shown intrest in her amma haka taki sam  Shiyasa ake ganin ko spirit ne suke son su aureta, and dats why akeson amata auren cikin gaggawa. Kasan in spirit suka aureta she wll be living in _Akai_  in the evil forest and dats bad for her family..no body will come close to her again _mba,tufiakwa_.


Ahmed ya gyada kai kamr irin abin bai wani darashi ba,cikin basarwa yace its okay,..tnks..


Nan Mutumin yaje ya dauko kwalban giyansa yafata sha yana zubama Ahmed free stories akan adiaha musmmn da yaga kmr yana da kudi awajenshi sosai.


Tashi guda Ahmed yasan kusan komi da komi gameda rayuwarta harda wanda bai taba tsammanin zaiji ba.


Adiaha is like a star agarin su, a 3 times winner of the calabar canirval beauty peagent context,dan haka kusan dukkan wani lamarin rayuwarta da sirrikan familynta a fili yake kowa yasan komi akansu...


Yamma na neman rufawa Ahmed ya kara ma mutumin nan kudi snn ya rubuta mata short note adan paper ya dunkula ya bashi yace yakai mata yace mata Dr Ahmed,.


Jiki na rawa mutumin ya amshi takardan duk dama yasha mamakin sunansa dayace Ahmed ganinsa zubin kabila da sunan musulunci,shidai bai damu ya tambayesa komi ba dan a tunanin sa inyaje ya dawo da wuri hala ahmed zai kara masa kudi, sam ba a bari a shiga wajen yan matan amma nan danan yayy yar cukucuku ya kutsa kansa cikin ribibin taron, ana janshi yana kusawa yana ihun sunan Adiaha, da kyar har saida yakai mata letter da ahmed ya bayar abata hannu da hannu yaga ta riƙe toh kafin yace mata doc ahmed dinne har an koreshi awajen anyi firo dashi wajen fili.


Ta rike letter a hannunta tana shan mamaki ganin yadda yake mata alama koda zata dan dubi inda Ahmed din yake,daga can nesa Ahmed yaketa kallonsu ganin ta da ltter a hannunta yasa yy dan murmushi sai ya juya ya bar wajen dan aransa yasan inhar ta gane shi dinne toh babu tantama zata biyosa har inda yake bada jimawa ba, tanata son ta juyo  kenan sai wata mata ta jawo hannunta da karfin tsayi paper ya kubuce ya fadi a kasa, daga nan she was soo busy kowa dai yana son ya dauki hoto da ita.


After a while bayan an gama taro waje ya soma rufawa duk yan matan sunaa shiri zasu koma babban hotel dressing room inda zasuje su farayin shirin beauty peagent walk dinsu.


Can motarsu yazo debarsu da ita da crew dinta zasu tafi hotel din kenan sai ga wann town crier din ya fito yana layi, hannu ya daga mata, sai ta tuna dacewa ya bata wani paper dazu, da harshen yarensu ta tambayesa meyene ya bata dazu, ya rage muryansa kasa kasa yace mata aika ne daga Dr. Ahmed, sauka tay a motar babu shiru jikinta harna rawa tazo sameshi cikin gaggawa cikin harshen yarensu tace "ubonna what did u say?

Da harshen yaren Yace 

"Ai kin jini" tace no no say it again?..dayake abuge yake baiya cikin hanklinsa sosai nan ya soma yimata describing din kamanin Ahmed sosai wanda tun kafin nan ya kammala fada mata Adiaha ta daskare a tsaye tana kallon sa, bakin sa take kallo yanayinta a ragwabe ta tsaya stifff kamar wanda akayi mutum mutuminta awajen.


Yace indan baki bani wani abu na fashin baki ba, i swear bazan gaya miki sauran labari akanshi ba.


A Take ta ciro dubu biyu daga cikin purse dinta ta mika masa  yasaka hannu ya amsa dan dama abunda yasaka ya tsaya kenan, murya kasa kasa yace mata ai takardan nan daya mika mata Dr ahmed din ne ya bashi akan ya bata.


Muryanta harna rawa tsabar kaduwa da mamaki "Tace what? are u really serious? Cikin layi yace mata "tare da shi ma suka zauna awjen taron har aka gama.


Take taji wani irin yanayi na kwasarta tun daga brain dinta har izuwa kan yatsun kafarta, cikin muryan damuwa sosai tace ..Ubonna why dind u tell me? shine bazaka fada min alkcin ba,yanzu ina yake? Ubonna yace mata oho,ni bansani ba "muryanta kamar na wanda zatay masa kuka tace ubonna why na? Why,why ..did u knw what u did to me? Sumone that i have been looking for all these years chaii ..ubonna.. but This is not a matter of joke  naaaa..ohhh god ooo, chaiii i am finished. Im soo unfortunate, Ta dora hannu aka idonta a rintse sosai aranta tanamai tafka mummunan nadama tanata cewa a ina zanga takardan nan yanzu?...


Kallonta ubonna ya dingayi yana tura baki dan yasan dolene dama zata nemi takardan shiyasa dayaga sun yar akasa dazu ya lallaaba ya dauka domin ya samu hanyar yin ciwucuwn kudin da zaije ya ci abinci yasha giya. 


Har an akammala shiri motansu yanata mata horn alaman zai tashi amma Adiaha bata dena bubbbuga kafa akasa tana cizan yatsa cikin takaicin kanta dana ubonna ba.


 Saida ya bari tagama kaguwa idonta ya kawo ruwa snn yace mata suyi ciniki, ta cika masa kudin data bashi ya dawo 5k saiya bata letter, yace mata ya tsinta a inda ta yar amma bazai bata a free ba.


Dukkan kudin purse dinta ta cire ta damka masa harda kari snn tabishi da masifa akan meyasa bai gaya mata cewa ya boye letter ba akan lokaci.


Yana ciro takardan ta fauce hannunta harna rawa ta juya masa baya taga babu komi ajiki face adress din hotel dinsa, da lambar room dinsa da kuma sunansa, da can har zai rubuta mata sakon harda new phone numbersa akasa wanda yake amfani dashi agarin koda zata nemeshi dan bada layinsa yake amfani ba, wani sabo dal ya siya  yasaka danma kar kowa ya nemeshi amma sai ya fasa rubuta mata lmbr saboda tsaro.


Tunda ta karanta sakon ta kasa jin nitsuwa a zcyarta da jikinta duk jikintan saiya dau rawa rawa ta rasa akan me guda daya zatayi tunani, 


dama kuma haka lamarin Dr Ahmed din nan yake mata tamkar wanda aka mata asiri akanshi,dan  daga zarar taji sunansa shikenan sai taji kamr ta rasa hanklinta ne gabaki daya ta haukace, ta tuna lokacin daya tafi yabar garin she was so angry and heart broken becos of him har ruwa saida aka saka mata agadon asibiti akansa dakyr ma ta iya mancewa da shi.


Yau kuma sai gashi nan wai ya dawo garin nasu out of no where sai taji kuma babu wani abunda take so aranta aynzu face ta ganshi ido da ido koda dataji sanyi.


Babu tantama inhar dan bayarbe ya amsa sunan sa na bayarbe dolene akira shi da inkiyarsu na "yoruba demon" din nan.


Cos omo, yoruba guys are surely deal breakers, irrestible, and hard core players, gasu nan sune agaba wajen iya daukar wanka, hakama zasu walakanta mace son ransu amma bashine zai hana same girl din ta bibiyesu ba.


Tunda Adiaha ta samu takardan ahannun ubona sai bata kara kulashi ba ta jefa takardan a purse dinta cikin sauri ta koma cikin motar ta zauna aka wuce babban hotel din da ita.


Tasan Ahmed yana zama ne a can transcorp hotel na kusa da airpot, su kuma hidiman nasu a nan A tinapa lake side hotel za'a yishi, tunda adiaha ta zauna acikin yan uwanta tay tagumi tayi shiru batako motsi bare magana tsabar hanklinta yay wani waje, lissafe lissafen yadda zatayi ta isa wajen muradin zuciyarta acikin gaggawa Kawai takeyi har suka isa location na night progrm dinsu



Sai sum sum kawai takeyi sabida mind dinta ya riga ya rabu kashi uku, 

Daya yanakan Progrm din da zasuyi yanzu, daya yana kan Gida, dan mum dinta tace mata duk rintsi duk tsiya yau ta tabbata cewa agida zata kwana sabida za'a turo da suitor dinta da aka zaba mata yau agidan sarki zasuzo da elders  suganta da sassafe tana amincewa da shi ranar ekpo festival zasu taru asaka mata ranar bikinta da yardan spirit of the ancesstors dinsu,.

komawarta gida a daren yau is very very important sabida a shiryata wa zababben suistor dinta, amma kuma zuwa wajen Ahmed a tanscorp hotel too is equally her life time oppurtunity bazata taba iya bari wann daman ya wuce ta ba.


She is soo confused duk ta rasa me zatay guda daya, in bataje gida ba hakan zai jawo babban matsala a wajen iyayen ta da uncles dinta, idan kuma bataje wajen AHMED ta same shi ba karyazo ya tafi garinsu tay loosing chance dinta dashi na har abada.


It will all be her fault since he came back kuma har ya nemeta, aranta tasan inhar ta barshi ya tafi ahaka bataje ba toh bazata iya yafema kanta cikin sauki ba.


The way she loves Ahmed is out of this world dan tun da kakarta ta bar al'adansu ta auri musulmi a yola taga yanayin rayuwarta data gina mai kayu a north take mugun jin sha'awar musulunci. Its been an honour for her to meet a muslim guy duk dama tasan ko mutuwa zatay a familynta bazasu amince ta aureshi ba. Canja addinin da kakarta tayi shine babban dalilin daya ruguza mata zaman lpya da hadin kan dake cikin familynsu haryau.


Gashi itama tazo tana son taje wajen Ahmed snn bata son ta batawa familynta rai duk sai taji kanta na juyawa da rudani ta rasa wanne zata bi guda daya.


Yar uwarta Ekaete dake lura da ita itace tay noticing din yadda Adiahar ta canza musu lokaci guda ta dawo kamr wanda hanklinta gabaki daya baya tare da su.


Anata shirin beauty context,kowa yana zaban kayan fitarsa da kalan make up din da zai saka,wasu sunata warm up catwalk na walking styles dinsu da zasuyi akan stage amma Adiaha bata ko saka ranar tashi tsaye awajen ba, lissafin yadda zata zille taje transcorp hotel wajen ahmed tafarayi she just cant control the feeling cos she loves him soo much.


A Can abuja kuwa tun bayan faruwar abunda Ahmed yay musu kowa ya zamo cikin tunani musammn ma kafaya.


Hjya khadija tana iya bakin kkrinta wajen ganin ta kwantar Ma kowa hankli amma tunda su anty mojoshola suka fara ririta magana basu bari ba saida suka sakashi ya dawo wani babban al'amari.


Yanzu haka sunbar kan kafayat sai suka dawo da gurmin Kan Dan uwansu Alhaj bello jimada dake baya gari tun da asubah yaje jos on a 2dys visit gobene zai dawo,duk da haka basu hakura sun kyale maganan harsai ya dawo ba,tun ficewarsu hjy khadijatu suka kirashi awaya suka sakoshi agaba da munanan kalamai na zugi akan matarsa da dansa Ahmed.


Anty ramatou narrated evrtyhing to him amma saida ta juya gaskiyar maganan ya dawo karya, she make sure ta maida duk wani karamin magana ya dawo babba....


Tace masa hjiy fatihat tazo gidansu tay musu tijara akan dansa Ahmed, tace masa wai har marin anty moju ta tashi yi saboda abunda Ahmed ya aikata musu akan kafayat. They stresses evrything yadda kasan tare da Ahmed din aka shirya engagemnt din.


Kowani laifi saida suka daura ma mahaifyarsa hajya khdija, karshe ma sukace Ahmd ai jininsu dan haka baida laifiin komi,uwarsa ce take sakashi a mummunan hanya sabida jinin ta na northener wanda suke training din yaynsu da rashin sanin darajar mace.


Anty moju ta dinga kuka

Tana jan masa Allah ya isa, tanata tuna masa yadda takijinin auren da da hajy kahdijatu tin farko sabida kawai dan ita bahaushiyace kuma tasan zatazo ne cikin zuriarsu ta lalata musu zuria kamar yadda yanzu ta tarbiyartar musu da jininsu Ahmed ya dawo kmr mazan hausawa wanda bai san darajar mata ba.


Babu irin dagamai hanklinsa da basuyi ba duk yakasa zama haka ya nade garinsa ya dawo abuja a cikin dare bai je gidansa ba saiya wuce family house dinsu.


nanma da suka gansa adame wani sabon rikicin suka tayar masa suce wann suce masa wann harsaida yaji kamar idan yagamu da Ahmed zai iya yankashi 


Kai hatta matarsa ma haushinta ya somaji aransa sosai sabida yadda suka fassara masa ita,dan boro boro suka nuna masa cewa itace babban mai laifin dan itace ta daure masa gindi yay tafiyarsa.


wajajen karfe 10 na dare Ahj bello jimada ya dawo gidan ransa a bace ya tarar da matarsa tare da kafayat a falo ta kawo mata ruwa da panadol kenan ta mika mata tanamai lallabata akan datasha sai taje ta kwanta tay bacci.


Da murmushi mai sanyi hjya kahdija ta tarbe mijinta da suka hada ido

Saita dan ja baya cos He look frusted and annoyed  lkcin angama cikamai cikinshi da maganganu akanta harya koshi


..sosai yake jin haushinta akan batun ahmed duk dama yasan bata biye ma ahmed but the way anty moju was crying and swearing  yasan bazata masa karya akansu ba.


Tun shigowarsa data dube sa tasan ba lpya ba dan ko sallamarta bai wani amsa mata ba, wa kafayat din kawai yy ma magana ta amsahi a ladabce ta gaishe shi yanata jajanta mata snn yace mata yana son ganinta a sashensa.



Daga nan ya wuce sashen nasa yana shiga saiga hjya khadijatu tabiyosa abaya amma baiko kulata ba 


Fuska bayabo fa fallasa tafara masa magana akan dawowarsa dayay acikin gaggawa sai tsareta yay da tuhumar inda Ahmed yaje..


A fusace ya soma mata magana da alaman ranshi sosai ya baci.


This boy has become a problem for me, sai kace shikadai na haifa? Komi sai anyi rigima dashi dan baida mutunci? kuma kece Khadija, laifin kine kin lalata min yaron na gabaki daya bayajin maganan kowa sai naki.


Nasan kinsan inda yake inhar kinason kanki da lpya agidan nan kice masa ya dawo gidan nan maza maza befor i loose my temper on both of u.


Ranta sosai ya baci da ihun da yay mata amma haka tay kkri ta danne bacin ran azcyarta, bada dagon murya ba tace masa "itama bata san inda Ahmed yaje ba. Dan bai gaya mata komi ba.


Tun bata kammala rufe bakinta ba ya tsareta yace sam karya take masa, duk wani karyan da su anty mojun suka gaya masa yafara tuhumarta da shi yana mata fada akai sosai.


It turns out that sunce masa ta hada bakine da danta ya gudu dan karya aure kafayat sabida ita ba bahaushiya bace, wanda hakan ya jawo musu cin mutunci harda mari awajen hjy fatihat.

Da Karfi dayaji saida su anty moju suka maida ta makira, munafuka a idon mijinta ayau.


Wani Duhu duhu ta fara gani tsabar yadda maganganun nasa suke konata taciki, tana ta so tay loosing temperta itama tay masa kaca kaca amma inta tuna cewa kafayat na bakin kofar dakin tanajinsu sai ta hadiye fushinta tay shiru..


Shikuwa ganin tay shirun yasa ya dauka ko gaskiya ne bata da shi shiyasa bata iya kare kanta agabansa ba.


Yanata surutu haryakai ga ya soma jefa mata bakar magana akan sauran yayansa da suke masa biyayya bakamar danta Ahmed ba.


Yace mata Duk cikin yayansa da girmansun nanma baitaba fada musu magana sun tsallake ba sai danta Ahmed, kuma duk dan akan tana daure masa gindi ne agidan yake masa abunda yaga dama, ya cigaba da tuhumarta da cewa tana amfani da danta tana cutar da kafayat, haryace mata soyayyar da kulawar munafurci take nunawa kafayat din tunda har ta kasa iya controling din danta.


Hawayen bacin rai dayake zuba acikin idanunta ta share dan sosai take tafarfasa ta ciki tana konewa, she really wanted to blast him back koda zai dawo cikin hayyacin shi, dan tun daya soma maganan ta fahimci inda ya dosa tagama fahimtar cewa pumpa shi akayi na musammn akanta da ita da danta ahmed.


Daga bakin kofar kuwa Jikin Kafayat sai rawa yakei dan duk zaman datay dasu na shekaru aru aru bata taɓa ganinsu suna rikici irin wnn ba.


Jin ya soma zafafa magana akanta yasaka tadan kwankwasa kofar danta dakatar dashi,yana yin shiru kuwa sai ta shigo ciki jikinta a sanyaye sosai.


Agabansu ta dan rusuna

Ita kanta kafayat din ta budi baki knan zatay magana ya tsareta da fada Yanamai cewa ita yarinyace bazata gane makircin manya ,dan haka tayi shiru snn ta zauna a site dinsa kawai, he will take care of her dakan shi kmr yadda su anty moju suka umarce shi. Yace bazai kyaleta ta zauna awajen wanda suke causing mata pains ba dan itama tamkar yarshi ne tunda sune suka raineta kuma tana musu biyayya.


Hajiya khadijatu ta share hawayenta ta dubeshi rai abace sosai idanuwanta sukayi ja, ajiyar zxya tay ahankli snn tace masa "shikenan Alhaj, naji duk abinda kace, tunda nice na dawo maka munafuka

..Allah ya baka hakurii..


Tana fadin hakan ta juya zata bar wajen a kidime kafayat ta mike taje har wajenta ta riko hannunta tana hawaye sosai "ahhhh mamy pls im sorry dan Allah kar ki tafi ki tsaya kuyi magana da daddy this whole issure is all a misunderstansing


 hjya khadija tay wani murmushi mai ciwo tace Kafayat stay out of this okay? kizauna awajen shin kawai tunda ya amince da abunda aka gaya masa akaina..


Tana fadin hakan ta kama hanya ta bar musu dakin alhaj yaja tsaki ransa na kona sosai.


Hawaye taf idon kafayat ta taho wajensa ta rusuna da muryan magiya tanamai cewa.

"Daddy u over reacted with mumy, is not her fault at all..itama fa bata san komi ba.


Ya bata rai yace keep quiet kafayat ke me kika sani..just forget about that, ya nemi waje ya zauna snn ya dubeta yace"oya zonan ki fada min how are u feeling?


Bata iya miƙewa zaune ba sabida damuwar data shiga ciki na ganin bacin ran hjy khadija, kafin ta budi baki sai taga har ya dagota daga tsugunen ya zaunar da ita akan kujeran falonsa ahankli.


Kusa da ita ya zauna snn ya soma lallabarta based on abunda aka gaya masa na tausayi yanamai bata hkri yace mata shine zai dauki mataki akan Ahmed daga ynzu. 


Ran hjya khadijatu sosai ya sosu da abunda su anty moju suka mata na makirci.


Dan ta tabbata sune suka hade mata wann wutar masifar a tsakanin ta da mijinta harda cewa a kwace kafayat a hannunta sosai ta fahimce su so suke har kafayat dinma ta tsaneta ta juya mata baya.


Looking sad and frustrated ta zauna a sashenta ita kadai ta rasa abunda yake mata dadi ga kishi dayake so ya fara damunta cos how can her husband took a full blown up girl ya ajeta a sashensa da dare bacin ba muharramnsa bace.


kowani juyi tay saita ja tsaki Wani zuciyar yanata ce mata taje ta dauko kafayat din amma kuma bata son tay loosing temper dinta dan sosai ranta ya baci.


Daga sashensa kuwa har tea mai dadi yy wa kafayat din da kanshi ya bata da cream biscuit taci yanamai janta da hira. Tun tana jin nauyi aranta harta sake tafara biye mashi suna dariya sosai, after a while tafara jin bacci ya rakata har extra room dake gidan ta shiga ta kwanta yay mata addua ya rufe mata kofarta snn ya koma dakinsa.


Around 1pm na dare hjy khadijatu ta kasa samun nitsuwa aranta hakanan ta fito ta zo site din domin ta dubasu.


Tana wucewa falonsa ta samu babu kowa taje bedroom dinsa ta samu harya kulleta ciki da keys alaman har yay bacci.


wani iri ta dingaji aranta sai can kafin ta samu nitsuwa wani tunani na daban ya zo mata snn  ta wuce extra room dinsu direct ta bude kofar, ajiyar zuciya ta sauke ganin kafayat akwance tana kan baccinta hankli kwance. .ta dan jima a bakin kofar tana kallonta tare da jin tausayinta aranta. Ta juya kenan zata bar wajen taji motsin mutum tana daga kai sai taga mijinta ya fito daga shi sai kayan baccinsa alaman motsinta ne ya tadashi a bacci.


Suna Haɗe ido ta bata ranta sosai ..shima ya tsime baice mata komi ba ya wuce yaje ya duba kafayat din snn ya dawo ya sameta awajen tana tsaye.


Yace iya dami, Meya kawo ki nan? Havent i warn u to stay away frm dis girl? Meyene damuwanki  da ita.


Ta dauke kanta murya ciki ciki tace "No matter wat u will say bazai canja 

Gaskiya ba..i care about kafayat.she is like a doter to me amma In baka yarda ba shikenan.


Yaja tsaki aranshi sai ya fara zargin ko kishi da zargine yasata tazo dubasu amma bakomi ba dan haryanzu ganin munafuka yake mata akan lamarin kafayat kamr yadda su anty moju suka fada.


Tsaki kawai tay Tana barin wajen ya biyota har sashenta suka fara wani sabon musu acikin daren.


Yace sam zarginshi takeyi shiyasa tazo dubasu amma bawai danta damu da kafayat ba.


Ta kasa hakri tace masa

Dama inba halinka da kabila ba wani mutum mai hankline zai aje budurwan dansa wanda ma ba muharamnsa ba a sashensa bayan matarsa tana nan.


Data fadi hakan kuma sai yaji maganan nata yay masa zafi sosai saiya kasa hkri ya daga hannunsa ya wanka mata mari akan fusknta..

Ransa a mugun bace yace."haaaaaa, khadijat, U cannot disrespect like dis khadijat, u can be a hausa girl all u want amma karki sake ki kawomin raini cikin gidaana, i will not tolerate disrespect in my house..dama an sha fada min cewa kece kike koyawa dana damilare rashin jin magana ban yarda ba, but today uve finally shown ur true colours,my son cant be like you rara oti rara...

..so even anty moju was right about u, kece kika lalata min tarbiyan dana damilare, no wonder dat boy is soo disrespecful, i wll sure teach u both a lesson..yarinya baki sanni bane..dont try me ooo...


Jikin hjy khadija yafara kyarma hannunta dafe da kuncinta hawaye masu yawa na zubowa daga cikin idanunta sosai take huci..


Batace mai uffan ba har ya kammala surutunsa ya fice a dakin, yana fita ta sulale kasa ta fashe da kuka mai cin rai..


She was soo frusted da bacin ran Ahmed dana ubansa hade dana su anty mojushola da suka haddasa mata faruwar komi dake wakana tsakaninta da mijinta aynzu.



A fannin su Adiaha kuwa wajajen karfe goma aka kammala beauty peagent  context cikin girmamawa tay handing over na crown dinta ma next canival beauty gueen saidai duk ankasa gane mata dake hanklinta ba sosai ne ajikinta ba.


Farewell Speech dinta was meaningless and short kowa sai magananta yakeyi awajen yau ko tsayawa tay signing sauran document na handing over ma next queen din batayi ba,nan da nan ta shiga changing room tay sauri ta sauya kayanta izuwa wani hadadden cleverage red gown mai fidda shape dan guntu dashi iya gwiwa inda malamalan cinyoyinta suke nunawa sosai..


Gaban rigar inda ya matse mata kan nonowarta ta gayyara snn ta fetsa turaren gashin dokinta ta dada gyarashi, ta kara shafa make up tay kyau sosai.


Jakarta ta dauka cikin sauri zata sulale ta fita saiga yar uwarta ekaete ta fito cikin tsareta acikin gaggawa.


Da mamaki take kallonta

Yadda duk ta tsorata Tace Adi? Where are u going bayan anata nemanki a stage kizo carnival manager na son ganinki cikin gaggawa.


Muryanta kasa kasa tace Ekaete pls, karki daga muryan kowa yaji am going out righ now, gaskiya bazan iya tsayawa ba, this visit is very important to me, i beg u in gods name karki fadawa kowa komi.


Ekaete tace not untill u tell me inda zakije, Adi meke damunki ne? tunda dazun na lura dake ure not urself Adiaha wat is going on can u pls tell me?.


Ta kalli idanun ekaete wanda tasan inhar bata fada mata ba bazata rufa mata asiri ba sann ta sauke ajiyar zuciya tace."okay .ekaete i have a visitor in town,zanje wajensa ne yanzu,just trust me, ..yanzu dan ina saurine da zan fada maki komi,hannunta ta riko a matse snn tace pls ekaete dan Allah ki rufamin asiri karki fadawa kowa cewa na fita wani waje i promise ina dawowa zan gaya miki komi da komi.


Motsin kafafun da sukaji awajen yasaka ekaete ta kasa magana sai suka bar maganan cikin sauri sukayi sallama Adiaha tabi ta kofar baya ta shiga cikin motar taxi ta bar wajen agaggauce.


Karfe 11 da rabi saura na dare ta isa transcop hotel, babban hotel ne na gani na fada sai wane da wane suke kamawa.


Saida akamata security check snn receptionist ya bukaci yaji appoitment dinta, sai ta bashi lamabr room din Ahmed da sunanta, wasu lambobi ya danna a bell phone ya saka a kunnenshi after like 3 min ya kammala magana da Ahmed inda yay confirming isowarta.


Yana sauke wayar a kunnenshi yace mata ta shiga kawai anbar mata kofar dakin a bude..


Godiya tay masa snn ta haura ta lifter yakaita hr floor din da room dinsan yake,tafiya take kirjinta na bugawa har takai bakin kofar dakinsan zuciyarsa bai dena bugawa da sauri da sauri ba.


Harsanda taji ta dan samu nitsuwa snn ta tura kofar ahankli ta shigo cikin hadadden room dinsan wanda ya bala'in gaurayewa da wani irin sanyin qamshin turaren sa mai mugun ratsa gangan jiki,lumshe idanuwanta tay abata jin yadda sanyin a.c dake gauraye da qamshin turaren yake kkrin mamaye jikinta yanamai saukar mata da wani irin kasala.


Ahankli ta bude idon snn ta hangoshi akwance yay shiru kamar marar lpy jikin shi sanye da wani irin hadadden white armless shirt da dark three qtr shot shikuma grey colour.


Qamshin turaren taya jiyo ya juyo yaganta a tsaye alaman mamakin ganinsa ya daskarar da ita sosai ,cikin sanyin murya mai tafe da kyarma tace is that you Doctor? My love is dat u?


wani dadi yaji aransa datace haka suna kara hade ido ta taho da sauri ta taho ta fada jikin shi ta kankame sa wani ajiyan zuciya mai nauyi ya sauke sannan ya kankame ta shima yana shunshunata yana  furta mata i missssss u acikin kunnenta sunfi 10 minute suna juyi cikin shaukin hakan xuciar su tana bugu da tsananin kewar da sukayi wa juna,.


Ahankli ya saketa kallon cikin idanunshi take hade da wata tsiga ta daban tana sake jin wani irin tarin kaunarsa Mara iyaka da misaltuwa 


Ayayin da shikuma ya shagala wajen kallon yanayinta daya canza ta wanku sosai, ganan tsayayyun nonowarta wanda suka cike mata kirji tam suka harbo acikin dan fingilin rigar data saka gashi ta matse duk shape din jikinta na waje, ahankli ya dora hannunshi akan waist dinta yana kare mata kallo sosai,suman kanta dayaji gyara duk yabi bayan ta tayi kyau ji yake kamar mafarki yakeyi dayaganta ahaka.


Itama yanayin surar jikin san kawai take cigaba da kallo me cike da tsantsar haiba da kamala tattare da jarumta domin kallo daya Zaka masa ka tabbatar da hakan.


Take Ta tsinci kanta a matsayin wanda ta mance komi ta shagala acikin shaukin sanin cewa shidin cikakken namiji ne na bugawa ajarida wanda samun irinsu ke da wuya Sannan kuma abin bukata da muradin kowace cikakkiyar Mace me ji da kanta tako ina Ahmd ya hade iya haduwa bashida makusa.


...muryarsa a sarke ya fuxgo magana dakyar abakin sa yace Hey babe, Im so happy ure here, kinsaka naji dadi sosai na gode..


cikin murza hannun shi anata tace no need huhn

Kasan zan iya maka fiye da haka,i misses u alot Dr kasan dai kaine hasken rayuwata ko? Witou u i am soo lost.


Daga nan wani tsiririn kiss ta masa bazata saida ya daburce tace


"I love u soo much.."

"i regret not telling u this befor" ,"Did u love me too?"


Shiru yy Ya rasa mezai ce mata dan baison ya amsa ya mata karya, dan haka Da Wani irin sauri ya hade bakinsu guri daya yana xukota tana murmushi ta masa wani irin tsotsa na fitar hankali  wanda shi ya hanashi kirkiro abinda yake son fada din..


Ganin kamar zatafi shi kwarewa yasa Ahnkli ya cirota ajikinshi ganin yanayinta dabai gane ba 


Wani sororo yayi yana kallonta ido cikin ido suke kallon juna yana Lumshe mata rikitattun idanunshi da suka soma canza kala zuwa wani yanayi na daban ya sake rungumeta gam a kirjinsa kafin daga bisani ya sausauta rungumar dayayi mata ya dan makaleta ajikinsa yana shin shina wuyanta zuwa jikinta tana sauke wani irin numfashi tana kakkama shi can Ya fixgota Jikinsa cike da matsanancin shaukin sha'awarta ya rungumeta tsam tsam a fadadden kirjinsa yana rada mata magana cikin  kunneta 

Yace babe, Can u Spend the nite wth me here?i misss u soo much softy.

..Yakarasa fadar hkn yanamai hura mata iskan bakinsa a fuskarta wanda hakan yake haddasa mata wani irin gagarumin faduwar gaba wani lamoo tayi ajikinshi dan jinsa take yana mata yawo a dukkanin ilahirin sansar jikinta da ruhinta.


Wani irin jarabben kallo ta dago take binsa da shi ayayin da ta dora hannun ta akan kirjin sa tana wani irin shafo sa daga sama zuwa kasa tana mai xiriya, Tuni jikinshi ya mutu yanajin yadda dukan jijiyoyin jikin sa suke amo suna amsar sakonta, kowani jijiyar sa tana mimikewa tare da saukar masa wata muguwar jarababben sha'awar ta wanda kwata kwata baison tay nisa dan ba niyyarsa kenan yay amfani da ita ba dan bai taba zina da wata mace ba saidai suyi shirmen romance dinsu dan shi namiji ne da baison raina kansa.


Duk wani abunda yakeyi anan din is planned, tun ranar abokinshi banji yace masa kwakwalr mata duk daya ne, daga zarar ka taba jikinsu sun dan ji dadi toh shikenan, yace masa inhar yana son yay avoiding apology daga wajenta dolene kawai ya fito mata ahaka ata sigar romance din dats when she will be totally emotional and weak.


Shiyasa ya saki jikinshi yana biye mata suna romancing junan su sosai, yana son ya shagalar da ita dan baison ta samu karfin gwiwar tuhumarsa akan abunda ya mata abaya, 


wani zautaccen yanayi ya shigar da su duka yana sucking din lips dinta kamr his life depend on it, itama ta danna ta hura ta matsa ta masa tsotsan lips dinsa kamr ta sami alawa, kamar wanda ake cire ranta haka ya dawo da ita jikinta ybi ya mutu murus se numfashinta dayake daukewa...


sanda ya kusa sumar da ita sann ya dan mirgina ya tureta ajikinshi ahankli yay maza ya tashi ya zauna abakin gadon dan baison abun nasu ya wuce gona da iri inda bazata iya controlling kanta ba dan shikam yasan ba da gaske yakeyi ba.


Jikinta na rawa sosai ta tashi jin koina ajikinta na matukar begensa,nan da nan ta biyosa zata kamoshi jikinta da wata muguwar shauki ya kara tureta ahankli yanamai cewa babe please stop it..its okay.


Yana furta hakan sai taji ta dawo hayyacinta da kyar, nan Ta mike ta zauna tana wani irin kallonsa kirjinta na tsananta bugawa sosai dan batay tunani mai yawa kafin ta sake mishi kantaba gashi har ma sha'awar ta ya motsa.


Nannauyar ajiyar zuciyace ya kufce mata ganin Ahmed na yunkurin tashi zai wuce toilet yasa ta diro gabanshi ta rikesa jikinta da muryanta na rawa rawa...


A raunane sosai take kallonshi tace why did u stop? 


Idanunshi yy rolling zai bata attitude sai taji ranta ya fara baci a tsawace tace i said why did u stop?,....Doctor Ahmed ina magana pls answear me...ko kazo ne kawai dan ka kara yaudarata ka tafi garinki kamar na wancan lokcin? "Is it another research work?..


Zata kara budan baki azafafe cikin tsareta da mayun idanunshi mai narkarwa ahankli yace "no'...


Hannunta ya riko yanamai jona idanunshi acikin nata yace i come for u Adi...just for you..

Ya manna mata kiss a goshi cikin numfashinsa  yanamai furta cewa im here just for u..believe me.


Jikinta sosai ya mutu jin harya jawota jikinshi ya rungumeta sosai suna daga tsaye..


Take taji brain dinta na disco acikin rudani sosai ta rasa mema zatace masa...


Tana dago kai zata masa magana kenan wayarta yafara ringing ya saketa ahankli taje ta dauko kirjinta na dukan tara tara dataga lambar mahaifiyarta ne.


Daga tsayen yana kallonta yace who is it?

Ko har kinmin rival ne?


Ahankli ta girgiza kai snn tace its my mum..


Girarsa na sama a dage da sigar yaudara yace  "tell her ure spending the night with me"...ko bakiyi kewata bane?..


Batace komi ba tay blushing sosai, dan bai taba sake mata har haka ba saiyau shiyasa duk takejin kanta daban ..


Tasan dai tana daukar wayan nan mamanta zata rufeta ne da masifa so she cant give her any silly excuse..musmmn ma irin wanda yace tace din.


Saidai kuma tana mugun son ta zauna tare da Ahmed since he said he came just for her dan tana da tarin tambayoyin datake so ta masa duba da bai taba cewa yana sonta baki da baki ba.


Aganinta zuwansan kamr wani dama ne na daban yake kkrin bata na nuna masa soyayyar data dade tana masa aranta.


Wayar yana kara ringing akaro na biyu Ahmed ya dan karaso kusa da ita ya zauna yana kallonta jiran ganin mezatayi ..


She just cant resist his charm Duk datasan mahaifyarta zata mata masifa dan haka wayar yana kara ringing sai tay offing dinsa mai gaba ki daya ta sakashi ajaka.


Jikinshi ta dawo ta rungumesa sosai snn tace im all urs, yace good girl..now lets go and play games outside..me kike son kici?...


Kafin nan ta amsa taji ya jawota kasa nan da nan suka dan kimtsa yakaita hotel premisses yayita kashe mata kudi duk abunda take so saiya siya mata, sanda yay make sure tasha wine ta bugu jikinta yy nauyi sann ya kinkimota suka dawo dakin yana dan kwantar da ita akan doguwar kujera ta fara bacci harda minshari.



Wanka ya shiga ya dan kimtsa jikinshi dan already karfe 2 na dare ya buga dare yay sosai daganan ya haura kan gadon shikadansa ya kwanta baijima ba shima bacci mai nauyi ya kwashesa. 

SURAYYAHMS WAHTSAP

08060712446.....*KISHIYAR ƘABILAH... 9*



BY SURAYYAHMS..


THANK U ALL FOR THE WONDERFUL LOVE AND MOTIVATIONS. THE VIBE IS TIMELESS FANMILY!!


Tunda suka kwanta bacci a dakin hotel din sautin gurnanin kwartin Adiaha ne kawai yake tashi, kararshi marar dadi mai sauka kamar na sautin engine markade ya kuma bala'in cika atmosphere na ilahirin dakin wanda yasaka Ahmed yin bacci rabi da rabi sai juyi yakeyi akan gadonsa yana jefa tsakin takaici sabida bai saba ba kuma ya mugun tsanar mace mai karfin gurnanin gwarti.



Washe gari da safe Da kyar Ahmed ya farka a baccin daya kwashe sa da kyar, yana bude ido yaga lkcin har wajajen karfe bakwai saura duk jikinshi a muce sabida gajiya da kuma rashin kwantawa da wuri da jiya baiyi ba. Yana miƙewa zaune baiko kalle inda Adiaha take ba ya sauka akan gadon snn ya wuce bathrum direct ya kunna ruwa yay cikakken wanka snn ya fito ya shimfida prayer mat dinsa yahau yin sallah abunshi. 


Bayan ya idarne ya juya yadan kalleta a nitse ganin Wani irin baccin datakeyi ta wangale cinyoyinta bakin ta a bude ya dafe kanshi ganin da alaman har wani sabuwar minshari ma takeyi dan ko alaman motsawa batasaka ranan yi ba.


Zama yay a nitse yana mai kafe bango da idanunshi da sukayi sanyi cikin tunanin irin yaudararun kalmomin da zai mata na maganan auren nn nasu dashi dan shikansa baison ya kara kwanaki dayawa anan garin ahaka dan baison wani abu mai suna zina ya shiga tsakaninsu tun yanzu..


So yake ta amince ma qudirinshi ayau din nan if dats possible sabida ya samu ya koma Abuja ga mahaifyarsa dan ya duba halin da take ciki, aransa yasan ynzu halama tay fushi dashi sosai, snn kuma yasan zata damu da rashin jin wayarsa a bude na kwana biyun sosai, wani lumshe idonsa yay kirjinsa na bugawa da tsananin damuwa akan hakan dan yasan baiya mata adalci a matsayinshi na danta datafi kauna a duniyarta.


Tunanin mahaifiyarsan sosai ya ciƙe masa zuciyarsa da kwakwalsa wanda shi yake dada hura masa wutar jin tsananin son samun cikar burinsa akn adia cikin gaggawa kodan yay hanzarin komawa ga mahaifiyarsa.


Yana cikin wann tunanin Adiaha ta farka tana mai kiran sunan jesus acikin yanayin gigin barci da kuma bankararen miƙa..


Idonta a lumshe Tana yar murmushi ta hau tattaba gefe da gefe koda ma zataji shi Jin kanta akan kujerar itakadai shiyay mugun bata mamaki sai kuma tay tunanin hala ko giyar datasha ne jiya ya jefata awajen sai ta kalli kan gadon taga da alaman kmr shikadai ya kwanta awajen batare da ita ba sai tay shiru dai batace komi ba.


Kallo daya yy mata da gefen idonsa yanamai sauke boyayyar ajiyar zuciya cikin sanyin muryansa mai taushi da dadi sosai yace "hey, u re awake? Da kyar ta bude idonta sosai ta kalle shi cikin gigin baccin sosai tace "gud morning babe".


Ya kyabe bakinsa yace 

"Yan mata kenan, kin shayu dayawa jiya fa..are u sure bazaki kara komawa baccin nan kidan huta ba kuwa?.. ba acikin hayyacinta sosai ba ta gyada mai kai da can har zata koma ta kwanta sai hannunta ya danna kan wayarta by mistake sai ya kunnu dakanshi sai zutt zuuttt vibrations na shigowar sakonnin ya firgitar da ita.


Lokci guda taji gigin baccin ya watse ta mike zaune tanamai tunowa da cewa mahaifyarta ta nemeta jiya da daddare bata daga ba.


Bude wayar tay da pin taga 15 text messages atake taji zuciyarta ya tsinke rigip,saidai duk ba wann ne yafi damunta ba tana kallon yadda lkci ya tafi saida taji gabanta ya dada tsinkewa, tay kamr a mafarki taga wai har karfe bakwai da rabi ya wuce harma ana neman 8 saura, dafe kirjinta da yake bugawa kamar zai fito ya fado kasa ya tarwaste tay, nan da nan ta hau saka kayanta ajikinta agaggauce.


Yanayin yadda ta daka tsalle ta sauko kasa daga kan kujerar tanamai saka takalminta zata bar dakin agaggauce yasaka Ahmed ya miƙe tsaye yanabinta da kallon mamaki..


Takai hannu zata dau jakarta kenan ya amshe jakar ya rike yana kallon idonta yanamai binta da wani yaudararren harara, fuskansa ba asake ba yace "wait, wai ina zakije haka kike sauri tun bamu gama gaisawa ba and u knw i wnt to talk u about sumting ryt?bana ce miki wajenki nazo ba?


Ahankli Ta lumshe ido ahankli snn tace yes i knw, im sorry doctor i have to rush home, my mumy..tun bata karasa ba ya wani harde ransa ya miƙa mata jakarta a fusace ya dangwala mata ahannun ta yace "just take ur bag,ya isa haka i dont want to hear it".. 


yadda yay maganan da wani irin arrogant and dissapointing attitude yasa jikinta yay mugun sanyi sai kuma taji wani iri sosai...


Ajiyar zuciya mai nauyi ta sauƙe snn ta matso kusa dashi zata rungumosa ta fara lallaba shi nn ya tsime ya dan tureta ajikinshi ya matsa gefe ayanayin fushi.


Binshi tay cikin lagwame masa wuya da saukar ta kuma muryanta kasa kasa, Muryanta kmr na wanda zatai masa kuka tace "doc Ahmed pls now, karkay fushi mana kayi hkri, i was just carried away, ina sone na isa gida cikin gaggawa yanzu..my mum is angry with me am sure, wai jiya baka na kalla ta kikkirani awaya ba?im sure she is mad at me..dats why i hv to rush home now 


Yy rolling idanunshi yana mata wni irin kallo da daurarren fuska, murya ciki ciki yace "toh shikenan, jeki mana. Nagode da kika nuna min cewa fushin mamakin yafi fushin nawa maman.

..did U knw dat my mum is also not happy with me dat i left her just to come over here and see you.? fushin mum dinki is more importnt than mine ko? Wowwww, Okay thnks..nima bari na koma Abuja wajen mahaifyta kawai.


Yana fadin hakan sai kuma taji gabaki daya ta rude musmmn ma dataga harya isa gaban wardrobe yana kkrin jawo trolly dinshi jikinta har na rawa ta rikoshi ajikiinta tafara bashi hkri with all her might sai shan qamshi da basar da ita yakeyi ya harde ransa sosai yanamai dada daga mata hanklinta sosai.


Lallamin duniyan nan tay masa amma duk ya basar ta rasa meke mata dadi gashi tana cikin matsatsin sauri, karfe shida da rabi na safyar yau din yakamata za'a shiryata dan karfe bakwai ne suitor dinta zai zo gashi har karfe takwas ya wuce bata ma je gidan ba tana nan tana fama da rokon ahmed daya mugun bata ransa.


He alwys love taking advantage of her weakness na mugun son shi datakeyi shiyasa ya zamo soo comfortable wajen aikata mata duk wani abunda yaga dama dan yasan dolene zata bishi snn ta lallameshi.


Saida tay kmr zata masa kuka kafin nan Da kyar ya kyaleta ta wuce gida tare da masa alkwarin zasu hadu awajen next event suyi magana anjima da yamma.


Tafiyarta keda wuya ya kimtsa kansa ya fita yaje yaci abinci ya koshi snn ya samu wajen shan iska mai sanyi inda babu wani hayaniyan surutu ya kira abokinsa oyebanji suka fara shirya maganan da zaije ya gayawa brother hamzat dimeji a office ayau game da zancen auren ahmd da adiaha.


Ahmed yana son lallai yayanshi hamzat dimeji shine zai shige masa gaba akan auren nan dan yasan da wuyane ya shawo kan mahaifinsa acikin sauki musmmn ma da ba kafayat din tasu zai aura ba.



A fannin hajya khadijatu kuwa yau haka ta kwana tana kuka bata samu wani runtsawa ba sabida bakincikin marinta da mijinta yyi. Tunanin duniyan nan tay amma bata samu wani mafita ba. Duk danta Ahmed ya gama daureta da jijiyan jikinta, aynzu dai tasan babu ta inda zata iya bullo ma mijinta ya fahimceta cikin sauki musmmn ma data lura da cewa kamr zugin da su anty moju suka masa wnn karon yay mummunan tasiri a brain dinshi.


Ranta a mugun bace yake da danta Ahmed danta nemesa a waya sau babu adadi amma kirar baije ba, dacan har taci alwashi bazata kara nemansa ba,aranta tace ko ya dawo ma bazata kulashi ba, amma wani bangaren zcyarta kuma acike yake da damuwar son tasan inda Ahmed din yake takuma ji lpyarsa.


Da kyar tay sallah tay wanka snn ta dan samu nitsuwa ajikinta, coffe kawai tasha tana zaune saita soma tunowa da shawarwarin da mahafiyarsu take yawan basu tun dacan kafin Allah ya amshi ranta na cewa idan ransu ya baci kar su sake su bari hanklinsu yana gushewa.


Dacan taso ta fita aharkan mijinta kodan ya wahala ya gane kuskusren dayay na marinta akan maganan da baizamo gaskiya ba.


Daga baya kuma sai taga kmr sharesa da yin shirun shine zai iya sakawa munafukai irinsu anty moju su karacin galaba akan aurenta da salon makircnsu.


Zama tay tana tunanin yadda zata bullowa sha'anin mijinta da yan uwansa. Tasan dai kishinta sukeyi tuntuni.


Amma batay tsammanin zasu riƙe abun har sukaishi wann matsayin ba. She have lived with them for more than 30 yrs, amma sai taga kamr kullum kabilancinsu sai dada huruwa yakeyi akanta.


Tashi tay ta shirya cikin wata milk colour lace mai ratsin fararen duwatsu masu kyalli ta gyara fuskarta yay kyau ta fito rass kamr ba itace take cikin damuwa jiyan sosai ba. Yadda ta fito cikin gidan ta tanamai zuba qamshin turarruka masu tsananin qamshi iri kala kala zaka rantse babu wani abinda yake damunta aranta bacin damuwar danta Ahmed ma kawai ya isheta taciki shikadai..


Falon mijinta ta dosa kai tsaye inda qamshin turarenta ya soma musu sallama kafin nanma ta iso, a cikin takunta na nitsuwa ta shugo ciki bakinta dauke da sallama fuskarta ba awani sake ba ganin har sun farka suna shan shayi atare. Ido ya zuba mata azauce ganin yadda tay kyau sosai tana zuba uban qamshi masu tsananin dadi.


Nn kafayat dake sanye da nite gown riga da wando tay saurin rusunawa tafara gaisheta,a cikin sakin fuska hjy khadjatu ra amsa mata tanamai tambayarta ya jikinta yake.


Har suka kammala gaisuwarsu baice mata uffab ba, Shiru yay yana jinsu dan bai sauko daga fushin dayake kanyi da ita ba msm ma na marin anty moju da akace anyi danshine yafi komi cin masa rai danji yake kmr mahafyarsa aka mara.


Ta juya ta kallesa ba yabo ba fallasa ta gaishe sa ya amsa da sakin fuska badon ya so ba saidan kyan datayi, snn tace "Alhaj ina son magana dakai..tun kan ya amsa kafayat ta miƙe respectfully zata fice ta basu waje, muryansa ciki ciki yace mata my doter ki dawo ki zauna..im enjoying ur company.


"Jiki a sanyaye kafayat din ta koma ta zauna sai kuma tay saurin maida hnkli izuwa kallon tv, hjy khadija sai kallonsa take tana kan shan mamkin sauyawarsa akanta.


kyabe bakinta tay batace mishi uffan ba ya daga ido ya kalleta sama sama snn yace iya dami, ure joking with me ryt? Nagaya miki bazan tsaya yin wani bayani dake ba hatta saikin umarce danki Ahmed ya dawo gidan nan..cikin dagon murya yace "im tired of all this nonsense, tunda kece kika daure masa gindi ya gudu just comand him to come back here and face me like a man, ai makanku kuka rainawa hankli bani ba..


Da kyar ta shanye maganan snn tace alhaj Amma nagaya maka ban san inda Ahmed yaje ba..kuma sakon daya turo kowa yaji shi..how isit my fault?


Hararata yy snn Yace "wani sako?Ahmed ya turo sako ne?.. Zatay magana cikin katseta yace "ohhhh ohh, wato har Kin taho min da wani salon sabuwar makricin yau kuma ko? See erhnn ki bace min anan wajen _oya jade.._ duk sanda danki ya dawo kika kawomin shinan zan saurareki..


Shiru tay nadan wani lokci tanamai sassaita zuciyarta ta ciki, duk ba dan Ahmed  ne ya jawo mata wann walakncin ba tasan da wallh ba'a isa ayi mata hakan asha ba,  aranta tace amma ai bakomi akwai ranar kin dillanci, daga nan Batace uffan ba ta juya jikinta a sanyaye zata  bar wajen kenan sai ga sautin live broadcaster daga can calabar international trade fair center. Kafayat ne ta fara hango Ahmed agaba tare da sauran likitoci adan gaggauce ta wara idonta snn tace "Dady Watch!!! Isnt dat dami?


Kusan a lokci guda iyayen nasa suka maida idonsa kan tv hjy khadj nadaga tsaye kafayat ta dauki remote ta kara sautin tvn.


News report aketayi akan HIV/AIDs confernce/walk din da akayi a calabar jiya Ahmed na gaba gaba dan haka kusan dashi jounarlist din yay hira yna dan tambyarsa yana amsawa.


Shiru falon ya dauka suka zuba ido suna kallon sa harya kammala magana akan progrm din which is alwys cool nd impressive. Alhaj bello sai yaji wani iri aransa sosai dan duk cikin zugin nan da aka masa babu wanda yace masa dansa ahmed ya turo ma family sako ajiyan bare ma suce masa wani abu na aiki yajeyi awani waje, sude kawai ce masa sukayi uwarsa ta daure masa gindi ya gudu dan karya engaging din kafayat, snn dansa ya kunyarta dasu ya jawo  musu cin mutunci harda mari daga wajen hjy fatihat.


Kafayat kuwa sai bayani taketayi, tace "mammy kin ganshi ashe har can calabar yaje..sounding proud of him tace i knew Ahmed will neva joke with his work i shhud have known dat..


Murmushi kawai hjy khadija ta mayar mata data furta hakan wanda yasata jin nauyin hakan sosai sabida tasan dukansu biyune basu mata adalci. Ahmed ya tafi ya jawo mata abun magana, itama ta daga hanklinta ta jawo mata baqar magana awajen dangin mijinta da mijinta.


Muryanta a sanyaye cikin nadaman zuci tace "Its all my fault for over reacting duk dama ahmed ya tura mana sako ya sanar damu amma na kasa kwantar da hanklina.


Maganan takeyi acikin aranta amma ya fito fili bata sani ba duk suna jinta..


Da ta farayin bayani akan sakon alhaj bello kuma sai ya soma dawowa cikin hayyacin shi, he was like so Ahmed really send them a messge to even apologise for his absence amma toh meyasa basu gaya masa hakan ba? Nan ya juya zai kalli idon matarsa da yanayin sanyin jiki da rudani lokcin kuma hjy khadiya tana tsaye tana kallon danta a tv batace musu uffan ba ta kuma mugun daure fuskarta.


Budan baki yy zai mata magana sai caraf suka hade ido da hajy fatihat adetunji balogun datake kkrim shigowa ciki.


Babu sallama karar taunar cingam dinta ne ya saka dukansu suka maida hankli su kanta.


Hjya khadijatu ta daure fuskarta sosai uffan basuce ma juna ba.


"Excuse me"

Hjy fatihat ta fada tana kada duwaiwaka ta wuce ciki har gaban yarta kafayat data mike tsaye tana kallonta da bacin rai ayanayinta.


Hjy fatihat ta kare musu kallo dukansu snn tay wani shuumin murmushi

Kafin ta budi baki cikin tsareta kafayat tace Stop mumy, What are u doing here?


Kafin ta amsa alhaj bello jimada ya miƙe tsaye cikin harshen yarensu yafara mata magana yanamai ce mata bata da hankline Da Zata shigo musu gida gatsau ba gaisuwa ba komi.



Da harshen yaren itama ta maida masa martani a fusace tana cewa


"How dare u question me When u took my child custody by fire by force?ku kuka haifamin ita ne?Alhaj bello im warning u ooo, ka rike wa'azinka makanka,ni badan nazo duba yata bama mezai kawoni gidan ka? U can rant all u wnt but No matter waht u say kafayat is my child kuma babu wanda ya isa ya hanani duba lpyarta musmmn ma da danka yake wasa da feeling din yata sabida baisan darajar ya mace ba.


Hakan data fada yasaka shima ya maida mata martani akan marin da akace tay wa anty moju.

Ya zaxxageta irin zagin huce takaici innan.


Saidai da mamakinsa wani Dariyar mugunta tayi masa dan Abun ya mugun bata mamaki dataga alaman baisan komi ba sai tafara kallonsa a matsayin wawa soko musammn jin irin zagin dayay mata na cewa bata da respect da tarbiya..


A masife ta dunkula masa baqar magana da yarensu akansu anty moju snn ta yaɓa masa.


Tace duk rashin tarbiyata dai bazan yi karya da tsufan shekaruna ba,so i dint slap her, i just ask what hppen to my doter is dat a crime?..yy shiru baice mata komi ba, tace " toh shikenan tunda sun iya hadamin hada munafrci i promise u next time muka hadu da anty mojushola saina wanka mata mari dagske dan ni ba tsoranku nakeji ba,  Ransa a bace ya tashi zai mata tsawa ta tsaresa.


Masifa da Borin datayi masa awajen ayayin da take warware masa asalin abunda ya faru jiyan yasakashi kara shiga cikin rudani cos abunda take cewan its totally difrnt da abunda su anty moju suka gaggaya masa akan matarsa da dansa.



Hjy fatihat Tana kammala sauke masa buhun masifa ta jawo hannun yarta tace mata suje waje  da niyyar mata magana privately tana yi tana nanata musu cewa zata zame musu kashin kfi a wuya akan batun yarta muddin dansu ya cigaba da walaknta ta.


Duk dahaka bata hkra ba ta dinga jefe masa baqar magana a iska tana tafiya tana cewa ce ai yan uwansan dayake ganin girmansu sune asalin gagaruman munafukan gidan tunda sune suka fara shirya komi snn ta gaya masa yadda suke damun kafayat da waya da fake promises tace zata kaisu court kwanan nan akan yarta,and she wll sue them for emotional damage and mental torture.


Tay ta bambami tana masiifa akan yarda ake juya kan yarta agidan.


Basuji sakat ba harsaida taja kafayat din suka tafi can waje..



Wani Sororo alhaj bello yy jikinshi duk yy sanyi yanajin kanshi yana juyi da magangnun hjy fatihat da kuma abunda yagani a tv dazu...


Tunda aka fara maganan hjy khadijtu ta tsime tay kyamm ta hade rai bata ce musu cikanku ba ta kuma mugun daure fuskarta kamar wacce bata taɓa dariya a duniyan nan ba...


Ganin maganan hjy fatihat ya shigesa ya dawo dashi hayyacin shi yasa hjy khdij taji dadi aranta amma ko nuna hakan batay ayanayinta ba ta kada kai itama ta dubeshi snn ta yaɓa masa baqar magana mai zafi akan marinta dayay jiya, snn taja tsaki ciki ciki ta kama gabanta.


Juyawarsa ke da wuya da niyyar bata hkri su sasanta saiyaga wai harta bar wajen jin karar rufewar kofan ta kawai yay. 


Nan Ya rasa me zaiyi gabaki daya.


Adan gurguje yabiyo bayan matarsan yanamai kiran sunanta waidan ya tambayeta sauran wasu abubuwan tanajinshi amma ko kulashi batay ba bare ta amsashi.



Wucewarsa a kidime yana bibiyar matarsa hjy fatihat da kafayat suka gani lokcin sukuma sun kammala fadarsu kenan harsun shirya kansu.


wani file ne a hannun hjya fatihat datazo dashi tanamai nuna ma yarta kafayat na wani boyayyr kudin mahaifinta data kwaco mata shi a hannun accountant dinshi.


Kafayat naganin kudi ta fara washe baki nan da nan ta canza tafara bin mahafyartan sau da kafa kmr ba ita ba.


Daure fuska hjy fatihat tay tamau tafara mata gori akan yarda take treating dinta agaban mutane witou respect.


Cikin magiya sosai Kafayat tace mummy sorry now. Kinsan fa bacin raine but u know i respect u alot ure the only one i have in my life.


Da harara mai mugun zafi ta tsareta tana cewa "lie lie ooo, i no hear dat one..kafayat, kafayat sau nawa zamuyi haka dake?kedai saidai namiki abu dan Ni na haifeki amma badan halinki ba, kece yau kin tuba kinyi hnkli gobe damilare na dawowa zaki dawo kmr wata shegiya yar iska.. Akan damilare U have calld me a witch,ko jiya ma sanda kika ce min munafuka agaban kowa da kowa kamr banice na haifeki ba,sam baki san darajana ba kwata kwata kafayat kina sani kunya agaban enemies dina 

..bazan ma iya kirga sau nawa kika cemin banida kirki dan kawai ina fada miki gaskya akan damilare ba dat boy is just using u.,me, I only care about ur life amma sam baki gani, Wayene zaiki jininshi ehn? Nina sukuna na haifeki, babu abunda nake so a duniyan nan face rayuwarki yay kyau but ure alwys againts me. 


Kan Kafayat akasa krm wacca taji magana a cikin sigar nadama sosai tace e pele maaa, am sorry mum pls am sorry


Tace "Saboda kinga kudi ba? Kafayat ure just like ur father very deceptive human beings..


Tace aaahhh no maa, badan ina jiran ahmed ya dawo ba da tuni nazo na baki hakri, my consience do judge me anytime i misbehave with u,ure not a witch ma, nasan ke kika haife ni..blive me mum i love u soo much..


Hjy fatihat taja numfashi mai dan nauyi Ayanayin rashin amincewa da zancentan snn ta basar cikin cewa its okay..


Nazo ne zan duba zamanki anan din domin zanyi tafiya for some few days i want to make sure ure fine kafin na wuce

 ..murmushi kafayat tayi ta rungume mahaifyartan tanamai cewa "Dont worry maaa im fine..they are both taking care of me _o seun_ .


cikin kyabe baki matar Tace ehhhn..dats good to hear, Inde akwai wani problem just call me zanzo da gaggawa cos i dont trust dis ppl amfani dake kawai sukeyi..and rember what i said,inhar damilare ya dawo abuja baizo ya yanke decision akan aurenki da shi ba,belive me nine zan dauki nawa matakin akanki and u must obey me.


Kafayat ta gyada mata kai tanacewa hakan ma bazai faru ba, cos his dad is angry with him banajin idan ya daawo zasu barshi yay kwana biyu batare da an daura mana aure ba.. 


Hjya fatihat tay shiru bata amsa taba ganin yadda gulma yake ciccin yartan duk ta kasa tsayawa waje guda..


Harta budi baki zata tambayeta kenan sai tace mum kinsan meya faru agidan nan jiya kuwa? 


Da mamki hjy fatihat tace meyafaru oya gist me..


Gefe da gefe kafayar ta kalla kmr barauniya danta tabbatar da cewa bamai zuwa tawajen sabida ta kwarance a iya zuba zancen gulma.


Nan ta fara warware ma mahafyartan duk abunda ya faru tsakanin alhaj bello da hjya khadijat tiryan tiryan batare tsallake ko digon aya ba.


Murya kasa kasa tanayi tana tsarguwa tace mumy jiya ina barci kawai naji suna musu can u belive it matar nan kishi na takeji? When thy left my room sai nabisu abaya, Har naji tana ce masa wai yen yen inba halin kabila ba wazai kai budurwan dansa a side dinshi da dare kiji fa mamy? Hmmm hehehe..he even slaped her..Allah yaso dai basu ganni ba nayi gudu gudu na koma room dina naje na kwanta nayi kamr ina bacci.


Shiru hjy fatihat tay tana mamaki tana kuma jinta kamar mai nazari akan wasu abubuwan..


Dan dai koda kafayat din bata mata gulman ba alama ya nuna cewa suna rikici tun daga ganin yadda alhaji bello yake bibiyar matarsa dazu yana kwala mata kira tana basar dashi.


Kafadun kafayat din ta dafa tace just stay close to them babu ruwanki acikin fadarsu..kedai idan wani abu ya shafeki dont hesitate to call me okay? Tace yess maaa.

I wish u Safe journey. 


Nan Ta rungumeta kadan sukayi sallama saita juya ta tafi..



*******


A bangaren Adiaha kuwa ba ita da isa gidan su ba sai wajen karfe 9am saura lkcin kowa yanata aikin gabansa, tafiya take kirjinta na tsananta bugawa har ta iso bkin gate din gidansu.


Babban gidane irin family house bungalow compound din nan mai Zagaye da jan gate wanda yadan tsufa amma ba sosai ba ahankli ta tura gate din ta shigo ciki cikin sanda luckly enougg bataga kowa a tsakar gidan ba.


Da Wani irin sauri ta fizgi kanta da gudu zatay sashen su taji an damko kafadunta tana juyi taci karo da jajayen idanun mahaifyarta dayakenan cike da baqar masifa.


Jawota tay waje tsakar gida ta wullata tsakiya dede inda aka jera wasu kujeru na tarban baki.


Kamr adiaha zata saki fitsari ajikinta haka  nan ta tsaya cak tana sose sose gefen kunne tsabar tasan bata da gaskiya.

A mugun masife matar tace "mrs carnival From Where are u coming from? adiaha ta bude baki zatay magana kenan mahaifiyarta ta ta rufe ta da fada ta inda take shiga batanan take fitowa ba.


Tun safe suitor dinta  sukazo da elders karban consent dinta amma basu same ba sabida bata nan, duk iya kkrin boye musu cewa adiahar bata kwana agidan ba duk yaci tura dan saida suka fahimce cewa adiaha kam bata kwana agidansu ba on such an important ocassion..


Hakan bakaramin abun magana da kunya ya zamo ma mahafiyarta da sauran kawunan ta da sukazo karban bakin ba sabida rashin zuwan ta wajen kadai zai saka a dinga kallon familynsu a matsayin wanda basu da cultural values.


Sosai Adiaha tasha masifa amma batace komi ba saidai ta basu hakri..


Duk sun dauka taje irin yawon nan nasu na matasa ne inda suke zuwa sudan sha giya su kwana da maza..


Ita kanta mahaifyartata a matse take Adiaha tay tay aure sabida duk sanda taje tay cikin shege dakyar cikin yake fita ajikinta sabida jininta yana da mugun karfi....


A gidansu Ahmed kuwa tsakanin hjy kahdijatu da alhaj bello jimada haka akay ta drama agidan yau dan sosai tay fushi itama tafara jan masa aji saidai ita acikin sauki take nata ramokan bata fada amma cikin ruwan sanyi take ramawa haka sam taki ta saurare shi musmmn ma dataga ya fahimce gaskiyan yasan cewa babu hnnunta acikin tafyar da ahmed yay, tunda safe yake ziriya a sashenta yanata son ta zauna ya bata hkri ya lallameta amma haki fir taki. Duk sai yaji bai kyauta mata ba.


Tanajinshi ya harzuka ya kira anty ramotou dake itace take kasa dashi ya titsiyeta snn ya bata rai ya zazzageta yay mata warning akan gulman da suka kawo masa wrongfully akan matarsa.


Duk wani abunda akeyi kafayat tana tare da shi tanajinsu itadai bata cewa kowa komi sai ido sai ciye ciyen abinci dake yanzu sosai hanklinta ya dan dawo jikinta data gane cewa Ahmed yana calabar duk ta dauka aikine yakaishi can.


Wajajen karfe biyu na rana Banji yaje ya same brother hamzat dimeji a office dinsa cikin nitsuwa sukayi magana akan batun Ahmed kafin nan ya kirashi awajen suka kara tattaunawa.


Da kyar ma brother hamzat din ya fahimce shi akan batun auren amma still dai ya bashi cikakken goyon baya yace masa duk abunda macen dayagani yake so a duniya shi yana tare dashi.


Sunyi akan indan har Adiahar zata aureshi kuma iyayenta sun amince zai kirashi ya sanar masa, snn shi saiya fadawa babban yayansu dake kasar waje wato brother kasim aremu sai su san yadda zasu bullowa maganan kafin sukaiwa mahaifinsu for approval.


Sosai Ahmed ya ji dadin yadda brther hamzat ya fahimce shi snn bashi cikakken goyon baya, abunda ya rage masa ayanzu shine kawai ya samu yardan Adiaha dana iyayenta snn ya nemeshin kmr yadda yace masa


2:30 na rana za'ayi hidiman festival dinsu nayau wanda shima a filin kasuwa ne za'a gabatar, toh daga wnn ranar sai ranar karshe na fitowar spirits na ekpo wanda shine rana na karshe kuma ranar da ake saka ran saka ranar auren yan mata dayawa wanda suka dan girma suka wuce 25yr kamr irinsu adiaha.


Tsabar takaici da fushin abunda tay musu yau yasaka ko magana ta fatar baki mahafyarta bata son yi mata agidan sabida kaf yan matan da ake jiran suitors dinsu suzo da safe kowa taga nata suitorn dn harma sun zaɓa, yarsu adiaha ce kawai batanan batama gana da nata suitor din bama bare ta zabeshi a matsayin tsayayye.


Abun haryana son ya dawo wani abun gori wa mahaifyarta mrs grace udofia.


Uncles dinta kuwa banda masifeta babu abunda sukeyi. Wucewa goma in zatayi sai sun mata tuni sau dari na cewa itace kadai ta rage musu su aurar a danginsu kuma dataki dataso sai an aurar da ita wnn karon sabida kowa ma ya huta


Ko ajikinta maganan nasu bai wani dameta sabida tunanin yadda suka rabu da ahmed dayake mind dinta, sun rabu yana fushi fushi hakan shi kawai ta sako agaba, Allah Allah take lokci yay taje ta same sa awajen festival suyi maganan dayace yanason suyi dan ta kagu taji menene zai gaya mata.


A tunaninta tagama sakawa aranta cewa zai ce mata yana sonta ne dan tun da taganshi sai taji duk wani sha'awar yin aure agarinsun ya fice mata aranta gabaki daya she just want to be with ahmed right now koda ma ba auranta zaiyi ba.


Karfe biyu daidai filin taron traditional music festival din ya cika da tsala tsalan yan mata dake musical ceremony ne kida, da raye raye da wakokin yararukkan garin daban daban ya cike koina anata rawa masu daukar hankli.


Tsala tsalan Yan matan kyawawa masu jini ajika sun sako wani hadadden colourful Traditional attires dinsu wanda sukan daura zani ne snn su saka white shirt sai su kara dora wani colourful wrapper akan waist dinsu.


Wuyansu kuma sukan saka abun wuya ne mai suna okpomokpom da beautiful beaded shoes da hula shima da akayi shi da colourful beads.


Rawa mai kyau sukeyi ayayin da suke tahowa filin wajen dan kuwa bakaramin kyau yay ba sabida high theme na difrnt colourful cultural displays daga yaruka daban daban dasuke ta tururuwan tahowa.


Hankli kwance Adiaha ta saka one of best cultural  attires, multi color wrper ne mai wani irin azaban kyau da dauke ido kowa sai sha'awarta yakeyi aransa maza da mata.


Yau kwalliyarta ma na daban ne, dan sosai tay kyau daga kaganta zaka san wa wani na musamman tay wann adon.


She look like a queen kowa sai son hada hanya da ita yakei, koda ta fito filin rawa tana rawa tare da sauran yammata acikin kwarewa lkci guda potential suitors dinta suka rude wanda aka zaɓar matan kuwa nan da na  ya fara tunanin sake komawa gidansun da yamma domin asake yin sabuwar consent taking tunda dazu ba asameta agida ba.



Duk kwalliyarta da fara'arta yau tanayi ne domin aranta tanajin cewa hala Ahmed zaice mata yana sonta. She just cant wait ya furta mata hakan Dan sosai tay makanta alkwarin bashi dukkan zucyarta da imaninta inhar zai kasance nata.



Ahmed yana hotel yana kammala wasu yan ayyukansa a computer yanata kallon kirarta a wayarsa baiko kula ba dan yau bayason yaje wajen sun da wuri yafison daga yaje ya samu attention dinta zai gaya mata abunda ya kawoshi cos he cant keep wasting his time here hanklinshi gabaki daya yakoma gida.



Tun karfe biyu aka soma taron har wajajen karfe 3.30 ahmed baizo ba duk sai hanklinta ya soma tashi tafara dube dube amma bata gansa ba.


Dacan harta cire ranta tay fushi ta koma can gefe tanata rubuta masa tex messg har ana daf za'a fara shirin rufe taron sai gashi nan ya taho.


Sanye yake da wani irin red t shirt mai tsada  da kuma bakin wando ya saka sneakers data mugun dacewa da kayan sai ya rufe fuskarsa da facing cap da hadadden clean eye glasses mai dan fadi. Fadin irin kyan da simple dressing din yay masa ba a magana dan duk inda ya ratsa sai anyi yuuu ana kallonsa.


Bata ganshi ba harsaida ya taho daf kusa data inda take snn ta taso tana dube dube har saida taga babu wani mai kallonta sann ta wuce wajensa da gudu taje ta rungumesa sosai tanamai jin tsananin dadi da sabuwar kaunarsaa dake neman mata yawa aranta.

 

Dressing din datay yay mata kyau shiya saukaka masa wajen fidda zancen sa acikin hikima ta inda yasan bazai zurfafa maganan soyayya tsakaninsu ba.


 Sai ya tsaya kawai akan yaba kyaun datayi baije da nisa ba.


Wani irin yaba kyaun datayin yakeyi acikin raha mai kama da gaske yana ce mata tafi dukkan yan matan garinsu kyau da iya wanka shiyasa yake kulata sosai..


Tunda adiaha take arayuwarta namiji irinsa kyakkwan mai aji mai kudi kmr ahmed bai taba kodata kamar na yau ba...


Wani iri nadaban tadinga ji aranta tana jin sonshi na cizonta a kwakaltrta.


Itakam ta furta masa tana sonshi alokcin yafi sau goma amma bai iya amsata koda sau daya ba saidai ya wayance da wani zance na daban daya shafi na yabon surar jikinta ko kwallyarta.


Tsakaninta da Allah take sonshi har ranta shikuwa sauri kawai yake ya cika burinsa akanta ya samu ya koma gidansu akan lokci.


Gefe suka koma inda bamai ganinsu ya mannata akan kirjinsa yanadan shafata suna shan hirar soyayyarsu kamar na dagaske, Saida ya tabbata ya zurma zucyarta sosai da yaudararrun kalamai masu kama zucya snn ya fara gaya mata abunda ya kawosa garin nasu.


Bawani boye boye yace mata "indai harta tabbata tana sonshi, shi yana sone ya aureta. Suyi aure kawai tabishi garinsu a matsayin matarsa.


Da can adiaha ta dauka giyar soyayyace ta debe sa ya furta mata wnn maganan bata yarda ba harsaida ya fidda zoben gold mai kyau acikin aljihunsu ya tambayeta ko zata aureshi.


Tunda taga wai dagske yake jikinta ya mutu dan har wani Suman tsaye tayi nan hawaye suka fara sauka daga cikin idanuwanta jin kamar mafarki takeyi amma ba gaske ba.


She tried her best to wake up daga mafarkin amma ta kasa, saida ya saka mata zoben a ytsarta snn ta dawo hayayyacinta ta rungume sa tana kukan murna sunfi minti 10 ahaka manne da jikin juna.


Gabaki daya ta rasa amsar da zata bashi sabida rudewar datayi


Tafi kowa sanin kalar jan aji da iya walakancin ahmed sai yau rana daya kwasam yazo yace mata zai aureta ai abun daban mamaki kwarai dagaske

Dan duk a burinta data saka akanshi bata taɓa kawowa dacewa hakan zai taba iya fitowa daga bakinsa ba.



Jikinta har rawa yake taciki Hawayenta ya ki tsayawa sai kallon zoben takeyi jin kmr haryanzu a wani duniyan take.


Ganin ta shiga shock dayawa yasaka yace mata taje tay tunani akai xuwa gobe, shi kam a shirye yake zai aureta amma inta amince, snn yace mata zai iya jurar duk wani abunda hakan zai jawo muddin dai zata aureshi shikoyanzu ne zai iya auranta, snn basai ta canja addininta ba, indai bata so is fine with him..he just want her to marry him and dats all. 


Yau dukkan wani kalamai da Ahmed ya furta mata bakaramin narkan da zuciyarta yay ba..


Tana son ta amsashi  snn tay masa bayanin halin da ake ciki da yadda rikicin familynta yake amma ina lokaci ya riga ya kure musu yamma yafarayi snn itakanta tasan batada nitsuwar da zata iya gaya masa wani abu mai muhimmanci ayanzu.


She is just overwhelmed har suka rabu bata dena share hawayen murna ba gashi ya bata kudi har dubu hamsin kyauta.


Wajajen  karfe shida ta dawo gidansu tazo ta samu an gama shiri ita kawai ake jira tazo taga suitor dinta ta amsa ma elders tana sonshi sai akai maganan aurensu wajen ekpo sprits gobe asamusu rana.


Duk wani abubuwan daya dace na al'aada suitor din nan nata ya kawo dake daga gidan sarauta yake bakaramin bajinta sukayi ba.


Kawayenta dayan uwa duk an taru ana jiranta tazo ta badaa consennt dinta agaban elders by offering her suitor a cup of pure palm wine and share of kolanut to the elders and few visitors.


Sharp sharp akaje aka shiryata aka saka mata typical igbo dress wani white blouse da double wrpper da head.


Cousin sis dinta Ekaete da wasu kawayenta sune agewaye da ita sai iyayen ta abaya har aka kawota cikin fili..


Rawa ake ana waka ana murna yau adiaha is finally going to make a decison once nd for all 


Saidai tunda ta shigo filin basu gane mata ba dan babu abunda ke yawo a kwakwlarta face maganganun ahmed na zancen aurensu..


Binsu a filin takey kawai amma haklinta baya jikinta sam dan Bataji bata gani muryansa ne kawai yake mata yawo acikin zuciyarta bana wasa ba.....


Kawayenta ne suka rakata ta rabawa elders kolanut kowa ya dauka yana saka mata albarka.


Bayan nan aka rakota har gaban suitor din tare da cup of fresh palm wine akace tay kneeling akasa ta miƙa masa inya karba yasha toh shikenan saidai gobe ajira jin ranar bikin aurensu daga bakin chief priest.


Har adiaha tay kneeling kasa Maganganun Ahmed bai dena yawo a kwakwarta ba, rawa rawa hannunta da jikinta yafarayi ta soma jin wani irin kasala da jiri jiri.


Kowa jira yake yaga ta miƙa cup din tana kuwa dagawa ta kwara shi akasa...nan kowa ya miƙe tsaye cikin mamaki.


Ganin duk an mike ana kallon abunda tay yasa ta yaye rufin kanta ta watsar akasa ta fice a filin da gudu bata tsaya ko ina ba sai cikin jeji tana huci tana furta cewa bazata iya auran wani namiji a duniyan nan inba Doctor Ahmed ba..Surayyahms chat *08060712446*

*Wanda ba su yi saving number ta ba su yi sai su mini magana ni ma zan saving ta su* 👍🏻

Reply with "saved" is enough😍*KISHIYAR ƘABILAH...10*



BY SURAYYAHMS.



Saida Adiaha tay nisa sann ta tsaya da gudun datakeyi ajikin jejin tanayi tana dan juyawa baya tana sauke haki.


Mannuwa tay da jikin wani katoton mahagony tree mai wani irin tsayi da duhu idanuwanta a lumshe hannunta dafe da kirjinta tanamai sakin wani irin zazzafan huci..


Wani abu takeji ajikinta na mata yawo zurrrrrrrr tare da sunan Ahmed dake mata amo mai ruri acikin kololuwar zcyarta da kwakwalwar kanta tanajin wani iri irin sassakewar jiki tamkar wanda sihirin soyayya mai karfi ke fuxgarta akanshi wanda bata san daga ina yake fitowa ba.


"Ji take kamar bazata ma iya rayuwa a duniyan nan in batare da Doctor Ahmed bello jimada ba"..


Wani irin bugawa zucyrta yakeyi akansa, kirjinta na sama da kasa cikin hucin tsoron mai tafe da tashin hankli na rashin sanin me zatayi da rayuwarta aynxu.


Kara lumshe idanunwanta tayi tabi tay tsamm ajikin bishiyar jin har an biyota ana kwala mata kira acikin jejin acikin tashin hankli da alaman kowa yafito ne anata nemanta.


ADIAHA...ADIAHA..ADI?

Muryan kawunanta mr akpan da mr udo da na kawayenta duk ya cika koina ajejin,jin muryan

sun a kusa kusa yasa ta sake ballewa aguje ta kara shigewa can cikin jejin taje ta buya akan wani boyayyen tsaunin ciyawa inda tasan ba lallaine suyi tsammanin ta awajen ba.


Banda kuka mai sanyi babu abunda takeyi, ahankli tay ta rakube harta haura can saman tsaunin ta zauna ata inda ba wanda zaiji motsinta koya san tana cikin jejin gabaki daya.


Haka har aka karace nemanta aka dawo gida ba aganta ba. Wani tashin hanklin da ba'a saka masa lokci shiya shiga wanzuwa tsakanin kawunanta, mahaifyarta da kuma bakin da sukazo neman aurenta.


A Daren ranan saida ran kowa ya bala'in baci akan abunda tayi.


Mutane dayawa sunyi Allah wadarar da ita snn babu kalar tsinuwa da ba'a yi akan rashin isashen tarbiya da dattakon gidan nasu da ake cemasa gidan mr bassey ba.


Guduwan da Adiaha tayi saida yazamo wani babban taɓo agare su, harga shi kansa yaron da ake son ahadata dashi, iyakan abunda tay masa ayau kadai ya isa ya zamo masa abun gulma, snn duk inda ya shiga neman aure za'a nunashi ace shine wanda budurwa takishi snn ta gudu masa awajen consent taking dinsu.


Sum ppl now will start seeing him as a cursed ko wanda yake da bakin jini acikin al'umma...


Taruwar dangi elders din yankin sukayi akan familynsu adiaha kowa na fadar albarkaciin bakinsa Musammn ma dayake bayau aka fara samun babban abun kunya acikin wann familyn nasu ba.


Bayan kura ya dan lafa kowa ya watse bakin ciki mai tsanani shine ya rufe fuskokin mrs grace tare da uncles din adiaha wato uncle akpan da uncle udo.


Uncle akpan shine yake bin mahaifinta,shikuma uncle udo twin brother mahaifinta ne sune manyan yaƴa acikin mahafiyarsu mrs chidara

Wanda ahalin yanzu bata tare da su sabida musuluntar dataje tay aure a garin adamawa.


Har wajajen karfe 9 na dare adiaha na zaune ajeji tanamai tunanin rayuwarta wanda yake da yawan rikici da rudani mai yawa aciki.


kokri take ta raba gardama tsakanin soyayyar datakeyi wa familynta da kuma wanda takeyi ma rayuwarta ayanzu.


Dan tabbas idan ta zabi tay rayuwarta yadda take so toh komi zai lalace musu tsakaninta da familynta dan tasan babu abunda zai iya hanata musulunta domin ta aure babban muradin zuciyarta wato dr Ahmed.


 

Idan kuma ta zaɓi ta hakura da soyayyr Ahmed dan familynta tasan hakan zai kawo martaba wa iyayenta da familynta nata saidai ahalin yanzu batajin aranta kmr zata iyayin rayuwa agidan wani da namiji inba doc Ahmed ba.


This war is btwen her heart desire and her family, abun na damunta sosai dan acikin su duk wanda ta zaɓa dolene tay asara mai girma.


Idan har ta zabi ahmed dolene ta rasa wani babban gurbi acikin zuciyan iyayenta da zuriarta gabaki daya kamar yadda kakarsu mrs chidara ta fuskance tsana, da kyamata snn ta zama tsinanniya a zuriarsu gabaki daya data aure northenr kuma musulmi acan garin adamawa.


Idan kuma ta zabi familyn ta bar soyayyar doctor Ahmed to tabbas tamkar mutuwarta ta zaba dan batajin zata so wani namiji kamr yadda take sonshi. He is evry woman dream, komi na rayuwarshi is perfect to her, kominsa gwanin ban sha'awa ne asaninta doc ahmed baida wani aibu a idanunta haryanzu.


Tay iya tunanin duniyan nan amma at the end kanta kawai take zaba, saidai abu mai matukar wuyane agareta ta yanek hukuncin raba kanta da zuriarta da mahaifiyata kai tsaye shiyasa banda kuka babu wani abunda yake sakata jin dadi aynzu..


Dadin karawa da tasan dukkan wani abunda yake tafe da wanda yake wakana acikin familynsu na auren wani kabila, kabilanma ace moslem.


gaskiyan shine tasaa  iyayentq bazasu taba amincewa ta auri wanda ba yarensu ba and worst part ma wai bayarben musulmi.


saidai komi arayuwa lamarine na nuna sonkai da son zuciya shiyasa kowa da yadda yake daukar rayuwarsa


.tadai tasaka aranta cewa Ahmed din kawai zata zaba amma har yanzu bata kammala amincewa da wann tunanin acikin kwakwalrta ba tukuna.


Rabuwa da familynta na har abada wani Babban lamari ne wanda yake da ciwo matuka..


Tana cikin wann yanayin taji an dafata, a firgit ta daga kanta sama suka hade ido da babban kawarta kuma causin sister ta dinta ekaete.


Tana ganin itace ta firgita ta Rungume ta sosai tana sauke sheshhekar kukanta ahankli ajikinta duk sai ekaete ta dada shiga cikin rudani.


Rarrashinta ta kawai ta farayi batare da tasan asalin cikakken matsalar tata ba, har sai can da Adiaha ta dan samu nitsuwa snn Ekaete ta riko hannunta cikin taushin murya snn tace "Sister Adi, meya faru, why did u run away from ur consent taking moment? Kinsan kuwa irin bala'in da hakan  jawo ma family?pls Why must u do this to us? 

menene ke damunki..tun ranan na fada maki u are behaving weird, nagane  kamar baki cikin hayyacinki pls wats wrong with u can talk to me now,..jin Adiaha tay shuru yasa ta dada rikota Cikin lallami sosai tace "ko bakison auren ne?

Are u spritually bound by the spirit??Ko kinyi blood oath da wani ne if not why are u rejecting ur own marriage proposal while ure not getting any younger?


Da kyar Adiaha ta dago ta kalleta da jajayen idanunta da suka kara cikowa da hawaye snn tace" listen Ekaete,nifa inada wani matsala mai girma kuma bana jin zaki iya fahimta ta aynzu.


Hannunta ekaete ta dada rikowa snn tace "just say it" inajinki, kinsan i will alwys support u.


hawayen data suka taru acikin idanunta ne suka sauko zurrrrr snn tace "babban matsalata shine ina mutuwar son shi, i love him soo much  i feel like i cant even breath witout him"..


..Da mugun mamaki ekaete tace and who is dat?...i dont get u..


Tsaye Adiaha ta mike ahankli snn ta juya mata baya tana zubda hawaye masu sanyi sosai, cikin dauriya ta soma fada mata labarin yadda ta hadu da dr Ahmed har izuwa abunda suke ciki ayanzu.


Tun kan ta kammala Ekaete ta miƙe tsaye tana kallonta babu shiri dan tabbas ta gane kan labarin tun akan ciwon da adiaha tay daya tafi wancan karon, duk jikin ekaete sai yay la'asar tanajin kamar mafarki takeyi ba gaske ba.


Adiaha na hawaye masu sanyi ta cigaba da cewa "ekaete yace min na aure shi, wai zai tafi dani garinsu, see i love him, i just have to marry him, cos i cant live witout him..


Da wani irin muryan razani ekaate ta taho ta juyo da ita suna fuskantr juna cikin jijjigata a zafafe tace "chimooo, adiaha ,a moslem guy? "A Moslem yorouba, a Moslem u say,..Adiaha kinason ki auri musulumi and a yoruba guy too?chaiiiii , ta rike kanta tana girgiza kan a raunane jin abun adiahan tafadi kamr wani labarin cikin tatsuniya tanamai cewa chaii chaiii _ewoo chi nke, tufi akka machibidoro_ 


Adiaha batace komi ba tay shiru tana kallon can kasa, ekaete ta dada rikota tace _Adiaha pls tell me,i tufuru ya?_ (kin haukace ne) ta kara jijjigata sosai snn tace..amma kinsan me kike cewa kuwa? _ị bú onye ara?_ Are u insane?..


Da karfi adiiaha ta kwace kanta a hannun ekaeten data birkice mata da masifa atsawace snn tace "i am not mad, "ekaete nasani,nasan menace miki mana, i said i want to marry him cos i love him..what is wrong with that..ko bani da iko da rayuwata ne .ni baiwar su ce?see I am not a slave ohh  Inada daman na zabi duk wanda nake so arayuwata snn in aura


Ekaete ta wanka mata mari mai zafi cikin jin tsananin takaicinta hade da wani irin tsananin bakinciki da mamaki jin abunda take cewa...


Tace So you think u know wht ure saying ryt? _ewoooo, Adiaha, ị na-akpọ onwe gị nsogbu_ (ure calling troubling upon urself/kina kiran makanki bala'i) _Iwe nke chi_(wrath of gods upon u/da tsinuwan allolinmu akanki)


Jiki a sanyaye sosai ekaete ta nemi waje ta zauna tana girgiza kai alaman maganan nan ya tabata sosai ta kasa hakuri nan Ta sake kallon Adiaha datake tsaye snn tace ynzu Acikin dukkan mazan dake fadin kasar nigeria baki kalli wanda zaki aura ba sai moslem? Adiah You have really lost it. _Adiaha nke ụmụ nwoke niile nọ na nigeria ị hụghị di, ịchọrọ ịlụ onye alakụba?_ i still cnt believe this chaiii..


Ayanayin damuwa sosai adiaha ta taho ta sameta azaunen snn tace pls pls stop discouraging me ekaete. Nazo nan ne dan nayi tunani akan rayuwata badan in nemi shawarar kowa ba, ina son nasan yadda zanyi in fada ma family nane ni gaskiya zan auri doc ahmed since he propose to me kuma nima ina sonshi..



Da karfi Ekaete ta tureta ajikinta azafafe acikin wani irin yanayin takaici mai mugun shakure wuya snn tace "get out my friend ure totally blind, na rantse da Allah kin haukace..Adiaha kina kallon zaki jefa kanki acikin wata masifa da damuwa amma ba soyayya ba. 


Abun na ci ma Ekaete rai tana maganan ta fara kuka mai zafi tana cewa nasha mamakinki adi narasa ke wacce irin yarinya ce, ace Mutimin daya walakanta ki yay treating dinki like a donkey while u worship him, snn ya tafi ya barki kmar zaki mutu da sonshi agadon asibi babu ko sallama ..amma wai daga ya dawo just one night har kinzo kina cewa zaki rabu da kowa naki dan ki aureshi..


please where is ur worth adiaha? Please where is ur worth..ina da darajarki na ya mace yake?


Menene murumin nan yake dashi wanda bazaki samu awajen wasu maza ba. Can u tell me one thing about him thats true and special?..adiaha ko mahaukacine by now yasan kece kikeson mutumin nan amma bashine yake sonki ba but look at u, u just want to secrifice ur family and ur religioun for him, all for what?..


Ido a rufe Adiaha ta mike tsaye jikinta harna rawa tace "All for love, i love him..kinji?And I dont care what u said nidai inason shi kuma shi zan aura..he is my happiness dats all that matters to me..koya walakanta ni ko baiyasona nide  kawai shizan zaba sabida shi zuciyata take so.


Cikin girgiza kai ekaete ta share hawayenta snn tace toh shikenan, zakizo wata rana kice na fada maki cewa ure making a big mistake in ur life since kinzabi ki zamo baiwar zuciyarki..


And Rember dis oo,a woman dat chooses to honour her heart desire will suffer, she wll have no self worth, no self respect and dats what u are getting from him adiaha.


Tace eh din, naji, kije kita kishi na, nasan kinajin haushina ne dan na samu saurayi doctor kyakkwa mai kudi, see ehnn..idan har ya aureni I will use my love to win his respect and be worth it awajensa cos i have all it takes to lured him tafada tana rausaya hadadden jikinta dayaji komi da komi.


Ekaete ta girgiza kai tace 

"Yarinya Ki tashi a barci, dan ni danayi soyayyr hauka irin taki aigara na sha poison na mutu

,..alredy bakida mutunci ko daraja wajenshi  Allah kadai yasan meyasa ma yazo har garin nan yace miki zai aureki..babu bincike babu komi..and u just accept him, kinsan familynshine? Kinsan ya behvrs dinsu yake? Zasu karbe ki acikin familyn su?..will dat bloody ahmed of a guy also live his family and religion for u? chaiiiii, Adiaha oooo . bantaba ganin jaka irinki ba, mmmm na today i see the height of desperacy in you, toh wani namijine ma zai soki tsakani da Allah ahakan bayan baki san darajan kanki ba.


Rai abace adiaha tace 

"Toh Ya isa haka, Dat Is none of ur business tunda bazaki supporting dina ba..


Nan Ekaete ta miƙe tsaye  tanacewa yes please say it again...i wont support u akan abunda zai cutar da rayuwanki dan haka kinga tafiyata, Inkin ga dama kiyi tunani akan abunda nafada maki inkinga dama kibari tarihi ya memeta kansa akanki...shey u see how ur grand mother ends up?


Tace yes, i saw it. Kije north kiganta she is happier than us. Tana da mijinta, tana da addinin ta, tana kuma da good business and she dont even need anyone


Ekaete tace karya kikeyi, 

She might have evrything amma bazaki taɓa sanin bakinciki da ciwon dake cikin zuciyarta ba ayanzu musmmn inta tuna cewa duka yayanta na cikinta sun tsaneta snn dukkan zuriarta sun juya mata baya.


Adiaha tace oho dai Wann ai damuwarsu ce

Dama menene suke kara ma rayuwarta? Nide i want to be like grand ma..kuma zan shiga moslemi badan Ahmed ba, i have admire them since..they are peaceful they cover and..


Ekaete tace Abeg abeg Shut ur mouth idiot girl...u dont knw them..suma sunayin dukan abunda mukeyi so cut the crap..


Tace eh, Amma ai bakamar namu ba, we do illicit sex and taking bear is almost part of us gashi bama covering kanmu kamrsu.


Ekaete tace Thank god u said part of us, but not path of christianity, dan addinin christa baice ay adultery ko fornication ko shan giya ko atafi tsirara ba, those things are sins too, mother mary also cover and she did not fornicate u rmbr?

..all thos bad things are inventions of our selfs not our religion, ke kije kawai kiyi addininki in zakiyi but stop tryng to find reason againt us.


Adiaha tace naji, zanje.


Ekaete ta karkada kafarta tace gudluck and please count me out of ur way ooo babu ruwana da lamarinki gaskiya.


Adiaha batace komi ba har ekaete ta sauka ta bar wajen sai kuma taji wani irin bakin ciki mai yawa ya mamayeta jikinta a rwgwabe ta sulale kasa ta kara fashewa da wani irin kuka mai tafe da rudani..


Saida tay mai isarta snn ta nitsu ta zauna shiruuu dan tsabar damuwa datake ciki ko yunwa yau bataji ba haka nan takai tsawon lokci tana tunani akan rayuwarta harsaida ta yanke makanta hukuncin auren Ahmed mai kankat.




Ahmed ya kammala yin waya da yayan sa kenan sai yay wanka ya fito waje domin cin abinci, yana isowa nan saiga wata hadaddiyar yarinya irin kyakkywawan yan matan calabar runs girl din nan fara doguwa kamr mami water saidai wann din mai aji ce, tun tahowarsa ta lura da cewa shikadai ne namijin daya zo ta wuce ta amma ko kallo na biyu bai mata awajen ba, tana ganin shi zai zauna itama tazo tayashi zama nan tafara dan janshi cikin hira suna cin abincin a tare.


Tayi sa'a kuwa ya bata fuska sabida alkcin He is feeling quite disturbed sabida rashin sanin halin da mahaifyrsa take ciki yana neman abunda zai dan dauke hanklinshi daga tunanin gida daya addabeshi. 


Hira sukey sama sama amma sosai yagane cewa babe din sha'awar shi takejii dai yanata jajja mata aji baison nuna kamr yagane manufarta aknshi danko sunanta bai gama rikewa ba.


Tana cikin masa hira mai dadi wayarsa tay kara baiko yi excusing dinta ba ya daga wayarsa confidently yanamai katseta unexcused ayanayinsa na tsinannen jan aji da rainin hankli, nan ya saka wayar akunnen shi yafara magana da friend dinsa bankole dayay kwana biyu bai gansa awajen aiki ba.


Da yare suka fara hirar su sam baiyi tsammanin babe din gabanshi tana fahimtar meyake fada ba cos she is a typical calabar girl amma mum dinta yoruba ce,sai tay tsuru tsuru tanata kallonshi jin  yadda yake magana full of i dont care attitude har yana refering dinta da sunanta na karuwa and he even mention dat ko sunanta ma bai kama ba.


Bankole kuwa sai zugashi yake akan cewa ya tafi da ita room dinsa kawai yaje ya kwashe rabonsa ajikinta tun da ita ta kawo masa kanta 


ahmed yanata dariyar karfin hali yanamai ce masa ajinshi yafi karfin yay zina da yar mutunci bare kuma da katuwar karuwa irin wnn babe din.


Yadda suke maganan cikin kadadi da raha bazaka taba tsammanin abunda suke fada ba kenan.


Ahmed yazauna ya kushe mata masu saurin bibiyar maza iya kushewa baisan duk tanajin duk abunda yake cewa



Aganinsa inda shi mace ce da komin muninshi da tsiyarshi wallh bazaibi namiji bare har yana cusa masa kansa..


yace shiyasa sam baiya ganin matan da suke bibiyarshi da daraja sabida aganinsa basu da aji da mutuncin da zai sosu aransa.


Yace daga mace ta fito fili ta nuna tanason shi tun baice yana sonta ba toh tamkar wata shara yake kallonta dan shi yafi daraja mace mai kare kimarta, koda ace tana sonshin ma kardai ta nuna cewa ita yar araha yar sauki ce  dan harga Allah shikam ya tsani  yay wata muamala da duk wani abu mai araha.


Yace koda shi a karuwa ya fito wallh da bazai zubda mutuncin sa yana bibiyar opposite gender karara ba saidai in karyay kasuwa har abada 


Sunata hirar duk ya shagala suna dan toshewa da dariya da abokinsa bankole.


Ganin babe dib ta kafe sa da ido kmr na wance zatay kuka yasa yay mata yar murmushin yake itama ta maida masa da kyar dan sai yanzu tasan da dan rainin hankli take zaune..


Da can har zata ja tsaki ta bar masa wajen sai kuma taga ya katse wayar sai kawai ta wayance ta zauna tana kallonshi.


Tex messges ne suke shigo masa akai kai wanda rabonsa dayaga ana turo masa sako haka tun rabuwarsa da kafayat a Abuja. Tsaki yaja aranshi Yana budewa yaga lambar adiaha ne

Cewar harta zo hotel din wajenshi gata nan tana waje.


Ya daga kai zai kalli ta bakin kofar shigowa kenan sai gatanan harta shigo ciki, wani irin kallon sa takeyi tun daga can nesa ganin datayi masa da kyakkwan budurwa suna zaune sai taji ranta ya sosu sosai bana wasa ba.


Idonta a rufe da tsananin kishinsa ta iso waje tana zuwa ta shiga watsa ma yarinyar wani irin kallon banza shidai yanata kallonsu baice musu uffan ba,nan yarinyar ta miƙe sikinini tana jan tsaki, da har zata bar wajen snn ta juyo ta kalli Ahmed cikin harshen yorubanci tayi masa sallama dan ya san taji duk abunda yace akanta wanda yasakashi kyabe bakinsa sabida mamakinta dayaji.


She looked very annoyed as she left.. aransa yace can miki .


Nan Adiaha ta zauna cikin yanayin fushi da huci snn tace masa Doctor and who is she?

..kuma meyasa tazo nan harkuke cin abinci tare?


Jin yanayin yadda ta fadi magana with anger and comand saiya shareta yay kamr baisan dashi takeyi ba.


Hakan sosai ya kular da ita rai abace tace hey i am asking u?


Cikin basarwa sosai yana danna wayarsa a tsime Yace "repeat ur self "..


Tace nace wancan yarinyar..


Tun bata karasa ba ya hade rai snn ya katseta da cewa Adi bana son yarinta fa, kawai daga na baki ring dazu kinsaka a ytsunki shine har zaki fara rainani ko?


Tace "what? Ahmed mani kake ce ma haka,me kake nufi?. Ya shareta baice mata uffan ba.


Ajiyan zcya ta sauke snn tace see is not just like that..kasan damuwar danake ciki kuwa akanka kake cemin haka? I cant even go home..banda inda zan kwana fa yau.


Bai amsata ba, yay shiru saida ya gama latsa wayarsa snn yace lest go to my room toh sai muyi maganan acan ko?...

08060712446 SURAYYAHMS:*Wanda ba su yi saving number ta ba su yi sai su mini magana ni ma zan saving ta su* Reply with "saved" is enough.👍🏻*KISHIYAR KABILAH..11*



BY SURAYYAHMS.



Kafin Adiaha ta dago kao ta amsashi har yay caraf ya kamo hannunta ya mikar da ita tsaye duk ranta a dagule yake da yanayin yadda yake treating dinta acikin rashin nuna kulawa sosai amma ahakan nan tafara binshi suka haura sama izuwa room dinshi wani babban abun takaicin ma shine baima san tanayi ba.


Harsanda suka kai izuwa dakinsan snn ya sake ta snn ya aje wayarsa akn table yazo ya zauna daf da ita ganin tana hawaye sosai ,habarta ya riko ahankli yanamai kashe mata jikinta da wani irin sassanyar kallo mai sanyi da shiga jiki 


Muryansa mai dadi kasa kasa cikin lallami Yace "babe din doctor why are crying? wai Waya taba min ke ne? kodan kinganni da wata babe dazu muna cin abinci shine kike kuka, nan yay dariya kasar wuyarsa snn yace hmm su kishi manya, look I dont even knw her okay..kawai fa zuwa tay ta zauna awajen abunta,wai ko so kike dama daga tazo sai na koreta tunda hotel din gidan ubana ne? Yafada yana harararta.


Ta turo baki tace amma ai abinci kuke ci tare har tay maka magana da yarenku, and what was she saying ina son nasani?


Ya daga kafadunshi cikin rashin son mata wani dogon bayani dan aganin shi batakai ba, sai yace i dont knw,nima bansan metace ba"..


Tace ba yarenku bane yoruba?


Yace ehhh, amma bance miki komi da komi ne nakeji ba. Kinga baabe mubar wann maganan kawai, wai meya faru ne meyene matsalar taki dakike son gayamin?..ko bazaki fadamin yanzu ba sai munyi wanka?...tun kafin ta amsa shi yajawo ta jikinshi ahnkli ya fara da rungumarta yana dan cukuikiyata tun bata son sake jikinta tay dariya dashi sosai harta fara biye mashi tafara dariyar sosai kamar ba ita ba..


Duk ta dauka bathroom zai dauketa cak suje suyi wankansu tsirara inda zata samu kyakkwan acccess da jikinshi cos she have been dying to touch him kuma tana son yasata taji kanta a matsayin ciiakkiyar mace ayau sabida tana son su samu wann connection din sex din a atsakaninsu she badly wants to feel him acikin jikinta kota halin kakane...


Saidai ta lura da shi sosai tana fara zarcewa sai taga ya tureta koya hade rai yace mata a'a baison hakan, yauma hakanan yay mata wayo ya jata sukaje swimming pool awaje, jikinshi sanye da guntun wando da singlet ita kuma tasaka swim suits sukayi ta wasan throw and catch da wani ball na tsawon lokaci acikin ruwan tare da wasu tsirarrun mutane aciki..


It was fun and romantic amma ba hakan taso aranta ba.


Harsai wajajen karfe biyu da rabi na dare kafin nan suka fito ta bakin ruwan suka zauna tare lokacin wajen yay shiru kusan kowana cikin room dinsa na bacci..


Nan ne adiaha taje ta dauko strong wine mai dan tsada snn ta bude ta zuba a cup ta fara bashi labarin familynta da yadda matsayin aure yake ata fannin iyayenta da zuriarta baki daya.



Asalin Adiaha yar garin calabar ce amma sunyi dukkan wata rayuwarsu ne acikin yarukan ibibios na cross river state nigeria.


mahaifin Adiaha yan biyune,sunan sa mr bassey yana da husaininsa wanda take cemai uncle udo, sai karamin su kaninsu wato uncle Akpan, babu mata dayawa acikin zuriarsu face wacce ta haife su wato mrs chidara.


Zuriar mahaifinta dana mahaifiyarta gabaki dayansu sunajin yaren juna sabida dukansu yarukan suna zamane a south east na nigeria under igbo land. Sukan ji yarensu na calabar snn sunajin yaren igbo sosai.


 mahaifyarta mrs grace udofia is an efik woman wanda al'ada da addinin su na gargajiya ya shige jikinta sosai danharyau ita wa Allolinsu na tun kakankanin kawai take bautawa musammn ma daya kasance mijinta mr bassey shima dan kiyaye al'adan iyaye da kakanni ne.


Kamr kowani normal igbo family hakanan suma Suka gina babban zuriarsu, mr bassey wato mahafin adiaha ya zamo kamr shine babba kuma jagoran dukkan yan uwansa bayan mutuwar babansu, da mahafinsu ya rasu shine yasaka aka raba musu gado kowa yay familynsa daban.


Nan ne kuma babban iftilain rabuwan kai da jarabawar rayuwa ta fara afkuwa acikin familyn nasu musamman  ma da mahafiyarsu mrs chidara ta turje ta zabi ta auri wani tsohon customer dinta a adamawa.


Shi musulmine dan bafulatani sunan shi alhaj Aliyu gadanga mai yourghut, soyayyarsu mai tsafta sukayi kafin nan sukayi aure bayan ta amshe addininshi na musulunci ta dawo ana kiranta da Hajiya hajara.


Akan wann abunda tay

Saida kowa ya girgiza duk dangi suka tsine mata kowa ya cire alakar dake tsakaninsa da ita 


Babu irin Tsana da kyamata da yayanta basu nuna mata ba musammn ma mahaifin Adiaha wato mr baseey dan shi sosai yake kishi ma mahaifinsa da kuma al'adansu na gargajiya da uwarsa ta juya ma baya taje ta auri musulumi.


Tun da tay auren suka raba jini da ita, ta tafi adamawa da mijinta su kuma anan calabar sukayi rantsuwar cewa ko mutuwa akace musu tay bazasuje bisonta ba snn duk sanda ta dawo garesu saisun kasheta.


Taurin kan datay ma al'ada da kuma fafatawar datayi da Allolinsu yasaka kowa ya dada tsanar ta a garin.


Wnn abu ya zame ma gidansu mummunan taɓo kuma babban abun kunya Fushin hakanne yasaka mr bassey ya kauracewa gidansa gabaki daya ya koma jeji da zama shikadai sabida aganin shi bazai iya zama acikin mutane da irin wann abun kunya da takaici duk inda yaje saidai yaji ana kafa misali da mahaifyarsa ba.


Tun bayan tafiyar mahafiyarsu shekaru aru aru yake zaune a jeji haryay makansa dan bukka snn haryau bai saka ranan dawowa gida ba saidan duk wanda yake son ganinshi yaje can ya sameshi.


Dan uwansa Mr uno shikam ya hkra har ya auri matarsa wata igbo woman mai suna mrs margaret suka haife yaya maza duk suna abuja suna aikin kwadago.


Shikuma mr akpan ya haifi yarsa Ekaete wanda tsirarsu da adiaha baifi shekara biyu ba sudin ma duk sun kammala karatunsu na universiry.


Adiaha itace babba agidansu, asalin sunanta shine "Adamma", amma ana ce mata adiaha ne sabida kalman Adiaha yana nufin yar farko.


Bayan ita iyayenta sun haifi yara biyu da Namiji mai suna Abasi da kuma mace mai suna Urua.


Su Dukansu kannentan har sunyi aurensu at a very young age amma haduwar Adiaha da Ahmed yasaka taki sam tay aure duk dama ba'a taba sanin hakanne dalilin dayasata taki aure ba.


Duk an dauka ko wani matsalane agareta hatta ciwon datayi da Ahmed ya tafi duk an dauka spirit ne suke tabata.



Nan adiaha tafara kurban giya tana bawa Ahmed labarin yadda Abubuwa suka kasance da kakarta mrs chidara ta kawo namiji musulmi tace zata aura.


Labarin Duk wani gwagwrmayr da akayi da elders da bokayen garinsu saida ta fayyace mishi tanayi tana shan giya cos is not easy for her datake fada mishi sirrin familynta.


Duk jikinshi sai yay sanyi sai yaji  ma tafara bashi tausayi musmmn ma data fara ce masa itama tana son ta dawo addinin shi suyi auren cikin gaggawa saboda su koma garinsu atare tun kafin nan elders su mata auren dole kuma tasan idan mahafinta yaji wann zancen hala ma kasheta zaiyi mai gabaki daya dan da bakincikin mahaifyarsa yake zama acikin jeji in aka sake ce masa yarsa ta fari itama zata sake aikata irin hakan batasan ya zaiji aransa ba.


Ahmed yay iya bakin kkrin shi wajen convincing dinta dan karta canja addinintan amma haka taki mishi sam tace masa ra'ayinta ne snn inhar yana tare da ita zata iya yin komi.


Basu kammala karkare maganan bama sai bacci

Ya kwaceta sabida ta bugu da giyar sosai..


Hakanan ya daukota ya kawota room dinsa ya shimfidata akan gadon shisai ya koma kan kujera ya kwanta.


Kasa iya runtsawa yay tsabar yadda labarin adiaha ya rikitashi cos der is sooo much to loose gashi shibawai asalin sonta yakeyi aransa ba.


Aransa saiya fara jin mugun tausayinta wani tunani yay da har ya ya ke hukuncin zai tashi kawai ya tattara kayansa ya sake guduwa ya koma gida sai kuma ya tuna abunda tace mishi lokcin datake bashi labarin ta na cewa inhar bata aureshi ba tabbas zata kashe kanta saboda tana sonshi sosai.


Ya rasa me zaiyi dan baison ya cutar da rayuwarta musammn ma dayasan idan har zata aureshi zata shiga babban matsala da iyayenta,he felt sumhow restless and guilty msmn datace mishi zata canja addininta tabishi bayan yasan intay hakan ta rabu da iyayenta kenan na har abada, duk damuwarsa shidai baison ace yarinyar tayi secrifising rayuwarta akanshi dayawa bayan shi yasan Bazai iya mata rabin hakan ba.


Deciding yay kawai ya fahimtar da ita washe gari akan su hakura kawai da juna inyaso zaije ya neme wani mafita amma bazai iya rabata da komi nata ba.



Washe gari da safe da kyar adiaha ta farka daga bacci idonta yay ja ta rike  kanta dake mata ciwo sosai sabida giyar datasha..


Ya idar da sallah kena   sai gatanan ta sauko kasa suka gaisa bai wani boye mata ba yafara kkrin fahimtar da ita akan su hakura da juna kawai taje ta aure wanda iyayenta suke so din dan baison ya rabata da kowa nata akan selfish interst dinsa na son ya aureta..


Aikuwa kamar da wasa Adiaha tayi fushi sosai da furucin nan nasa ta harzuka ta dauki kwalba ta fasa zata cakkashi a cikinta da kyar ya kwace ya hanata tanata mishi kuka.


Duk Ya rasa me zaiyi bayan ya rarrasheta saiya fita waje yaje ya kira abokinshi banji ya fara gaya masa abunda ake ciki dan ya sama masa mafita, anan kuma Ita ADIAHA duk ta dauka tsorata kawai Ahmed yay da labarin rikicin dake cikin familynta data bashi jiya shiyasa yake son yakara dumping inta.


She just concluded dat babu wanda ya isa ya hanata auren wanda take so a zuciyarta dan haka ta dauko wani tsohon simcard dinta acikin jaka ta saka awayarta snn ta kira lambar kakarta hajy hajara dake chan garin adamawa.


Duk sanda taga kirarsu daga gida tabbas tasan akwai babban matsala dan haka tana daukawa ta fara tambayarta damuwarta.


Kuka kawai Adiaha takeyi tana gaya mata cewa tana son ta auri Ahmed amma gashin nan har ya tsorata da rikicin familyn su yace ya hakura da ita.


Rarrashinta tay sosai dan dama ita abunda take so kenan wani jininta ya zamo yana tare da ita kuma Alhamdullhi sai gashi babbar jikarta ce ma takeso ta musulunta tay aure arewa.


Atleast she wll have sumone by herside now



Dan haka ta daura dammaran yaki snn ta kudiri goyawa adiaha baya akan kudirinta na auran Ahmed ta ce mata ta kwantar da hanklinta itace zata mata komi.


Ahmed da hanklinshi gabaki daya ya tashi yaje gefe yana kan waya da banji sai gata nan ta kawo masa wayar kakarta hjya hajara


Baima iya katse wayarsu da banjin ba dake nasu wayar a speaker yake sai ya fara gaisheta acikin mutuntawa, bayan yan tambayoyi masu yawa data mashi akan gidansu da aikinsa sanda taji kominshi zam zam she is now well impressed da background dinshi,wa'azi ta fara masa mai shiga jiki akan batun lamarinsa da adiaha.


nan take ta shiga gwada masa cewa haduwarsun ma ai babban alherine agaresa tunda har gashi tana son ta musulunta a sanadiyar aurensa datake so tayi .


Ta hada masa harda roko tanamai lallabashi cike da kafa masa misalai masu yawa akan kanta ta gwada masa cewa duk borin bogi iyayen adiaha zasuyi amma bazasu iya hana afkuwar komi ba.


Duk maganan nan da akeyi abokinsa banji yana jinsu shima.


Tsohuwar ta dinga rokonshi hartana hawaye akan karya yanke hukuncin rabuwa da jikarta akan matsalar familynsu


Ahmed ya nitsu duk ya rasa me zaice mata kanshi yaji tana mai zafi, 


Nauyinta dayakeji aransa ne kawai yasaka ya iya amsata yace zaiyi tunani akan maganantan amma bawai dan yaso har ransa ba dan harga Allah yasone ya kyale musu yarsu ya kama gabansa dan baison ya jefa yar mutane acikin wani irin cakwakiyar rayuwa mai wuyan fassarawa...


Bayan sun kammala wayar da hjya hajara nan Adiaha tace masa zata wuce gidansu sabida kakartan tace mata karta tay rashin kunya ko ta bijire ma iyayenta taje gidan ta lallamesu ta fada musu gaskiyar lamarinta da Ahmed dan suma su sani


Amma tace inhar basu amince ba toh ta nemeta awaya tasan mezatayi.


Da karfin gwiwar jin hakan adiaha ta koma gida da safen ko wanka bata tsaya tay ba.



Ahmed kuwa ya koma dakinsa ya kwanta snn ya cigaba da magana da abokinsa, saidai Da mamakinsa banji ma magana daya yake fada masa akan Adiaha, nan shima ya dinga cusa masa ra'ayi irin nasu na cewa lallai kawai ya amince ya aure adiaha cos all these tradional stuff is not a big deal.


Shidai Ransa bai wani kwanta akai ba musmmn ma da abun ya zamo na rikici  amma duk da haka sanda abokinshi banji yasakashi akan ya amince musu kawai har dai yace zai yi kkri yaga taimaka ya auretan.



Da sassafen Adiaha ta isa anguwarsu ganin duk wanda ta gamu dashi ahanya sai yabita da wani irin kallon banza dana gurmin gulma wasu harsuna karkada kai irin tayi abun kunyan nan 


Duk ta basar dasu sabida maganan kakarta ne kawai ayanzu acikin kwakwarta tanajin wani irin karfin gwaiwa atattre da ita, saidai tana shiga gidansu  gabanta ya tsinke nan ta tarar da mahafiyarta azaune kallo daya zaka mata kasan ko bacci batayi ba.


Zuciyarta na dar dar ta karaso duk gabanta sai faduwa yakeyi amma bata daddara ba.


Tana isowa daf ta tsaya tana sose sosen gefen kunne ganin mahaifiyar tan na karkada kafa batace mata uffan ba yasaka ta hau gaisheta.


Bata amsata ba tsabar harzuka yasa ta rarumo wani katoton itace zata gwada mata akai nan adiaha ta balla aguje suka fara zaga cikin gidan atare.


Ran mahaifyata a matukar bace tafara zaginta kamar Allah ne ya aiko ta sabida bada karamin takaicinta ta kwana ba.


Babu kalar tsinuwa da Allah wadar da batayi wa adiaha ba, duk wani laifukan ta datay saida ta tuno mata tana zaginta dashi, duk ta birkice da bacin rai ta kasa iya controlling kanta ma bare ta saurare abunda adiahar zata fada maata.


Adiaha taci kuka tana rokon ta akan ta tsaya ta saurareta amma taki jinta sam, dan Aganinta kawai dagangan adiaha take musu hakan dan hala tafi damuwa ne da tazauna maza kala kala waje suna ciinta anyhow akan ta nitsu tayi aure shiyasa take zubar musu da mutuncinsu agari tana walakantasu.


Haka Ta dinga zaginta tana kirarta ashawo bata barta tay magana koda na minti biyar ba 


Ita kuma adiaha tazo ne dama da niyyar gaya mata Abunda take ciki da Ahmed tunda dai basu taba saninshi ba, saidai irin over reaction din datasamu awajen mahafiyartan yasaka itama ta mugun harzuka tay fushi sosai idonta ya bushe ta fara amsata da tsagwaron rashin kunya musmman ma da mahafyartan ta tsiri kiranta da sunan karuwa tana ta mata gori akan zubar da cikin da tayayyi agabansu.


Yau Kusan cacan baki sukayi duk dama hakan bai taba faruwa a tsakanin su sabida gidansu gidan da ake respecting din babbane sosai 


Sosai mrs grace tasha mamakin amsata da Adiaha tay cikin tsananin fushi  da rashin kunya snn ta kara ficewa agidan tana kuka sosai tace mata baza aure wanda suke so din ba.



Adiaha tana ficewa  agidan abun duniya yabi ya ishe mrss grace dan haka ta sabi dankwalinta ta daura akanta snn ta fito ta dauki jakarta ta wuce direct wajen babban bokarsu na garin domin ta bashi go ahead akan cewa idan akazo taron festival dinsu na akpo ayau tana son Tay auren sadaka da yarta Adiaha wa former suitor dinta na jiya data dizga shi,snn basai an kawo wani sadaki ba, snn tana so ne ayi komine bayan a samu albarka da shaidar dukan ancesstors dinsu sabida ta gaji da ita .....

Contact 08060712446 SURAYYAHMS:*Wanda ba su yi saving number ta ba su yi sai su mini magana ni ma zan saving ta su* Reply with "saved" is enough.👍🏻*KISHIYAR KABILAH...12.*



BY SURAYYAHMS.


MAMAN HAIDAR' APRODISIACS....

ALBISHIRUNKU MATAN AFRICA DA KEWAYE SHAHARARRAR MAISAIDA KAYAN MATAN WADDA KUKAFI SANI DA MAMAN HAIDAR TANA YIMAKU ALBISHIR DA CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE AFADIN NIGERIA DA NIGAR KARKU MANTA MACE MAI GYARA BATA BORANCE💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃08040448621

    Akwai zafafan kayan mata masu kyau da arha cikin sauki zamu aika miki da kayanki cikin aminci da yardar Allah ba cuta ba cutarwa karku bari abaku labari

   Muna kawo kalolin kaya kamar haka 💥💫💥💫👇👇👇👇

1-Maganin sanyi

2-Maganin gyaran nono

3-Maganin hips

4-Akwai gumba kala kala

5-Maganin matsi masu ciko da gaba ki koma kamar budurwa

6-Kalolin garirrika masu bawa mace ni ima da jimawa yana aiki

7-Akwai tsumi sha yanxu magani yanzu

8-Akwai jigidar sirri kala kala

    Sannan kuma muna dahuwa kamar haka 💥💫💥💫👇👇👇👇

1-dahuwar kaza

2-yan shila

3-ciccibi 

Dadai sauran su.Abubuwa dayawa gaskiya bazasu lissafu bah saboda lokaci maiso tabini PC don ganin Kalolin kayan da muke dasu 08040448621




Atsakanin Adiaha da mahaifiyarta mrs grace kowa yay hanyarshi ita ta wuce wajen priest dinsu mai jagorantar kungiyar akpo, Adiaha kuma ta shiga yawo agari cikin rasa wajen wanda zataje dan izuwa yanzu kusan kowa baison yay wnai mu'amala da ita sabida abunda tay na guduwa wajen consent taking na aurenta, kowani gida ka leka zaka samu ana Allah wadai da halinta sabida aganinsu rashin tarbiyane kawai yake damun Adiahar shiyasa take kunyatar da iyayenta sosai.


Tafiya take batare da tasan ina ta dosa ba, wajen sosai yay shiru, daidaikon mutane ne awaje suna hada hada dan Yau kusan duk inda ka ratsa shiri akeyi na hidimiman akpo festival wanda shine hidima na karshe da za'ayi kwata kwata a wann shakrar.


hidiman yau din is more of spritual events sabida rana ne da za'a fito domin ayi muamala na musammn tsakanin duniyar rayayyu da na mutattu.


A Al'adansu sun yarda cewa dodonin da zasuyi wasa a filin yau ba ordinary masquerade bane,wasu irin spirit ne da ruhi na iyaye da kuma magabatansu da kuma Allolinsu da suka shude tun zamanin kakanni.


Ko ina shiri akeyi domin tabbatar da yuwar wann hidima cikin nishadi kmr yadda aka saba wanda da misalin karfe sha biyu na rana suke farawa.


Tun fitowar Adiaha daga  gidansu take tafiya cikin sanyin jiki da tunanin irin masifa da zagin cin mutuncin da mahaifyarta tay mata wanda hakan ne yasaka bata kara jin sha'awar komawa gidansun ba.


A Wani wajen shan coffe acikin kasuwarsu can inda suka saba haduwa da Ahmed taje ta zauna tay shiru,har sai bayan da ta dan samu nitsuwa aranta snn ta dau wayarta ta tura masa sako akan cewa tana bukatar ganinsa cikin gaggawa..




Daga can Abuja kuwa hanklin mahaifin Ahmed, Alhaj bello jimada yadan samu kwanciya ne musmmn da yake da tabbaci akan inda dansa yake aynzu, Saidai gidan nasane har iyanzu bata masa wani dadi sosai duba da yadda matarsa hjy khadijatu take yawan daure fuska dashi sosai akan batun makircin da yan uwansa suke mata ita da danta ahmed.


duk dama yasan sun zalunce ta amma shi so yake ta mance da komi ta yafe musu kai tsaye batare da sun nuna nadamarsu ko sun bata hkri ba, aganinshi ai anty moju matsayin uwa take awajenshi, snn tunda yana girmamata sosai, babu wani amfanin tuhumarta da dalilin tay musu laifi saidai ayi hkri da ita, hjy khdijatu taki sam ta amince da wann zance nashi na sonkai haka ma taki ta saki jikinta da su sam.


Kwanan biyu Duk saida ta dibi tasharsu ta watsar. Dan a Yanzu damuwarta baifi taga danta Ahmed ya dawo izuwa gareta ba dan ita haryanzu hanklinta bai wani kwanta da shirun san nan ba. Yawancin lokuta, idan  tafara jin faduwar gaba mai tsanani akanshi bata jin sakat aranta, tay ta neman layinsa kenan amma haryau saidai tajishi akashe, gashi tunda kafayat ta koma son hira ata sashen baban san sai bata wani fiye wani janta ajikinta sosai ba,yawanci saidai ta zauna a dakinta ta kira babban dadarta hajy maimunatu suyi magana dan itace kawai aynzu take kwantar mata da hanklinta sosai.


Duk wani abunda take ciki agidan saida ta fadawa dadarta dan rashin Ahmed agidan na kwana biyu ya saka ta fahimce cewa itace kadai bare agidan mijinta saboda bambamcin da suke nuna mata na kabilanci.


Gashinan dai har marinta mijinta yay akan laifin da bata aikata masa ba amma Kwata kwata baiya son ya nuna mata afili cewa yan uwansa ne su kayi kuskure dari bisa dari saidai ya nuna kamr cewa ykmta ita tay hkri ta mance da komi kawai itace din zatay hakurin zama da su.


Har mamakin yadda suke nuna son kansu takeji aranta. They dont even care about her feelings musammn ma da makircinsu ya jawo mata mari da rashin mutunco awajen mijinta, sosai Ta lura da su, kai hatta kafayat tana da wnn dabi'ar tasu na son kansu dan duk sanda aka tashi fadin wani aibun danta Ahmed ko laifin sa sam ita bata tunowa da nata aibun saidai tayi shiru ko tay nadaman zuci.


Tasani sarai da cewa kafayat haryau tanakan  zarginta aranta da tunanin hala ko itace take juyawa Ahmed kai ne akanta, kwana biyun nan shiyasa taja jikinta da ita agidan sosai.


Aranta tana zargin cewa son hira da Zama da kafayat takeyi kwana biyu a gefen mijinta bana lafiya bane saidan ta cusa mishi kai donta cimma burinta na tunxira shi domin ya aura mata Ahmed acikin gaggawa.


Ta rasa yadda zatay ta fahimtar da kafayat cewa dukansu basu da masaniya akan dalilin dayasa Ahmed yake kaucewa da yin jinkiri akan batun amsawa aurensun ba.


Sosai kafayat ta zanca mata, wani bin sai taga tana behaving ne kmr bata yarda da ita ba musammn ma dataga ta fara samun cikakken kulawa daga wajen mahaifin Ahmed din shikansa..


Shidin ma tunda yaga kafayat ta fara nuna masa yarda sosai da amincewarta agareshi shikenan saiya fara zargi da tunanin hala hjya khadijatun tana nuna mata bakin hali da warayya ne, aynzu dia kafayat nunawa take yi kamr da shi kawai tafi amincewa, ta fi saka hope dinta akanshi ne sabida aganinta koda za'a mata kabilanc shi ai bazai mata ba.



Sosai kafayat ta dage wajen kyautata ma mahaifin Ahmad, Kwana biyun nan ma tun kafin nan hjya khadijatu ta fito tsakr gida zata zo ta samu har kafayat tay masa komi na girki da arrangin kaya mostly saidai yazo yaci abinci ya tashi ya tafi batare da yanemi kowa ba. 


Wani bin intayi nazari akan yanayin halayyar danta Ahmed a lokaci guda take fahimtar cewa ajinin mahaifin shi ya dauko wasu banzayen halayyar sa dayakewa yan mata.


They just love taking advantage of girls dan tunda kafayat ta soma zama ata wajenshi haka nan yake sakata tay masa wann tay masa wann kmr ya samu jaka.


Da abun nasu yabi ya isheta duk ta ibi kashinsu ta watsar agidan duk dama babban dadarta Maimunatu sam bata amince da irin wann dabi'ar na kafayat ba.


Ita tuntuni aranta ba son tarayyar Ahmed da kafayat takeyi ba dan gani take kamar Zata lalata masa rayuwarsa ne kawai dan bata da isashen tarbiya ajikinta.


A tunaninta a al'adance ma bai kamata kafayat din tazo tazauna musu a gida ba, wann dabia na rashin kamiya da wasu kabilu sukeyi sosai yake bata mamaki,saidai ayanzu tasan idan har yar ta turasa yar uwarta tay magana kowa zai juya maganan akanta ko ace ta zalunci kafayat din ko ace tana zargin mijinta wanda zai iyayin sanadiyar zaman aurenta datayi sama da shekara talatin dan tasan kiris yarbawan nan suke jira su tozarta mata yar uwa.


Transcop hotel

Calabar: 10 am.


Da safiyar yau din Ahmed da babban yayansu kazim aremu da kuma brother hamzat dimeji suka hada long video confrence call mai dan tsayi dan su tattauna akan batun auren sa da Adiaha.


Sunzo suji dalilinsa na aje batun aurensa da kafayat shikuma yay iya bakin kkrinsa wajen nuna musu cewa hanklinsa ne kawai bai gama kwantawa akanta ba amma bawai don baisonta aransa ba.


 bai dai wani bude musu dalilansa sosai ba sai ya gaya musu cewa adiahan ma tafi sonshi dan  har kashe kanta takeso tay dayace ya hakura kuma baison yay sanadiyar mutuwar yar mutane.


Duk da hakan Hanklin Brother Kazim aremu bai wani kwanta sosai da yaji cewa da akwai jinin inyamuranci ajikin Adiaha ba, cos normally they are this little skeptical  particularly da igbo ppl sabida dukansu yare ne wanda basu wani yarda da junansu sosai ba.

 

Aransa yaso ace da duka iyayentan mutanen garin cross river, calabar ne. da hala bayanin nasu zaizo masa da sauki, shi duk tunanin shi yadda su aunty mojushola zasu dauki maganan ne, dan yasan basa kaunar hada jininsu da inyamurai sam sam.


Sosai suka tattauna akan hakan atsakaninsu Brother hamzat dimeji ne ya dan kwantar masa da hankli dayace masa ai mahaifin Adiaha wato mr bassey ba inyamuri bane asalin dan calabar din ne dan shi yaren calabar din yakeyi dake yaren mahafinsa ne.


Saidai uwarsace mrs chidara data kasance inyamura gaba da baya take inyamuranci, dan haka yana ganin kamr yaren adiaha bazai zame musu wani matsala ba Cos technically,duk yaren uba ake bi so za'a iya cewa Adiaha calabar girl ce not an igbo girl duk dama ansan yes tana da jininsun ajikinta sosai ta wajen kakannin ta mata.


Ahmed Bai wani bude musu abunda ake ciki da rikicin dangin Adiaha ba amma ya gaya musu cewa da akwai babban matsala wajen iyayenta sabida basu son yarsu ta canza Addini ko tay aure anan arewa. Snn ya gaya musu yadda sukayi da grand mum dinta hjy hajara da iya abinda tace mishi na cewa inhar da gaske yakeyi zai aure jikarta adiaha ita zata yi musu komi na batun auren nasu.


Ahmed ne dan autarsu snn Dukansu Sunason dan uwan nasu sosai dan haka suka masa alkwarin tsaya masa akan batun auren nasa dik rintsi duk wuya.


Brother kazim aremu yana kasar waje dan haka suka bar komi na formalities din auren a hannun brother hamzat dimeji, shikuma brther kazim din yay musu alkwarin cewa shi zai fayyace ma mahafinsu komi da komi dan sunada fahimtar juna tsakaninsu sosai.


Brother kazim yasan cewa abu mai wuya ne duka familynsu su aje maganan aurensa da kafayat a lkci guda amma dake yana da shirinsa na musammn dayake musu duk sai abun bai wani damesa ba.


Shidin yana da arziki sosai dan har kamfanin kanshi ya gina inda ake processing din kayan abinci ana kaiwa kasar waje. Yanzu haka ya siya

ma iyayensun wani irin makaken gida family house size irin hadadden luxury bunglow din nan nagani na fada mai sashe sashe wanda kowane acikinsu zai iya zama da familynsa aciki anan A Abuja cikin anguwar garki.


Yana so ne ya kammala furnishing din gidan kafin yace musu su duka su koma can tare da matar sa wato aunty adizat da yaransa uku maza, Da shikansa brother hamzat din da matarsa aunty nurat da yayansu, Da Shi Ahmed din duk dai yace zasu iya zama a kusa da iyayensu acikin gida daya in har suna son hakan. 


Yay hakan ne sabida babban burin mahaifinsa kenan yaga kan yayansa duka ahade kuma familynsa su rayu a waje guda cikin hadin kai da taimakawa juna.


Already brother hamzat baida matsala da wnn plan din dan dama gidan dayake zaune aciki mortgaging dinsa yay da bank,hakama anty adizat tana son duk adawo waje guda dan tasamu daman bada hankli akan aikinta, hakan zai iya yuwa ne idan yaranta suna gida agaban idanun kakanin su ana kula mata da su. Saidai haryau basu san ra'ayin Ahmed akan hakan ba tukuna.


Tunda suka kammala maganan auren brother kazim ya soma bada oder wa client dinsa dan asamu agaggauta kammala furnishing din babban gidan nasu dan yasan da hakan ne kawai zai iya rufewa mahaifin su da su anty moju shola bakinsu akan maganan auren Ahamed da Adiaha acikin gaggawa.


He believe dat Komi arayuwa yana bukatar nitsuwa da kuma siyasa, dan haka bai damu dayin komi ba musmmn in hakan zai samar ma dan uwansa Ahmed damilare kwanciyar hankli.


Ata fannin mahaifyar Adiaha kuwa tana isa wajen chief priest dinsu da fushi da takaici ta zauna gaya masa iya bukatun ta akan yarta adiaha,saidai bai wani bata goyon baya tay ma yarta auren sadaka ba sabida al'adansu yana daraja kimar mace sosai musmmn ma akan batun aure, shawara ya bata yace mata tay hakuri tabi yarinyarta ahankli 


council of elders zasu taru suyi mata fada snn aja kunnenta ahankli zasuyi komi domin a aurar da ita ayadda al'adansu yace.


Badon ranta yaso ba tay hakuri ta koma gida da tunanin abunda ya gaya mata na cewa taje ta jawo yarta ajiki ta lallame ta snn ta fara jin damuwarta tukuna.


Tun dawowarta gidan ta aika anemo mata adiaha amma ba'a ganta ba, duk kuma sai taji ta damu sosai da taji shirun yartan yay yawa,nemanta takeyi agari taje duk gidajen kawayen ta, sai can data gamu da wani crier ahanya zashi kasuwa snn ta lallabeshi ta bashi kudi snn tace masa yaje ko ina lungu da sako dayasan adiaha tana zuwa ya nemota ta dawo gida acikin gaggawa.




Ahmed yana kammala magana da yayunsa yaga sakon Adiaha almost 30 minutes ago, ya gaji sosai da fitinanta amma haka yay Refreshing kansa ya saka wata black dubai jallabiya mai laushi da kyau snn ya fito domin yaje ya dubata.


Lokacin ita kuwa harta gaji sosai da jiransa ta siye abinci tanaci kenan sai gashi nan ya taho awani motar haya.


Miƙewa tay ta koma ta can ta inda babu wani hayaniyar mutane sosai snn ta tsaya tana ta kallonshi  ayayinda yake karasowa ta wajenta.


Wani iri ta dingaji a ranta dataga irin azaban kyan dayayi dayasaka simple sutura ajikinshi,yanayin shi mai cike da aji da kasaita take kallo ayayin da yake zuba nitsatuyar takunshi mai tafe da kamiya da wata iriyar nitsuwa,tsikar jikinta duk saida suka motsa ganin ya zuba idanunshi shima tun daga can yana kallon ta,ahankli ta lumshe idonta snn ta bude cos she feel soo very lucky to have him, atake wasu irin zafafan feelings masu wuyar fassarawa suka fara shigarta tundaga tsakar kanta zarensa yabiyo harta kololuwar sawayen kafafunta yanamata tsitta mai saka ragwabewar jiki.


Tun kafin ya iso taji duk wani damuwarta ya kawar tafara masa murmushi, dan abunda tazo gaya masan ma  gabaki daya sai taji yay escaping mind dinta sabida farincikin datake tsintar kanra acikin inta kallesa, yana isowa daf suka hade idonsu waje guda yanamai kashe mata jikinta da kyakkwar murmushin sa mai taushi wanda ya tarbeta dashi snn suka gaisa tq riko hannunshi cikin nata sauya fara tambayarta halinda ake ciki.


 Hannunshin ta dada rikowa cikin nata tana sauke ajiyan zucya sann ta fada masa cewa "tsoro takeji" Da mamaki Yace mata tsoron me takeji ko wani abu ya farune agidan nasu?


Tace masa a'a, tana tsoron dai kar ya watsa mata kasa a idonta ne dan ta riga da ta fara fahimtar cewa kamr iyayenta bazasu amshi batun auren nan nasu ba.


Tace masa" dolene itace zata hkra ta sadaukar da komi nata dan tay fighting ma soyayyarta .


Ahmed sam baison jin tana furta hakan sabida yasan abunda yakeji aransa akanta baikai haka ba. Aransa yasan Inda ace adiaha bata zafafa mgn aurensun ba,hala da tuni shikam ya hakra ya bar garin ya koma Abuja abunsa sai dai gani yake kmr a zauce take da giyar soyayyrshi ayansu da wuyane ta iya rabuwa dashi tacikin sauki


ynzu kawai tabbaci take nema daga wajenshi na cewa bazai guje mata ba duk rintsi duk wuya zai kasnce yana tare da ita harsai sun cimma burin su na aure.


Cikin rashin wata mafita Ahmed Yace mata karta damu babu inda zaije  snn har yay magana da brothers dinsa shi ata fanninshi kusan ma a shiryesuke ita kawai suke jira.


Sosai wann maganan ya faranta mata rai snn ya kara mata karfun gwiwa gani take a brain dinta kamr dagaske ne Ahmed yana mutuwar sonta aranshi.


Nan ta soma masa bayanin abubuwan da zai iya faruwa yau izuwa gobe Dake duk abababen daya shafi a'aldarsu ta dabbaka bautar Allolinsu ne tun na kaka da kakkani, nan Tafara gaya masa yadda akeyin wnn festival din, suna cikin maganan sai tafara ji ajikinta kamar wani ya labe yanata kallonsu saidai kodata juya baya tana dubawa bata ga kowa awajenba.


Tay murnushi snn Tace masa dodonin Allolinsu zasu bayyana yau asarari da siffofi mafi muni da kuma ban tsoro Dan haka bazaiyu yau tazo wajenshi ba harsai an kammala komi sabida wann festival nayau din is very spritual for all the tribes din dake wann yankin nasu basu kadai ba.



Yanzu haka dodonin nasu suna kiillace ne a makewayensu inda ake ginashi da fresh palm tree leaves mai tsawon dayakai 15fts sabida ba a bukatar kowa yay ido biyu dasu harsai lokcin fitowarsu sarari yay.


Suna cikin wann hirar tasu cikin nishadi sai ganan motsin kafafu ata bayansu da alaman mutane suna tahowa ta wajensu agaggauce.


Dukan tara tara kirjin adiaha yay tay saurin kwace hannunta ana Ahmed snn ta leƙa ta bayanta agurguje kafin nan ta dawo da baya jikinta yanamai barkewa da wani irin rawa mai tattare da rudewa.


Mahaifiyarta tagani tare da wani crier sun tattaro kattin maza har su guda uku masu jini ajika sun runtumo manyan sandu na a hannayensu suna tahowa ta inda suke dashi. Gabanta ne yay mummunan fadi dan sai yanzu ta gane cewa dagaskene dazu da jikinta ya bata ashe tuntuni da akwai wanda yake lekensu da alaman shine yaje yakai gulma.



Tsabar bugawar da kirjinta yakeyi sama sama numfashinta yake hawa, ta juyo a rikice ta kamo hannun Ahmed tace masa dolene ya boye kansa anan wajen inda suke kar  mahaifyarta tazo  ta ganshi su tada wata fitina harsu jawo ace za'a kashe shi.


Yace mata shi bazai buya ba saidai in ya tafi 


Ta dada lekawa taga sun riga sun iso kusa dasu inhar Ahmed ya juya ya tafi toh tabbas zasu bishi sumasa illa awajen dan asananinta da fushi da fada suka rabu da mahafiyarta dazu agida dan haka koda tazo nan hala ma bazata tsaya ta fahimceta anan din ba.


Jawo hannunshi tay cikin gaggawa da narkakken magiya idanunta cike da tsananin tsoro tanace masa karyay mata taurin kai, duk yabi ya gaji da lamarinsu, amma hakann take janshi, nn ta bude wani old sac tace masa ya daure ya shiga ciki ta rufeshi, da taurin kanshi da komi da kyar dai ya shiga ciki ta rufeshi acikin wani katoton buhu snn taja ta tsaya awajen abunta.


Tana kammala rufe bakin buhun saigasunan sun fantsamo cikin wajen a hargitse, "wher is he?tambayar da kowaa ya jefo mata kenan aka barta da zare ido tana kallonsu.


Da kyar Taja taci fuska jin yadda mahaifyarta ita kanta take cika ta da tambayoyi akan mutumin da akace anganta dashi saidai batace mata uffan ba


Matasan nan kuwa atake suka fara bincika wajen suna hargagi kusan dik inda suka taba sai sun buga ma wajen sanda dansu razanar da su sosai, aganinsu inma boyeshi tay ai zaiji tsoron rasa ransa ya fito amma ko motsi Ahmed baiyi awajen ba


Duk borin da Adiaha tay musu na cewa ita kadai ce awajen bai hanasu komi ba har jikin sac din suka bubbuga wanda yay sanadiyar jima Ahmed ciwo agefen kunnenshi.


Da kyar dai suka hakura suka kyaleta musammn ma da adiaha taki ta amsa tambayoyin su.


Crier kuwa yace musu tabbas yaganta anan tare da wani hausa man yasaka jallabiya snn da dukkan alamu sun saba da junansu sosai.


Hade da mahaifiyarta da wayann matasan duk suka taru suka mata barazanar cewa indan ta yarda har suka ganta da irin wayann mutanen da crier ya fada toh zasu mata abunda bazataji dadinshi aranta ba.


Inhar yarinya budurwa fara biye biyen strangers irin haka She will be question by the gods.


Sanin hakan yasaka mahaifyarta tamata jan karfi ta tasota agaba har suka kai gidansun atare.


Tun ahanya take turawa Ahmed tex duk ta damu da yadda ta barshi awajen shikadai, ta tura masa sako ajere yafi sau takwas tana tambayarsa koyana lpya, ciwo kansa ya dingayi sabida buga sac din nan da suka dingayi da karfi. Tsabar baison wani fitinan kawai sai ya rubuta mata cewa he is fine, hakan ma ai bakomi bane. Sosai hnklinta ya kwanta daya rubuta mata hakan.


Daga isarsu gidansun kuwa wani sabuwar cece kuce ne ya kaure a tsakaninta da mahaifyarta.


Mrs grace ta matsa daa cewa lallai sai Adiaha ta fito fili ta gaya mata wayene mutumin da aka gansu tare da shi.


Tun Adiaha tanajin shakka da nauyin fada harta soma fayyace abun ahankli ahankli, matsalar shine sudin suna bala'in mutunta iyayensu dan haka bata iya fitowa fili gatsau ta fayyace mata komi dake wakana a tsakaninta da Ahmed ba 


Kawai ce mata tay aynzu tana da wanda take so, shiyasa gaskiya bazata iya auran zabin da aka mata ba.


Wann bai dame mrs grace sosai ba dan ta riga tasan halayyar yaran zamani da canze canzen ra'ayi na banza.


Babban Damuwarta shine ta tabbatar da cewa ba wani hausa man din bane kamr yadda labari yazo mata dazu


Da kyar ta samu nitsuwa aranta akan hakan, sann ta tutsiye yarta adiaha  akan data gaya mata wanene wann masoyin nata,daga in ya fito, snn waye shi? tsoro da fargaba saiya hana Adiaha iya furta komi, tin mahaifyar tata nabinta cikin lallami harta soma fahimtar cewa da akwai abunda yarta adiaha take boye musu. Gashi dai crier din nan ya riga daya fayyace mata siffar yaron ya tabbatar mata da komi, amma sam batason ma ta fara amincewa da hakan aranta dan aganinta inhar hakan ne toh kwakwalrta ma bazai iya daukawa ba bare ajega ta furtashi da bakinta wani yaji.


Duk wani wayo da uwa takeyi domin ta samo bayani awajen yarta saida tay ma Adiaha saidai the more tana tursasata ta fada the more tana fahintar cewa da akwai babban lamarin da adiaha take son gaya musu mai girgizawa da kuma nauyi sosai wanda shine take boye musu ayanzu.


Tun ba'aje ga bayyana komi a fili ba jikin mrs grace ya soma mutuwa, jiknta a sanyaye tace "Adiaha, ki rantse da ubangiji cewa baki da wata alaka da wani bako

Dayazo garin nan..


Adiaha tay shiru kanta na can kasa harsaida hakrin mrs grace ya kare ta daka mata tsawa snn tay motsi ta dago kai tana kallonta awani irin yanayi na rashin sanin inda zata fara furta wann maganan

Nasu da ahmed a fili.


Ahankli Tace mum, its true ina da wani saurayi, he is not from here...

..amma ina sonshi,..ina son Doctor Ahmed 

..shinake son na aura..


A rikice mahaifyartan take kallonta ayanayin shock ta kunce zani ta yar akasa snn ta daka wani rikitaccen tsalle snn tace "Doctor who?kikace A..Ahmed,ewoooo a Hausa man?.Adiaha a hausa man, cikin girgiza kai tace _mba nu_ banji ki da kyau ba..zoki min bayani i dint get u..


Adiaha bata iya cewa uffan ba tafara ja da baya baya sabida tsananin tsoro, acikin bambami ta karashe cewa mumy im serious ooo, ni dai shi  kawai zan aura. .


Mrs grace ta harzuka ta na shirin cafkota ta firgita ra ruga aguje ta shiga dakinta ta kulle kofarta da key jikinta na tsananta rawa jin inda mahaifyartan take dada kwala mata ihu cikin tambayarta daga waje.


"Adiaha you must come out and explain urself ooo..


Shiru tay ayayinda ta jingina bayanta da jikin kofar tana jinta tana ta rusa mata buhun masifa


mrs grace sosai ta fara fahimtar inda yarta adiaha ta dosa, duk sai taji jikinta ya mutu, After a while adiaha sai taji shiru bata karajin motsinta a bakin kofar ba.


Da kyar ma ta leko ta windo taga ko ina shiru da alaman babu kowa agidan nasu ji take hala duk anje ne ayi shirin festival dan haka ahnkli ta bude kofar ta fito tana mamakin inda mahaifyarta zata kasance ayanzu.


Wayar Ahmed ta kira bai dauka ba ta tura masa text messg ta gaya masa cewa mahaifyarta ta soma fahimtar komi game dasu tunma bata fayyace mata ba.


Ficewar mrs grace agidanta yau sam bai mata kyau ba dan kuwa koda taje tay kyakkwan bincike abakin mutane saiji take ana ce mata lallai ana ganin adiaha da wani bakon mutumi wanda basu taba ganinshi ba.


Kanta duk ya daure, Wani tunani tay snn ta wuce gidan dan uwan mijinta uncle uno,tana isa direct ta aika aka kirawa mata yarsa ekaete.


Agaba ta sakota har gaban iyayenta inda tasan bazata iya boye musu komi dake tafe da yarta adiaha ba.


Haka suka saka ekaete agaba ta tambayoyi har saida tay musu bayanin komi batare da son ranta ba..


Ita kanta ekaete din sai data jibgu sosai awajen iyayenta data kammala fayyace musu kan lamarin..


Tsabar rudewa da mugun gudu mrs grace tay hanyar jeji tana kuka tana mai kiran sunan mahaifin adiaha, tunma kafin ta isa gareshi muryanta harya soma dishewa..



A gigice ta isa gaban bukkan da mijintan ya gina Lokacin yana kan bishiya yana hutawa.


Da asalin  yarensa na calabar ta soma gaya masa cewa ya sauko kasa kawai yaje yagani da idonshi Tarihi zai memeta kanshi agidansu


Tace masa Yarsu adiaha ta kawo namiji dan hausa tace lallai sai shi zata aura kuma hartana zuwa wajen shi batare da sannunsu ba, Kafin ma ta kammala fada masa sauran bayanin na cewa yarsa na cikinsa harta yanke hukuncin cewa zata sauya addini tuni zuciyarsa tay fat fat ta buga garin saukowa kasa cikin gaggawa nan ya rikito ya fado kasa sumamme.


Daga nan asibiti kawai aka wuce dashi inda atake yan uwansa suka kewayeshi,koda ya samu ya dan farfado tun akan gadon yake famar tsine ma yarsa adiaha, yanamai cin alwashin cewa zai kasheta ya huta da bakincikin datake so ta gundura masa anata daddaneshi ana bashi hakri. Ekaete ne tay kkri wajen sanar da adiaha halin da ake ciki batare da kowa ya sani ba, dan ko kadan bata son ta rasa aminiyarta akan namijin da tasan hala basonta yakei ba.


Tunda Adiaha taji abunda yake faruwa da mahaifinta a asibiti take bari kar kar dan atake ta fara jin wani irin fargaba da tsananin tsoro mai rudarwa yanamai nakasa mata gabobin jiki


Tasan tabbas sukayi ido hudu da mahaifinta yau kasheta zaiyi har lahira dan haka dolene ta san abunda zatayi, tunanin 

Duniyan nn tay amma da kyar ta samu wani mafita kwara daya wanda bata da kwakwaran tabbaci akansa amma tasan shine iya hanyar tsirar wanda zai iya kubutar da ita daga mutuwa awajen mahaifinta ayau.



Sako take shirin rubutawa wa Ahmed sai kuma taga kamar sakon bazai iya fayyace masa muhimmacin plan din nata ba.


Acikin sanda ta sudade jiki ta wuce hotel din taje ta sameshi, yau ko zama batay ba ta hau gaggaya masa abubuwan da takeson yay acikin gaggawa kafin yamma yay. Nan ta aje masa phone number da home adress na kakarta tace masa duk yadda za'ayi dai yanemeta ya gaya mata halinda takeciiki.


Tana kammala masa bayanin komi tay masa sallama cikin yanayin gaggawa ta barshi ta komo gidansu adan gaggauce dan batason wani ya biyota abaya bare har asan inda Ahmed yake bare ajega zancen cutar dashi.


Dan aynzu ji take kamar Ahmed din nan shine kawai rayuwarta ..


Tana isowa compound din gidansu ta samu daf lkcin an dawo da mahaifinta daga asibiti ganan yan uwan da elders na zuriarsu duk an taru a tsakar gida ana jiran aga kalar hukuncinn da iyayenta zasu dauka akanta kai tsaye.


Da kyakkwar shirinta tazo dan haka ta zube kasa tafara birgima tun daga gate tafara kuka mai yawa tanamai nuna nadamarta akan abunda yake faruwa.


A farko duk sun dauka tsorone ya sakata ta rikice amma daga bisani da sukaga cewa ta kama kafafun mahaifinta tana kukan fitar rai tana cewa ta tuba duk sai jikinsu kuma yay sanyi.


Tay kneeling agaban kowa tana kukan makirci harda majina ta shiga gaya musu yadda ta hadu da ahmed da irin son datake mishi, sai kuma ta wayence tace musu aynzu tay nadamar abunda tay na cewa zata aureshi bayan tasan irin baqin cikin da hakan zai jawo ma iyayenta.


Atakaice dai Adiaha ta nuna musu cewa ta yanke alakarta da Ahmed

Yau Snn ta tuba hardace musu ta amince ayi mata auren kawai da duk wanda sprit of the ancesstors dinsu ya zaba mata ayau awajen festival.


Yadda ta dinga neman gafararsu da zuciyarta har Saida ta bawa kowa tausayi kowa jikinshi yay sanyi aka fara tausayinta sosai..


Duk da haka saida aka dan yiyyi mata masifa aka kara ja mata kunne


Nn mahaifinta ya yanke hukuncin cewa daga an zabi mijin adiaha awajen apeasing gods dinsu yau, gobe da sassafe za'a fara shiryata domin bikin aurenta.


Ahaka suka tsaya da maganan kowa yaje ya hau shirin fita wajen festival hnkli kwance dan adiaha sam taki ta nunawa kowa cewa badagaske takeyin dukkn wayann biyayyar ba hatta ekeate ma saida ta boye mata wnn shirin nata.


A bangaren Ahmed kuwa iya abunda tacemai yay shidin yayi, ya tura ma kakar tata sako, snn sukayi waya sai tace masa zata biyo jigi tazo calabar daganan zasu taho yola tare da jikarta adiaha, amma kafin nan tana da bukatar shima ya je gida yataho da nasa magabantan domin ayi maganan aurensu a lokci guda komi ya wuce musu.*KISHIYAR KABILA... 13*



BY SURAYYAHMS.



Bayan sun kammala waya da hjy hajara a tsanake Ahmed ya dau wayarshi ya nemi lambar yayansa wato brother hamzat dimeji snn yay masa bayanin komi acikin nitsuwa.


izuwa yanzu har ya yanke hukunci akan cire ransa ya gama sadaukarwa domin ya fahimce kamar Adiaha da kakarta baza su taba kyaleshi ba harsai anyi auren nan.



Nan ya fadawa brother hamzat cewa hjy hajara tace masa acan yola zasu hadu bayan tazo ta dauke Adiaha daga nan. 


umartan sa brother hamzat yay akanda yabar garin calabar din immidetly for his safety kar ma azo ace shine ya sace musu yarinyarsu.


Yace masa marmaza ya shirya ynzu ya taho ya samesa, zasu hadune awani protea hotel acikin garin jos daga nan zasu san abunda zasuyi.


Babu bata lokci Ahmad yahau tatattara kayanshi yay booking available flight tun karfe 2 na rana ya wuce airpot around 3pm sai gashi nan agarin jos direct ya wuce hotel din domin haduwa da dan uwanshi brother hamzat.


A fannin Adiaha kuwa bayan komi ya lafa aka fara shirin zuwa wajen festival din nasu na karshe. Duk abunda akeyi hanklinta baya jikinta amma hakanan ta waske take biye musu.



Yau Kowa yasako kayan shi mai kyau na A'alda sunyi matukar kyau snn aka haɗa wani gigantic stage perfomance a village square inda za'a yita nishadi ayi rawa na karshe. 


Lokacin gabaki daya mutanen communityn duka an taru an fito kwansu da kwarkwatnsu an kewaye filin wajen.


 wajajen karfe biyar da rabi na yamma aka harɓa ritualistic volley of canon shots wanda dashi ake kiran Sprits din Allaloinsu dasu izuwa sarari.


Jim kadan kowani dodo ya fara bayyana daga mabuyansa, kowanne yana fitowa a style dinshi suna tahowa izuwa filin taron daya bayan daya ayanayin siffansu Mafi duhu da muni da kuma tsananin razanarwa.


Kowani halittar dodo yakan bayyanane a siffar fatalwa shiyasa siffarsun yake da matukar muni, duhu da kuma firgitawa sosai,kowanensu ya fito filin sai yayi rawa snn ya wuce snn wani ma yabiyo bayansa, Jama'an gari kuma suna bibiyarsu abaya abaya suna wakoki suna rawa mai kyau da burgewa.


Adiaha da iyayenta da dukkan mutanen garinsu kowa ya fito ana rawan atare, bayan anyi rawa anyi wasannin dodoni sann aka dauko tumbin doya aka kai har shrine inda ake tsammanin spirit na allolinsu yana wajen. Bayan Cheif priest yay yan maganganunsu na yaren mutattu ya miƙa doyoyin gaban shrine  din nan ma akayi rawa.


Daga bisani ya saka hannu ya dauko doyan yanamai sanar dasu cewa goda of they lands sun amshi ziyararsu sun kuma saka albarla akan abincinsu na wann shekarar dan haka kowa zai iya cin abincinsa batare da wani shakku ba


Duk wani shagali na al'ada anyishi har da batun aure na yan matan da suka girma chief priest da elders da iyayen yaran duk aka taru aka tsaida kwakkwarn magana snn aka saka musu ranar shagalin bikin aurensu bisa al'adan yarukansa.


Anan aka kammala tattauna komi dazai wakana aka fara shirya hidiman bukukuwan yan matan,Adiaha da sauran yan matan da ake shirin aurar dasu din kaf aka fara shirin fara yimusu shiri da kuma hidima da sukaa sabayi na al'adansu.


Saidai tsabar matsuwa irrina iyaye da gaggawa anan atake suka miƙa yarsu Adiaha agidan da ake kai amare domin a farayi musu al'adansu na "fattening"..


Agidan ne bride to be zata zauna a kula da ita na musamman, zata zamo bata aikin komi and the elders will take very good care of her harsai tay bulbul tay kiɓa tay fresh tay kyau sosai kafin nan ranar bikinta


Fattening session shine abuna farko da suke farayi wa yan matansu kafin ayi musu bikin su na aure musammn idan yarinyar tadanja shekaru.


Wajajen karfe 8 na dare aka kammala hidimar mai gabaki daya kowa ya watse sabida idan waje yay duhu akwai babban dodonsu dayake fitowa daga land of death yay nashi rawar ayayinda shine zai tattara sauran dodonin su koma land of death sai kuma wani shekara in lokcin festival dinsun ya zago.


Bayan an kammala komi Adiaha da wasu tsirarrun yan mata da za'a aurar dasu tun acikin daren aka kaisu makaken gidan direct bayan ankammala sallamarsu daga gidajen iyayensu da duk wani abunda suke bukata.


A daren ranar sosai Adiaha ta rungume iyayenta tanamai neman gafararsu tana kuma kuka sosai dan aranta ta riga tasan ba lallaine su kara ganinta acikin dadin rai ba. Tasan in har Ahmed ya nemi kakarta yay mata bayani awaya yau din kamr yadda tace mishi toh babu shakka zata iya kasancewa acikin garin iyanzu dan ta dauketa dan sun riga sun yanke hukuncin cewa zatazo ta dauketa ta gudu da ita inhar iyayen ta basu amince mata akan batun auren Ahmed acikin sauki ba.


Kowa saida yaji tausayin Adiaha musammn yadda ta nemo yafiyar dukkan yan uwa da kawunan ta duk andauka ko nitsuwa da nadamar abunda tay ne yasakata take wayann emotional dramas ne.


Haka kuwa Har aka rakota gidan da ake musu fattening din aka sallamata cikin iyayenta babu wanda ya fahimce komi datake ciki..



Dagata fannin gidan Alhaj bello jimada kuwa

Komi na tafiyane yadda yake gidan ya zamo boring sabida kowa sauraran ranar dawowar Ahmed yakeyi akota wani bangare .


Banda cin abinci da tsinannen gulma babu abunda kafayat takeyi agidan, harsai ta gaji da zaman shige da fice sann zakaga tay shiri ta fice kasuwa wajen business dinta kafin nan sai ta dawo da can yamma.


Fanninsu Anty mojushola kuwa bakaramin kullatar hajya khdijatu sukayi aransu ba musmamn ma da suka san da cewa aynzu dan uwansu alhaj bello yana musu kallon wanda basada gaskiya.


Sosai anty moju take baza mulkinta cikin hargagin borin kunya.


sune da laifin amma kuma sunfi kowa hatsala da yin tsananin fushi da nuna cewa suna gaba da kowa. Duk damuwarsu sudai sunfiso ace ita da sukayiwa laifin ita ta saukar da kanta ta zo hargidan ta basu hakuri.


Hajy khadijatu tana da saukin kan da zata iya yin musu hakan dan kokadan batason fitina kuma Allah baiyi ta da girman kai ba, saidai babban dadarta hajy maimunata ta dau zafi sosai akan marinta da mijinta yay, snn tay mata iyaka akan su anty moju tace mata sam bata amince mata dataje har gidansu snn ta basu wani hakuri ba musmmn ma akan gaskiyarta.


Haka suke zama haryau su anty moju shola basa amsa gaisuwarta basa ma son wani abu ya hadasu bare sumata magana dan gani suke ta gama da dan uwansu bello.


Hjy khadijatu bata wani jin dadin yanayin nasu sosai sabida fushin nasu yana bala'in girgiza mata duk wani nitsuwa da kwanciyar hanklin zaman aurenta ata fannin mijinta sabida shi mutum ne da baison amsar laifin yan uwansa acikin sauki ,ta lura da cewa borin kunyar tasu kadai ma yana raunana masa zuciyarsa sosai dan har gani yake kamar taurin kai kawai takeson nuna masa da girman kai irin tasu na matan hausawa shiyasa taki sakin fuskanta da su haryanzu.

.


Ata fannin Ahmed kuwa tun isarsa jos bai iyayin ma yayansa bayanin komi ba har saida ya huta sosai snn yaci abinci sann suka zauna suka fara tattaunawa.


Brother hamzat yana da few contacs dayayi contacting awajeje kala kala domin a abincika masa komi da komi game da rayuwar Adiaha dana iyayenta dan su tabbatar da kima da kuma darajarsu.


Daga can kasar waje ma har brother kazim ya biya kudi yay hiring private investigators yau ne aka kawo masa dukkan wasu bayanai akan familyn Adiaha, komi an tattaro musu acikin file including family background, education, Level of IQ, blood group, Heredity sickeness irinsu genetic diabetes, cancer,  malformations, da blood diseases, mental illnesses,harda blood counts dinta.


Komi da komi saida sukasa aka binciko musu basu kyale koda kwayar zarra na information din su ba..ahakane suka san cikakken labarin abunda ya faru atsakanin kakarta hajy hajara ayayinda ta kawo miji daga yola da tace zata musulunta da irin rikicin da akayi


Private investigators will tell u evrything about ur clients life including time date where and when.


Hakan yasaka suka samu cikakken ilimi akan su batare da saninsu ba, Anan ne Ahmed ya jijji irin rayuwar da Adiaha tay abaya, duk sunayen samarukanta da yanayin yadda tay rayuwa da su, wanda yasaka ya dadaji aransa kamar kawai taimaka mata kawai zaiyi amma badon takai da ya aureta ba dan ya lura kmr bata da class sam sam.


Yayunsa kuwa duk idonsu arufe yake akan son dan uwansu dan duk yadda yake nuna musu adiahar ce kawai ta matsa tana sonshi haka suma suke kallon abun a brain dinsu. Tun daga nan inda yake fassara musu ita ta rasa kima da darajarta na ya mace gabaki daya. Shirin auren nasu sai ya zamo kamar temakon ta kawai zasuyi amma bawai dan ta zame musu wani abu mai matukar muhimmaci ko daraja ba.


Har gara gara ma abokinshi banji idan sunyi waya yakan tuna masa da cewa Adiaha zata bukaci space a zcyarsa tare da kulawar sa sosai duba da cakwakiyar da ta jefa rayuwarta aciki sabida shi, amma yayunsa kam dukansu babu ruwansu da wann, sai abunda Ahmed yace musu yana so sukeyi, inda ma ace yau zaice musu ya fasa auren da babu fashi suma duka bayanshi kawai zasu bi dan sosai suke da dabiar nuna cewa nasu nasune na wani dan banza.



Bisaga yanayin yadda aka gaya musu ake aure a al'adar garinsu adiaha suka hau tsara kominsu dan su zamo ready dan Kirar kakar tata kawai suke jira domin suje yola suji me ake ciki kuma.


Ahmed ya mugun matsuwa  akarkare komi dan yau yake cika sati guda awajen amma duk ya matsu yanason yaga angama ya koma Abuja bakin aikinsa.


Ata fannin Adiaha kuwa jiyan wani sabuwar dare ne agareta mai cike da tsananin firgici da dumbin damuwar rashin gani da kuma jin Ahmed koda awaya ne.


Tunda aka kaisu gidan kulawar taga kowa na bacinshi peacefully amma ita Sam ta kasa iyayin baccin dan daga ta runtsa kadan saita fara mafarkin cewa gatan nan da kayan aurenta amma sosai kayan yakeci da wuta sai kuma taga ta fada awani irin rijiya mai tsananin duhu da ban tsoro.


Hanklinta sosai ya tashi da irin wann mafarkin dan acikin daren kusan sau uku tay irin wann mummunan mafarkin kuma duk abu dayane yaketa maimaituwa


Batadai san ma'anarsa ba amma yanayin yadda take ganin kanta acikin ha'ulai acikin mafarkin yakan sakata jin tsananin fargaba da tsoro tare da nanikakkyar kokonto akan batun Auren nan nata da Ahmed.


Yadda taga rana jiya hakan yau ma taga dare


Da sassafe ne ta samu tadan runtsa kadan kafin lokcin tashinsu yay dan shiryasu.



Tana cikin baccin taji kamar ana tabata tana dan farkawa taga wata tsohuwar mata tana ce mata lokcin wankansu yay..da kyar adiaha ta sauka akan gadon tana share kan kumburarrun idanunta da suka haura sama tsabar bacci bai ishesu ba.


Tsohuwar matar ce tay mata jagora aka kaita har wani dakin wanka inda aka shirya wani tangamamen traditional sit bath bowl da kuma ruwan wankan dilka da akeyiwa amare. Towel din jikinta ta cire gabaki daya ta aje akan cliff hanger duk ta kasa iya daga idonta sama ganin yadda tsohuwar ta kure surar jikinta da kallo da wani irin yanayin kyabe baki da gulma a fuskarta.


Da kamr bazata ce mata komi ba harsanda ta jawo ta kusa snn ta dube ta sama da kasa da harshen yarensu acikin salon karin magana tana cewa "jikin mace tamkar rubber yake wanda indan aka jashi zai dawo dede amma ba tear tear rubber irin wann ba. Da Wani irin kallon rashin fahimta da jin haushi Adiaha tabi matar musmmn ganin yadda take jan fatar jikinta snn ta turo baki gaba tace i dont understand. What do u mean by dat?


Matar ta kyabe baki ta dubeta a tsaye tun daga kan nonowarta har izuwa kan cikinta, da cinyoyinta da kuma kasan mararta snn ta dafata ahankli cikin yanayin fada mata gaskiya tace .."Nne, My doter, ur body look loose,i bet u most have slept with so many men or have been married before? Why did u look older than ur age?


Adiaha tay mata wani irin kallon irin 'can pls mind ur own business?


Murmushi tsohuwar tay snn ta dafata ahankli tana cewa "Aure zakiyi yan mata ,jikinki shine zai dauki kashi 70% na duk wani wahalar zaman aurenki (ya akayi kina karaman yarinya mai kankantar shekaru amma jikin ki baida karfi sam sam) ta ja fatar adiaha ta sakeshi tana cewa "ur body lacks its elesticity, tace "my dear This your body will not last long ooo..irinku ne daga haihuwa daya jiki ya ragwabe tayay kenan zaku iya rike mazan zamanin nan?


Ayanayin damuwa sosai Adiaha ta kalle jikintan sosai, snn tace " i dont know, what shud i do maaa? Cikin sauke ajiyar zuciya Matar tace inde kinason jikinki ya dawo hayyacinshi dolene sai kin dauki lokaci anan kina shirya kanki batare da kin nemi namiji ba..


Muna da duk wani abunda zamuyi amfani dashi domin a gyara maki jikinki ciki da waje dats if u so wish.


Cikin sauke ajiyar zuciya da kokonto adiaha tace " ok, zanyi tunani akai.


Matar batace mata komi ba ta bata waje dan tasan irinsu daga angaya musu gaskiya zasu fara tunanin kudinsu ake so aci. But in her heart she really pitty adiaha.


Hankli kwance Adiaha ta shige cikin bahon ta zauna ruwan zafin na turarata sosai ayayin da tunani kala kala suka shiga dawo mata mind dinta, she is soo woried akan Ahmed, ta damu sosai akan batun yuwar cimma burinsu ayau, tunanin hakan bakaramin faduwar gaba da bugun zuciya yake saka mata ba, sai can snn ta soma tunani akan abubuwan da matar nan tafada mata akan jikinta dazu. Ita dai harynzu a brain dinta bata yarda da cewa jikintan nan bazai iya jure wahalar zaman aure ba, "aure is not about sex and sumbmission? Well, she had sex tun tana 15 years,tasan dai she is very good in bed izuwa yanzu, ta iya sex styles kala kala, dan datake karama kafin tagama scndry mazan da sukayi saurayi da budurwa da ita in suna sexing dintq wasu har suma sunayi ajikinta tsabar ta iya sosai. Saidai komi yana iya canzawa da shekaru, tasan dai datake karama sosai kafin ma taje tafara karatu a  university maza dayawane suke kwadayin jikinta har takejin ko farinjini ne yay mata yawa. But during her university days tasha wahala dan sosai ta fahimce cewa ba hakan ba ne, kawai kowa rabonsa yake dauka ajikinta sabida batasan darajarshi ba, tunda ta fahimci hakan saita soma ganin salo salo na yaudara da walkanci kala kala daga wajen maza. Har ya kaiga maza sun gama raina mata hankli kowa yakanzo yayi manipulating dinta ne da kalman baki inya samu iya abunda yake so ajikinta sai ya rabu da ita koma yaci mata mutunci.


Not long bayan ta tuba da harkan biyewa maza ta gamu da doc Ahmed and she tot dat namiji irinshi nadaban wanda yazo daga wani waje zai iya sauya mata rayuwarta na har abada. 


She is bruised, hurt, and used many times by men shiyasa kwata kwata bata da cikakken nitsuwa acikin zuciyarta game da irin namijin datake so arayuwarta, sau tarin yawa kawayenta suna gaya mata cewa itace da laifi da take nunawa maza cewa batasan darajar kanta ba,.


Asalin Adiaha irin matan nan ne masu sanyin zuciya,helpless,hopeless and self critizing, gani take kamar kowace mace ta fita sa'a shiyasa duk sanda akazo mata da kalaman soyayya na yaudara take saurin amsarsu da wurwuri dan itama so take tay rayuwa mai dadi irin na sauran yan mata. Bata tacewa bare kuma tantacewa.


Idan taga kawayenta nayi wa maza yanga sai taga kamar sunfiye nuna isa ne da rayuwar karya ita kuma aganinta saukar da kai wa namiji shine hanyar da zaisaka yaji yana sonka. Haryau a haka take daukar karatun maza. Wanda suke gaya mata gaskiyar kuma gani take kamar basusan me sukeyi ba. Deirs nothing wrong in being soft and kind, inta fadi hakan sai taji kawayenta suna ce mata not to men of this generation.


Yes,koda ace ma wani bin kawayen nata sunada gaskiya wajen cewa wasu mazan mugaye ne mayaudara ne amma batajin kamar doctor Ahmed dinta yana cikin irin wayann mazan da ake fassarasu


Tun haduwatta da shi shine kadai namijin da bai nemeta akan gadon shi ba, hatta romance din sai a wann karon daya dawone taga ya bata fuska har yana taba jikinta. Tasha jin labarin cewa only real men who loves u truly sune sukeda self control kmr doc Ahmed din. Shiyasa kowani rana takejin tana karason shi dan shine kadai ya fito daban acikin dukkan majazan datayi mu'amala dasu arayuwarta izuwa yanzu.


Gani take kamar asalin sonta yakeyi,shiyasa bayason taba jikinta a araha kamr sauran maza, dan babu wani namijin da zai ganta full mace tsayayya har ya iya danne sha'awa da kwadayinsa akanta sai shi،.


Idanuwanta a lumshe take wann tunanin ayayin da soyayyar Ahmed uake dada ninkuwa acikin ranta adede wnn lkcin motsin datajine yasata dago kai ta kalle wasu mata subiyu sun shigo.


Dayar matar tace

Adiaha Kiyi sauri ki taho ki shirya lokcin cin abincinki yay.


A ladabce ta amsa mata sann ta sauko kasa, ta dauraye jikinta tay asalin wanka snn ta daura towel dinta ta wuce wani killataccen daki.


Tasaka hannu zata jawo wani towel din kenan taji anbiyo bayanta a sadade  gabanta ne yay mugun fadi ta juya sai taga wata mata sanye da mayafi akanta ta shigo.


Lokci guda taji kirjinta na bugawa matar na karasowa kusa taganeta da wani irin shauki suka rungume junansu sosai dan saura kiris ya rage tay ihu tace grand ma, matarce tay maza wajen toshe mata baki.


Hawaye taf idonta ta riko kakar nata hanmunta na rawa sosai tace 'grand ma har yaushe kika iso?


Murya kasa kasa tace

Jiya naxo cikin dare jikata.


Tace Ahmed ne ya kiraki ko? I know he will ai na fada maki yanasona sosai,  Grandma i almst tot dat hala bazaki xo nan ba ,komi ma baxai faru dani ba,pls help me i just cant losse Ahmed..


Kakar tata tace shushhhh snn ta ciro wasu kaya nadaban ta mika mata tace" banda lkcin yin maganan anan kiy marmaza ki saka  wyann kayan ajikinki, naxo nan ne a matsayin masu kawo muku abinci..huryy up befor thy notice us Muyi mubar nan our flight is in 30 min


Da mamaki Adiaha take kallonta tafara shiri cikin kankanin lokci suka sace jiki suka bar gidan suka kama hanyar airpot atare Isarsu keda wuya suka samo baifi saura minti 5 jirginsu ya tashi ba.


Duk farinciki ya mamaye adiaha batama tunanin komi aranta alkcin harsanda jirginsu ya tashi snn ta juyo ta kalle garinsun zatay ma kasarsun bankwana sai kuma taji wani irin aranta jin kamar rayuwarta gabaki daya ta budawa wuta ta konashi. Ahankli komi ya shiga dawo mata kanta tafara tuna cewa "hala fa shikenan dagayau din nan bazata kara dawowa nan garin ba nahar abada..the tot of loosing all her family strike her badly, sai taji jikinta ya mutu murus da jimamin rasa su. Tun daga nn tay shiruuuu tanajin grand ma tana ta mata bayani akan yadda sukayi dasu Ahmed.


Har tagaji tau shiru adiha Bata amsa ba,dan tunda ta aje kanta akan kujera take kukan zuci, she remain sobby and emotional har suka iso garin yola da kakarta.


Wani hadadden anguwa aka kaisu na masu shi.



Gidan alhaji Aliyun babbane dake shidin babban dan kasuwa ne.


Yaransa duk sun girma sunyi nasu gidajen har jikokinsa wasu sunyi aure, matarsa ta fada masa komi akan batun lamarin Adiaha shiyasa bai damu da kawota da tay ba. Tun isowarsu gidan Adiaha takejin kanta daban duk taji kmr ta rasa nitsuwarta, duk damuwar rabuwa da gida sai ya rufeta ta rasa wani irin tunani guda daya zatayi.


Da kyar ta iya cin abinci tay wanka ta fara bacci saboda dama jiyan bawai baccin ta samu ba. Yanayin Adiahan ne yasaka kakartan ta nemi abata lkci ta dawo hayyacinta dan tasan akwai wuya da rudani acikin wann lamarin nan nata.


Ita kanta shaidace ba abu mai sauki bane rabuwa da iyaye da yan uwa, ba abu mai sauki bane rabuwa da rayuwar daka taso aciki tun kana dan karami. Tasan Dolene tadan bawa Adiaha dama don ta samu space din da zatay tunani mai dan tsawo akan lamarim rayuwarta.


Ya kasance duk wani kalar hukuncin da zata yanke akan rayuwarta ya zamo nata ne ba abisa tursasawar kowa ba.


Daga can gidan fattening kuwa anjira aga fitowar Adiaha amma sai shiru.


Dake sunada client dayawa sai basu damu ba sundauka tana daukar lokcinta me wajen shiryawa, hatta waccan tsohuwar data dan bata shawara tay tsammanin cewa Adiaha zata yi tunani mai kyau tasaka a daga aurenta dan abata cikakken lokacin da zata kimtsa jikinta amma sai shiru.


Har wajajen karfe sha daya na rana da basu ganta ba yasa akaje dakin aka duba sai akaga bata nan, dudduba ta sukayi agidan kafin suka aika gidan iyayenta inda atake hanklin kowa ya tashi aka fara neman Adiaha..


Iyayenta da kawunanta kowa ya bazama gari lungu da sako suna nemanta amma sai shiru. Mahaifinta yace xaiy filing complain wa hukuma mahaifyarta tace masa a'a, su jira ta cika 24hrs.


Hakanan sukayi wunin su acikin rashin nitsuwa da kwanciyar hankli sai can karfe 7 na dare suka kama hanya zasu kai complaint ahanyar sune wani dan aika ya taresu da wasika wanda basusan daga ina ya fito ba.


Dan uwan Mahaifin nata wato mr uno shine ya bude takardan yahau karanta musu da karfi takarda ne mai dauke da kalaman datazo musu a matsayin kalma mafi muni da saka tukukin bakinciki da dukansu suka fahimce cewa sakon daga wajen mahaifyarsu ya fito.


Tasani sarai zasu nemi yarsu Adiaha, snn tabbas iyayen Adiaha suna da cikakkem right susan irin rayuwar da yarsu ta zaba ma kanta shiyasa yau batayi niyyar boye musu komi ba. Koda bazasu amince ba sudin iyayenta ne, komin lalacewar lamarin tasan sune sukafi kowa iko da ita asama da uban kowa tunda sune suka haifeta.


Babu amfanin boye musu abunda ake ciki game da rayuwar yarsu

Dan haka bata ragar musu duk wani bayanin da ake ciki ba. Dukan wata gaskiya da basu sani na saida ta fallasa musu snn ta gaya musu cewa Adiaha tana wajenta a yola..if they care to talk about it, su zo har yola asasanta.


Wani darene agaresu mai cike da girgizarwa da tashin hankli hade da takaici da tsananin bakinci, yau sau uku mahaifyar Adiaha tana suma ana tada ta.


iyayen ta mazan kuwa yadda kasan anmusu wani mutuwa data girgiza su hakanan suka dulmuye kansu duka cikin duhun jimami da fushi mai tsanani.


 Cikinsu duka babu wanda ya samu runtsawa acikin daren har izuwa washe gari 


Dukansu sun taru a tsakar gidan amma an rasa mai karfin gwiwar yanke wani hukunci acikinsu dan sun riga sunci alwashin cewa bazasu taɓa taka inda mahafiyarsu take ba har su mutu.



A Fannin gidan Alhaj bello jimada kuwa yaune suka farka da kyakkwan labari daga wajen babban dansa kazim bello jimada, inda ya sanar dasu cewa komi ya kammala sufara shiri domin komawa sabuwar luxury mansion dinsu na family a anguwar garki.


Murna da farinciki awajen Alhaj bello jimada yau bazai iya fassaruwa ba,...


Wann din shine babban burinsa na rayuwa tun safe da dansa ya sanar dashi cewa komi ya kammala zasu iya komawa acikin satin nan yaji kamar yahau sama yay rawa tsabar murna


Yau kamar zai zuba ruwa akasa yasha, duk yadda hajiy khadijatu taki saida ya jawota sukayi rawar farincikin hakan atare, he is soo happy, yoruba music and jazz all over the house kamar ana party, kafayat sai murna takeyi tana rawa tana tafi fiyeda kowa aganin ta da ita za'a shiga sabuwar gidan nan a matsayin ta na amaryan Ahmed damilare jimada,.


Atake ya kira yan uwansa su anty mojushola ya gaya musu news din da dansa kazim yay breaking masa yau da safe. Daga can ma murnan sukeyi sosai duk dama badasu za'a koma can ba, amma bazaka iya tantance dumbin farincikin da suka shiga ciki da familyn dan uwansu zai bunkasa ya kasance awaje guda ba.


They family are finnally going to live together as one, shima dan uwansu zai kasance mai alfahari da gidansa sa zuriarsa tun kafin nan ya mutu yabar duniya. 


Wann labari na sabuwar gida shine yadan dedeta komi tsakanin su hjya khadijatu da su anty mojushola aka bar gaba agefe aka dawo ana murna atare.


Atake kafayat da anty ramatou suka kawo shawarar cewa ahada babban taro na waliman murnan komwa babban gida as a whole family of jimada.


Ranar kalar adduar da brother kazim yasha bazai kayyadu ba dan hatta mahaifyarsa saida su anty moju suka tuno dan kawai su kara sakawa hajya khadijatu jin kishi aranta amma itakam batama san sunayi ba.


She is genuinly happy da yaran kishiyarta shiyasa suma suke respecting dinta sosai suna bata gata irin na uwa dan bata taba nuna musu bambamci ko muzanta wa ba. Adacan ma kanwarsu zainab moturayo itace mai matsala amma tun da tay aure shikenan ta mance da duk wani bakin hali.


Dukansu sunsan They lived as one family sabida kokarin hajya khadijatu ne wajen iya hakuri, kau da kai da dauriya da halayyar kowannensu dan tay fama dasu amma tay juriya harsaida kowa ya fahimceta acikin yawan shekarun nan.



Yau na musamman aka tada zumunci aka dawo ana raha ana hira kamar basune sukayi fada last week ba, Agidan alhaj jimada yau akayi abinci aka ci akasha akayi addu'oi..


Wani bidirin murnan ma bai tashi ba saida sukayi zuga akaje duka ganin gidan a anguwar garki,


Sosai aka kyafe gidan aka masa fari da ash din fenti dake kalar gate din gidan ash colour .


Komi na gidan is brand new, babban gidan sama ne mai shashe sashe har 

Gida takwas aciki


Babban bungalo dake gaba wanda shi zaka fara gani daga bakin gate shine bangaren iyayen nasu,sashuna biyune da babban falo da wani sashe na daban mai kyau da aka gina naa baki self contain ne.


Dayan duplex flat din kuma na Anty adizat ne da yaranta, dayan kuma na anty nurat da brothe hamzat shima da yaransu sai wanda yake baya na Ahmed ne.


Kowani bangare akwai 3 bedroom da isashhen falo mai dinning area da full rectangular size kitchen da bathrums


..wajajen parking motocin su kuwa guda biyu ne gari guda. 


Sai akayi katon family lobby a main house akasa snooker table da blue pond swimming pool dan madaidaci.


gidan is perfect and amazing, kafayat tay imagining din yadda aurenta zai kasance one in town idan aka kawo ta wann hadadden sabuwar gidan a matsayin amarya. She have been imagining yadda itama zata baza mulkinta agidan inta haifowa ahmed yayn sa. The whole stuff is going to be fun and everlasting.


She is over excited, Tun komawarsu gidan ta kira mahafiyarta ta shafa mata labarin irin kyaun gidan da girmansa da kudin da brothr kazim ua kashe wajen furnishing musu gidan da kayan alatu na zamani.



The whole weeek suka fara tunanin shirin welcoming party and walima na komawa gidan duka atare. 


Alhaj bello jimada yace yana sone akoma gidan ranar asabar dats in 5dys time. Ahaka akabar maganan kowa ya fara yar shirinsa na komawa sabon gida. Duk dama an siye musu komi amma still wasunsu sanda sukaje shpping domin su kara fayyace komi nasu.


Alhaj bello yana cikin tsananin farinciki da babban dansa kazim tun ranar da ya gaya musu wann maganan basa wuni basuyi waya ya saka masa albarka ba.


Brother kazim daya fadawa Ahmed irin murnan da iyayensu suke ciki shikansa yasha mamaki ya kuma ji dadin hakan aransa sosai duk dama baison zama tare da family house, but yasan inhar ya fito ya furta hakan yayunsa hala bazasuji dadi ba shiyasa ya danne abun aranshi kawai yabiye musu aka sha shagali.


Suna kan jiran kirar kakat adiaha, yau kwana biyu kenan da zuwansa jos amma basu kirashi ba tukuna,in some part of his heart yanason ace anfasa yin auren nan amma kuma tunanin halinda adiahan zata shige cikine yake bala'in kashe masa jikinsa sosai.


Ata fannin su Adiahan kuwa kwana biyun gabaki saya a sukurkuce kwakwanrta sa tunaninta yake musmmn ma da grand ma dinta ta gaya mata cewa tagayawa iyayenta komi tun ranar amma haryanzu basuce komi ba tukuna..


Sam batajin sauki acikin ranta, tay ta tunani akan iyayenta amma kuma son datakey wa Ahmed

Yafi rinjaye yay nisa sosai acikin zuciyarta.


Grand ma dinta ne take yawan bata shawara akan rayuwarta.


Wani bin kuma alhj aliyu mijin grand ma dintan yakan zaunar da ita yay mata nasiha mai shiga jikiu akan zancen canza addini datace zatayi.


Yace mata karta yadda tace sabida namiji ne zata canza addininta no matter what. Sabida in har tay hakan, babu shakka zatazo tay nadama marar amfani.


Snn batun iyayenta yace mata duk rintsi duk tsiya kartay sa insa dasu saidai tayita basu hakuri harsu huce inhar ta amince cewa bazata iya hakura da abunda yake cikin zuciyarta ba.


Acikin kwanaki biyun nan sosai suka soma fahimtar kamar itace take son Ahmed din sosai amma bakamar yadda shi yakesonta ba.


Har tausayi take basu sabida duk yadda suka bullo mata sai ta zille, bata son kwata kwata ace mata ahmed baisonta, daga an fada sai tafara kawo dalilai tana kareshi.


Sukansu a yolan sun yi ikan bakin kkrinsu har sukayi shiru suka kyaleta da ra'ayinta sunamai mata fatan alheri akan abunda tasaka agaba..


Ranar tuesday din Adiaha da yamma alhaj aliyi yakaita wajen wani imam na babban masallaci ta karbi addinin musulunci abunta snn aka dan fara gaya mata abubuwan daya dace tafarayi a matsayinta na musulma.


Anan ma saida aka kara mata jan kunne akan karta karbi addinin sabida wani cikar burinta ko akan namiji duk Adiaha tace taji ta gani.


Sunan data zaba makanta shine "REEMA" and She goes by Miss REEMA BASSEY cos she wanted an anynomys name wanda kowa zai iya kiranta dashi batare da an kawo maganan canjin addini ba.


She was fine for a bit sabida wa'azi da nasiha da aka dinga mata akan sabuwar rayuwar data daukar makanta beyond all odds.


Ata fannin iyayenta kuwa Har sai Bayan kwana uku da tafiyarta yola snn iyayen nata suka dan samu cikakken nitsuwa da sassauci daga cikin bakincikin da suka shiga ciki..


Yau Ranar tuesday da sassafe kowa ya taho a shirye suka hada family meeting a tsakanin su yasu yasu suka yanke hukunci akan abunda zasuyi da lamarin adiaha 


Mahaifinta mr bassey da yan uwansa na jini mr udo da mr effiong suka yanke hukunci zuwa yola.


Mahaifiyarta mrs grace ma tace itama dolene aje da ita ayi komi agabanta dan inna tsinewa ta tsine ma adiaha ido da ido dan ta huce takaicin bakin cikin data saka ta aciki yan kwanakin nan..tun anan iyayen nata suke cikin nadaman haihuwar ta da sukayi musmmn ma babanta mr baseey dayakejin kamr zucyarsa ta kusa bugawa sabida bakincikin rayuwa.


Basuda isashen kudin jirgi hakan yasa suka hada kudi suka sauka agarin jos daga nan suka dau shatar mota yakaisu har cikin garin yola inda sukayi isar dare wajajen karfe goma da rabi dan haka suka nemi hotel suka zauna da niyyar washe gari da sassafe zasuje gidan hajy hajara ayita ya kare.


Adiaha was kind  of excited about her new religion identity danko bacci batay yau ba, she likes he new name very much, har ji take inama ace Ahmed  was der lokacin data sauya komi nata,maybe haka da suna dayazaba mata dashine zata dinga amsawa. Saidai tabi raayin kanta ne sabida kallon zargin dataga hjy hajara da alhaj aliyu suke mata na tunanin ko duk akan ahmed taje wayann abubuwan da rayuwarta


She dont want them to go againts her shiyasa tajine ta nuna musu komi dan ra'ayin kanta takeyi badon ahmed ba, while deep down in her heart she just want to fit in perfect into ahmed's world a matsayin matarsa na har abada.


Mafarkin ta kenan, babban burin zuciyarta kenan, muradinta, da kuma farincikin ruhinta taganta atare da Ahmed suna wani rayuwa na daban mai bala'in dadi.

*Wanda basuyi saving contact dina ba suyi SURAYYAHMS 08060712446,then reply with saved thank u**KISHIYAR ƘABILAH...14*



BY SURAYYAHMS.


Washe gari.


wajajen karfe biyar da rabi na asubahi iyayen Adiaha da uncles dinta suka farka a barci suka hau shirin zuwa muhallin mahaifyarsu hajya hajara (mrs chidara).


yanayi ne mai matukar wuyar dauƙa agaresu dan dukkansu sun farka ne da tunanin yaune zasuje su kalli fuskar mahaifyarsu bayan sun shafi shekaru sha bakwai batare da sunga junansu ba, dan a Lokacin da ta barsu a garin calabar ta dawo yola kwata kwata su Adiaha basufi shekaru 10 ba gashi duk sun cika shekaru asihirin da bakwai yanzu..


yau yadda kasan dutsi haka fuskan mahaifin adiaha ya kasance. Babu wata annuri Sam baison yin wata dogon magana bare kuma murmushi dan ayadda kasan kurma hakanan ya maida kansa dan bakincikin biyune ya hadu masa ayau acikin ransa yake masa ciwo da radadi bana wasa ba.


Kallo daya zaka masa a karo na farko ka fahimce cewa yanacikin tukukin takaicin karya alkwarin daya daukar makansa na cewa bazai taka inda mahaifyarsa take ba har abada ,na biyu kuma takaicin yarsa Adiaha ce data watsa masa kasa acikin idanunsa data bari  wnn mummunan tarihin ya memetu acikn zuri'ar su.


Kusan A zaune ya kwana cikin radadin zuci da tunanin yadda zaiyi ya jure wani asararar ta rasa babban yarsa kmr yadda yay asarar mahaifyarsa.


Yaso ace yasan yaron da yarsa Adiaha take hauka akai din nan dasai yaci alwashin babu abunda zai hanashi kashesa har lahira dan bayaji aransa kmar bakin cikin da suka sakamasa a zcyarsa mai goguwa ne har abada.



Karfe 5 saura Hjy hajara ta shigo guest room ta tashi adiaha dantayi sallahn fajr kamr yadda jiya aka fara koya mata.


Tana tsaye tana gyara mata har tay alwala snn tafara koya mata sallah harsai bayan ta idar ne ta koma bacci.


Ata fannin iyayen Ahmed kuwa cikin zumudi yau suka farka kowa yana dokin shirye shiryen komawa sabon gida, yaune wasunsu suka shirya zuwa siye siyen dan abunda baza'a rasa ba da shirin gagarumin walimar da sukace zasu haɗa dan su shashe snn su nuna murnansu.


Yau da wuri Kafayat ta farka daga bacci ta fito cikin gidan tabi ta gaishe da kowa yadda ta saba, itace ta shiryawa kowa breakfast dinsa nayau akaci akasha snn ta tsaftace gidan ta shirya zata fita kasuwa da niyyar inta fice din zata kai pictures din sashen Ahmed na mansion din wa home decorators and designer dinta dan susan irin kalolin da za'ayi mata amfani da shi in sukayi aure.


Aranta har ta gama amincewa tare da yanke hukuncin cewa itace matar Ahmed dan haka ta sallamar wakanta iko da shashen Ahmed din na sabon gidan gabaki daya.


Hakan ya saka takeji aranta kamar bazata yi sanya wajen yin tanadin kawata sashen nasu da kayan duniya ba.


Tunda tabar gidan a motarta tunanin datakeyi kenan, Agaban First city mornument bank (fcmb) tay parking motartan snn ta shiga ciki tay filling cash out form aka ciro mata kusan fiyeda rabi na kudin asusun bankin ta wanda take saka ran da shine zatayi saye sayen ta ta aje.


Duk wani lissafi da tsare tsare ta gamayi dan jiya ko runtsawa batayi ba.


Iya Videon sashin Ahmed dake wayarta data dauko shikadansa bazai kyaleta ta iya runtsawa, kowani part na sashen saida ta dauko videon sa, daki, palor, kitchen har bayin gida. Duk sanda ta bude videon ta kalla takanji kamar abunda zai faru na cigaba a rayuwarta gabaki daya take kallo.


Tayita kwana cikin shauki da tunanin kanta dana Ahmed suna soyewarsu acikin wann dankakkren sashen yafi sau tamanin Shiyasa take ganin kamr idan ta dada kawatawa shi da kayan alatu hala soyayyar tasu zaifi armashi.


Tun jiyan fuskarta yake cike da murmushi farin ciki sosai yake mamayeta sam ta kasa iya danne annurin dake zubowa akan kowani saukar murmushinta.


dan madaidaicin jakar kudin ne ahannunta ta fito dashi ta bude motar ta kenan zata shiga sai taji wayarta na ringing ta duba taga lambar ashe mahaifyarta ne.


Sama da kasa tay rolling idanunta bata amsa ba harsaida ta shiga motar ta zauna ta kulle har kusan zai yanke snn ta dauka ta saka a kunnenta tace "mum..Da harshen yare hjy fatihat ta tsareta da masifa tana cewa "hold it..i just saw an alert? Wai Ina zaki kai wann uban kudin tukuna? 


Cikin runtse ido da budewa kafayat tace "mum bazan iya miki bayanin komi ayanzu ba..inason ..Tun bata karashe kalamn ba cikin tsareta hjy fatihat tace "shur up jare, koma miyene kke so da kudi bazaiyu ba kafayat..i will not allow u waste my hard earn money kinji mena ce miki?..kodan kinga komi nasaka sunanki ne akai zaki faramin barnan kudi? Haaaaa, Kafayat tace mum pls now, inada bayani akan hakan just trust me, hya fatihat tace 

" _Rara oti rara_ haaaa kafayat, ni bazan taɓa yarda dake ba fa, and if u touch that money kafayat ahhhhh Ahhhhh consider urself a gunner cos i will soo deal with u errrrn?Idan na ci ubanki ma Wallah sai an kasa ganeki.cikin turo baki kafayat tace mum amma ko tambayana mezanyi dasu da bakiyi ba


Tace bazan tambaya ba, ke kin tambayeni kafin ki cire wnn uban kudi? "Harke kin isa ki kwashe min rabin kudina a banki? Toh wai Wani Gidan xaki siya ko Macca zakije? Kinci sa'a dana ga alert din nan bn turo maki police men an kamaki awajen ba,nasan kinsan zan iya cos dat money is mine karki bar sunanki da nasaka akai yana rudarki. Karki mance dukiyar ubanki yanacan hannun yayansa maza suna cin duniyarsu dashi u were left with nothing xcept the house dn haka duk wani kudi nawa ne


Kafayat kmr zatay kuka tace mum baki tsaya kinji mexan ce miki bafa haryanzu kede damuwarki shine kudi?


Tace eh,kuma bazanji ba, if u want me to trust you akan dukiyata yanzun nan kixo nasarawa state kisameni kawai, ina can wajen  ALFAH Lamidi, infact huryy up now now ai dama shima yace yanason yaganki,yace min ur matter is a matter of emergency ooo, toh wayasan ma akan kudin nan ne dakika deba min yanzu..he said it seems like sumting bad is about to strike ur life, kafayat bazan fa kyaleki ki jawo ni cikin talauci bafa, what ever it is da kike kullawa da rayuwarki ya tsaya akanki ke kadai ooo karki yadda kijawo ni ciki..

kibar duk abunda kikeyi yanzu kizo nan kisameni.


Cikin rasa na cewa kafayat tace toh naji ina zuwa yanxu, hjy fatihat batace mata uffan ba ta katse wayar ajiyar zuciya kafayat ta sauke dan tasan inhar bata kyale maganan spending kudin nan taje nasarawa state ba mahaifyarta zata iya mata abunda batayi tsammaninsa ba


..daga nan ta juya kan motar bata tsaya ko ina ba tadauki hanyar nasarawa state dake baida wani nisa da garin abuja..



 _Yola:_ 



7:30 am Iyayen Adiaha suka samu isowa babban gidan Alhaj aliyu wato mijin mahaifyarsu hjy hajarat(mrs chidara)


Ransu duka a dagule yake suka shigo ciki basu cewa kowa komi ba mai aiki takaisu babban falo inda suka samu har an shirya musu breakfast maiji da lpya na Abincin yare kmr irinsu _ekpang nkukwo_ _cocoyam_ da _banga soup da tuwo_ .. 


jiyan cikin dare ta samu labarin cewa zasu taho yola gidantan yau daga bakin wani secrt spy dinta wanda agunsa ne take jin labarinsu tsawon lokcin nan batare da sanninsu ba.


Acikin yayanta duka babu wanda yay gaisuwa bare su zauna akan kujerar palonta duk suka ja can gefe suka tsaya atsaye kowa acikinsu ya hade hannu sun mugun daure fuskarsu kmr basu tabayin dariya arayuwar su ba,mahaifyar adiaha mrs grace itace ta daure ta gaishe ta, snn ta gaishe da alhaj aliyu da tuni ganin yanayinsu yasaka ya fita agidan domin yadan basu waje.


Dauriya tay irin na mata snn tafara gaishe da yaran nata tyi musu tayin abincin karyawa duk dama bawanda yace mata tak bare chas.


Kallo daya zaka musu kasan cewa Kowannen su yay kewarta aransa amma haryau ji suke kmr bazu taɓa iya yafe mata laifinta data aikata musu na ficewa acikinsu ba.


Duk wani shan qamshi da daure fuskarsu dake ita uwace agaresu saida tasaka suka zauna saidai kowa yaki kallon abincin nata bare kuma suce zasu ruwa.


Mahaifin Adiaha na zama rai abace yahau kallonta da wani irin yanayi dan zuciyarsa na kuna sosai, out of suffocated feeling yace "mrs hajara,.ta dago ta kalleshi suka hade ido atake idanunshi yay ja yanami tara ruwa yace "where is my doter? I want to see my doter ryt now bana son bata lokaci dan abunda ya kawoni nan garin kenan.


Atake Sauran yan uwansan ma duka suka mara masa baya suna masu kallonta da fushi fushi da daurewar fuska ayanayinsu kowama tambaya daya yake mata na cewa afito musu da adiaha.


Bata tanka su ba saida ta lura da yanayin kowannensu na tsananin damuwa snn ta miƙe acikin nitsuwa tawuce dakin da adiahar take.


Bacci take famanyi taji kamar ana tattabata, da kyar ma ta bude idonta tana dagowa ta kalle grand ma dinta saita mike zaune tanamai goge idanunta acikin yanayin sauke hamma tace


Gud morning grand ma.


Irin kallon datay mata da sassanyar jiki yasata fahimtar cewa da akwai matsala. Tace get up dear".. Atake taji baccin ya watseka.


Tashi zaune tay snn ta riko hannun kakar nata da murya mai sanyi tanacewa "meya faru?


Ajiyar zuciya kakar nata ta sauƙe sann tay mata murmushi irin tasu na manya mai boye damuwa..cikin nitsuwa tace "my dear, iyayenki ne sukazo suna son kallonki. Caraf Adiaha ta sake hannunta snn ta miƙe tsaye a mugun razane batare da tasan tay hakan ba, muryan ta na rawa rawa haryana shakewa tace "my..m.my parents?. Bata amsa ta ba ta kureta da ido snn ta gyada kai tace "kiyi hakuri, nine na gayyace su.


Hannu adiaha ta saka akai tare da fashewa da wani irin ragwababben kuka mai cike da firgici

Tace "Grand ma why now? "Meyasa zaki kirasu "mesa zaki gaya musu ina nan..meyene kike tunani ? Tace Shine abunda ya dace".


Cikin katse ta Adiaha tace no, Tunda har ke da kika haifesu basu fahimceki ba aganinki zasu fahimce ni ne? i am really scared bazasu barni na aure Ahmed ba, inajin tsoro sosai, ni ban shirya fuskantarsu ba grand ma bikonu,kema kinsan My father and mother will join hands to kill me today, ewooo,my own don finish today,.. chaiii i'm finished, ta cigaba da kuka tana cewa But grand ma why now.  Why why Pls meyasa kikay min haka Tafada hawayenta na zubowa kasa kamr ruwa duk ta rude ta birkice da wani irin azaban tsoro mai kada hanjin ciki.


Wani irin rawa jikinta ya farayi shikadansa tafara jeka ka dawo cikin tashin hankli, kanta a mugun dore yake dan batasan yadda zata fuskance su ba, me zatace musu?


Tana cikin wnn zullumin taji an  riko hannunta cikin sanyin yanayi tare da zaunar da ita akan gadon ganin ta mugun razana jikinta na rawa rawa nan hjy hajarar ta saka mata fuskar lallabi sosai snn tace "karki damu my dear, im older and wiser than dukanku, nasan menakeyi, ki yarda dani Wann ne miki lokacin daya kamata ki gaya musu komi da bakinki, decisions dinsu akanki doesnt matter sabida mune zamu dauki nauyinki yanzu,saidai kisani, iyayenki ba abun wasanki bane domin sune silar duk wani rufin asirin dake rayuwar ki, rayuwa babu yarda da albarkan su sam sam baida sauki kuma bazai miki dadi ba, nan gaba i assure u indan akan namijine ure bound to feel alone and unhappy..


Idan kinsan kin gaya musu gaskiyarki yanzu komi zaizo miki da dan sauki anan gaba, amma idan kika musu taurin kai ki tuna suma fa suna da hakki akanki na ci da shayarwa da rainonki da sukayi tun kina ciki har kikai iyanzu, bijire musu ba abunyi bane ko kadan, koda bazaki samu albarkansu ba,karkiyi abunda zai jawo miki fushinsu na har abada.


Ta kara riko hannunta tace "my dear ke jina ne fa i want the best for you bana son raywarki ya lalace shiyasa ma na dauko ki, but Idan kikay aureb nan batare da sannin iyayenki ba ni bazanji dadi ba dan na tabbata da cewa auren nan bazai tabayin albarka ba. Dont u know dat fushin Iyaye tamkar makamashi ne ga fushin ubangiji akan bawarsa? Yau Idan suka furta wani mummunan kalma akan aurenki zai iya binki har abada sabida haka make ur choices wisely .god wont purnish u if u are  being fair to them..yadda zaki musu adalcin shine  kije ki fuskance su kisanar dasu halinda kikeciki..any decision u take is for ureslf sabida rayuwarki ne.


Tunda kakar nata tasoma mata wnn maganan kuka marar sauti takeyi jin zuciyarta na fat fat kamr zai ballo waje dan tsananin fargaba daya lullubeshi.


Tasan duk abunda grand ma tafada gaskiya ne saidai ra riga tasan da cewa iyayenta bamasu brain din fahimtar hakan bane ,zatayi ne dai don kawai tanason aurenta da Ahmed karya samu tangarda daga sharrin mugun bakin iyaye.


Saida maganan ya kammala shiga jikinta da brain dinta snn ta share hawayenta tacewa grand ma din akan taje tace musu tana fitowa yanzu.


Batay mata musu ba ta tashi ta fice a dakin dan tasan hala adiaha tana son ta taro karfin gwiwar fuskantarsu ne.


Tanayin sallama  afalon tagansu a tsaye sun mimmike alaman fushi da kaguwa.. tun ma kafin su jefo mata tanbaya tace musu Adiaha tana fitowa yanzu 


Sai ta kama hanya ta fice waje domin kirawo mijinta dan tasan zasu iya jawo musu hayaniya mai yawa agidan ynxu, anan tabarsu atsaye dukansu kowa ya kau dakansa suna jiran ganin fitowar yarsu.


After like 3 min saiga nan footsteps dinta nan na karatowa ta cikin palon


Tafiya take kirjinta na bugawa da tsananin sauri duk ta rikice ta ciki da tunanin abunda zataje ta tarar aciki.


Tana isowa bakin kofar ta tsaya ta kasa gaba ta kasa bata, ahankli ta dan Lumshe idanunta snn taja wata doguwa kuma nannauyar numfashi snn ta fuske ta karaso ciki jikinta a mugun sanyaye..


Tana yn sallama a palon duka suka juyo suka kureta da idanunwasu..


Sabon Hijabin datayi sallah ne ajikinta purple colour bakaramin kyau yay mata ba..


Tana tahowa kusa iyayen nata tare da kawunanta duka suka tsandare a tsaye acikin tsananin mamakin ganin shigarta na saka hijabi.


Jiri jirine ya so ya kwashe mahaifin nata dan uwansa uncle uno ya rikosa atake. Yanacewa "Control urself brother..


Adiaha ta rusuna kan gwiwarta agabansu, tana yin hakan hawaye masu dumi suka fara zubowa daga cikin idanuwanta, muryanta na rawa ta budi baki zata gaishe su kenan mahaifyarta mrs grace ta daka wani irin tsalle ta cakumota ta wanka mata wani irin balamin mari mai tattare da tsananin fushi.


Cikin harshen yarensu tafara ihu tana zaginta da kowani irin kalma daya fito daga bakinta ayayinda uncles din nata suka hau tayata.


Tamkar zasu daga gidan haka suka taru mata akai kowa na daka mata na tsawa suna masu tambayarta abunda yasaka tay musu haka


Kuka kawai takeyi bata iya amsa kowa ba sabida level of fushinta dataga sunzo dashi. They are all blinded by anger, tasani dama dolene abunda tay ta kuntata musu dan haka bataga laifinsu na haura mata ayanzu ba


"Uve betrayed and disgraced us,kinci amanar mu Allah sai ya tsine miki. Nay nadaman haihuwar yarinya irinki..

Danasan abunda zan haifa kenan dana zubar da cikinki tuntuni, ure a wasted child..a curse to my family. I regret giving birth u..


Adiaha ta runtse idonta sosai cikin kuka sosai tanajin abunda mahaifyarta take ta fada cikin tsananin fushi


Dukkan wani hayaniyar da akeyi awajen mahaifinta bai motsa ba sabida zuciyarsa data kusa bugawa dan baisan me zai soma cemata dan ya huce fushin dake ransa ba.Hijabin daya gani ajikinta shine ya bala'in daga masa hankli, Yatsar Hannunshi daya daga yana nuna ta dashine ya soma rawa rawa, ya budi baki zai mata magana kenan jiri ya debesa sai daram ya fadi kasa yana kiran sunanta acikin wani irin yanayin baqinciki, a mugun razane Adiaha tayo kanshi tana kuka sosai tana mai ambatar sunansa da yanayin tsorata tanamai bashi hkri. Jijjiga shi ta dingayi har saida ya dawo dede Yana dan dawowa hayyacinshi  ya turera akasa saida tay tumbul a rikirkice. Muryan sa mai tsananin bacin rai taji yana cewa "i am not ur father..i am not ur father. Shame on u..Yafara nashi maganan yana zage zage tun daga kan mahaifyarsan har ita yana cewa sun cuce rayuwarshi. Yafara cewa bazai taba yafe mata akan yaudara da karyan datay masa na cewa ta hakura da yaron nan ba.


Cikin yanayin fidda kalamomin tsinuwa 

"Yace mata "a yadda ta yaudareshi ta gudu itama anan gaba sai an mata yaudarar dayafi wann ciwo da saka bakinciki.


Yace mata she is the worst of all of them, harma gara mahaifyarsa bata yaudaresu da karya ba. Ya kara cewa "Inde shi ya haifeta toh yay cursing dinta da samun baqinciki da koma baya acikin rayuwarta.


Adiaha ta mike tsaye a daburce jikinta na rawa rawa da mugun sauri ta fado gabansa ta kama kafafunsa tana ta kuka tanamai bashi hakuri akan ya yafe mata karyay mata wayann mugayen bakin.


Duk yadda ta kasance abun tausayi awajen baisaka kowa yaji tausayinta aransa ba.


Sosai taji ta tsorata da mugayen baki da iyayenta sukayi  mata Yadda ta tamke kafafunsa ya tokareta dashi saida ta isa bakin kofa ,shigowar Alhaj aliyu da hajiy hajara kenan suka rirriketa.


Kukan fitar rai takeyi tana memeta kalaman da iyayenta suka fada akanta "mahaifinta yay mata fatan bakinciki da yaudara, mahaifyarta kuwa tay mata Allah ya isa. Kanta kamr zai hura wuta haka takeji tsabar yay zafi. 


Haka suka rikota suka shigo da ita falon alhaj aliyu ya zaunar da ita agefensa yanamai rarrashinta ganin duk ta rikice cikin kuka.


Hjy hajarar da yayanta sune suke haura ma juna. Cikin fushi tace musu meyesa bazasu bi adiahan ahankli domin suji ta bakinta ba? 

Cikin masifa tace dabiarku na hukunci cikin fushi yasaka adiaha ta dawo haka, ta bijire tay taurin kai snn ta yaudare ku ne sabida tasan bazaku taɓa ku saurareta ba. If she is bad child then u must be a bad parents.


Suka dawo kanta tamkar an sosa musu abunda ke musu kaikayi suka fara tuno mata nata laifin itama,mahaifin adiahar shi yace mata" uwar data bi namiji ta canja addini ta tafi ta bar yayanta itace har zata kirasu bad parents? Uncle uno yace "ure a bad mother too so how did u expect us to be a good parent..mr effiong yace "kece kika jawo mana dukkn calamity dake faruwa a familynmu and god will judge u.


Taja tsaki batace musu uffan ba..


Mijinta Alhaj aliyune yay kkri ya sassaita situation  din bayan kura ya lafa kowa ya fidda masifar dake ranshi snn suka zauna aka taso adiaha agaba aka fara magana ta hankli.


She was finally given a chance to explain herself out. Anan ne suke jin zancen cewa Ahmed din ma bayarbe ne wanda iya hakan ma kawai saida ya dadayi jawo musu ciwo aransu bana wasa ba.


Koda tace ta amshi Musulunci iyayenta basuga wani laifinta har can can ba dan aganinsu laifin kakarta ne itace kawai ta juya musu kan yarsu har ta canza addini.


Alhaj Aliyu yace yay bincike akan familyn Ahmed kuma ya gane cewa basuda matsala.


They are well to do, educated and well known familynsu daga zuria mai kyaune.


Mahaifiyar Adiaha tun anan ta fara fahimtar matsalar da yarta ta jefa kanta aciki..


Sai tafarayiwa Adiaha tambaya akan alakarta da yaron sabida aranta tasan Adiaha must be the one tripping on him, she just LOST in lust, Bata san me take kkrin saka kanta aciki ba.


Iya bakin kkrinsu sunyi dan su sakata ta dawo hayyacinta tafasa auren Ahmed tabisu sukoma gida ko da bazata sauya addini ba amma hakanan Adiaha tace musu sam bazata iya rabuwa da Ahmed ba.


She boldy told them inhar suka saka tabisu tabar Ahmed anan toh su tabbata zasuyi asarar ranta dan kuwa tabbas ta koma gida zata kashe kanta dan bazata rayu babu ahmed ba 


Mahaifyarta sai hawaye takeyi masu sanyi Cikin jimamin tausayin yarta aranta tace ohh god ooo, my poor doter Adiaha big trouble await u..oh god pls! Sai kafa kafafunta take dan Aranta Ta riga tasan Adiaha ta gina tubalin rayuwarta ne acikin imagination dinta najin cewa zata aure namiji kamar Ahmed wanda is almost perfect nd faultless da tunanin zata samu rayuwa mai kyau da kuma kwanciyar hankli na har abada, a tunaninta shine she wll have a perfect life and family with him tunda dai babu abunda ya rasa, snn shi din mijin nunawa sa'a ne.


Gani take kmr Aurenta Ahmed shine zai bata new life,new identity, new peace and new financial security plus new family and new parents.


Wann tunanin ne ya sa ta iya sadaukar da kominta acikin sauki  dan tunanintan ya riga ya bata cewa zata samu abunda yafishi awajen Ahmed.


Tattaunawar tasu sam bata kare acikin dadin rai ba, dan koda komi ya fito fili..duk saida suka fahimce inda Adiaha ta dosa, da alaman babu wanda zai iya sauya mata ra'ayinta dan sosai tay imani da cewa auren Ahmed shine zai canza mata rayuwarta na har abada.


Uncles dinta ne sukayi Allah wadarar da ita suka kama hanyarsu sukayi waje suna masu raba hanyarsu da ita na har abada, mahaifinta ya jadadda mata cewa sun cireta a zuriarsu, yace ko mutuwa yay karta sake ta zo kan gawarsa ya tsine mata taje gata ga sabon rayuwarta. Shima Ya tashi ya fita.


Mahaifiyarta ce ta zauna wajen ta dinga zubda hawaye dan sosai tausayin adiaha ya rufeta ya kuma kashe mata jikinta sosai. Tay niyyar ta gaya mata cewa zata yi mummunar nadamar juya musu baya, da dora burinta akan ɗa namiji dan in akwai abunda yake gaba da rashin tabbas a duniya da sunan shi namiji ne.


Cikin kukan ta girgiza kanta ta daga ido ta kalle Adiaha snn ta mike tsaye tace "lokaci na zuwa da zaki neme mu adiaha.

I wish u gudluck with ur marriage. Tana fadin hakan ta fice itama jiki a sanyaye bata kara juyawa baya ta kalleta ba


Alhaj aliyune ya bi bayansu domin ya kara musu nasiha koda da za su sassauta ma adiaha aransu amma dukansu basu kulashi ba.


Hanklin hjy hajara bakaramin tashi yay ba sai taji tsoro wa rayuwar adiahan bana wasa ba


Tana hawaye cikin lallabi Tace ma Adiaha tayi tunani sosai fa, intasan hakan datay bai dace ba marmaza ta tashi tabi bayan iyayenta tabisu  sukoma garinsu koda zasu yafe mata.


Irin birkicewa da kukan da Adiaha take yi awajen zakayi tsammanin cewa zuciyarta akarye yake sosai amma ina a duk sanda ta tuno da cewa rayuwa zatay da Ahmed na har abada zai taji kamar bazata iya juyawa da baya ba ta gwammci ta rasa komi a duniya amma banda lamaribta da Ahmed dan sosai tasaka aranta.


Haka Taki sam tacema grand ma dinta auren Ahmed is her final wish tunda iyayenta sunki bata goyon baya sun tsine mata ai shikenan itama bata bukatarsu ai akwai Allah. Bayan nan ta wuce daki tanata kuka gashi a musulunci baa ashan giya, dan haka kukan kawai tayi tayi dan abun ya fice mata aranta koda zataji sakat.



Ata fannin kafayat kuwa wajajen karfe sha biyu na rana ta isa nasarawa state ta wuce gidan Alfah lamidi inda ta tarar da mahaifiyarta tana zaune akan dadduma ta idar da sallah kenan ta nemi waje kusa da ita ta zauna

Bayan ta samu nitsuwa tafara gaya mata duk abunda ake ciki da familyn jimada she was so sooooo excited akan maganan komawa sabon gidan dan gani take kmr a matsayin amarya za'a kaita.


After a while bayan Alfah ya dawo daga wajen sallah acikin wani private 

Masjid din gidansa inda sukenan da shi da almajiransa..


Daga dawowarsa ya aika aka kirawo su ciki suka shiga suka zauna akan tabarma, nan suka fara magana mai dan tsayi da yarensu, yafara gayawa kafayat abunda ya gano acikin qaddararta da Ahmed damilare, kafayat taji kamr kanta bazai iya daukawar komi ba, can sai ga kafayat din nan ta fito daga cikin wajen a rikice cikin tsananin fushi da firgici tana kuka sosai ta rike kirjinta datakeji kamr zai balle ya fito waje, kuka takeyi tana girgiza kanta har ta isa gaban motarta snn ta rgwabe ta fadi kasa awajen tanata kuka sosai.


Mahaifyartan ce ta biyo bayanta arikice zata yi waje,Alfahn shima yabita yanamai kara jadadda mata yana cewa "iya kafayat, ki nitsar da yarki sosai fa, inba haka ba both of u will regret.


Ta juya tana kallonshi da fuskan neman alfarma da tausayawa da harshen yarensu ta kuma tsugunawa har kasa tana rokonsa koda akwai abunda zaiyi domin ya temaka ma yarta 


Alfah yace mata ai zancen destiny akeyi duk yadda sukayi qaddarar mutum saiya cika shi, yace mata "kafayat ba matar Ahmed bane" tauraronsu baiyi matching ba sam sam snn daren dadewa kuwa qaddarar kowa zai cika, yace mata destiny can only be delayed but can neva be erased kawai ta riƙe yarta suje sunemi wani mafita acikin gaggawa amma tasani cewa duk evil din da zataje tay aure tsakanin kafayat da Ahmed bazai taɓa yuwa ba. Inhar ya yuwa to tasani yartace zata mutu a ranar da aka daura auren.


Godiya tay masa itama ta bar wajen a rikice tanamai kiran sunan kafayat da tuni takai kanta can waje


Ganinta a kasa tay rigijib ajikin mota tanata kuka wanda hakan yasaka tay saurin tsugunawa kasa tare da rungumeta ajikinta sosai cikin sigar lallashi.



Kafayat dake bori kamar na wanda iyayenta suka mutu suka bar duniyan sai ihun sunan Ahmed takeyi tare da nata tana karyata zancen cewa shi ba mijinta bane na qaddara har saida taso tarawa mahaifyarta mutane awajen.


Da kyar ta kwasheta ta sakata a mota suka bar wajen izuwa gidan babban aminiyar mahaifyarta wato hajiya rakiya. Dukansu yayn goddess of fire ne a harkan tsafin su suka soma shakuwa, hjy rakiyan Itace shakijiyar ta aharkan business snn atare suke duk wani infidelitynsu na rayuwa.


Nan ta kai yarta kafayat dan ta rarrasheta inda suka taru ita da kawartan sunata bata baki duk dama kafayat tay ta bori tana zarginsu da cewa ko biyan Alfah kudi sukayi dan amata karya su rabata da Ahmed dinta. Saida suka sha wuya kafin su kayi controlling din kafayat din har ta rusuna ta dan samu bacci.



Ata fanninsu Adiaha kuwa tunda Kura ya lafa sai adiaha ta taurara ranta ta aje komi agefe saidan in abun ya fado mata kaga tana zubda hawaye musmn inta tuno da kalaman iyayenta aknta.


Tanajin tafara shiga damuwa zata bige da tunanin rayuwarta tare da Ahmed sai kaga kuma hanklinta ya kwanta sosai .



Ata fannin Hjy hajara kuwa tunda hakan ya faru ta rasa nitsuwarta yau din gabaki daya ko wani abincin kirki bata iya sakawa abakinta ba


Tunanin rayuwar jikarta Adiaha shiyafi komi daga mata hankli bama tunanin yadda komi ya kare musu tsakaninsu da familynsu da kuma zuriarsu ba.


Yau har dare ya raba bata samu sukuni aranta ba dan tasan Lamari mai wuya Adiaha ta jefa aknta aciki dan duk wani mai hankli yasan namiji badan goyo da zani ba tunaninta kar Adiaha tay auren nan taje ta gamu da wani sabuwar tabun da bazata iya gogeshi acikin zuciarta a dalilin da namiji ba.


Sosai ta damu, mijinta Alhaj aliyune ya zauna da ita washe gari ya dinga bata ingantattun shawarwari, ciki harda maganan kawo zancen auren Adiaha da ahmed din anan kurkusa dan hanklin kowa ya kwanta.


Dukansu sun manyanta sunga rayuwa shiyasa jikinsu yake ta basu cewa Adiahan ce kawai take son yaron sosai.



Washe gari da safe kafayat ta farka da wani irin zazzabi mai zafi irin mai saka maganganun nan, sai maganan Ahmed takeyi, tana cewa sai ta aureshi, itace matarsa.

Duk dai ba acikin hayyacinta ba.


Rashin ganin dawowarta a jimada family yasaka hajy khadijatu ta kikkira wayarta lokcin tana barci sai basu dauka ba.


Kusan sau uku tana nemanta bata same ta ba, sai can dare kafin nan Alhaj bello ya kira sabida matarsa ta riga ta gaya masa abunda ake ciki na cewa bata samu kafayat a waya ba, sau biyu ya kira hjy fatihat na kallo bata daga ba, sai can hajy rakiya ta zugata akan cewa ta dauka ta gaya masa cewa kafayat din tana tare dasu batajin dadin jikinta ne tana bacci.


Hakan kuwa akayi ta fada masa cewa kafayat na wajenta, as usual sai yadan nuna damuwarsa akanta sabida tamkar yarsa haka yake jinta aransa.


Tunda suka fara wayar hajya rakiya take ta lisafe lisafe aranta amma batace maa kawartan komi ba. 


Duk zamansun nn zagin familyn jimada sukeyi dake ma abun nasu ya hadu da haushin rashi da kuma hassada sabida kowa yasan jimada family sunada kashin arziki azuriarsu shiyasa kaf yayansu suke tasowa  a matsayin hardworking men masu gina kansu da kansu da kuma taimakawa iyayensu .


Bakowa kecin sa'ar samun kansa acikin family mai kyau irin wnn ba wanda babu wata gaba ko fada mai tsanani, bbu kyashi tsakanin yan uwa, babu cin kafa ma juna sai kkrin kawo cigaba da nunawa yan uwansu hanyar cigaban suma 



Washe gari da safen ma saida Alhaj bello jimada ya kira wayar kafayar domin yaji ya jikin kafayat din yake suka ce masa da sauki amma bata farka abacci ba tukuna.


Sam sam hjy rakiya taki sukale maganan kafayat

Da jimada family tun jiya take cewa mahaifyar kafayat akan su dauki fansa, kar ta bar rayuwar kafayat ya kare alalace, kawai ra zage su yage rabonsu ajikin familyn jimada amma haryanzu bata fito mata da maganan cikin sarari ba.



Dagata bangaren Su hajya khadijatu kuwa shiri kawai sukeyi na komawa sabon gidansu 


Yau da sassaafe babban dadarta hjy maimunatu ta kirata take gaya mata cewa nan da wata daya zasu dawo nigeria gabaki daya dan haka ta amince mata afara batun neman wa yarsu yasra gurbin karatunta a Abuja .


Sosai wnn kalma yay wa hajy khadijatu dadi sosai aranta,yau ta kasance cikin nishadi ne marar misaltuwa dan dama can tana da bukatar wani na jikinta wanda zai zauna agabanta a babban sashenta na sabin gida dan tasan cewa danta Ahmed zaiyi aurenshi snn attention dinsa zai fara komawane ta wani waje ba aknta ba.


Bisa ga behaviour din kafayat na kwana biyun nan ma sosai ta fahimce cewa in ta aure mata danta hala Bazata ma kyaleta dashi acikin sauki ba dan taga alama sosaine yarinyar take zumudi akan zancen aurensu .Amma idan har yasra tana zama a gabanta a matsayin yarta hala komi zai iya kasance mata cikin sauki Kuma dama babban burinta ne ta nunawa yasrar gata sosai. 



Bayan kwana biyu.


Yau Ahmed yake kkrin cika kwana goma sha daya dayin tafiyarsa.


Yau da safe tana farkawa yaga sako daga wajen kakar Adiaha da cewa suna son ganinsa da shi da magabantasa.


Kanshi yaji yafara maaa ciwo dan harga Allah bawai son auren na  harcan can yakeyi aransa ba amma toh ya zaiyi yariga da yafara dolene kawai ya karasa..


Tura tex din yay ma duka yayunsa maza bai cire ko kalma daya ba.


Kafin ya kammala wanka ya shirya yay break fast saiga video call na brother kazim daga U.S 


Duk abunda yakey ya bari ya taho Saida ta nemi waje ya zauna snn ya dauki kirar tare da rusuna har kasa cikin girmamawa yahau gaishe shi da yarensu na yorubanci cikin bashi girmansa sosai.


Yace masa sun gama magana da brother hamzat da wani dan uwan babansu uncle bakre , dan haka ya shirya Suje yola yau yau  yake son ayi maganan auren nan agamashi gabki daya .ko musu Ahmed baiyi ma yayansan ba ya amsa masa  da toh acikin ladabi Bayan ya kammala fada masa dukkan abunda zasuyi insunje can snn ya katse wayar.


Ahmed ya kira abokinshi banji yace masa yazo ya rakasu yolar shima, around 10:30 am na safe kowa ya iso garin jos sukayi booking next availble flight to yola su hudunsu sukazo garin yola inda suka dan kama lodge awani five stare hotel dansu shirya kansu.


A fannin adiaha kuwa tun jiya da safe alhaj aliyu da hajy hajarat suka zaunar da ita suka mata nasiha ahead of rayuwar data zaɓa ma kanta, anan ne suka nemi shawarar ta akan maganan auren tundata amince musu shikenan sai suka gayyace magabatan Ahmed din dan suzo sai asamu akarkare komi.



Kafayat kuwa tunda ta samu saukin jikinta takewa mahaifyarta bori saidai dake hjy karimat tana wajen yasaka rashin kunyartan yake yin sanyi sabida yadda hajy karimat din take fayyace mata komi tanamai shigar mata da reality cikin kwakwarta.


Sosai suke taruwa su kashewa kafayat gwiwarta musmamn idan suka soma jefa mata bakar magana da gori kala kala akan cewa Itace take son Ahmed amma Ahmed basonta yakeyi ba..


Tun kafayat bata son fahimtar gaskiya har saida ta fahimce gaskiyar sarar amma sin shi datakeyi yasaka ta cigaba da musu taurin kai tanata zarginsu da cewa sun hada baki ne da Alfah lamidi dan amata karya ta rabu da Ahmed.


Sukanso basu san da cewa duk zugi da bakar maganan da suke gayawa kafayat na shigarta sosai ba, hjy karimat ta dada ce mata ai mahaifyar Ahmed da Ahmed din shikansa da mahaifinsa duka sune suka taru suka lalata mata rayuwa.


Acewarta sune saka bawa zuciyarta hope din jin cewa ita tasu ce bayan sunsan ba hakan bane bazasu taɓa bata  space arayuwarsu ba.


Duk suka maida maganan ya dawo kamar kafayat ne victim na betrayl a gidan jimada.


Sai suka nuna mata cewa suna jin matkar tausayin ta yadda ta zama kamar kwallon kafa atsakanin familyn jimada.


Kwana biyun nan haka suka hanata yin waya da kowa agidan suka ki su gaya mata cewa hjy khadijatu takan kira wayarta, saidai ma suce mata ai gashinan tunda kika bar abuja bata taɓa ta nemeki ba sabida bata damu dake ba kuma tana jin kishinki, hjy karimat tace mata lallai kishi hjy khdijatu takeyi da ita shiyasa take jin kanta insecured inta na gangan da mijinta.


Kafayat ta nemi karya acikin maganganunsu duk ta rasa, bisaga abubuwan da ita kanta tay nazari duk gani tay kamar gaskiya kawai suke gaya mata wanda tunda can ta kasa bude idonta ta gani amma duk da haka sai bata nuna musu alaman cewa magangnunsun ya taba mata zuciyarta ba.


Tunda suka mammata wnn magangnun take zama tay doguwar nazari akan rayuwarta.


Ata dayan bangaren kuwa tuni hjy karimat ta fayyace ma Hajy fatihat duk wani shirinta na daukar kyakkwan fansa acikin familyn bello jimada wanda tuni itama tay na'ammm da wa n shirin nata aranta ayanzu haka kafayat kawai suke jira ta basu hadin kai.*KISHIYAR ƘABILAH 15.*




BY SURAYYAHMS.


Yola:


Wajajen karfe 4pm na yamma su Ahmed suka kammala shiryawansu izuwa gidan Alhaj Aliyu mijin kakar adiaha.


Already brother kazim Aremu daga can u.s haryay magana da wani Abokinshi mai kudi dan siyasa ne honourable sabo, nan da nan aka musu arranging motoci guda uku na kece raini da zasu je gaisuwar dashi, black colour lexus guda biyu da DBX jeep, dukan su suna zuba kyalli aka dire musu agaban hotels din snn aka hadasu da official drivers.


Dukan su manyan kaya suka saka, dan uwan mahaifinsu mai suna uncle bakre da brother hamzat sun sako shadda ubansu mai gare da hulunansu masu shegen tsada wanda daga ganin su za kasan cewa shigar tasu ta barazana ce kawai da suka shirya musu dan suja girma wa familynsu sosai, brother hamzat dimeji yasaka golden colour shikuma uncle bakre ya saka wata royal blue getzner, Banji ya saka black half jumfa bugun kamfani, Ahmed kuma ya saka full fitted jumparsa sky blue colour mai wani irin kyau da sheqi dukansu sun sako hulunan da sukai matukar dacewa da kayansun sosai.


Fadin irin kyan da sukayi dukansu acikin shigar tasu bazai iya misaltuwa ba,banda qamshin turare masu dadi babu abunda yake bibiyarsu dan a kallo daya kamasu zaka iya sanin cewa tabbas suna dashi snn sun kece raini.


Already sun siyo duk wata tsarabar gaisuwar su ta aure na alfarma wanda zasu kai gidan alhaj aliyun domin Adiaha,brother kazim ya riga ya gaya musu cewa yana son ayi komine a lokaci guda batare da bata lokaci ba,yace idan har mutanen Adiaha basuda wata matsala har kudin sadaki ya tanadar su bayar sabida baison ayita memeta jeka ka dawo tsakanin Abuja da yola.



Tun safe Adiaha take cikin zullumin abunda zatayi kafin su Ahmed suxo danko kayan da zata sakanma ya zama mata damuwa dan data gudu agarinsu batazo da kayanta ba sai wanda yake jikinta. Tay girki kala kala ta aje dan al'adarsu ne su bada abinci awajen neman aure. Komi tay ta shirya snn tay wanka tay kwalliya Karshe wani tsohon Abaya mai kyau hjy hajarat ta dauko ta bata akanda tasaka kafin suje sumata siyayya washe gari. Shekarun su yaja sosai yanzu ba wani neman kudin sukeyi sosai ba, iya dan abunda suka tarar ne suketa lallabawa ahankli sai temakon da yayan alhaj aliyun suke kawo musu.


Wajajen karfe biyar saura motocinsu Ahmed suka bayyana acikin harabar gidan alhaj Aliyu inda aka musu iso izuwa cikin babban falonsa ta alfarma.


sallama sukayi daga waje sai akazo aka shigo dasu ciki, nan suka tarda shi a falonsa tare da manyan yayansa maza su biyu, da kuma limamin da ya musuluntar da Adiaha da wani dan uwansa malam shehu.


Tunda su Ahmed suka shigo ciki Sai satar kallonsu awajen akeyi sabida yanayin shigarsu ta kece raini da wayewa.


Cike da girmamawa

Da karrawa akayi yar gaishe gaishe snn aka fara tattauna dalilin daya tarasu.


Tunda manya suka shiga tattauna zancen auren Ahmed baice uffan ba dan tunda ya rusuna kanshi ƙasa babu abunda yake tunani sai komawarsa gidan dan sosai ya gaji da batun auren nan. Iya abunda yaji awajen shine da akace musu ai Adiaha ta riga ta musulunta snn harma ta amshi sabuwar sunanta na musulunci wato REEMA BASSEY


Sunan REEMA suna ne mai kyau na larabci,duk dama wasu yararruka suna amfani dashi da wata ma'ana daban,a harshen larabci sunan REEMA yana nufin "white gazelle" or "a Good and polite at heart person"...


Sosai sunan ya dace da Adiaha dan ita yarinyace mai kyawun hali da saukakken zuciya mai taushi.


Saida akayi kabbara snn Ahmed ya daga kai shima yay dan murmushi jin kowa na mata murna, yanajin su uncle hamzat da uncle bakre suka karkare maganan nasu acikin mutuntawa. 


An yarje an amince za'a bawa Ahmed auren Adiaha,saidai ko da aka kawo zancen saka rana sai dukansu suka fara yin baya baya da zancen hidiman biki musmmn ma da aka ga kamar su Ahmed din suna da shi sosai


Alhj aliyu bai boye musu komi gameda abunda ake ciki da iyayen Adiaha ba sabida inma wata hidimar biki ne zata tashi susan dacewa Adiaha fa bata da kowa ata fannin iyaye bare ace zasu mata wani hidiman aure.


Bayan ya musu bayanin hakan ne uncle hamzat yy magana cikin katse musu hanzarinsu shi yace musu subar zancen dukkan wani hidiman biki da kayan gara su zasu mata komi tunda basu rasa ba. Atakaice dai mata kawai suke so.


Jin hakan yasa Kowa yy hamdala aka sanya musu albarka, Anan aka yanke sadaki Aka ce musu su kawo ko dubu hamsin ma yayi,nan Uncle hamzat suka ciro kudi suka bada dubu dari biyu da hamsin. Snn suka ce musu sunason adaura auren ne ranar Asaba dats nan da kwana uku..nan aka tsaida magana.



Ata cikin gidan kuwa

Sosai Adiaha ta matsu dan tana mugun son taga Ahmed ido da ido yau sosai, dan sosai tay kewarshi aranta kwana biyun nan da basa tare, tana son ta fada masa abubuwa dayawa aciki harda damuwarta dale damunta aranta na rabuwa da iyayenta.


She want him to atleast hold her and comfort her abit sabida haryanzu abin bai dena damunta aranta ba.


Saidai koda aka kammala shirya komi Ahmed din ne yafara matsa wa yayansa akan su tafi kawai shiya gaji.



Alhaj aliyu ne ya matsa akan lallai su tsaya suci abincin da aka shirya domin su, musmmn ma ganin irin kayan tsaraba na Alfarma da suka kawo na auren Adiaha. Duk wasu abubuwanda yake wajen brother kaxim da bro hamzar ne sukayi shi shibaima san komi akai ba dan sosai yayunsan suke sakaltashi tun yana dan karami.



Da kyar Ahmed ya daure ya shiga cikin gidan suka gaishe da hjya hajarat a falonta wanda yawanci ma banji ne yake amsata dan Ahmed kam ya dawo musu tamkar amarya kmr wanda baison yay magana a cikinsu sosai,hjy hjara ta lura da shi yaron bakaramin jamusu aji yakeso yay ba, yanayin sa da kasaita, da kuma kamiya musammn ma dayaga jikin Adiahar na rawa akansa duk ta zautu da alaman tana sone su kebe sugaisa suka dai.


Koda ta gaishe sa acikin mutanen ma bai wani sake mata fuskansa sosai saidai kawai yay mata murmushi, batun zanca addininta saiyace mata "congrats" daganan baisake kulata awajen sosai ba sai sama sama in ana hirar lamariin tasu.


Badon banji yana ta saka su dariya yanajan su a hira ba da tuniwani zaice ko hala auren dole za'ayi ma Ahmed da yarinyar danko ruwan da adiaha ta kawo musu awajen shi baisha ba abun duk saiya dame hajy hajara ganin inda Ahmed yake dan babbasar da komi.


Bayan tafiyarsu ne hjya hajara ta dinga yima Adiaha surutayya akan behaviours din Ahmed.


Takaici kamar zai kashe tsohuwar ganin yadda Adiaha take ta murnan kayan tsarabar gaisuwar 

Da suka lodo suka kawo.


A tunaninta soyayya ne yasaka aka kawo mata kayan tsaraba na Alfarma.Ga goro, ga buhunan abinci,manja, gishiri,doya,kudin katoton rago, banda kananan carton carton na wasu abubuwan.


Suna zama zasu ci abinci grand ma ta kasa hkr Cike da masifafen mita Tace Adiaha kina bani kunya fa, am actually ashame of u today.. Dolene ma yaron nn yana hura mana hanci ni banga laifinsu dasuce su zasuyi komi ba saboda kin nuna masu we are nothing,memakon ki kare martaban familynki ure here getting excited kinzo nan kinata murna akan abun duniya bakiga yadda yaron nan yake daukar kansa agabanmu tamkar wani sarki ba...


Why is he behaving like temakonmu zaiyi, mune zamu bashi mata amma

Shine yake mata fadi da jan aji ? See oo My grandoter, ki bude idonki dan Bai kamata ace Duk wann wahalar da kikayi akansa kwana biyun nn ace  ko minti biyar bazai samu dominki ba, Atleast ai yasan halin da kika shiga ciki na rikici da iyayenki akansa but im deeply suprise all he has to say to u is congrat, Kai kai..nide wann abu baimin ba. He is such a jerk.


Adiaha ta bata rai sosai tace grand ma wai sau nawa zan gayamaki ne haka fa Ahmed yake, shi bamai son magana sosai ba idan kin fahimce shi sosai zakigane cewa he is a good man.


Hjy hajara batace komi ta nade hannu cikin mamaki tanata kallon yadda maganan yy ma Adiaha zafi tanata hargagin fushi.


Nan ta fara kare Ahmed akan dukkan korafin da kakartan tay, harda ce mata ai yanajin kunyan yayunsa ne shisa bai sake jiki da ita ba, snn dan yace mata congrt akan zanca addini ai dama badan shi ta sauya ba.


Babu ta yadda zaka kushe Ahmed agaban Adiaha batare da kawo maka wani dalilin da zai kare shi ba. Sai cewa take ai tausayin halin da take ciki da iyayenta tare soyayyar dayake mata ne yasaka familynsa suka ce zasu mata komi na hidiman auren and she is happy nd grateful for that.


Adiaha ta dauka duk wasu kalmomin nata datake kare Ahmed dashi agaban grandma masu ma'ana ne saidai batasan da cewa Maganganun datake furtawan yanayiwa kakarta ciwo aranta bana wasa ba.


Aranta cewa take Adiaha is blind and desperate about this guy. Batasan da cewa mutuncinta take sayarwa ba. She wont have value to them musmn ma indan sunajin kansu a matsayin cewa sune sukayi komi na aure.


Ta rasa abunda zata ce mata kawai ta fasa cin abincin ta tashi cikin fushi ta koma dakinta tabarta awajen ita kadai tana ta bawa kanta dalilai akan Ahmed na cewa lallai yana sonta ne sosai shiyasa zai aureta


Jin abun yafara dan damunta saita tura masa sakon tex a sabon layin sa and she foolishly told him cewa grand ma dinta is not really pleased with him, ganin hakan ne  yasaka ya daure ya kirata suka fara gaisawa.


Rabon shi da kiranta awaya tun ranar da suka rabu a calabar dan yace mata bayason tana kirarsa koyaushe musmmn ma indan tana tare da familynta.


suna kammala gaisuwar Yy kmr bai karanta tex din sosai ba, sai Yace mata ta memeta masa meyene grand ma dintan take cewa akansa..


Tafara gaya masa duk abunda kakarta ta fada da irin bayanin da itama tay mata akanshi.


Ahmed ya daure fuskan sa sosai cikin yanayin basarwa da bata rai yace "Toh shikenan naji,.zan gayawa yayunq sai azo ayi magana a tsaida batun auren tunda grand ma dinki tace bata aminta da halina ba.


Adiaha ta kwalo ido waje tace "Ahmed meyasa zakace haka? Da Bai amsa ta ba sai jikinta yay mugun sanyi dan Sam batay tsammanin jin hakan daga gareshi ba.


Tuni yanayinta ya canza cos its seem he is gaslighting her now sabida yasan babu yadda ta iya dashi, Cike da bugun zuciya da damuwa Adiaha tace Ahmed pls ni ba hakan nake nufi ba, kay hakuri karkakai maganan gaba,grand ma is just being worried about me sabida yadda taga na rabu da iyayena duka akanka.


Cikin yanayin hade ransa Yace " okay, yanzu kenan laifina ne da iyayenki suka rabu da rayuwarki Ko dama akaina ne kika zanca addini? Zatai magana cikin katseta da shakurarren murya yace "silent,ya isa haka.

"kar ke ko kakarki ku fara tunanin daura min wani laifi akan wani abu daya shafi rayuwaki dana iyayenki sabida ni aurenki kawai nace zanyi Amma bance ki canza Addini ko ki bijirewa iyayenki akaina ba...ya lumshe ido jin tafara kuka tanamai neman tafara bashi hkri, ya kuma bata ransa muryansa kasa kasa cikin shan qamshi sosai yace ..'look ni ba hkuri nake so daga gareki ba, i' m quite disapointed in u ryt now, kukan ki bazai nuna komi min ba, nifa bangane miki ba, shin aurena zakiyi dan Allah ko dan in bauta miki dake da kakarki? Wn ai duk laifinki ne, dan inba kece kika nunawa kakarki cewa ure blaming me for ur personal issures a mind dinki ba da hala bazata fara dora bururakarta akaina ba. 


"Me kakarki takeso?dan nazo gidanta shikenan sai In lashe kafarki ko in goyaki a baya na? Da nace zan aurekin is dat not enough for u ppl? why wud ur grand ma expect me to take all the burden of ur pain...nine na dauke ki daga gaban iyayenki ne ko nine nace ki rabu dasu?


Cikin tashin hankli Adiaha tace Ahmed pls listen bahaka bane kasaurareni mana


Tashi zaune yay cikin katseta tare da nuna mata bacin ransa a fili, Adiaha tafara kuka sosai ganin ya dau abunda da zafi sosai ,ransa a harzuke yace bana da lkcin wnn rigimar, yau alhamis ne, kije yanzu ki gaya mata cewa inhar bata aminta dani ba toh suy gaggawar fada ma yayuna kawai mubar garin nan yau yau,as for kudin sadaki da duk wani abunda muka kawo gidanta karsuji tsoron kin fadin mana komi mu bamu damu da wani abun duniya da muka kawo muku ba,ina son kusani cewa auren nan fa ba dole bane akaina, ko akace muku babu mata ne da suka fiki a duniya?ya kyabe bakinsa cikin yanayin basarwa, muryansa a kasa kasa yace "Ohh pls, she can marry you off to wanda hanklinta ya kwanta akai for all i care, amma dai bazan dauki laifin da banawa in dorawa kaina ba,and no one shud think of controlling my life, akanme?mace zan aura ko rai zaku ban?..


Cikin shesshkar kuka Adiaha tace Ahmed ka dau magann nan da zafi mesa zaka fadi haka


Yace  Da zafi mana, daga na bada sadaki yau ko kwana daya baiyi ba sai afara tunanin juyamin tsarin rayuwata?ni ba karen mata ba, in a al'adanku maza suna bautawa mata mu bamu yi, our women are expected to be very peaceful nd respectful...

nide na fada maki, Better do sumting about it koni na fadawa yayuna da kaina..u can't insult my family..snn bana wasa da martaban iyayena ko acikin mafarki, idan har kunada matsala dani then we wll call this weding off and leave.


Yana fadin hakan ya katse wayarsa Adiaha tay rigib ta sulale kasa ta dinga rabza kuka tana cewa hello hello Ahmed pls listen, ba haka bane, sai shiru, ji tay tsoro da fargaba mai tsanani yana neman dabaibayeta.


Kukan datakeyi anan yajawo hanklin kakarta izuwa dakin hankli tashe ta yo kanta tana tambayarta ko lpya? Cike da bori ta haura mata tana cewa duk laifinki ne Ahmed yaji haushi yana fushi dani..grand ma why wud u complain about him dat way, gashi ai yace ina disrespecting familynshi, yace babu ruwanshi, wai idan kina da matsala dashi zai fasa aurena kinema min wani..


Hjy hajara ta rike kirjinta dataji ya dau zafi sai ta rasa baqincikin Adiaha kona ahmed din zata fara dubawa.


Tace Reema kina hauka ne Meyasa zaki je ki gaya masa maganan da mukayi dake anan gidan tsakanina dake? Na fada ne dan in wayar miki dakai why wud u tell him ashe bakida wani sirrin kanki komi aka gaya a gidanku sai kigawa Ahmed?


Tana kukan tace oho..


Nide kisan yadda xakiyi Ahmed ya dena fushin nan dani sabida duk kece kika jawo min,ai gashi nan yanata cewa wai zai fadawa brother dinsa cewa zamu fara controling din rayuwarshi dan ya kawo sadaki na..

Grand ma what if he call off the weding? I wll kill myself, wallai bazan iya rayuwa babu Ahmed ba.


Hjy hajara batace komi ba tsaban bacin rai jikinta sai rawa rawa yakeyi shikadansa sosai, a mugun fusace ta dauki wayar Adiaha ta dinga kirar layin Ahmed waidan ya dquka ta gaggaya masa bakaken maganganu masu zafi ta huce takaicinta amma sai bai dauka ba.


Suna cikin hakan saiga Alhj Aliyu ya shigo dakin, ganin yanayin su yasaka ya fara neman karin bayani, hjy hajara hartana kunfan baki da hawayen takaici tafara maida masa maganganu, 


Tace "Alhaji kafa nemo yayun yaron nan, kace musu suzo yau yau su tattara abun duniyansu an fasa auren..sudin wa? Sudin banza.."Me Ahmd din nan ya taka? meyake ji dashi da har zai gaya min baqar maganan dayaga dama akan dan zai aure jikata? Akwai maza dubu wanda suka fishi kyau da kudi,shi ba komi bane agaban wasu mazan wllh, shashasha dashi ma wanda baisan halacci ba, wani irin wahala ne yarinyar nan batasha akansa ba har shine yau zaixo yana dagawa mutane kafada da jijiyar wuya dan anfadi masa gaskiya? Ai gaskiyan kenan baidamu da halinda Yarinyar nan take ciki ba, gani yake kmr sadakan kobo za'a bashi sam baiya kallon mutane da daraja katon bayarben banza.


Anan ne adiaha ta gane cewa ashe kakarta neman Ahmed take donta ci mutuncin awaya amma badon ta bashi hakuri ba.


Anan ma suka fara wani sabuwar cece kucen ran hjy hajara ya baci sosai alhaj aliyu kuwa yanata lura da zallan kalaman tsagwaron rashin kunyar da Adiahar ta kara fandarewa da shi.


Alhaj aliyu daya fahimce komi yajawo matarsa gefe suka bar dakin ya dinga rarrashinta har saida zuciyarta yay sanyi sann yafara gaya mata cewa hikiman daya ne zai iya budewa Adiaha ido ta gane cewa shayi ma ruwa ne, wann hikiman shine su kyaleta ta aure Ahmed din,yace mata nan da bada jimawa ba ita dakanta zata dawo bayan ta shiga hanklinta ayayin da duniya ya gama koya mata wayo.


Da kyar hjy hajara ta Amince da wann shawaran dan taso ace kawai afasa auren kodq mutuwa Adiahar zatayi, Abun nada matukar ciwo kana kallon jininka zai fada acikin halaka boro boro amma ka kasayin komi akai.


Saida ta nutsar da zuciyanta sosai snn ta iya danne komi aranta tay hakuri snn ta daura niyyar bin shawarar da mijintan ya bata akan Adiaha.



Ata fannin Ahmed kuwa tunda ya kammala waya da Adiahq bai sake kallon inda wayar take ba, duk tulon miscals dinsu da suka masa shi baisan sunyi ba, wajen hotel din da suka kama yaje ya samu abokinshi Banji yana zaune nan yafara gaya masa situation din, yace masa ai kakar Adiaha tana son ta dora masa laifin komi shiyafara tunanin fasa auren ma sabida baison rainin hankli.


Banji ya sha mamakin jin hakan, musmmn yadda Ahmed ya fayyace masa maganan da sigar cewa sunason suyi controlling dinsa with emotional blackmail dan ace ai tunda sabida shine Adiaha ta bar iyayenta da addininta dolene ya bauta mata sai yadda sukayi dashi.


Ran banji sai ya baci sosai dayaji hakan, suka ta bambami sunata kushe halin irinna matan da suka kasance yaren kakar Adiaha dake ita inyamura ce,.


Saidai Duk da hakan Banji baiyi fushi sosai da Adiaha ba, yay tunani mai kyau akanta dan yasan abun da tay ma abokinshin da wuya sosai.


Yace ma Ahmed yay hakuri yaji tausayin yarinyar sabida tana sonshi sosai..


Ayanzu ma basai an fada masa cewa Adiaha tana mutuwar kaunarsa ba, banji yace bakowace mace bace zata bar komi nata tazo domin namiji kai hatta kafayat dasuka dade suna tare baya zaton zata masa irin wnn  sadaukarwan da Adiaha tay masa.


Abokinshi Banji ne ya dinga lankwasashi da dalilai kafin nan zucyarsa tay sanyi har ya rusuna yabar zancen, suka fara wani hirar na daban.


Tambayarsa yakeyi yadda zaiyi da kafayat bayan ya aure Adiaha


Ahmed Yace bai sani ba.

Amma yasan bazai bawa kowa hakuri dan bai aure ta ba, yace "rayuwar shi ce, dan haka yana da ikon da zai canza ra'ayin sa akan duk wacce yaga dama witout owing them any explanation.


Banji baice komi ba duk dama yasan akwai kura agaba.


Washe gari ranar juma'a hjy khadijatu ta idar da sallah kenan ta turawa kafayat tex message mai cike da nuna kulawa tanamai tambayarta ya jikinta kuma yaushe zata dawo, ko tazo ta daukota ne sabida gobe ne za'ay walima na komawa sabon gida and she wants her to be deir tunda a matsayin ƴarsu suke daukanta.


She care soo much about kafayat dan tunda akace mata batajin dadin jikinta kusan kowani lkci suka hadu da mijinta saita tambayeshi ko yay waya da ita amma ko wani lokci amsar dayane dukansu basu samu damun magana da ita ba

Gara gara ma shi dayake yakan samo musu bayani awajen mahafyarta.


Kafayat na zaune a bakin gadonta ta farka a barci kenan zata shiga wanka

Taji shigowar sako,jikin ta duk a muce yake dan kwana biyun nan tunanin Ahmed ne kawai yake fado mata acikin ranta  musammn ma da Alfah yace babu aure a tsakaninsu. 


Maganan ya shige jikinta da kwakwalrta sosai harma fiyeda yadda itakanta take zato.


Duk zuciyarta a hatsale yake da damuwa Tana kammala karanta tex din hjy khadijatu memakon taji sanyi aranta sai taji fushi da damuwa mai yawa ya hautsina mata jiki, agefe ta jefar da wayar tare da jan wata doguwar tsaki dan inhar akace Maganan Alfah ya zamo gaskiya to babu shakka an cuceta.


Jin kanta takeyi very frustrated with her life har yau haushin kowa da komi takeji aranta.


Wanka tay ta fito ta sanya english wear riga da skirt blue colour ta baza kitson attacemnt dinta ya sauko har gadon baya yana shan iska, nan ta sauko kasa izuwa falon kawar mahafinyar tata, ko ina yay shiru acikin gidan da alaman ita kadaice tasamu har sun kammala karyawan su sun fita. Ido ta daga ta sake kallon agogo ganin karfe bakwai da rabi saura na safiya


Mamaki takesha aranta dan tasansu da baccin asara, sai tarasa miyene mai matukar muhimmancin haka har da zai fitar dasu da sassafen nan. Wani zuciyar yace mata hala harkan business dinsu ne yasaka sukayi sammako


 Nan ta zauna tafara hada tea makanta dan saiyaune tafara jin dama dama ajikinta, cikin nitsuwa tasha tea din da two slice of bread, ta dade azaune awajen ganin basu dawo ba har wajen karfe goma na safiya hakan yasaka taje kitchen tafara fere doya ta tafasashi yay laushi ta hau daka sakwara.


They have varieties of soups a fridge cikin kankanin lokci ta hada komi abunta hadi da cewa batada gwuyar aiki arayuwarta, bayan ta kammala komi ta fito  dashi falo tanakan ci batare da sanninta ba awajen wani irin baccin bazata ya kwasheta.


Ata wani bangaren kuwa

Hjy fatihat da kawarta hjy rakiya sune agaban goddes sunata kallon ta acikin wani kwarya.


Wani ruwa goddes ta miƙawa hjy fatihat tace ta zubashi akan setin inda zucyar Kafayat yake daga cikin kwaryan.


Babu musu ta amshe goran ruwan goddess tana fada mata wasu kalmomi da yarensu itama tana nanatawa ahankli ta juye ruwan akan kirjin kafayat duka tana kammalawa sai gq wani irin yawun bacci mai yawa ya fara fita daga bakin kafayat yana zubowa acikin kwaryan


Bayan ya taru sai kafaya din ta bace musu a kwaryan bat.


Dariya goddes ta bushe musu dashi alaman aiki ya kammala, kafin nan ta daga kwaryan can sama tare da yawun kafayat din, tana saukarwa ta saka hannu aciki tq dauko wani garin magani a cikin kwaryan da ya bayyana dakansa,nan ta miƙa musu tace su bawa kafayat garin da shine zasu cimma burinsu acikin sauki.


Zuciyarsu fari tasss suka bar wajen goddesss suka dawo gidan suka samu kafayat tanakan bacci tuwonta haryay sanyi sosai.


Saida suka kammala tattaunawarsu snn hjy fatihat tace duk da sun karbo maganin daukar fansa amma batason tay ma yarta komi na dole arayuwarta, dan haka kafin suy amfani da maganan sai tay magana ta fahimta wa kafayat.


Hakan kuwa akayi kafayat ta farka a daburce ganin kan kirjinta ya gama jikewa da ruwan da batasan daga ina yafito ba 


Ganin ta daburce sosai saisuka hau lallabata sunace mata wai Ac ne ta mance bata kunna ba da kuma damuwar auren Ahmed damilare data saka Aranta


Nan Suka zauna kamar mutanen kirki suka fara lallashinta sunata bata shawara kamar iyayena na gari, hjy fatihat ta nuna mata cewa  ita dai harga Allah bawai bata son Ahmed bane, kawai bata son yarta ta aure namijin da baisan darajarta bane kwata kwata,tacewa kafayat inda ace Ahmed yana sonta kamr yadda take sonshi da sosai zata goyamusu baya, amma duk wata uwa bazata so taga yarta tana bautawa soyayyar namiji ba a sune sukesonkan ma ya ka kare bare ace kaine kake sonsu.


Duk suka taru suka kashe ma kafayat jiki ta hanyar nuna mata cewa duk abunda sukeyi dan suna son cigaban rayuwarta ne.


Cikin salon yaudara Hjy rakiya tace mata ai itace ta matsa wa hjy fatihat akan suje sunyi bincike da kyau akan batun aurenta da Ahmed, kuma sunji cewa maganan Alfah gaskiya ne, amma suna son su kara gwadawa. Nan ne suka fito da garin maganin suka bawa kafayat 


Hjy fatihat ta hade rai salon yaudara irinta nuna bada son ranta take hakan ba saidan farin cikin yarta duk dama aranta manufarta dabanne wanda kafayat din bata fahimce wayonsu ba.


Sam basa son kafayat taga laifinsu akan komi

Su sun riga sun mince da Alfah dan bai taɓa fadin musu karya ba, babban damuwarsu ayanzu shine yadda zasu dau mummunan fansa akan famlyn bello jimada batare da kafayat ta san nufinsu ba.


Suna damka mata garin maganin suka hau yi mata bayani dalla dalla


Anty rakiya tace mata sau uku ake so tay amfani dashi akan mutanen da suke fada aji agidan su Ahmed..


Kafayat tace hjy khadijatu ne da alhaj bello da kuma anty mojushola


Sukace mata sam, koda zasu amince da sauran amma dole ne ta bar zancen hjy khadija agefe sabida itama babban munafukace itace take juyawa Ahmed kansa akanta.


Hjy fatihat tace, Alhaj bello jimada, da anty mojushola da anty ramatou sune zatay targeting dinsu da maganin.


Sann a abinci ko abunsha zata sakawa kowannensu ta dai tabbata sun shanye magananin sau uku uku.



Cike da salon yaudara Hjy rakiya tace mata wnn maganin ne zai saka kowa acikinsu ya yi iya abunda suke so akan Ahmed..


Tunda aka fadi hakan kafayat sai taji kamr andawo da haskene cikin zuciyarta, take taji wani irin farinciki mai yawa ya mamayeta, tay musu godiya tare da basu tabbacin zatayi abunda suke so din.


Bayan nan ta shirya komawa Abuja and she was planning to surprse them kowa saida ta siya masa cookies mai dadi da tsada, na anty moju da anty ramoutu duk saida ta barbada maganin aciki she also bought a very good strwberry wine too wanda akayishi da crisp of fermented strwberry fruits.


Shikuma alhaj jimada acikin wani park din dabino mai dankon nan ta barbada mashi snn ta kama hanya ta dawo Abuja.


Da fara'arta ta shigo gidan kowa na murnan ganinta, hjy khadijatu tana kallo ta raba musu tsaraba dukansu itace kawai bata bata komi ba.


Hakan bai dameta ba duk dama tanashan mamakin yadda kafayat din ta saka su agaba saida suka cinye tsarabar data basu. 


evryone is happy, atleast she is back and healthy, da yamma ranar friday din itace taje tay musu girki agidan su anty moju 


Tun anan ta badawa sun anty moju magani acikin miyarsu suka ci abinci.


Sann ta debo abincin a cooler ta kawo ma Alhaj bello har gida acikin sashen sa takai masa inda shikadaine zaici, tare da fruits wine din tay masa serving komi tazauna gefensa tanata zuba mashi tadi tare da nuna godiyanta akan kulawar da suka nuna akanta shida matarsa.


She said she make the food speacially for him harda drink din ma...


Tass tass ta saka shi yacinye tana ta masa murmushin da bai gane kansa ba,aranta lissafi take, ance sau uku, so ta bashi acikin dabino, ta bashi a wine, da kuma dinner, ta gama dashi kenan saura su anty mojushola, tasan gobe asabar ne ana rububin waliman komawa sabon gida hala bazata samu daman bashi maganin ba shiyasa ta gwammaci ta gama dashi ayau ta huta makanta.



Yaji dadin hirar data zo tana tayashi cos kafayat is very kind and sweet, sosai yake sha'awar ta ma dansa Ahmed koda zai shiga hanklinsa ya nitsu ya aureta cos aganinsa babu namjin mai lpyar bazaiso mace kamr kafayat ba, ta mallake komi da mata ke nema, ta iya magana tana da respect, gata da iya zama da mutane snn ta iya abinci.


Shigowar hjy khadijatu ne yasa hirar tasu ta katse, hjy khdja tana shan mamakin kafayat wai har taje can gidan su anty moju tay girki amma bata gaya mata ba bare ta kasa da ita. Batace komi ba kafayat din ta fara kame kame tana murmushi tace mata karta damu mai aiki zata girka mata spaghetti jolof dan shine takejin sha'awar ci yau ba tuwo ba. Acikin raha suka kare maganan duk dama jikin kafayat yabata cewa hjy khadijatu hala zatace ko tana fushi da ita ne.


Ita kuwa hjy khadijatu aciki kawai ta bar zancen bata nuna a fuskanta ba, tasan dolene dai akwai abunda kafayat tasaka aranta game da ita akan Ahmed. Fatar ta shine Allah ya bayyana mata gaskiyar lamarin dan wata rana tasani cewa bata mata bakinciki akan lamarinta da Ahmed.


Hirar Ahmed din suka farayi da mijinta dake duk sun bari aransu akan cewa Ahmed yana calabar ne yana aikine 


Suna kan hirar su mai dadi sai ga kirar brother kazim ta video call ya shigo, da murnansu suka dauki kirar suka fara gaisawa dashi  cike da nuna masa soyayya shikuma yanamai basu girmamawa sosai


Yaji mamakin ganinsu atare duk dama bukatarsa kenan ya samesu atare dan gobe ne yake son aje a daura auren Ahmed acan yola.


Baice musu komi ba tukun,iya Hirar waliman komawarsu sabon gida na gobe suka fara masa cike da nuna farincikinsu agareshi..


Hajy khadijatu take ce musu cousin din Ahmed yasra hussain zata zo yin karatunta abuja zata zauna agabanta gida zai karayin dadi with young young ones around them sunata dariya sosai.



A siyasance brother kazim ya fara shigo musu da maganan dan uwansa Ahmed,ya tanbayesu ya suke ciki da batun shirin aurar dashi?duk sun sha mamaki da sukaji cewa Ahmed damilare yana comunicating sosai da dan uwansa bayan su insuka nemeshi basa samunshi koda awaya ne.


sun fara tattaunawa akansa kenan suna kawo masa complain na yadda Ahmed yake musu taurin kai akan batun tsaida matar aurensa sai ga kafayat ta shigo wajen da plate din spaghetti dataje ta dafawa hjy khadijatu, suna jin sallamar ta suka katse maganan sukayi shiru har ta iso,tana zuwa ta ajiye wa hjy khdjatu abincin agabanta cikin girmamawa tanamai saka mata albarka, jiki na rawa ta tsuguna har kasa ta fara gaishe da brother kazim, ya amsa mata ba yabo ba fallasa tanata masa murmushi mai fadi ganin ko sake mata fuskansa baiyi ba, aranta kuwa so take yace wani abu mai dadi akanta dan tasan ko shima yana son ta ma ahmed kmr sauran family members, dake tun abakin kofa tajishi yana dan ambatar sunan Ahmed dinta duk ta dauka zancen auren ta da Ahmed din zasuyi.


Da murmushi tay masa sallama bai wani kulata sosai ba, Bayan nan ta fice a dakin domin ta basu waje, tana fita taje ta laɓe abakin kofa nan tasaka kunnenta tanajiyo maganansu daga waje.


jim kadan sai ji tayi brother kazim yana tuhumarsu akan dalilin dazai saka subar ta tana zama acikin gidansu da sunan tana jiran Ahmed ya aureta dan bata da kunya.


Kafayat tanajin yadda brother kazim ya fito fili ya kukkushe zaman datake musu agida yace musu sam babu mutunci aciki.


Shiru suka masa dan kaf din sun nan tausayin kafayat din sukeji aransu shiyasa suke bata wann gatan sosai.


Brother kazim yace sam baiji dadi ba, acewar sa mutuncin yarinya budurwa shine ta zauna agaban iyayenta namiji zaije gidansu ya nemo aurenta bawai itace zatazo har gidansu tazauna da sunan tana jiran shi  dan ya aure ta ba.


Ran kafayat ta bai wani baci ba da korafin brother kazim ba sabida tasan gaskiya ya fada mutane dayawa ma sunsha gaya mata cewa she is making her self too cheap and desperate akan Ahmed msmmb datake zama agidan su akan dan ya aureta.


Haka kawai taji kmr korafin brother kazim din ya shige jikinta da mind dinta, jikintan asanyaye ta bar wajen ta tafi tabar wajen batare da taji karshen bayaninsan ba.


Kayanta ta deba ajaka ta bar gidan acikin daren ta koma gidan iyayenta da niyyar washe gari zataje nasarawa taje ta fada ma mum dinta abunda brother kazim ya fada.

Surayyahms chat *08060712446*

*Wanda ba su yi saving number ta ba su yi sai su mini magana ni ma zan saving ta su* 👍🏻

Reply with "saved" is enough😍*KISHIYAR KAƁILA...*



BY SURAYYAHMS 


This is For you NOOR EEMAN💞


FINAL EPISODE.



Bayan tafiyar kafayat gidansu bada jimawa ba brother kazim ya soma bullo musu da maganan Auren Ahmed da Adiahar a siyansance,cikin salo yabi dasu har sai bayan daya kwato hanklinsu duka izuwa gareshi snn yabita hanya mai sanyi da hikima cike nitsuwa da kammala tareda sako tausashiyar muryansa ya musu maganganu masu bala'in shigajiiki akan sanin darajar yayansu.


Yace duk wa yann yan mata da suke bibiyar rayuwar Ahmed da aure shikansa yasha sawa ayi bincike akansu snn ya fahimce cewa yawancin su sunada wata manufar su na daban shiyasa bai yarda da zancen fifita burin wata ya mace akan na dan uwansa ba. Yay maganganu masu dumbin ma'ana tare da basu misalai wanda suka shigejikin baban nasu sosai suka sakashi yin nazari da tunani.


Yace musu kowa a duniyan nan is being selfish intakama akan batun auren dansa ,toh Meyasa su bazasu iya tsayawa tare da Ahmed dan susan asalin damuwarsa akan batun aure ba saidai suyita tursashi akan mace daya.


Acikin salo yay amfani da lamarin kafayat ya gaggaya musu laifinsu da sukeyi wa Ahmed na cusa masa damuwar auranta aransa, yace musu alkawari kuka mana cewa bazaku mana auren dole ba amma Sai gashi kuna kan cusawa Ahmed kafaya kmr dan dolenshi ne saiya aureta.


He agree with them da cewa Ahmed ya dade suna tare da kafayat, bayan nan kuma sai ya  kawo musu tauhidi yanamai cewa ai ba doka bane yuwar aurensu,xai iya yakasancewa zuciyar Ahmed ya canza with time, ko na kafayat din ya zanca, ko kuma kalamn aure ba qaddara bane atsakaninsu,  Saiyake tuhumarsu da cewa inhar ata fannin kafayat ne aka samu jinkiri suna tunanin iyayenta zasu amince su tursasata ta aure Ahmed ne in bata da ra'ayin aurensa ba?..


Sunfi awa biyu tare da brother kazim yana musu magana cikin hikima yanamai kawo musu dalilai daban daban da zai saka su dena saka ra'ayin kowace mace asama dana dansu Ahmed.


Saida ya lura jikinsu yay sanyi sosai snn ya fara kawo musu maganan cewa shikansa yasan sirrikan Ahmed dayawa wanda su basu sani ba. yace Ahmed yakan fadamashi damuwarsa inta masa yawa. Snn ya razanasu cikin salo yace musu Ahmed is going tru anxiety nd depression saboda su,yace yanajin mugun tausayin dan uwansa ga matsi awajen aiki ga pressure agida yace musu Ahmed yanacikin damuwa sosai musmmn akan dalilin family pressure da suke saka masa akansa na batun auren kafaya.


acikin ruwan sanyi brother kazim yamaida maganan ya dawo wani babba snn ya nuna rashin jin dadinsa akai har saida yasaka su acikin tunani da jin fargaba.


 Koda suka damu suji damuwar Ahmed din daga bakinsa yace musu shi bazai gaya musu komi ba.


Ranar har karfe goma na dare suna masa bayani  akan manufarsu akan Ahmed kowa yana kkrin yayi explaining kanshi, ahakan ya samu daman amfani da nadamarsu yace musu Ahmed yana son kafayat din ai bawai bayasonta ba amma magana ta gaskiya shine akwai wata wacce yake son ya aura.


Bakaramin mamakin jin hakan sukayi awajensa ba, musammn daya fara tsakura musu irin son fitina da yarinyar takeyi ma Ahmed, yace musu idan sukaga yarinyar ma wallh saisun tausaya mata,sai sunce kafayat batayi komi ba wajen nunawa Ahmed kauna, Bai karasa musu labarin ba Yace musu su kwanta haka suyi bacci kawai

Sai gobe da safe zai kirasu dashi da brother hamzat su musu cikakken bayani akan abunda ake ciki.


Duk zakuwarsu da tashin hanklinsu saida suka hakura suka bar zancen izuwa washe gari da safe duk dama aransu basuji dadi da akace Ahmed  ya kullace su aransa har yakaiga depression ya kamashi ba. Dake suna son ƴayansu duk sai hakan ya daga musu hankli bana wasa ba, nadaman matsa masa da sukay akan kafayat din sai yafara cinsu akasar ransu sosai.


Hakan ne yasaka har washe gari ranar waliman bude sabon gida dukansu basu wani nemi inda kafayat din take ba dake sun santa da son aiki hala har ta wuce gidansu anty mojushola tayasu shirye shiryen bidiri.



A ta fannin Adiaha kuwa daren gaba daya bata samu runtsawa ba dan duk hanklinta atashe yake da furucin Ahmed akan abunda kakarta tace akansa.


Ta tura masa tex na ban hakuri yafi a kirga baiyi replyn ko daya ba, tana kiran layinsa kuma zataji akashe kusan kwana tay tana cikin damuwa akansa sosai.


Washe gari da kyar ta tashi zatay sallah dake bata wani iya sosai ba saida ta danne zuciyar ta taje sashen hjy hajarat.


A zaune ta sameta akan daddurma tanajan charbi

Kallo daya tay mata ta dauke fuskarta dan bakaramin takaicinta takeji aranta ba.


Ganin yanayin kakar tata ya sakata jin bata kyauta mata ba, dake tana da tausashiyar zuciya hakanan ta zauna kasa kusa da ita tafara bata hakuri akan rashin kunyar datayi mata jiya agaban mijinta.


Hjy hajara taso ta karayi ma Adiaha magana akan Ahmed koda zata shiga hayyacinta a fasa auren nan amma yanayin Adiahan yasaka ta kasa iya ce mata komi.


Cikin sauke nannauayr ajiyar zuciya Tace mata ai komi ya wuce Snn ta amince mata tay aurenta da duk wanda take so tunda Abunda ta zaɓa ma kanta kenan..


Adiaha ta y murmushi tace ta gode,hjy hajara bata karace mata uffan ba harsaida ta kammala guiding dinta tay sallan safiya kafin suka zaune take ce mata Alhaj Aliyu zai kira Ahmed din ya bashi hakuri. Snn za'a daura auren ne da misalin karfe 2 da rabi na  rana dan sunce yau zasu koma Abuja tareda ita.


Nasiha na zaman aure ta dinga mata, dana hkrin zama acikin dangin miji da iyayen mijin gabaki daya musmmn ma da dukansu suka kasance kabilu, tanayi tana jefa mata hannunka mai sanda acikin zantukan nata wai koda zata dan fahimceta tay makanta karatun ta nitsu amma ina Adiaha tay mugun nisa a son Ahmed bata gane komi  idan ana fadin laifinsa agabanta.


Sassafe Alhaj aliyu ya danne zuciyarsa ya nemi Ahmed awaya privately ya masa magana man to man akan abunda ake ciki, Abun yadan ba Ahmed mamaki amma dake abokinshi banji ya riga ya bashi hakuri sai ya bawa alhaj aliyun hakuri kawai yace masa ayi masa afuwa lkcin datazo masa da maganan ranshi a bace yake shima badon ransa yaso yagaya mata hakan ba.



Tunda sukadan samu fahimtar juna da Ahmed  shikenan kowa hankalin sa ya kwanta aka dawo ana jiran lokacin daurin aure.


Iya bakin kkri alhaj aliyu da hjya hajara sunakan yi wajen hidiman abincin da za'ai awajen daurin aure kominsu dan daidai gwargwado.


Banji ne aka aiko da safe yazo gidan ya kawo ma Adiaha kudi kimanin dubu dari biyu akan ta siya kayayyakin da zata saka da duk wani irin kwalliyar datake so tay na daurin aurenta ayau.


Tun da safen suka shiga kasuwa da kudin ita da kakarta hajya hajarat dan adan kimtsata tay kyau tunda yau ranar aurenta ne.


Bangaren su hajiya khadijatu kuwa tun asubahin fari da suka idar da sallah suka dokawa brother kazim kira atunanin su gara ayi maganan tun yanzu kafin ashiga hidiman waliman komawar sabuwar gida.



Suna kiranshi kuwa ya dauka sai yace musu bari ya fita a office dinshi zai kirasu dan lokacin mun ba daya bane dana can, yace zaiy connecting da brother hamzat sabida maganan babba ne.


Duk hanklinsu a tashe ya barsu yaukam ma sama sama sukayi break fast hanklinsu nakan waya suna jiran kiransa, da safe ne amma sosai gidan yay shiru duk anje gidansu anty mojushola dan anan ne za'ayi duk wata shirin hidima.


8clk dot saiga kirar brother kazim ya shigo.

Suna dauka sai brother hamzat shima yay kira daga yola sai suka hadu akan screen na computern mahaifinsu. Sunkai minti biyar suna gaishe da iyayen nasu cikin nitsuwa da nuna girmamawa sosai.


Kafin nan sufara tattaunawa akan Ahmed a farko ma saida brother kazim ya musu albishir da sabuwar mota jeep high lander ta tayi yar 20 million daya siya musu na gida yace kyautarsa kenan dazai basu na murnan komawa sabon gida, brother hamzat kuma ya dauki nauyin cewa shine zaina ciyar dasu agidan daga yanzu.


Murnan jin hakan yasaka har iyayen nasu har suka mance da damuwarsu akan Ahmed na lkcin sukadinga saka musu albarka suna musu fatan Alheri a rayuwarsu dukansu biyu har suna hawayen murna.


Each time suka shirya kawo maganan auren Ahmed sai sundan yi wasa da emotions dinsu


Koda sukaga sun yi sanyi suna cikin tsananin jin dadi da farinciki anan ne suka dawo a siyasance suka kama kan Maganan rayuwar Ahmed.


Lokaci guda kowa ya nitsu.


Tiryan tiryan Brother hamzat ya fara magana yanamai basu labarin duk wani abunda ake ciki da batun Ahmed da Adiaha yanayi brother kazim din kuma yanamai kara yima abun kwalliya sosai yadda zai saka sunajin tausayin yarinyar sosai.


Abu dayane basu gaya musu ba shine zancen zuwan Ahmed garin calabar akan Adiaha.


Kawai dai sun killace labarin ne ta hnyar nuna musu cewa poor Adiaha ta hadu da Ahmed ne during his reaserch kuma gashi harta sadaukar da komi nata sabida shi, yace "iyayenta, addininta da kabilarta, duk ta aje akan dan uwansu Ahmed kuma tunda Ahmed din yace musu hanklinsa ya kwanta da ita su sun yanke shawarar kawai ayi hakuri kawai abashi ita inyaso daga baya asasanta da kafayat.


Da mamakinsu kuwa Alhaj belllo ne ya fara amincewa da maganan dan bakaramin tausayin Adiahan yaji aransa ba duk dama bawai sun gaya masa asalin labarin ayadda yake azahiri bane.


Saidai jin cewa ta sadaukar da komi nata harta gudo yola domin Ahmed yasan cewa tabbas yarinyar tanason dansa sosai, brother hamzat yace musu yay bincike akanta sosai kuma ya hadu da kakarta a yola sunce in Ahmed din ya shirya zasu bashi auren yarinyar.


Daga hajy kahdijatun har alhaj bellon mamakin yayansun suka dinga sha jin sunyi komi aboye batare da sanninsu ba.


Sun dade suna tattaunawa akan lamarin har dai brother kazim ya fito musu sarari yace yana son aje adaura auren Ahmed din yau domin akawo yarinyar Abuja cos she dont have anyone anymore face Dan uwansu AHMED.


Iyayen sunso suja maganan amma hakanan yayunsa suka cinye su da kalamai masu dadi, duk inda aka bullo saisun toshe.


Brother kazim yace zai turo musu harda files na private investigation akan familyn Adiaha inma suna son suga shaida akan komi domin hanklinsu ya kwanta. 


Alhaj bello da hjy khadija still basu amince da zancen auren kai tsaye ba saidai sunce  sudai bazasu hana auren ba amma maganan ayishi yau yau sai sunyi shawara atsakaninsu tukuna, Sukace a basu nan da karfe 10 na safe zasu nemesu suji.


Bayan sun kammala wayar suka zauna tsakaninsu suka dan tattauna Akan lamarin Kadan kafin kowa ya koma sashensa domin yin cikakken tunani.


Banda tausayin Adiaha babu abunda ya cikama alhaj bello jimada kai.


Shikansa gani yake kmr tabbas koba dan komi ba iyakar jihadin zanca addini da Yarinyar tayi ta baro iyayenta akan dansa kodan wnn zai bari Ahmed din ya aureta dan su samu ladan shahada dukansu.


Ata fannin hajya  khadijatu kuwa kanta sosai ta kulle tsakanin labarin Adiaha da kuma lamarin kafayat da already take zarginta da juya mata baya.


Wani bangaren na zuciyarta na gaya mata cewa idan sukayi hakan basuma kafayat Adalci ba duba da irin jiran Ahmed datay tun tsawon lokcin yaranatar su,awani bangaren kuma inta tuno da labarin adiaha sai taji aranta cewa babu yadda zasuyi su watsa ma yarinyar nan kasa a ido musammn ma data sadaukar da komi nata domin Ahmed.


Jin cewa kamr bata da alqibla yasaka ta kira sister ta hjy maimunatu, 

Taci sa'a kuwa dan a aiport take zatazo south africa cikin birnun johannesburg domin tattaunawa da shugaban kasarsu tacan.


Nan ta gaya mata abunda ake ciki dan sosai ta rasa bayan wanda zatabi.


Bugu daya kuwa hjy maimunatu ta zaɓar ma Ahmed auren Adiaha, ta fito fili ta gaya ma hjy kahdijatu cewa yan uwan mijinta sun anty mojushola sunaso suyi amfani da kafayat din ne dansu mallake gidan ta batare da tasani ba,sann tace mata tunda Allah ya kawo mata babban mafita tayi marmaza kawai tay grabbing din shi, wann din wani oppurtunityne babba, tace mata tabi bayan danta Ahmed kawai akan abunda ya zaba makansa karta sake tay sanya akan ra'ayin kowa cos evryone is selfish about his son.


Yau har fada tay mata sosai akan nunawa datakeyi wai tanajin tausayin Kafayat tace mata duk layinsu dayane

Zatazo ne ta mallake mata danta bawai dan tazauna da su lpya ba.



Dake bata da wani lokci sosai maganan a tsaye sukayishi tace inhar ta kammala meeting dinta a south africa da wuri zatazo nigeria sama sama taga me ake ciki dan bazata taɓa kyalewa ayi ma yar uwanta taron dangi ba.


Bayan nan suka kammala wayar.


Ajiyar zuciya hajiy khadijatu ta sauke dan kuwa tabbas tasan babu yadda zatayi face tabi shawarar yar uwarta tabi bayan danta akan abunda yake so din.


Ta tuna jiya jiyan nan ma saida kazim yay musu irin wnn nasiha akan batun cusawa ahmed ra'ayi na daban. Zancen depression din da akace ya shiga ciki akansu sosai ya dameta dan tasan danta yanasonta sosai dolene yasaka abubuwa aranshi muddin zata juya masa bata.



Zama tay tanamai dogon nazari kafin nan ta tashi ta sake yin wanka ta saka wani irin cool royal blue ceibo lace dayaji wani irin aikin stones na alfarma, sosai tay kwalliyarta sama sama mai fidda kwalisa tay kyau ta fetsa turarenta masu qamshi snn ta dawo sashen mijinta ta sameshi yana kan danna wayarsa shikadai



Sau biyu ya kalleta sai yaji yakasa dauke idonsa akanta yafara mata murmushi hartazo ta zauna kusa dashi duk ya rude yana kallonta kmr sabon maye sabida hjy khadijatu kyakkwar bafulatana ce fara sol mai yellowish skin colour tana da tsiririn hanci zar kamr pencil, dirinta na zamani nne irin wanda tsufa baiya nunawa sosai ajikinsu din nan.


Har saida tay murmushi mai sanyi tare da lumshe ido tanamai kwantowa ajikinshi kafin nan ya dawo hayyacinshi sosai yasaka hannunshi slowly ya rungumota jikinshi sosai yanamai shunshuna qamshin turarenta mai dadi da shiga jiki, har wani lullumshe ido yake alaman dadin qamshin yana bugar dashi sosai.


Kaunarta ya dingaji aransa yanamai ratsashi sabida yanason mace irinta yar kwalisa da zata rika waiwayo masa da zamanin kuruciyarsa dan ya dingajin kanshi kamr matashi ba tsoho dan sittin ba.


Kisses masu zafi zafi yake sakar mata akan labbanta da goshinta

Ahankli har abun ya fara yin nisa sukaje dakinshi atare suka biyama junansu bukata cike da shaukin juna kamr ba atare suka kwana jiyan ba.


Bayan kura ya lafa kanta na bisa kan kirjinshi ya rungumota yana shafata kadan suka fara hirar lamarin dansu Ahmed, tunda ta fito fili tace masa itadai inhar Ahmed ya amince itama ta amince dan bata son tayima Ahmed dole a batun rayuwanshi amma zataso idan ya samu nitsuwa yay considering din auren kafayat din itama.



Alhaj bello dake cikin shaukin soyayya yace mata shima ya amince, amma inhar Ahmed baida ra'ayin auren mata biyu kwata kwata bazai sake takura mashi akan aure ba..yace mata duk sakacinsu ne ya jawo Ahmed ya tsallakesu da damuwarsa yakai kukan sa wajen yayunsa.


Haj khadija tace hakane 

Sunyi kuskure ahaka amma komi zai gyaru.


Daga nan ta rungume mijinta gam gam ajikinta tanamai yaba mashi sosai akan irin hadin kan  yayansa da hallacinsu saijin kanshi yake acan sama yana kara huruwa sama sama tsabar dadi.


Kamar jiki baisha ruwa ba haka ya sake komawa duniyar soyayya da matarsa dake ita kadaice matarsa daya auro mai karancin shekaru snn yayi tarawar aure da ita a matsayinta na budurwa wanda bata taba saduwa da kowani namiji ba saishi shiyasa haryau yake mugun ji da ita a harkan kwnciyar gadon aure.


Saida suka murza junansu akan gadon suka gaji snn suka shirya suka fito cike da shaukin soyayyarsu su mai dadi.



10.30 am suka kira Brother hamzat shikuma yay connecting da brother kazim suka basu go Ahead akan ayi komi daya dace akan batun ahmed din, hjy kahdija ma tace ta amince musu dan tasan hakan datayin ma zai saka dadarta taji dadi sosai 


..tsabar alhaj bello ya yadda da yaransa bai wani ja ba da sukace karfe biyu zasu daura auren yace musu suyi komi zai aiko da kudi shima tare da wasu yan uwansu a matsayin magabantan ahmed din daga nan abuja, yace su tabbata bayan an daura auren zasu tura masa file din information familyn Adiaha zai duba izuwa yamma idan an kammala walima zaije ya sanar dasu anty mojushola komi kuma yasan suma bazasuki ba.



Komi ya kammala Alhamdullhi aka watse kowa na farinciki aransa.


Daga nan iyayen nasu suka shiga bidirin walima tare da family members aka fara hidima na komawa sabuwar gida, 


hjy khdija da mijinta yau wani sabuwar soyayya suka bude kowa yanata kallonsu yadda suke makale da juna kusan kowani lokaci.


Bakaramin haushin hakan su anty mojushola sukeji aransu ba, kafayat is no where to be found, sai can har an kammala kawo duk wasu nau ikan abinci sann ta kirasu awaya tace musu taje wajen mum dinta for an emergency signature akan wasu document na babanta dayabar mata amma zata dawo sharp sharp kafin yamma dan bazatayi missing wann ranar ba.


Duk basu saka komi aransu game da kafayat ba nan aka cigaba da hidima anata bidiri ana shashewa sabida kaf yan uwan da abokan arziki sun halacci waliman an cika gidansun bana wasa ba dan har ankon leshuna farare saida akayi mata da maza.


A fannin kafayat kuwa tun yau da safe take rikici da mahafiyarta da kuma kawartan da suka kawo mata wani irin maganan banza akan waisuna son ta aure mahaifin Ahmed.


Tsabar takaici Kafayat saida tay kamar zata fasa musu kai da kwalba.


Yadda ranta ya mugun baci da suka ambace hakan yasaka sukayi saurince mata wasa suke mata amma har acikin ransu dagske sukeyi domin kuwa plan dinsu kenan sun fada ne dansukaga reaction dinta


Da kyar kafayat tay hakuri tabar maganan ya wuce dan awajen kamar zaginta akayi da akace ta aure tsoho dan shekaru sitttin da wani abu bayan ga Dan autarsa Ahmed nan dan talatin da biyu maijini ajika. Waima Me zatay da tsoho a duniyan nan? Kai ko brother kaxim ne akace ta aura batajin zata aure shi bare kuma babanshi..sosai maganan ta ƙona mata rai duk dama awasa suka mata shi.



Bangaren su Ahmed kuwa shikansa saida yasha mamaki matuka dayaji irin amincewar da iyayensa sukayi afarat daya cikin gaggawa.


Wanda aransa yasan cewa badon brother kazim ya hada musu harda siyasa ba da abunnan bazai taba yuwa acikin sauki ba.


Lokaci guda suka inviting dayan abokinsu bankole

Cos They plan the weding to be secret, shikam bankole akan abun munafurci dama yafi kauri dan ya fara tsanar halin kafayat tun ranar ta taɓa nunamishi cewa batason tarayyarsa da AHMED akan dan yana harka da yan mata.


Dukansu atare suka taso tun suna yara amma banji ne kawai yakeson Ahmed da kafayat, banky baison lamarin aransa ko kadan.


11.am ya iso yola ya same su a hotel, suna da ankonsu na kece raini da sukayi dayawa dan haka samun kayan sakawa baizamo musu tashin hnkli ba. Ahmed ne kawai aka kawo masa sabon kaya daga Abuja. 


Brown Shadda ce mai tsada da mahaifinsa ya aiko dashi tare da mutanen da ya aiko su suzo ayi dauren auren dasu.


Basu iso yola basai bayan zuhr prayer,..


Su kusan su bakwai alhaj bello jimada ya turo yolan duk yan uwansane da abokan arziki wanda shekarunsu ya danja sosai. Nan da nan su banji suka taya Ahmed shiryawa, kayan kuwa bakaramin kyau tayi masa ba duk dama baiji aransa kamar aure zaiyi yau ba.



Bangaren adiaha ma sosai aka shiryata awani beauty lounge dake babu lokacin dinka mata kayan aure haka sukayi odering bridal ready made lace flowing gown mai kyau dark green and gold in colour Da duk wani abu na kwalliyar Amarya.


Da kayar da accessories dinta duk saida suka cinye duba dari da sittin dake set biyu ne aka siyo mata harda mayafai da jewries masu kyau da kayan kwalliya.


Kafin 2pm na rana yayi Adiaha was already looking breathlesslessly beautiful irin kyan da bata tabayiwa kanta ba


Koda kakarta da sauran mutanen da suka danzo suka soma yaba kyaun datayi sai kuma taji kuka da damuwa mai tsanani yana gumeta taciki.


She become sooo emotional and weak tayaya ne  ma har zatay aure babu iyayenta aganganta?


 she tried to call them ta waya amma taji layinsu kaf baya shiga harda na yar uwarta ekaete.


Duk sonta da daurewa bata iyayi ba saida tay kukan jin tsananin kewar familynta ayau din sosai.


She wish and wish suna nan sukagan irin kyan datayi aranar aurenta.


Da kyar aka kwantar mata da hankli da aka nuna mata hoton a

Ahmed awajeb daurin aure taga yadda yay kyau shima tare da friends dinsa hakan yasaka taji sanyi ranta kadan.



2 .30pm na ranar asabar din aka taru a masallacin kofar gidan Alhaj aliyu mutanen Ahmed suka bazama wajen cikin shigarsu ta kece raini da motocinsu masu daukar numfashi.


Batare da wani bata lokaci ba akayi duk wata abunda ya dace snn aka daura auren "Ahmed damilare bello jimada, da matarsa miss Reema bassey.


Bayan ankamala komi cikin mutuntawa akayi pictures Dr banky dayaga Adiaha ta fito saiyaji jininsa ya hadu da ita sosai, haka ya dinga yabonta yana cewa ahmed tafi kafayat tsari da hankli nesa ba kusa ba.


In no time suka dawo tamkar abokanta suna sakata jin dadi aranta sosai musmm ma banji dayasan komi akanta sosai, Adiaha tana bashi tausayi inya tuna cewa Ahmed only married her out of pity and no way out compulsion badon soyayya ba.



Ciwo kan kafayat ya dingayi mai tsanani da kyar ta shirya kanta tsaf taci ado da yamma ta kamo hanyar dawowa Abuja domin tazo a karashe hidiman da ita snn ta zubawa su anty mojushola final drop na maganin acikin abinci suma ta gama da su.


Ciwon kan data dingaji yasaka bata iso Abuja ba sai wajajen karfe shida na yamma saura tazo ta samu angama taro anata daukar hotuna.


Kawai sai ta shiga rubibi akay hotunan tare da ita 


Ta zuba drink da magani ta kawo masu anty mojushola ta basu suka sha tasaka su a gaba tana basu labarin tafiyarta na karya.


Ta lura kamr hanklinsu baiya jikinsu dan sama sama suke bata kulawa duk idonsu na waje guda musmmn ma da sukaga kamr alhaj bello da haj khadijatu sun hada kansu yau da alama suna boye musu wani abu.


Harsaida aka daura auren Ahmed kafin nan brother hamzat ya hadasu dashi a video call yay magana da iyayensa suka saka masa albarka sosai. Alhaj aliyu daya kasance kamar shine waliyyin auren ta ln shima saida aka hadasu sukayi magana da alhj bello jimada da hjya khadijatu aka dan gaggaisa.


saida ya dawo cikin gidansa snn yadan fayyace ma hjy hajara yanayin iyayen Ahmed din sai asann tafara jin sanyi sanyi a zcyarta.



Da yamma lis akazo daukar adiaha dan karfe biyar da rabi jirginsu zai tashi izuwa abuja in less than 40 minutes zasu iso Abuja inda za'a kawota family house ta zauna awajensu anty moju shola.


Shiyasa yau din suka daga batun komawa cikin sabon gidan nasu duk dama anyi waliman an kammala


Saukin abun shine brother kazim da brother hamzat duk sun gayawa matayensu dawuri akansu shirya tarban amaryan Ahmed, tare da warning dinsu akan cewa karsu gayawa kowa news din auren sai sun iso da amaryan Abuja.


Anata hidiman waliman nan suna nasu shirin suma agefe duk dama gulman abun na ciccinsu agindinsu musmmn ma anty nuratu.


Duk sunsan masu anty mojushola ake boyewa komi dan ba'ason atada rikici acikin mutane mutuncin familynsu yaje ya zuba. Suna son suyi gulman amma suna mugun jin shakka da tsoron mazajensu



Wajajen karfe biyar na yamma aka kammala shirya Adiaha da wani brown bridal gown na atampa wanda  shima siyenshi a dinken sukayi aka rufa mata hadadden mayafi mai kyau akanta golden colour kalar jakarta da hadadden takalminta, duk ta rude ta makale sosai ajikin hajy hajara tanata kuka ayayinda take kan mata nasiha tanamai dada ja mata kunne akan zaman aure.  


lokacin har Ahmed ya sauya kayansa na auren izuwa wata simple yadi fari kal dashi yolo yolo datay masa kyau sosai amma baiko saka hula ba acewarsa kayan auren sunmasa nauyi ajiki.


Biyar na cikawa sukazo gidan domin su dauketa nan ne hjy hajara ta kira Ahmed gefe ta masa nasiha tare da bashi amanan Adiaha harta so ta bashi tausayi duk dama ya lura kamr batason auren aranta itama.


5.30 aka kammala musu nasiha atare snn aka rako adiaha cikin mota tanata kuka Ahmed baice mata uffan ba har suka kai airpot abokansa ne kawai suketa lallashinta hartayi shiru.


Koda suka iso Abuja ana kkrin shiga magrib agidan banji suka sauka tare da ita, after sallahn isha'i ne suka dauko hanya daga ita sai Ahmed din a mota har suka iso family house dinsun kamar yadda iyayensa suka umarcesa. 


Tun ahanya yafara fayyace mata cewa wasu daga cikin manya a familynsa basusan da zancen auren ba so she wll have to bear with their first shock and unruly coments.



Akaci sa'a kuwa Lokacin kafayat bata gidan har ta sabule ta wuce gidansu sabida haryanzu maganan brother kazim yana taba mata zuciya sai taji batajin sha'awar kwana agidan kuma.


Karfe 8 na dare daidai Ahmed suka iso kofar gidan aka bude musu gate suka shigo ciki saida ya kashe motarsa snn ya samu nitsuwa ya fara mata bayanin yadda zatay gaisuwa da sauransu.


Duk sai taji ta rude ganin komi ya mata na daban da yadda ta saba gani arayuwarta.


Tun tana cikin motar take karewa gidan kallo ganin gidan babbane ba laifi. 


Ahmed yace mata ta zauna acikin motarsan tukuna shi zai je ciki ya dawo kafin azo a dauketa saisu shiga ciki atare. Har ya bar wajen kallonsa takeyi tsabar yadda kirjinta yake bugawa da sauri da sauri.


Daga ta cikin gidan kuwa

Babu wani mahalukin da ba'a kirashi a falon yau ba.


Duk wani mai amsa sunan jimada ya hallara su anty moju kansu ya bala'in daurewa tunda sukaga an kirawo meeting din gaggawa nabazata.


Yaransu ne kawai basa wajen amma tunda ga kan brother hamzat da aunty nurat, aunty adizat da any zainab da su manyan gidan kowa ya halacci taron, sai brother kazim daya kira a video call dan ayi komi dashi.



Tun kafin zuwan su Ahmed gidan anty mojushola ta matsa sai dai agaya mata dalilin taron nan dan ta matsu taji meyene, nan alhaj bello jimada ya nitsu bai boye mata komi ba ya fara musu da bayanin yadda aka ciki da batun Adiaha snn yace musu dansa Ahmed ne suka yiwa aure yaudin zasuyi introducing matarsa wa duka family.


Anty moju tay ihu tace karya suke yi batasan da wann zancen ba, tun tunin nan wa ita kawai akeyiwa bayani amma shock din data shiga ciki najin cewa har anma Ahmed aure yasaka ta dawo musu tamkar wacce bata fahimtar mesuke cewa harsanda akace ga Ahmed din ya iso da matar da ya aura.


Kowa awajen jikinshi yay sanyi dasukaji ance ga labarin Adiaha amma banda su anty moju 


Babban damuwarsu shine da ba'anemi shawarsu tun farko ba akayi komi da hjy khadijatu. Gani suke an raina musu wayo snn dan uwansu ya kaskantar dasu sosai, ya dora matarsa a sama da matsayin dayake basu na respect aransa.



Brother hamzat yace ma su aunty nurat akan da suje waje ita da anty adizat su shigo ciki da Adiahan kowa ma ya ganta, caraf anty ramatou ta tashi tabi bayansu cos she just cant wait for this bomb blast gani take kamar karya ake musu.


Lkcin Ahmed yana sauri dan ya shigo ciki sai gasunan suna fitowa suma, a kofa suka hadu ya tsaya cak dan gani yay kowa na kallonsa kamar basu taba ganinsa a rayuwarsu ba, ko ajikinsa ya tsime snn ya wuce ciki dan ko gaishe su baiyi ba ya haɗe ransa sosai.


Anty ramatou ce ta tsaya dagata kofa bata karasa can din ba ta zuba ido tanata kallonsu, kirjin Adiaha bakaramin bugawa yakeyi ba musammn dataga manyan mata subiyu sun doso ta inda take, da wuri ta ja mayafi ta rufe fuskanta da mayafin mai gabaki daya.


Anty nurat ce ta bude kofar motar tsabar gulma saida ta yaye fuskan adiahar duka suka kunna hasken bulb din motar suka mata kallon tsaf tsaf dasukaga bata da aufi nan suka buga wata shewa tareda rangwada mata guda a kunne.


 _Iyawo wa_ 

"Ure welcome our bride"


Lokcin Kirjin Adiaha kamar zai fito wajen dan tsabar bugu,take sai taji hawaye masu dumi na neman kufce mata a idanunta jin yadda suketa yaren yorubanci atsakaninsu suna mata dariya kadan kadan.


Calmy and politely anty adizat ta cirota a mota sunata mata sannu da zuwa jikin adiahar sai rawa yakeyi batace musu komi ba har suka fara tahowa da ita cikin gida.


Ahmed ya shiga cikin familynsa yay gaisuwa ya zauna acikinsu kenan

Suka fara jin karar gudu  anty ramatou ne ta dawo cikin gidan tana ihu da yare bayan ta tabbatar da cewa dagaske ne batun auren nasa.


Gaban anty moju ta tsuguna hartana haki muryanta kasa kasa tana cewa _Ahhhhhhh Anty moju jẹ otitọ ooo, jẹ otitọ. Is truee oo is true_


Zumbur anty moju ta mike game da maida hanklinta bakin kofar tana jiran ganin shigowarsu. 


Ahankli suke tahowa da ita har suka iso ciki.


Brother kazim yafara magana da yare yanamai ce masu anty moju suyi controlling emotions dinsu su kama kansu dan kar yarinyar tazo ta rainasu a matsayinsu manya, maganganun daya dingayi ne cikin mita yasaka suka dan daure suka zauna atsomare anty moju tana ta karkada kafarta kmr wacce aka mata mutuwa.


Daidai bakin kofa suka saka Adiaha tacire takalmi tay bisimillah aka mata adduoin sann aka shigo da ita cikinsu cikin nitsuwa.


Tafiya take kirjinta na tsananta bugawa dan Tsabar kallon da ake mata a palon yasaka tafara jin kafafunta na harhadewa sai wani jiri jiri dataji yana debarta.


Hakanan daita daure har saida aka zaunar da ita snn aka dan yaye mata mayafin fuskarta tare da kammala zagawa da ita kan manyan gidan tana tsugunawa kasa tanamai gaishe su snn aka dawo da ita wajen zamanta danta samu nitsuwa.


Babu wanda zai iya kushe halittar Adiaha dan kuwa itadin ma Allah ya bata kyaun fuska bazaka dai ce mata tana da muni ba kuma ba ramammiya bace.


Tanajin akayi introducing dinta wa family members Din Ahmed daya bayan daya.


Anty moju taki sam ta kulasu sosai. Sai jefa musu bakaken maganganu take cikin jimami wanda inba kana jin yarensu bazaka fahimce cewa masifa da bala'in take sauke musu.


Acikin salo take kada kafarta tana maganan tanayi tana share hawaye dan gani take hjy khadijatune ta jawo musu wann abun


 _Emi ko le gbagbọ eyi._ 

I dont belive dis. _bawo ni o ṣe le ṣe Bello?_


 _haaaaaa nitori obinrin ti o yi ẹhin rẹ pada si mi?_ 

(Haaa, akan mace yau ka juyamin baya?)


Kowa sai hkri yake bata ana dada mata bayani akan yanayin situation din amma takijinsu sam sai maganganu take tun Adiaha bata fahimta harta soma ganewa.


Anty ramatou ta rirrike ta


 _bawo ni o ṣe le ṣe itiju mi bi eyi? kini mo ti ṣe lati tọsi eyi lati ọdọ rẹ_ _brother bello, how can u disgrace me like dis? what ive done to dersve dis from u._ 


 _Emi ko ni iye ninu igbesi aye rẹ, Bello_ (baka daukeni da daraja a rayuwarka ba bello).


Awajen kusan kowa ya amshi batun auren Ahmed hannu bibbiyu sabida tausayin Adiaha amma bandasu anty mojushola da suke kan kukan cewa dan uwansu bai darajasu ba.


Hakanan dai aka yanke hukuncin cewa Adiaha zata zauna agidan tare da hjya khadijatu zuwa gobe da safe idan komi ya lafa su anty moju shola sun sauko sai a saka ranar da za'ay mata waliman kaita sabuwar gida.


A dalilin rikicinsu yasaka aka daga tarewar Adiaha da mijinta acikin dakin daya akan harsai sun koma sabuwar gida nan da sati guda.


Yau kusan kwana su anty mojushola sukayi suna tsinewa hajy khadijatu a dakin su.


Sam kwanansu a gidan nayau tare da Adiahan bai wani musu dadi ba sabida yadda anty moju take daukar komi da zafi zafi.


Tunda aka yanke maganan cewa sai bayan kwana bakwai su tare Ahmed yay hamdala aransa dan dama bai shirya tarawa da mace acikin waynn yanayin tashin hanklin ba.


Brother hamzat ya miƙa ragamar komi a hannun su anty adizat na batun koyawa Adiaha wasu abubuwan kafin akaita sabon gida.


Washe gari da safe aka sake taruwa a falo anata bawa su anty mojushola hakuri Sabida cewa datakeyi an raina ta a matsayinta na babba an dauki matsayin ta an bawa hjy khadijatu.


Sosai ta tuma ta dawo da maganan ya dawo wani babba ta daura laifin komi akan hjy khadijatu, tun safe ta tarasu tana ta surutu ran Ahmed saida ya sosu sosai idonshi yy jaaaa jin yadda suke fassara masa uwansa agaban idonsa suna ce mata babbar munafuka.


Taruwar dangin suka so suyi mata subiyun sai ga hjy maimunatu tay sallama acikin gidan.


Wani sabuwar rikicin ne aka bude dan kuwa nan ne itama tabude musu wuta tace musu bata yadda da rainin wayon nan ba. Haka sukata jefawa junansu baqaqen magana harsuka rusuna sukayi shiru sabida hjya maimunatun babbar mace ce mai izza da kudi gata da matsayi kowa na jin shakkarta awajen sosai.


Zuwarta gidan da safen sosai yay amfani wa kowa dan kuwa itace kadai ta tsaya agabansu anty mojushola ta wankesu snn ta ajesu a matsayinsu ta musu tass tass ta rufe musu baki.


Tunda tay musu gori akan rashin kulawa da suka nuna akan lamarin Adiaha data baro komi nata tazo cikinsu zaman aure sai basu kara kushe zancen auren ba.


Dramar da akeyi aciki har waje ana jinshi dan haka kafayat datayi isowar safiya tazo ta samu ana kan baje kolin maganan auren Ahmed wanda ya doki kahon zuciyar a bazata.


Bari jikinta yakeyi sabida babu abunda bataji ba.


Harda warware maganan da akayi akace anty ramatou da anty adizat sune zasu shirya Adiaha kafin ranar tarewarta a sashen Ahmed na sabon gida.


Adiaha was so down to earth sam batada  hayaniya duk kiciniyar da akeyi dinnan saidai tay hawaye tashare wasu abun ma baji takeyi ba.


Saiyau da safe da hjy maimunatu tazo ta saita kan kowa snn Adiaha taji dan dama daman zama acikinsu ganin har anty ramatou ta sauko da fushinta tadan amsa gaisuwarta ta fara kulata kadan kadan.


Lokcin Kafayat tana daga waje ta jikin windownsu tana jeka ka dawo tanakan jiran wanda zaizo ya gaya mata gaskiyan abunda taji dan she is in shock irin daukewar brain dinan batama san mezatay ba.


Tana cikin hakan sai ta hango motar banji yay parking a tsakar gidan.


Ta Hanyar baya taga yay ta wawuro cikin sauri tabi ta wajen da niyyar zataje ta tsaresa, ko ina ajikinta rawa yakeyi har ta isa wajen bata cikin hayyacinta.


Banji yana dosowa ta wajen saiga Ahmed nan ya fito daga cikin gidan nan ya biyosa ta baya inda babu hayaniya da waya a hannunsa.


Cak kafayat ta tsaya tanata kallonsu daga dan nesa.


Daga cikin gidan kuwa tunda aka kammala magana sai Kowa ya watse ababbn falonsu aka bar Adiaha da su hjy khadijatu suna masu kare mata kallon tsaf din suma. Har yanzu Adiaha ta kasa sakewa acikinsu dan tsoro takeji aranta sosai.


Hjy maimunatu ne tacewa Adiahar akan da taje ta kirawo musu Ahmed suzo tare zata musu magana.


Babu musu ta mike tabar wajen suka bita da kallo cikin kyabe baki Hajy maimunatu tacewa yar uwartata " Da dan juma ne da dan jummai, saiki saka mata ido itama karko kyaleta tazo dana nata salon kabilancin dan duk layin iri dayane ya kwasosu.


Har Waje Adiaha ta zaga dan batasan inda zata sameshi ba,ahnkli take tafiya tana juye juye har tabiyo wani hanyar daya kawota waje



Lkcin Magana Ahmed sukeyi shida abokinsa banji wanda bama jinsu kafayat takeyi ba, sai data matso kurkusa takejin yadda banji yake tambayarsa lpyar matarsa da yadda family suka amsheta, tun bai amsa Banji ba, kafayat ta katsesu, a mugun haukace ta karaso wajensu tanamai shigewa tsakiyarsu kamr wata tababbiya wanda ta rasa hanklinta shekaru tamanin da suka shude.


Awargaje ta tsaya tana kallon cikin idanun Ahmed, nan take hawaye masu dumi suka wanke mata fuskarta then She decided to confront him akan abunda takeji akan zancen aurensa, muryanta na rawa zosai tace Ahmed wai dagaske ne kayi aure?...daidai fitowar Adiaha kenan sai ta tsaya agefe tanata kallonsu ...kafayat ta memeta masa tambayar ajere yakai sau biyar..


 sosai Banji yaji tsoron yadda kafayat din take ɓari kar kar kar idanunta suka jujjuya sukayi jajir duk yadda taso tay control kanta ta kasa tafara masa tambayar acikin ihu da kuka mai ragwabarwa.


Yadda kasan baisan me takeyi ba hakanan ya kalleta a kiyasce cikin bata wani irin cold attitudes mai bala'in kufularwa zaka rantse da Allah Ahmed baida imani ne acikin zuciyarsa. 


Wani irrin balamin gurnani kafayat taja wanda yasaka Banji ya sulale sidif sidif ya barsu wajen.


Tafara masa raki cikin birkicewa tanakan  tambayarsa akan meyasa zai yaudareta har yaje yay aure? Wacece ya aura? Yar waye a kasar nan?snn Dame ta fita?


Yace mata ra'ayinshi ne yasaka yay aure, and he wont explain himself to her.


Kafayat tafarajin kamr ta shakureshi awajen ta kaishi har lahira, inzai wuce saita birkita tasha gabansa, ran Adiaha sosai ya sosu datagan su a hakan,dan ba laifi ta fahimce cewa da alaman wnn din budurwan Ahmed ne koda ba agaya mata ba, yadda suke hargagin rikicin zaka gane cewa sun dade suna tare, a birkice kafayat take tambayarsa ko sonta ne bayayi yaje ya auro wata ba ita ba.


"Tafara tuna masa irin dadewar datay tana dakon sonshi, da irin burikan data daura akansu.


Rikici mai yawa ta balle masa dashi Har saida ta hatsala shi yace mata "baice mata baisonta ,

haryau yana sonta,She is his first love, kawai Allah ne baiyi ita zai aura ba.


Numfashinta taji yana shirin daukewa cak dahar zata fadi kasa yay sauri ya tarota ya rungumota jikinshi, tafara masa bori sosai,sai kuka kawai takeyi ajikinshin ta wani tantameshi tammm jikinta na rawa rawa anashi jikin sosai, cikin yanayin tallafota jikinshi yace mata ta fahimce shi snn tay hakuri shima ba hakan ya tsara ba amma hakan Allah yay auransa da yarinyar qaddararsu ce ya jawo.


Adiaha sai taji kishi mai yawa ya dabaibayeta musmmn ma dataji ahmed yace auransu na qaddara ne kuma yana son kafayat


Hawayen da ya soma gangaro mata ne tashare da sauri taje ta buya awani bayan pillar dan kar aganta awajen.


Ahmed yana barin wajen kafayat ta juya itama zata bi bayanshi,tana sauri zata wuce suka hade ido da adiaha nan suka tsaya jefawa juna kallon kallon batareda sunsan junansu ba.


Duk jikinsu ya basu matsayinsu amma basucewa juna uffan ba kowa ya kama gabansa.



Bayan yar nasihar da hajy maimunatu tay musu da Ahmed sai tay musu sallama akan cewa zataje gidanta dake katsina tay sati biyu kafin nan ta koma turkey dan su shirya dawowarsu nigeria gabaki daya nan da wasu kwanaki



Tay musu nasihan zaman aure snn Tasaka musu albarka amma hanklin Adiaha baiyaji jikinta sabida tunowa da maganganu da kuma rungumar da kafayat din datagani sunayi tare da Ahmed dazu ya tsaya mata a wuyanta sosai.


Hjy khadijatu tay musu sallama agidan itama nan suka fito tare ta raka yar uwanta har cikin mota, ta fito zata shige nata motar kenan sai ta hango Kafayat atacan baya tana tahowa a tsandare tana bari bari kamar wancce ruwa ya kwashota.


Kallo daya tay mata ta fahimce cewa she is in shock na jin batun labarin auren Ahmed.


Bakinta dauke da salati tazo ta rukota tana tabata kuwa ta sume mata a hannu.


A motarta ta sakata suka bar gidan takaita asibiti saida ta farfado snn ta dawo da ita gidanta inda babu hayaniyar kowa.


Haka ta dinga rarrashin kafayat tanamai bata hakuri, kafayat tay kuka harta dena, hjy khadija babu abunda bata gaya mata dan zucyarta yay sanyi ba. Itace ta bata labarin Adiaha da dalilin daya saka suka amince suka bar Ahmed din ya aureta, Karshe dai kafayat tace mata ta fahimce qaddara ne ya kawo Adiaha rayuwar Ahmed tace zata bukaci lokcin da zatay tunani akai domin ta samu nitsuwa akan hakan sosai.


Har gida hjy khadijatu ta rako kafayat har cikin gidansu snn tazauna da ita nadan wani lokci ta dinga lallashinta tamkar yadda uwa zatay wa yarta na cikinta harsaida kafayat din dankanta ta fara nuna mata babu komi ta fahimce komi.



In 7 days time za'a koma sabuwar gida tare da sabuwar amaryan Ahmed kowa na shiryawa wann ranar.


Ahmed tuni ya koma bakin aikinsa..


Anan family house aka aje Adiaha,kowa yasan kan labarinta shiyasa daga ta zauna su anty mojushola saisuyita zaginta da yarensu suna kiranta matsayaciya yar ciranin arziki. Idan suna son cimata fuska sai suyi ta mata tambaya akan gayan gara ko akwatin aure ko suta zakwalo mata zancen iyayenta wanda azahiri yana sakata jin wani iri aranta sosai.



Ga ahmed ya fara focusing akan aikinsa sosai sai baida lokacin zuwa dubata wani binma saida dare zaizo gidan inyazo ma baiya dadewa saiya koma gidan iyayensa dan bayason gulman su anty moju.



Kafayat was going tru a mental depression duk dama kowa yana kkri akanta amma mahafiyarta taki bari suna zuwa ko suna kiran yarta awaya.


Ahakan ta samu babban damar cusawa yarta ra'ayin plan dinsu.



Ana saura kwana biyar a koma sabuwar gida jikin kafayat din haryau babu kanta, sosai hjy khadijatu ta damu, kusan kowani lokci takan mata aika dan taji lpyarta a boye, 



acikin daren kwana na biyar din ne hajy fatihat ta tasheta a barci takaita cikin jeji da tsakar dare suka yi wani ritual na musamman akan Adiaha( refer to prologue to read this part in detail)


Bayan dawowarsu ne washe gari anty moju shola da anty ramatou suka fara fita suna yawo ixuwa wajajen da babu wanda yasan inda suke zuwa sai Allahnsu.


Hkama aka kasa ganewa kan alhj bello jimada agidan kwana biyu sam baya walwala sosai sabida yawan kiranshi meeting da sukeyi a boye suna tattaunawa da shi



Kwana biyu akaji sakat gidan yay shiru dasu anty moju suka dawo basa zama agida sosai,


Nan kuwa Adiaha harta fara sabawa da zama da su anty adizat dake suna koya mata sallah da dabiarsu na al'adansu sosai musammn ma gaisuwa ladabi da yadda suke girki idan hidima ya taso ko idan akayi baki.


Ranar da aka cika kwana bakwai ranar komawarsu new jimada mansion ranarne kowa acikinsu ya cancada ado aka ma Adiaha rufi mai kyau da kayan amare na alfarma da hjy maimunatu ta aiko mata da su kyauta,yau kowa saida yamugun shan mamakin irin gayun da sun anty mojushola sukayi.


Da yamma lisss bayan duk an hallara, aka nemi alhaj bello aka rasa kwata kwata. Haka nan har aka debi motoci daga gida aka fara sako amaryan ahmed agaba za'a koma sabon gida da ita.


Sun shiga gidan kenan har anyi addu'oi kowa ya wuce sabuwar sashen jim kadan saiga hayaniya da gangamin mata ana kida ana rawada yaren yorubanci, na musammn aka debo mawakar shela mata na yarobawa suka rako sabuwar amarya cikin sabuwar gidan jimada.



Su anty mojushola ne agaba sun riko hannayen kafayat dayaji lalle an bata tsamiya da goro tanaci tana kumsa yawun abakinta tana tofarwa ana binta da kida ana mata wakoki masu dauke da habaice habaice masu zafi sosai.


Wakokin da suke yi a tsakar gidan suna rawa suna shewa saida yasaka Kowa ya fito a sashensa acikin gaggawa kowa ya tsaya yana kallonsu.


Tun hajiya khadijatu bata kammala isowa filin ba tafarajin rade raden cewa mijinta ne ya kara aure.


Tana kuwa fitowa sarari tazo ta samu su anty moju da anty ramoutu tare da hajy fatihat da kawayenta na kasuwanci suna wani irin rawa suna karkada duwaiwakansu kafayat na tsakiyarsu tana taunar goro da tsamiya tana zubda yawu wanda hakan wani  alamane na habaici da cin fuska da akewa uwargida na nuna mata cewa ita ta tsufa, dan haka ankawo fertile young woman wanda zatazo ta haihu da mijinta agidan.



Haka suka cika mata gaban site dinta har ta inda take tsaye kafayat na tsakiyarsu idanunta a bushe tana rawar itama.


Daukewar cak hjy khadijatu tay tanamai kallon ikon Allah.


Wani doguwar capert suka shimfida akasa inda kafayat zata bi ta shiga gidan mijinta wato alhaj bello jimada kowani step tay sai anzuba wani irin ruwa a gora anyi habaici tare da addua kafin nan ta karaso.



Hjy khadijatu data tabbata da cewa wai kafayat ne ta aure mata mijinta sai tay na maza ta juya abunta zata koma ciki saidai shock din ya riga dayay mata yawa ko wani nisa batayi ba jiri ya kwasheta tafadi ajikin danta Ahmed dayay sauri wajen rikota jikinshi.


Agurguje ya karasa shiga da ita ciki dan shima shigowarsa gidan kenan jikinshi a ragwabe Bayan sunji labari awaje cewa mahaifinsu ne ya auri budurwan dansa kafayat yau a masallaci.


Nan brother hamzat da su anty adizat suka yo kansu suka tayashi rike mahaifiyarsan jin har ta dena numfashi sukayi sauri suka sakata a mota hankli tashe suka wuce asibiti da ita batare da sun kula kowa ba.


Hanklin Brother kazim ya mugun tashi sabida kukan da matarsa anty adizat takeyi data kirawoshi awaya abirkice tana gaya masa abunda yake faruwa musu agida, tun daga nan yay dialing lambar mahaifinsu yanata kirar wayarsa danya tabbatar amma baya daukar kiran.


Jininshi har tafasa yakeyi yana diri shikadai Ji yake kamar ya bace yaga kansa a nigeria acikin dare Dayaji wai kafayat ce mahaifinsu ya aura...



A rikice Anty nurat da Adiaha suka fito zasu bi bayansu,lokcin anty nurat taje dauko key din motar ta kenan Adiaha taji an riko hannunta an wani matseta da karfin tsiya.


 juyawarta keda wuya suka hade ido da kafayat da tay wani irin mugun hade rai tanai mata irin shakurarren kallo mai cike da baqar kishi da tsananin tsana.


Sanda tay mata zagin kare dangi da yarensu snn ta zungureta tace mata "su zuba su gani, "yau tay maganin Ahmed saura ita, ynzu ne wasan zai fara atsakaninsu dan ita ba zaman aurene ya kawo ta ba"..tazo ne dan ta kwace Ahmed dinta kmr yadda taje ta kwace mata shi agarinsu, Tace tay mata alkwarin cewa saita kwaceshi agaban idonta tana kallon komi babu yadda ta iyayi..


Da wani irin kallon mamaki Adiahan take binta dashi taja tsaki mai zafi aranta tace mata "ga fili ga doki.


Itama kallonta take ranta sai cewa takey Indai har bata samu Ahmed ba alkwari tay cewa babu wata ƴa macen da zata zauna lpya tare dashi hr Abada...... 


Galala Adiaha ta tsaya tanata kallonta harta juya cikin sauri bar wajen ta koma cikin yan kawo amarya ganin anty nurat tana dawowa kallonsu takeyi har suka bar gidan.


Tun ahanyar asibitin Adiaha ta buga tagumi tay shiru kmr wacce akamata mutuwa dan babu abunda yake nanatuwa a kwakwlarta face maganganun kafayat na cewa zata kwace mata Ahmed dinta...

ALHAMDULLHI...


DOMIN JIN YADDA ZATA KAYA ACIKIN LABARIN AHMED BELLO JIMADA DA MATARSA ADIAHA DA KUMA  MATAR UBANSA KAFAYAT.


DA KUMA YAR UWARSA YASRA HUSSAIN YARINYA YAR SHEKARU SHA TAKWAS DA ZATA ZO TA KASANCE WATA SABUWA ACIKIN SHAFIN QADDARAR RAYUWARSU DASHI DA MATARSA ADIAHA..


KISHIYAR KABILA IS AN INTRIQUIENG EMOTIONAL STORY OF HATE TURN INTO ROMANCE


 KINDLY SUBCRIBE @ *500 NAIRA*


*VIA 0152983148*

*MOHD SULE SURAYYA GTB*


EVIDENCE TO *08060712446*


MTN CARD SEND ONLY PIN OR PICTURE TO *080607124476*


OR TRANSFER VTU TRU *09132352275*





©SURAYYAHMS2023.


MEENA VIP GROUP HAUSA NOVEL DOCUMENT for more information contact on

+234 7014979567

WhatsApp ONLY

No comments