Recent Updates

Kana Naka Book 1 Complete Hausa Novel

 

[6/12, 12 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA..!*

*Wattpad:Jamilaumar351*


*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

_Saturday 10june_
*Time:12:00pm.*

*Wannan Labarin tundaga farkonsa Har zuwa K'arshen sa Sadaukarwa ne gareka MUHAMMAD KARIM(MK)*

*Labarin KANA NAKA,Tukwai ci ne tare da kyauta na musamman zuwa ga Antyna ANTY SIS♥️Ba rubutu na kike so ba*
*Ni kike so,yadda kika kaunace ni domin Allah kema Allah ya so ki ya kuma lullube rayuwarki da alheri Ameen*

*KIRKIRARREN LABARI NE DUK ABUNDA AKA GANI YA YI DAIDAI DA NA SUNA,KO HALLAYA,GARI KO DABI'A TO ARASHI NE,JUYA WANNAN LABARIN KO SARRAFA SHI TA HANYAR FILM KO D'ORASHI A YOUTUBE CHANNELS SABA'MA HAKKIN MALLAKATA NE*

_Da sunan Allah mai Rahma mai jinkai_

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/DWmMEYuvM0QH3eJh17wR4X

            *🅿️01*

*Shimfid'a.*
Katsina.
Area:Layout.

Karfe Tara ya shigo gidan nasa kamar yadda ya saba duk da yau yayi dare agidan mama chan kofar soro tunda tachan ya fara sauka bayan isowarsa Dazu da mangariba dagachan inda yake aiki a birnin Abuja.
Da kansa ya Tuko kansa Daga Abuja wannan Satin sakamakon Direbansa mallan iliya,mahaifinsa ba Lafiya ya tafi garinsu ya Dubasa bayan ya mai izini..shiyasa gabadaya agajiye yake gabobinsa gabadaya sun sake suna Bukatar Ruwa mai zafi tare da Tattausan Hannun wajen kwantar dasu su koma Daidai kuma Gajiyarsa ta Hada harda Dadewar da yayi mai baiyi Dogon Tuki ba ko Chan karofi zai Tafi Mallam Iliya ke tukasa Abu ne mai Wahala ka gansa yana Tuki da karan kansa.
Cikin muryansa mai Cike da Zati kamar ko yaushe yayi sallama bayan ya shigo Kyakyawan falon gidan nasa,wanda yara duk sun bata Fentin da Rubutu da Maker da Pencil,sun gama Lalata kyakyawan fentin Dake cikin Falon da ba'a sabuntasu ba Sannan ga kujerun nan duk sun ji jiki,sun fara yagewa Kushin din zaman duk yayi kasa,ya yamushe,shi kanshi Cafet din Tsakar Dakin ya fita Hayyacinsa Duk yayi Wusu wusu sannan yayi Datti Sosai.
Sau tari irin wad'anan abubuwan ke saka yayi zamansa Abuja baya kaunar ya shigo Katsina ya Shigo Gidansa yaci karo da yanayin yadda MATAR gidan ta bar yara suka barnata komai na gidam kamar gidan wata mai Saida Kuli kuli Tsabar yadda gidan ya fita Hayyacinsa.
Cikin yanayin kallonsa ya kare ma Falon kallo karamin Tsaki yaja ganin harda Takardun yaran duk sun yaga sun gama Haukata Falon bai nemi kowa ba sanin ba Sautin dawowarsa zataji ba Wacce ko agabanta kake sai kayi mgana kana Faman maimaici take iya jinka.
Yana Sarsarfa zuwa Bangaransa,wanda ke Rufe sai in ya Dawo ne yake budesa da kansa kamar Daga sama yaji Daga bayansa ance"Sannu da zuwa Yaya ISHAQ.."
Cak ya tsaya kafin ya juyo lokaci D'aya yana kara rike yar Jakar Laptop din dake Hannunsa,Girman Idonsa ya kara na ganinta domin har ya koma wanchan Satin bata agidan kenan bayan Tafiyarsa ne tazo gidan kenan..?
Bai damu ba illah baki Daya mele kafin ya ce"Sannu da gida.."
Ta amsa mai tana kokarin Tattara kayan yaran da suka gama Bidirinsu yanzu afalon kafin Yaya Fa'iza ta ja su ciki Domin su yi Fitsari su kwanta.
Bata Damu da yanayin da ya amsa mata  ba inda Sabo ta saba tun tasowarta bata Taba ganin Fara'ar Ya Ishaq acikin gidan yayarta ba sai dai in chan gidan Mama kofar soro ce ko kuma yana Tare da yan'uwansa su a Gare su mutum ne mai wahalan mu'amala.."
Agabanta ya Bude kofar Shashensa ya shige ya rufo kofa ta bisa da kallo ta jinjina kai Gaskiyan Anty Binta batagwara ce Data Dad'e tana Fadin ban da Kaddaran aure ta ina Yaya FA'IZA ta Dace da Ya Ishaq..?Ya Ishaq Dogo ne Farin Buzu tas dashi Domin Mama kofar soro Buzuwar Yamai ce,Sannan Baba Kabiru marigayi Cikakken batsine daya fito Daga Korofin katsina Sai dai kaf ya'yan mama ita suka Dauko Wajen kyau da Nasaba Domin har yau da shekaru suka ja kyanta bai Zube ba Tanan nan mai kyau da ita.
Kuma yanayin Tsahon sa ya biyo na Dangin su Baba ne dake Karofi suma Dagayen katsinawa ne marasa Lalaci sannnan sai ya Hada da Hancin Mama da Sirantar ka ta yasa Ishaq ya zama mai kyau kuma mai aji sannan mai Tarin Ilimi Addini dana Zamani Wanda Duniya ta san sa kuma take ji dashi,Ayanzu haka Babban ma'aikaci ne A Hukumar Tattara Haraji na kasa reshen Abuja(FIRS)Federal Inland revenue Services,Ya dade yana aiki a wajen shekaru hudu da suka gabata da farko a reshen su na Jahar katsina ya fara aiki da su shekara uku kafin ya samu karin matsayi sai aka yi Transfer dinsa ya koma babban Ofishin su na Abuja,sosai yake jin dadin aiki a abuja musamman ma da samun Adalin Shugaba irin Dr. Lawal bako da yakasance shine Shugaba a ofishin su na Abuja kuma Uba garesa ko nace wanda ke shirin zama Surukinsa nan da Lokaci kad'an.

Yaya FA'IZA kuwa iyakarta primary School,primary  di'n ma ba ta gama ba,a karatun Boko kenan na addini kam Saukakkiyace ta wannan Fanni sannan ta karanci sauran littafan addini iya abunda ya sauwaka ammh Duba da wannan Zamanin da muke cike domin kina da karatun muhammadiya ke bakowan kowa bace in baki Hada Fukafukan Ilimin Boko ba,Bama wannan ba Yaya Fa'iza ba irin Zabin Ya Ishaq ba ce ba cin haka ma Tana dq Laluran rashin ji,Bata iya jin mgana ahankali sai an mata da karfi take ji Dashi aka Haifeta Laluran TaMADINA ce ya shafeta Tunda ita din BEBIYA ce da shi aka Haifeta ba ciwo bane.
Tana wannan Tunanin tana Faman gyara Falon acikin ranta Tana Tunanin Yaya Fa'iza batasan ya Ishaq zai dawo yau ba domim kwata kwata bataji tayi zencen ba sannan basu da abinci agidan Taliyace ta Dafa ma su AMIR da Daddaren nan kuma D'ayace duka suka cinyeta ba Saura.
Kayan yaran ta kwashe ta tattara Takardun da suka yanka suka Zubar ta kai waje ta kofar Kitchen ta fita ta zubar a Abunda suke tara shara kafin ta Dawo Cikin Falon Dakin yaran ta Nufa inda yayar tata take domin ta shaida mata Dawowar Mijinta nata.
Da sallama ta shiga duk tasan ba lalle ta jita ba Amir Dake kwance ne ya amsa mata,Anum kuma har tayi barci mustapah musty Tuni har yayi barci,Ahmad ne a Hannunta tana Faman kiciniyar sanya mai pampers alamun wanka ta sake mai.
Karisowa shigowa Dakin yaran tayi mai Dauke da ciki Daya da karamin Tiolet,Adakin akwai gado guda uku kanana na yara,Daya na babban yaya ne Amir D'aya na Anun ce sai d'ayan na Mustpaha ne Ahmad na shan Nono Fa'iza bata yayesa ba wajenta yake kwana
Akwai Drowers na yaran guda uku acikin Dakin,inda suke ijiye kayansu na makaranta Dana gida,Har HAFSATU ta kariso ta zauna gefen Gadon Amir Fa'iza bata san ta shigo ba Hankalinta na kan saka ma Ahmad pampers ganin haka yasa Hafsatun watsa ma Amir Harara tana Fadin"Wai sau nawa zan maka Fad'an watsar da kayan ku duk inda kuka samu ne.?
Cikin muryan yarinta yace"Na Dauke nawa nasu Anum ne fa.."
Kayan ta Daga tana Fadin"Ai kai ne babba in suka bata sai ka gyara Amir din Umma.."
Jin Abunda tace ne yasa yayi mirmishi kafin yace"To Anty Hafsatu.."
Yafada Lokaci Daya yana kallon Fa'iza wacce har alokacin bata san Hafsatu na Cikin Dakin ba,Har sai da ta mike ta Zube kayan cikin kwandon da yaran ke tara kayan wanki Amir  D'an kimanin shekaru Shidda da wani abu aduniya yace"Anty Hafsatu..Umma fa bata san kin shigo ba, kiyi mata mgana."
Hafsatu tace"Zan mata ka kwanta kayi barci.."
Kai Tsaye yace"Umma nake jira ta gama shirya Ahmad ta mana Addu'an kwanciya barci.."
Hafsatu ta juyo Daidai Lokacin da Fa'iza ta Dago bayan ta gama saka ma Ahmad saukakkam kaya tunda zasu kwanta ne taci karo da idon kanwar nata akanta Cikin Sanyinta da yanayin mganarta Tace"Hafsatu..yau..she kika shigo..?
Ta Fada tana kokarin Daukan Ahmad.
Hafsatu ta zauna gefen gadon Amir tana Fadin"na da'n jima da shigowa.Amir oya bude Hannu muyi addu'an barci."
Ba musu ya Bude hannu itama ta Bude suna karanta addu'ar Barcin da Annabi ya koyar da karfi ita dashi zaku mamakin yadda yaron yake karantowa Tiryan Tiryan wannan kuma kokarin Fa'iza ne bata bari wannan Ilimin nata ya tashi a banza ba Tana kokarin Rabashi ita da ya'yanta.
Fa'iza kuma Ficewa tayi Daga Dakin ganin suna addu'ar Barci Bedroom din Dake kallon Shashen Ishaq ta Shiga ta Shimfide Ahmad a kan gadonta na Royal bed sai dai ya kwana Biyu duk yaji jiki.
Dakin shima dai kadahan kadahan,Wardrope ne babba adakin ssi kofar Tiolet,daga ganin yanayin Dakin shi kanshi Shirgi yayi masa yawa Sannan uwa uba Cafet din Daya malale bedroom din shima duk ya kode yaji Duniya Duk da karfinsa na Italiyan Cafet..
Ta kwantar da Ahmad din kenan zata Fito Daga Dakin suka kusa cin karo da Hafsatu daya sa ta koma da baya tana Fadin"Ban san zaki shigo ba.."
Hafsatu ta bi ta da kallon Tsausayi kafin tace"Yaya Fa'iza kinsan ya Ishaq zai dawo yau..?
Ta fada da dan karfi Saboda ta jita Da Sauri Fa'izan tace"Eh..Me kika ce..?
Tafada Cikin yanayin sanyinta da mganarta Hafsatu ta kara matsowa kusa da ita da dan karfi tace"Ya Ishaq ya dawo nace.."
Fa'iza ta zaro ido kafin tace"Yaushe..?
Wlh bansani ba..?
Hafsatu tace"Dazu ina falo kafin na shiga Dakin su Amir.."
Fa'iza ta kama Hanyar barin Dakin Tana Fadin"Yana bangaransa ne..?
Da karfi Hafsatu tace"Eh..!
Har ta fice tana binta da kallo ganin yadda take tafe tana kokarin Daidaita Hannun Rigar jikinta na Atamfa Daya dan mata yawa yana dan Fado mata.
Kitchen naa fara isa na Bude Fridge na Dauko mai lemu da ruwa na D'ora saman wani karamin Faranti na kuma Dora Kofuna guda biyu na fito lokaci d'aya na nufi bangaran Megidan.
Kofar shashen nashi yana Bude ne ta Tura ta shiga da sallamanta duk da tasan ba lalle yana Falon ba,Agidan kaf bangaransa ne ke da Falo da Bedroom har guda biyu ne,Kuma bangaransa ne yafi ko'ina kyau domin ayanzu ma kyakyawan Falo ne Dake Dauke da Manyan kujeru na alfarma masu ruwan zuma gabadaya Falon Ruwan zuma ne,harta da Labulayen kalansu ruwan zuma da Hadadden Tattausan Cafet din Dake Falon wani Sihirittacen kamshi na tashi na Irin Turaran da Ya Ishaq ke yawan amfani dashi ne..
Akan Center Table din dake falon na Sauke Farantin Hannuna kafin na karisa D'aya daga cikin Bedroom din Dake bangaran  inda na san Ishaq din yana ciki.
Da sallama na Tura kofar na shiga yana Tsaye gaban madubi ya gama saka kayan barcinsa masu Taushi Farare,riga da wando,waya ce a Hannunsa yana mgana cikin Sanyi da Tattausawa.
Ganin haka yasa Fa'iza ta juya zata fita har ta kai jikin kofa Hannunta kan marikin kofar ba zato taji muryansa Cikin Kaushinsa akoda yaushe ya Kirata.

  "FA'IZA.."

dayake da karfi yayi mganar na jisa Da Sauri nq juyo inaa gyara wuyar riga ta kallon da yake min ne ya sanyaya min Jiki D'aya sa na kariso gabansa Jikina na rawa ko kafin nq samu Zarafin mgana ya D'aga min hannu Cikin Fushi yana Fadin"Je ki ma kawai domin ganin ki karin Takaici ne a wajena.."
Yafada kai tsaye Lokaci D'aya yana kauda kai Dauke da matsanancin Takaicin daya Dade yana cinsa tun shekaru Takwas da suka gabata.
Duk da ba duka tna jisa ba nasan ransa ya baci sai na Durkusa kan gwiwiyoyina Cikin yanayina nace"Ka..kayi hakuri.."
Kamar na watsa ma Fushinsa Fetir haka ya taso min yana Fadin"An ki ayi Hakurin..?
Nace bazan hakuran ba..?
Aikin banza ni zaki raina haka Fa'iza..?In shigo gidan nan tund'azu kiyi banza Dani kamar wani kashi sannan kin ga Dama kin shigo bangarena kuma kin gan ina waya ki Tsaya in gama ki gaisheni ne ki ke ke jin asara ko..?
Har da juyawa ko kunya zaki Fice ga Dan iska ko..?
To tashi ki Ficemin Daga Daki bana son ganinki..Domin ganinki ba komai Cikin sa sai karin Takaici da bakinciki..wlh har gobe bazan Daina cewa Hajiyar Karofi da Baba sun cutar dani ba..Cuta ta har Abada da suka Hada aure na Dake FA'IZA.."
Ya karishe Fad'a yana nuna min babban yatsansa Lokaci Da'ya da wani banzan kallo dayake bina dashi kaina na kasa ko motsin kirkin na kasa yi daga inda nake durkushe Domin  indai ana Sabo da Tozarci da Mganangun Cin mutimci to ni na gama Sabo indai Daga bangaran Yaya Ishaq ne.
Baya ya juya min yana Faman kokuwa da bacin ransa yana jina Cikin yanayin mganata  ina kara Fadin.

"Kaayi hakuri don Allah..Ban ji shigowarka bane ina chan ina ma su Anum shirin barci sai yanzu Hafsatu ke shaidamin dawowarka..!
Sannu da zuwa.."

Kyaci yayi kamar wani maciji shifa ba Domin Ya Binta ta Kira sa akan  yazo yaga kayan lefensa da ya bata kwangilar hadawa ba,da babu abunda zai kawosa katsina cikin wannan Satin ballatana har yazo ya shaki wannan Bakinciki.
Juyowa yayi yana kallona Lokaci d'aya kawai ya tsaya yana kara kare ma Fa'iza kallo akasan ransa yana kara Tambayan kansa da gaske FA'IZA matar sace?
Fuskarta ya kara kalla yana jin Shima Tunda yake bai taba ganin mai baki,bakin Fuska irin Fa'iza ba, zai iya Rantsuwa ga Allah kaf ajikinta banda Hakoranta ba inda yake da Haske bakace ta kwantance irin bakin nan mai Duhu da Dususu,Sannan mummuna ce bata da kyau a ganinsa sannan bata da  Tsaho wanda Hausawa suke cewa mai cike Girman kyan y'a mace Gajera ce,da Fadin Fuskarta kamar Fanteka,Da guntun Hancinta da bakinta mai Fadi shima,Abu daya ne zai ce mai kyau a wajen Fa'iza shine tana da Kirar mata Wannan kam masha Allah Dirarriyace Kirjinta da kugunta suna cike da Fasali ya mace ko ayanzu Data Haifi ya'ya Hudu bata Sauya ba Ta na nan da Jikinta mai Fasali daidai misali bata da kiba sai dai Haihuwa ta d'an Budata.
Sai kuma bangaran Ni'imar jikinta ta wannan bangaran bai da ta cewa ya san Fa'iza fiye da yadda ya san kanshi Fa'iza bata shan kayan mata ko wani abun da zai kara mata Ni'ima duk abunda yaji in yazo tarayya da ita shine Hallitarta wanda Ubangiji ya yi mata,bazai kusheta ta wannan bangaran ba,abu daya ne ke masa cikas baya sonta sannan tun farko komai nata a wajensa bamai kyau ba ne shiyasa ta wannan bangaran ya gaza sakin jikinsa to ya saki jiki a wajen Fa'iza yaji me..?Matar da bata iya komai ba,Shiyasa ba kasafai ya cika Raba'arta ba.
Kayan jikinta ya kara bi da kallo,sai da Ransa ya baci har gobe yana jin Mamakin yadda Fa'iza bata taba saka kayan da yayi mata Daidai ba ko Rigar da hannu yayi yawa ko Sikat kagansa kamar Buhu in yayi mata mgana sai tace itake son haka kada watarana su mata Kad'an,Yau ma din riga da Zani ne ajikinta Rigar Hannun dai bai zama ya na yi ya na Sabule mata Jan Bra dinta Data sanya tana bayyana Saman kafad'anta.
Wani mololoon abu ya tsaya mai yaki wucewa a makogwaronsa Saboda Bakinciki kamar shi  ISHAQ KABIR KAROFI kamar shi Ace wannan abar ce Matarsa Uwar ya'yansa..?
In ya kalli FA'IZA sai yaji Fiye da madaukacin Takaicin daya ke ji in ya tuna itace yau MATAR SA..Fa"iza ba mafarkin sa bace a irin Rayuwar ISHAQ KABIR KARAFI..Sam Fa'iza bata dace ko kadan da Tsarin Rayuwarsa ba kowa yasan Ishaq dan gayu ne mai ilimi ne,kyakyawa ne dan Fafane d'an Alfahari ne Duniya tasan da zamansa mai Burin Auran mace FARA mai kyau mai Tarin kwalayen matakan karatun Zamani SAI DAI KASH"
Hakan bai samu ba..Sakamakon kutse da Fa'iza tayi cikin Rayuwarsa ta Ruguza Mafarkinsa har Abada bazai daina Hango FA'IZA a matsayin Nakasun Mafarkinsa ba.
Sannan karin bakin cikinsa yana da Burin kullum in ya Dawo aiki kyakyawan matarsa ta tarbesa ita da yan Gudi gudin ya'yansu Farare masu kyau kamar ya'yan Turaawa tun yana yaronsa yasha yin wannan mafarkin sai dai ina Hajiyar Karofi da Baba sun Saka almakashi sun Datse wannan Mafarkin nashi,Gabadaya ya'yan da suka Haifa da Fa'iza Shekara Takwas da auransu duka ita suka Biyo acikin su ba wanda ya Dauko ko da Hasken Fatansa ne sai Baki irin na uwarsu,Yana Tsananin kaunar yaransa ammh wani Lokacin yana kunyar nuna su ga Duniya Saboda a yanayin Tsarin Rayuwarsa bai kamata Tsarin Iyalansa su zama haka ba.
Duk da irin barnan kudin dayake yi a kansu Fa'iza bata da wannan Tattalin komai sai ta barshi su lalata shiyasa ya gaji ya barta ta karaci muguntarta sai dai yaci ta ita kadai.
Gefen gadon Dake Dakin nasa ya koma ya zauna yana Kad'a Fararan kafafunsa masu cike da gargasa yana kara kallon Fa'iza Dake duke har Lokacin kanta na kasa kamar tamai Sujjada,Kai ya girgiza yana Tunanin yadda yaso ya Dakile ma Fa'iza Haihuwa sai dai ina kana naka ne Allah na nashi,Kowani Tsarin iyali bai karbeta ba,da an saka mata lokaci kadan' sai ya bata matsala na karshe ma da aka saka mata yar Ashanan da jini ya Tsinke mata Dakyar ta sha Ashe Rabon Ahmad ne,Haihuwa take yi akai akai ita ko gajiya batayi da Hidiman yara da Haihuwa kamar akuya..?
Tsakani ga Allah ya'ya indai ta Bangaran Fa'iza ne shifa ya kai makuran Hakura da hakan.
Shi kadai kawai ya saki Tsaki"Mtsewww.."
Kallonta ya sake yi kai Tsaye kafin yace"Where is my Childreen.?
Yafada da dan karfi ta Dago tana Kallonsa Kafin tace"Eh me kace..?
Wani Tsakin yaja Kafin yace"Na manta ba Turanci..Ina yarana na nace..?
Mutum yayi ta wage baki yana mgana har sai makota sun gama jinsa ke ko Sirri ne bamai yi Dake domin kafin ki gama gane abunda mutum ke nufi Duniya ta gama jin Halin Dayake ciki..Mtswwwsss.."

  Yana gama Fadin haka ya mike ya Tsallaketa ya fice Daga Dakin,Kaina na kasa na saka hannuna na share guntun Hawayena kafin na mike Salau Salau nabi bayansa saman D'aya Daga Cikin kujerun falon na samesa ya kunna kallo remot a Hannunsa yana Sarrafawa.
Jikina na rawa na karisa inda na ijiye Farantin dana shigo dashi na Tsiyaya mai ruwa mai sanyi nataso nazo gabansa na Duka ina Fadin"Kayi hakuri..Ga ruwa kasha.."
Sai da ya ga Dama sannan ya kalleni kafin ya amshi ruwan kadan yasha ya maida mata yana Fadin"Da ruwa kadai kika iya tarban mijin ki da yayi kwana Goma baya nan..?
Ya fada yana mai Tsurata mata ido Fa"iza bata ji farkon mganarsa ba sai karshe yasa tace"Kwana goma..?
Tafada Cikin alamun Tambaya kai kawai ya Dafe kafin yace"Innalillahi..Gaskiya an gama Dani..Ishaq ka gama aiki kawai.."
Yafada kamar yayi kuka kafin ya kalleta yana Fadin"Ahmad yayi barci ne..?
Tana kallonsa ya kara ware murya yana Fadin"Eh nace Ahmad yayi barci ne..?
Da Sauri tace"Dukaa sun yi barci.."
Kai ya girgiza kafin yace"Ruwa k'adai ne kuke dashi agidan..?
Yafada muryansa asama kusan fa Fa'iza ta fara maida shi Sama sama ko ba da ita yake mgana ba ya yi mugun Sabon da sai ya Daga murya.
Cikin Ladabina nace"Taliya Hafsatu ta Dafa ma su Amir ina jin ta kare ma..Sai dai bari da sauri nayi maka ko Faten Dankali ne..
Dayake bansan kana Hanya ba."
Komawa yayi ya jingina jikin kujeran dayake kai yana maida Hankalinsa kan Tashar Mbc action din Daya sanya Reastling din da ake yi ya Fara Daukan Hankalinsa ganin haka yasa na Mike jikina na rawa na kwashi Farantin Dana shigo dashi na Fice ya Bita da kallo kamar ya saka kuka ai bazai ce A'a ba  inda kuma bazai Zagi Fa'iza ba kenan ta iya girki,girkinta ba inda baza'a Kaisa ba,Shi kadai ne abu mai kyau a rayuwar Fa'iza ban dashi shi dai bai gani ba ya Dade yana ganin mutane marasa sa'a a rayuwarsa ammh Rashin Sa'ar Fa'iza na musamman ne ta rasa wasu abubuwa masu Muhimmanci a Rayuwarta Rashin Sa'arta ne ma ya shafesa shima Gabadaya Rayuwarsa na neman komawa irin tata ba Domin Mama na Tsaye kansa ba, da Shima ya koma Dangin KURAME kamar yadda Zama da Kaddara ya Hadasa da Fa'iza.
Minti Talatin da wani abu na Sake Dawowa Dauke da Voul cike da Faten Dankali da Hanta sai maltina mai Sanyi Dana Hado mai dashi bai yi Tsaya mgana ba Domin yunwa yake ji Gidan Mama Tuwo sukayi shi kuma na Cimarsa bane abaya dai yaci banda yanzu Dayake cin guminsa.
Kasa ya Sauko ya tankwashe kafa ya sha Fantansa sosai,ya Dora da ruwa Maltina,Yayi gyatsa Lokaci D'aya da Hamdala Duk Fa'iza na gefensa yana Gamawa Jikina har rawa yake yi wajen kwashe kayan daya yayi amfani da su, na maida Kitchen adaran nan na wankesu domin Fa'iza in akwai abunda ta tsana kwano ya kwanar mata akitchen ba'a wanke ba.
Ita dai barta da barin shirgin yara da Rashin Shiga mai Fasali ammh ita da ya'yanta basu da kazanta ko yaya ne wanka ne Safe da yammah ita da yaran Duk Ranar duniya har sun saba suma.
Sai da nagama na kara leka Dakin na wajen Ahmad in sauri ban tsaya na  Tofe shi da addu'a ba yasa na bata Lokaci Wajen Yimai addu'a Hafsatu bata Dakin kila tana Dakin datake sauka in tazo Gidan.
Dayake nayi wanka Dazu da mangariba ban yi Tunanin Sake wani wankan ba na Sauya kayana zuwa wata Dogouwar Riga ta barci mai Taushi mai gajeren hannu,Duk da ina na da masu wando basa Burgeni nafi son Dogayen masu rufe min Har Cinyoyina Fa'iza ta Tsani ta saka kaya taga sun kamata ko sun nuna Tsiraicinta.
Ina cikin Daure gashin kaina Da na Tsefe shi yau da Safe,Hafsatu ce zata min Kitso yau bata samu Dama ba Karfanfan gashina tun na Virgin Dakyar yake Haduwa cika garesa bai da Tsawo inaa Hakin kamasa na Daure cikin Ribbon baji muryan ISHAQ asama yana Faman kiran sunana kamar yadda ya saba.

"FA'IZA.."

"FA'IZA.."

Da sauri na bar abunda nake yi lokaci daya na Rarumi Hulata ta barci na Saka ina niyar fitowa Daga Dakin ya shigo,ganinsa Tsaye a gaban ba Kikam da irin kallon Dayake min yasa nq rankwafa da Sauri ina Fadin"Gani ina..ina..!
Ban karisa ba ya Daga min Hannu Lokaci Daya yana Fadin"FA"IZA hala baki sam zan kara aure bane..?
Yafada yana Tsareni da manyan Idanuwansa.
Gabanna ya Fadi Ras! Sai na Daburce Da yanayin da yayi mganar,ba da karfi bane sai dai ai mganar auran nasa na Haddace ta akaina shiyasa nq karancin Bakinsa.
Cikin Fusata yace"Wai bada ke nake mgana bane kikamin banza..?
Da Sauri nace"Eh..Eh..Na sani..Mamakofar soro ta fadamin..Sannan sannan.."
Daka min tsawa yayi yana Fadin"Sannan me..?
Kinsan bana son wannan sanyin naki in muna mgana ko..?
Mgana bata kai ta kawo ba kiyi ta uban Rabata kamar wani abun arziki zaki Fada.."
Kokarim Boye Raunina nayi Cikin Dakewa nace"Anty Binta batagwara ta Fadamin wanchan satin da muka Hadu gidan Mama."
Wata Uwar Harara ya jefa min kafin yace"Kin sani ammh ko Fatan Alheri bazaki min ba Fa"iza..?
Kina bakinciki ne saboda zan kara aure..?
Da Sauri nace"Ahah.Naga baka nan ne,Shiyasa.."
Takaici ya kamasa kafin yace"Baki da waya ne..?
Ko lambatace baki da ita..?
Koda yake ke ai ba matar kiran jin Lafiyan miji bace za dai ki kira in wata Bukatarki ta taso miki."
Ya karishe Fada yana kallona Cikin Doguwar Rigar Barcin dana sanya kadan ya Rage bai yi Dariya ba.
Dariyan Takaichi wai zaki kwana da Miji ki saka wannan abu kamar kullib goro.
Karamin Tsaki yaja kafin yace"Na zata kina Bakinciki ne nace kin so kanki Fa'iza Shekara Takwas nayi ina Zaune Dake ban kara aure ba..Tsakaninki ga Allah ban miki alfarma da Mutumci ba Fa"iza..?
Fadamin da bakin ki na yi miki adalci ko ban yi miki ba..?
Ya fada da karfi yadda Zan jisa jikina  na rawa nace"kaayi min..sosai kayi min adalci.."
Naso na Daure ammh ina Raunina ya bada ni sai kuka hawaye sharr Tsayawa yayi yana kallon na kafin ya Tabe baki yace"Naji Dadi da kika Fahimci haka..Kada Goggon karofi  da yan'uwanki su tasaki suna Faman tambayanki kice musu ban yi miki adalci ba kiga yadda zamu kwashe.."
Malama ki kuma cire min wannan bargon Dake jikin ki wlh matukar wajena zaki kwana na Haramta miki kara sakamin wadanan Rigunan ai ba Cinikaya zamu yi ba..Ke kinga ma sha ma Zamanki ana tabaki Ke mai cikin Haihuwa Zan D'aure nan da Wata D'aya ne kamar gobe ne.."
Yafad'a Lokaci D'aya ya juya zai Fice Daga Dakin na Bisa da kallo ina D'igar kwallah duk da ba Duka mganarsa na ji ba ammh nasan yana kushe ni  ne kamar yadda ya saba.
Har ya fita Daga Dakin ni kuma har na juya kawai naji dawowarsa da kara Kiran sunana da yayi da karfi.

"FA'IZA..!

Da Sauri na Juyo  Cikin muryata Data Fara sauyawa saboda kuka nace"Na'am..!
Kallona ya tsaya yanayi lokaci d'aya yana rike da Kofar Cikin Mamaki na yace"Kuka..?
Na Dake ki ne..?
Da Sauri na Share hawayena ina Fadin"A"ah kamar wani abu ne ya Fadamim a ido na..!"
Bai Damu ba Kafad'a ya Zakud'a kafin yace"Mama ta fada miki gidana na Abuja Zeey zata zauna..?
Kai na gyada mai bai bani Damar mgana ba yacigaba da Fadin"Fa'iza kinga barin yaran nan suna bata gidan nan Duka duka yaushe muka tare acikinsa ammh kalli yadda suka maidasa..?
Komai naki ba kula ba Lura..?
Ko da yake ke kanki abar akula Dake ne bama ki kula da wani ba Anyway dai tunda kuka lalata gidan in ma mugunta ce ke zata ci..Sai da Safe.."
Daga haka ya Sakar min kofa ya fice na Bisa da kallo hawayena  na kara cika Idanuwana ina jinsa ya Bude kofa ya shiga D'akin  yaransa ya Dade kafin naji ya Fito ya Tafi bangaransa.
Kamar wacce aka Mangara kawai sai na fashe da kuka wiwi,Sai kuma nahau Rufe Bakina,lokaci D'aya da wayata Dake samam madubin dakin ta D'auki Karan neman agaji.
Da Sauri na mike na nufi wayar kirar Kamfanin Itel karama Tunda Anum tataba Fasa min Sreen din Samsumg din da Ya Ishaq ya siya min bai kara siya min wata babbar wayar ba ya Had'ani da karama acewarsa ba amfanin ma Siyan min Shafa shafan tunda ba iyawa nayi ba, ta bakinsa Fa'iza ba turanci.
Gabana sai da ya amsa ganin wacce ke Kirana Maman Naja ce Yaya ASIYA,Sunan d'iyarta ta fari ce wacce ta rasu Naja'atu ammh dayake sunan ya riga ya bita da Maman naja ake kiranta.

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA. SANNAN BASU DA BAURI MASU KIDIMARWA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*TUNTU'BI WANNAN LAMBAR DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.


*Janafty*
[6/12, 12:00 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA...*

*Wattpad:Jamilaumar351*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

*Fatan alheri gareki SURAYYAH DAHIRU GWARAM,Madallah da kawar arziki irin ki da karfafa Gwiwarki,Labarin nan yazo ma masu karatu Ina miki fatan alheri a koda yaushe na gaida Uwar Dakin Sa'ada da Gudiyo,sannan na ce Madallah da Uwar Dakin Yabi*🥰

            *🅿️02*

Da sauri na share Hawayena nayi kokarin daidaita yanayina domin ni Fa'iza ko Uwar data Haife ni bana kaunar taga raunina ballatana yan'uwana  da kullum suke kallona abar Tausayi wacce batayi dacen Gidan aure ba acewar su.
Saboda yanayin Raunin ji na, in aka kirani a waya a speaker nake saka ta wato amsa kuwwa yanzu din ma haka nayi na Daga kiran sannan na saka a speaker daidai Lokacin da naji muryan Ya Asiya na kiran sunana na amsa mata cikin dan D'aga murya.
Dagachan bangaran Ya Asiya tace"Fa'iza Ashe Yaya  Ishaq zai kara aure bamu sani ba..?
Fa'iza tayi wani mirmishin yak'e kafin tace"Eh Yaya Asiya zai kaara aure.."
Ya Asiya tace"Shi ne baki Fadamin ba,  kuma baki fada ma Mariya ba ko..?
Fa'iza tayi shuru batayi mgana ba Ya Asiya Haushi ya kamata ta fara Fada Tana Fadin"Kila ma baki sani ba..?
Domin sai ma an Dauke ka da Daraja da kima ne ake sanar dakai wani abun."
Da Sauri nace"Aaha nasani fa..Wlh na sani Mama ta fadamin sannan Anty Binta batagarawa itama ta fadamin."
Ya Asiya Dagachan bangaran ta jimjina kai kafin tace"Shi Uban gayyar bai Samu Fada miki ba kenan..?
Sai a bakin Uwarsa da yayarsa kike ji kenan..?
Anya Fa'iza wannan Rayuwar zata tafi ahaka kuwa..?
Shekara Takwas ai ba kwanaki Takwas bane."
Fa'iza ta share hawayenta da suka zubo mata kafin tace"Ai shima ya fadamin yau daya dawo.."
Ya Asiya tace"Umhh..!
Saboda takaici ma ta kasa mgana,Fa'iza kuma Daman ba ma'abociya mgana bace Ya Asiya Tagaji da shurun Fa'iza yasa ta katse mganar da cewa"Goggon Karofi ke Fadamin Zai yi aure yanzu muka gama waya da ita..Ita kema Fadamin Hafsatu tazo wajen ki shekaran jiya."
Fa'iza tace"Eh tazo shekaran jiya..tazo..."
Sai ta saki wanchan mganar Saboda bata son tayi Tsawo ita kanta Ya Asiya ai ta sani Fa'iza bata kaunar mganar Data Danganci Ishaq da Danginsa in ma ka matsa sai ta saka maka kuka Ajiyar rai ta sauke kafin tace"Yaushe ne Bikin..?
Fa"iza tace"Bansani ba.."
Ya Asiya tace"Allah ya kyauta zan shigo katsinar nima In nazo Duba Tamadina hala ba ma kiji bata ji Dadi ba..?
Ciwon kafafu take fama dashi."
Fa'iza tace"Naji Da Hafsatu tazo ta Fadamim."
Ya Asiya tace"Yaushe zaki leka ki Dubata ke da ke kusa ma Fa'iza yaushe Rabon ki da Dutsenmah Tun Sanda Ta madina ta kwanta asibiti an kusa shekara fa"
Fa'iza tayi shuru ta kasa mgana Saboda bata da tacewa Ishaq ne baya barinta tana son zuwa inda Mahaifiyarta take sai yace me zataje yi tana gidan wani..?
Ya'yansa bazasu je gidan wani suna Rab'e Rab'e ba.
Ya Asiya tayi  shuru yasa ta kyaleta sai ta shigo da mganar"Ina yaran nan..?
Hala sun yi barci..?
Ta amsa mata Ya Asiya tace"Shikenan Sai mun shigo zamu karisawa Tattauna ki kara Hakuri Fa'iza kowani bawa da irin tasa kaddaran..Mu Tamu kaddaran Rasuwar Baba ne itace silar Shigar mu duk Halin da muka shiga."
Fa'iza tace"Haka ne Daman ai KANA NAKA  ne Allah na nashi ne..Sannan na Allah ne Daidai."
Ya Asiya na jinjina kai tana Fadin"Hakane Fa'iza Allah ya mana mai kyau..Mu kwana Lafiya.
Fa'iza ta rakata da Fadin ta gaida yaranta Daga haka sukayi sallama Sannan na  ijiye wayar nq koma gefen gado na zauna ina mai kura ma Madubi Ido duk da ance ba kyau kallon kai a madubi in Duhu ya shiga ammh ni sai ta samu kaina da kare ma Jikinna kallo.
Tare da Fuskata ina Ayyana adadin Lokuta nawa ya Ishaq ya kalleni ya yab'a min..?
Koda yaushe cikin kusheni yake yi an samu ma bayan sun fara Tara zuru'a ya Daina jifana da kalmar Mummuna ammh kalmar Baka sai dai in yan Cin mutumcinsa basa kusa ni na sani Tazaran Dake tsakanina da Ya Ishaq kamar Tazaran kasa da Sama ne ko abaya ban taba mafarkim auran miji kamarsa ba Domin ba Tsarana ba ne, sannan ba kuma Had'i shi kanshi na san ni ba irin wacce ta Dace dashi bane Mama kofar soro kullum tana Fada min hakama Anty Binta batagarawa,To ammh Ba kai kake Tsarama kanka Rayuwa ba Allah ne Kana naka ne yana nashi kuma Tsarinsa ne akan gaba.
Na tabbata ba Domin kakkausan Bakin Baba kan Ya Ishaq ba, da Tuni bayan kasa ta shafe idonsa ya rabu dani  ya samu salama kamar yadda yake Fadi sai dai ina Ya Ishaq bazai iya Tsallaken mganar Baba ba Shiyasa har yanzu muke tare ina D'aukan dukkan cin kashi da Tozarcinsa
Bani da wani gata nan Duniya sai Ishaq shine uwaa na shine Ubana  da Duniya ta Tamadina ga yanayin yadda Rayuwa tazo mata sauran yan'uwanna ba waje daya muka tashi ba Bayan Rasuwar mahaifinmu  Raba mu akayi ni a karofi na fara Rayuwata Kafin dalili ya yanke zamanna achan Baba Kabiru ya maido ni katsina ya Damkani Hannun Mama.
Hawaye na haka suke faman zuba ban iya saka Hannuna domin na tare su  ba Saboda ko na goge su wasu ne zasu kara fitowa a irin wannam Lokacin nake samun Fitar da abunda ya dade yana Damuna,Ba bakinciki nake yi Saboda Ishaq zai kara aure ba,A'a ai daman na sani yafi shekaru yana ikararin zai auri Zab'insa Daidai da Ra'ayinsa tun kafin ma yakai haka zama a rayuwa ballatana yanzu dayake jin kansa ashi wani ne.
Sai dai abu D'aya na sani zuwan Amarya nan tozarcin danake sha sai ya Ninka wanda nake sha abaya abu daya ne naake gudu wulakanci ina tsoro da firgicin Amaryan tazo tasan duka labarina tazo tana ganina a wulakance ta goraanta min Kamar yadda Shima yasha Fadi Fa'iza ba kyau ba Turanci komai nata Total zer0 ne. ammh a raina bana mai Bakinciki don zai kara aure ai yayi ma kokari da muka kwarari wad'anan shekaru bai kara ba,sai yanzu na kuma ji Dadi da matar zatayi nesa damu ko Bakomai kazantar da baka gani ba Tsabtace akasan chan raina kuma ina da kishi Domin ina son mijina so irin wanda Duk Macetagari zata nuna ma uban ya'yanta,duk da tarin Nakasun da auran mu ya kunsa, duk da ko shi din' bai taba sona ba.
sai dai bazan barsa yayi wani Tasiri a kaina ba tunda inda Son ke da muhalli baza'a martabasa ba, zan iya Rantsuwa ko Kaffara bazan yi baa Ya Ishaq baya sona karfin Biyayyar Baba ce take Rike da igiyar auranmu.
Naso na sauya Rigar Jikina kamar yadda yace sai dai kuma Tunda yace na bar shi nasan ko da na bisa Shashensa sai ya koreni shiyasa ban bata ma kaina Lokaci ba na Haura kan gadona naa jawo Ahmad jiki na,na Rumgume sa Abu D'aya ke sanyayamin Rai ya'ya na Domin duk duniya bayan Ishaq bani da kamarsu basa san iya adadin Lokacin Dana Dauka inaa kuka ba ammh nasan Har barci ya kwasheni kukana bai Tsaya ba.
Kiran Sallar Farko na  tashi kamar yadda ya zame min  Jiki Fa'iza bata barcin Rana sannan karfe Hudun Asuba take tashi sai kuma wani Dare.
Fita nayi naje Dakin yaran na Tashi Amir da Mustapha zasu bi Babansu masallaci Bayan sun tashi na fita zuwa Dakin Hafsatu na isketa ta tashi har ta Shiga Tiolet sai na Fice su Amir ta Tsaya akansu sukayi alwala Daidai Sanda Ishaq ya fito Daga bangaransa Sanye da Jallabiya baka da Carbi Kofar Dakin yaran ya Coge duk Fadan sa bai isa yayi ma Fa'iza Fadan rashin Tarbiya da kula da yaransa ba wannan in bai Gode mata ba ai bazai Zageta ba.
Amir ne ya karisa ga Baban yana Fadin"Oyoyo Daada sannu da zuwa.."
Yafada yana rumgumesa rike sa yayi yana Shafa kansa kafin yace"Jiya na dawo lokacin kun yi barci.."
Ina musty..?
Yafada yana kallonsa Fa'iza na kiciniyar saka mai wata riga bayan ta cire mai na barci sai faman mutsike ido yake yi alamun barcin bai sake sa ba.
Dariya yayi yana kallonsa kafin ya Bude Hannunsa yana Fadin"Oya come Here..!"
Da gudu yaron ya nufessa ya Fada jikinsa yana Fadin"Daada.."
Shafa kansa yake yana jin Farimciki acikin ransa Fa'iza ya kalla Dake tashin Anum da dan karfi yace"Kyaleta mana.."
Fa'iza ta Dago tana Fadin"Suna da Hadda yau."
Yana rike hannun su Amir yace"Ai da Sauran lokaci ke komai naki na Hanzari ne karfe Biyar din Asuban ne zasu tafi Haddar..?
Bada karfi yayi mganar ba saboda Haka ban ma jisa ba nadai san yayi mgana kuma nasan bai wuce Fada ne irin nasa Daya saba ba,  shiyasa har yaja su Amir suka fice ban kara mgana ba..
Suna Fitan nayi kokarin tashin Anum Saboda tayi sallah ta wartsake kafin su Dawo Daki na muka koma Tare nima na Dauro alwala mukayi sallah Tare da Anum muna idarwa Ahmad ya tashi na Daukesa naga ya bata pampers dinsa,sai na mike na Goyasa na shiga Kitchen bayan na gargadi Anum kada ta koma barci ta zauna tayi azkar din Safe wanda yaran duk sun Haddace..
Ruwan Zafi na fara sakawa saboda nayi ma Ahmad wanka kafin sauran yaran su Dawo Sai kuma na fara kokarin Fere Doya saboda na soya musu na Tafiya dashi makaranta sai ga Hafsah ta shigo Kitchen din da Hijabinta.
Fa'iza Hankalinta na wajen aiki bata san Hafsatun ta shigo ba sai da ta tabata sannan ta dago tana kallonta kafin tace"Kin fito Hafsah..?
Da yanayin mganarta Hafsah tace"Eh Ina kwana.."
Da dan daga Sauti Saboda Fa"izan ta jita sosai.
Ta amsa mata Cikin Sakewarta Hafsah tace"Bari na amshe ki."
Fa"iza tace"A"a barin min wanan aiki..Ga dai ruwa nan na saka in ya Tafasa ki juyo ki yima Ahmad da Anum wanka kafin su Amir su dawo."
Tafada cikin yanayin Raba mganarta Hafsah ta amsa mata da Toh,ba Dadewa ruwan ya Tafasa ta Dauko wani Karamin baho ta juyo ruwan ta kai Tiolet din Dakin Fa'iza da suna da Shower na wanka ya lalace kuma ya Ishaq yace da gan gane saboda haka bazai gyara ba.
Dawowa tayi ta karbi Ahmad ta je ta fara mai wanka ta shiryasa sannan tayi ma Anum nata wanka alokacin har su Amir sun Dawo masallaci suna Falo Tare da Ya Ishaq Sanda Hafsat ta fito Dauke da Ahmad daya fara Rigima ne Fa'iza ta fito Daga Kitchen din tana gaida Ishaq ya amsa mata bai ko kalleta ba Hankalinsa na wajen Amir Dake bashi Labarin abunda ya Faru a makarantasu jiya shi kuma Musty bai da Hayaniya yana Lafe jikin Uban..
Hafsah ma tabi ayarin yar'uwanta ta gaisheshi ya amsa yana Dubanta ganinta Dauke da Ahmad yasa yace"Ina zaki kaishi..?
Hafsah tace"Kuka yake yi zan kai shi ta bashi Nono ne."
Hannu ya mika mata yana Fadin"A kitchen din zaki kai mata shi..?
Wato salon ta jefa shi Cikin wani abu kin santa bata da kula."
Hafsah dai batace komai ba ta mikamai D'ansa ya Cafe shi yana Daga sa sama cikin Fara"a Hafsah bata damu ba ta karisa kitchen din Domin kama ma yayar nata aikin itama gobe zata koma Daman Hutun Midterm break Aka basu a makaranta yasa Goggo ta barta ta taho itama tana Karofi ne wajen Hajiya Indo da suke kira Goggon Karofi ita take rikonta tun bayan da ta karbota wajen mahaifiyarsu Ta madina.
Suna Kitchen din suna aiki Hafsah taji Sanda Anum ta fito ganin babanta yasa ta nufesa cikin murna tana Fadin"Daada yaushe ka dawo..?
Daman Anum akwai kirniya da Rashin jin mgana Yana ganinta itama ya Tarbeta yana Fadin"Anum dina jiya da Daddare na dawo kun yi barci."
Kai Tsaye tace mai ina Tsarabanta yace sai an juma in ya sake fita Hafsah ce ke Sauraran Hiransa da ya"yansa banda Fa'iza da baji take yi Sosai ba sannan Hankalinta na wajen Soya Doya bata ma san Abunda suke ciki ba.
Kafin bakwai na Safe tayi Fa'iza ta gama komai sai ta bar Hafsah a kitchen din tana karisawa,ni kuma sai naje na Shiryan yaran saboda suna da Hadda Tahfiz ne tun Safe sai shida suke Dawowa Allah ya taimake ni Ahmad na wajen Ya Ishaq ya shiga Dashi Shashensa.
Koda bakwai da Rabi tayi sun karya sun shirya Tsab Cikin kayan makarantarsu Ga Basket din kowanne an shiryamai da soyayyar doya da miyar kwai,Sai lemu da ruwa Fa'iza na kokarin Tura Hafsah ta leka tayi ma wani wani makotanci Haruna mgana mai Tuka adaidaita shi ke kai yaran makaramtar Hadda da Boko a wata Ya Ishaq na Biyansa Saboda abaya motace har da Direba ya Daukan musu tunda Anum ta taba koke motar Mama ta sa ya bama Jamal kaninsa motar tana chan gidanta Kofar soro in ya Dawo Hutu Daga Kano inda yake karatunsa na Engeering yake amfani da ita su kuma Ishaq ya Daukam ma yaran mai adaidaita a cewarsa Tunda bata iya Tattali ba shi ba asararrre bane sannan kuma yace Mota bata Dace da ni  ba,irin mu yawo acikin Adaidatan yafi Dacewa damu,ni Dayake ban Damu ba, ba fita take yi sosai ba Daga Gidan Mama sai gidan Anty Binta shima na da'n Rage zuwa tunda ba maraba suke da zuwana ba Karofi kuma sai dai in an yi Rasuwa muje Gabadaya ammh ni kad'ai Ya Ishaq cewa yake bai yarda da ni ba zanje ne na Had'u da yan'uwana azagesa shiyasa ban ma Damu da Fitan ba nima.
Ina shirin aika Hafsah ne sai ga Ya Ishaq din ya fito yace shi zai kai su,jin Haka yaran suka fara Murna sosai,Tare da Ahmad suka tafi har Lokacin bai koma barci ba shima ai yasam Ishaq saboda gaskiya in yana Gida yana bama yaransa Lokacinsa nice dai bani da wannan matsayin.
Har sun fita naa bisu Haraban gidan ina kwalama Amir kira ya juyo yana Fadin"Umma menene..?
Ina Sosa gashin idona nace"Kada ku manta ku karanta addu'ar fita Daga gida."
Da Karfi Anum ta fara karantawa Amir na Binta shi da mustpaha suna gamawa nabisu da mirmishi ina Daga musu Hannu Ishaq dai Tuni ya Shige mota yana Dauke da Ahmad irin wad'anan Hallayar na Fa'iza ba wani Burgesa suke yi ba,Sai dai kuma a kasan Ranta yasan Tarbiya ce mai kyau shiyasa wani lokacin baya mgana.
Ganin ya shiga motar bai bude get ba yasa na karisa na Budemai motarsa ta Fice Daga gidan sannan na maida na Rufe,abaya munq da megadi wani Dattijo,Tunda lokacin da  Yaya Ishaq yaga ina basa Abinci yace don me..?
Ai yana Biyansa duk wata ba wata mgana kawai sai ji nayi ya sallamesa Daganan kuma bai kara Daukan mana wani megadi ba yace Tunda Zan iya na yi Hidiman get din da kaina
Sai da suka tafi naje nayi wanka na Sauya kaya zuwa wata Doguwar Rigar Shadda Dinkin zamani kan na gama Shiryawa Hafsah ta gyara Falon ta share in da yaran suka bata sannan ta gyaro Dakin yaran suma ganin haka yasa nayi mata sannu da aiki ni sai na shiga  Shashen Ishaq na gyara duk da ba sosai yayi Datti ba na Cika shi da Turaran kamshin Daki sanin sa mai son kamshi ne.
Kafin ya Dawo na jera mai kayan  karinsa,na koma Falo muka karya ni da Hafsah muna yi muna Taba Hira duk da Hiran Daga Hafsah ne ita Fa'iza nata Eh ne ko A'a sai mganar da batayi Tsawo ba.
Har muka gama karyawan bai shigo ba,Hafsah tatafi tayi wanka ni kuma na kwashe komai nakai kitchen na Fara kimtsa wajen,Bayan na gama nayi wanke wanke,ina cikin goge gogen kitchen din naji Sallama atsakar Falon Sai na leko da Towel din gogogogen a Hannuna,Baki na washe ina fadin" BADARIYA.."
Cikin bayyana Murna ta ganin wacce aka Kira da Badariya na Tsaye da katuwar leda a Hannunta yar matashiya doguwa Fara Fuska kamar ta Ishaq sai dai ta fisa Haske saboda ita macece Autansu ce Badariya Kabir Karofi.
Karisowa tayi Cikin Falon Tana Fadin"Anty Fa'iza yunwa nake ji wlh..akwai sauran abun kari kuwa..?
Tafada tana wanchalar da gyalen Hannunta Lokaci Daya da ledan Data shigo da ita.
Bata ma saurari Fa'izan Dake faman mata gaisuwan yasu Mama ba
Ta Shiga kitchen din tana Dube Dube ta samu Doya a kula da Miyar Kwai ta Dauko ta Fito Tana Fadin"Anty Fa'iza adana gaisuwarki sai naci na koshi Tukunna."
Dariya nayi  mata bance komai ba na koma kitchen din na Cigaba da goge gogen da na fara ina mai jin Dadin zuwan Badariya din duk cikin ya"yan Mama Ita kadai ce ke sona sai Jamal shi kuma bai da alkibla yau ya min Mutumci gobe kuma akasasin sa shidai baka gane ina ya Dosa,Ammh yana zuwa gidan nan wajen su Amir sannan yana zuwa cin abinci ba wacce tafi Tsanata Daman Tun zamana wajen Mama irin Anty Binta batagwara ita da Ya Ishaq daman basu so zamana agidansu ba Sun gama Dora min karan Tsana wanda har yafi ma wanda Mama take min tun ina da karanci shekaru kafin ma aure ya shiga tsakani da ya Ishaq
Sai da nagama aikin na Sannan ta sake Fitowa Falon na iske su Tare da Hafsah wacce tayi Rashe Rashe kasan Cafet tana Bude kayan da Badariya ta shigo Dasu ita kuma Badariya na kan kujera ta cin Doyarta suna mgana da Hafsah.
Ina Shigowa Hafsah tace"Anty Fa'iza kinga ankon Bikin ya Ishaq.."
Jin Shuru yasa Badariya tace"Bafa ta jiki ba..Anty Fa'iza ga ankon Ya Ishaq..kin gani..?
Sai alokacin najisu nabi Kayan Dake Hannun Hafsah da kallo sai na kasa mgana Badariya da Hafsah suka kalleni  Cikin wani yanayi kafin Hafsah tace"Kilama bata san da ankon ba.."
Badariya tace"Anya..?Anty Binta ta Dauko fa..Ranar agabana da tazo gidan Mama ta Kira ya Ishaq din tace zata Daukan ma Anty Fa'iza ,Anum kuma zata Hadasu dasu Hibba ne.
Hafsah tace"To ba mamaki."
Badariya tace"Wannan da kike Dagawa naki D'aya nawa daya..Yanzu Daga wajen tela nake bai Dinka Less din ba.."
Hafsah ta zaro ido tana Fadin"Wai nawa..?
Badariya ta mata Dariya ai sai tatashi ta Daga Tsalle tana murna ta Rumgume Fa'iza Dake Tsaye tana kallonsu tana Mirmishi Cikin Fara"a tace"Kinga Anty Fa'iza Badariya ta Dinka mana..!"
Fa"iza ta karbi Atamfan tana gani kafin tace"Sun yi kyau.."
Hafsah ta isa ga Badariya ta Rumgumeta tana Fadin"Nagode sister..Allah ya bar zumumci."
Badariya tace"Ameen ammh bani Zaki ma Godiya ba Ya Ishaq ne shi ya siya mana.."
Hafsah bata wani ji mamaki ba,Saboda in yayi Niyya yana da Alheri sosai tana ta godiya tana Santin kayan.
Badariya tace"Za dai kizo bikin ko..?
Nima yanzu aBakin Ya Ishaq nake jin kinzo Daga kai yara makaranta wajen Mama ya biya."
Hafsah tace"Zan zo tunda weekend ne."
Badariya tace"in Goggon Korofin ta bar ki ba..Domin ita kanta ban Tabbatar da zata zo ba..Naji suna waya da Mama tana Fadan Ya Ishaq bai Fada musu zencen auran nasa ba"
Hafsah dai batace komai ba Badariya ce tacigaba da Fadin"To waya fadamawa..?
Daga shi sai Mama sai Anty Binta suke abinsu Amaryan ma suna waya da Anty Binta tunda ita ta Hada lefen.
Hafsah tace"To yaushe  ne ma Bikin..?
Badariya ta tabe baki Tana kallon Fa"iza dake zaune gefe tana kallonsu kafin tace"Anty Fa"iza ta san Lokacin Bikin..?
Hafsah tace"Anya..? Batamin mgana ba."
Badariya tace"Karshen wata ne sauran Sati uku."
Hafsah tace"Allah ya kaimu nan za"a kawo Amaryan..?
Badariya tace"A"a chan Abuja zata zauna..Ai itama yar Abujan ce,mahaifinta shugaban ya ishaq ne a wajen aiki,Itama ai ma'aikaciya ce tana aiki da wani kamfani ban dai san ko na menene ba nima
Haka naji Anty Binta na fada ma mama cikin Hirarsu."
Hafsah tayi shuru jikinta yayi sanyi Tana kallon yar'uwanta wani Tsausayinta ya kamata sai taji Badariya na Fadin"Ya Ishaq ya samu Cikar Burinsa Mace mai kyau Fara Doguwa mai kwalayen zamani ga Kudi da Nasaba..Allah yasa a wanye Lafiya."
Hafsah ta amsa mata da Ameen kawai Domin bata da tacewa,Fa'iza ce ta dan Daga Sautinta tana Fadin"Badariya ya mama..?
Badariya tace da karfi"Tana lafiya..Tana chan tare da D'anta na barsu na fito amso dinki nan sanan kuma yunwa ce ta koroni."
Mirmishi kawai nayi ban ce komai ba ni kowa yasanni  bani dayawan mgnaa Saboda yanayina
Sai Hirar ta koma Tsakanin Hafsah da Badariya da Daman kawaye ne suna Hirar Hajiya Fatima wacce suke kira da Hajiyar Dala tana chan kano tana auran wani Babba a soja.
Hafsah ke tambayan su Suwaiba sun san Bikin ya Ishaq din..?
Badariya ta tabe baki tace"Ke share su basa min mgana ko achart kuma suna da Layina..Naji dai mama na Fadin Hajiyar dalar bata nan ta Raka megidanta India Cheekup,Kinsan ta bata Damu da zumunci ba.
Hafsah tace"Haka naji Goggo na Korafi kinsan zuwanta na karshe kaca kaca suka Rabu da Goggon.."
Badariya ta tabe baki tace"Shiyasa sau Daya na taba zuwa gidanta.
Hafsah tace"Ni ai ban ma taba zuwa ba.Yaya Asiya da ta zauna awajenta in tanaa baki Labari sai kin sha mamakinta."
Badariya tace"Shiyasa tasu tazo daya da Mama fa."
Dariya kawai Hafsah tayi suna ma Hirar Fa'iza ta koma Dakinta tana gyarawa,Hankalinta na kan aikinta duk yadda Tunani ke mukurkusanna naki bashi muhalli,na gyara Dakin Tas sai dai abu daya ne Fa"iza bata iya gyarashi ba shirgi bata iya yadda Zata kakkanta ko'ina yayi kyau ba,Sai dai ta gyara ko'ina ta kuma ta maida shirgin waje D'aya.
Mata kala kala ne, kuma kowacce da yanayin yadda ta iya gyaran waje,Ita fa'iza haka Allah ya yi ta tana da Tsafta jiki da na zuciya sai dai bata san yadda zata gyara komai a bisa muhallinsa ba.
Tunani nake yi anjuma zan yi wanki kayan yaran hade da Uniform dinsu Tunda Anum ta lalata injimin wankin su na koma yi da kaina domin duk abunda yara suka Lalata Laifin a kai na Ishaq ke dorashi.
Kayan Ahmad masu Datti nake fitowa Dashi Sanda Hafsah ta shigo ta kawo min Ahmad,alokacin nasan ya Ishaq ya shigo gidan ganin na riga ta kai mai abun karinsa yasa na zauna ina Bashi Nono,ko kafin ya gama sha yayi barci naa koma na shimfidar dashi,na kwashe kayan Ahmad da na Anum data cire dasafe zuwa Dakin yaran na wuce Badariya da Hafsah a Falo suna Hira Dayake Tv Din dake falon yara sun Lalata kuma Ishaq bai Damu daya gyara ba.
Sai da na gama Hada kayan waje daya na kullesu cikin wani Dankwali Sannan na fito ta nufi Shashen Ishaq.
Afalo na sameshi zaune kan kujera mai zaman mutum Daya ya lafe ni ban ma san waya yake yi ba Saboda ba Karfin ji gareni baa.
Kayan daya gama kari dasu na kwashe  na kai Kitchen kuma ban baro kitchen din ba sai da na wankesu,koda ma fito ta iske Badariya zata tafi mukayi sallama Hafsah ta fita domin ta taka mata...Shashen megidam na koma naji ko akwai abunda yake so saboda karamin abu laifi ne a wajensa..Ina  Shiga Har Lokacin bai gama wayarsa Daga yanayin yadda yake mgana zaka san yana bama wayar Muhimmanci kayan Haushi Fa'iza bata ma jin me yake Fadi shi da Zeey tana mai shagwaban jiya Daga Tahowarsa har tayi kewarsa.
Ganin yadda Fa'iza tamai zaune agabansa ne yasa yace ma Zeey ta bashi Minti biyar sannan ya datse kiran..
Fa"iza ya kura ma ido yana kallonta hankalinta na ma kan Tv dake aiki afalon cikin Tashar Mbc3 cartoon suke yi Ahmad ya kunna ma D'azu da Safe kafin fitarsu.
Mirmishi takaici yayi kafin ya Kirani a Kaushashe kamar yadda ya Saba.

"FA'IZA..!"

Firgigit nayi na Dago ina kallonsa Lokaci daya ina amsawa da Na"am
Kallonta ya karayi yana Nazarina domin Idanuwanta sun kumbura sai kuma ya waske cikin yanayinsa yace"Kin tasani agaba ina waya wani abu ne..?
Dayake a sama yayi mganar na jisa sai nace da Sauri"Kayi hakuuri..Daman nazo naji ko kana Bukatar wani abu ne..?
Karamin Tsaki yaja kafin yace"In ma ina bukata ai zam miki mgana ko..?
Tashi kije abunki ban cika son kina yawan zama a inda nake ba Fa"iza Allah Nagani."
Tsam na mike zan fice dagaa Shashen nasa, lokaci daya kuma ina daga rigata Daga kasa saboda tsawon yamin yawa kallo ya Bini dashi To ai Daman yasan Tunda wuyan yayi mata Daidai Daga kasan Rigar sai ta bata mtsala.
Har zan fice ya Kira sunana da karfi na juyo ina amsawa da hannu yayi min alaman na Dawo da Hanzari na na Dawo na Duka agabansa sai da ya sha Iskarsa sannan ya Tashi ya shiga cikin Dakinsa minti kad'an ya fito Hannunsa Dauke da wani Hoto ya zauna Lokaci Daya yana mika min Hoton na sa ka Hannu biyu na karb'a Fuskata da mamaki da neman karin bayani.
Ya Dora kafa d'aya kan D'aya kafin ya kalleni yana Fadin"Duba ta da kyau ki gani Fa'iza.."
Sannan ki Fadamin ya kika ganta..?

Fa'iza tabi Hoton Dake hannunta da kallo Wata kyakyawan Hallita nagani kamar ita tayi kanta wajen kyau Doguwa mai Dogon Fuska da Hanci har Baka Farace tss mai ja ja ja,Sannan tana da lobawar Kumatu,Wato Dimple Gashinta Har gadon bayanta yake,ga Diri na Cikar ya mace duk da Abaya ne ajkinta Shape dinta ya bayyana sannan tana da Wushirya hakoranta data Bude sun bayyana Farare masu Tsari ga Kunshinta ja ne ya fito akan Fararan Hannayenta masu kyau da sheki Fa'iza tana ganin Ya Ishaq mai kyau ne sai dai dataga wannan sai taga ai shi bamai kyau bane.
Ganin yadda ta bada Zuciyarta wajen kallon Hoton yasa ya Karbe Hoton batare data shirya ba na Dago ina kallonsa ya Daga Hoton yana Fadin"Ya kika ganta..?
Fa'iza cikin yanayin mganarta tace"Tana da kyau..!"
Ishaq yace"Eh ban ji me kikace ba..?
Fa'iza tace"Tana..tana da kyau sosai.."
Ishaq yayi wani irin Dariya kafin yace"Bayan kyau fa..?
Baki Fahimci ta mallaki komai na Kyau da Zatin ya' mace ba..?
Fa'iza tayi shuru batayi mgana ba Ishaq ya kalli Hoton na wani Lokaci kafin yace"Kinsan wacece wannan..?
Fa'iza ta girgiza kai kafin Ishaq ya Cigaba da Fadin"Matar da zan aura ce..Zabi na ce Fa'iza Zainab lawal Bako kenan..Mace ce mai kyau Kamar yadda kika ganni  Mai tarin ilimin Zamani Tana da Degree Biyu sannan tana Shirin komawa Phd dinta,Iyayanta masu Kudi ne da Nasaba ta mallaki Duka Burina na nan duniya nan da Sati uku zata zama matata zata cika min gurbin mafarkina da kika Tarwartsa Fa'iza.
Shiyasa na yanke shawaran zaki Dakatar da Haihuwa hakanan ki bar mai wuri tazo ta fara Haifamin kyawawan ya'yan da nike Mafarki.Yanzu ne zan san ni Ishaq nayi aure,abaya ina jin kunyar nuna ki a matsayin Matata ammh ayanzu banda Haufin Duniya taga Zeey a matsayin Matata ina Rokon ki Fa'iza nayi miki komai a Rayuwar ki yi Free d'ina ki barni naji D'adin Rayuwata ni da Matar data dace dani."
Ya karishe fada ya na kallon Fa'iza da kanta ke kasa ta kasa gane ina mganganunsa ya Dosa Cikin wani yanayi na Dago ina Fadin"Bangane ba..?
Kai Tsaye yace"Zamu jingine AURAN mu ne Fa'iza..Wlh in nace ashekara Takwas din da mukayi da aure ban cutu da auranki ba nayi karya kiyi ma kanki adalci kiyi min adalci nima"
Gaskiya ya Fada Tabbas gaskiya ya Fada Fa'iza ta fada acikin aranta.
Cikin wani karfin gwiwa na kallesa kafin nace"Jingina kamar ya..?
Kai Tsaye yace"Jingina ina nufin ba Saduwar aure tsskanimu a matsayin miji da mata  ba wata mu'alama ta aure ba Raba kwana Tsakaninki da Zeey..Sai dai zan cigaba da kula Dake saboda Darajan ya'yan dake tsakanin mu Kada ki manta ba Mu'alaman miji da mata Tsakanina Dake..Kawai zan kula Dake ne Saboda ya'yana kawai"
Har ya gama mganansa kallonsa nake yi Hawaye sun gama wanke min Fuskata ga mamakinsa sai kawai yaga nayi Mirmishi,mirmishin da zai iya rantsuwa bai taba ganin Fa'iza tayi irin sa ba.
Cikin wata irin muryan da baisan ina  da ita ba yaji nace

"Na Amince.."

Farinciki ya kamasa ya kalleni yana Fadin"Nagode Fa'iza ko bakomai kin yi sakayyah ga Alherin Baba agareki."
Ko kara Sauraransa ban yi ba na mike Zan fice ya Kira sunana na  waigo Cikin Kaushinsa yace"I ya ni da ke..Ban yarda wani yaji wannan mganar ba kina jina..?
Kai na gyadamai ina sharan Hawaye, muryata na rawa nace"Insha Allahu ba wanda zai ji sai indan kai kaso hakan"
Daga haka na fice da Sauri Saura kadan Rigar jikina ta Hardeni na Fadi bai Damu ba Murna yake zai samu Salama Shekara Takwas yana cikin kurkuku sai yanzu yaji sa kamar yana Shakan iskar yanci.
Har na karisa Dakina kuka nakeyi  bana ko ganin gabana sosai,kan gadona na Fad'a gefen Ahmad ina wani gunjin kuka Dake fitowa Daga kasan Raina  Hasbunallahu  wani'imal wakeel shin ni na Tsara ma kaina  Rayuwata a haka..?
Allah ne yayi ni baka mummuna Allah ne ya so ya ganni afasalin daya ijiyeni meyasa ya Ishaq bazai gane haka ba..?
Yau ni Ya Ishaq ke mganar zai jingine auranmu Saboda wata.? Na tabbata ba Domin mganar Baba ba da tuni aurane da Ishaq ya kare to ai yanzu ma ba Maraba..?
Zai jingine ne kawai saboda mganar Baba ba Domin Ra'ayinsa ba,sai kuma domin kuma ya'yansa Ba laifi na  bane domin na fito a mummuna ba, kuma ba Laifina bane domin na fito daga jikin Bebiya ba, ba Laifina  bane domin na kasance an Haifeni  da Laluran rashin ji sosai da yanayin mgana taba, ba Laifi na bane Allah ne ya Tsara min Rayuwata Daki Daki.
Sannan ba Laifi na  bane domin ban zama mai ilimin zamani ba Domin duk yadda ka kai ga Tsara rayuwarka To KANA NAKA ne Allah na nashi kuma na Allah shine daidai kuma Tsari mai kyau.
Ina cikin wannan halin bansan sanda na fara jin tunanin yadda yanayin rayuwata ya fara dawomin acikin kaina ba,tundaga farko har zuwa yau din da Ishaq yace zai jingine aure na saboda wata.
Nafara da Tunano yadda yanayin Rayuwata ta fara ne cikin Farinciki Tun mahaifinmu ALHAJI SIDI KAROFI na raye.

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA. SANNAN BASU DA BAURI MASU KIDIMARWA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*TUNTU'BI WANNAN LAMBAR DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.



*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*

*Madallah da ku masoyana naji Dad'i na kuma yaba muku da yadda kuka karb'i Labarin nan fiye da Zato na..Nagode kwarai Allah ya had'amu cikin Ladan gabadaya,Madallah da masoyan gaskiya da Amana,nace Madallah da y'an Amanar Janafty*

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

         *🅿️03*

Asalin kakanmu wanda ya haifi iyayan mu maza ni da Yaya ishaq bakatsine ne wanda ya fito daga Tsatson katsinawan Karofi.
Karofi kamar Anguwa ce ko wata alkarya dake cikin Garin karamar hukumar Dutsenmah ta Jahar katsina.
Tunda ga Dutsenmah,Katsina Kankara,malumfashi bakori,mahuta da Sauran kananan hukumomin dake zagaye da Garin katsina ba wanda bai san Waye Alhaji Sulaiman Karofi ba,Saboda tun lokacin yana Raye shekaru sama Hamsin da wani abu da suka gabata an yi Attijirin mai kudi,Domin kaf yankin nan ba inda ake siyan Siminti sai a wajensa manyan manyan Store yake kama haya ana cikamai su da Siminti tun yana matashinsa da wannan sana'ar ya fara kuma alhamdulillah ita ta Daukakesa har kuma Allah ya Dauki Rayuwarsa bai sauya sana'a ba.
A yadda Babanmu ya bamu labari Lokacin yana raye Saboda muma ko da mukazo Lokacin Allah ya karbi Ran Alhaji Sulaiman sai dai mun sha Labarin kirkinsa da Dattakonsa bakin Babanmu.
Ya sanar damu cewa Alhaji Sulaiman Kamfani kamfani na Siminti Mota mota ke shigowa Karofi Domin saukemai Siminti kuma ba'a sati duk sai ya kare bayan manyan yan kasuwa yana saida ma marasa karfi da masu siyan daidai misali sannan karin Daukakarsa baya tsawwalla kudi i ya abunda Allah yasa ya samu sai ya sanya musu albarka.
Mutum ne akace nagari kamili mai sanin Darajan dan adam da Dattako,da kowa yake yabonsa Daga uwa har uba duka haifaffun karofi ne,Kenan ba shi da wani garin da ya wuce mai Karofi alokacin.
Yana da matar auransa Daya Hajiya Suwaiba(Hajiyar karofi) ita ta Haifamai manyan ya'yansa guda Uku Hajiya Fatima ce Babba(Hajiyar Dala) sai Hajiya Aisha(Goggon karofi)
Sai karamin su Alhaji Kabiru(Baban katsina)
Sai Autan su Alhaji Sidi( Babanmu)
Wanda rabonsa ne yasa aure ya kullu Tsakanin Mahaifiyarsa Asiya da Alhaji Sulaiman Karofi.
Alokacin baya in aka auro mace daga wani waje ta shigo inda bata san kowa ba,to akan samu a makotan da aka kawo ki kina samu yar D'aki da zata rika shigowa tana tayaki zama da yan aikece aikece to haka ne ya faru da Hajiya Suwaiba ita din yar cikin garin Dutsemah ce kuma auran Soyayya ne ya kulla Tsakanin su mai karfi kafin ta kai su ga aure.
Yadda na samu Labari Hajiya tun tana matashiyarta macece mai kirki da Sanin ya kamata sai dai akan mijinta bata da kauda kai tana son shi Shiyasa take bala'in kishinsa.
Tun sanda aka kawota garin gidan da Alhaji Sulaiman ya gina gefen katangar gidan su Asiya ne, wanda garun gidan Alhaji Sulaiman shi ne garin gidan su Asiya talaakawa ne Futuk,mahaifinta mallan Haruna ya rasu bayan doguwar jinyar da yayi a baya masarin bishiya ne an ce Tun wani Sare wata bishiya da yayi shikenan bai kara lafiya ba har ya rasu Daga Asiya sai mahaifiyarta Atika suke Fafutukar Rayuwa to lokacin da aka kawo Hajiya Suwaiba Asiya ta kan shiga ta taimaka mata da yan aike ce aike ce tunda daman Asiya bata da kiywuya Lokaci kadan suka saba da Hajiya tun balle data fahimci suna cikin Halin matsi ita ke taimaka musu da abinci suturu har kuma ta saka Alhaji Sulaiman shima ya tallafa musu.
Cikin lokaci kadan Asiya ta zama yar Dakin Hajiya Suwaiba duk wanda yasanta yasanta da Asiya,Suna tare ta yi goyon cikin Fatima ta haifeta kowa yaga Asiya sai yaba da kokarinta da Himmanta Hajiya kuwa har ga Allah ta ke tare da Asiya bata taba jin wani abu aranta game da ita ba..
Ana haka har ta sake haihuwan Aisha,lokacin ne Alhaji Sulaiman yazo mata da mganar da ta kusa girgizata wai zai auri Asiya saboda yayi jihadi sannan ta zama abokiyar zamanta na Har Abada.
Ance a lokacin Hajiya Suwaiba tayi tashin Hankali har sai da ta koma gida Ma'ana tayi yaji kuma hakan baisan an fasa ba sai dai ta Dawo ta iske ya gyara ma Asiya dakin dake kusa da nata har an yi biki Asiya ta tare,Ance sillar wannan gabar daga wannan auran ne Hajiya ta kullaci Asiya da Mahaifiyarta Atika akan sun yi auran cin Amana ita kuwa Asiya bata mgana sai kuka ba Laifinta ba ne,Ita batace tana son Alhaji ba shi yace yana sonta batare da sun sani ba ya je ya gabatar da kansa wajen Dangin babanta su kuma sun ga Alhaji ga kudi ga Dattako nan da nan suka basa da Atika tayi mgana suka Rufeta da fada dole tayi shuru.
Sanadin wannan auran ne komai ya fara ko nace shine sillar komai bazan ce Hajiyar karofi ta fara assasan wutar kiyayyar ba Tunda kafin ta Mutu ta yi Tuba tuba irin na Taubatul nasuha.
Zan iya cewa Tsantsan Rabo ne kawai ya kawo mahaifin mu wannan Duniyan,Asalin sunansa ba Sidi ba ne Sidik ne Asiya ce ke kiransa da Sidi har ya bisa zuwa girmansa.
Kusan Lokaci daya Asiya da Hajiya suka yi goyan yaransu ita tana goyan Babanmu ita kuma Hajiya na goyan Baban katsina.
Hajiya ita ta ke zaunar da ya'yanta tana fada musu auran cin Amana mahaifinsu yayi da Asiya har aka samu Sidi saboda haka shi ba Dan'uwan su ba ne bare ne tunda auran cin Amana ne to ba d'an Sunna ba ne shege ne, mgana fa har ta fita Domin ba inda Hajiya bata yada mgana gidan biki ko suna har yakai ga Asiya ko Atika suka daina fita Saboda kananun mganganu.
Har sai da Alhaji Sulaiman yaji ya tsawarta mata ya kuma ja kunnenta da sai ya iya Rabuwa da ita Saboda haka ance ta sha kuka Ranar Asiya tasha zagi da gorin ita ta zama gatan taa ammh Daga karshe ta saka mata da Auran mijinta.
Adalilin irin wada'nan kalaman na bakin Hajiya suka yi tasiri a zuciyar Babbar yarta Hajiya Fatima(Hajiyar Dala) wanda har mahaifin mu ya koma ga Allah bata kaunace sa ba Duk da kuwa an ce Kafin Asiya ta bar gidan Duniya sai da ta rika rokon Hajiya gafara ammh taki yafe mata sai daga bayan ta jima ita da Atika a kushewarsu sannan Hajiyar Karofi ta gane kuskuranta ta gyara alokacin kuma komai ya kure mata.
Babbar Bakincikim Hajiya ganin da tayi Sidi da Kabiru sun taso kan su daya sannan komai Alhaji Sulaiman zai yi musu tare ne,ita kuma bata so har ko yaushe a shege take kallon Sidi Tunda auran cin Amana ne..azaba da ukuba ba wanda Sidi bai shata a hannun Hajiya ba ko kasheshi Hajiya zatayi Asiya ko Tarin ta bamai ji a Tsakar gida tana da hakuri da  kawaici sannan ga Ladabi da Biyayya ko da ta auri Alhaji bata daina yi ma Hajiya bauta ba sai dai bata gani Laifinta daya meyasa ta auran mata miji..?
Babanmu ya fada mana yana d'an Shekara goma sha uku a duniya Mahaifiyarsa Asiya ta rasu da tsohom ciki ta fito daga makewayi jirin Hawan jini ya fardar da ita kwananta Daya asibiti tace ga garin ku nan da Farko Mutuwar ta daki Hajiya ammh Daga baya sai ta saketa.
An yi tashe tashen hankula Har sai da iyaye suka shiga ciki kan zaman babbanmu a wajen Hajiya kememe ko tace bazata rika dan shege d'an cin Amana ba sai Atika aka kai mashi ta rikesa Gefe D'aya Alhaji Sulaiman na kula dashi sai dai duk yadda Hajiya taso ta raba Kabiru da Sidi ta kasa wannan jinin na yawo ajikinsu..sannan Fatima ce kadai ta ke bayanta Aisha kuma babu ruwanta bata Cika Daukan mganarta ba..
Babanmu ya d'anda'na gudarsa a Hannun Hajiya tun da duka bai Rufe shekara biyu a hannun Atika ba,ta rasu sakamakon amai da guduwa shi kuma Alhaji Sulaiman yace hajiya bata isa ba Sidi zai zauna agidan nan tunda shima gidan ubansa ne kamar sauran ya'yanta wannan dalilin ya kawo babban baraka tsakanin ma'auratan,In yana gidan Sidi zai zauna cikin salama ammh da zarar ya fita sai abunda Allah yayi ukuba ba irin wacce bai gani ba,Hajiya ta taba Cire masa riga ta zane shi da wayar radio mai karfi kawai saboda sun fita shi da Kabir suka dawo jikinsu duk kasa shine ta rufesa da dukan meyasa yake jan Kabiru ai ba Daya suke ba shi da'n Shege ne Kabiru kuma yaron sunna ne da sahihin aure ya samar dashi Ance sanadin dukan har sai da Sidi ya suma saboda azaba wannan dalilin yasa Alhaji Sulaiman ya saki Hajiya saki daya sakin daya girgizata ta Dade bata gidan ta kuma kwashe ya'yanta duka ta tafi dasu shi kuma sai ya kyaleta iyayenta sun shiga ciki ammh ba'a samu daidaito ba Saboda Hajiya ta riga ta kara hawa dokin naki kan bazata rike Sidi ba shi kuma Alhaji Sulaima yace ba inda zai kai shi in bazata rikesa ba to ta barshi kusan shekara daya Alhaji sulaiman shi ya Dinga wahala da Sadi komai shi ke yi mai Hajiya kuma ta Dauka Alhaji Sulaiman zai sauko yazo ya bata Hakuri sai taga ba haka ba ne ga su kabiru suna ta Damunta da Babansu shi kuma tunda haka ta faru bai taba Takawa wajenta ba ai yace ba shi yace tatafi da ya'ya ba ita taga dama Saboda haka ba zai bisu ba in har ya'yansa ne zasu nemesa.
Ganin Ba riba ne yasa da Umarnin Iyayanta Hajiya ta dawo gidan Alhaji Sulaiman ammh an yi musi tsakani da Sidi ba ruwanta da shi,Shi dai yana bata girmanta domin kamar uwa ya Dauketa ita kuwa ta tsani ma ta Bude ido ta gansa don dai bata da yarda zatayi.
Cikin wannan Halin Rayuwa ta rika ganganrawa Alhaji sulaiman bai tara dukiya ya rika siyan kaddarori ba sai dai ya gina ya'yansa ya basu kyakyawan ilimin zamani,Matan daga Sakandiri yake aurar da su,Ammh dukkansu sai da ya kai su Hajji suka sauke Farali Hajiya fatima Soja ta aura dan kano ne chan aka kaita,ammh daga baya an sauya mai wajen aiki ya koma Kudu,Kafin zuwa yanzu sun zauna garuruwa da dama kafin ya yi ta samun karin girma har ya kawo matsayin da ya kai a yanzu.
Sai Hajiya Aisha da ita kuma d'an karofi ta aura kuma kamar aboki yake wajen Alhaji Sulaiman sai dai tun alokacin ba'annin juna ba ne..
Alhaji sulaiman bai bar gidan duniya ba sai da ya gina ya'yansa sannan ya aurar da su bayan mata ma har da mazan har kuma ya bar duniya bai ga Nadamar Hajiya suwaiba(karofi),kan Asiya da zuru'ar ta ba,har alokacin bata ganin duk wani daya shafi zuru'ar Asiya da Atika da Daraja saboda abunda ya faru.
Daga kabiru har Sidi sai da suka fara samun Takardan Education kafin su Dora degree din su,Baba kabiru fanni Biology ya karanta,shi kuma Babanmu sai ya karanta Fanni Kasuwanci Business admistration.
Bayan kamallah karatun su dukkansu sun samu aiki Kabiru ya fara koyarwa a wata makaranta gwamnati dake Karofi shi kuma Sidi sai ya samu aiki a wani ma'aikatan littafai dake katsina chan ya tattara ma ya koma Saboda gidan baya mai dadin zama Hajiya ko zai gaisheta sau dubu bazata amsa ba sai tayi kamar bata gansa ba,Sai dai yana bata girmanta a matsayinta na uwa bai taba riketa aransa ba kuma kullun haka Alhaji Sulaiman ke gaya masa Hajiya uwa ce garesa komai zatayi mai kada ya Daukesa a wani abu ya Dauka ajizanci ne na D'an adam.
Shiyasa bai taba kallonta da wani abu ba,Balle da suka taso kamar uwa daya uba daya shi da Kabiru in ba mutun bai sani ba zai dauka uwar su daya ubansu daya sai an fada maka ne zaka san ba Uwa dayace ta haifesu ba ammh suna Diban kama Dukkan su Dogayen katsinawa ne marasa Lalaci Sannan shi kabiru yafi Sidi haske Saboda Hajiya farace,Sakamakon ita Asiya baka ce shiyasa sai hasken sa ya zama mai Duhuwa..
Yana shigowa karofi duk bayan Sati hudu kuma duk alherin da zai yi ma Dangin Mahaifiyarsa,zai yi ma Hajiya sai dai bata karba yana sauke ledan zata Dauka ta kone daga baya sai ta Daina konawa Tunda Alhaji Sulaiman ya ja mata kunnen tana albuzuranci da Dukiya da kaya watarana zanin Daurawa sai ya gagareta sai ta tsorata ta Daina Konawa sai dai ta Sadakar da su.
Kabiru ya riga Sidi aure saboda shi Daga baya shima katsinan ya koma da koyarwa a wata babbar sakandiri,Achan ya hadu da Saudatu ita din buzuwar yamai ce Kasuwanci ke shigo da su Katsina ta Jibiya anan suka Hadu Allah ya hada kauna Tsakaninsu har ta kai su ga aure Saudatu(Mama kofar soro) farace Doguwa kyakyawa kin kowa kin wanda ya rasa ga gashinta har gadon Baya Hajiya tayi alfahari da wannan auran ganin kamar Kabiru ya kece sa'a cikin maza zai auri buzuwa,Barin ma Hajiya Aisha da itace kamar makwafin Hajiyar tafi kowa Fi'ili da karairata Ita Hajiya Fatima babu ruwanta ita datake ma kusa.
Har chan yamai akaje aka nema ma Kabiru auran Saudatu,suka kuma Tare a gidan su dake karofi inda Alhaji Sulaiman ya gina musu barayi guda biyu,Na kabiru da Sidi shima sai da Hajiya ta rika yada mganar ai shi ba Dan gida ba ne bashi da gadon Alhaji shi dai bai kulata ba sai dai yayi mata addu'an shiriya tunda ganin Shekaru sun fara ja Hajiya bata Sauya ba,bai tunanin zata iya sauyawa sai dai shiriyan Allah kawai.
Tun zaman Saudatu karofi taga gata wajen Hajiya kamar ta lasheta barin ma har zuwa ake yi ganinta Saboda kyanta da gashinta,sai taji dadin haka Domin daman tana bakincikin Sidi na aikin kamfani Kabiru kuma ya zama malamin makaranta in tayi mai korafin haka dariya yakan yi kafin yace"Hajiya kenan ko wani bawa da kika gani yana tafe da kaddaransa arzikinsa da aurensa da Haihuwarsa da Mutuwarsa'"
In yace mata haka sai dai ta kallesa ta Harareshi kafin tayi kyafci Sai tace"Ai daman haka zakace Yaron nan Sidi ya gama dakai kai da Aisha Fati ce kadai tasan ciwo na"
Sun riga sun Saba da Halinta shiyasa suke Lallabata su rabu lafiya,yana katsina sai sati sati yake zuwa ganin gida Tun auran su daman Hajiya ta gama karanta ma Saudatu kaf Waye Sidi da auran cin amanan da Asiya tayi da  mijinta,Sannan ta fadamata Sidi ba dan sunna ba ne An haifesa da cin Amana ne,shi yasa ta tsane shi duk da ta Lura Kabiru na bala'in ji da kaunar Sidi shiyasa ranar da ya fara kawo mata shi kadahan kadahan ta karbesu sai faman tab'e baki take yi Sidi na lura da ita bai yi mamaki ba Daman yasan za'a rina shiyasa baya fatan in yayi aure ya kawo matarsa wannan gidan yasan ta zama Nama.
Sai da Kabiru da Saudatu suka Haifi Diyar su ta farko Fatima suna kiran ta Binta sunan Hajiyar Dala taci.
Ashekaran Sidi yayi aure auran da Hajiya taji dadinsa tunda ba auran kece sa'a ba ne,Sidi yar'uwansa ya aura da kakansa na wurin uwa da kuma kakan TAMADINA na wajen Uwa itama sun hada iyaye daya,su biyu kadai mahaifinsu ya haifa kafin ya rasu Tamadina da Usman kuma ba uwarsu daya ba kowanne da Tsatson sa Ita ta Madina mahaifiyarta haifaffiyar karofi ce ita kuma mahaifiyar Usman yar karaye ne dake kano Lokacin data gama Takaba ta roki alfarman Tafiya da Usman garinsu aka bata Tun yana da Shekaru goma aduniya ya bar Karofi.
Hafsatu(Tamadina) shine ainihin sunanta,kuma ta samo sunan ne tun tana karama tun da bakinta ya bude duk wanda yayi mata mgana sai tace madina zata tafi shikenan Hafsatu ya bace sai dai tamadina,sannan Tamadina Bebiya ce kuma ba Ciwo bane da shi aka Haifeta mganar ta baya fita Sosai sannan bata ji sosai,ahaka taso cikin rashin gata tunda kaf zuru'ar su Asiya ba wani mai arziki sai Buga buga kawai.
Tamadina baka ce kuma gajera shiyasa duk wanda yasan Tamadina ya ganni ni Fa'iza zai san kammaninta da suffanta duka na Dauko sakamakon su ya Asiya sun Dauko Tsawon babbanmu da Hasken Fatarsa ni kuma hatta bakin Tamadina ni na Dauko shi har da gadon Rashin ji, na duk daga wajenta na gaje shi.
Ba auran Tausayi Sidi yayi da tamadina ba shi ya ganta yaji yana sonta kuma manya suka shiga ciki,Musamman Alhaji Sulaiman da ya shige ma Sidi gaba,har akayi auran da farko yaso ya tafi da ita Katsina ne sai Alhaji Sulaiman ya hana yace ya barta agida kamar yadda Dan'uwansa yayi shi kuma bazai iya yi mai gaddama ba sai ya bar Tamadina a gidan karkashin Hajiyar Karofi da Saudatu(Mama kofar soro)
Ba iya ni na wahala da Mama ba Mahaifiyata ma taci wuyarta ita da Hajiya suka maidata kamar jaka gashi Tana da lalura sai su yi ta zaginta bataji,Gashi ba daman tayi mgana sai Hajiya ta hantareta tana fadin"Ta fi chan Dangin maciya Amana..Dangin bakake munana kawai masu bakincikin munafunci"
Kalaman tun tamadina bata gane su har ta fara ganesu ta kuma Haddace su,In Sidi na nan ne take samun salama sannan tana jin dadin zama da Uban mijinta Alhaji Sulaiman.
Da kuma Hajiya Aisha(Goggon karofi),Sai Kabiru wanda shima ba ruwan shi ammh Hajiyar Dala sai abunda ta manta cin mutumci in tazo gidan nan Tamadina sai tayi kuka Taruwa suke yi su yi ta cin mata Mutumci wani Lokacin batama jinsu har Jin dadi take yi da Allah yasa bebiyace ita da ta kunshi bakinciki.
Bayan Haihuwar Saudatu in da ta Haifi ISHAQ Bayan Haihuwar Saudatu,Tamadina ta haifi yarta mace Aka saka mata suna Asiya sunan mahaifiyar Sidi taci,Shekara shida tsakaninsu an yi sunanta ba jimawa Alhaji Sulaiman ya kwanta jinya ciwon sugar da bai tashi ba Gabadaya duk abunda ya tara sai da ya kare wajen neman mgani daga karshe bai tashi ba ya koma ga Allah.
Rasuwar sa itace silar Wargajewar komai an yi ta rigima wajen raban gado,Domin Hajiya ta yi tsaye tace Sidi bai da gadon Alhaji Saboda shi din d'an cin Amana ne ganin rigiman tayi girma sidi ya tattara matarsa suka koma katsina ya kama Hayar Daki biyu da Tsarkar gida sai kitchen,Ya kuma ce ya yafe gadon har Abada aka rasa rai ma aka Hakura ballatana Duniya tun faruwar lamarin yasan Hajiya bazata taba kaunarsa ba kawai sai ya Hakura wanda ya hada ya raba,Tundaga Lokacin sai ya Dade bai je karofi ba Sai dai suna mgana ta waya da Kabiru da Aisha tunda su kam basu yar da Zumunci ba..
Ko shekara basu shafe a katsina ba ya samu aiki a wani kamfanin Sarrafa leda dake malunfashi sun basa matsayi mai girma da gidan zama ya tattara tamadina suka koma malumfashi da zama
Acikin shekarun da suka gabata abubuwa dadama sun faru ciki har da Sauyin rayuwar da kowa ya samu Sannan da Nadamar Hajiya,Rana daya ta rika kuka tana a kira mata Sidi ta nemi afuwarsa dayake ita kadai ce agidan yanzu Kabiru shima ya Tattara sun koma cikin katsina da zama Tunda ya zama principal bayan yaje ya karo karatunsa
Sidi yayi matukar mamakin nadamar Hajiya daman bai taba riketa ba ya riketa yana share mata hawaye tare da Fadin bai taba riketa acikin Ransa ba kowa yaji dadin wannan al'amarin ban da Hajiyar Dala domin har Abada bazata kaunaci Sidi da zuru'arsa ba.
Hakama Saudatu(Mama kofar soro) itama ta tsani Sidi da zuru"arsa ganin tafi  TaMadina komai na bangaran kyau da Nasaba ammh a bangaran jin dadin gidan miji,Sai dai su goga domin bata fita komai na inganta Rayuwa ba, Sidi na yima Iyalansa komai sun gado Halin Dattako wajen mahaifin su Alhaji Sulaiman

*****

Shekaru goma da suka gabata.

A cikin wad'anan shekarun goman,komai ya faru kuma ya kare,mun fara samun ingantattaciyar Rayuwa a malunfashi,Bayan haihuwar Ya Asiya sai Yaya mariya sai ni Fa'iza da aka Haifeni da Laluran Raunin ji sai autarmu dataci sunan Tamadina Hafsatu ita an haifeta ma ne Babanmu na cikin Tsananin jinya shima Ciwon sugar yayi gado wajen mahaifin su Alhaji Sulaiman shima kamar shi din sai da komai ya kare tas wajen neman mgani kafin rasuwarsa sai da aka yanke mai kafa Da Hannu bazan taba mantawa ba ina Aji hudu na matakin primary a asibitin gwammatin garin Malunfashi Babanmu ya rasu a hannun Alhaji Kabiru(Baban katsina) da Tamadina Mutuwar da Sanadinta ta gama gigita Rayuwarmu gabadaya sanadinta muka san halin Rayuwa muka san maraici da rashin gata.
Da gidan da muke ciki kadai muka Tsira shima da aka saida shi duk a bashi ya tafi tunda jinya yayi kusan shekara uku sai da komai ya kare aka koma cin bashi duk da Baban katsina na Tallafa mana shi da Hajiyar Karofi.
Mutuwar Babanmu shine Silar Barowarmu Malumfashi muka koma Karofi daga Lokacin kuma komai na Cigabaman mu ya tsaya,Tamadina tana gama Takaba gidan su ta koma,mu kuma ta barmu gaban Hajiya da Farko da nan aka barmu da mun samu Rayuwa mai inganci saboda Hajiya tana kaunarmu kwatankwacin kaunar da take yi ma Sauran jokokinta.
Ammh sai hakan bai samu ba Baban katsina ya tara su Hajiyar Dala yace zasu rabamu a Tsakaninsu Saboda Rage ma Hajiya Dawainiya,Shi farko Yaya Asiya yace zai dauka Ita kuma Goggon Karofi  tace zata Dauki Yaya mariya ta hadata cikin ya'yanta ta rike Tsakani ga Allah.
Shi kuma Baban Katsina sai yace Hajiyar Dala ta Dauke ni Tunda Hajiya ta maida ma Tamadina Hafsatu tunda tana karama ne Lokacin sosai tace ta riketa tukunna har sai ta yi wayo sosai.
Ai Hajiyar Dala agaban kowa da kowa ta Daka tsalle tace bazata Daukeni ba takai gidanta ban ko ji sosai ta Daukan ma kanta Lalura ita bazata iya ba har Hajiyar karofi sai da tayi mata mgana tace bazata Dauki kowa ba,Sai aka kyaleta Baban katsina da ya fara fada Hajiya ta hanasa tace ita zata rikeni shi ya tafi da Ya Asiyan kawai ita zata rikeni Hajiyar Dala najin haka sai tace sai dai ta Dauki Yaya Asiya tunda ita Lafiyarta kalau Baban katsina yaso ya hana sai Hajiya tace abata,wannan shine Dalilin Rarrabuwarmu Yaya Asiya a kano ta tashi Ta samu tayi karatunta har Sakandiri ita kuma Yaya mariya ta taso Hannun Goggon karofi itama tayo karatunta ita kam har matakin N.C.E,Sai Hafsatu wanda Baban katsina yace in ta kara girma shi zai Dauketa Tunda ni Hajiyar karofi zata rikeni ammh duka Dawaniyata Na hannunsu.
Naji dadin barina a karofi da akayi Saboda Tamadina da Hafsatu sai kuma Yaya Mariya dake kusa Damu ko da yaushe suna gidan Hajiya tare damu Ni dai Dakyar Hajiyar Karofi ta bari na gama nakai aji Biyar na matakin primary domin na rubuta jarabawar fita ba  sai fada take yi Me zan ji a makaranta ko me zan gane Tunda ba ji nake yi sosai ba,Baban Katsina ya so nayi karatu ammh sai yaga bayan Hajiya Nima bana so Saboda ina shan Dariya da Wulakanci a makaranta wajen Sa'annina Saboda yanayin mganata da raunin ji na sannan kuma ni bakace bani da kyau shiyasa sai karatun ya ficemin Daga raina na,na saka araina sai mai gata ko mara Lalura yake zama mai ilimi bani da na ke nakasashiya ba.
Ammh Hajiyar karofi bata bari nayi Sakaci da na addina ba,Ta sakani Islamiya da Hadda da Makarantar allo ta Safe da Dare,Shi kam ban yi sakaci ba Kuma dayake karatun Qur'ani ne da Liffafan addini ina ganewa sannan Hajiya bata hanani ba shima na Bokon bazata iya juran dawowa da nike da kuka bane Saboda har waka ake yi min bebiya mamarta ma Bebiya sai nake jin guilt din abun acikin raina da yasa naji na Tsani bokon gabadaya sai Hajiyar Karofi ta maramin baya domin gatan Duniya ba wanda bata nuna min ba.
Rikon Hafsa ya koma Hannun Goggon Karofi Saboda Tamadina tayi aure a Dutsenmah ta auri wani magini ne matan sa Biyu itace ta uku,Sai Baban katsina yaso ya karbi Hafsah Mama kofar soro ta daka tsalle tace bazata rike zuru'ar Tamadina ba dangin Maciya Amana da Bebaye ba Hajiya tayi kuka kamar ranta zai fita tasan duk abunda ta Shuka ne take gani ta zaunar da Mama da Hajiyar Dala ta gaya musu komai ta kuma yi kokarin cire musu wannan Tunanin ammh batayi nasara ba Dole ta zuba musu ido ganin abun na neman ya lalace Sai Goggon Karofi ta raba Gardama ta Dauketa kawai ni da Farko ban san matsala ko matsin Rayuwa ba, sai da  sanadin ciwon Hajiya ya wujijjiga Rayuwata. sannan na kara Fahimtar bamu da gata sannan maraici ya gama Lullube rayuwarmu tun a baya na Fad'a muku ita kanta Tamadina ba su da wani gata balle mu yi Tunanin samun gatan ta barayinta gatanmu kenan Dangin Babanmu su kuma k'alilan din su ke son mu da Kaunarmu.
Bazan taba mantawa da wata rana na Dawo daga allon Safe ina shiga Dakin Hajiya na ganta kwance ba yadda take ni na Ruga na je na kira Goggon Karofi tazo ta gani,aka kwashi Hajiya sai asibiti ashe Faduwa tayi ta samu shanyewar barin jiki,ta koma sai dai a kwantar a tayas,ganin haka yasa Goggon Karofi suka yi shawara da Baban katsina ta maida Hajiya da ni gidanta tana kula Damu gabadayamu,Ko wata uku Hajiya batayi tana jnya ba,jikinta ya kara Rikicewa ga nauyi yayi ma Goggo yawa Mijinta ma'aikacin gwamnati ne ammh kuma akwai Dawainiya shi kuma Baban katsina Lokacin ya na matsayin Daractan Ilimi ne na Katsina gabadaya ya samu Rufin asiri sosai.
Shiyasa Saboda ya rage mata nauyi yace zai daukeni alokacin cikin Fargaba ta kallesa kafin tace"Abban Ishaq kana ganin ba matsala..?
Ajiyar rai ya sauke tabbas akwai matsala yasan Halin Saudatu ammh kuma ai gidansa ne kuma shi ke auranta Dole Fa'iza ta zauna karkashin kulawarsa shiyasa cikin karfin Hali yace"Kada ki damu ba wata matsala ta had'a kayanta da zarar na tashi da ita zan wuce"
Nayi kuka kamar zan mutu da naji Goggo tace na shirya nabi Baban Katsina gidansa Yaya mariya ne da Goggo suka rika Lallashina ni nasan gidan bamai kaunata,Daga maman har Anty Binta da Ya Ishaq wanda in dai suka yi Hutun Makaranta yakan Biyo Baban katsina ya gaida Hajiya wlh baya kallona bazan taba mantawa da Ranar da ya fara ganina agidan Hajiyar karofi ba kallon Sama da kasa yayi min kafin ya kauda kai ya yamutsa Fuska ya kalli Hajiya yana Fadin"Hajiya wacece wannan mummunar bakar yarinyar..?
Hajiya cikin yar Dariya tace"Baka gane ta ba ko..?
Fa'iza ce yar wajen Marigayi Babanka Sidi"
Ina kallo ya kara kallona ya yamutsa Fuska kamar yaga kashi kafin yace"Hajiya bata da kyau Sannan ban taba ganin baki irin bakinta ba kamar ta shafa shuni"
Yafad'a cikin Sigar Tozarci ita ko Hajiya Dariya tayi kafin tace"Kuma kai nayi ma kamu ba"
Agaba na ya Tofar da yawu kafin yace"Allah ya tsareni Hajiya ai ni Matata bata zo duniya ba tukunnah"
Alokacin Hajiya bata Dauka wani abu ba ammh ni da na taso cikin wannan yanayin nasan tozarci ne nayi kuka Sosai.
Ina kuka ina komai Baban katsina ya sakani a mota yana bani baki sai Katsina Hajiyar karofi kuma bata mgana Sosai jikinta yayi zafi,sai dai bin mutane da ido kawai sai hawaye bata mgana.
Tana kallona zan tafi na rike hannunta ta gyadamin kai ina kuka tana Hawaye itama a mota ma kukan na Dinga sharba sai da Baban katsina ya jawoni jikinsa yana Lallahina Fadi yake yi"Kwantar da Hankalinki Fa'iza zan kula dake kwantacin yadda sidi zai kula da dake in yana raye"
Lokacin ba jinsa nayi ba ammh nasan Lallashina yake yi.
Sai dare muka isa katsina anguwar Kofar soro Makeken gidan da Baban katsina ya gina Tun ranar da na saka kafata acikin gidan nan ban kara farinciki ba har fita ta zuwa gidan Ishaq babu abunda ya Sauya.
Nasan dai Baba na gaba ina Binsa a baya da jakar kayana ina kalle kalle har Babban Falon gidan in da mama ke zaune ita da Yaya Ishaq sai Anty Binta da tayi aure ammh acikin garin katsina Sai Jamal wanda ke bi ma Yaya ishaq sai Karamar su Badariya.
Dukkansu Baban suka zuba ma Ido da farko Mama ta fara mai lale bata ganni  ba sai da ya juya yana kallona kafin yace"Saudatu ga Fa'iza ta Dawo Hannuna da zama har na aurar da ita ki kaita Dakin yaran nan ta yi wanka ta Huta"
Ai ranar naga tashin Hankali agabanmu Mama ta dinga Bala'i tana fadin bazan zauna mata agida ba Dangin munana maciya amana Dangin kurame me zatayi dani ban da akara mata wahala Fada dai sosai tana Fad'a Baban katsina na Fad'a har yakai ga Baba ya kusa saka ma Mama Hannu sai da su Ya Ishaq suka Shiga Tsakani ita kuma tayi shewa tace da ya sa ke ya mareta wlh bazan zauna mata agida ba.
Ranar a falo na kwana rakub'e ina rawan sanyi da tsoro,Duk naji mganganun Mama Saboda da karfi take  mganarta Tunda Baba ya shige Ciki itama ta shige a Fusace ban kara ganin kowa ba Badariya ce tazo wajena Anty Binta tajata suka tafi gidanta saboda Kada ta rabe ni Jamal kuma daman ba wani babba ba ne alokacin tashi yayi ya shige Dakinsa ko ajikinsa Ya Ishaq ne ya taso yazo gabana yana min kallon Tsana da kaskanci kafin yace"Dama kece Kurman nan..?
Ko Bebiya ma zan ce..?
Ban ji sa ba shiyasa na kura masa ido kauda kai yayi ya wuce yana fadin"Abubuwan sun yi miki yawa..ga baki ga Muni ga maraici ga Ki kurma"
Daga haka shima ya Tsallake ashe wasa farin girki wani kukan Rahma ne Duk yadda Baban katsina yaso ya inganta Rayuwata ya kasa Domin Mama tafi karfinsa bashi da yarda zai yi da ita,Tunda nazo gidan ta sallami Duka yan aikinta a shekaruna sha Uku a duniya na bautu da aikin Wahala nau'i Dabam Dabam,in na tashi Tun asuba bana komawa sai wani Daran abinci kuma sai an rage nake samun naci Tun ban iya girki ba har na iya aiki kuwa ba wanda ban iya ba In Baba yayi mgana sai tace zata koreni.
Nayi wahala da Mama da ya'yanta sannan nayi wahala da Anty Binta da Ya'yanta Ya Ishaq ko ta gabansa na Gifta sai ya Hantare ni da Mummuna,baka,Tun bana Fahimtarsa har na fara gane hantara ce da Tsana shi da Anty Binta sun ce basa son kallon Fuskata baki na da muni na yayi yawa.
Baba yaso ya maidani makaranta Mama tace zai yi asaran kudin sa ne Tunda baji nake yi ba Sai yace zai maidani islamiya Dakyar ta amince ina zuwa ta Lasar zuwa shidda na yammah ammh sai nagama duka aikina sannan zan fita,anan na samu na Sauke alqur'ani daman kum na d'an yi nisa a karofi,sannan nayi karatun Sauran Littafan Addini da wannan zan iya cewa na Tsira a zamana a gidan Baban katsina.




*Janafty*[6/12, 12:11 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*

_*Barka da Zagayowar Ranar Haihuwa HAFSAT MUSTAPHA HAFNAN(SAHIBATU),Madallake da ke,Allah ya karo shekaru masu albarka Happy birthday*_

*Assalamualaikum! Phydoors* *collection (home of all you need)tazo muku da kayan gyaran girki masu inganci da Gina jiki da faranta Ran Mai gida harda Ma yaranmu domin inganta girkin uwargida Kai harma da amarya tazo muku da egusi,* *crayfish ,manja ogbono dadai sauransu Zaku iya tuntubar ta wannan nomber 08062181151 ko Kuma shafinmu na yanar gizo https://instagram.com/phydoors_collection?igshid=MzNlNGNkZWQ4Mg==Muna aikawa ko Wani gari da iKon Allah,ko gwada kayanmu da iKon Allah sai Kun dawo* 🥰🤗

       *🅿️04*

Sai kuma girken girken zamani da na gargajiya da na koya a iya zamana agidan mama shima ba wai ita ta koyamin ba,Ni na koya da kaina Saboda ina da karambani Mama bata taba Damuwa dani ba tsakani na da ita sai Harara da hantara,tana ganina a matsayin wata aba mara gata da galishu wuya ce da wahala yasa tun ban iya komai ba har na koya.
Na yarda ina da nakasun rashin ji ammh bani da nakasun wani abun Hallita ajikina ina da rai na da lafiyata to zan yin komai,Na iya wasu girken girken a tashar arewa24 na shirin su Akushi da Rufi wani Lokacin Tibin ita kad'ai afalo tayi ta babatu in nagama aikina sai na Lallabo nazo na zauna Duk da bana jin yadda suke koyar da girken girken ina bin yanayin yadda suke Hada komai ina ganewa.
Sannan da kuma Anty Mamah babbar Diyar mijin  Anty Binta ce mahaifiyarta ta rasu ne dalilin da yasa ma ya auri Anty Binta kenan.
Tana aure acikin asibitin Kashi wato Othorpedic na katsina mijinta Likita ne tana da Yan biyu wato Twins,Mama na yawan Tura ni gidanta Saboda reno Yaran nata duka mazane Hassan da Husaini masu Rigima ne Anty Mahma ba kamar Anty Binta take ba,bata da mugunta  sai dai akwai saka aiki,Kuma tana da kyauta sannan bata kyamatata ko tayi min fada, in naje gidanta kamar jaka har gwara ma gidan mama ina Hutawa sai dai ita bambamcin su bana girki da kaina ita da kanta take shiga kitchen tayi abunta ammh nakan shiga na taimaka mata da yanke yanke da miko miko to da haka nake zura ido ina Fahimtar wasu abubuwan nasan bani da gatan da zan yi karatu ko ina dashi ina jin tsoro zuwa makaranta saboda kada akusheni ko ayi ma Nakasuna Dariya shiyasa na kan kasa ido da raunannun kunnuwana ina duba wasu abubuwan da jin wasu abubuwan iya abunda zan iya ji na kuma d'auka.
Sannan agidan Anty Binta ma na koya su Snaks saboda Diyar Anty Binta ta farko mai suna Halisa zamu iya zama tsaran juna tunda Anty binta tayi aure tana da kananun shekaru alokacin to ita ke sana'ar yin Snaks in naje gidan nakan kasa idanuwana ina lura da abubuwan da take yi a hakan na nake daukan wasu abubuwan.
Da yake ita Halisa tana da bambamci da su ba kasafai take nuna kyama gareni ba sai dai bata shigemin sau tari nakan taya ta aikin Snaks din ta in an kawo mata dayake sana'arta ne tayi suna tunda tana amfani da Social media alokacin.
Tun ina da shekaru goma sha Hudu a duniya jikina ya gogu da aiki babu aikin da zai gagareni komai yawansa agidan Mama tun karfe Hudu nake tashi Daga barci naje kitchen na kintsa Sannan na Dora abun kari sai naje na tada Badariya bayan na saka mata Heater na wanka Saboda zuwa makaranta Domin dokar da Mama ta kwafanin kafin bakwai na Safe na gama komai kada ta fito bata iske abinci a saman dining ba,ko kuma taji kafafunta na taka Datti acikin Falonta Shiyasa ina yin abun kari wani Lokacin ina Share sharen dakuna hatta Dakin Jamal ni nake gyaramai in suka tafi makaramta Saukin ta ma shi bai cika mgana ba barshi da waya a Hannunsa irin su ba kasafai ake gane inda suka dosa ba.
Ya ishaq kuma baya gida sai an yi Hutu yake zuwa yana ABU Zaria inda yake Masters di'nsa nima abakin Anty Binta naji sunan karatun nasa har na iya rikewa,Hatta da kayan Jamal da na Badariya da na Mama ni nake wankewa ammh Baba bai sani ba Saboda yasan duk wata baya fashin bada kudin mai wanki da guga Tunda Mama ta sameni take soke yan kud'ade'nta,in wankin ya taru tun safe in naje baya na fara sai yammah watarana ma bana ko samin zuwa islamiya,Washegari kuma Baba na fita zan dasa guga har sai bayana ya kage ba ci ba sha sai na gama in kuma nace zan tashi ko sallah in yi sai Mama ta kai min duka tana Fadin"Me kika sani a karatun sallar..?Ni fa jin baban su kawai nake in yana Fadin kina da ilimin addini  ke da kike Bebiya gaki ba kyau ba fasalin y'a mace ai bautar da ta dace da irin ku kenan.."
In ta fadi haka bana damuwa sai naga gaskiya ta fada domin na fahimci in baka da kyau ko Asali da gata ko kana da wani nakasun Hallita baka da wani amfani Domin wad'anda suka fi kusanci dakai sune suka fi kowa kyamatarka to inaga na waje wad'anda basu san ka ba, mu'alama ce zata hadaku..?
Ina tuna Lokacin muna Malumfashi Iyayena sun san ina da Lalura ammh ko sau daya basu taba nuna gazawar su ba sun min dukkan gata a malumfashi makarantan da aka kaini ina gane karatu tunda ana yimin yadda zan gane sannan bamai kyamatata Saboda ina da gata alokacin ammh daga Lokacin da gata na ya kare sai nima nake fama da guilt din shiga cikin Mutane ina ganin ban kai ko wani matsayi ba sannan na aminta da mganar Mama iri iren mata irina Bautace ta Dace damu..
Shiyasa duk wahalan da nike sha bana Damuwa ina ganin ahakan ma ni kila nafi wasu ma ire irena,Baba duk baya sanin wasu abubuwan tun da in ya fita tun Safe sai Dare,in kuma ya Dawo yayi sallah yaci abinci zai kirani falo yayi  ta kokarin na bayyana mai abunda nake bukata ko nake so ammh bana iya mgana Saboda Mama ina bala'in jin tsoronta kamar wata mala'ikar Mutuwa.
Baban katsina irin mazan nan ne marasa Bibiyan al'umuran gidansu shiyasa Mama ta samu dama tana Damawarta,Komai na Cefane Mama yake bamawa,Duk watan Duniya ita kuma sai ta samu nata aciki Mama tasan kan kasuwanci,Tana saida dikkakun kayan mata da maza anan ake dinka mata tana aika ma yan'uwanta dake yamai suna Siyar mata kuma har anan tana samun ciniki sosai tana harka da manyan mata bayan dikakku har Tamfofi da Lesuna tana saidawa da takalma Shiyasa take da tarin kawaye da Mutanen arziki da ke shiga suna Fita agidan,Shiyasa ko Sutura ita Baba ke bama kudin ko na Mutanen karofi ne kuma baya Bibiya,Shiyasa sai wanda taga dama ta bawa,ba kuma wanda ya isa yayi mgana duk sallah har da su Yaya Asiya Baban katsina ke yi ma Dinki adadin yadda yayi ma Badariya dani ammh ni ko Sabo daya Mama bata bani na saka sai tace Mace irina da kwance ta dace ni kuma sai mganarta ta zaunamin kayan alfarma masu kyau sai ajikin kyawawan mata wad'anda basu da wani nakasu Mata kuma irina da kwance muka Dace yawancin kayan yaran kawayen Mama nake sakawa Domin na badariya bazai min ba Na girmeta sosai alokacin,Su Yaya Asiya kuwa Kala dai'dai take jifan su dashi Yaya mariya bata da matsala ita da Hafsatu Goggo macece mai Tsayawa akanta ita da iyalanta Yaya Asiya kuma tace duk mugunta Hajiyar Dala tana barinta da Suturu Saboda ita yar gayu ce sannan mijinta Soja ne ya'yanta fes suke itama haka saboda haka Itama Yaya Asiya badai a ganta da kama mara kyau ba.
Ni dai ko da yaushe cikin Tsumma da Ragga In Baba ya gani yayi mgana Mama ta lawayance zance ni kuma bana iya karyatata agabansa,bazan taba mantawa da wata sallah ba,Sallah da na fara yinta a gidan Baban katsina Lokacin na kwashe wajen wata Tara a katsina,kuma tunda nazo ko Karofi kafata bata kara takawa ba Ga Hajiya na raina in Baba zai tafi gaisheta sai naji kamar na bisa,tunda duk karshen wata yake zuwa wani Lokacin shi da Mama suke zuwa wani lokacin shi kadai da Direba ko shi da Jamal.
Hajiya na rai na ita da su Yaya Asiya musamman Hasfatu kewar Tamadina kuwa har na cire sa araina tunda ba samun ganinta zan yi ba Tun bayan dawowata Ko mutum daya Daga karofi bai leko mu ba na dai ga Hajiyar Dala da suka taba zuwa Bikin Dangin mijinta ta sauka anan kawaye ne ita da Mama sai muguntar su tazo daya sai dai ita tafi mama ji da kai da nuna ita din watace.
Sallar azumi ne Dama da azumi duk na Rame na kara lalacewa,Ni bansan gayu ba, bansan komai mai kyau ba ni na dauka abu mai kyau a wajen mata masu kyau ake samun sa,Wani Riga da Sikat na saka cikin kwancen kayan ya'yan kawayen Da mama ke bani ne wuyan zamemin yake haka ma Sikat din yayi min yawa sai da na saka Tsumma na Taresa ajikina Hijabi ne kadai Sabo Shima Anty Mahma ce ta dinkamin domin jiya gidanta na wuni na tayata soyan Nama da aikin cinci Sai Dare ita da mijinta suka maidoni gida ita ta na da kyauta in nayi mata wahala tana min alheri takalmin kafata na Roba ne shima din Na jamal ne da ya daina amfani da shi na Dauka
Da farko Mama bata so aje dani Sallar idi ba,Sai Baba yace dani za'a tafi Ya Ishaq ya dawo agida yayi azuminsa Shi na lura kamar baya ma san kallo na shiyasa ban cika giftawa ta gabansa ba.
Lokacin da na fito Kofar gida Baba ya ganni sai da yaji kwallah ta cikamai ido,Ya kalli Badariya ta kure adaka ita da Mama,Jamal da Ya ishaq sun ci Fararan Shaddodi sai Faman sheke suke ni kuma bazar bazar kamar mahaukaciya wata yar aikin ma tafini kyan gani ni kuwa bakina kamar zai Tsage Saboda murna zan fita masallaci naga jama'a Tun kafin Baba yayi mgana Mama ta rigasa da fadin"Ke Fa'iza meyasa kika saka wadanan kayan..? Ina naki irin na Badariya..?
Sai na kasa mgana Saboda ni dai bansan da wani kaya ba,ba'a bani ba ganin Baba ya saussauto yana kallonta yasa ta kara karya murya tana Fadim"Bansan meke damun Yarinyar nan  ba Abban Ishaq ko da yaushe bata da aiki sai saka Tsumman kaya nama ce ta hada su in zaka Karofi ka tafi da su arabama mabukata"
Ban yi mamakin kalaman Mama ba Domin tun zuwana gidan ba Dadewa,Ta daina Fada da Baba akaina sai ta koma aiki da Kissa shima shawaran wata kanwartace daga Yamai hure ita tace mata in tana so taci Ribar Rayuwa to ta daina tada Hankali ta yi amfani da kiss,kuma Tabbas kissanta tana Tasiri wajen Baba don nan take ya kalleni kafin yace"Haba Fa'iza ya zaki saka wadanan kaya..? Baki ga sauran yan'uwanki ba ne.?maza je ki sauya kaya mu tafi kada mu makara'"
Da Sauri Mama tace"Zamu bata Lokaci Alhaji muje in mun dawo sai ta sauya"
Sanin Halinsa na rashin bincike kan al'umura yasa tace haka,Haka muka tafi su kamar zara cikin wata ni kuma kamar yar aikin su Shikenan ko da muka Dawo Baba yayi baki yana falon waje har Dare bai kara bi ta kaina ba,Sai da Washegarin Sallah da kwana Biyu mukaje Karofi ranar dai Mama ta bani Sabon kaya na saka ta kuma ja kunnena in taji wata mgana sai na Raina kaina ni ko araina nace wazan gayamawa.?bata san ina da zurfin ciki ba ba tun yau ba,bakomai ake jinsa bakina ba.
Duk da Sabon kayane ammh da na sanya kamar wata Dussa komai ba Tsari ni kaina nasan ba kyakyawa bace ban mallaki komai na mata masu sa'a da gata ba,Kusan daman Hausawa kan ce in kana da kyau ka kara da wanka to ni bani da kyau din sannan ban iya wankan ba ballatana na kara dashi,Wani Lokacin sai Dare nake samun Damar yin wankan Tunda Dakin da nake ciki akwai karamin Tiolet to iya wankan ne ko shi ba don kyau nake yi ba Komai bazar bazar ne bansan iyakarsa ba.
Da mukaje karofi na hadu da su Ya Asiya har sai da sukace har baki na kara na rame sun yi tambayan Duniyan nan kan wani irin rayuwa nake yi agidan Baban katsina naki ce musu komai sai dai in kallesu ina mirmishi naji dadin ganinsu haka barin ma Hafsatu da ta zama kamar ba ita ba ta kara wayau da girma.
Ina jin su a tsakaninsu suna tattauna yadda Rayuwa ta jefa su a inda suke ni dai bana ce musu komai nadai san na Tambayesu tamadina suka fadamin tana Lafiya Yaya mariya na zuwa Dubata ita da Goggon Karofi sukace In Baba ya barni gobe sai muje na ganta.
Ganin Goggon Korofi yasa Mama batayi mgana ba,Baba kuma ya amince washegari chan muka wuni sai yammah muka dawo ita kanta Tamadina ta na cikin wahala gida cike da yara,wahalar tayi mata yawa sai dai ba yadda zatayi ne kwanan mu biyu muka koma Katsina,Na koma da Tausayin Hajiyar Karofi ganin jikinta duk ya kara rikicewa yanzu ma dayan barin shima ya Daina aiki Goggon Karofi da ya'yanta suna matukar kokari kan Hajiya.
Haka rayuwata ta cigaba da tafiya a gidan Baban katsina duk da irin azaban da nike sha achan ban taba jin na gaza ba sai ma nake ganin Sun yi min komai tunda zan ci na sha na kuma samu wajen barci Baba na jin Takaicin rashin Karatu na ko da yaushe naje gaishe shi da Safe sai ya kalleni yace min"Fa'iza kin k'i makaranta ko..?
Baki san ilimin zamani ginshiki ne ga rayuwar ya'mace ba..?
Ni kuma bana iya mgana sai dai na Dukar da kaina cikin Tausasawarsa yake cigaba da Fadin"Da kin Daure Fa'iza ai kina jin mgana zaki gane komai sannan zan yi ma malaman ku bayani kamar yadda nayi ma malamanki na islamiya bayanin Laluran ki"
Ina Dagowa muka Hada ido da Mama ta Sakar min harara sai jikina ya fara rawa cikin yanayin mgana ta nace"Baba shi na addinin ba Ilimi ba ne..?
Sannan shi ba Ginshiki ba ne ga rayuwar mu ba..?
Baba ya jinjina mganata kafin yace"Ginshiki ne Fa'iza babban ginshiki ba kuwa..Sai dai ka hada duka fufukan guda biyu sai ka samu na zaman duniya da Lahira"
Alokacin sai nace ma Baba"Baba ka barni haka..na islamiyan kadai ya isheni"
Zai matsamin sai Mama ta taresa tana nuna mai Tunda ban so to ya kyaleni,Shi kuma bai da Zafi sai ya Rabu dani ammh ko da yaushe kalamansa akaina na alheri ne har ya bar duniya ko kallona yayi sai yace"Fa'iza Allah yayi miki albarka In sha Allahi bazaki Taggyara ba..Ina ji ajikina kina da wata baiwar da Sanadinta zaki Daukaka watarana"
In naji haka sai nayi Dariya araina Domin bana hango ma kaina hakan
Na amince Baban Katsina ya karbo ni Hannun Goggo karofi ne domin ya inganta Rayuwa ta,sai dai bashi da Mafita ne Mama ta fi karfinsa ammh har yau bazan manta kokarinsa akaina ba.
Shi ya fadama malaman islamiyan da nake zuwa yanayina suke bani kyakyawan horo ko an gama karatu gabadaya sai an kara min bita ni kadai,Bani da wata kawa shiyasa ni kadai nake zama iyakata da kowa Mirmishi ko Sannu nasan ana mgamata ammh da yake bana ma ji Sosai ban cika Damuwa da su ba.
A farkon zuwa na gidan Mama cikin kasuwar katsina take zuwa siyayyarta ammh sai Kawarta Hajiya Barira irin masu son kudin nan ne ita ta bata shawaran ta rika zuwa kano kwantin kwari tana saro kaya alokacin Mama sai tace"Kai Barira ya yi nisa ni kinsan ban san wahala"
Hajiya barira ta rika nuna mata yanayin komai tare da fadin nachan sun fi sauki sannan zata hadata da yan kasuwar chan tunda itama tana siyayya achan har sai da Maama ta amince bazan manta ba na zo kawo ma Hajiya Barira abinci na juya naji tana ce ma Mama"ko wannan bakar yarinyar kika tara sai kuje tare ta rika Daukan miki kaya"
Mama ta kalleta kafin tace"Ko Hajiya barira"?
Tace to zauna Daman meye amfanin irin su in ba aikin wahala ba.
Da wannan shawaran Mama ta zauna tana fadama Baba ya amince tunda shi ba mutum ne mai Takura ga iyalansa ba.kuma da tace dani zata bai yi gaddama ba domin nuna mai tayi ina kokari zata nuna min komai Domin tana Tunanin nan gaba ko ban yi karatu ba zan yi kasuwanci to ai Daman haka take fadamai ko na wahalan da nake yi ne,Girki ma Baba yace nayi kankanta Mama tayi Karaf tace gwara na koya Saboda gaba gidan wani zani Daganan Baba bai kara mgana ba.
Daman tun anan ni nake kaimata Dinki chan batagwara kusa da gidan Anty binta,in ba'a gama ba sai na zauna an gama Wani Lokaci anan nake wuni buhu ne shake da kaya zam Dauko akai zuwa bakin Titi na samu Daidaita sannan in na Dawo na Hau ware ma masu kayan nasu,wad'anda za'a tafi da su yamai kuma duk ni ke shirya su Mama na gefe tana lissafin komai ban isa nace nagaji ba.
Ranar da muka fara zuwa kano sai da na raina kaina Wuni guda acikin kasuwa kuma bata Dauki dan dako ba ni ke daukan mata kaya akai kamar mahaukaciya ga yunwa ga kishi Takalmi a Hannu hijabi a hannu Wlh ko abinci bata siyamin ba Da muka Dawo sai da nayi rashin Lafiya Saboda na Jigata matuka alokacin Mama fada ta Dinga min akan na fara zama mai son jiki to in zam mike tun wuri gwara na mike Bani da wani amfani in ba Bauta ba.
Ni ba kyau ba,Ba ilimi ba,Ba ji ba,ba komai na inganci rayuwa ba,bai kamata na rika nuna gazawata ba tabbas gaskiya ta fada ba ni da wani gata a Duniya Bautar dai da ta Fada shine ya fi dacewa da mata marasa galihu ire irena
zuwa Lokacin da na shafe shekaru Shidda Cif a wajen Baban katsina bazan iya fadin irin bautar da nayi ba abu daya na sani ni Fa'iza ban sauya ba Sai dai na kara girma ammh ba Domin na sauya Daga yadda nake ba Ina nan a  mai raunannan ji,Mara gata baka Mummuna mara sa'an rayuwa in ji ya Ishaq in ya ganni yakan ce Bai taba ganin mace mara sa'a ba irina komai Total zero ne a bangarena ba wani abun so ko sha'awa tare dani nima nasan haka ko badariya dake tasowa mai kyau ce sannan yar gayu kuma yar gata ni kuwa ban ma san me ake kira da gayun ba,Ni dai kawai nayi wanka na suturta jikina mganar gyaran jiki da Tsaftan jiki ban san shi ba Ba kuma wanda ya ke zaunar dani ya koyamin Ko kitso sai ni nagaji da kaina na tsefe shi kitso kuma sai in Mama taga dama zata bani kudi naje,ayi min.
Zuwa Lokacin rayuwa ta Daga,Sosai ba kamar baya ba,kawayen Mama da suka sani tun abaya in suka gani sai like sai suka rika ce ma Mama Daman wannan mummunar dangin mijin naki na nan baki aurar da ita ba.?
Mama kan basu amsa da cewa wazai kwashi Baki da muni da bebanci sannan uwa uba ba ilimi sai su yi ta Dariya suna cema Mama shikenan ta samu yar aiki to ai daman ba marabata da mai aiki maraban mu daya in da Daukoni akayi da sunan aiki za'a  rika biyana albashi,Shine kawai bambamcina da mai aiki acikin wannan gidan.
Su Yaya Asiya duk sun yi aure ita da Yaya Mariya Ya Asiya acikin garin kano tayi aure wani malamin makaranta ne yana da mata da yara,Mai karamin karfi ita kuma Yaya Mariya A karofi tayi aurenta wani dan kasuwa ta aura mai rufin asiri.
Kusan tare akayi Bikin su sai dai na Ya Asiya aka fara yi ,Duka naje bikin su ammh na Ya Asiya sai da Goggon Karofi ta kira Baba ta mai mgana domin tasan Halin Mama munje kano mun yi kwanaki Tunda Bikin tare da manyan ya'yan Hajiyar Dala babansu ya Hada, da Asiya harta duka kudin siyayyan kayan Daki tare ya bada ammh Mama ta zuga Hajiyar Dala akan su ya'yanta suna da gata Asiya kuma ayi mata na Daidai da ita Daga karshe ma ita taci kudin domin duka Dawaniyar Yaya Asiya Baban katsina yayi mata shi,Duk ciki ita kadai ta auri mai karamin karfi gidan falo daya ne sai Dakuma nata da na uwargidan Ba Shakka Baba yayi mata kokari sosai,Bangaran Yaya mariya Goggo da Mijinta sukayi komai ita gidanta ita kadai wannan bikin ne har Tamadina tazo,na Yaya Asiya ne bata je ba, in naga yadda Rayuwar Mahaifiyarmu ta koma sai na kara tabbatarwa lalle bamu da gata gatanmu ya fadi tun Lokacin Rasuwar Baba.
Da ace Hajiyar Karofi na Da lafiyanta da kila abubuwa sun sauya ammh kuma tana kwance sai dai a kwantar a tayar bama wanda ya zata kai haka araye,ana zuwa gida ana Dubata har yau tana nan jiya iyau bata ko mgana Sai wanda ya kara kunnensa yake ji me take fadi in naje Hajiya ta rika kallona kenan na rike hannunta ina Fadin"Allah zai baki lafiya Hajiya"
Sai dai kaga Hawaye na Bin gefen fuskarta Hajiya na bani Tausayi sosai shekaru kusan bakwai tana jinya tana kwance waje daya,Gidan su na karofi Babban Yaron Goggo Yaya Isa ya gyara da yayi aure yake zaune da matarsa kada abar gidan ba kowa ya mutu Baba ya matsa sai ya zauna da Farko Goggon Karofi bata so hakan ba gudun Rigiman zumunci.
  Ya Ishaq ya dawo gida ya gama karatu har ya samu aiki a Hukumar Tattara Haraji na kasa reshen jahar katsina,Shekaru uku da suka gabata,Sai dai baya zaman gidan in ya fita tun safe sai dare in kuma ya Dawo yana Dakinsa na fada muku tun a baya shi baima son ganina shiyasa bamu cika Haduwa ba, bana zama inda nasan zai ganni Saboda yafi kowa iya kallon wulakanci da kaskanci.
Akwai watarana tana cikin cikin Ranakun da bazan manta da su ba acikin kaddarorina ba,Muna gabda Riskan kaddaran auren mu ni da Ya Ishaq al'amarin ya faru watarana ya kira Mama a waya yace yana son abincin Mutum hudu abokansa zasu zo su yi Dinner anan biki sukayi na wani abokin aikinsu.
Nan da nan Mama ta tasoni na shiga Kirchen daman na fada muku a bangaran girki ni Fa'iza bani da makusa,Harta Mama yanzu in ba girki na ba bata iya cin abinci,Shi ko Baba kullum Mama yake godemawa yana ganin ita ta tallafamin na iya girken girken zamani zuwa kuma Lokacin na rage wasu walwahalun,Saboda Mama ta daina aike na ta samu yaron aike bangaran kasuwancinta kuma komai ta waya ne sai dai a saka mata a mota a aiko mata dashi,sannan ta dauki masu wanki da guga da kuma mai wanke wanke na koma gyaran gida da girki.
Jin baki ya ishaq zai zo da su na Zage nayi musu girki mai rai da lafiya fatan pototo,da Hanta sai white rice da Miyar kifi,Sai nayi musu lemun Abarba Sai na hada musu da na Gwangwani kafin ya kariso Mama ta sani na je na shirya komai afalon Baba,na koma kitchen na Dora abincin dare na gida har bakin suka zo ni bansani ba Na gama girkin Dare doya da Miya Mama tace ayi naje nayi sallar mangariba ina zaune saman sallaya Jamal ya shigo Dakin da nake mai karamar katifa sai tarkace yace min Ya Ishaq na kirana afalon Baba sai da gabana ya fadi ban cire Hijabin jikina ba yamin yawa yana neman gadani na nufi Falon Baba
Ina shiga da sallama gabadaya zaratan mazan dake falon suka Dago suna kallona ni ban iya kallon su ba,Saboda yadda jikina ke kyarma,ina ji Ya Ishaq ya dakamin Tsawa yana Fadin in kariso,Ni dai nasan nazo gabansa na durkusa kaina na kasa ina ji yace musu"To ga wacce tayi girkin nan da kuka matsu ku ganta"
Ya fada cikin sigar Dariya da karfi yayi mganar yasa naji abunda yace gabadaya shuru sukayi kafin naji sun kaure da Dariya gabadayansu sai naji na muzanta matuka muzantan da ban taba yi ba suna ta mganganu wasu ina ji wasu kuma bana ji nadai ji sanda Ya Ishaq yace"Kai ka yi mata da Hausa No Turanci..Sannan Ears."
Gabadaya suka gwalalo ido kafin ya kalleni yace"Yes..sai kunyi mgana da karfi zata jiku Bebiya ce"
Na kusa dani ne ya matso saitin kunnena yana Fadin"What is your Name.?
Aoh Sorry ya sunanki..?
Na dago idanuwana sun cika da kwallah nace"Fa'iza"
Cikin yanayin mganata gabadaya sai suka sheke Da Dariya har suna Tafawa da junansu Sai naji na kara raina kaina Nasan ni ba bebiyace ba ce ina dai da Raunin ji ammh ba Kurma bace ni Mutane ne suka kara Raunana jina da kushe da Tsangwaman su akaina,Ninasan inaji sai dai sai an yi mgana da karfi Sannan mganata tana  da Tsami Tsami Kuma ina Rabe ta kamar ina in ina kuma saboda Raunin ji na ina karantar bakin mutum in yana mgana Ko Tamadina ba Kurma bace tana mgana sai dai mganata tafi nata fita sannan na fita karfin ji.
Ammh yadda suke kankanba Bebanci na abun bai kai haka ba.
Ban taba jin guilt irin wanda naji ba  Ranar hawaye suna bin fuskata na mike zan fita Ya Ishaq ya dakamin tsawa yana fadan sun sallameni ne..?sai na Dawo kawai na Durkusa ina jin Ya Ishaq na fadin bai taba ganin baki da muni ba sai a wajena su ma abokan irin sa ne suna ta Dariya na kamar sun ga abun dariya ajikina ko acikin Abunda suke ma Dariya aciki akwai wanda na bama kaina ba Allah ya bani ba? abun da nake sakawa araina kenan ina jin wani irin abu a kasan raina.
Sun dade suna kallona suna Dariya kafin Ya Ishaq yace na kauce daga gabansa na mike idona ya rufe bana ko gani,bansani ba na ture Teburin dake gaban su jug din lemu ya fado ya zube Lemun ya fallatsa a jikin abokan nasa dashi kanshi har ga Allah ban lura ba,ba karfi ji ne dani ba shiyasa ban ji karar faduwar wani abu ba,ba ma haka ba yanayin da nake ciki gabadaya ji na sa ganina ne suka Dauke a lokaci d'aya.
Na dai san kafata ta bigi wani abu ammh yanayin da nake ciki bai sa na Tsaya Dubawa ba.
Sai ji kawai nayi an dawo dani baya an yarfar dani akasa ya Ishaq ya Daga Hannu ya wankeni da mari acikin kalmominsa na tsinci kalmar"Banza Jaka,Mummuna useless har na isa na wulakanta abokansa ko akwai sa,a na acikin su ne..?
Ina dafe da kuncina na bisu da Kallo ya fadi gaskiya ba sa'a na acikin su kamar yadda yake kyakyawan gaye haka suke suma,jikina na rawa na fara bashi Hakuri sai yace sai na juya na basu hakuri haka na Durkushe ina basu Hakuri sai da sukace sun hakura ya bi ni da Hambari ina Rarrafe na bar Falon ranar kwana nayi ina kuka har na fara neman nayi Sabo sai na zauna nace meyasa Allah bai yo ni mai kyau kamar kowa ba..?
Ko dai da gasken ne bani da Sa'a..?
Washegari Da Mama taji Labari Allah ya kara tayi har da fadin da ya fada mata Tun jiya sai ta karamin da Duka.
Ina Falon ina goge goge ne alokacin naji sanda Jamal yace"Kai ma Bro meyasa ka kirata cikin abokan ka.?
Sai da yayi tsaki mai karfi kafin yace"Su suka matsa sai sun ga wacce tayi abincin"
Daganan ban ji meya ke fad'i daga karshe ba,Saboda ya Rage murya Ranar ina aiki ina kuka abaya bana Damuwa in an kusheni ammh yanzu sai naji kamar da gaske ne ni Fa'iza bani da Sa'a
  Ashe abunda Ya Ishaq bai sani ba Matarsa ya Tozarta,Agaban abokansa Domin ko sati ba'ayi ba Baba ya tafi Karofi Sakamakon kiran da Goggo tayi mai kan cewa jikin Hajiyar ya tashi Abun mamaki tana ta kiran sunan sa shi da Mama da ya Ishaq suka tafi suna chan ne nima ina gida Hankalina nakan Hajiya ban san me ya faru ba, ni dai nasan sun Dawo gidan cikin Hargitsi da Rashin kwanciyar Hankali mama sai kuka take yi tana Fadin bamai hada mata zuru'a da Dangin munana da kurame.
Washegari fada ita da Baba har Falo alokacin naji Baba yace"ko bayan Ransa sai auran Fa'iza da Ishaq ya kulli sai dai ta mutu"
Dayake da karfi yayi mganar naji sa ni kaina sai da na gigice ana haka sai ga Ya jamal yazo yana fadin Ya Ishaq ya kwashe kayansa ya bar gida Mama ta fadi kasa Hannunta akai tana kururuwam ta shiga uku ta Lalace
Haka Baba ya tsallake ya barta ban bari kowa ya ganni ba na koma Daki ina rawan jiki mai nake ji,Wai ni Ya Ishaq zai aura.?
Tirkashi ni kaina na hango tashin Hankali acikin lamarin ranar har Anty Binta tazo ita da Anty Mahma da kawayen Mama na kusa,sai mganganu suke ni,ni ina Daki baji nake yi sosai ba, ranar ko girkin ban iya yi ba kuma ba wanda ya nemeni.
Nima Badariya ta shigo take fadamin Wai Hajiyar Karofi tace a hada aurena da Ya Ishaq,ance Dakyar ma aka gane me take nufi Saboda Harshenta ya karye.
Ba Ya Ishaq kadai Hajiyar Karofi ta cuta ba  wlh har dani ina ni ina Ya Ishaq ai tazaran ma mai yawa ne.ranar kafin Baba ya Dawo Mama da su Anty Binta suka kirani Falo suka min Fata fata zagi da gori ba wanda ba su yi min ba har da gorin mu dangin maciya Amana ne to wanda ma naji kenan wanda kuma ban ji bansa me suka fada ba,Dayake da karfi suke mganar Anty Binta ko har tana Hadamin da dunguri Mama taci kuka har ta godema Allah idanuwanta sun kala sun yi jajir Ita damuwarta Ishaq ba bawanda yasan inda ya tafi ya kuma kashe duka wayoyinsa Mama taja kunnina da cewa in Baba ya Kirani ya tambaaye ni in na amsa mganar auran nan sai na gwammace rashin amsawata Domin bata fatan Had'a zuru'a dani Har gaban Abada.

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

*Littafin KANA NAKA paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*



*Janafty*
[6/12, 7:52 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

*Assalamualaikum! Phydoors* *collection (home of all you need)tazo muku da kayan gyaran girki masu inganci da Gina jiki da faranta Ran Mai gida harda Ma yaranmu domin inganta girkin uwargida Kai harma da amarya tazo muku da egusi,* *crayfish ,manja ogbono dadai sauransu Zaku iya tuntubar ta wannan nomber 08062181151 ko Kuma shafinmu na yanar gizo https://instagram.com/phydoors_collection?igshid=MzNlNGNkZWQ4Mg==Muna aikawa ko Wani gari da iKon Allah,ko gwada kayanmu da iKon Allah sai Kun dawo* 🥰🤗

      *🅿️05*

Lokacin da Baban katsina ya kirani Falonsa adaran da su Mama suka ja kunne ne ammh na kasa iya d'ago ido na kalli Baba ballatana nayi mai gaddama kan lamarin da yazo min dashi cikin wani yanayi na roko da Tausasawa Baba ya sanar dani Umarnin Hajiya na had'a aurena tsakani na da Ya Ishaq shi Uba ne gareni zai iya aurar dani ko da ban sani ba addini ya basa wannan damar ammh bai yi haka ba, sai ya zabi da  ya kirani yana Roko na na amince don ya samu damar da zai cika Muradin Hajiya..
Ina kallonsa da kumburarrun idanuwana da suka tasa saboda kuka Da damuwa Hawaye suna Biyo Fuska ta wasu na korar wasu Baba nake kallo wani Mutum da nake gani Da kima da Daraja mutumin da nake ganin shi Kad'ai ne ya ragemin gata na aduniya ta ya ya zan iya bude baki nayi mai gaddama.? Amsa masa kuma Daidai yake da Fadawa Ukuba kamar yadda Mama ta shaidamin ita da su Anty Binta..
Na bude baki da niyar nayi mgana kalmar
" Baba.."
Kad'ai ya iya fita a bakina sai kawai na saka ma Baba kuka shi kuma bai duba yanayi na ba ya shiga sakamin albarka da Fatan gamawa da Duniya Lafiya sai harshe na yayi nauyin da har Baba ya sallame ni na kasa Furta ko kalma d'aya ammh a kasan raina nasan wannan auran bai kamata ya tabbata ba Domin babu had'i ko gami acikin sa gabad'aya.
Ranar nasha kuka kamar raina zai fita Tun cikin Dare Mama da Baba suke Rigima da karfi suke mganar Shiyasa nake jiyo su sama sama Tunda Baba ya fita sallar asuba bai Dawo ba Mama ta rude ta shiga tashin Hankali Saboda rashin Sanin inda Ya Ishaq ya shiga Tunda yaji mganar auran mu
Ni dai ban san ya akayi ba ina kwance sai ji nayi an rufeni da duka kota ko'ina,ina kuka ina ihu ammh Mama bata Tausayamin ba kuka take yi tana Dukana fadi take yi"Dangin jaraba dangin masifa Saboda ke Abban Ishaq yace zai iya rabuwa dani...?Saboda ke Ishaq ya bar gida ban san ina ya shiga ba..? Kuma ahaka zan amince na hada Zuru'a dake..?wlh sai dai ki mutu ammh ni Saudatu bazan taba Hada zuru'ata da b'ara gurbi irin ki ba Shegiya ya'yan shegu dangin maciya amana Mummuna dake D'ana yafi karfin ki"
Da karfi take mgana shiyasa na ke jinta ina ta bata Hakuri bata jini ba Badariya na gefe tana kuka tana rokon Mama ta kyaleni ammh bata tanka ta ba Jamal kuwa yana Tsaye shima Fadi yake yi"Mama duka wayoyin ya Ishaq suna kashe ne sannan na kira abokan sa na kusa sun sanar dani bai zo ba kuma bai kira su ba..Gaskiya Baba shima bai yi Tunani ba Ta ina Ya Ishaq ya Dace da Fa'iza..?
Ina ji Mama ta wurgoni Falo tana Fadin"Ai yadda ta saka ya bar gidan nan nayi Rantsuwa bazan yi kaffara ba itama ta gama zama a wannan gidan yau ba sai gobe ba sai ta bar min gidana"
Da duka da gori da Tsinuwa Mama ta rakani waje ta maida kofa ta Rufe,Dagani sai rigar jikina ta atamfa sai dankwali shima tana Dukana na Rarumeshi na rike a hannuna kafata ba Takalmi Mama ta koreni nan na rakube jikin gidan ina ta kuka na Duba gabas da yammah kudu da arewa bani da wani gata a garin katsina kuma Mama Tunda tayi Rantsuwa to da gaske take Dankwalina na warware na yane kaina Dashi gidan Anty Mamah ya fadomin tana da Sauki Sauki kila ita zata iya taimakamin da kudin motan da zan koma karofi domin chan ne gata na anan duniya..
Da kafata Tun daga Kofar soro har Cikin asibitin kashi,A kafata ina tafe ina kuka kamar zararriya,ban gaji ba Domin halin da nike ciki gajiya bata da Muhalli a wajena Sai dai Anty Mahma ta ganni kwatsam kamar Daga sama tayi matukar kad'uwa da na zube ina bata labarin korar da Mama tayi min Kai ta girgiza kafin tace"Kai Mama meyasa bata bin abu a Hankali ne..?
Bari na kirata.."
Da Sauri na rike mata Hannu naji tana mgana ban ji me tace ba sai dai Yanayin mganarta da wayarta data Dauka sai Tunani na ya bani Mama zata kira ko Anty Binta ni kuma na shiga Tsaka mai wuya acikin wannan Halin Karofi nake son zuwa na Durkushe gaban Hajiya na Roketa ta janye wannan mganar in tana so na cigaba da Rayuwata yadda Allah ya Tsaramin in  bata so ta kara jefa Rayuwata cikin wani Sabon kangi.
Dakyar Anty Mamah ta amince da Rokona ta bani kudin mota ta Daukeni a motar ta da kanta ta kaini Tasha ta sakani a motar Karofi ina ta kuka ta Tausayamin ta Dafa kaina Dake cikin Sabon Hijabin data bani da Takalmi tace"Ki daina kuka Fa'iza ba matsala in sha Allahu Mama zata Sauko"
Har na kai karofi kuka nake yi sai da Muryata ta dishe kukan rashin gata da kuma Tunanin yadda yanayin Rayuwata ya fara na fara jin kamshin gaskiya kila bani da sa'a ne komai nawa ba mai kyau ba ne irin na kowa rayuwata ba Daidai take da Sauran mata ba.
Sai dai Goggon Karofi ta ganni yarkace yarkace kafin na fadamata abunda ya faru sai ta nemi dukana sannan na Zayyane mata komai bazan manta ba sai da ta share kwallah ta kamani ta Rumgume tana Fadin"Abunda Saudatu ta aikata miki kenan..? Daina kuka Fa'iza watarana sai Saudatu tayi kuka idanuwanta akan abunda ta aika miki akwai Allah"
Araina ban taba Hango hakan ba ni kuwa wani matsayi zan taka da Mama zatayi kuka Saboda ni..?
A daran ta Kira Baban katsina ta fadamai Halin da ake ciki yace da Safe zai shigo garin ni kuwa Lallashina Goggo ta dinga yi Hatta Hafsatu dake da karancin shekaru ta shiga Damuwa ganina cikin wannan Halin Hajiyar karofi kuwa tana kwance sai bina da kallo take na kasa na mata wata mgana domin sai naji bakina yayi nauyi ganin yanayin datake ciki Goggo tace tun ranar da Baba ya bar nan jikin Hajiya ya kara rikicewa.
Washegari Baba yazo sun kai ta ba dadi da goggo ta nuna mai ya janye mganar auran nan ita zata rikeni Allah ya bani wani mai sona in yi aurena ammh ba Ishaq d'an Saudatu ba shi kuma Baba yace indai yana Raye sannan shi ne Uba ga Ishaq kamar ya aureni ya gama ina Durkushe gabansu suka rika wannan Hayaniyar ad'akin da Hajiya take jinya itama tana kwance bata iya mgana ba sai gyad'a kai hawaye na bin gefe da gefen Fuskarta.
Baban katsina ya tafi ko sallama bai yi ma goggo ba Allahu akbar adaran Hajiya ta amsa kiran Mahallacinta,Tun daga Lokacin da naji goggon na Salatun mutuwar HaJiya da kaina ya amsa Dum! Har gobe in na Tuna da mutuwar Hajiya sai yanayin ya Dawomin da gaske ne ni Fa'iza bani da Sa'a?
Meyasa duk wad'anda suka Tsayamin suke tafiya su barni Farko Babanmu Sannan ga Hajiya itama har aka kai Hajiya kushewarta bana cikin Hayyacina gida ya cika Har Hajiyar Dala da duka zuru'arta suna nan Hadda Mama da su Anty Binta su Ya Asiya sun Dauka mutuwar Hajiya ce ta tab'ani basu san abunda ke Faruwa ba har kuma lokacin ba'a san ina ya Ishaq ya shiga ba.
Ranar da bazan manta ba,Itace Ranar da aure ya kulli tsakani da Wanda bai Taba sona ba har ko yau da muka Tara zuru'a dashi aurena da Ya Ishaq wanda yau har gobe Mama bata daina aibatani da zuru'aar maciya Amana Dangin Tsiya ba,Ranar addu'ar bakwai din Hajiyar Karofi Baba ya tara Mutane ya Biya Sadaki aka Daura aure na ba wanda ya sani sai da aka Daura Gidan mutuwa sai ya koma Gidan Fad'a da Hayaniya domin Mama kaina tayi tana fadin sai taga bayana Goggon Karofi ta shiga Tsakani Ranar ba iya ni kad'ai ba hadda Mahaifin mu dake kasa yasha zagi Taamadina na gidan sulalewa tayi ta koma gidansu tana kuka,kukan maraici da Tausayin ya'yanta.
Sai alokacin kowa yasan Halin da ake ciki Goggon Karofi ce kad'ai da ya'yanta ke tare dani ban da Hajiyar Dala data mara ma Mama baya,Aranar Mama ta koma katsina ta sha alwashin sai taga yadda auran nan zai Tabbata shi kuma Baba yace sai dai in ba shi ya Haifi Ishaq ba.
Ya Asiya da Yaya Mariya sun koma Gidajen su da Tunanina aransu da Tausayina su kan su sun hango Yadda rayuwa da kaddara suka kara gangarawa dani.
Kwana Ashirin da Rasuwar Hajiyar Karofi Sai ga Baba ya zo shi da Ya ishaaq,wanda ya gama gudun nasa ya Dawo jiya da Daddare ya samu labarin An daura masa aure dani Ya Ishaq ya kasa katabus domin Baba ya Daga mai murya yace in har yaki karb'ata a matsayin mata to sai dai ya chanza wani uban ba shi ba.
Wannan mganar shine Sarka na Farko da ya fara kulle aurena da ya ishaq,Baba ya bama Goggo kudi ta yi min siyayya sannan ya kama mana Haya a katsina cikin gari in da zamu zauna ni da Ya Ishaq,har suka tafi ban gansa ba shima bai nemi ba,Tun kuma Daga Lokacin Baba ya fara shirin Tarewata Mama kuwa tayi Kukan har tagaji ta Saduda ganin Da gasken Baban bazai fasa ba.
Kafin Ranar arba'in din Hajiya karofi hatta jere na Goggon Karofi da ya'yanta da Yan'uwana sun gama min komai Domin Baba yace ranar addu'ar arba'in Zan tare agidana Yaya Mariya ita takaini gidanta ta tsifemin kai ta wanke ta kaini akayi min kitso da Kunshi Ina ta ce mata ta barshi kunshi da gyaran jiki sai Mata masu kyau ba irina ba ban taba manta kalamanta alokacin Kaina ta Dafa kafin tace"Kema kina da kyan ki Fa'iza sai dai in ba'a gansa yanzu ba ne..Ammh na tabbatar miki nan gaba zasu ga abunda nake gayamiki"
Alokacin mirmishi nayi mata Domin nasan ta fada ne ni kaina nasan bani da kyau sannan ina da nakasu ta bangaran Ji na da mganata
Aranar da Hajiya ta cika kwana arba'in a kushewarta ranar na Tare agidan Ya ishaq aurena ba irin na mata masu kyau da gata ba ne,Daga ni sai kayana da Goggo ta d'inkamin Sabbi ita da Baba domin da Goggo Taso su yi min Rakiya sai ya Ishaq yace baya Bukata dagani sai shi a mota sai Baba da Direbansa.
Daga Mama har ya'yanta ba wanda ya Leko karofi,Baba da kansa ya shiga Dani karamin flat din da ya kama mana mai Falo da Dakuna Biyu sai kitchen da Tsakar gida,Shi ya damka Amanata Hannun ya Ishaq da karin wasu manya manya sarkunan da Tun abaya na fada muku su suke rike da wannan auran namu yau har da nike baku wannan Labarin,Domin cikin kaukkausan murya yace mai"Ishaq ga Fa'iza nan na baka auranta ba Domin ta rasa me son ta ba sai domin cika Muradin mahaifiyata..Wlh tallahi ko da Rana daya in ka zalunce ta ban yafe maka ba Ishaq..Kuma ko da rana d'aya kabi Hudubar mahaifiyarka ka Tozarta Fa'iza shima nace ban yafe ba..Daga karshe matarka ce ta sunna ka Kula da ita kuma in ka Danne mata Hakki Allah na kallon ka sannan nima bazan yafe maka ba Sannan kasani Ranar gobe kiyama bazaka Rabauta ba Ishaq in dai ka saba ma Umarnina.."
Kafin ya tafi sai da ya kara Jadaddamai in ya danne min hakkina na aure ko guda d'aya ya sani bazai kara samun albarkarsa ba,ya tafi bayan yayi min nasiha hakuri sannan ya sanar dani na zauna nayi ma aure Biyayya bazan taba Tabewa ba Duniya da Lahira Tabbas wannan Biyayyar da Baba ya Rokeni har bayan mutuwarsa ban sauka daga kanta ba,nima ita ke rike dani acikin rayuwar aure na da Ya Ishaq.
Warware tarin kalubalen da na Fuskata a zama na da Ya Ishaq abu ne mai yawa da bazasu fadi a cikin k'urarren Lokaci ba sai dai abu d'aya na Sani mun yi zama ne na Biyayyar Iyaye shi Mganar Baba ke rike sa da Bakinsa a kansa nima kuma Karfin Biyayyan da ya Rokeni akanta na ke zaune.
Tunda na auri Ishaq daidai da rana D'aya bai taba kallona ya yab'amin ba,Bai taba jin dadin zama dani ba bai taba godemin ba,Bai tab'a godema Baba Bisa aurena da ya basa ba,Bai tab'a sona ba bai tab'a kallona da Idon Rahma da Salama ba  bai tab'a jin zai iya bani matsayin matarsa mai kima ba nayi Rayuwa dashi cikin k'askanci da Tozarci ko da yaushe cikin aibatani yake yi da Kusheni,Ni fa'iza na Fuskancin Guilt din kushen miji har tsawon shekaru Takwas da auran mu,Ya kulleni agida cikin tozarci bai barni nayi zumunci da yan'uwnaa da Dangi ba,Alwashin da Mama ta Dauka ta cikashi bata bari na kara jin Dad'in Rayuwa Sai da tabbattar da duk abunda tace ma Ishaq akaina shi yake amfani dashi bai horar dani da yunwa ba Yana sauke min kayan abinci duk wata sutura kuma yana yi min ta Hannun Mama sai ta ga Dama sannan na saka abu mai kyau cewarta kullum abu mai kyau bai dace da mace irina ba,ina jin Tsoron Ishaq kamar yadda nake jin Tsorom Mama Tunda muka yi aure bai taba yarda ya nuna ma wani ni matasar bace ko abokansa ba su san yayi aure ba, acewarsa matar Ishaq sai an zo a ganta Mai kyau ce mai ilimi ce sannan yar gata gaba da baya ni kawai wata Tsani ce wacce nayi kutse tare da Ruguzamai dukkan Farincikinsa.
Da gaske yake yi ya fad'i gaskiya ni kaina in na kallesa na kalli kaina sai naji Tabbas na yi mai kutse acikin mafarkin sa Ya Ishaq dogon Namiji ne kyakyawan gaske fari mai Hanci d'an Fafa mai ilimi dan alfahari da son komai mai kyau da Tsari ni kuma Bakace Gajera mummuna,wacce bata da gata,ba ilimi kamar ta bakinsa yace Total Zero Fa'iza komai nata ba sa'a acikinsa.
  Ya Ishaq kunyar nuna ni yake yi a matsayin matarsa domin bai taba gayyato wani inda nake ba yace shi kan shi kunyar kallo na yake yi a matsayin matarsa ma ballatana wani,Ko Ya'yan da na Haifa tare da shi Kaddara ne da Rabon su daman Domin Tunda Baba ya kawoni wannan gidan nake rayuwa ni kad'ai Sai dai ina aikace aikace na bana ganin kowa Dagani sai ni kamar mayya Ba ni da waya bana jin kowa sannan bana ganin kowa sannan ya min gargadin ko kofar gida na fita sai na raina kaina shi kuma sai chan dare yake dawowa da Farko gidan Mama yake biyawa yaci abinci Baba d'aya lura da Haka ya mai fad'a sai ya daina Daman na Fada muku yana morata ta bangaran abinci zai ci kafin ya fita in ya Dawo yaci acewar Mama Ai abinci daman bani na siya ba dafawa ne kawai nawa Saboda haka na Dafa daman Mata ire irena da Bauta muka dace,Sai suzo gidan ita da Anty Binta su yi ta zagina da Gore gore Ishaq na zaune kanzil bazai ce ba Wani Lokacin Anty Mamah ce kan musu mgana sai su Sasaauta.
Bazan manta da muna da wata biyar da aure Anty Hure kanwar mama tazo katsina suka zo ita da Mama Ya Ishaq na gida ranar baije aiki ba,Naje kitchen na kawo musu ruwa ina rawan jiki na fice ashe Mama ta kira Sunana ban ji ba, tamin uzuri bani da karfin ji ammh sai Mama tace naji kawai yanzu na raina ta ne agabansu Ya Ishaq ya mareni ya sani na Duka na bama Mama Hakuri taki hakura Anty Hure ta yi ta Dukana tana rankwashina Ya Ishaq na zaune ko ajikinsa haka suka tafi suka bar ni ina kuka kukan da ya riga ya zame min jiki.
Ko wata rana na Shafin Rayuwata ba ranar da bazan yi kuka ba babu wannan ranar,Sai da na fara tara ya'ya sai suka zamemin sanyin idanuwana ko Ya Ishaq ya kunsamin Takaicinsa in na Kallesu sai naji raina yayi sanyi Tabbas ko wacce uwa ya'yanta sune Duniyarta.
Muna da wata shidda da aure,Baban katsina ya kawo mana ziyara yayi mana Fad'a da kakkausan murya musamman ma Ya ishaq ni kuma yace na rame na lalace yayi tambayan Duniyan nan ko Ishaq na min wani abu ne nace mai a'a bakomai haka ya tafi  bayan ya kara fadama Ya Ishaq cewa in bai Sauke hakkina dake kansa ba ya sani Allah na kallonsa.
A wannan Daran Ya Ishaq yazo min ya karbi Mutumcina da kimata ta y'a mace cikin kaskantattacen yanayi,Cikin Tozarci da bana jin wata mace ta taba Fuskarta ban sani ba ammh a kasa raina naji cewa mata marasa kyau ire irena bai kamata su fuskanci wannan tozarcin ba.
Tunda ya gama dani ya tsallake ya barni cikin mayuwayacin Hali,Halin da ni na tallafi kaina bazan iya fadin irin wahalan da nasha ba,ba wanda ya kula dani sai ni kadai,Nafi Sati bana ji na Daidai da taamakon Allah na Samu na Dawo cikin Hayyacina Tun kuma daga wannan Had'uwar tamu bai kara kallo na ba ko da yaushe ni ke mai Hidima ina rawan jiki a kansa shi kuma kalamansa Daya ne Hajiyar karofi da Baba sun cucesa har fadi yake yi tasan zata mutu ammh kafin hakan sai da ta jefa rayuwarsa a wani Hali sannan ta bar Duniya har yau bai taba gode musu ba ban kuma jin akwai ranar da zai gode musu.
Ashe wannan haduwar tamu itace sillar Zuwan Amir(Kabir) duniya ne Wata uku tsakani nayi ta ciwo a tsaye,Zazzabin Dare da amai kasala da yawan barci,Ya Ishaq baisan Rashin Lafiyata,baisan komai akaina ba ban da na girka mai abinci yaci yana ci yana bi na da mganganun kushe da Tozarci.
Fahimtar ma ban da lafiya girkin da na kasa yi ne yasa ya lekani ya ganni kwance Ba domin yaji Tausayina ba sai Domin Harshen Baba akansa yasa ya Daukeni ya kaini asibiti,Gwajin farko aka tabbatar da ina da shigar ciki dan watanni biyu da wani abu Bansan wani yanayi Ya Ishaq ya shiga ba, ammh nasan muna Hanyar komawa gida ya kalleni kafin yace"Ke haka kike daga tabaki sai ciki Fa'iza..?
Yaushe na tsara ma kaina aure ballatana har na haihu?
Ya manta Haihuwa na Allah ne,Bani na bama kaina ba Allah ya bani ammh da Gudummuwarsa,Cikin Amir ciki ne da nayi sa mai Laulayi na sha bakar Wahala acikin gida ni kadai,ina haka watarana Goggon Karofi ta zo ganina ita da Yaya mariya su suka iskeni ba yadda nake suka kwasheni sai asibiti dalilin kwanciyata a asibiti Cikina ya fallasa ga su Mama kowa yaji ina da ciki sai kowa mamaki ya kamasa.
Mama kuwa mamaki yasa ta kasa mgana,Anty Binta sai kallon Ya Ishaq take yi basu taba zaton zai iya kallona na da sunan auratayya ba.
Baba kuma sai murna yake yi shi ya Kira Ya Ishaq da kansa ya fadamai da yazo asibiti ga Halin da nake ciki Sanda yazo,Baba sai da ya Rumgumesa yana murna lokaci d'aya yana sakamai albarka.
Mama ta fad'a agaban kowa da kowa Bata kaunar hada zuru'a dani,Goggon Karofi tace Tunda Allah ya had'a ita bata isa ta raba  ba,har sai da suka yi ta Hayaniya,naji jiki sai da nayi sati a asibiti likita nata fadan bana cin abinci sannan jinina yayi kasa Goggo kamar ta wuce dani karofi Baba ya Hana Akace gidan Mama tace ai har Abada na gama zaman gidanta Dole gidana aka maidani Goggon Ta zauna Dani tayi sati,Yaya Mariya ita kadai ta koma Karofi,A bakinta Ya Asiya taji tazo har Katsina ta Dubani bana ganin Tamadina bata taba zuwa gidana ba na Tambayi Goggo tace min tana gidanta ni nasan rayuwata cike take da abun Tausayi.
Har Amir yazo duniya ni Fa'iza babu abunda ya sauya gareni daga zuciyar,Ishaq a kaina na wahala wajen Haihuwa kamar bazan rayu ba sannan Amir yazo duniya wanda yaci sunan Baban katsina Kabir,lokacin da na Haihu Anty Binta na asibiti ana kawo musu abunda na haifa ta duba kunnensa ta Kira mama tace"Mama sai hakuri Dangin tsiya yaron ya Debo"
Nayi kuka sosai da wannan kalmar sai dai a kallah na samu wanda zai san zafina wani abu daya fito daga Tsatso na wanda kila shi zai kaunace batare da ya Duba yanayin Halitta na ba ko nakasun jina ba,An kai ruwa Rana kafin Ya Ishaq da su Mama su amince Goggo ta tafi dani karofi nayi jego shima sai da Baba ya saka baki,sannan ya amince a cewarsa wai Goggo sai tayi ta nuna yana zalunta ta na sannan baya so naje na had'u da su Yaya mariya wai ana zaginsa mganganu dai haka yayi ta yi kan yan'uwana da iyayena bani da tacewa.
Sai da na koma karofi sannan Tamadina tazo ta ganni ta rike Amir gam a Hannunta kafin ta mikamin shi ta dafa kaina kawai tayi miirmishi na kalleta sai naji kuka duk ta lalace ta rame ta kara tsufa kamar ba ita ba,Bazan taba mantawa da Goggon Karofi ba domin ita ta kula dani ba,da kila sai da na Rub'e ni kadai ban san komai ba.
Ina yin arba'in ba Dadewa Goggo Karofi ta maidani gidana Ni da Amir mun yi bulbul duka duka sau biyu Ya ishaq yaje ya ganmu kamar Amir din ba D'ansa ba ne,Goggon Karofi da yan'uwana sun yi kokarin wajen gyarani ni kam ban ce musu komai ba, to ina zan fada musu sau daya tak Ya Ishaq ya taba hada jiki dani Rabon Amir ne..?
To kamar na Amir itama haka Rabon Saudatu(Anum) ya had'amu shima duka Duka Haduwar bai wuce sau uku ba ma na samu ciki Amir nada wata Goma sha hudu wannan karon Ishaq yafadamin sai dai a zubar da cikin ni kuma nace ban amince ba Karo na Farko da na taba kai karas gaban Baba Dalilim da yasa Baba Ya mari Ya Ishaq ya kuma nunasa da yatsa yace"Kada na kara jin wannan mganar a bakin ka..kasan baka son cikin ka yi sa..?
Ka kiyayi ranar da Fa'iza da ya'yanta zasu zame maka inuwa wacce zaka iya rab'ar ta ina jiye maka watan watarana kada kayi nadamar abunda ka aikata"
Wannan marin ya jamin abubuwa Dadama tsakani da Ya Ishaq,kamar ni na bama kaina cikin Dalilin Baba yasa Saudatu tazo duniya(Anum),Da kulawarsa na haifeta Lafiya ita ma kamar Amir ne Baka ce irina,Basu da yadda zasu yi su sauya wannan kaddaran tunda haka Allah ya Tsara Mama ta tsane ni ammh ta kasa Tsanar jokokinta Amir ma ita ta karbesa ta yayesa sai wahalan tamin Sauki,Goggon Karofi Sati daya tamin ta koma ni na mike na Rika kula da kaina har nayi arba'in din Anum.
Ya Ishaq baya barina fita ko'ina Sai gidan Mama ko gidan Anty Binta Su kuma har naje na Dawo bana samun kallon arziki,Karofi kuwa Tun da nayi jego ban kara komawa ba Har Haihuwa Ya mariya tayi ya Ishaq yace gulma zai kaini bazani ba.
Gidan Yaya Asiya kuwa tun bayan auranta kafata bai kara taka kano ba,Ya Ishaq ya rabani da kowa ciki har da mahaifiyata domin har Haihuwa tayi yaron bai zo da rai ba bai barni naje ba wai zan kwaso ma Anum Sanyi Baya sona ammh kuma yana kaunar ya'yan sosai yake kula dasu kamar yadda yake kula da kansa.
Anum na da wata Hudu watarana Baba ya fara rashin Lafiya anje asibiti an yi gwaje gwaje sai aka gano Hantarsa ce ta tabu ba'a sani ba,Ya kwanta asibiti yafi sau hudu duk Hankalin su Mama ya tashi ni kaina Hankalina baya kwance domin Baba shi kad'ai ne ya ragemin Saura gata na,Kwanciyarsa asibiti na Karshe an sallamosa Da ya ishaq zai fita yace na shirya naje na Dubasa Amir daman yana chan tun yaye bai Dawo ba.
Naje na dubasa yana kwance ne yana ganina sai da ya mike,Ya miko min Hannu na Kwanto Anum daga baya na mika masa ita yana ta mata wasa Baba yayi ta min Nasihan hakuri da kuma Umrtana da na zauna nayi Biyayyan aure zan rabauta Ranar gobe kiyama..
Ashe wasiyya yake barin mu yace na kula da ya'yana na basu tarbiya kada na Biye ma Ishaq,nayi hakuri dashi Sannan na kara hakuri da su Mama watarana dani da ya"yana duk sai mun zame musu Inuwar Rab'a,na dawo gida da Tunanin mganganun Baba ashe bazai kwana ba adaran Allah ya Dauki ransa.
Alokacin mutuwar Baba na kara yarda Tabbas ban da sa'a domin duka wada'nda nake gani agata na sun kare bani da kowa anan duniya da zan kallah nace Gata na ne duka sun tafi Na tabbata ko Mama bata kaini kukan mutuwan Baba,na fade lokaci d'aya nayi zuru zuru tabbas Mutuwar Baba ya sanyaya ma Ishaq zuciya sannan ya sa ya rage wasu abubuwan.
Rasuwar Baba ba'a rufe shekara ba Ya ishaq ya samu karin girma zuwa Abuja,chan ya koma aiki sai bayan Sati biyu yake zuwa katsina sai nauyin su Mama da su Jamal duk ya koma wuyansa abubuwa duk suka Tabarbare daman karfin zumumcin Baba ne to yana Rasuwa sai ahankali Hajiyar Dala ta matse kanta gefe itama Goggon Karofi sai ta kama kanta itama Daman basa shiri da Da Mama sai ta Dade bata zo katsina ba ba ita kadai ba Saboda Sanin Halin Ya Ishaq yasa ba mai son Rabata abu kadan yace munafunci ake yi shiyasa Dole dai su Mama ne bani da kowa a garin katsina sai su da ya'yana.
Samun karin girman Ya Ishaq yasa sai ya samu rufn asiri fiye da baya ya gyara ma Mama gida ya koma Fasalin na zamani shi kuma ya siya Fili ya fara gini a Anguwan layout,Jamal kuma ya shiga jami'a sai Badariya da ta zama yammata yanzu sai ni da ya'yansa wanda Darajan su yasa yake Ragamin shima ba wai don ya daina Tozartani ba ne A'a har yau har gobe ni Fa"iza ba kowa bace a wajen Ishaq kabir Karofi
Cikin mustapha ko ni bansan ina da shi ba sai da yakai wata Biyar Mama data ganni da ciki ta Dinga bala'in na zama kamar beran masar bani da aiki sai Haihuwa ta manta ba ni kad'ai nake samar da cikin ba har da Gudumuwar D'anta ammh bata ganin Laifinsa sai nawa,Na haifi Mustapah ba Dadewa muka tare a sabon gidan da Yaya Ishaq ya gina katon gida mai shashe biyu,Shashen farko mai 3Bedroom da Falo sai kichen,Nawa daya sai na yara sai guda d'aya na baki,Ya ishaq shi ya Zuba Sabbin kaya agidan komai bamu Dawo da Tsoho ba, Mama ta kwashe su ta kyautar ni ko da har nayi Tunanin na aika ma Tamadina da su Dakinta Sai leda ba kujeru ganin Mama tace akwai wacce zata bamawa ban yi mgana ba, Sanin Halinta.
Haihuwar Mustapah yazo da Budi sosai Ya Ishaq har motar hawa ya mllaka ya siya mama nata,Budi ta ko'ona sai hamdala da Godiya yana Dinkamin suturu daidai gwargwardo sai dai na yaransa Dabam suke,Ni wani Lokacin ko yayi niyar yimin Rantsatsun kaya sai kalaman Mama su Dishe niyyarsa tunda tasha fadin siyamin kaya na alfarma barnan kudi ne, Tunda ba kyau zasu yi min ba sannan bansan yadda ma ake gayun ba kuma gaskiya suka fada ba karya sukayi ba ban san komai na gayu ba.
Ni dai iyakata nayi wanka na shafa mai na saka kaya,Abaya telan su mama ke min dinki Mama ta koma ba wata mace saboda sai nace yana kamani ni kuma bana so kaya su kamani na fison a shatamin na rika yawo aciki,ya Mariya ko Ya Asiya ko da wani Lokaci suna kokarin gyarani ni ko bana jin su gani nake yi gyara da gayu na wajen mata masu kyau da gata ban da ni da bani da ko  d'aya daga ciki Dalilin dayasa Ya Ishaq yake Biye ma Mama kenan in ta fadi mgana hakan take indai a kaina ne ballatana ba ran Baba ita ke tafiyar da komai.
Mama ta bada shawaran nayi Tsarin iyali sai dai bai karbeni ba wannan yar ashanan aka sakamin ya sakarmin jini Dole aka ciremin ana ko Ciremin ko wata Biyar ban yi ba na Samu Cikin Ahmad,na haife su kusa da kusa domin a shekara ta takwas da auran mu da Ya Ishaq duka na Haifesu haihuwan gwarne na rika yi don ma Allah yasa ina da jarumta daukan duka kwarmiyan yaran
Cikin ikon Allah cikin ya'yana ba wanda ya Dauko Lalurata sai na godema Allah Ammh wani ikon Allah susan Lalurata barin ma Anum da Amir susan bana ji sosai in zasu yi min mgana sai sun daga muryansu.
Allah ya bani yara masu kirniya,musty Da Amun basa jin mgana komai suka gani sai sun taba abunga ga wanda bai da karfin ji ina chan ina aiki su kuma suna Falo suna barna bana sani kuma Duk abunda suka Lalata sai Ya Ishaq ya dora komai akaina,Shiyasa ya dinga masifan na bari duk sun bata gidan sun bata kayan kallo sun bata in ji min wanki kuma Mama sai tace bazai kara siya ba, a kyaleni na wahala ai da gangan na bari suka bata komai.
Ni kuma bana cewa komai,Saboda bani da wani zabi,Har zuwa yanzu da girma ya kamani da ya'yana ban daina samun tozarcin Wajen Mama da Anty binta ba tun ba'a sani ba har kowa ya sani,Goggo karofi dai hakuri take bani,in ta kirani a waya sai dai fa ta wayan ammh Sai na shekara kafata bata taka Karofi ba Tunda nayi aure Sau Daya naje naga Tamadina Shima Haihuwan Mustapah ne da naje karofi da Ya Ishaq yaji Labari masifa ya farayi wai baya son ya'yansa suna zuwa gidan wasu suna Rabe rabe.
Haka nan nake daga ni sai ya'yana sai Danginsa alhalin yasan bana jin Dadin su ammh ni nawa yan'uwan sai dai zumunci ta waya ya rabani da kowa nawa.Hafsatu ce kawai tana ta da Kulafucin yan'uwana bai da yarda zai yi da ita in sun samu Hutu tana zuwa ta zauna dani hakan sai yasa na Shaku da ita fiye da su Yaya Asiya.
Nasan Tabbas Ya Ishaq zai kara aure watarana ban daukesa alokacin da najisa ba Nima abakin Anty Binta na farajin mganar auran sannan Mama ta Fadamin nasan bani da wata Daraja a wajen ya Ishaq ammh na Dauka zan ci albarkacin ya'ya ashe bani da wannan alfarman na Kunshi Bakinciki Tundaga ranar farko da na wayi gari agidan Ya Ishaq a matsayin matarsa,Na kunshi takaici a matsayina na Uwar ya'yansa na fuskanci Tozarci a matsayina na kanwarsa tun a baya to wani tozarci ne ni Fa'iza da ya rage ban gani ba..?
Nayi Rayuwar aure shekaru Takwas da wani abu ammh Daidai da Rana d'aya ban Taba Danda'na yadda Dadin aure yake ba na dai yi shekaru Takwas ina Sanin yaya matsayin Tozarci da Gori yake sannan na kara zama Guilt akan kushen Hallita da kuma aibata Nakasa ta nayi rayuwa cikin Guilt din jin ban da sa'a na rayu cikin Guilt din Sannin ni bani da gata na zauna cikin Tunanin Mata ire ire na basu dace da suyi Farinciki ba.
Basu chanchanci miji mai kirki ba, basu chanchanci samun soyayyar ko wani Namiji ba,Sannan basu chanchanci Rayuwar Farimciki ba.
Mata ire irena Rayuwar kaskanci da Torzarci da Bauta  ya dace damu,Ba kokarin mu goga kafad'a da kafad'a da mata masu kyau da gata ba shi yasa na Rayu cikin Tunanin kayan alfarma da shigar alfaarma da Kwalliya  basu dace da ni ba, sun fi dacewa da mata masu kyau da Nagarta kamar yadda Ya Ishaq da mama ko Anty Binta ke yawan fadi akaina.
Tabbas na aminta da duka zencen su da Tunaninsu"

*Littafin KANA NAKA book 1 free ne book 2,3 paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*


*Janafty*[6/12, 12:11 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*

_*Barka da Zagayowar Ranar Haihuwa HAFSAT MUSTAPHA HAFNAN(SAHIBATU),Madallake da ke,Allah ya karo shekaru masu albarka Happy birthday*_

*Assalamualaikum! Phydoors* *collection (home of all you need)tazo muku da kayan gyaran girki masu inganci da Gina jiki da faranta Ran Mai gida harda Ma yaranmu domin inganta girkin uwargida Kai harma da amarya tazo muku da egusi,* *crayfish ,manja ogbono dadai sauransu Zaku iya tuntubar ta wannan nomber 08062181151 ko Kuma shafinmu na yanar gizo https://instagram.com/phydoors_collection?igshid=MzNlNGNkZWQ4Mg==Muna aikawa ko Wani gari da iKon Allah,ko gwada kayanmu da iKon Allah sai Kun dawo* 🥰🤗

       *🅿️04*

Sai kuma girken girken zamani da na gargajiya da na koya a iya zamana agidan mama shima ba wai ita ta koyamin ba,Ni na koya da kaina Saboda ina da karambani Mama bata taba Damuwa dani ba tsakani na da ita sai Harara da hantara,tana ganina a matsayin wata aba mara gata da galishu wuya ce da wahala yasa tun ban iya komai ba har na koya.
Na yarda ina da nakasun rashin ji ammh bani da nakasun wani abun Hallita ajikina ina da rai na da lafiyata to zan yin komai,Na iya wasu girken girken a tashar arewa24 na shirin su Akushi da Rufi wani Lokacin Tibin ita kad'ai afalo tayi ta babatu in nagama aikina sai na Lallabo nazo na zauna Duk da bana jin yadda suke koyar da girken girken ina bin yanayin yadda suke Hada komai ina ganewa.
Sannan da kuma Anty Mamah babbar Diyar mijin  Anty Binta ce mahaifiyarta ta rasu ne dalilin da yasa ma ya auri Anty Binta kenan.
Tana aure acikin asibitin Kashi wato Othorpedic na katsina mijinta Likita ne tana da Yan biyu wato Twins,Mama na yawan Tura ni gidanta Saboda reno Yaran nata duka mazane Hassan da Husaini masu Rigima ne Anty Mahma ba kamar Anty Binta take ba,bata da mugunta  sai dai akwai saka aiki,Kuma tana da kyauta sannan bata kyamatata ko tayi min fada, in naje gidanta kamar jaka har gwara ma gidan mama ina Hutawa sai dai ita bambamcin su bana girki da kaina ita da kanta take shiga kitchen tayi abunta ammh nakan shiga na taimaka mata da yanke yanke da miko miko to da haka nake zura ido ina Fahimtar wasu abubuwan nasan bani da gatan da zan yi karatu ko ina dashi ina jin tsoro zuwa makaranta saboda kada akusheni ko ayi ma Nakasuna Dariya shiyasa na kan kasa ido da raunannun kunnuwana ina duba wasu abubuwan da jin wasu abubuwan iya abunda zan iya ji na kuma d'auka.
Sannan agidan Anty Binta ma na koya su Snaks saboda Diyar Anty Binta ta farko mai suna Halisa zamu iya zama tsaran juna tunda Anty binta tayi aure tana da kananun shekaru alokacin to ita ke sana'ar yin Snaks in naje gidan nakan kasa idanuwana ina lura da abubuwan da take yi a hakan na nake daukan wasu abubuwan.
Da yake ita Halisa tana da bambamci da su ba kasafai take nuna kyama gareni ba sai dai bata shigemin sau tari nakan taya ta aikin Snaks din ta in an kawo mata dayake sana'arta ne tayi suna tunda tana amfani da Social media alokacin.
Tun ina da shekaru goma sha Hudu a duniya jikina ya gogu da aiki babu aikin da zai gagareni komai yawansa agidan Mama tun karfe Hudu nake tashi Daga barci naje kitchen na kintsa Sannan na Dora abun kari sai naje na tada Badariya bayan na saka mata Heater na wanka Saboda zuwa makaranta Domin dokar da Mama ta kwafanin kafin bakwai na Safe na gama komai kada ta fito bata iske abinci a saman dining ba,ko kuma taji kafafunta na taka Datti acikin Falonta Shiyasa ina yin abun kari wani Lokacin ina Share sharen dakuna hatta Dakin Jamal ni nake gyaramai in suka tafi makaramta Saukin ta ma shi bai cika mgana ba barshi da waya a Hannunsa irin su ba kasafai ake gane inda suka dosa ba.
Ya ishaq kuma baya gida sai an yi Hutu yake zuwa yana ABU Zaria inda yake Masters di'nsa nima abakin Anty Binta naji sunan karatun nasa har na iya rikewa,Hatta da kayan Jamal da na Badariya da na Mama ni nake wankewa ammh Baba bai sani ba Saboda yasan duk wata baya fashin bada kudin mai wanki da guga Tunda Mama ta sameni take soke yan kud'ade'nta,in wankin ya taru tun safe in naje baya na fara sai yammah watarana ma bana ko samin zuwa islamiya,Washegari kuma Baba na fita zan dasa guga har sai bayana ya kage ba ci ba sha sai na gama in kuma nace zan tashi ko sallah in yi sai Mama ta kai min duka tana Fadin"Me kika sani a karatun sallar..?Ni fa jin baban su kawai nake in yana Fadin kina da ilimin addini  ke da kike Bebiya gaki ba kyau ba fasalin y'a mace ai bautar da ta dace da irin ku kenan.."
In ta fadi haka bana damuwa sai naga gaskiya ta fada domin na fahimci in baka da kyau ko Asali da gata ko kana da wani nakasun Hallita baka da wani amfani Domin wad'anda suka fi kusanci dakai sune suka fi kowa kyamatarka to inaga na waje wad'anda basu san ka ba, mu'alama ce zata hadaku..?
Ina tuna Lokacin muna Malumfashi Iyayena sun san ina da Lalura ammh ko sau daya basu taba nuna gazawar su ba sun min dukkan gata a malumfashi makarantan da aka kaini ina gane karatu tunda ana yimin yadda zan gane sannan bamai kyamatata Saboda ina da gata alokacin ammh daga Lokacin da gata na ya kare sai nima nake fama da guilt din shiga cikin Mutane ina ganin ban kai ko wani matsayi ba sannan na aminta da mganar Mama iri iren mata irina Bautace ta Dace damu..
Shiyasa duk wahalan da nike sha bana Damuwa ina ganin ahakan ma ni kila nafi wasu ma ire irena,Baba duk baya sanin wasu abubuwan tun da in ya fita tun Safe sai Dare,in kuma ya Dawo yayi sallah yaci abinci zai kirani falo yayi  ta kokarin na bayyana mai abunda nake bukata ko nake so ammh bana iya mgana Saboda Mama ina bala'in jin tsoronta kamar wata mala'ikar Mutuwa.
Baban katsina irin mazan nan ne marasa Bibiyan al'umuran gidansu shiyasa Mama ta samu dama tana Damawarta,Komai na Cefane Mama yake bamawa,Duk watan Duniya ita kuma sai ta samu nata aciki Mama tasan kan kasuwanci,Tana saida dikkakun kayan mata da maza anan ake dinka mata tana aika ma yan'uwanta dake yamai suna Siyar mata kuma har anan tana samun ciniki sosai tana harka da manyan mata bayan dikakku har Tamfofi da Lesuna tana saidawa da takalma Shiyasa take da tarin kawaye da Mutanen arziki da ke shiga suna Fita agidan,Shiyasa ko Sutura ita Baba ke bama kudin ko na Mutanen karofi ne kuma baya Bibiya,Shiyasa sai wanda taga dama ta bawa,ba kuma wanda ya isa yayi mgana duk sallah har da su Yaya Asiya Baban katsina ke yi ma Dinki adadin yadda yayi ma Badariya dani ammh ni ko Sabo daya Mama bata bani na saka sai tace Mace irina da kwance ta dace ni kuma sai mganarta ta zaunamin kayan alfarma masu kyau sai ajikin kyawawan mata wad'anda basu da wani nakasu Mata kuma irina da kwance muka Dace yawancin kayan yaran kawayen Mama nake sakawa Domin na badariya bazai min ba Na girmeta sosai alokacin,Su Yaya Asiya kuwa Kala dai'dai take jifan su dashi Yaya mariya bata da matsala ita da Hafsatu Goggo macece mai Tsayawa akanta ita da iyalanta Yaya Asiya kuma tace duk mugunta Hajiyar Dala tana barinta da Suturu Saboda ita yar gayu ce sannan mijinta Soja ne ya'yanta fes suke itama haka saboda haka Itama Yaya Asiya badai a ganta da kama mara kyau ba.
Ni dai ko da yaushe cikin Tsumma da Ragga In Baba ya gani yayi mgana Mama ta lawayance zance ni kuma bana iya karyatata agabansa,bazan taba mantawa da wata sallah ba,Sallah da na fara yinta a gidan Baban katsina Lokacin na kwashe wajen wata Tara a katsina,kuma tunda nazo ko Karofi kafata bata kara takawa ba Ga Hajiya na raina in Baba zai tafi gaisheta sai naji kamar na bisa,tunda duk karshen wata yake zuwa wani Lokacin shi da Mama suke zuwa wani lokacin shi kadai da Direba ko shi da Jamal.
Hajiya na rai na ita da su Yaya Asiya musamman Hasfatu kewar Tamadina kuwa har na cire sa araina tunda ba samun ganinta zan yi ba Tun bayan dawowata Ko mutum daya Daga karofi bai leko mu ba na dai ga Hajiyar Dala da suka taba zuwa Bikin Dangin mijinta ta sauka anan kawaye ne ita da Mama sai muguntar su tazo daya sai dai ita tafi mama ji da kai da nuna ita din watace.
Sallar azumi ne Dama da azumi duk na Rame na kara lalacewa,Ni bansan gayu ba, bansan komai mai kyau ba ni na dauka abu mai kyau a wajen mata masu kyau ake samun sa,Wani Riga da Sikat na saka cikin kwancen kayan ya'yan kawayen Da mama ke bani ne wuyan zamemin yake haka ma Sikat din yayi min yawa sai da na saka Tsumma na Taresa ajikina Hijabi ne kadai Sabo Shima Anty Mahma ce ta dinkamin domin jiya gidanta na wuni na tayata soyan Nama da aikin cinci Sai Dare ita da mijinta suka maidoni gida ita ta na da kyauta in nayi mata wahala tana min alheri takalmin kafata na Roba ne shima din Na jamal ne da ya daina amfani da shi na Dauka
Da farko Mama bata so aje dani Sallar idi ba,Sai Baba yace dani za'a tafi Ya Ishaq ya dawo agida yayi azuminsa Shi na lura kamar baya ma san kallo na shiyasa ban cika giftawa ta gabansa ba.
Lokacin da na fito Kofar gida Baba ya ganni sai da yaji kwallah ta cikamai ido,Ya kalli Badariya ta kure adaka ita da Mama,Jamal da Ya ishaq sun ci Fararan Shaddodi sai Faman sheke suke ni kuma bazar bazar kamar mahaukaciya wata yar aikin ma tafini kyan gani ni kuwa bakina kamar zai Tsage Saboda murna zan fita masallaci naga jama'a Tun kafin Baba yayi mgana Mama ta rigasa da fadin"Ke Fa'iza meyasa kika saka wadanan kayan..? Ina naki irin na Badariya..?
Sai na kasa mgana Saboda ni dai bansan da wani kaya ba,ba'a bani ba ganin Baba ya saussauto yana kallonta yasa ta kara karya murya tana Fadim"Bansan meke damun Yarinyar nan  ba Abban Ishaq ko da yaushe bata da aiki sai saka Tsumman kaya nama ce ta hada su in zaka Karofi ka tafi da su arabama mabukata"
Ban yi mamakin kalaman Mama ba Domin tun zuwana gidan ba Dadewa,Ta daina Fada da Baba akaina sai ta koma aiki da Kissa shima shawaran wata kanwartace daga Yamai hure ita tace mata in tana so taci Ribar Rayuwa to ta daina tada Hankali ta yi amfani da kiss,kuma Tabbas kissanta tana Tasiri wajen Baba don nan take ya kalleni kafin yace"Haba Fa'iza ya zaki saka wadanan kaya..? Baki ga sauran yan'uwanki ba ne.?maza je ki sauya kaya mu tafi kada mu makara'"
Da Sauri Mama tace"Zamu bata Lokaci Alhaji muje in mun dawo sai ta sauya"
Sanin Halinsa na rashin bincike kan al'umura yasa tace haka,Haka muka tafi su kamar zara cikin wata ni kuma kamar yar aikin su Shikenan ko da muka Dawo Baba yayi baki yana falon waje har Dare bai kara bi ta kaina ba,Sai da Washegarin Sallah da kwana Biyu mukaje Karofi ranar dai Mama ta bani Sabon kaya na saka ta kuma ja kunnena in taji wata mgana sai na Raina kaina ni ko araina nace wazan gayamawa.?bata san ina da zurfin ciki ba ba tun yau ba,bakomai ake jinsa bakina ba.
Duk da Sabon kayane ammh da na sanya kamar wata Dussa komai ba Tsari ni kaina nasan ba kyakyawa bace ban mallaki komai na mata masu sa'a da gata ba,Kusan daman Hausawa kan ce in kana da kyau ka kara da wanka to ni bani da kyau din sannan ban iya wankan ba ballatana na kara dashi,Wani Lokacin sai Dare nake samun Damar yin wankan Tunda Dakin da nake ciki akwai karamin Tiolet to iya wankan ne ko shi ba don kyau nake yi ba Komai bazar bazar ne bansan iyakarsa ba.
Da mukaje karofi na hadu da su Ya Asiya har sai da sukace har baki na kara na rame sun yi tambayan Duniyan nan kan wani irin rayuwa nake yi agidan Baban katsina naki ce musu komai sai dai in kallesu ina mirmishi naji dadin ganinsu haka barin ma Hafsatu da ta zama kamar ba ita ba ta kara wayau da girma.
Ina jin su a tsakaninsu suna tattauna yadda Rayuwa ta jefa su a inda suke ni dai bana ce musu komai nadai san na Tambayesu tamadina suka fadamin tana Lafiya Yaya mariya na zuwa Dubata ita da Goggon Karofi sukace In Baba ya barni gobe sai muje na ganta.
Ganin Goggon Korofi yasa Mama batayi mgana ba,Baba kuma ya amince washegari chan muka wuni sai yammah muka dawo ita kanta Tamadina ta na cikin wahala gida cike da yara,wahalar tayi mata yawa sai dai ba yadda zatayi ne kwanan mu biyu muka koma Katsina,Na koma da Tausayin Hajiyar Karofi ganin jikinta duk ya kara rikicewa yanzu ma dayan barin shima ya Daina aiki Goggon Karofi da ya'yanta suna matukar kokari kan Hajiya.
Haka rayuwata ta cigaba da tafiya a gidan Baban katsina duk da irin azaban da nike sha achan ban taba jin na gaza ba sai ma nake ganin Sun yi min komai tunda zan ci na sha na kuma samu wajen barci Baba na jin Takaicin rashin Karatu na ko da yaushe naje gaishe shi da Safe sai ya kalleni yace min"Fa'iza kin k'i makaranta ko..?
Baki san ilimin zamani ginshiki ne ga rayuwar ya'mace ba..?
Ni kuma bana iya mgana sai dai na Dukar da kaina cikin Tausasawarsa yake cigaba da Fadin"Da kin Daure Fa'iza ai kina jin mgana zaki gane komai sannan zan yi ma malaman ku bayani kamar yadda nayi ma malamanki na islamiya bayanin Laluran ki"
Ina Dagowa muka Hada ido da Mama ta Sakar min harara sai jikina ya fara rawa cikin yanayin mgana ta nace"Baba shi na addinin ba Ilimi ba ne..?
Sannan shi ba Ginshiki ba ne ga rayuwar mu ba..?
Baba ya jinjina mganata kafin yace"Ginshiki ne Fa'iza babban ginshiki ba kuwa..Sai dai ka hada duka fufukan guda biyu sai ka samu na zaman duniya da Lahira"
Alokacin sai nace ma Baba"Baba ka barni haka..na islamiyan kadai ya isheni"
Zai matsamin sai Mama ta taresa tana nuna mai Tunda ban so to ya kyaleni,Shi kuma bai da Zafi sai ya Rabu dani ammh ko da yaushe kalamansa akaina na alheri ne har ya bar duniya ko kallona yayi sai yace"Fa'iza Allah yayi miki albarka In sha Allahi bazaki Taggyara ba..Ina ji ajikina kina da wata baiwar da Sanadinta zaki Daukaka watarana"
In naji haka sai nayi Dariya araina Domin bana hango ma kaina hakan
Na amince Baban Katsina ya karbo ni Hannun Goggo karofi ne domin ya inganta Rayuwa ta,sai dai bashi da Mafita ne Mama ta fi karfinsa ammh har yau bazan manta kokarinsa akaina ba.
Shi ya fadama malaman islamiyan da nake zuwa yanayina suke bani kyakyawan horo ko an gama karatu gabadaya sai an kara min bita ni kadai,Bani da wata kawa shiyasa ni kadai nake zama iyakata da kowa Mirmishi ko Sannu nasan ana mgamata ammh da yake bana ma ji Sosai ban cika Damuwa da su ba.
A farkon zuwa na gidan Mama cikin kasuwar katsina take zuwa siyayyarta ammh sai Kawarta Hajiya Barira irin masu son kudin nan ne ita ta bata shawaran ta rika zuwa kano kwantin kwari tana saro kaya alokacin Mama sai tace"Kai Barira ya yi nisa ni kinsan ban san wahala"
Hajiya barira ta rika nuna mata yanayin komai tare da fadin nachan sun fi sauki sannan zata hadata da yan kasuwar chan tunda itama tana siyayya achan har sai da Maama ta amince bazan manta ba na zo kawo ma Hajiya Barira abinci na juya naji tana ce ma Mama"ko wannan bakar yarinyar kika tara sai kuje tare ta rika Daukan miki kaya"
Mama ta kalleta kafin tace"Ko Hajiya barira"?
Tace to zauna Daman meye amfanin irin su in ba aikin wahala ba.
Da wannan shawaran Mama ta zauna tana fadama Baba ya amince tunda shi ba mutum ne mai Takura ga iyalansa ba.kuma da tace dani zata bai yi gaddama ba domin nuna mai tayi ina kokari zata nuna min komai Domin tana Tunanin nan gaba ko ban yi karatu ba zan yi kasuwanci to ai Daman haka take fadamai ko na wahalan da nake yi ne,Girki ma Baba yace nayi kankanta Mama tayi Karaf tace gwara na koya Saboda gaba gidan wani zani Daganan Baba bai kara mgana ba.
Daman tun anan ni nake kaimata Dinki chan batagwara kusa da gidan Anty binta,in ba'a gama ba sai na zauna an gama Wani Lokaci anan nake wuni buhu ne shake da kaya zam Dauko akai zuwa bakin Titi na samu Daidaita sannan in na Dawo na Hau ware ma masu kayan nasu,wad'anda za'a tafi da su yamai kuma duk ni ke shirya su Mama na gefe tana lissafin komai ban isa nace nagaji ba.
Ranar da muka fara zuwa kano sai da na raina kaina Wuni guda acikin kasuwa kuma bata Dauki dan dako ba ni ke daukan mata kaya akai kamar mahaukaciya ga yunwa ga kishi Takalmi a Hannu hijabi a hannu Wlh ko abinci bata siyamin ba Da muka Dawo sai da nayi rashin Lafiya Saboda na Jigata matuka alokacin Mama fada ta Dinga min akan na fara zama mai son jiki to in zam mike tun wuri gwara na mike Bani da wani amfani in ba Bauta ba.
Ni ba kyau ba,Ba ilimi ba,Ba ji ba,ba komai na inganci rayuwa ba,bai kamata na rika nuna gazawata ba tabbas gaskiya ta fada ba ni da wani gata a Duniya Bautar dai da ta Fada shine ya fi dacewa da mata marasa galihu ire irena
zuwa Lokacin da na shafe shekaru Shidda Cif a wajen Baban katsina bazan iya fadin irin bautar da nayi ba abu daya na sani ni Fa'iza ban sauya ba Sai dai na kara girma ammh ba Domin na sauya Daga yadda nake ba Ina nan a  mai raunannan ji,Mara gata baka Mummuna mara sa'an rayuwa in ji ya Ishaq in ya ganni yakan ce Bai taba ganin mace mara sa'a ba irina komai Total zero ne a bangarena ba wani abun so ko sha'awa tare dani nima nasan haka ko badariya dake tasowa mai kyau ce sannan yar gayu kuma yar gata ni kuwa ban ma san me ake kira da gayun ba,Ni dai kawai nayi wanka na suturta jikina mganar gyaran jiki da Tsaftan jiki ban san shi ba Ba kuma wanda ya ke zaunar dani ya koyamin Ko kitso sai ni nagaji da kaina na tsefe shi kitso kuma sai in Mama taga dama zata bani kudi naje,ayi min.
Zuwa Lokacin rayuwa ta Daga,Sosai ba kamar baya ba,kawayen Mama da suka sani tun abaya in suka gani sai like sai suka rika ce ma Mama Daman wannan mummunar dangin mijin naki na nan baki aurar da ita ba.?
Mama kan basu amsa da cewa wazai kwashi Baki da muni da bebanci sannan uwa uba ba ilimi sai su yi ta Dariya suna cema Mama shikenan ta samu yar aiki to ai daman ba marabata da mai aiki maraban mu daya in da Daukoni akayi da sunan aiki za'a  rika biyana albashi,Shine kawai bambamcina da mai aiki acikin wannan gidan.
Su Yaya Asiya duk sun yi aure ita da Yaya Mariya Ya Asiya acikin garin kano tayi aure wani malamin makaranta ne yana da mata da yara,Mai karamin karfi ita kuma Yaya Mariya A karofi tayi aurenta wani dan kasuwa ta aura mai rufin asiri.
Kusan tare akayi Bikin su sai dai na Ya Asiya aka fara yi ,Duka naje bikin su ammh na Ya Asiya sai da Goggon Karofi ta kira Baba ta mai mgana domin tasan Halin Mama munje kano mun yi kwanaki Tunda Bikin tare da manyan ya'yan Hajiyar Dala babansu ya Hada, da Asiya harta duka kudin siyayyan kayan Daki tare ya bada ammh Mama ta zuga Hajiyar Dala akan su ya'yanta suna da gata Asiya kuma ayi mata na Daidai da ita Daga karshe ma ita taci kudin domin duka Dawaniyar Yaya Asiya Baban katsina yayi mata shi,Duk ciki ita kadai ta auri mai karamin karfi gidan falo daya ne sai Dakuma nata da na uwargidan Ba Shakka Baba yayi mata kokari sosai,Bangaran Yaya mariya Goggo da Mijinta sukayi komai ita gidanta ita kadai wannan bikin ne har Tamadina tazo,na Yaya Asiya ne bata je ba, in naga yadda Rayuwar Mahaifiyarmu ta koma sai na kara tabbatarwa lalle bamu da gata gatanmu ya fadi tun Lokacin Rasuwar Baba.
Da ace Hajiyar Karofi na Da lafiyanta da kila abubuwa sun sauya ammh kuma tana kwance sai dai a kwantar a tayar bama wanda ya zata kai haka araye,ana zuwa gida ana Dubata har yau tana nan jiya iyau bata ko mgana Sai wanda ya kara kunnensa yake ji me take fadi in naje Hajiya ta rika kallona kenan na rike hannunta ina Fadin"Allah zai baki lafiya Hajiya"
Sai dai kaga Hawaye na Bin gefen fuskarta Hajiya na bani Tausayi sosai shekaru kusan bakwai tana jinya tana kwance waje daya,Gidan su na karofi Babban Yaron Goggo Yaya Isa ya gyara da yayi aure yake zaune da matarsa kada abar gidan ba kowa ya mutu Baba ya matsa sai ya zauna da Farko Goggon Karofi bata so hakan ba gudun Rigiman zumunci.
  Ya Ishaq ya dawo gida ya gama karatu har ya samu aiki a Hukumar Tattara Haraji na kasa reshen jahar katsina,Shekaru uku da suka gabata,Sai dai baya zaman gidan in ya fita tun safe sai dare in kuma ya Dawo yana Dakinsa na fada muku tun a baya shi baima son ganina shiyasa bamu cika Haduwa ba, bana zama inda nasan zai ganni Saboda yafi kowa iya kallon wulakanci da kaskanci.
Akwai watarana tana cikin cikin Ranakun da bazan manta da su ba acikin kaddarorina ba,Muna gabda Riskan kaddaran auren mu ni da Ya Ishaq al'amarin ya faru watarana ya kira Mama a waya yace yana son abincin Mutum hudu abokansa zasu zo su yi Dinner anan biki sukayi na wani abokin aikinsu.
Nan da nan Mama ta tasoni na shiga Kirchen daman na fada muku a bangaran girki ni Fa'iza bani da makusa,Harta Mama yanzu in ba girki na ba bata iya cin abinci,Shi ko Baba kullum Mama yake godemawa yana ganin ita ta tallafamin na iya girken girken zamani zuwa kuma Lokacin na rage wasu walwahalun,Saboda Mama ta daina aike na ta samu yaron aike bangaran kasuwancinta kuma komai ta waya ne sai dai a saka mata a mota a aiko mata dashi,sannan ta dauki masu wanki da guga da kuma mai wanke wanke na koma gyaran gida da girki.
Jin baki ya ishaq zai zo da su na Zage nayi musu girki mai rai da lafiya fatan pototo,da Hanta sai white rice da Miyar kifi,Sai nayi musu lemun Abarba Sai na hada musu da na Gwangwani kafin ya kariso Mama ta sani na je na shirya komai afalon Baba,na koma kitchen na Dora abincin dare na gida har bakin suka zo ni bansani ba Na gama girkin Dare doya da Miya Mama tace ayi naje nayi sallar mangariba ina zaune saman sallaya Jamal ya shigo Dakin da nake mai karamar katifa sai tarkace yace min Ya Ishaq na kirana afalon Baba sai da gabana ya fadi ban cire Hijabin jikina ba yamin yawa yana neman gadani na nufi Falon Baba
Ina shiga da sallama gabadaya zaratan mazan dake falon suka Dago suna kallona ni ban iya kallon su ba,Saboda yadda jikina ke kyarma,ina ji Ya Ishaq ya dakamin Tsawa yana Fadin in kariso,Ni dai nasan nazo gabansa na durkusa kaina na kasa ina ji yace musu"To ga wacce tayi girkin nan da kuka matsu ku ganta"
Ya fada cikin sigar Dariya da karfi yayi mganar yasa naji abunda yace gabadaya shuru sukayi kafin naji sun kaure da Dariya gabadayansu sai naji na muzanta matuka muzantan da ban taba yi ba suna ta mganganu wasu ina ji wasu kuma bana ji nadai ji sanda Ya Ishaq yace"Kai ka yi mata da Hausa No Turanci..Sannan Ears."
Gabadaya suka gwalalo ido kafin ya kalleni yace"Yes..sai kunyi mgana da karfi zata jiku Bebiya ce"
Na kusa dani ne ya matso saitin kunnena yana Fadin"What is your Name.?
Aoh Sorry ya sunanki..?
Na dago idanuwana sun cika da kwallah nace"Fa'iza"
Cikin yanayin mganata gabadaya sai suka sheke Da Dariya har suna Tafawa da junansu Sai naji na kara raina kaina Nasan ni ba bebiyace ba ce ina dai da Raunin ji ammh ba Kurma bace ni Mutane ne suka kara Raunana jina da kushe da Tsangwaman su akaina,Ninasan inaji sai dai sai an yi mgana da karfi Sannan mganata tana  da Tsami Tsami Kuma ina Rabe ta kamar ina in ina kuma saboda Raunin ji na ina karantar bakin mutum in yana mgana Ko Tamadina ba Kurma bace tana mgana sai dai mganata tafi nata fita sannan na fita karfin ji.
Ammh yadda suke kankanba Bebanci na abun bai kai haka ba.
Ban taba jin guilt irin wanda naji ba  Ranar hawaye suna bin fuskata na mike zan fita Ya Ishaq ya dakamin tsawa yana fadan sun sallameni ne..?sai na Dawo kawai na Durkusa ina jin Ya Ishaq na fadin bai taba ganin baki da muni ba sai a wajena su ma abokan irin sa ne suna ta Dariya na kamar sun ga abun dariya ajikina ko acikin Abunda suke ma Dariya aciki akwai wanda na bama kaina ba Allah ya bani ba? abun da nake sakawa araina kenan ina jin wani irin abu a kasan raina.
Sun dade suna kallona suna Dariya kafin Ya Ishaq yace na kauce daga gabansa na mike idona ya rufe bana ko gani,bansani ba na ture Teburin dake gaban su jug din lemu ya fado ya zube Lemun ya fallatsa a jikin abokan nasa dashi kanshi har ga Allah ban lura ba,ba karfi ji ne dani ba shiyasa ban ji karar faduwar wani abu ba,ba ma haka ba yanayin da nake ciki gabadaya ji na sa ganina ne suka Dauke a lokaci d'aya.
Na dai san kafata ta bigi wani abu ammh yanayin da nake ciki bai sa na Tsaya Dubawa ba.
Sai ji kawai nayi an dawo dani baya an yarfar dani akasa ya Ishaq ya Daga Hannu ya wankeni da mari acikin kalmominsa na tsinci kalmar"Banza Jaka,Mummuna useless har na isa na wulakanta abokansa ko akwai sa,a na acikin su ne..?
Ina dafe da kuncina na bisu da Kallo ya fadi gaskiya ba sa'a na acikin su kamar yadda yake kyakyawan gaye haka suke suma,jikina na rawa na fara bashi Hakuri sai yace sai na juya na basu hakuri haka na Durkushe ina basu Hakuri sai da sukace sun hakura ya bi ni da Hambari ina Rarrafe na bar Falon ranar kwana nayi ina kuka har na fara neman nayi Sabo sai na zauna nace meyasa Allah bai yo ni mai kyau kamar kowa ba..?
Ko dai da gasken ne bani da Sa'a..?
Washegari Da Mama taji Labari Allah ya kara tayi har da fadin da ya fada mata Tun jiya sai ta karamin da Duka.
Ina Falon ina goge goge ne alokacin naji sanda Jamal yace"Kai ma Bro meyasa ka kirata cikin abokan ka.?
Sai da yayi tsaki mai karfi kafin yace"Su suka matsa sai sun ga wacce tayi abincin"
Daganan ban ji meya ke fad'i daga karshe ba,Saboda ya Rage murya Ranar ina aiki ina kuka abaya bana Damuwa in an kusheni ammh yanzu sai naji kamar da gaske ne ni Fa'iza bani da Sa'a
  Ashe abunda Ya Ishaq bai sani ba Matarsa ya Tozarta,Agaban abokansa Domin ko sati ba'ayi ba Baba ya tafi Karofi Sakamakon kiran da Goggo tayi mai kan cewa jikin Hajiyar ya tashi Abun mamaki tana ta kiran sunan sa shi da Mama da ya Ishaq suka tafi suna chan ne nima ina gida Hankalina nakan Hajiya ban san me ya faru ba, ni dai nasan sun Dawo gidan cikin Hargitsi da Rashin kwanciyar Hankali mama sai kuka take yi tana Fadin bamai hada mata zuru'a da Dangin munana da kurame.
Washegari fada ita da Baba har Falo alokacin naji Baba yace"ko bayan Ransa sai auran Fa'iza da Ishaq ya kulli sai dai ta mutu"
Dayake da karfi yayi mganar naji sa ni kaina sai da na gigice ana haka sai ga Ya jamal yazo yana fadin Ya Ishaq ya kwashe kayansa ya bar gida Mama ta fadi kasa Hannunta akai tana kururuwam ta shiga uku ta Lalace
Haka Baba ya tsallake ya barta ban bari kowa ya ganni ba na koma Daki ina rawan jiki mai nake ji,Wai ni Ya Ishaq zai aura.?
Tirkashi ni kaina na hango tashin Hankali acikin lamarin ranar har Anty Binta tazo ita da Anty Mahma da kawayen Mama na kusa,sai mganganu suke ni,ni ina Daki baji nake yi sosai ba, ranar ko girkin ban iya yi ba kuma ba wanda ya nemeni.
Nima Badariya ta shigo take fadamin Wai Hajiyar Karofi tace a hada aurena da Ya Ishaq,ance Dakyar ma aka gane me take nufi Saboda Harshenta ya karye.
Ba Ya Ishaq kadai Hajiyar Karofi ta cuta ba  wlh har dani ina ni ina Ya Ishaq ai tazaran ma mai yawa ne.ranar kafin Baba ya Dawo Mama da su Anty Binta suka kirani Falo suka min Fata fata zagi da gori ba wanda ba su yi min ba har da gorin mu dangin maciya Amana ne to wanda ma naji kenan wanda kuma ban ji bansa me suka fada ba,Dayake da karfi suke mganar Anty Binta ko har tana Hadamin da dunguri Mama taci kuka har ta godema Allah idanuwanta sun kala sun yi jajir Ita damuwarta Ishaq ba bawanda yasan inda ya tafi ya kuma kashe duka wayoyinsa Mama taja kunnina da cewa in Baba ya Kirani ya tambaaye ni in na amsa mganar auran nan sai na gwammace rashin amsawata Domin bata fatan Had'a zuru'a dani Har gaban Abada.

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

*Littafin KANA NAKA paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*



*Janafty*
[6/12, 7:52 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

*Assalamualaikum! Phydoors* *collection (home of all you need)tazo muku da kayan gyaran girki masu inganci da Gina jiki da faranta Ran Mai gida harda Ma yaranmu domin inganta girkin uwargida Kai harma da amarya tazo muku da egusi,* *crayfish ,manja ogbono dadai sauransu Zaku iya tuntubar ta wannan nomber 08062181151 ko Kuma shafinmu na yanar gizo https://instagram.com/phydoors_collection?igshid=MzNlNGNkZWQ4Mg==Muna aikawa ko Wani gari da iKon Allah,ko gwada kayanmu da iKon Allah sai Kun dawo* 🥰🤗

      *🅿️05*

Lokacin da Baban katsina ya kirani Falonsa adaran da su Mama suka ja kunne ne ammh na kasa iya d'ago ido na kalli Baba ballatana nayi mai gaddama kan lamarin da yazo min dashi cikin wani yanayi na roko da Tausasawa Baba ya sanar dani Umarnin Hajiya na had'a aurena tsakani na da Ya Ishaq shi Uba ne gareni zai iya aurar dani ko da ban sani ba addini ya basa wannan damar ammh bai yi haka ba, sai ya zabi da  ya kirani yana Roko na na amince don ya samu damar da zai cika Muradin Hajiya..
Ina kallonsa da kumburarrun idanuwana da suka tasa saboda kuka Da damuwa Hawaye suna Biyo Fuska ta wasu na korar wasu Baba nake kallo wani Mutum da nake gani Da kima da Daraja mutumin da nake ganin shi Kad'ai ne ya ragemin gata na aduniya ta ya ya zan iya bude baki nayi mai gaddama.? Amsa masa kuma Daidai yake da Fadawa Ukuba kamar yadda Mama ta shaidamin ita da su Anty Binta..
Na bude baki da niyar nayi mgana kalmar
" Baba.."
Kad'ai ya iya fita a bakina sai kawai na saka ma Baba kuka shi kuma bai duba yanayi na ba ya shiga sakamin albarka da Fatan gamawa da Duniya Lafiya sai harshe na yayi nauyin da har Baba ya sallame ni na kasa Furta ko kalma d'aya ammh a kasan raina nasan wannan auran bai kamata ya tabbata ba Domin babu had'i ko gami acikin sa gabad'aya.
Ranar nasha kuka kamar raina zai fita Tun cikin Dare Mama da Baba suke Rigima da karfi suke mganar Shiyasa nake jiyo su sama sama Tunda Baba ya fita sallar asuba bai Dawo ba Mama ta rude ta shiga tashin Hankali Saboda rashin Sanin inda Ya Ishaq ya shiga Tunda yaji mganar auran mu
Ni dai ban san ya akayi ba ina kwance sai ji nayi an rufeni da duka kota ko'ina,ina kuka ina ihu ammh Mama bata Tausayamin ba kuka take yi tana Dukana fadi take yi"Dangin jaraba dangin masifa Saboda ke Abban Ishaq yace zai iya rabuwa dani...?Saboda ke Ishaq ya bar gida ban san ina ya shiga ba..? Kuma ahaka zan amince na hada Zuru'a dake..?wlh sai dai ki mutu ammh ni Saudatu bazan taba Hada zuru'ata da b'ara gurbi irin ki ba Shegiya ya'yan shegu dangin maciya amana Mummuna dake D'ana yafi karfin ki"
Da karfi take mgana shiyasa na ke jinta ina ta bata Hakuri bata jini ba Badariya na gefe tana kuka tana rokon Mama ta kyaleni ammh bata tanka ta ba Jamal kuwa yana Tsaye shima Fadi yake yi"Mama duka wayoyin ya Ishaq suna kashe ne sannan na kira abokan sa na kusa sun sanar dani bai zo ba kuma bai kira su ba..Gaskiya Baba shima bai yi Tunani ba Ta ina Ya Ishaq ya Dace da Fa'iza..?
Ina ji Mama ta wurgoni Falo tana Fadin"Ai yadda ta saka ya bar gidan nan nayi Rantsuwa bazan yi kaffara ba itama ta gama zama a wannan gidan yau ba sai gobe ba sai ta bar min gidana"
Da duka da gori da Tsinuwa Mama ta rakani waje ta maida kofa ta Rufe,Dagani sai rigar jikina ta atamfa sai dankwali shima tana Dukana na Rarumeshi na rike a hannuna kafata ba Takalmi Mama ta koreni nan na rakube jikin gidan ina ta kuka na Duba gabas da yammah kudu da arewa bani da wani gata a garin katsina kuma Mama Tunda tayi Rantsuwa to da gaske take Dankwalina na warware na yane kaina Dashi gidan Anty Mamah ya fadomin tana da Sauki Sauki kila ita zata iya taimakamin da kudin motan da zan koma karofi domin chan ne gata na anan duniya..
Da kafata Tun daga Kofar soro har Cikin asibitin kashi,A kafata ina tafe ina kuka kamar zararriya,ban gaji ba Domin halin da nike ciki gajiya bata da Muhalli a wajena Sai dai Anty Mahma ta ganni kwatsam kamar Daga sama tayi matukar kad'uwa da na zube ina bata labarin korar da Mama tayi min Kai ta girgiza kafin tace"Kai Mama meyasa bata bin abu a Hankali ne..?
Bari na kirata.."
Da Sauri na rike mata Hannu naji tana mgana ban ji me tace ba sai dai Yanayin mganarta da wayarta data Dauka sai Tunani na ya bani Mama zata kira ko Anty Binta ni kuma na shiga Tsaka mai wuya acikin wannan Halin Karofi nake son zuwa na Durkushe gaban Hajiya na Roketa ta janye wannan mganar in tana so na cigaba da Rayuwata yadda Allah ya Tsaramin in  bata so ta kara jefa Rayuwata cikin wani Sabon kangi.
Dakyar Anty Mamah ta amince da Rokona ta bani kudin mota ta Daukeni a motar ta da kanta ta kaini Tasha ta sakani a motar Karofi ina ta kuka ta Tausayamin ta Dafa kaina Dake cikin Sabon Hijabin data bani da Takalmi tace"Ki daina kuka Fa'iza ba matsala in sha Allahu Mama zata Sauko"
Har na kai karofi kuka nake yi sai da Muryata ta dishe kukan rashin gata da kuma Tunanin yadda yanayin Rayuwata ya fara na fara jin kamshin gaskiya kila bani da sa'a ne komai nawa ba mai kyau ba ne irin na kowa rayuwata ba Daidai take da Sauran mata ba.
Sai dai Goggon Karofi ta ganni yarkace yarkace kafin na fadamata abunda ya faru sai ta nemi dukana sannan na Zayyane mata komai bazan manta ba sai da ta share kwallah ta kamani ta Rumgume tana Fadin"Abunda Saudatu ta aikata miki kenan..? Daina kuka Fa'iza watarana sai Saudatu tayi kuka idanuwanta akan abunda ta aika miki akwai Allah"
Araina ban taba Hango hakan ba ni kuwa wani matsayi zan taka da Mama zatayi kuka Saboda ni..?
A daran ta Kira Baban katsina ta fadamai Halin da ake ciki yace da Safe zai shigo garin ni kuwa Lallashina Goggo ta dinga yi Hatta Hafsatu dake da karancin shekaru ta shiga Damuwa ganina cikin wannan Halin Hajiyar karofi kuwa tana kwance sai bina da kallo take na kasa na mata wata mgana domin sai naji bakina yayi nauyi ganin yanayin datake ciki Goggo tace tun ranar da Baba ya bar nan jikin Hajiya ya kara rikicewa.
Washegari Baba yazo sun kai ta ba dadi da goggo ta nuna mai ya janye mganar auran nan ita zata rikeni Allah ya bani wani mai sona in yi aurena ammh ba Ishaq d'an Saudatu ba shi kuma Baba yace indai yana Raye sannan shi ne Uba ga Ishaq kamar ya aureni ya gama ina Durkushe gabansu suka rika wannan Hayaniyar ad'akin da Hajiya take jinya itama tana kwance bata iya mgana ba sai gyad'a kai hawaye na bin gefe da gefen Fuskarta.
Baban katsina ya tafi ko sallama bai yi ma goggo ba Allahu akbar adaran Hajiya ta amsa kiran Mahallacinta,Tun daga Lokacin da naji goggon na Salatun mutuwar HaJiya da kaina ya amsa Dum! Har gobe in na Tuna da mutuwar Hajiya sai yanayin ya Dawomin da gaske ne ni Fa'iza bani da Sa'a?
Meyasa duk wad'anda suka Tsayamin suke tafiya su barni Farko Babanmu Sannan ga Hajiya itama har aka kai Hajiya kushewarta bana cikin Hayyacina gida ya cika Har Hajiyar Dala da duka zuru'arta suna nan Hadda Mama da su Anty Binta su Ya Asiya sun Dauka mutuwar Hajiya ce ta tab'ani basu san abunda ke Faruwa ba har kuma lokacin ba'a san ina ya Ishaq ya shiga ba.
Ranar da bazan manta ba,Itace Ranar da aure ya kulli tsakani da Wanda bai Taba sona ba har ko yau da muka Tara zuru'a dashi aurena da Ya Ishaq wanda yau har gobe Mama bata daina aibatani da zuru'aar maciya Amana Dangin Tsiya ba,Ranar addu'ar bakwai din Hajiyar Karofi Baba ya tara Mutane ya Biya Sadaki aka Daura aure na ba wanda ya sani sai da aka Daura Gidan mutuwa sai ya koma Gidan Fad'a da Hayaniya domin Mama kaina tayi tana fadin sai taga bayana Goggon Karofi ta shiga Tsakani Ranar ba iya ni kad'ai ba hadda Mahaifin mu dake kasa yasha zagi Taamadina na gidan sulalewa tayi ta koma gidansu tana kuka,kukan maraici da Tausayin ya'yanta.
Sai alokacin kowa yasan Halin da ake ciki Goggon Karofi ce kad'ai da ya'yanta ke tare dani ban da Hajiyar Dala data mara ma Mama baya,Aranar Mama ta koma katsina ta sha alwashin sai taga yadda auran nan zai Tabbata shi kuma Baba yace sai dai in ba shi ya Haifi Ishaq ba.
Ya Asiya da Yaya Mariya sun koma Gidajen su da Tunanina aransu da Tausayina su kan su sun hango Yadda rayuwa da kaddara suka kara gangarawa dani.
Kwana Ashirin da Rasuwar Hajiyar Karofi Sai ga Baba ya zo shi da Ya ishaaq,wanda ya gama gudun nasa ya Dawo jiya da Daddare ya samu labarin An daura masa aure dani Ya Ishaq ya kasa katabus domin Baba ya Daga mai murya yace in har yaki karb'ata a matsayin mata to sai dai ya chanza wani uban ba shi ba.
Wannan mganar shine Sarka na Farko da ya fara kulle aurena da ya ishaq,Baba ya bama Goggo kudi ta yi min siyayya sannan ya kama mana Haya a katsina cikin gari in da zamu zauna ni da Ya Ishaq,har suka tafi ban gansa ba shima bai nemi ba,Tun kuma Daga Lokacin Baba ya fara shirin Tarewata Mama kuwa tayi Kukan har tagaji ta Saduda ganin Da gasken Baban bazai fasa ba.
Kafin Ranar arba'in din Hajiya karofi hatta jere na Goggon Karofi da ya'yanta da Yan'uwana sun gama min komai Domin Baba yace ranar addu'ar arba'in Zan tare agidana Yaya Mariya ita takaini gidanta ta tsifemin kai ta wanke ta kaini akayi min kitso da Kunshi Ina ta ce mata ta barshi kunshi da gyaran jiki sai Mata masu kyau ba irina ba ban taba manta kalamanta alokacin Kaina ta Dafa kafin tace"Kema kina da kyan ki Fa'iza sai dai in ba'a gansa yanzu ba ne..Ammh na tabbatar miki nan gaba zasu ga abunda nake gayamiki"
Alokacin mirmishi nayi mata Domin nasan ta fada ne ni kaina nasan bani da kyau sannan ina da nakasu ta bangaran Ji na da mganata
Aranar da Hajiya ta cika kwana arba'in a kushewarta ranar na Tare agidan Ya ishaq aurena ba irin na mata masu kyau da gata ba ne,Daga ni sai kayana da Goggo ta d'inkamin Sabbi ita da Baba domin da Goggo Taso su yi min Rakiya sai ya Ishaq yace baya Bukata dagani sai shi a mota sai Baba da Direbansa.
Daga Mama har ya'yanta ba wanda ya Leko karofi,Baba da kansa ya shiga Dani karamin flat din da ya kama mana mai Falo da Dakuna Biyu sai kitchen da Tsakar gida,Shi ya damka Amanata Hannun ya Ishaq da karin wasu manya manya sarkunan da Tun abaya na fada muku su suke rike da wannan auran namu yau har da nike baku wannan Labarin,Domin cikin kaukkausan murya yace mai"Ishaq ga Fa'iza nan na baka auranta ba Domin ta rasa me son ta ba sai domin cika Muradin mahaifiyata..Wlh tallahi ko da Rana daya in ka zalunce ta ban yafe maka ba Ishaq..Kuma ko da rana d'aya kabi Hudubar mahaifiyarka ka Tozarta Fa'iza shima nace ban yafe ba..Daga karshe matarka ce ta sunna ka Kula da ita kuma in ka Danne mata Hakki Allah na kallon ka sannan nima bazan yafe maka ba Sannan kasani Ranar gobe kiyama bazaka Rabauta ba Ishaq in dai ka saba ma Umarnina.."
Kafin ya tafi sai da ya kara Jadaddamai in ya danne min hakkina na aure ko guda d'aya ya sani bazai kara samun albarkarsa ba,ya tafi bayan yayi min nasiha hakuri sannan ya sanar dani na zauna nayi ma aure Biyayya bazan taba Tabewa ba Duniya da Lahira Tabbas wannan Biyayyar da Baba ya Rokeni har bayan mutuwarsa ban sauka daga kanta ba,nima ita ke rike dani acikin rayuwar aure na da Ya Ishaq.
Warware tarin kalubalen da na Fuskata a zama na da Ya Ishaq abu ne mai yawa da bazasu fadi a cikin k'urarren Lokaci ba sai dai abu d'aya na Sani mun yi zama ne na Biyayyar Iyaye shi Mganar Baba ke rike sa da Bakinsa a kansa nima kuma Karfin Biyayyan da ya Rokeni akanta na ke zaune.
Tunda na auri Ishaq daidai da rana D'aya bai taba kallona ya yab'amin ba,Bai taba jin dadin zama dani ba bai taba godemin ba,Bai tab'a godema Baba Bisa aurena da ya basa ba,Bai tab'a sona ba bai tab'a kallona da Idon Rahma da Salama ba  bai tab'a jin zai iya bani matsayin matarsa mai kima ba nayi Rayuwa dashi cikin k'askanci da Tozarci ko da yaushe cikin aibatani yake yi da Kusheni,Ni fa'iza na Fuskancin Guilt din kushen miji har tsawon shekaru Takwas da auran mu,Ya kulleni agida cikin tozarci bai barni nayi zumunci da yan'uwnaa da Dangi ba,Alwashin da Mama ta Dauka ta cikashi bata bari na kara jin Dad'in Rayuwa Sai da tabbattar da duk abunda tace ma Ishaq akaina shi yake amfani dashi bai horar dani da yunwa ba Yana sauke min kayan abinci duk wata sutura kuma yana yi min ta Hannun Mama sai ta ga Dama sannan na saka abu mai kyau cewarta kullum abu mai kyau bai dace da mace irina ba,ina jin Tsoron Ishaq kamar yadda nake jin Tsorom Mama Tunda muka yi aure bai taba yarda ya nuna ma wani ni matasar bace ko abokansa ba su san yayi aure ba, acewarsa matar Ishaq sai an zo a ganta Mai kyau ce mai ilimi ce sannan yar gata gaba da baya ni kawai wata Tsani ce wacce nayi kutse tare da Ruguzamai dukkan Farincikinsa.
Da gaske yake yi ya fad'i gaskiya ni kaina in na kallesa na kalli kaina sai naji Tabbas na yi mai kutse acikin mafarkin sa Ya Ishaq dogon Namiji ne kyakyawan gaske fari mai Hanci d'an Fafa mai ilimi dan alfahari da son komai mai kyau da Tsari ni kuma Bakace Gajera mummuna,wacce bata da gata,ba ilimi kamar ta bakinsa yace Total Zero Fa'iza komai nata ba sa'a acikinsa.
  Ya Ishaq kunyar nuna ni yake yi a matsayin matarsa domin bai taba gayyato wani inda nake ba yace shi kan shi kunyar kallo na yake yi a matsayin matarsa ma ballatana wani,Ko Ya'yan da na Haifa tare da shi Kaddara ne da Rabon su daman Domin Tunda Baba ya kawoni wannan gidan nake rayuwa ni kad'ai Sai dai ina aikace aikace na bana ganin kowa Dagani sai ni kamar mayya Ba ni da waya bana jin kowa sannan bana ganin kowa sannan ya min gargadin ko kofar gida na fita sai na raina kaina shi kuma sai chan dare yake dawowa da Farko gidan Mama yake biyawa yaci abinci Baba d'aya lura da Haka ya mai fad'a sai ya daina Daman na Fada muku yana morata ta bangaran abinci zai ci kafin ya fita in ya Dawo yaci acewar Mama Ai abinci daman bani na siya ba dafawa ne kawai nawa Saboda haka na Dafa daman Mata ire irena da Bauta muka dace,Sai suzo gidan ita da Anty Binta su yi ta zagina da Gore gore Ishaq na zaune kanzil bazai ce ba Wani Lokacin Anty Mamah ce kan musu mgana sai su Sasaauta.
Bazan manta da muna da wata biyar da aure Anty Hure kanwar mama tazo katsina suka zo ita da Mama Ya Ishaq na gida ranar baije aiki ba,Naje kitchen na kawo musu ruwa ina rawan jiki na fice ashe Mama ta kira Sunana ban ji ba, tamin uzuri bani da karfin ji ammh sai Mama tace naji kawai yanzu na raina ta ne agabansu Ya Ishaq ya mareni ya sani na Duka na bama Mama Hakuri taki hakura Anty Hure ta yi ta Dukana tana rankwashina Ya Ishaq na zaune ko ajikinsa haka suka tafi suka bar ni ina kuka kukan da ya riga ya zame min jiki.
Ko wata rana na Shafin Rayuwata ba ranar da bazan yi kuka ba babu wannan ranar,Sai da na fara tara ya'ya sai suka zamemin sanyin idanuwana ko Ya Ishaq ya kunsamin Takaicinsa in na Kallesu sai naji raina yayi sanyi Tabbas ko wacce uwa ya'yanta sune Duniyarta.
Muna da wata shidda da aure,Baban katsina ya kawo mana ziyara yayi mana Fad'a da kakkausan murya musamman ma Ya ishaq ni kuma yace na rame na lalace yayi tambayan Duniyan nan ko Ishaq na min wani abu ne nace mai a'a bakomai haka ya tafi  bayan ya kara fadama Ya Ishaq cewa in bai Sauke hakkina dake kansa ba ya sani Allah na kallonsa.
A wannan Daran Ya Ishaq yazo min ya karbi Mutumcina da kimata ta y'a mace cikin kaskantattacen yanayi,Cikin Tozarci da bana jin wata mace ta taba Fuskarta ban sani ba ammh a kasa raina naji cewa mata marasa kyau ire irena bai kamata su fuskanci wannan tozarcin ba.
Tunda ya gama dani ya tsallake ya barni cikin mayuwayacin Hali,Halin da ni na tallafi kaina bazan iya fadin irin wahalan da nasha ba,ba wanda ya kula dani sai ni kadai,Nafi Sati bana ji na Daidai da taamakon Allah na Samu na Dawo cikin Hayyacina Tun kuma daga wannan Had'uwar tamu bai kara kallo na ba ko da yaushe ni ke mai Hidima ina rawan jiki a kansa shi kuma kalamansa Daya ne Hajiyar karofi da Baba sun cucesa har fadi yake yi tasan zata mutu ammh kafin hakan sai da ta jefa rayuwarsa a wani Hali sannan ta bar Duniya har yau bai taba gode musu ba ban kuma jin akwai ranar da zai gode musu.
Ashe wannan haduwar tamu itace sillar Zuwan Amir(Kabir) duniya ne Wata uku tsakani nayi ta ciwo a tsaye,Zazzabin Dare da amai kasala da yawan barci,Ya Ishaq baisan Rashin Lafiyata,baisan komai akaina ba ban da na girka mai abinci yaci yana ci yana bi na da mganganun kushe da Tozarci.
Fahimtar ma ban da lafiya girkin da na kasa yi ne yasa ya lekani ya ganni kwance Ba domin yaji Tausayina ba sai Domin Harshen Baba akansa yasa ya Daukeni ya kaini asibiti,Gwajin farko aka tabbatar da ina da shigar ciki dan watanni biyu da wani abu Bansan wani yanayi Ya Ishaq ya shiga ba, ammh nasan muna Hanyar komawa gida ya kalleni kafin yace"Ke haka kike daga tabaki sai ciki Fa'iza..?
Yaushe na tsara ma kaina aure ballatana har na haihu?
Ya manta Haihuwa na Allah ne,Bani na bama kaina ba Allah ya bani ammh da Gudummuwarsa,Cikin Amir ciki ne da nayi sa mai Laulayi na sha bakar Wahala acikin gida ni kadai,ina haka watarana Goggon Karofi ta zo ganina ita da Yaya mariya su suka iskeni ba yadda nake suka kwasheni sai asibiti dalilin kwanciyata a asibiti Cikina ya fallasa ga su Mama kowa yaji ina da ciki sai kowa mamaki ya kamasa.
Mama kuwa mamaki yasa ta kasa mgana,Anty Binta sai kallon Ya Ishaq take yi basu taba zaton zai iya kallona na da sunan auratayya ba.
Baba kuma sai murna yake yi shi ya Kira Ya Ishaq da kansa ya fadamai da yazo asibiti ga Halin da nake ciki Sanda yazo,Baba sai da ya Rumgumesa yana murna lokaci d'aya yana sakamai albarka.
Mama ta fad'a agaban kowa da kowa Bata kaunar hada zuru'a dani,Goggon Karofi tace Tunda Allah ya had'a ita bata isa ta raba  ba,har sai da suka yi ta Hayaniya,naji jiki sai da nayi sati a asibiti likita nata fadan bana cin abinci sannan jinina yayi kasa Goggo kamar ta wuce dani karofi Baba ya Hana Akace gidan Mama tace ai har Abada na gama zaman gidanta Dole gidana aka maidani Goggon Ta zauna Dani tayi sati,Yaya Mariya ita kadai ta koma Karofi,A bakinta Ya Asiya taji tazo har Katsina ta Dubani bana ganin Tamadina bata taba zuwa gidana ba na Tambayi Goggo tace min tana gidanta ni nasan rayuwata cike take da abun Tausayi.
Har Amir yazo duniya ni Fa'iza babu abunda ya sauya gareni daga zuciyar,Ishaq a kaina na wahala wajen Haihuwa kamar bazan rayu ba sannan Amir yazo duniya wanda yaci sunan Baban katsina Kabir,lokacin da na Haihu Anty Binta na asibiti ana kawo musu abunda na haifa ta duba kunnensa ta Kira mama tace"Mama sai hakuri Dangin tsiya yaron ya Debo"
Nayi kuka sosai da wannan kalmar sai dai a kallah na samu wanda zai san zafina wani abu daya fito daga Tsatso na wanda kila shi zai kaunace batare da ya Duba yanayin Halitta na ba ko nakasun jina ba,An kai ruwa Rana kafin Ya Ishaq da su Mama su amince Goggo ta tafi dani karofi nayi jego shima sai da Baba ya saka baki,sannan ya amince a cewarsa wai Goggo sai tayi ta nuna yana zalunta ta na sannan baya so naje na had'u da su Yaya mariya wai ana zaginsa mganganu dai haka yayi ta yi kan yan'uwana da iyayena bani da tacewa.
Sai da na koma karofi sannan Tamadina tazo ta ganni ta rike Amir gam a Hannunta kafin ta mikamin shi ta dafa kaina kawai tayi miirmishi na kalleta sai naji kuka duk ta lalace ta rame ta kara tsufa kamar ba ita ba,Bazan taba mantawa da Goggon Karofi ba domin ita ta kula dani ba,da kila sai da na Rub'e ni kadai ban san komai ba.
Ina yin arba'in ba Dadewa Goggo Karofi ta maidani gidana Ni da Amir mun yi bulbul duka duka sau biyu Ya ishaq yaje ya ganmu kamar Amir din ba D'ansa ba ne,Goggon Karofi da yan'uwana sun yi kokarin wajen gyarani ni kam ban ce musu komai ba, to ina zan fada musu sau daya tak Ya Ishaq ya taba hada jiki dani Rabon Amir ne..?
To kamar na Amir itama haka Rabon Saudatu(Anum) ya had'amu shima duka Duka Haduwar bai wuce sau uku ba ma na samu ciki Amir nada wata Goma sha hudu wannan karon Ishaq yafadamin sai dai a zubar da cikin ni kuma nace ban amince ba Karo na Farko da na taba kai karas gaban Baba Dalilim da yasa Baba Ya mari Ya Ishaq ya kuma nunasa da yatsa yace"Kada na kara jin wannan mganar a bakin ka..kasan baka son cikin ka yi sa..?
Ka kiyayi ranar da Fa'iza da ya'yanta zasu zame maka inuwa wacce zaka iya rab'ar ta ina jiye maka watan watarana kada kayi nadamar abunda ka aikata"
Wannan marin ya jamin abubuwa Dadama tsakani da Ya Ishaq,kamar ni na bama kaina cikin Dalilin Baba yasa Saudatu tazo duniya(Anum),Da kulawarsa na haifeta Lafiya ita ma kamar Amir ne Baka ce irina,Basu da yadda zasu yi su sauya wannan kaddaran tunda haka Allah ya Tsara Mama ta tsane ni ammh ta kasa Tsanar jokokinta Amir ma ita ta karbesa ta yayesa sai wahalan tamin Sauki,Goggon Karofi Sati daya tamin ta koma ni na mike na Rika kula da kaina har nayi arba'in din Anum.
Ya Ishaq baya barina fita ko'ina Sai gidan Mama ko gidan Anty Binta Su kuma har naje na Dawo bana samun kallon arziki,Karofi kuwa Tun da nayi jego ban kara komawa ba Har Haihuwa Ya mariya tayi ya Ishaq yace gulma zai kaini bazani ba.
Gidan Yaya Asiya kuwa tun bayan auranta kafata bai kara taka kano ba,Ya Ishaq ya rabani da kowa ciki har da mahaifiyata domin har Haihuwa tayi yaron bai zo da rai ba bai barni naje ba wai zan kwaso ma Anum Sanyi Baya sona ammh kuma yana kaunar ya'yan sosai yake kula dasu kamar yadda yake kula da kansa.
Anum na da wata Hudu watarana Baba ya fara rashin Lafiya anje asibiti an yi gwaje gwaje sai aka gano Hantarsa ce ta tabu ba'a sani ba,Ya kwanta asibiti yafi sau hudu duk Hankalin su Mama ya tashi ni kaina Hankalina baya kwance domin Baba shi kad'ai ne ya ragemin Saura gata na,Kwanciyarsa asibiti na Karshe an sallamosa Da ya ishaq zai fita yace na shirya naje na Dubasa Amir daman yana chan tun yaye bai Dawo ba.
Naje na dubasa yana kwance ne yana ganina sai da ya mike,Ya miko min Hannu na Kwanto Anum daga baya na mika masa ita yana ta mata wasa Baba yayi ta min Nasihan hakuri da kuma Umrtana da na zauna nayi Biyayyan aure zan rabauta Ranar gobe kiyama..
Ashe wasiyya yake barin mu yace na kula da ya'yana na basu tarbiya kada na Biye ma Ishaq,nayi hakuri dashi Sannan na kara hakuri da su Mama watarana dani da ya"yana duk sai mun zame musu Inuwar Rab'a,na dawo gida da Tunanin mganganun Baba ashe bazai kwana ba adaran Allah ya Dauki ransa.
Alokacin mutuwar Baba na kara yarda Tabbas ban da sa'a domin duka wada'nda nake gani agata na sun kare bani da kowa anan duniya da zan kallah nace Gata na ne duka sun tafi Na tabbata ko Mama bata kaini kukan mutuwan Baba,na fade lokaci d'aya nayi zuru zuru tabbas Mutuwar Baba ya sanyaya ma Ishaq zuciya sannan ya sa ya rage wasu abubuwan.
Rasuwar Baba ba'a rufe shekara ba Ya ishaq ya samu karin girma zuwa Abuja,chan ya koma aiki sai bayan Sati biyu yake zuwa katsina sai nauyin su Mama da su Jamal duk ya koma wuyansa abubuwa duk suka Tabarbare daman karfin zumumcin Baba ne to yana Rasuwa sai ahankali Hajiyar Dala ta matse kanta gefe itama Goggon Karofi sai ta kama kanta itama Daman basa shiri da Da Mama sai ta Dade bata zo katsina ba ba ita kadai ba Saboda Sanin Halin Ya Ishaq yasa ba mai son Rabata abu kadan yace munafunci ake yi shiyasa Dole dai su Mama ne bani da kowa a garin katsina sai su da ya'yana.
Samun karin girman Ya Ishaq yasa sai ya samu rufn asiri fiye da baya ya gyara ma Mama gida ya koma Fasalin na zamani shi kuma ya siya Fili ya fara gini a Anguwan layout,Jamal kuma ya shiga jami'a sai Badariya da ta zama yammata yanzu sai ni da ya'yansa wanda Darajan su yasa yake Ragamin shima ba wai don ya daina Tozartani ba ne A'a har yau har gobe ni Fa"iza ba kowa bace a wajen Ishaq kabir Karofi
Cikin mustapha ko ni bansan ina da shi ba sai da yakai wata Biyar Mama data ganni da ciki ta Dinga bala'in na zama kamar beran masar bani da aiki sai Haihuwa ta manta ba ni kad'ai nake samar da cikin ba har da Gudumuwar D'anta ammh bata ganin Laifinsa sai nawa,Na haifi Mustapah ba Dadewa muka tare a sabon gidan da Yaya Ishaq ya gina katon gida mai shashe biyu,Shashen farko mai 3Bedroom da Falo sai kichen,Nawa daya sai na yara sai guda d'aya na baki,Ya ishaq shi ya Zuba Sabbin kaya agidan komai bamu Dawo da Tsoho ba, Mama ta kwashe su ta kyautar ni ko da har nayi Tunanin na aika ma Tamadina da su Dakinta Sai leda ba kujeru ganin Mama tace akwai wacce zata bamawa ban yi mgana ba, Sanin Halinta.
Haihuwar Mustapah yazo da Budi sosai Ya Ishaq har motar hawa ya mllaka ya siya mama nata,Budi ta ko'ona sai hamdala da Godiya yana Dinkamin suturu daidai gwargwardo sai dai na yaransa Dabam suke,Ni wani Lokacin ko yayi niyar yimin Rantsatsun kaya sai kalaman Mama su Dishe niyyarsa tunda tasha fadin siyamin kaya na alfarma barnan kudi ne, Tunda ba kyau zasu yi min ba sannan bansan yadda ma ake gayun ba kuma gaskiya suka fada ba karya sukayi ba ban san komai na gayu ba.
Ni dai iyakata nayi wanka na shafa mai na saka kaya,Abaya telan su mama ke min dinki Mama ta koma ba wata mace saboda sai nace yana kamani ni kuma bana so kaya su kamani na fison a shatamin na rika yawo aciki,ya Mariya ko Ya Asiya ko da wani Lokaci suna kokarin gyarani ni ko bana jin su gani nake yi gyara da gayu na wajen mata masu kyau da gata ban da ni da bani da ko  d'aya daga ciki Dalilin dayasa Ya Ishaq yake Biye ma Mama kenan in ta fadi mgana hakan take indai a kaina ne ballatana ba ran Baba ita ke tafiyar da komai.
Mama ta bada shawaran nayi Tsarin iyali sai dai bai karbeni ba wannan yar ashanan aka sakamin ya sakarmin jini Dole aka ciremin ana ko Ciremin ko wata Biyar ban yi ba na Samu Cikin Ahmad,na haife su kusa da kusa domin a shekara ta takwas da auran mu da Ya Ishaq duka na Haifesu haihuwan gwarne na rika yi don ma Allah yasa ina da jarumta daukan duka kwarmiyan yaran
Cikin ikon Allah cikin ya'yana ba wanda ya Dauko Lalurata sai na godema Allah Ammh wani ikon Allah susan Lalurata barin ma Anum da Amir susan bana ji sosai in zasu yi min mgana sai sun daga muryansu.
Allah ya bani yara masu kirniya,musty Da Amun basa jin mgana komai suka gani sai sun taba abunga ga wanda bai da karfin ji ina chan ina aiki su kuma suna Falo suna barna bana sani kuma Duk abunda suka Lalata sai Ya Ishaq ya dora komai akaina,Shiyasa ya dinga masifan na bari duk sun bata gidan sun bata kayan kallo sun bata in ji min wanki kuma Mama sai tace bazai kara siya ba, a kyaleni na wahala ai da gangan na bari suka bata komai.
Ni kuma bana cewa komai,Saboda bani da wani zabi,Har zuwa yanzu da girma ya kamani da ya'yana ban daina samun tozarcin Wajen Mama da Anty binta ba tun ba'a sani ba har kowa ya sani,Goggo karofi dai hakuri take bani,in ta kirani a waya sai dai fa ta wayan ammh Sai na shekara kafata bata taka Karofi ba Tunda nayi aure Sau Daya naje naga Tamadina Shima Haihuwan Mustapah ne da naje karofi da Ya Ishaq yaji Labari masifa ya farayi wai baya son ya'yansa suna zuwa gidan wasu suna Rabe rabe.
Haka nan nake daga ni sai ya'yana sai Danginsa alhalin yasan bana jin Dadin su ammh ni nawa yan'uwan sai dai zumunci ta waya ya rabani da kowa nawa.Hafsatu ce kawai tana ta da Kulafucin yan'uwana bai da yarda zai yi da ita in sun samu Hutu tana zuwa ta zauna dani hakan sai yasa na Shaku da ita fiye da su Yaya Asiya.
Nasan Tabbas Ya Ishaq zai kara aure watarana ban daukesa alokacin da najisa ba Nima abakin Anty Binta na farajin mganar auran sannan Mama ta Fadamin nasan bani da wata Daraja a wajen ya Ishaq ammh na Dauka zan ci albarkacin ya'ya ashe bani da wannan alfarman na Kunshi Bakinciki Tundaga ranar farko da na wayi gari agidan Ya Ishaq a matsayin matarsa,Na kunshi takaici a matsayina na Uwar ya'yansa na fuskanci Tozarci a matsayina na kanwarsa tun a baya to wani tozarci ne ni Fa'iza da ya rage ban gani ba..?
Nayi Rayuwar aure shekaru Takwas da wani abu ammh Daidai da Rana d'aya ban Taba Danda'na yadda Dadin aure yake ba na dai yi shekaru Takwas ina Sanin yaya matsayin Tozarci da Gori yake sannan na kara zama Guilt akan kushen Hallita da kuma aibata Nakasa ta nayi rayuwa cikin Guilt din jin ban da sa'a na rayu cikin Guilt din Sannin ni bani da gata na zauna cikin Tunanin Mata ire ire na basu dace da suyi Farinciki ba.
Basu chanchanci miji mai kirki ba, basu chanchanci samun soyayyar ko wani Namiji ba,Sannan basu chanchanci Rayuwar Farimciki ba.
Mata ire irena Rayuwar kaskanci da Torzarci da Bauta  ya dace damu,Ba kokarin mu goga kafad'a da kafad'a da mata masu kyau da gata ba shi yasa na Rayu cikin Tunanin kayan alfarma da shigar alfaarma da Kwalliya  basu dace da ni ba, sun fi dacewa da mata masu kyau da Nagarta kamar yadda Ya Ishaq da mama ko Anty Binta ke yawan fadi akaina.
Tabbas na aminta da duka zencen su da Tunaninsu"

*Littafin KANA NAKA book 1 free ne book 2,3 paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*


*Janafty*[6/13, 12:28 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

         *🅿️06*

Filon da nake kwance akai sai da ya jike saboda hawayena,na kara birginawa ta b'arayin hannun haguna domin hannuna na dama yayi min Tsami sai naji kamar na Danne Gefen Kafafun Ahmad dake kwace gefena da Sauri na mike ina kara gyara mai kwanciyarsa barci yake yi hankalinsa kwance domin akwai haske acikin dakin ban riga na kashe ba ina kallonsa ne ammh a kasan zuciyata fad'i nake shi kam ya huta bai san duk wasu walhalhalun duniya da tashin Hankalin dake cikinta ba.
Hawayena har suna d'iga saman cikinsa nayi saurin matsawa ina sharesu da duka hannayena kafafuwna na zuro kasa kafin na dukar da kai na haka kurun nake jin kamar na yi ta rusa kuka da dukkan karfi na,na Dad'e ina so nayi kuka da karfi ammh bansan Kafad'an da kirjin da zan kwanta na rera kuka a lallasheni ba kawai sai na durkushe saman Dadad'den Cafet din dake cikin bedroom dina na fashe da wani marayan kuka hannayena duka biyu na tallafe fuskata da su wani irin kuka ne dake fitar da karar sauti cikin Yanayin da ni ke ciki.
Meyasa zan damu don Ya Ishaq yace zai jingine aure na dashi..?
Na dauki tsawon Lokaci daman ina jiran ranar da zai auro zab'insa na yi tunanin zan fuskanci tozarci ninki ba ninkin wanda nake karba a wajensa da wajen su Mama ammh bantab'a Tunanin zan fuskancin irin wannan cin Fuskar ba duk da nasan kalaman Baba sune suka yi ma wannan auran nawa tsakani da Ishaq sarka ba domin haka ba Tuni ban kawo lokacin nan acikin gidan sa ba.
Menene laifina domin na kasance a yadda Allah yake fatan ya ganni..?
Nayi kuka,kukan da ban taba irin sa ba Tun bayan da abubuwan suka fara zame min jiki sai dai wannan kukan nawa ya sha bambam da na kowani Lokaci na yau ina kukan yadda Rayuwata zata kare ne ni da ya'yana.
Kwarin gwiwa naji yana shigana irin wanda ban taba ji ba alokacin da wata zuciya ta tunasar dani ni uwace ina da ya'ya bai kamata na zama mai Rauni ba in na Raunana ya'yana suma zasu Raunana in na karfafa nima watarana ya'yana zasu zama karfafa.
Nasan Rad'ad'in maraici daga na uba har na uwa Tamadina tana raye ammh ban san Dad'inta ba,bayan Laluranta kaddara tazo ta raba tsakanimu da ita gwara ko wa dani Domin ni kam Ya ishaq ya rabani da kowa nawa ciki da har da uwar data Haifeni.
  In ni nayi maraici ya'yana bazan bari su yi wannan maraicin ba, zan zame musu komai a wannan rayuwar zan zauna na basu tarbiya sannan na zama Tsani wajen inganta rayuwarsu domin sune Duniyata a yanzu bani da kowa daga Allah sai su sai yan'uwana.
Kamar kiftawan ido naji kukana ya Dauke na kurama Bangon Dakina ido ina Lissafin yadda zan fara gudanar da Sabuwar rayuwar da kaddara ta kara Budemin.
Abaya komai lalacewar aure na da Ya Ishaq bai furta zai jingine ni ba ammh ayau ya furta kuma alama ce ta angaji dakai ana neman maraba dakai,ni ba jahila bace ta bangaran addini nasan menene ma'anar Jingina amusulunci,Nasan zai kula da ya'yansa Saboda Dolensa ammh a yanzu ni ban zama Dolensa ba ya zama Dole na sama ma kaina mafita mafitar rike kaina tsayawa ga kafafuwa na ba saboda kaina ba sai Saboda in inganta rayuwar ya'yana anan gaba.
Ji nayi wani irin karsashin gwarin gwiwa  na kara shiga har cikin Tsokar jikina,Hawayena na share kafin na yunkura na mike,Fuskata nake ta faman gogewa araina ina nanata sunan Allah,Afili na furta"Tunda ka bukaci hakan ya ishaq zan yi maka hakan kamar yadda ka fad'a domin rama alheri da Baba yayi min..Sannan kamar yadda nayi maka alkawari babu wanda zai ji wannan mganar indai daga bakina ne sai dai daga bakin ka da ikon Allah zan zama Jajirtattaciya uwa ba domin na karfafa kaina ba sai domin na inganta Rayuwar ya'yana anan gaba"
Daga haka na fara laluban wayata dake saman madubin Dakin,Na dannata naga 1pm na dare ta wuce biyu saura,sauke wayar nayi nan saman madubin dakin nawa na Tura kofar Tiolet na shiga na dauro alwala nafito nazo na shimfida Darduma na Fara Nafilar da tazame min jiki duk daare na saka yakinin araina Bayan kowani Tsanani Allah na samar ma da bayin sa masu hakuri Sauka'kawa
Abaya in nayi sallolina na cikin Dare ina addu'ar Allah ya shiryamin yarana,ya saka musu tausayin junansu aransu,ya inganta goben su ya saka musu albarka acikin karatun su,Sannan na kan roki Allah ya sausauta zuciyar Ya Ishaq a kaina Ya sa ka Mama tasoni ta kaunaceni,ammh daga daran yau sai na sauya alakar addu'ata na roki Allah ya bani karfin gwiwa ya ciremin rauni da karaya yasa na tsaya nayi tsawon rai da zan zama Bango abun jigina wajen ya'yana na roki Allah da kyawawan sunayensa Chasa'in da tara akan ya tayani Tarbiyan y'ayana ya kular min da su ya zama gatansu ya tausaya musu ya shiryamin su duniya da Lahira yasa su zama abun alfaharin al'umma da musulaimai gabadaya.
Ban kwamta ba sai wajajen karfe uku na Dare,shima Ahmad ne ya farka da kuka na isa garesa na Daukesa na Fara Lallashinsa ganin yaki daina kuka sai na bashi Nono yana kamawa sai shuru ashe yunwa ce yana koshi sai barci,Garin nima na shimfid'ar da shi sai barci ya kwasheni sai jin Mganar Hafsatu nayi a kaina tana ta kiran sunana Lokaci d'aya tana Buga kafafuwana..
Firgigit din da nayi na farka sai da Ahmad dake rumgume dani ya farka shima a tsorace sai ya fashe da kuka mikewa nayi ina mika Sosai Hafsatu kuma na Tsaye a kaina ita ta D'auki Ahmad tana fadin"Kai sarkin kuka ai garin ka ya waye"
Sama sama na jita mikewa nayi a kasalance,na sauko daga kan gadon cikin yanayin mganata nace"Lokacin sallah ya yi ne..?
Tana zama gefen gadon da Ahmad a Hannunta tace"Eh har su Ya Ishaq sun tafi masallaci da su Amir yau kin makara"
Da karfi tayi mganar shiyasa na jita idanuwana na mutsike bina da kallo tayi lokaci d'aya tana nazarina kofar Tiolet na Tura na shige na rufo alwala nayi a gurguje na fito na iske tana cire ma Ahmad Pampers naji tana fadin bai ma yi komai aciki ba.
Ina kokarin Tada sallah domin har na sanya Hijabi na juya ina kallonta Lokaci daya ina fadin"Ha..Hafsatu..Kin yi sallar ne..?
Kai tsaye tace"ina Hutu dame zan taimaka miki kafin ki idar da sallar..?
Shuru nayi ina nazarin abunda zasu tafi da shi makaranta babu cefane komai ya kare hatta lemun yaran da Biskit sai kawai cikin yanayina nace mata"Babu indomie ta kare dafa musu farar shinkafa ki yi musu amfani da miyar nan"
Da toh ta amsa min ta fice Dauke da Ahmad ni kuma na tada sallah sai da nayi raka'atul fijir sannan nayi sallar asuba ina cikin azkar sai ga Anum ta shigo da karamin hijabinta alamun itama tayi sallan ne bayana ta D'ane tana fadin"Umma ina kwana"
Yaran sun san raunin jina in zasu yi min mgana sai sun daga murya musamman Anun da Amir.
Mirmishi na saki na saka hannu na Jawota gabana, na zaunar da ita ina Fadin"Ina kwana Anum d'ita"
Lokaci d'aya ina jan kumatun ta Anum irin yaran nan ne masu yawon tsiya in suna mgana sai ka zata ana gaya musu ne.
Kuri tayi min da ido ni kuma hankalina na kan littafin azkar din dake Hannuna ina karantawa sai ji nayi kamar daga sama tace"Umma kuka kika yi ko..?
Waya dake ki..?
Ban ji mamakinta ba sanin Halinta da Sauri nace"A'a wani kwaro ne ya fadamin a ido Anum."
Da Sauri ta bata rai kafin tace"ko Daada ne ya yi miki Fad'a?
Shuru nayi ina bin ta da kallo yarinya ce yar shekara biyar da wannan mganar ina laluban amsan da zan bata sai ga su Amir sun shigo yana rike da Hannun Musty dukkan su jikina suka fada Amir dai gefe yayi agabana kusa da Anum yazauna Musty daman akwai son jiki shi ya lafeni sai na rike sa ina jin wani Farinciki in na Tuna nima uwace ina da iyalaina da zasu iya zama abun alfaharina watarana.
Amir ne ya daga murya yana fadin"Ina kwana Umma"
Na amsa masa ina shafa kansa Musty ma da gwarancinsa ya gaisheni na amsa ina Dariya zama na gyara ina Fadin"Kun yi azkar din Safe..?
Amir yace"Umma Daada bai barmu mun yi a masallaci ba ana ta kiran sa a waya sai muka dawo gida"
Amir da kasafai ya cika mgana ba, sai in yaga dama,ban ce komai ba sai na kauce mganar nace su karanta azkar din su na Safe kafin Lokacin wanka yayi.
Nan suka zauna gabana suna karantawa in da suka yi kuskure sai na gyyara musu har Musty da bai gama iya mgana ba yana ta garancinsa.
Muna cikin Hakane Hafsatu ta shigo tace ruwan wankan su yayi zafi sai nace ta bari zan yi musu wankan ita taji da abun karyawan su.
Ko kafin bakwai na Safe gabadayan su sun shirya cikin Uniform din Tahfeeez din su,Babansu ban gan shi ba Domin tun jiyan nan bamu sake had'uwa ba.
Farar taliyar Hafsatu ta dafa musu sukaci da Sauran miyan jajjagen da nakedashi,Sauran kuma nace ta saka musu a basket din su babu lemo ko Biskit sai kawai nace ta dura musu aruwa a gororin su.
Suna zaune afalon suna cin abincin ni kuma ina gyara ma Anum littafanta da ta wargazasu,Ahmad na bayan Hafsatu yayi barci tun da yaji Ruwan zafi ni ban yi wanka ba Hijabin da nayi sallah ne dogo ajikina.
Hafsah na Durkushe gaban Musty ta na bashi abinci abaki Anum sai ta rika Sako hannu tana d'ibar masa abincin sa da karamin Fork din su farare na cin abinci shi kuma sai ya fashe da kuka daman duk ya fisu Rigima.
Hafsah ta gaji da mgana ta kai ma Anum Rankwashi akai tana Fadin"Babbar banza wacce bata san kaninta ba"
Ni ban jin me suke fadi ina dai kallon su Lokaci bayan Lokaci ina Mirmishi sai kukan Anum naji kamar wacce ake yankata na saki littafin Hannuna na mike a firgice da yanayin mganata na fara tambayan Hafsah me ya faru Hararan Anum tayi kafin ta fara min bayani ta karishe da fadin"Anty Fa'iza rankwashinta fa kawai nayi shine ta wani yanka mana ihu kamar ana yankata in baki ma mutane shuru ba sai na bige ki yanzu nan"

"Karki kara dukar min yarinya kada ki Sake Hafsah.."

Kamar daga sama domin mu dai bamu san fitowarsa daga shashensa ba dagani har Hafsa mun ji mganarsa Saboda a kausashe yayi maganarsa,Da sauri dukkanmu muka juya muna kallonsa yana sanye da Jallabiya mai ruwan madara Kansa ba Hula fuskar nan nasa kamar ko yaushe a had'e,Anum na ganinsa ta tashi da gudu ta nufesa lokaci d'aya ta fad'a jikinsa cikin sangarta da shagwaban da ya bani mamaki tace"Daada kaga Anty Hafsah ta Dake ni ko..?
Riketa yayi Lokaci d'aya yasa ka hannu ya Dagota ya riketa a hannunsa ya Tako falon duka yaran suka mike suka bar abincin gabansu suka nufesa suna fadin"Daada.."
Zama yayi kan daya daga cikin kujurun falon yana Daga musty shima ya Daurashi kan cinyarsa Amir ne kawai ke tsaye a gabansa.
Kansu ya Shafa gabadayan su yana Fadin"Eyee..Ya'yan Daada yan makaranta..Mutsy me kaci haka bakin ka duk maiko.?
Da yanayin mganarsa yace"Chaliya"
Dariya yayi yana kwaikwayonsa Hafsah ce ta rankwafa ta gaisheshi ya amsa yana wani had'e rai nima na gaisheshi ya amsa a Dakile.
Kallonta yayi kafin yace"Hafsah ba na so ana dukan min ya'yana..Bana so..Har nawa Anum take da zaki dake ta.?
Hafsah mamaki ya kamata cikin mamakin tace"Rankwashin ta kad'an nayi akai kuma musty take sawa kuka"
Kai tsaye yace"Nace dai bana so kiyaye Ok"
Kai ta dagamai cikin wani yanayi kafin ta Dago ta kalleni sai naji wani iri araina ashe Ni ma kenan bazan iya Hukunta Anum ba tunda Hafsah ai kanwatace,Ahmad ya tambaya tace gashi a bayanta yayi barci daganan ta shige Daki jikinta duk ba Dad'i sai naji ban ji dadi ba sama sama nake ji yana Hira da ya'yansa ni kuma ina Had'a musu jakunkunansu waje daya na shiga kitchen na fito musu da Baskets din su guda uku nazo na ijiye ina Fadin"Anun Amir Musty kowa yazo ya Dauki jakarsa da abincinsa"
Amir da yazo ya Dauki nasa na taimaka masa ya rataya jakarsa,Anum kuma sai ta fara rigiman ba Biskit ba lemu.
Ya ishaq ya Dago yana kallona ni kuma kawai sai na Dauke kai na cikin Yanayin mganata na yi mata tsawa ina Fadin"Anum zan saba miki fa yaushe kika koyi rigiman ban..za.?
Kuka take neman ta sakamin sai na ware mata idanuwana na Daga Hannu kamar zan daketa sai ta yi shuru tana kallon Uban nata nima nasan ni yake kallo sai naki yarda na kallesa kada tsoron sa yayi tasiri a kaina.
Cikin Fadansa yace"Ammh kina ji na fada ma kanwarki bana son ana dukamin ya'ya shine zaki kwantata agabana ko Fa'iza...?
Kaina na kasa kawai sai nace"Ka..kayi hakuri"
Sai na koma na zauna,Kallona yayi kafin yace"Meyasa ba Biskit ba lemu a basket din nasu..?
Kai tsaye nace"Babu sun kare gabadaya"
Cikin Fad'a ya fara fadin"Gaskiya kina da matsala..Ke shikenan kamar ba mace ba..?komai na Dubaran mata baki iya ba..?to sun kare da kika yi shuru da bakin ki baki fadamin ba ke zaki siyo ki kawo..?
Ya karishe fad'a cikin hayaniyar mganar dayace saboda yanayina ya koya kaina na kasa na kasa mgana suma yaran sai suka yi shuru duk sun yi tsuru tsuru.
Fad'a ya cigaba da yayi yana fadar duk mganar da tazo bakinsa ya karishe da Fadin"Ya'yanki ma baki san yadda zaki kula da su ba Fa'iza to meye amfaninki..?
Komai naki zero ne baki da wani amfani wlh aikin banza kawai"
Dagowa nayi ina kallonsa Hawaye sun cikamin ido bana so su zubo saboda yaran duk sun kuramana ido Kama hannun Anum da Musty yayi yana Fadin"Muje zan siya muku a hanya ku jira anan bari na dauko key din mota dina"
Kai suka gyada mai ya juya ya koma Shashensa yana ta tsaki yana shigewa hawayena suka kawo sai na kauda kaina ina kokarin sharewa sai jin Hannun nayi a kan fuskata ina dagowa naga Amir cikin Wani yanayi da Sauri na kakaro mirmishi ina Fadin"Amir..kwaro ne ya fada min a ido"
Bai ce komai ba yasa Hannu ya Sharemin hawayena Lokaci daya yana fadin"Kiyi hakuri Umma"
Kawai sai naji wani Dum acikin kaina jikina yayi sanyi nabi Yaron da kallon Duka duka shekarun Amir bakwai ne ammh yasan ya ganni ina kuka ya sharemin hawaye ya bani Hakuri kawai sai naji wani abu ya tasomin daga kasan raina bansan Lokacin da na kamasa na Rumgumesa ba da dubara ina Dauke Hawayen idanuwana.
Mganar Ya ishaq kawai naji a tsakar kaina yana fadin"In bazaki barsa yaje makarantar ba ne sai ki gayamin na tafi na kai masu zuwa"
Da Sauri na sake sa ina shafa kansa a sannu nace"Kada ku manta ku yi addu'a"
Suka gyadamin kai,Gabadayan su suka dagamin hannu kafin ya tasasu su fice,bayan fitan su na Dade zaune ina Tunanin rayuwa kafin na mike Dakin Hafsah na shiga na isketa ta shimfidar da Ahmad nata barci ita kuma tana Hada kayanta a karamar Jakar gabanta na tsaya ina Fadin"Yau zaki tafi.?
Mganata yasa tasan na shigo ta Dago tana fadin"Eh Yau goggo tace na dawo gobe muna da makaranta"
Gefenta na zauna na Dafa kafadarta ina fadin"Kiyi hakuri kin ji Hafsatu.."
Mirmishin da yafi kuka ciwo tamin kafin ta kalleni Lokaci d'aya tace"Ni mai sauki ne Anty Fa'iza kece za'a bama Hakuri..Allah ya kara miki Hakuri"
Ban ce komai ba sai mirmishi da nayi shuru mukayi na wani Lokaci kafin tace"Zan biya ta Dutsenmah na Duba Tamadina na riga na fadama Goggo zan biya tachan"
Kai na gyada mata kafin nace"Kice ina gaisheta nima in sha..Allahu zan..zan zo na Dubata"
Da kai ta amsa min kafin tace"Allah yasa"
Bamu cigaba da Hira ba na mike na koma kitchen na dora ma Ya Ishaq ruwan tea bayan ya tafasa na juye mai a falas ba komai na cefane har kwai ya kare wani sauran dankali ne bashi da yawa na fere na soyamai sai namai miyar albasa,na tattara komai na kai Shashensa na shiryamai afalonsa na fice Ganin Hafsa ta karbi gyaran gidan ni kuma sai na kwashi wankin yaran da suka taru naje bayan  inda tankin ruwa da famfo yake yi na Fara wanki Uniform na fara wanke musu da Hafsah ta gama sai tazo ta sameni tana tayani sama sama muna Hira,Saboda yanayina Allah yasa bani kuma da yawan mgana sosai

Muna cikin wankin Ya Ishaq ya Leko dauke da Ahmad a Hannunsa yana fadin"Sai ku bar Cikin gida ba kowa sannan ku bar yaro shi kadai adaki..?
Wannan wani irin rashin Hankali ne..?
Da Sauri na tsame Hannuna a ruwan Sabulu na karisa wajensa na karbi Ahmad ya juya batare da yayi min mgana ba sai nabi bayansa muna zuwa Falo ya tssya ya juyo yana kallona Lokaci daya yana fadin"Ga cefane nan..Ki lallaba kinsan ina da Hidima yanzu haka wajen Milyan daya zan yi ma Anty Binta ciko na Hidiman bikin nan sannan ba Lalle na kara miki wani cefane ba sai karshen wata"
Da kai na amsa mai kafin a Sannu nace"Angode Allah ya saka da alheri"
Ko amsa ni bai yi ba yayi gaba daidai Lokacin da wayarsa tayi kara kafin ya shiga ya Daga wayar kasa kasa yayi mganarsa ban ji ba.
Zama nayi na bama Ahmad Nono na maidasa baya na kwantar Domin bazai yarda na ijiyesa ba.
Na dauki Ledojin na shiga da su Kitchen Katan din Bobo ne sai na maltina sai Biskit kwali biyu sai Na ruwa faro sai kwai da doya sai Dankalin Turawa sai kayan miya,na Zazzage komai na jera a muhallinsa
Sannan na koma muka cigaba da wanki ni da Hafsah duka sai da muka wanke har da nawa muna bayan Ya Ishaq ya fice daga gidan bamu sani ba fitowa kawai nayi naga bayanan sannan ba Motarsa nasan bazai wuce gidan Mama ba..ga Hafsah zata tafi bani ko da naira Biyar balle na bata na Mota.
Ina so na bata wani abu ta kaima Tamadina bani da komai sai na Dibar mata Sabulin wanka da na wanki muna da Sauran su bai kare ba, nace ta kai mata,mganar kudin mota kuma tace min kada na Damu goggo ta bata 3k da zata taho zasu isheta ta koma Gida ina ji ina gani Hafsah ta tafi ni na rakata har kofar gida muna Daga ma juna Hannu.
Na dawo cikin gida Nepa sun kawo wuta na zauna na fara gugan kayan Su Amir saboda sai yammah zasu dawo,haka ma Ya ishaq sai da yammah sai nayi Tunanin sai da yamah nayi girkin ni kuma Daman cikina ya cushe hafsah kad'ai taci taliyan nan na Safe ni kuma sai na barta sai an juma.
Ban tashi Daga wajen nan ba sai da na goge rabi da kwatan kayan nan tas sai wad'anda basu bushe ba kawai Sallah kawai ke tadani sai bayan Sallar la'asar na tashi daga wajen shima Saboda girki ne.
Sai alokacin nayi wanka na saka wata bubar doguwar rigar wata atamfa da Yaya Asiya ta dinka mana mu hudu har da ita.
Na shiga kitchen na fara Tunanin me zan sarrafa sai kawai nace bari nayi jallop din shinkafa tunda ina da Sauran kayan lambu sai na Hada da su,Naso na hada ko lemu ne to bani da kankana ba aya ba abarba ba Sinadrin hadawa kayan zobo kuma Daman Badariya ke siyon irin wad'anan abubuwan duk Ya Ishaq baya siyan su sai abunda ya zama Dole.
Sai da na gama komai naje nayi sallar mangariba Allah ya taimake ni Ahmad yau barci ya yini yi bai yi rigima ba Tunda naji su Anum shuru nayi Tunanin Babansu ya Dauko su suna gidan Mama.
Shiyasa na idar da sallah sai na fara jera ma kowanne kayan sa a dirowansa ina Dakin wayata na kara ammh ban ji ba sai chan sama sama naji karan a cikin kaina.
Na daukota na Duba Goggon Karofi ce Ina hada Hausa Ina karantawa wanda bai da wahala sosai in dai kamar na sune ko mgana wacce ba'a rubuta tayi tsawo ba.
Ina Daukan kiran na sakata a speaker Hafsah ce muka gaisa tace ta Sauka lafiya taje wajen Tamadina taji sauki tana ta godiya Daganan ta bama Goggo muka gaisa ta yi tamin nasiha daman ita nata kenan Fadi take yi "Fa'iza ki yi hakuri kin ji ko..?Allah bai manta dake ba..In sha Allahu zaki ci Ribar wannan biyayyar taki"
Shuru nayi ban ce komai ba ta yi ta bani Misalai da matan da suka yi Biyayya agidan aure sannan suka Rabuta ranar Lahira hawaye suka kawo Cikin idanuwana ina tuna Baba a mganarta shima duka kalamansa ne..daga karshe tace min"Naji Isahaq zai kara aure ko..?to sai kin kara Hakuri Fa'iza daman abunda Saudatu take nema ne ya samu ki koma gefe ki rumgumi ya'yanki Allah yayi albarka Allah ya baki Dangana"
Ina share hawayena nace"Ameen Goggo ammh dai zaki zo ko..?
Goggo tace"To sai nagani in zan samu zuwa ammh yara zasu zo su zauna Dake"
Daga haka mukayi sallama na koma na cigaba da aikina naki bari Tunanin auran nan ya shiga zuciyata.
Tun ina saka ran dawowar su da wuri har na sare gani  har Tara tayi nayi sallar isha'i nayi ma Ahmad wanka har yayi barci nima wanka na Sake yi na saka Riga da wando masu taushi na barci Diyar Goggon karofi Anty Nasara ta kawo min su Tsaraban Umra.
Ina zaune afalo ni kad'ai kamar mayya naji Hayaniyar yaran da shigowar su dukkansu jikina suka fado suna murna nima na rike su ina Mirmishi Tun kafin nayi mgan Amun tace"Umma Gidan Mama fa Daada ya kaimu"
To daman yana da inda yafi gidan Maman ne..?
Suka fara gwadamin Tsaraban Kayan lashe lashen da ya siya musu sai ga shi ya shigo yana shigowa da sallama bai ko bari na amsa ba ya fara fada yana fadin"Don iskanci kina ji ina ta Hon bazaki iya fitowa ki budemin get ba..?
Ni wlh har ga Allah ban ji ba cikin sanyina nace"Ban ban ji ba wlh..kayi hakuri"
Tsaki kawai yaja ya wuce Shashensa yana fadin"duk kin ji..ai ba hayaniya a inda kike balle ki fake da Lalurarki"
Ina jinsa ban ce komai  ba sai ma kirkiri mirmishi Saboda yaran kada su Fahimci wani abu,ni ke kokarin kauce ma wasu abubuwan ammh yadda Ya ishaq baya jin kunyar tozartani gaban ya'yana in da ina Biyesa da tuni yaran tun tashi da shi a ransu,sai dai in dai suna wajen da ya fara fadansa zan yi saurin ba shi hakuri na nuna komai ba komai ba ne.
Kayan makarantan su nace suje su cire kafin su ci abinci sukace min sun sha tea agidan Mama.
Suna shigewa d'aki ni kuma nabi Ya Ishaq Shashensa kada yace ya dawo nayi banza dashi daman na hada mai abincin sa tuni na kai mai shashensa.
Koda na shiga yana Cire kayan jikinsa sallamanta ma aciki ya amsa min na Rankwafa ina mai Sannu da zuwa ya amsa sau d'aya ya dauke kai ya Tura kofar Tiolet ya shige ni kuma sai na karisa cikin bedroom din na Tattara kayan daya cire na ninke mai na bude Wardrope dinsa na sakamai na gyara mai Dakin Dazu daman saboda bai bar key din bane shiyasa.
Ina Dakin ya fito yana Digan ruwa da Sauri na Dauko mai Towel na basa ya amsa yana Goge jikinsa Lokaci d'aya yana kallon kayan jikina ni kuma ban ma Lura ba wardrope dinsa na Bude ina Fadin"Jallbiya zan dauko maka..?
Kai tsaye yace"Bar shi kawai"
Ban damu ba na rufe na koma gefe na Tsaya kaina na kasa kamar Daga sama naji yace"Ina kika samu wad'anan kayan barcin kuma..?
Shuru nayi kafin nace"Anty..Na..Nasara ta kawo min Tsaraban Um umra."
Tabe baki yayi kafin yace"Shi yasa da zata baki sai da ta zabo kalan da zai yi daidai da yanayin ki.. Green wannan kayan ba su yi ba ammh ke kin ga abun sawa da sunan ki yi ma mijinki kwalliya dashi.."
Sai naji na muzanta duk da ya saba kusheni ammh na yau sai yafi Dafani barin ma da ya kara fadin"Kwata kwata na rasa wani abu ne zaki saka ya Dace dake Fa'iza..Alhamdulillah da Allah ya bani Zeey yarinyar mayar dressing ne komai tasa ajikinta sai kin ga kamar don ita aka Hallici kayan zata zo kuga juna don Allah in kun had'u ki fara D'aukan gyara daga kanta"
Kaina sai da ya yi Dum jikina sai yayi min ba Dadi ammh ban nuna ba kayan jikina na kallah har ga Allah  ni ban ga Aibun su ba kore ai kalan yan aljannah ne sai dai daman shi tozarcin sa ba inda baya tashi.
Da naga zai saka kaya sai na fice abuna na zauna afalo ina jiransa haka ya fito yazo ya zauna ya fara cin abinci sai da ya gama sannan na kwashe komai na kai kitchen na koma nayi mai sai da Safe naga yana waya da Hannu kawai yayi alamun naje ni kuma na fice na koma Dakin yarana na iske Amir na koyama Anun aikin da aka bata a makaranta Musty har yayi barci na gyaramai kwanciya na mai addu'a na koma cikin su Anum na zauna ina ganin abunda suke yi ina mirmishi sai da suka gama na saka Amir yaje yayi fitsari shi da Anum suka kwanta muka karanta addu'an barci atare suka Shafa na gyara musu kwanciya  na rage musu fanka na kashe musu wutar Dakin na fita zuwa D'akina na gyarama Ahmad kwanciya nima na kwanta agefensa ina addu'an barci.
Karfe uku na dare yau na tashi nayi Nafilfiluna sannan na fita naje na tashi su Amir,sai ga Baban su ya fito suka tafi masallaci ni kuma muka yi tamu ni da Anum agida.
Kamar yadda n Saba kafin bakwai din Safe sun shirya cikin kayan makarantar su Ahmad na bayana sai rigima yake yi,Ba ya ishaq zai kai su ba Haruna mai adaidaita ne wanda ya saba kai su  baban nasu yau zai koma Abuja.
Shashen shi suka je suka mai sallama sannan suka fito ni na saka Hijabi na rakasu har waje muka gaisa da Haruna sannan suka shiga suka wuce ina Dawowa a gurguje na had'a ma Ya Ishaq abun karinsa buredi da kwai na Soyamai sai ruwan tea na kai mai Shashensa ya fito cikin shirin Tafiya sanye da Suit bakake ya tsuke kamar ba shi ba har da wani damfararen bakin glass na ba mutumci.
Yana zaune yana karyawa ina Gabansa Ahmad na Hannuna ina Lallashinsa sai da ya gama sannan ya mike yana fadin"Fa'iza zan tafi kuma kila sai satin biki zan shigo.karbi ki ga."
Kudi ya miko min yan Dubu na saka Hannun na karba ina godiya Karamar Jakarsa ya Dauka na mike ina Sabe da Ahmad zan karb'a da Sauri yace"Kada ki damu da wannan..Ki kularmin da yarana in akwai wani abu ki kirani a waya..koda yake nasan zaki kira indai kina da bukatar wani abun"
Nidai ina biye dashi har Haraban gidan Ahmad ya karba yayi masa sumba kafin ya miko min shi Sai da ya shiga mota sannan ya Leko yana fadin"Anty Binta zata aiko miki da kayan fitan biki da wasu kaya da ta matsa sai na siya miki in ma da wani abu zaki ji wajen su Mama na tafi..Ban da yawo..Fa'iza gidan Mama da Gidan Anty binta kad'ai kike da izinin zuwa ki Kiyaye"
Daga haka ya rufe motarsa lokaci daya yana fadin"Ki budemin get"
Haka na tafi zugwi zugwai ga goyo a bayana,na saka karfina na bude mai get ya fice na bisa da Allah ya kiyaye hanya na maida get din na Rufe ina Haki sai da na koma falo sannan na Kirga kudi Naira dubu biyar itama nasan Saboda matsalan yara ne daman duk sati in yazo haka ya ke bar min.
Kuma kafin ya Dawo ta kare ko Kudin motar da nake zuwa gidan Mama ko Anty Binta sannan ga Dawaniyar yara yau Anun tace bata da pensil gobe Amir yace zai siya Drowing duk anan kudin ke tafiya.
Tunda ya tafi sai na maida Hankalina wajen kula da ya'yana Kwana Hudu Tsakani da Tafiyar Ya Ishaq Anty Binta ta kirani a waya mu hadu agidan Mama ranar jumma'a da Safe bayan su Anum sun tafi makaranta na shirya na tafi bayan nace ma Haruna gidan Mama zai kawo su Anum in ya Dauko su daga makaranta.
Naje na iske gida cike da kawayen Mama ana ganin kayan lefen da za"a tafi dasu Abuja agobe.
Akwatuna goma shake da kayan alfarma ni ko Aleda Anty Binta ta bani nawa Less d'aya atamfa biyu sai takalmi sai Hijabi na karba da Hannun Biyu ammh sai Mama ta harareni tana fadin"Naga kin karba a wulakance kin raina ne..?
Kaina na kasa na kasa mgana Hajiya Barira aminiyar Mama tace"To ina Laifi wannan kayan Hajiya Saudatu..?ai wlh naga kokarin Ishaq ma matar farko ai ba kowa ke wani wahalar da kai akan su ba"
Mama ta tabe baki kafin tace"Matar ma irin wannan abar ba.."
Suka kwashe da Dariya suna nuna ni, Anty Binta ta kyabe fuska tana Fadin"In ma ta raina ita ta sani..Kila wad'anan take kalla ai inda suka dace za'a kai su Yarinya ba inda basu dace ba"
Ni dai kazil ban ce ba Saboda suna so naji cin mutumcin su da karfi suke mganar su,Haka suka sallameni na kwashi kayana zuwa Dakin Badariya bata nan tana makaranta.
Ba domin nace Haruna ya wuto da su Anun nan ba da gida zan koma saboda su yasa na jira sai da suka Dawo nazo musu da kaya suka sauya ni nayi girki daman indai nazo to kamar jaka haka take komawa agidan Mama.
Sai La'asar na koma gida ni da ya'yana da kayan da Anty Binta ta bani duka an dinka su daman,Washegari kuma Badariya tazo take gayamin an tafi kai lefe har da Hajiyar Dala da Anty Binta da Hajiya Barira kawayen Mama.
Sai fada take wai ba su sanar da Goggon karofi ba araina nace ita din banza ai in dai su Hajiyar Dala na waje kowa ma bai da kima a wajen Mama.

*Littafin KANA NAKA Book 2,3paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*

*Janafty*
[6/13, 9:25 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
*Book 1*

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

            *🅿️07*

Bayan ta gama fad'an rashin gayama Goggon karofi sai ta koma fad'an kayan da aka bani bayan tace na dauko mata ta gani Badariya karama ce acikin ya'yan mama ammh da ace itace Babba da abubuwa da dama sun gyaru tana da kyakyawan zuciya da Hali mai kyau.
Ina kallonta ta d'aga kayan a rene tana tabe baki kafin tace"Yanzu Anty Fa'iza abunda suka baki kenan acikin Uban kayan akwati goma da suka tafi kaiwa Abuja..?
Duk da ba duka naji mganar ta ba,ammh na dauki wasu,Sannan ina Bin bakin wanda na saba mgana dashi na kan Fahimci abunda yace ko da ban ji ba.
Ban ce mata komai ba sai ma wani mirmishin takaici da nayi,na sani ko Lokacin aurena ya ishaq bai min lefe ba ballatana yanzu ba da bani zai aura ba,Daman a wanchan Lokacin Baba ne ya matsa masa akan sai yayin lefe ba Sadaka ya aura masa ni ba, awanchan Lokacin Mama ta shiga mganar tayi ruwa tayi tsaki akan ita da kanta zata had'amin lefe nagani na Fad'a da ya kara tambayata sai tace tuni ta bama ya ishaq ya kaimun kaya ahalin kaya ko kala goma basu kai ba sannan saukakku dai ba masu tsada ba daman tun a baya na fada muku Baba shi ba magidanci ba ne mai bin diddigin abunda ke faruwa a cikin gidansa ba  shiyasa wani Lokacin Mama kan yi nasara a kansa da kuma kila an yi masa surkullen mutanen yamai.
Ni ban damu ba saboda ba kayan ba ne a gabana, ko su bani ko kar su bani bazai kankare yadda bani da Daraja a idanuwan ya ishaq da su kansu ba.
Har ta gama fadan ta ban bude baki nayi mata mgana ba to me zan ce..?duk abunda zan ce alokacin bashi da amfani Saboda ajiyan agaban Mutane Anty Binta ta kara maimaita Dakyar ta lallaahi Ya ishaq ya amince ya siyamin ma kala ukun da aka bani Domin da farko cewa yayi bazai siya ba Saboda ko ya siya zai yi asara ne ban san Darajan su ba sai da tayi ta basa baki sannan ya amince to saboda mene zan damu..? Awannan gabar da auran mu ya zama jingina ba lalle ne Hakkokina su rataya a wuyansa ba ni ba Dolen sa ba ne yanzu Saboda haka raina ya daina Damuwa kan duk Tozarcin da zai aikata agareni.
Kuma na kudiri araina bazan saka kayan sa ba,Akallah dai zan fara Dogara ga kaina ko Saboda ya'yana na fara Tunanin zamana ahaka bazai yuyumin ba in ya'yansa Dolensa ne,ni na tashi adolensa bazan bar gidansa yanzu ba Saboda lokaci bai yi ba ya'ya na suna Bukata ta, sosai in na tafi na bar su basu da wanda zai kula da su da Tarbiyan su ina tsoron su tashi Cikin maraicin uwa kamar yadda muma muka tashi cikin wannan maraicin muna da uwa a raye ammh kamar bataa raye ne a wajenmu.
Tattara komai nayi na tusa cikin Wardrope d'ina ban kuma yarda nayi mganar da kowa ba Daman Ya Asiya ce kadai take kirana kan Sha'anin Bikin Yaya mariya ko sau d'aya bata kirani ba ita ta na da Zafi ne Ko zuwa tayi had'uwa goma sai sun yi Cacan baki da Anty binta gata irin tanada Sauri Saurin mgana ne kafin Anty Binta ta fadi daya ta maida mata Biyar Shiyasa bata cika zuwa katsina ba sai da Dalili mai girma waya kuma bamu cika mgana ba Saboda abu kad'an zataji ranta ke baci kuma bata da Hakuri ko kada'n.
Biki nata karatowa barayin su Mama suna ta shirin su gayya Mama tayi bani da Gayya ba Domin tace sai yanzu ta san Ishaq zai yi aure ni ina gida bansan halin da suke ciki ba,bani cikin kwanciyar Hankali Saboda ina ta mafarkin Tamadina sai na tsorta kada tazo ta mutu itama bamu gana ba sai na fara Tunanin ya kamata naje na gaisheta na Dubata Saboda mahaifiyata ce in na rasata a wannan gabar sai nafi kowa kuka Saboda dani kad'ai ne bata gana ba.
Na fara Tunanin Tafiya sai dai matsaalan kudi ne Dubu daya da Dari Biyar suka Ragemin a hannuna cikin Dubu biyar din da Ya Ishaq ya barmun da zai tafi sannan Tunda ya tafi ko sau daya bai kirani yaji Halin da muke ciki ni da yara ba nima kuma ban kirasa ba Sai dai na riga na kuduru niyyar zuwa gaida Tamadina Cikin Satin nan da zai shiga kafin Lokacin Bikin yazo.
Na shirya tafiya ta Ranar asabar in su Amir sun tafi Hadda,Shiyasa Ranar jumma'a da Daddare na yi ma Ya Ishaq flashing Saboda wayata ba kati na ma manta Rabon da na saka mata kati ba na kira daman sai dai mai son mgana dani ya kirani bansan adadin Flashing din da nayi masa bai kira ba sai chan naga kiransa na dauka jikina na rawa na saka ta a amsa kuwwa na kara kunne tun kafin nayi mgana ya Dakamin Tsawar da sai da tasa na razana Cikin Fadansa yace"Haba don Allah wai meye haka Fa'iza..? Sai flashing kike yi min tunda kika ga ban kira ba ai kinsan ina wani abu mai muhimmanci ne ko ina tare da wani mutum mai muhimmanci ke duk abunda kika fara Hankali bai isa ya baki ki bar shi haka ba..?
Sai naji kwallh ta ciko cikin kwarmin Idanuwa na cikin rawan zuciya da na Murya nace"Kayi..ka..yi hakuri..Ban..Sani ba ne.."
Karamin tsaki yaja kafin yace"Zan kiraki in na koma gida ina tare da Zeey ne.."
Daga haka ya katse wayarsa ina jin muryanta kafin ya katse tana fadin"Honey kai da waye kake ta Ihu haka..?kamar a kusa da wayar tayi mganar shiyasa na ji ta.
Ban ji me yace mata ba ya katse kiran sai na Sulale gefen gadona na fashe da kuka Allah yasa yaran duk sun kwanta har ta Ahmad yayi barci kuka nayi wanda naji ya isheni nasan bani da wata Daraja a idanuwan Ishaq ammh ban dauka har agaban wacce zai aura ma bani Daraja ba ,Sai na fara tunanin wani irin karb'a amaryan sa zatayi min in muka fara Had'uwa sannan me ya fada mata akaina..?
Wata zuciya ta amsamin ya fad'amata ke bakomai bace face bebiya mummuna baka mara gata sannan mara ilimin zamani wacce bata da komai atare da ita tuna haka yasa kuka na ya karu bansan tsawon Lokacin da na Dauka ina kukana ba sai da nagaji sannan na tashi na Shiga Tiolet na wanke fuska ta na fito na k'i yi barci ina jiran kiransa na riga na sakama raina Gobe zan je na Duba Tamadina kuma ba yadda zan iya tafiya batare da izininsa ba..
Bai kira ba sai wajen sha d'aya da Rabi na Dare sannan ya kirani ina D'auka fada ya hauni da shi wai ni bai san me nake yi ba sannan bani da Hankali komai ba cikin lissafi nake yi ba ni dai Hakuri nayi ta basa sai da ya sha iska ya gama wulakacin nasa sannan yace"Ina yara na..? Ina fatan suna nan cikin koshin lafiya ko..?
Nayi saurin amsa mai da suna lafiya jin nayi shuru yasa yace"Fa'iza fadi abunda yasa kika addabeni da Flashing ina da shiga office da Safe zan kwanta akan Lokaci"
Cikin yanayin mganata nace"Da dama..Ina so ne gobe naje Dutsenmah na Duba Tamadina"
Cewa yayi bai ji ba na sake bud'e muryanta na kara gayamai sai kawai yace"wacece haka..?
Ban yi mamaki sanin Waye Ya ishaq kai tsaye nace"Babarmu.."
Karamin Tsaki yaja kafin yace"Daman nasan bana ganin kiranki sai wata Bukatarki ta taso miki Fa'iza baki da wani Amfani sai kina da bukatar wani abu..me akayi da kike son ki tafi..?
Kai tsaye nace"Tayi rashin lafiya ne ni kad'ai ne ban je na Dubata ba"
Kyafci yayi kafin yace"Kada nace bazaki je ba kice na hanaki ganin mahaifiyarki Allah ya kiyaye hanya..Sai dai kada ki kuskura ki tafin min da yara na gidan da ba wanda yasan su, salon suje suna Rab'e rab'e ke kanki ai araben zaki je Ahmad na amince kawai ki tafi dashi Shima Saboda yana shan Nono ne"
Ban damu ba nace"Eh daman suna Hadda haruna in ya Dauko su in ban dawo ba gidan mama zan ce ya kai su"
Da Sauri ya tasomin yana fadin"Au Dare ma zaki kai?ko nufin ki Daman chan zaki kwana..?
Cikin daburcewa nace"A"a..Dama..Dama ina so na Biya Karofi na gaida Goggo ne"
Kai tsaye cikin D'agawar Harshe yace"Ban amince ba..Ban kuma baki izinina ba..Dutsemah kadai zaki je shima Dubiya ce in kika Kai dare Fa'iza wlh sai ranki ya baci..Wato ki je a had'u ayi ta gulmana ana zagina nan Goggon karofi ta kirani tana min Fad'a duk akan ki wai in nayi aure  kada na wulakantaki to in tana ganin ban taimake ki ba meyasa sanda Baba ya nuna zai Aura min ke bata famsheni ta aura miki Isa ba..?karewar tana kaunarki da Tausayin ba..bana son Rainin wayau kada ki sake naji kin taka Karofi in kuma naji wlh tallahi kin ji Rantsuwan musulmi Fa'iza zaki ga Other side of me da baki Taba gani ba.."
Hawaye wani na koran wani suke zuban min cikin wani yanayi nace"Ko gidan Ya..ya mariya..?
Dogon Tsaki yaja kafin yace"Ita kuma wannan na yi miki iyaka da ki kara Takawa gidanta tunda bata da mutumci bata da,kunya har ni nan zata rika gani na, tana min kallon banza kamar taga kashi..?,Sannan naji Labarin ta raina Mama ta kuma raina Anty Binta har sa'insa tana yi da ita in dai ni ke auran ki kin bar kara taka gidan da ake cin zarafin Uwa ta da yayata sannan itama ki gayamata kada ta kuskura na kara ganin kafarta agida na in kuma ta bari muka Hadu sai na Koreta wlh"
Daga haka kit ya kashe wayar sai nayi sororo da waya a Hannuna Hawayena suna D'iga a saman wayar gefen gado na koma na zauna kukana ya kasa Fitowa sai dai Hawayen kawai ina Tuna mganganunsa in ya zagi Yaya mariya bazan damu ba Tunda har Goggo bata tsira ba awajensa ni Ya ishaq daman ya saba kirana da duk sunan da yaga Dama,na yarda yace ban da amfani sannan bana Kiransa sai in ina da Bukata Saboda tun farkon fara aikinsa a abuja ina kiransa Ranar ya Dauka ya yi min  fata fata yana min ihu akan  me zan rika Damunsa na D'auka Abuja irin katsina ne..?
Abuja yana harka da Mutane Dabam Dabam bazai zo cikin jama'a yana wage baki da murya Saboda mgana dani ba kada na kara kiransa kada na kunyatasa watarana cikin jama'a Tunda ga ranar ban kara gigin kara kiransa ba kada na kunyatasa kamar yadda yace d'in sannan Halin ko in kula da ya nuna kan Tamadina bai Dameni ba Domin bashi ba ne na farko ba kuma Kila bazai zama na karshe ba.
Tunda ya ke aure na bai Taba taka gidan da Tamadina ke aure da,Niyyar gaida mahaifiyata ba akwai wani zuwan da mukayi karofi bayan Haihuwar Anum ne da Mama da shi a motar abokinsa Dakyar ya aminnce ya biya dani zan kai mata Anum saboda sanda aka haifeta bata zo ba Shima din Sai da na roki Mama ta saka baki ya Biya  dani ammh K'iri k'iri yaki bari na shiga da Amir sannan Daga shi har Mama suka ki' shiga Gidan suka tsaya a mota ni kuma ya bani Minti goma.
Ina shiga ko zama ban yi da kyau ba ya fara Hon ta na rike da Anum a hannunta ni na fad'amata tare da su Mama muke bata damu ba tayi Lullubi ta fito har kofar gida suka gaisa Ya ishaq kuma ki'ri kiri yak'i fitowa Daga mota Mama ce ma ta fito suka gaisa duk yadda Tamadina taso ta Dauki Amir ya ishaq ya ki fitowa da shi yana rike dashi,Sannan ya hanani komawa cikin gidan ko cikakken gaisuwa  bamu yi da ita ba yace na shigo mota mu tafi da nace bamu gaisa ba sai yace sai dai ko na san yadda zan yi na Dawo gida wlh in ya tafi bazai dawo ya Daukeni ba.
Ina ji ina gani na shiga mota  bayan Tamadina ta bani Anum,Tana d'agamin hannun idanuwanta sun cika da kwallah,ni kaina kwallar ta kawo cikin Idanuwana da Dubara na share mun D'auki Hanya Ya Ishaq ya juyo yana fadin"Tab Mama ashe kice Allah ya Dubi Fa'iza da idon Rahma ana jin mganarta har ana gane me take fad'i naji Babarsu ba'a ko jin abunda take fadi sai uban Ihu kawai ake ji tana yi"
Da Dauri na Dago ina kallonsa shi kuma ko ajikinsa maimakon Mama ta kwab'amai a'a sai cewa ma tayi"Eh mana ai uwar su ce ainihin Bebiyan Sai dai kaji tashin Ihu nan kuma wai mgana take yi"
Ya Ishaq yayi dariya yana kallona kafin yace"Allah ya taimake ki Fa'iza da yanzu kema ihun kawai zamu rika ji"
Daga shi har Mama Dariya suka saka har muka iso gida ina kuka Tozarcin ya tashi daga kaina da yan'uwa ya koma Har kan mahaifiyata shiyasa abunda yayi yau ba zame min Sabo ba sai dai shi Tozarci baka Sabo da shi ko yau aka yi maka shi sai kaji ba Dad'i.
Ban karaya ba sannan na yi kudurin sai naje shiyasa da wuri na tashi na shirya yara suka tafi Hadda sannan na yi wanka na shirya Ahmad Na fara Tunanin me zan kai mata bani da komai ban ijiye ba sannan ban bama wani ajiya ba ina bakincikin wannan Rayuwar da nike ciki ko da bani da shi akwai Hakkin uwata a kaina sannan wazai amince bani da shi Tunda kowa yasan Ya Ishaq nada Rufin asiri sanna  ba kowa yasan yanayin Rariyar ba ballatana yasan yanayin zubar ruwanta ba Nasan Su Yaya mariya suna iya bakin kokarin su ammh suma ai ya'yanta ne kamar yadda nake yarta akwai Hakkin kyautata mata a wuyana.
Da na rasa abunda zan kai mata sai na D'ibar mata garin rogo wanda Ya Ishaq kan siya saboda yara in yaga Dama sannan shima yana son gari da siga,sabulin wankan mu ya kusa karewa sai na Dibar mata na wanki da na Klin,sai na Daukan mata Maltina guda hudu na kulle aleda ina da Burin ko kaya na bata ammh bani Dashi sannan bazan iya bama mahaifiyata tsohon kayana ba kamar na ci mata mutumci ne.
Sai nayi Hakuri na Dauki iya abunda nake da shi koda goma tayi na isa Dutsemah sai dai Tamadina ta ganni kamar Daga sama Allah Sarki Uwa bakinta yaki Rufuwa ta rasa ina zata sakani Saboda Murna taji Sauki Sai dai kafafun sun kumbura abokan zamanta sun ce Daga dare zuwa Safe ta tashi da Kafafu a kumbure ana ta dai shafa mganin sanyi.
Tunda muka zo ta kama Ahmad ta goya ram a bayanta sai kallonta nake yi farinciki ya cikani ta tambayi su Amir nace suna makaranta tace meyasa ban kawo su ta ga yadda suka kara girma ba..? Idona ya ciko da kwallah ya'ya na ne suma ammh bani da iko da su ballatana mahaifiyata tayi iko dasu suma dai  ce mata kawai nayi zan kawo su watarana.
Abokiyar zamanta Maman isuhu suke kiranta tayi danwake ta kawomin naci abuna muna ta Hira Da Tamadina duk da mganar nata sai a hankali ammh mu ya'yanta da ta zame mana Dole muna ganewa ni dai ban gayamata wani abu da zai tada mata Hankali ba ko mganar auran Ya ishaq ban mata karfe biyu nayi na tashi na fara shirin tafiya bayan nayi sallah na bata abunda nazo da shi ta Dafa kaina tana ta sakamin albarka.
Ta bani Ahmad na goya a baya na,na saka Hijabina nayi ma mutan gidan Sallama ta rakani har zaure tana D'ingisawa ina ta koma sai tace sai ta Rakani mun yi sallama kamar kar mu rabu har zan tafi ta riko Hannuna na Juyo ina kallonta ta kuramin ido sai naji jikina yayi sanyi cikin mamaki nace"Manene ke faruwa Tamadina..?
Kawai sai ta Dafa kaina ta jijjiga nata kafin tace"Kiii....yi....hakuri..Fa'iza..!
Sai naji raunina ya bayyana da Sauri na kauda kaina ina Boye hawaye na kafin na gyada kai ina fadin"In sha Allahu..Allah ya baki lafiya"
Daga haka muka yi sallama har na kule tana Dagamin Hannu.
Tunda bai amince na biya karofi ba Daganan ma hau motar katsina,na koma gida hud'u saura sallah kawai nayi na fara kokarin dora girki Saboda yan makaranta ammh gabadaya sai ina jin jikina duk yayi wani irin sanyi komai nawa yayi sanyi kamar an zare ma jikina lakka.
Ko su Amir da suka Dawo makaranta sai da suka ga yanayi na Amir mai wayon ciki ne ya dinga ce min"Baki da lafiya ne Umma..?
Sai nace mai a'a saboda kada na tayar musu da hankali sai na warware na shiga cikin su mukaci abinci bayan sun gama mukayi sallar isha'i tare bayan mun idar nayi musu karatun Qur'ani na kara ma kowannen su inda ya ke sannan nace su yi na makarantan bokon su da aka basu amatsayin aikin gida.

****

Tunda Ya ishaq ya tafi bai Dawo ba sai ana Saura kwana uku D'aurin auran sa,sannan ya Dawo shima din gidan Mama ya sauka sai Dare na gansa,gari kuma na wayewa ya kara fita Jamal ya Dawo tare naga suna ta zirga zirgan karbo dinkuna Gidan Mama kuma ya fara cika da baki Badariya ta fadamin Hajiyar Dala ta iso tun jiya sannan da yan'uwan Mama na yamai ni dai ta barayina bana wani shiri Saboda ban ga abunda zan shiryamawa ba.
Ana jibi Daurin aure da yammah sai ga Anty Mamah da Halisa sun zo gida na karb'e su hannun Biyu Saboda suna da kirki Har Halisa ba ta Dauko Halin Anty Binta ba.
Na kawo musu ruwa kenan na zauna muna gaisawa,ba islamiya Saboda alhamis ne Su Amir suna gidan Mama dazu da Jamal ya kawo wasu kayan Shahen Ya Ishaq ya tafi da su Ahmad ne kad'ai tare dani.
Bayan mun gaisa Anty Mamah ta kalleni sama da kasa har sai na Tsargu ina sanye da Riga da zani na atamfa da dankwali kaina na maida kasa ga Ahmad bayana na goya shi.
Anty mahma ta bude murya tana Fadin''Fa'iza ina kunshi ina gyaran kai..? Haka za'a dauko miki amaryan a ganki yarkace yarkace.?
Ban ce komai ba saboda basan me zan ce musu ba  halisa tace"Ko Saboda ba anan Amaryan zata zauna ba ne shiyasa kika zauna ba wani gyara..?
Anty Mamah tace"Wannan ba Hujja ba ne..ya kamata ko kunshi tayi saboda gyaran kanta da kanta Halisa"
Ni dai kaina na kasa ban ce komai ba kamar daga sama sai da ya Ishaq ya shigo Gidan yana waya kamar Sauri ma yake yi Anty Mahma ta tsaida shi ya katse wayar yana Fadin"Mahma jira na fa ake yi a waje"
Da Sauri ta mike tana fadin"Ya ishaq me zan gani haka Uwargida ba kun shi ba gyaran kai anya zakayi adalci kuwa..?
Kallona yayi sama da kasa ina ganinsa ta kasan idona sannan ya kwashe da Dariya kafin yace"Tab a bakin Fatar Fa'iza daman in akayi mata kunshi zai fito?
Ba ni kad'ai ba hatta su sai da mganar ta musu wani yam!
Ina gani suna kallon juna ita da Halisa suka kuma kalleni sai na nuna kamar ban ji me yace ba,menene sabo acikin mganarsa a wajena a wajen su ne sabo.
Anty Halisa ne tace"Kai Uncle akwai ma wadanda suka fi Fa'iza bakin fata kuma suna kunshi ko ita da kake ganin bakinta ka saki kudi a sama  mata mayuka masu kyau da Tsada kaga yadda Fatarta zata goge tayi Fresh kamar ba ita ba,ko Anty Mahma"?
Kai ta gyad'a kafin tace"Sosai ma yadda mayukan gyaran jiki da na fita suka cika Duniya ai da yawan mata ma ba Farin fatar su bane karawa suke da kwaskwarima"
Baki ya tabe kafin yace"Haka kurum na ba'ta kudina kan wannan abar."
Ya fada ya nuna ni da baki kafin yace"ko an yi mata ba kyau zai yi ba asaran kudi na kawai zan yi sannan ku daina cewa wai farin wasu har da kwaskwarima na Zeey din'a  Inganttace ne babu algus,daga mahaifiyarta har mahaifinta Haifaffun Fulanin Adamawa ne"
Halisa tace"Uncle baka taba nuna mana Hoton ta ba"
Ina kallom su ya duba a waya ya nuna mata ta kallah ta kara kalla kafin tace"She is so Beautifull"
Baki ya washe yana jin Dadi Anty Mahma ya mikamawa ta karb'a tana Fadin"Hoto ba zahiri ba ne sai mun ganta ido da ido.."
Dariyan jin Dadi yayi kafin yace"Zaku ganta sati uku zamu yi zamu zo gaisheku in sha Allahu"
Sukace Allah yasa Daganan ya shiga Shashensa ya Dauko abu a leda ya Sake fita suma basu Dade ba sukamin Sallama suka tafi Anty mahma dai kallona kawai tayi tace min kiyi hakuri Fa'iza nayi mata mirmishi kawai ban ce komai ba.
Washegari sai ga Yaya Asiya ta Diro ita da Hafsah da Anty Nasara Goggo karofi ta rantse tace bazata zo ba Tunda dai Mama bata gayamata ba ayi sha'ani Lafiya.
Goggon karofi ta basu kayan miya da yawa sun zo min da shi,Sannan Yaya Asiya ta zo min da kayan kamshin girki da su kori saboda sana'ar da take yi a chan kano kenan Anty Nasara tazo min da less sabo dinkin Buba mai Tsada ta dinkamin kamar in yi kuka Allah Sarki dan'uwa mai rana.
Hafsah kuma ta tsifemin kai ina ta cewa bazan yi ba Anty Nasara tace"Zauna fa'iza ta tsefe miki ki wanke sai ayi miki kitso ki gyara jikin ki ba domin auran da mijinki zai yi ba Sai Domin kema kiji Dadin jikin ki"
Mganar ta yasa na zauna ta tsefemin kai Ahmad na Hannun Yaya Asiya su Amira kuma Daga makaranta basu Dawo gida ba da Jamal ya Dauko su da Motar Babansu gidan Mama ya sauke su tunda naji su shuru.
Ina ta tambayan su Ya mariya sukace zata taho dinki ne ba'a karisa ba ta tsaya karbowa
Da daddare kuma sai gata lokacin har Hafsah tamin kitso tana min yanka Salatif din da zata zana min dayake tana koya,Ko da Yaya mariya ta iso sun wanke kayan miya har sun bada nika sun tafasa sun tambayeni Cafanen girki nace bai bani komai ba kuma bai ce komai ba.
Yaya Asiya tace"Fa'iza kuma baki mai mgana ba..?
Anty Nasara tace"Ban da abun ki Asiya sai tayi mai mgana ai yasan ya kamata..?
Yaya mariya na gefe ta tabe baki bata dai yi mgana ba hira suka cigaba da yi bayan sun bar mganar acikin Hiran ne Yaya mariya tace ita ta fadama Tamadina Ya ishaq zai kara aure tace mata naje ammh ban fada mata ba Cikin Sanyina nace"Kawai sai na fada mata mijina zai kara aure..?
Duka sai suka kalleni Cikin Tausayawa ammh basu ce komai ba
Sai Dare Ya ishaq ya shigo gida Daman ina ta fargaba,ban san wani Rashin mutumci zai yi ba in yaga Yaya mariya agidan ba,Aiko da ita ya fara cin karo ta fito daga dakina,kallon kallon suka yi ma juna ni kuma ina falo zaune kafafuwana cikin leda Tunda an saka Lalllin,Hafsah ke gefena ta na sakamin na Hannu,jikina ya fara rawa bana so ya wulantamin yar'uwa,Hafsah ce ta gaishe shi ya amsa kamar bai santa ba Yaya mariya kuwa kamar bata gan shi ba haka tazo ta wucesa Ina ganinsa ya Dago yamin wani kallo ni kuma sai na sadda kaina kasa jikina na rawa fitowar su Yaya Asiya yasa bai yi mgana ba suka gaisa har zai shige shashen shi Anty Nasara tace"Ishaq wai me zamu dafa ne na taron Fa'iza gobe..??mun zo mun ga ba komai na cefane ko a wani waje za'a Dafa abincin namu ci ne kawai..?
Ta karishe fad'a cikin Zolaya kansa yasosa kafin yace"Na sha'afa ne ammh bari zan kira Mama ko Anty Binta"
Daga haka ya shige Ciki ya bar mu nan suka bisa da kallon mamaki,Ni dai gabana sai fad'i yake kada ya yi Tijaransa a gabansu,Kunshin da na saka ya Ceceni Domin sai chan Dare na cire sa kuma ya riga ya kwanta sai ban nemesa ba na yi sallar isha'i nayi shirin kwanciya ni da Yaya Asiya muka kwana Daki d'aya Yaya mariya da Anty Nasara da Hafsatu suka kwana Daki d'aya.
Kwana tayi bani baki da Shawarwari ina jinta kuma ina Dauka kalmar dai guda Dayace nayi hakuri to in ban yi hakuri ba ya zan yi..?
Da Safiyar ranar asabar karfe tara na Safe tawagan ango da waliyansa suka mika ko sallama Ya Ishaq bai min bai,bai kuma barmin komai ba,ina wanka naji su Anty Nasara na mganar sun fita shi da Jamal,a tunanin su zai dawo sai zuwan Badariya ta tabbatar da sun mika Hanya kuma ba dawowa zai yi ba Tunda chan amaryan zata zauna.
Ban yi amfani da kayan da Anty Binta ta bani ba Domin Yaya Asiya ma ta dinkama na atamfa mu hudu har da Hafsah dinkin ne Yaya mariya ta tsaya  ta karbo mana.
Ganin har sha Daya tayi kawai sai nace su Dafa sauran shinkafar data ragemana Daman bata wuce tiya hudu ba Tunda Ya ishaq din bai ce komai ba kayan miya kuma sai suyi miya dashi Yaya mariya sai fada take tana fadin"Haba aiko Dai darajan kashin miya ma samu"
To kafin ma a tashi a d'aura sai ga Anty Binta tazo da mganar chan gidan Mama zamu koma ayi bikin gabadaya.
Yaya mariya ta Daka tsalle tace wlh ba wanda ya isa shikenan saboda sun maidani banza a banza taron ma ni da Dangina sai an yi min iko da shi.
Anty binta ko taki tafiya tace kafarta kafarmu ai nan din da gidan Maman duk D'aya ne
Su Yaya Asiya suka shiga tsakaninsu ammh sun fara cacan baki,nayi kuka kukan bakinciki da wannan tozarcin da aka shiryamin Yaya mariya tayi rantsuwan bazata je gidan Mama ba,ko sallama haka ta Dauki kayanta ta wuce karofi ni da Yaya Asiya sai Anty Nasara da Hafsatu dake goye da Ahmad muka tarkata zuwa gidan mama a ka kulle gidan key din ma na Hannun Anty Binta.
Dakin Badariya muka sauka Saboda nan muke da Daraja,kallon mutumci cikin Dangin Mama ko kawayenta ba wanda yayi mana gida cike da mutane sai harkan arziki akeyi su Amir sun shige cikin yara sa'o'in su suna ta wasa Anum ta saka anko Mutsy kuma kayan yan kanti Amir dai ban gansa ba Anum tace dashi Uncle Jamal suka tafi.
Abinci ma sai chan da Rana aka kawo mana shima sai da Anty Mahma ta shigo ne taganmu baki bude tace an kawo mana abinci mukace a'a ita ta fita ta samo mana waina da Jallop din shimkafa sai alala.
Duk yadda naso na Daure ma wannan wulakancin na kasa har ta su Yaya Asiya abun ya tabasu suna tare dani sun kasa fita Hafsatu ce Badariya ta jata.
Kawayen Mama sai dai su lekomu suna Dariya a wulakance,sanda yan Daurin aure suka kira sukace an Daura aure haka Anty Binta ta rika rangad'a gud'a ita da kawayenta itama Mama ance har da rawa sai da ta taka Anty Nasara ta kalleni ina ta sharan kwallah ta dafani kafin tace"Ki yi hakiru Fa'iza ki bar kuka..Watarana sai Labari"
Yaya Asiya abun ya ciwota sai ta kasa ma mgana har da kidan kwarya sai da yan yamai sukayi sannan da Daddare suka kure kid'a da wakar Bikin Ishaq da zainab suna rawa ni dai ina kan sallaya tun bayan da nayi sallar isha"i ban Daga ba ina kai ma Allah kukana.
Washegari ma Anty Mahma ne ta kawo mana kosai da koko muna gama karyawa su Yaya asiya suka yi Haraman Tafiya na kallesu a marairaice kafin nace"Tafiya kuma zaku yi..?
Yaya asiya tace"Kiyi hakuri Fa'iza ya zama Dole ga Hafsah nan ta zauna sai gobe sai ta dawo mukan yau zamu tafi in sha Allahu"
Ban hanasu ba domin suna da gaskiya gwara kayi nesa da in da ba'asan Darajan ka ba.
Da zasu tafi har Dakin Mama sukaje sukayi mata fatan alheri Hajiyar Dala bata ta nan da ita aka tafi Abuja ita zata tarbi Amarya ance suna hanya yau zasu dawo.
Mama sai mgana take har tana fadin"Nasara goggon taku dai taki zuwa to ku shaida mata an daura auran ba'a fasa ba"
Su dai basu mayar mata da mgana ba suka musu sallama suka kama Hanya ransu ba Dadi.
Naso aranar na koma gida Anty Binta tace ban isa ba,Sai an watse taro Sai Yammah mutanen abuja suka Dawo Hajiyar Dala murya har waje ta na bada Labarin gidan arzikin da Ya Ishaq ya nemi aure tazo da Turamen tamfa na iyaye guda goma da kayan gara mota guda har da shaddodi da kuloli kayan uwar miji da Uban miji Robobi cike da kayan fulawa har da nakiya da alkaki.
Nima Anty Binta ta kawomin alkaki da Cin cin,Sai kula mai biyu guda daya na karb'a na saka albarka a bakin Badariya nake jin har da Turmin Atamfa akace abani Mama ta Dauke tace ba za'a abani ba araina nace ko an bani bazan Daura ba ai ban dace da kayan alfarma irin shi ba da su yafi Dacewa.
Agidan muka kara kwanaa sai Ranar Lahadi da yammah muka koma gida bayan ni da Hafsah mun zage mun gyara gidan Mama tas sannan Anty Binta ta bani key din gidan na Tattara duka ya'yana  muka koma gidana Hafsha kuma nace ta bari sai washegari sai ta tafi."

*Littafin KANA NAKA book 2,3 paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*



*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewa book:Jamilaumarjanafty*

*Nagode sosai da addu'o'in ku ga kawu Madalla da ku naji dad'i Allah ya amsa, shi kuma kawu Allah ya jaddada rahma a kabarinsa Ameen summa Ameen.*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT Y'A SKWATO__SAKINA HASSAN 08066726866

INA MATA Y'AN KWALISA MASU SON GYARAN JIKI MACCE DA TASAN KANTA KULLUM CIKIN GYARA TAKE

INA MATA MASU FAMA DA RAMA KU KINSA KAYA BASU KAMA JIKIN KI 😫

INA MATAR DA ADDA JIKI BAKI DA HIP BAKIDA BAYA IN KINYI DRESS BAYANKI A SHAFE

INA WADDA KE FAMA DA ZUBEWA NONO KU KE BAKI JIN DADIN GANIN SU KAMAR SILIFAS

KINYI TA GYARAN BRST HAR KIN GAJI HJY TA GYARAN BRST WAHALA GARESHI DUK WADDA TACE MIKI GA MAGANIN BRST DA SHA ZAIYI TO KARYA TAFADA MIKI GYARAN BRST YANA SON JUREWA DA DAGEWA IN KIN FARA BA'A TSAYAWA INSHA ALLAH SAI KIGA SUN ZAMA NORMAL

MUNA DA INGANTATA ZUMA BRST DA MUNKA SARRAFA DA KAYAN ORGANIC HERBAL SU MACA DASU AGUAJE WADDA INDAI KIN RIKE TA INSHA ALLAH ZAKI GA SUN CIKO SUNYI KOSHI RUBA 2 KU 3 SUN ISA YAZAMA MIKI YADDA KK SO 4K

MUNA DA GARIN HIP DA BRST YAKE GYARA DA GYARAN JIKI DA KARIN NIIMA YAKE YI 4K

MUNA DA INGANTATA ZUMA TA HIP ITA MA MUN SARRAFA TA DA KNGAN TATUN KAYAN ORGANIC HERBAL DA KE FIDDA MIKI HIP 6K

MUNA DA ZUMA KIBA WADDA ZAKIYI FRESH DA BULBUL ITAMA RUBA 2 KU 3 ZATA YIMIKI YADDA KK SO 2K

MUNA DA GARIN GYARAN BRST DA KARIN NIIMA SHIMA GUDA 2 KU 3 ZAKI SHA 2K

GASKIYA DA AMANA ITACE NASARAR.MU

MUNA AIKA KAYA KU INA CIKIN YARDA DA AMINCI

MMN MUJAHID __SAKINA HASSAN MUNA SOKOTO DA KEBBI 08066726866

        *🅿️08*

Da muka koma gida na zame jikina na shige daki nayi kuka na rarrashi kaina daga baya ranar ban yi moruwa ba ina kwance acikin d'aki ina Tunanin makomar rayuwata,Yaran suna tare da Hafsatu har ta ko da Ahmad Amir ne ya dame ta da Ina Umma sai tace na kwanta bana jin dad'i ne tunda taga yanayi na.
Ita ta yi musu girki cikin sauran k'wayanim taliyan da suka rage mana ta dafa sai ta dib'i Tumatir din nan Tafashasshe tayi miya da shi suka ci ta zubomin nace ta dauke sa bazan iya saka wani abu aciki na ba.
Tare da yaran suka yi ta burumtun su afalo ina jin su kafin ta yi musu shirin barci ta rakasu d'aki suka kwanta Ahmad kuma tayi mai wanka sannan ta kawo min shi ya fara rigima na bashi Nono sai yayi barci ni kuma na Rarrafa na tashi na yi alwala nayi Sallar mangariba da isha'in da kasalan Rayuwa ya danne ni na kasa tashi.
Washegari tun safe Hafsah ta shirya bayan su Amir sun tafi makaranta Haruna mai adaidaita na roka ya kaita inda ta hau motar Karofi,ta barni Dagani sai halina acikin gidan da bansan makomata ba.
Tun kuma bayan tafiyarta ban karaji Daga kowa ba hatta Yaya Asiya bata kirani ba Daman goggo nasam tayi Fushi ga abunda kuma daman ya sake Faruwa nasan tun kafin su Anty Nasara su koma Yaya mariya taje mata da Labarin komai.
Harta bangaran su Maman ba wanda ya kara nema na ballatana ace bari a kaga Halin da nake ciki ni da ya'ya to wanda ma Hakkinsa ke kan mu ai bai Damu damu ba ballatana wani ya nuna Damuwarsa a kanmu.
Tunda bayan auran Ya ishaq da Abar kaunarsa ban kara jinsa ba bai kirani ba kuma bai min sakon kudi ba an wayi gari bani da ko sisi a hannuna.
Na shiga damuwa ga shi kayan abinci duk sun kare daga shinkafa sai sauran Taliya ta ragemin Indomie ta kare saboda ina dafa musu sau biyu a sati suna tafiya da shi a makaranta sau ukun kuma na dafa musu taliya Ranakun Hadda kuma sai na Dafa musu shinkafa,Doya da Dankali Sun kare kwai daman kires daya yake siya nama daman ba Cefanen sa ba ne sai in yana gari ne yakan siya in baya gari kuma sai abunda ya zama Dole a garesa.
Lemun yara na makaranta ya kare harda kayan Tea komai ya kare, sauran maltinan da ya siya tun wanchan dawowar na rika basu suna tafiya itama tazo ta kare na koma Hada musu biskit guda biyu suna tafiya da shi Saboda makaranta sai uku ake tashi ana kuma tashi akwai islamiya ana shiga,asabar da Lahadi kuma Tahfez duk makaranta D'ayace sai biyar suke shigowa gida akwai yunwa da gajiya ga yara kanana tunda su basu wayon su fahimci babu ba ballatana su yi hakuri.
Sati biyu da auran Ya Ishaq Dubarata gabad'aya ya kare na zauna nayi lissafin zama a haka bazai haifarmin da D'a mai ido ba dole na mike na nemi sana'a ba domin ni kaina ba sai Domin Ya'yana su Dogara dani.
Na fara Tunanin sana'ar da zan yi sai komai ya kwancemin me na iya..?
Babu abunda na iya sai girke girke shi kuma in ba aikatau zani nayi ko agidajen mutane ko gidajen masu abinci na kan hanya bansan ina zani ba Kuma in wannan ne Ya Ishaq bazai taba barina ba ko ma ya barni Mama sai ta Dakile duk wani abu indai na Cigaba ne Daga bangarena.
Nagama Tunanin ko na samu sana'ar da zan yi ai bani da jari shima din wata mganace mai zaman kanta sai na Saki wannan Tunanin na fara Tunanin yadda zamu kwashe da Anum gobe litini in zasu tafi makaranta bana jin Amir shi ya fi Anum natsuwa ita kam sai a hankali ita da Mutsy tunda yara ne kanana a kan Amir din.
Tun da na tashi a sukuku na dinga yin musu komai inda Allah ya taimakeni tun wannan kayan miyan da su Yaya Asiya suka zo min dashi nayi miya dashi sauran kuma na sakashi cikin karamin Fridge d'ina shi nake diba kad'an kada'n ina amfani dashi Taliya ta kare itama sai na Dafa musu farar shinkafa da miya na zuba musu kowannen a basket din su bani da biskit ba lemu ballatana na Had'a musu da shi kamar yadda suka saba.
Ni da kaina na zauna ina goye da Ahmad da yaki kwanciya sai rigima yake yi,kamar ya tashi da zawon hakori ne jikinsa duk ya saki,Haka na rika bama Anum da Musty abinci nan a baki Amir kuma yana ci da kansa bayan sun gama rigima bai tashi ba sai da Anum ta duba basket din ta ba Biskit ba lemu sai ta fasa kuka ina zaune ina kallonta baki na sake kawai ina kallonta a kasan raina naji bacin rai kawai yana taso min daman ina jin Haushi yadda Anum ta koyi shagwabar banza abu kadan za'ayi mata sai kawai ta fashe da kuka wani Lokacin har da birgima.
Mikewa nayi dakyar bata sani ba sai dai kawai taji saukan mari sai tayi tsit na kalleta raina a bace cikin fada nace"Ki ka ka..ra..min kukan banza anan sai nayi miki dukan tsiya zan baki Babu ne Saudatu..?.
Na kirata da ainihin sunanta sai ta kasa mgana ta koma ta zauna ana son kara fashewa da kuka tana jin tsoro Amir da Musty sai suka tsorata suka koma suka lafe a zaune idanuwansu ya ciko da kwallah ganin yanayin su sai Tausayin su da tausayin kaina ya kamani na koma na zauna na jawo Anum jikina na Rumgume ina share mata Hawaye.
Ta lafe ajikina tana sauke numfashi sai na Fahimci yara irin su Anum basa bukatar tsawa ko fad'a ko Duka a jasu ajiki sannan a lallashe su cikin yanayin mganata na fara lallashin ta ina fadin"Anum biskit din ku ya kare da lemu kuma bani da kudi ki yi hakuri ku tafi in na samu zan siya muku."
Ta dago idanuwanta da alamun kuka tace"Umma Daada fa ya na ina..?
Sai na kasa bata amsa Amir ne yace"Daada na Abuja"
Mamakin sa ya kamani a ina yaji Babansu na Abuja wata zuciyar ta fadamin zai iya sani ai baban nasu na zauna yayi hira da su kamar manyan yara.
Ni dai na samu na Lallashe su suka tafi hakanan na dawo na zauna tayi Tagumi ina tunanin in yau sun hakura gobe fa..?
Ko Badariya da kan lekomu lokaci bayan Lokaci itama shuru naji ta ni ba kudi a waya ba ballatana na kirata,Ina gane lambar kowa saboda da ajami na Rubuta na iya rubutu da Ajamin labarci tunda Hausan ban iya ta sosai ba, ba komai nake ganewa ba.
Haka washegari ma Dakyar Anum da Musty suka yarda suka tafi a makaranta ba biskit ba Lemu,na rasa yadda zan yi da su,kuma ko giyan wake na sha bazan taba kiran ya Ishaq nasan sauran abunda zai biyo baya shi da ya ijiyemu bai Tuna damu ba sai nice zan neme sa,ai ko bai neme ni ba sai ya Tuna da ya'yansa ya Tuna da Hakkin kula da komai nasu yana wuyansa ne ammh bai iya tunawa da wannan ba Tunda ya samu Cikar Burinsa bai damu da komai da kowa ba ni tunda ya jingine ni sai ya tuna da ya'yansa tunda su bai jingine su ba.
Hakanan na cigaba da lallab'a rayuwata yadda Allah ya tsaramin Tun su Anum na rigima har suka zo suka Hakura,Sai kuma suka fara Damuwa da ina Daada bai taba Sati Hudu bai zo gida ba sai wannan karon in suka tambayeni ina Daada kasa mgana nake yi in suka Dameni sai nace ya kusa dawowa aiki ne yayi masa yawa Ranar da Dadaddare bayan mun gama sallar isha'i suna zaune suna aikin makaranta da aka basu Amir na taya mutsy nayi na shi Dayake shi yana primary 1 ne Anum Nursey 2 take Musty kuma Nursey 1 ni ban yi boko ba,ban san komai a bangaran su ba sai dai ina gane wasu abubuwa  na y'an Nursey,iyakata da su bangaran islamiya da Hadda da karatun Qur'ani da azkar wannan bangaran ban yi waasa da shi ba,shi na iya shi kuma zan koyama ya'yana.
Anum ce ta kara tambayata Daada sai nace mata ya kusa Dawowa Amir ya Dago kansa yana fadin"Umma Daada wata Umman ya samo mana achan Abuja..?
Mamakin sa ya karamani na kallesa na kasa mgana Amir tun  yana Shekara Biyu da wattani ya fara  mgana yaro me mai wayau sosai cikin Mganata nace'wa..ya fada maka..?
Kai tsaye yace min"Uncle Jamal..Ba mun je har chan ba..Umma naga Daada yaci gayu sosai"
Daganan ban kara mgana ba ina jin Anum na girgizani tana fadin"Umma da gaske ne..?
Musty na tayata da gwarancinsa,Dakyar na iya bude baki na amsa musu da hakane sai kawai suka fara Murna Anum kenan Amir kuma bai tashi ba Musty kuma ganin ta mike tana Tsalle shima ya mike yana Tayata Ahmad na jikina ya lafe ba barci yake yi jikinsa ne ba Dad'i zawon hakori sannan ba kudi ballatana na kaishi asibiti.
Amir ne ya kalkeni kafin yace"Umma to ta na ina ita Sabuwar Umman tamu..?
Kai tsaye nace"Tana tare da Daadan ku achan Amir"
Cikin mganarsa ta kuruciya yace"Umma to me yasa Muma Daada bai tafi damu dake gabad'aya  mu zauna achan ba?
Mirmishi nayi wanda yafi kuka ciwo kafin nace"Watarana zamu je Amir in sha Allahu"
Zai kara mgana nace su cigaba da aikin da aka basu a makaranta Anum kuma sai ta koma wasa da musty ni kuma sai na zurfafa cikin Tunanin haka rayuwa zata cigaba da tafiya har yara sun fara gane wani abum..?.akwai nan gaba akwai matsala in dai abubuwa suka cigaba da Tafiya a yadda suka faro.
  Ranar da Ya Ishaq ya cika kwana Talatin a abuja,ranar jumma'a da yammh sai ga Anty Binta batagwara tazo nayi mamakin zuwanta ammh ban nuna ba naje na Debo mata ruwa mai sanyi da nakan diba na saka a fridge saboda ruwan ledan ya kare na famfo muke sha.
A wani karamin jug na dibo mata na Hado mata da karamin kofi na koma ma zauna a kasa ina gaisheta Amir da Anum suna Haraba suna wasa Musty kuma ya kwanta Ahmad ne ke goye a bayana.
Ina gaisheta a wulakance ta amsa tana kallona da ni da Falon sama da kasa tana wani yamutsan fuska kamar taga kashi ruwan da na kawo mata ta kallah kafin tace"Wannan ruwan fa..?ba ku da na Gora ne..?
Cikin Ladabi nace"Ya kare wannan na famfo ne nake sakawa a Firij Saboda yayi sanyi"
Baki ta tabe kafin tace"Shi ne kuma D'an pure water bazaki iya siya ba komai kina jiran sai bawan ki yazo ya siya miki,ko ke irin Dubarun nan na mata da suke yi na taimakon mazajen su baki iya ba sai dai komai ki kwanta Shi d'an wahalan  yayi miki ko..?
Na kasa Dagowa ma in kalleta da karfi take mganar shiyasa na ji ta sosai duk da ba duka ba.
ina jin ta har ta gama cin mutumcinta ban iya Dagowa ba,Sai chan ta mike tana zagayen falon tana leka Dakunan ta Dawo tana fadin"Gaskiyan Ishaq ne da yace gwara nazo na duba kada ya kawo Amaryansa yaji kunya..Ji yadda kika lalata ko'ina na gidan nan Fa'iza..?
Tsiyan a kawo wacce bata dace da irin gidan nan ba kenan ba sanin Darajan sa kika yi ballatana ki Lura da shi"
Taja karamin tsaki kafin ta koma ta zauna kafa kan d'aya ta Dauko Jakarta ta Ciro wayarta ta yi Danne danne ta kara kunne ina ji tana mgana ban ji me take fadi ba Daga karshe dai naji tace"kada ka damu ai zan ja mata kunne in ta yi ba Daidai ka dauki mataki a kanta"
Daga haka ta Datse kiran ta kuramin ido kafin ta daga murya tana fadin"Ke wai baki da aiki sai goye ne..?
Kaina na kasa nace"Ba ba shi da lafiya ne..".
Baki ta tabe kafin tace"Uhm..Kina ji..?
Tafada har da rike kunnewanta na Dago kaina ina kallonta na gyada mata Tsawa ta dakamin tsawa tana fadin"Matso kusa dani domin bazan iya Ihu ba ina mgana"
Dole na ja jikina kusa da ita kunnena ta kama guda d'aya ta rike tana fadin"Abunda nake so na gaya miki shi ne..Gobe Ishaq zai zo shi da Zainab   kuma nan zai sauketa da farko yace gidan Mama saboda yasan Halin ki kada ki basa kunya ni nace nan zai sauketa tunda tasan yana da gida har da Mata da ya'ya Saboda haka gargad'i na Farko shine zaki gyara gidan ko'ina yayi fes sannan ki shiga shashensa ki gyara ko"ina nan Zainab zata sauka har ta gama kwanakinta ta koma"
Ta fada cikin daga murya Lokaci d'aya tana kara jan kunnina zafi nake ji ammh na Daure na kasa nuna mata Raunina cikin kara rike kunnina tace"gargadi na gaba shine ki kama kanki kin dai san ba D'aya kuke ba..Zainab yar boko ce sannan yar gatace gaba da baya ki kula sosai ki Tsaya iya matsayinki ki karbeta hannun Biyu ki mata Hidima duk abunda tace tana so ki yi mata kada kice zaki yi gaddama zaman ki lafiya shine Zainab ta koma Abuja ba bu abunda ya faru Ishaq yace na Fad'a miki kada ki kunyata sa agabanta yasan Halin ki baki da Tunani wani Lokacin kina jina ko..?
Idanuwa sun kawo ruwa ammh sai na maida su cikin Rawan murya nace"Eh..e..Naji"
Sannan ta saki kunnena tana fadin"Sannan ki yi wanka ki d'an gyara jikin ki in tazo ta ganki wannan yarkace yarkacen shi zai kunyata sannan yaran nan suma ki yi musu wanka ki sanya musu kaya masu kyau kina jina ko..?
Nan ma kai na gyada mata key din Shashen nasa ta ciro a jaka ta bani na saka Hannun Biyu na karba sannan ta kara da cewa"Zaki yi musu girken girken Tarba sosai yace tana son Sakwara da miyar agusi,Sannan ki yi mata kunun aya da Ferfesun kayan ciki,ki soya mata Naman kaza ki yi pepe dashi"
Kaina na kasa ban dago ba nace"kayan abincin mu duka ya kare shinkafa kadai garemu"
Bata Damu ba ta mike tana fadin"Daman ai kamar ya san zaki kawo korafin babu komai anjuma Jamal zai kawo miki Cefane..Wlh Tallahi Fa'iza in kika kuskuere mganata ki ka bamu kunya gaban Zainab sai kin Raina kanki ki kuma sani ki kara Sani matsayin ku ba D'aya ba Zainab yar gatace gaba da baya sannan yar boko ce mai kyau yar babban gida"
Har Haraban gidan na rakata tana kara ja min kunni da kara Jaddamin matsayina sai naji ban damu ba Domin ko bata fada ba ban isa na Hada kaina da wacce suke kira da Zainab ba,na ganta a hoto na kuma san ruwa ai ba'asan kwando ba ne.
Nayi kokarin yakice duk wani abu dake cikin raina Hankalina ya tafi kan Ahmad da Zazzabin jikinsa yayi zafi panadol na ruwa nake basa shima Sauran na Musty ne da yayi zazzabi kwanaki Ya Ishaq ya siyomin Hankalina duk ya tashi,ga shi yana ta zawo bani da pampers sai napkin nake yi mai kafin Safe ya bata kaya da yawa ina tashi da wankin na tashi,Sai da na gama tsabtace sa sannan na yi musu shirin Tafiya Hadda.
Saboda bani da masaniyar sanda Bakin da zasu iso,Bayan tafiyar su sai ga Jamal ya kawo min cefane nake tambayansa ashe bai koma ba..?
Sai yace min bai koma ba sai sati na sama shima ko zama bai yi ba yayi min sallama ya tafi.
Sai da na fara zagewa na gyara Shashensa,tas na turara turaren wuta mai kamshi sannan na gyara Falon da Sauran Dakunan daidai yadda zan iya sannan na Fad'a Kichen Hankalina ya kwanta Ganin jikin Ahmad yayi sauki har ya samu barci.
Cefane ne da yawa saboda bakuwa zata zo shiyasa aka siyo aka kawo har da Lemuka da ruwa kwai,Dankali Doya,Kayan lambu taliya macaroni da Buhun Shinkafa sai Couscouss,na Sauke komai a muhallinsa har da aya nagani Saboda ai Anty Binta tace Zainab nasan kunun aya.
Banji kyashi ko mugunta ba na zage na fara aiki kan jiki kan karfi miyar Sakwaran na fara yi sannan nayi ferfesun kayan cikin araina ina jin Dadin Dalilinta yara ma zasu samu chanjin abinci.
Na zuba a kololi na rufe naje nayi sallar azahar na zauna na Huta saboda ina Tunanin sai yammh zasu shigo,ashe ma sun zo garin gidan Mama suka fara sauka Badariya ta shiga makaranta sai ta Biyo ta iskeni ina makarda ayan a blander dina wacce Dakyar ma take yi tana yi ta na mutuwa ta tsufa duk taji jiki.
Tana ta fadamin uban kayan da Zainab din ta kawo ma su Mama har da ita an zo mata da abaya ni dai sai dai yake na kasa cewa komai.
Bata jima ba ban yi sakwara ba Ferfesun ta Diba taci sannan tayi sallah Tatafi jin sun iso yasa na mike na Cigaba da aikina kafin La'asar na gama komai hatta dakan sakwaran,nasha wahala sosai ga Ahmad a baya na ya tashi ya saka Rigima Dole na goyasa haka na yi ina yi ina Hutawa ina Haki,Kazan a karshe na Soyata kamar guda biyu ce ta Turawa sannan nayi pepe chicken na shirya komai na ijiye anan kichen din sannan naje nayi wanka na Sauya kaya na saka Atamfa ta riga da Sikat,ko Hoda ban shafa ba domin bani da ita,ban kuma ji ina son na Burge kowa ba sanin ko nayi bazan burge kowa ba.
Karfe hudu daman nace Haruna yaje ya Dauko min su Amir,Shima din yana da Hakuri da Darajan makota wajen wata biyu Ya ishaq bai basa kudin sa,ina Tunanin ranar da yagaji ya daina kai su sai dai na kai su a kafa kuma akwai tazara mai yawa Tsakanin gidanmu da makarantar tasu.
Suna Dawo na taya su suka cire kayan makaranta ko alama ban gaya musu Babansu zai dawo ba Na riga daman na Dibar musu sakwaran ni dai ko ban ci ba,su dai su samu su ci,daki na jasu sukaci achan kada su ci afalo su lalata Su shigo fada'n komai ya Dawo kaina na shiga uku.
Bayan sun gama Daman sun yi sallar su a makaranta,Sai na saka musu Sabbin kayan su Anum nata Murna Amir ne yace"Umma anguwa zamu?
Sai nayi masa shuru ban ce komai ba sai na Tuna naji wani malami yana mgana kan tarbiya yara yace kada yaro ya jefa miki tambaya ki yi shuru to a ransa zai saka wani abu.
Sai nayi saurin cewa"Sabuwar Umman ku ne zata zo Amir"
Dukkansu suka bini da kallo ban damu ba na cigaba da fadin"Tare da Daadan ku zasu zo in kuka ganta ku je ku gaisheta itama Umman ku ce"
Anum da Amir suka Dagamin kai Musty na chan na wasa da kwalliyar jikin Yan kantin da na sakamai riga da wando.
Hatta Ahmad da bai jin Dadi na sakamai yan kati riga da wando,nayi mai Napkin duk da zawon yayi sauki ba kamar jiya ba na goyasa Tunda baya jin dadin jikinsa har alokacin.
Su dai yaran suna ta Tsalle tsalen wasan su ni kuma ina zaune nayi jugum ina Tunanin wani irin Tarba amaryan Ishaaq zatayi min..?
Sannan wani zama zamu yi da ita acikin gidan nan..?
Nayi zurfi cikin Tunanina naji Amir a saman kaina yana fadin"Umma wayarki umma."
Nayi firgigit na kallesa wayatace a Hannunsa ana ta kira ya mika na karba sai da gabana ya fadi da naga Sunan Ya Ishaq na kirana cikin Rawan jiki na Daga kiran tun kafin nayi sallama naji muryansa cikin Kaushi yana fadin"Ina kika kuma jefar da wayar ina ta kiran ki baki D'auka ba..?
Cikin yanayina nace"Ban ji ba ne.."
Karamin tsaki yaja kafin yace"Ina fatan kin gyara ko'ina..?
Yanzu zamu baro gidan Mama"
Kamar yana ganina na gyada kai sannan nace Allah ya kawo ku lafiya
Bai ko amsamin ba ya katse kiran ya barni da waya a hannu ina Tunanin mafita da farko wlh jikina bai saki ba sai da ya kirani yace gasunan zuwa naji gabbaina sun saki jikina ya fara rawa ina nan zaune ina fama da Faduwar gaba naji kamar ana taba Kofar falo ko Hon dinsa banji ba ballatana Shigowar Mota,to ina ma nake da karfin jin ballatana,yadda hankalina ya bar jikina raunannun kunnuwan nawa ba su saka naji ko motsin shigowarsu ba.
Sai da naji Sallamarsa da mganarsa Su Amir na dago na kalla basu bi ta kaina ba suka fice da gudu suna kiran sunansa Daada kamar yadda suke kiransa.
Ni kuma ina zaune na kasa tashi Jikina gab gab yake yi kamar mazari gabana ya fara Dif Dif kamar an sakamin Wutar lantarki ji na nayi na kasa motsi sai yanzu nake jin yanayi na ba Dad'i ina Tunanin da wani irin kallo Amaryan tasa zata karbeni,?Kamar acikin kaina naji yana Kiran sunana a kausashe kamar yadda ya Saba.
Sai na zabura na mike da Hanzari Daidai Anum na shigowa Dakin ta fara jan Hannuna tana fadin"Umma Daada na kiran ki"
Kamar rakuma da akala haka Anum ta rika jan Hannuna har Tsakiyar Falo inda Ishaq da amaryan suka samu mazauni saman kujera mai zaman mutun biyu Amir na jikin Babansa Musty na Dauke ajikin wata Farar mace Doguwa Lalle tsarki ya tabbata ga Allah shugaban Hallitun Duniya.
Lalle gaskiyan su Anty Binta ne kada na Had'a kaina da zainab,tazaran kamar sama da kasa ne a wajen nisa ashe a Hoto ma an rage mata kyau da Haske kamar balarabiya tana sanye da Wani leshi daga ganinsa mai Tsada ne doguwar riga taci Daurinta gashinta ya zubo har gadon baya Fuskata Dauke da kwalliya mai kyatarwa kafafunta da Hannayenta Sun ci kunshi Lalle baki da Fari kamar don ita ma akayi zanen Saboda yadda kunshin ya haskata kafarta da Takalmi daga ita har Ya Ishaq basu cire takalmansu ba har zuwa Tsakiyar Falon.
Kanta na kasa tana ma Musty wasa yana mata gauranci bata san da ni a Falon ba ni kuma kawai ita nake kallon Sakin Hannuna Anum tayi ta nufi Babanta tana fadin"Daada Umma"
Shima sai Lokacin ya Dago yana kallona ina ganin sanda Fara'arsa ta Dauke kamar yaga mutuwarsa hararata yake yi kasa kasa ni kuma Chanzawarsa nake gani yayi kiba kamar bashi ba Daga gani ya samu kwanciyar Hankali sosai.
Na kasa gaba ballatana baya sannan bakina yayi nauyi shine da yaga haka ya D'aga baki yana fadin"Haka ake tarban baki a karofi ko Fa'iza..?
Sai alokacin ta Dago kanta muka Hada ido hudu da ita ni dai a bangarena sai naji na muzanta ni bansan yanayinta a bagaranta ba sai dai ban gane yanayin da take ciki a Fuskarta ba.
Tayi saurin Shanye mamakin ganina ta kallesa tana fadin"Maman su Amir right..?
Tafada tana bin sa da wani irin kallon da Sai da na kauda kaina kai ya gyad'a mata yana fadin"Yes Fa'iza"
Dukkansu a tare suka sakarmin ido sai naji kafufuwana na rawa lojaci d'aya  sun kasa D'aukana sai na bi ra'ayin su na Durkusa kaina na kasa cikin yanayina nake fadin"Sannun..Sannun ku da zuwa an zo lafiya..?
Bakina har rawa yakeyi Ta kalleni ta kara kallona sannan ta kallesa ya gyada mata kai Cikin Zakin muryanta da ta karye da Turanci tace"Hy Am Zainab Nice to mee u Fa'iza"
Tafad'a cikin wani irin Turancin da na kasa ma jinta ballatana na gane ina jin yana mata mgana kasa kasa ban ji me yace ba nadaj ji tace"Oh sorry Honey..Kiyi hakuri Fa'iza ban san bakyajin Turanci ba kina lafiya..?
Yasu Amir ina Ahmad ko shi ne a bayanki..?.honey goye kada kafafunsa sun lamkwashe ita kuma ta samu problem da kirjinta fa"
Duka alokaci daya ta fad'a,kunnina na kasa yasa naji wasu daga cikin mganar nata sannan na Dago kaina ina kallonsu jin nayi shuru yasa yace mata"Tun kafin mu taho na fada miki yanayin Fa'iza bebiya bataji sosai sai kin yi mgana da karfi sannan zataji jiki Honey"
Kwabe Fuska tayi kafin tace"Really..?
Kai ya gyad'a mata kafin yace"Yes bata ji ki ba sai kin d'aga murya"
Ta kalleni cikin Tausayawa kamar taga mai bara tace"Ayya am sorry"
Ni dai kaina na kasa ban ce komai ba kawai sai naji tace"Whta is bebiya Honey..? I did get u..?
Da Harshen Turanci naji yana mata bayani bana jin me yakefadi sai dai ina gani tana kallona tana d'an kwabe Fuska gani nayi bazan iya jure ganinsu ba yasa na mike da Hanzari zan koma Daki Ishaq ya Dakatar dani da Fadin"Kin ga Kwantomin Ahmad"
Ba musu na karisa na kwantomai na mikamai har ya fara barci su Anum kuma sun samu Chaculate basu ma bi ta kan mu ba.
Kallona yayi lokacin da yake karban Ahmad yace"Ki bude shashena ki kwashe kayan zeey da nawa zuwa chan"
Cikin rawan jiki na koma Daki na Dauko key din ina ganinta tana bina da kallo,ni dai na bude Dakin nazo na Rika daukan jakunkunan da suka zo dashi sai ta karshen ne zan Dauka tace"No.."
Sai ta juya tana fadin"Honey tok to her kasan ban iya mgana da Karfi ba..Tsaraban Kids d'ina ne"
Shi ya fadamin tace tsaraban yara ne sai na kalleta cikin yanayina ina fadin"Sun gode Allah ya saka da alheri"
Ta amsa da fadin"My pleasure"
Mganar abinci nayi yace sai sun yi wanka sun yi sallah tukunnah Jikin Ahmad dayaji zafi yasa yace min ba shi da lafiya ne na dagamai kai sai ya kalleni yana fadin"Meyasa baki fadamin ba.?ai da ko Jamal yazo kun je asibiti an dubasa".
Nidai ban ce komai ba itama kuma wayarta ta Dauko a wata karamar jaka mai kyau tana Dannawa kafin ta mike tana Fadin"Honey am Tired ina son nayi taking Shower'
Mikewa yayi yabi bayanta yana fadin"Me too duk a gajiye nake"
Ina kallon su suka shige suna rangaji Jikinsu na Dukan juna karamar jakar Hannun Zainab Ishaq ya amsa ya rike mata ita kuma sai lamkwashewa take yi tana Turancin da bana ganewa.
Su Amir kuma sun samu Chaculate basu lura ba na Dauki jakar da tace Tsaraban yara ne zuwa cikin Dakina na Bude naga kaya masu tsada Kala biyu biyu na Anum har da riga da wando da takalma ni ma har ni naga Doguwar riga da pakistan riga da wando sai naji kayan basu burgeni ba na Tattara na ijiyesu na fita nace su Amir su yi alwala an kira sallar mangariba.
Tare da yarana muka yi sallar mangariba muna zaune muna azkar Ishaq ya leko ya sauya kaya zuwa Jallabiya yace na kawo abinci,da Hijabin da nayi sallah na shiga Kitchen na Fara Daukan abincin nasu zuwa Shashen megidan basa Falon suna ciki na gama jera musu komai na Fice na koma D'aki duk da cikina na jin yunwa ammh na kasa cin komai a fatar bakina nake jin abinci bazai iya shiga ba sai kawai na sha Ruwa na koma ma kishingid'a ina kallon su Amir nata wasa Ahmad yayi barci,ina zaune a wajen har akayi sallar Isha'i sai na mike nace su bar wasa su sake yo alwala suzo muyi sallah
Bayan mun idar Anum nata rigiman zataje wajen Daada dakyar na lallasheta da yayi barci,kafin su kwanta sai da suka kara cin abinci sannan nayi musu shirin barci sai da sukayi addu'a na tayasu suka Tofa sannan na baro Dakin nasu na koma nawa Ko barayin Shashen Ya Ishaq ban kallah ba Tunda suka shiga Ciki ban kara jin motsin su ba.
Ni kuma na kasa barci da ya fara Fizgata sai na farka gajiya nayi da juyi na shiga tiolet nayo alwala nazo ina ta nafila sai wajen uku na Dare na kwanta shiyasa na makara sallar asuba rana ta farko da Ya Ishaq bai fito ya tara su Amir sun tafi masallaci ba Amir sai fadi yake yau Daada bai je masallaci ba ne Umma..?
Sai nace musu yaje yaga suna barci ya kyalesu har nayi musu shirin hadda nayi abun karyawa Haruna ya Dauke su ya kaisu basu fito ba yaran dakyar na janye su suka tafi batare da sun ce zasu je gaida Daadan nasu ba.
Suna tafiya nayi ma Ahmad wanka na shiryasa nima nayi wanka sai nasha Tea kad'an naji cikina ya Toshe Breakfast din Amarya da ango a kicthen na bar musu komai na shige D'akina araina nace me yasa zan damu..?Ai ya jingine auran mu alfarma yake min da nake zaune ma agidansa yana ci da ni.'

*Littafin KANA NAKA book 2,paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*

*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewa book:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT Y'A SKWATO__SAKINA HASSAN 08066726866

INA MATA Y'AN KWALISA MASU SON GYARAN JIKI MACCE DA TASAN KANTA KULLUM CIKIN GYARA TAKE

INA MATA MASU FAMA DA RAMA KU KINSA KAYA BASU KAMA JIKIN KI 😫

INA MATAR DA ADDA JIKI BAKI DA HIP BAKIDA BAYA IN KINYI DRESS BAYANKI A SHAFE

INA WADDA KE FAMA DA ZUBEWA NONO KU KE BAKI JIN DADIN GANIN SU KAMAR SILIFAS

KINYI TA GYARAN BRST HAR KIN GAJI HJY TA GYARAN BRST WAHALA GARESHI DUK WADDA TACE MIKI GA MAGANIN BRST DA SHA ZAIYI TO KARYA TAFADA MIKI GYARAN BRST YANA SON JUREWA DA DAGEWA IN KIN FARA BA'A TSAYAWA INSHA ALLAH SAI KIGA SUN ZAMA NORMAL

MUNA DA INGANTATA ZUMA BRST DA MUNKA SARRAFA DA KAYAN ORGANIC HERBAL SU MACA DASU AGUAJE WADDA INDAI KIN RIKE TA INSHA ALLAH ZAKI GA SUN CIKO SUNYI KOSHI RUBA 2 KU 3 SUN ISA YAZAMA MIKI YADDA KK SO 4K

MUNA DA GARIN HIP DA BRST YAKE GYARA DA GYARAN JIKI DA KARIN NIIMA YAKE YI 4K

MUNA DA INGANTATA ZUMA TA HIP ITA MA MUN SARRAFA TA DA KNGAN TATUN KAYAN ORGANIC HERBAL DA KE FIDDA MIKI HIP 6K

MUNA DA ZUMA KIBA WADDA ZAKIYI FRESH DA BULBUL ITAMA RUBA 2 KU 3 ZATA YIMIKI YADDA KK SO 2K

MUNA DA GARIN GYARAN BRST DA KARIN NIIMA SHIMA GUDA 2 KU 3 ZAKI SHA 2K

GASKIYA DA AMANA ITACE NASARAR.MU

MUNA AIKA KAYA KU INA CIKIN YARDA DA AMINCI

MMN MUJAHID __SAKINA HASSAN MUNA SOKOTO DA KEBBI 08066726866

       *🅿️09*

Saboda barcin da ban samu jiya sosai da Daddare ba, ina zuwa shimfid'ar da Ahmad da ya yi barci nima sai na bingire barcin ya fara figata sama sama naji kamar ana kiran sunana a saman kaina Dishi dishi na bude ido na kafin naji ana tab'a kafata guda daya da sauri na mike zaune har wuyan rigana yana dan ja ya yage kada'n,Ido hudu muka yi da Yaya Ishaq da ke tsaye a kaina yana sanye da Riga da wando sauka'kku na zaman gida.
Mitsike ido nayi kafin na fara kokarin saukowa daga kan gadon Lokaci d'aya ina Fadin"Ina..ina kwanaa.."
Amsawa yayi da lafiya lau kafin yace"Ina abun karyawan mu fa..?
Ina kokarin gyara daurin D'ankwalina nace"Yana kitchen"
Juyawa yayi zai fita lokaci Daya yana Fadin"To fa'iza sai na fad'a miki abunda ya kamata ki yi..?
Da kika gama sai ki shigo mana da shi ciki ko..?
Daga haka ya fice nima sai na maramai baya shi ya koma Shashen sa ni kuma na fada kitchen na samu Babban Faranti na hada komai na nufi bangaransa yau ma ba kowa afalon sai dai duk sun yi kaca kaca da kwanukan da suka yi amfani da shi jiya Bayan nasauke na Hannuna ni na Duka ina tattara na jiya na kwashe na kai kitchen na Dawo Daukan jug da kananun kofina shi kuma Ya Ishaq ya fito daga cikin bedroom din sa yana ganina yace"Yauwa Fa'iza wai me kika yi mana na karyawa ne yau..?
Kaina na kasa na lissafa mai Baki ya tabe kafin yace"Zeey kuma tace Fatan dankali take so da Safen nan"
Kallonsa nayi kai tsaye Lokaci d'aya ina Fadin"Akwai dankali sai ayi mata"
Da Sauri yace"Yauwa Hanzarta Fa'iza in dai yau bataci abunda take so ba Rigima zata dinga yi min"
Ko kala ban kara cewa ba na fice Ina zuwa Kitchen sai da na yi wanke wanke sannan na fere dankalin na Dora mata ko araina ban ji Haushin su ba,Sai nake ganin ma ai taimako na yayi yana min alfarma ya bani wajen kwana sannan yana ci da ni duk da ya Jingine aure tsakanina da shi..
Kafin na gama ya leko kitchen din nan yafi sau uku ban gama ba yana ta fadin baya son Rigiman zeey,ina gamawa na juye mata a kula na kwasa na kai mata ina shigowa ya karb'a na Hannuna Lokaci daya yana fadin"Fa'iza tayani dauko sauran yau mulki take ji bazata iya fitowa ba tace kinsan mun sha gajiyan Hanya..Dayake tafi sabawa da Tafiyar Jirgi ita"
Ni dai ban tankasa ba,Dayake ma ba Duka mganarsa naji ba yana gaba ni kuma ina bayansa da Farantin kayan karyawansu har zuwa cikin bedroom dinsa nan saman cafet din na Sauke komai ita Amaryan tana nad'e cikin Blanket dakin na bi da kallo komai ga shi nan a kasa hatta kayan da suka cire Kayan zeey din ta bakinsa duk gasu nan a zube a kasa kila wajen daukan wani abu ne ta zazzago kayan kasa ni dai kaina na kasa bazan iya juran ganin Ishaq ya sunkunya yana mata mgana a kunne ba.
Mikewa nayi zan fice da Sauri cikin dan Daga Sauti yace"Ki tsaya ku gaisa da Honey mana Fa'iza"
Dawowa nayi na durkusa nan gabda kofa sannan na Dago ina kallonta itama Lokacin ta D'ago ammh Rabin jikinta yana jikin Ya Ishaq ne da Sauri na maida kaina kasa ina Fadin"Ina kwana..?ya bakunta.?
Cikin yanayin mganata Hannu ta Dagamin kafin ta juya tana ce mai"Honey ni dai zan rika daga mata hannu..kasan ban iya mgana cikin Ihu ba.."
Mirmirshi yayi batare da yayi mgana ba sai ma karan Hancinta da yaja yana fadin"Kin gan ki ko..?ga Abunda kikace kina jin ci nan Fa"iza tayi miki ki taso mu karya kinsan nayi ma Daddy alkwarin zan kula dake sosai"
Kasa kasa suke mganar ina jin tashin Dariyan su,ta kasan ido nake kallon su shi ya tallafota ta mike tsaye jikinta Daga ita sai wata rigar barci Fara iyakarta gwiwanta sannan shara shara ce ana ganin jikinta..
Ni dai kafafuwan su na gani a gabana da yasa nayi Saurin mikewa ina fadin"Sai..i..anjuma.."
Ina jinta tana fadin"Honey ita tayi Dinner din jiya ka tabbata ba oder d'insa kayi ba"
Ina ji yana gayamata da gaske ni nayi da karfi tace"Hy..Sai kuma ta koma tace"Sorry Fa'iza ko..?
Ta fada tana kallonsa sai ya Daga mata kai kara kirana tayi da karfi sai na Dakata da Fitan na juyo ina amsa mata tana jikinsa har Lokacin ni kuma sai nayi kasa da kaina cikin mganarta da sanyin Muryanta tace"Kina jina..?..
Sai na Daga mata kai Da Sauri tace"U are good in cooking..I Mean..Honey plz Help me ka fadamata da Hausa zai bani Wahala"
Ina jin Sautin Dariyansa Lokaci d'aya yana Fadin"Fa'iza Abunda Honey ke nufi shi ne Kin ,iya girki sosai"
Baki ta washe tana gyada min kai sai nayi mata martanin Mirmishinta ban ce komai ba ta kalleni ta kara kallona ina gabansu ne shiyasa naji abunda take fadi"Honey ammh ba ka ce min matarka cousin sister d'inka ce Dad din ka ya aura maka ita ba..?
Da kai yayi mata mgana cikin kara bayyana mamakinta tace"So meyasa bakwa kama da juna..? Infact She is  Blank and.."
Sai ta kasa karisawa ta tsaya tana kallona ni kuma sai na kauce ma ganinsu idanuwana suna kallon Kwalliyar Cafet din dake D'akin.
Kai Tsaye Ishaq yace"Kuma gata Mummuna ko..?
Haka kike son fad'a ko..?
Sai ta Rufe baki alamun taji mganar ta mata girma gira ya D'aga mata kafin yace"Yes ki fada kanki Tsaye ai ba karya kika yi ba Fa'iza bata da kyau..Yes Cousin Sister dina ce Ammh da daad din mu da nata baban D same Father suka hada uwa kowa da tasa..Shiyasa zaki ga muna da bambamci sosai da su"
Ina jinta tana fadin"Ok"
Daganan ni ko kara tsayawa jin su ban yi ba, na fice daidai yana ce mata"Shiyasa kika ga su Amir basa kama da ni..Ita suka debo gabadaya"
Ammh nasan soon kin kusa Haifamin masu kama da ni Honey"
Tashin Dariyan su naji ban ko Tsaya ba Sai da na koma Daki sai kuma naji san mganarta bata batamin rai ba,Komai yaje ya Dawo wanda baisan Darajata ba ne ya tayata suka tozartani Saboda na kauce ma Tunanin kayan su Amir da ya fara Taruwa na kwashe na kai baya na fara wanki ina yi ina tilawar Karatun Qur'ani acikin raina bana so kuma Tunani ko damuwa su shiga raina.
Na gama wankin kenan ina Shanya sai ga shi ya leko cikin Shirin Fita sai Tashin kamshi yake yi da key din mota a Hannunsa.
Gayamin yayi zasu fita sai yammah zasu dawo nayi musu fatan Dawowa Lafiya har ya juya sai kuma ya Dawo yana Fadin"in kin gama wankin nan Fa'iza ki shiga Shashena ki gyara saboda kinsan zeey bata saba kowani aiki ba chan ma yan aiki gareta  suke mata komai Dakin duk ya Hargitse ki dan kintsa mana shi kafin mu Dawo"
Batare da wata Damuwa ba na amsa mai ya juya yana fadin na kula da Ahmad ya lekasa yaga har Lokacin bai tashi ba.suna fita ba Dadewa na gama wankin na koma cikin gida Bangaransa na shiga kamar yadda yace na gyara Hatta da Rigar barci da pant da Bra din ta bata Dauke ba nan ta Watsar da su ni na Tattara komai na gyara na kwashe kwanukam da suka yi amfani dashi na kai kitchen nazo na share Dakin na yi goge goge na Fesa Turaren kamshi na Rufe masa Shashensa na koma Dakina nayi alwalan sallar azahar bayan na Idar Ahmad ya tashi da Rigima ni kuma ban wani ci abinci ba sai na Hada Tea na bashi Nono na ba ruwa sosai aciki.
Naji dadin jin jikinsa da Dama yau ya fara Dawowa da kuzarinsa.
Yunwa ce ta kusa min illah yasa na tashi na Dafa Farar shinkafa naci da manja da yajin da Yaya Asiya tazo min dashi muka kwanta barci sai La'asar na tashi bayan nayi sallah na Goya Ahmad na Fada kitchen.
Jallop din Cousscouss nayi da Kifi Saboda acikin Cefanen da Jamal ya kawo har da kifi,Sai na Dibi Naman jiya da ya rage nayi musu Ferfesu da shi.
Kafin mangariba na gama komai Lokacin Haruna ya Dauko su Amir Daga makaranta sai da suka cire kaya muka yi sallah sannan na zubo musu abinci suka ci Anum sai tambayan ina Daada yake shi da Sabuwar Umman su nace sun fita ammh yanzu zasu dawo wasa waasa sai wajen tara da wani abu suka Dawo Lokacin ma ina koya ma Amir Haruffa ne Anum kuma suna ta wasa da Musty suka shigo suna ganinsu suka tashi suka nufesu gabadayan su suna musu oyoyo ita ta Daga Musty shi kuma ya Daga Anum sai ya Rungume Amir..
Daga inda nake ban tashi ba nayi musu barka da dawowa shi ya amsa ita kuma Hannu ta Dagamin saboda bazata iya Daga murya ba ammh Tana da Fara"a sosai nima sai na Daga mata Hannu.
Su da yaran shashen shi suka shiga sai na mike na Shiga kitchen na kwaso musu abincin su na bisu da shi sun baje afalo yaran suna ta wadaka da Ice_cream da su Sweet har da gashishiyar kaza,Zeey din tana zaune gefen Ya Ishaq har kafadunsu na dukan juna tana mgana a waya sai dai ba Hausa take yi ba,sannan ba Turanci ba kamar dai Fullanci.
Na sauke farantin Hannuna na mike kenan ya kirani na Dawo na durkusa a gabansu ya tambayeni abunda na Dafa na gayamai ya juya yana kallonta da ido suka ma juna mgana naga ta tashi tana wani Rangaji Har Lokacin tana mgana cikin Shagwaba ta shige ciki shi kuma kamar wani Sauna ya Bita da kallo ni kaina na kalleta ballatana shi.
Ahmad ya tambaya nace yana barci Sai cewa yayi"Meke damun yaron nan ne..?barcin sa ya fara yawa fa!
Ni dai ban ce komai ba na tashi na fice bayan nace ma Amir suzo su kwanta da Wuri Saboda makaranta gobe.
Falo na koma na Tattara musu littafan da jakunkunan su na kai musu Dakin su na gyara musu in da kowanne zai kwanta na fito musu da kayan barcin su,nayi ta jiran su har goma ta wuce suna tare da su sai kawai na wuce Dakina naje na Duba Ahmad sai sharan barcinsa yake haka kawai na kasa barci batare da ya'yana sun kwanta ba,Ban samu natsuwa ba sai da naji Hayaniyar su afalo na fito falon Amir nayi ma fad'an meyasa basu zo sun kwanta da Wuri ba su san gobe suna da makaranta"?
Anum ya kallah yana fadin"Umma Anum ce taki tasowa."
ina kai kallona wajenta ta wani kwabe Fuska tana Fadin"Umma ni wajen Anty da Daada zan kwana"
Sai yarinyar ta bani Dariya in ban yi wasa ba Anum ta Dauko iyayi wajen Ubanta to in ba Salo ba da shi ta Saba kwana ko yaushe ta san Anty ma..?
Dariya nayi, da yasa yaran suka Tsaya suna kallona hannunta na kama da na Musty Amir na bayan mu zuwa Dakinsu Lokaci daya ina Fadin"Baki san ba kyau yaro ya kwana inda Babba yake kwana ba. ?
Na fada ina zama gefen karamin gadon Anum cikin kallona tace"Umma to ba Ahmad na kwana a wajen ki ba..?
Kai na girgiza ina Dariya Anum akwai kalkalin baki cikin Mgana ta nace"Shi bai girma ba ai bai kai ku girma ba..Da shima ya kai kamar Mutsy ko Anum dina zan daina kwana da shi zai Dawo Cikin yan'uwansa"
Zata kara mgana na Dakatar da ita da Fadin"Shii..Sai gobe sai mu karisa Anum yanzu Dare yayi gobe akwai makaranta ku sauya kaya Mai jin Fitsari ya shiga yayi kafin ku kwanta"
Suka amsa min da Toh ni na saka ma Anum da Musty kayan barcin su araina ina Tunanin in na yaye Ahmad ya kara girma zai dawo kwana wajen su Amir ita kuma Anum Lokacin ta kara girma ita macece sai na cireta cikin yan Maza na koma muna kwana tare.
Sai da na tabbatar da sun kwanta Mun yi addu'an barci na taya muka Shafa jikinsu sannan na baro Dakin na koma nawa nima nayi shirin kwanciya yau da wuri barci ya kwasheni,Kila Saboda na gaji ne sosai sannan abun mamaki har barcin rana nayi ammh kuma na samu ishashen barci da Daddare.
Da Safe ma kamar jiya ne har su Amir suka tafi makaranta basu fito ba Haruna mai adaidaita sai da yayi min mganar kudinsa yace ayi ma megidan Tuni Tunda yaga yana gari nace zan gayamai in sha Allahu yayi hakuri.
Kamar jiya yau ma har kuryar Daki na kai musu abun karyawan su ita Zainab din tana Tiolet kamar yadda yace ban jira ta ba nayi fitowa ina gasgata mganarsa da yace bata aikin komai bata ma iya ba ganin yadda komai kuma ta kara Birkitasa kamar jiya ban gyara ba yau din basu fita da wuri ba sai yammah,Suna cikin Shashen sa sun kule,Ga shi nayi ta Dakon sa nayi masa mganar Haruna basu fito ba sanda kuma suka fito suna tare da ita Hannunuwan su sarke da juna shiyasa ban yi mai mganar ba yace min gobe zasu koma Saboda aikin su zai kaita gidan Anty Binta da gidan Anty Mahma sai kuma su zaga gari nayi musu adawo lafiya.
Yace kada nayi abinci da su zasu ci a waje na amsa mai da toh sannan ya kara Umartana da in shiga bangaransa na gyara musu kamar jiya nan ma na amsa mai da toh.
aiko basu dawo ba sai goma da Rabi na Dare ina Falo ina fama da guga Anum da Musty sun gaji da jiran Dada da Anty  sun yi barci Amir ne ke taimakamin in na goge daman kayan su ne, sai ya rika Dauka D'aya bayan d'aya yana kaima kowa cikin Dirowan kayansa.
Albarkacin Zainab har aka kawo ma su Amir Chips da su pizza,Sai kuma suka Tarar da su Anum din sun yi barci Ya Ishaq shi kadai ya shiga bangaransa ita ta tsaya tana waya naji dai Tana ta ambaton wani suna Daddy tana mgana cikin shagwaba irin na ya'yan gata..sai da ta gama sannan ta Dagamin Hannu sai nima na Daga mata Amir ta yafito da hannu yazo wajenta tana mai mgana ni ban ji me take fadamai ba.
Ta mike tana kallo na inaga abun gugan da taga ina yi ya bata mamaki kusa dani ta kariso da takalminta mai Tsini ta Duka a gabana tana fadin"Sannu fa"
Na amsa mata da mirmishi kallona tayi kafin tace"Hannun ki da bayan ki basa ciwo ne..?ba mai wanki da guga ne..?
Sai ta karkato kanta tana Fadin"Kina jina..?.
Sai ta ma bani Dariya cikin yanayina nace"Ina jin ki mana..ai ina jin mgana in kika yi a kusa dani"
Kai ta jinjina kafin ta kara kallona ta ce"Sannu fa"
Na kara amsa mata sai tace"kina kokari fa..na ji dadin girkin ki..In da a Abuja kike da kin samu kudi..Gidajen mu duk kukus suke d'auka sannan irin ku kuna samun aiki a manyan Restaurant wajen saida abinci kin gane..?
Tafad'a tana kallona Saboda Hausan nata sai a hankali bai zauna ba sai na daga mata kai alamun ina jinta sai kawai taci gaba da fadin"Meyasa baki yi karatu ba Fa'iza..?na tambayi Honey yace kece baki so why.?
Sai kawai na kalleta abunda na Lura da Zeey din macece faram faram bata da girman kai ko D'agawa sannan ita Kai Tsaye ce duk abunda ya shige mata Duhu sai ta yi mganarsa shiyasa ban damu da mganarta ba sai na yi mirmishi kafin nace mata"Ba ni ba ce ba na so..Karatun ne bai dace da Kaskantattun mata irina ba..Wad'anda basu da gata sannan masu nakasun ji irin ta Lalurata.."
Kallona ta tsaya tanayi ina ganin bakinta na motsi ta kasa mgana ita kuma tana so tayi mgana ammh hausan bata san yadda zata min na gane ba,Muna cikin hakane sai ga Ya Ishaq ya leko ya kirata sai ta tashi ta tafi ammh sai da ta waigo ta kalleni nima na kalleta ina tunanin mamakin mganata take yo menene ban sanin mata ba.
Daganan bamu kara haduwa ba sai da Safe da zasu tafi,misalin karfe goma na Safe yara tuni sun tsufa a makaranta,ganin har suna shirin tafiya yasa na yi mai mganar Haruna ina ga saboda a gabanta ne yasa bai yi Fada ba,ya cire dubu goma sha Hudun sa ya bani Saboda duk wata Dubu takwas ne,Sannan ni kuma ya bani Dubu uku na rike a hannuna wai bashi da kudi nidai na amsa ina godiya,Zainab ta bani Hannu mun yi musahaba tana ce min"Sai na ganki kun zo min hutu Abuja ke da yarana"
Mirmishi kawai nayi mata ta Dauki Ahmad har Haraban gidan na Rakasu ko Saboda ganinta ne yasa ya bude get din da kansa Dubu biyar ta bama Ahmad sabbi tace ya raba shi da su Anum,Har motar su ta bar Haraban gidan tana Dagamin hannu nima ina Daga mata bayan sun fice sai na maida get din na kulle na koma cikin Gida ina Sauke Numfashi.
Ban zata haka amaryan tasa zata karbeni ba sai ga shi na sameta a yanayin da ban zata ba.
Da yammah da Haruna ya Dauko su Amir daga makaranta na basa kudinsa yana ta godiya Anum har zata min kukan banza don nace Daada da Anty sun koma Abuja sai da nayi mata jan ido sannan ta shiga Taitayinta.
Tunda suka tafi bai kirani ba,nima ban kira ba nadai san shuru lafiya ne in da ba Lafiya da naji Labari sai nima na kama kaina na cigaba da kula da kaina da ya'yana tafiyar su da Sati Daya Sai ga Goggon karofi tazo min kamar Daga sama nayi murnan ganinta har bansan yadda zan kwatanta ba.
Tazo min da su kuka,Kubewa garin kunu garin Danwake,kayan miya da kuli kuli,Sai ta zo ma da su Amir gyada da mai gishiri da mai bawo,Sai alewan yara,Suna makaranta ko da ta iso da rana ne Lokacin nama zata ko Daga gidan Mama take sai tace min Daga Dutsemah take ta biya ta gaida ta Madina ta dade bataje ba naji Dadin jin Tamadina tana lafiya.
Bakina yaki Rufuwa da Goggo tace min kwana zatayi sai gobe zata koma ni kawai tazo dubawa.
Su Amir nata tsalle da suka Dawo suka ganta,suna son zuwa karofi ammh Ya Ishaq baya bari daga makaranta sai gida sai ko gidan Mama in ma sun je to yini ba kwana ba.
Bamu samu kebewa ba sai Dare bayan yaran sun kwanta Goggo ta na gayamin taji duk abubuwan da suka faru basu yi mata Dadi ba Sai dai tayi ma Yaya mariya fada meyasa ta biye ma Binta ai ko banza ni yar'uwanta ce bai kamata ta taho ta kyaleni ba,Goggo tace kinsan mariya da bakar Zuciya,Sannan ta riga ta rantse ne yasa bata ce ta Dawo ba,ni nake fadama Goggo zuwan ya Ishaq da amaryansa na gayamata mun zauna Lafiya da ita har suka koma Goggo ta cigaba da min nasiha duk akan nayi hakuri ne watarana sai Labari.
Sai Wajen d'aya saura na Dare muka kwanta da Safe kuma da Goggo Tayi shirin tafiya nace ta leka gidan Mama su gaisa tace min bazataje ba Dakyar na Lallasheta tace zata biya tayi mata Murna dagachan zata wuce a bakinta nake jin Hajiyar Dala ta kirata a waya tana mata fadan bata kyauta ba da bata zo ba Goggo tace nayi mata Tas daga Lokacin bata kara kiranta ba.
Sha d'aya na Safe na raka Goggo Har bakin Hanya mun rabu tana ta kara jadaddamin nayi hakuri da rayuwa watarana komai zai wuce sannan na Dage da gayama Allah shine Sarkin Duka Duniya gabadaya.
Mun rabu kamar na bita haka nakeji ammh ba Dama,har da kwallata sai da nayi,Bansan ya Goggo suka kare da Mama ba sai da washegari Badariya tazo take bani Labari Mama har da kuka ta kira Anty Binta da Ya Ishaq akan Goggo Tazo tayi mata cin mutumci Saboda ni..
Gabana ya fadi na zare ido ina kallon Badariya kafin nace"Sabo da ni kuma..?
Badariya tace"Tabbas..Kinsan Halin Mama har Hajiyar Dala sai da ta kira ta fada mata..Ni dai nasan kila Goggo Fada tayi mata shikenan sai cibi ya zama kari Anty Binta nata fada haka ma shi kan shi Ya Ishaq din a waya sai Fada yake barin ma jin Mama nata kuka"
Sai jikina ya fara rawa nasan komai kaina zai dawo aiko hakan ce ta faru Badariya ta tafi ba Dadewa daman Daga makaranta ta biyo sai ga Anty Binta da Mama har cikin gida wanda bazan iya tuna zuwan mama gidan nan na karshe ba.
Zagi da gori da cin mutumci ba wanda basu yin ba ina da goyon Ahmad a baya na Mama ta saka Hannu ta tsinkeni da mari,na Dafe kuncina Hawaye suka Gocemin,Ahmad na barci ne ammh sai da ya tashi Hayaniyar Mama yasa ya tsorata ya fashe da kuka shi yana na Sarari ni ina na zucci.
Mama ta kama kunnuwana ta murde tana fadin"Ni zaki hada ma gulma da munafunci har Goggon karofi ta taka har gidana taci min mutumci don Ubanki..?ai nayi miki komai Tunda na rike ki kuma sannan daga karshe Mijina ya aura miki D'ana kika shiga Cikin zuru'ata duk da bana so..Shegiya mai bakar aniya,Wlh fa'iza na tsaneki na tsani na bude ido na ganki a matsayin surukata"
Anty Binta ta karbe da Fadin"kuma ban da Ishaq din uban waye zai aureta ya zauna da ita ahaka..?
Mama tace'Ki barta zan yi mganinta Tunda bata san mutumci ba"
Haka suka gama zage zagen su,suna yi suna Dungurina suna murdemun kunni sannan suka saka kafa sukayi tafiyar su haka na zauna na Rumgume D'ana ina kuka shima yana kuka har sai yaushe ne zan daina Fuskartar wannan Tozarcin..?
Ba mai Lallashina na gama kukana na Share hawayena,Ashe ban tsira ba Sati biyu da Tafiyar su Ishaq,sai gashi ya Diro ranar asabar da yammah,Abunda yayi min yasa na Fahimci daman saboda yaci min Mutumci ya Dawo.
Har Bangaransa ya kirani na Duka gabansa shima ya ci min mutumci,har yana fadin ba Domin mugun kalaman bakin Baba akansa ba wlh da sai ya Sakeni sai naje Goggon ta auramin Isa ko Yusuf cikin manyan ya"yanta sannan ya kara jamin kunne akan yaya mariya da gaske yake yi kada ta kara zuwarmai gida in kuma wlh tallahi ya kara ganinta sai ya wulakantata.
Na Dago kaina cikin Hawaye muryata ta shake cikin wani yanayi nace"Kayi hakuri..Ba..zan iya fada mata ta daina zuwa ba ne"
Sai kawai na Fashe da kuka Tsawa ya Dakamin yana fadin"To ni zan gayamata in muka hadu Tunda gidan nan nawa ne ina da iko da shi kada na kara ganinta acikin su..In kina Tunanin yar'uwan ki ce in kun had'u wani waje sai ku gaisa ammh ba"a gidana ba kin ji maa na gayamiki"
Sai na kasa mgana kaina na kasa na Share majina kafin nace"Kayi hakuri don Allah.."
Mikewa yayi a fusace yana fadin"Ke dai kika sani kin dai ji abunda na gaya miki..daman abunda ya kawoni kenan Har ga Allah bana son zama agidan nan chan yafiye min kwanciyar Hankali ki kula Fa'iza kada a kara kirana afadamin an hada baki dake an tozarta uwata in hakan ta kara Faruwa zan manta kalaman Baba da komai kema na wulakanta Rayuwarki wlh"
Daman Tozarta ne yazo yi kuma yayi washegari tun Safe ya Dauki hanya,ko sallama bai min ba sai zuciyata ta kara Kek'ashewa na kara Fahimtar cewa ni din ba kowa bace a zuciya Ishaq da duka ahalinsa akwai yuyuwar na nemi abunda zan tsaya da kakafuna ko Saboda gaba da kuma ya'yana domin na Lura hankalinsa yayi gaba daidai da su Yaran ya daina Damuwa da su Sosai.
Tun tafiyar nan da yayi sai da yafi wata bai zo ya ganmu ba,Kudin Hannuna duka ya kare bamai lekomu dagamu sai Allah,kayan abincin mu sai ya kare mun fara shiga yanayi sannan ake aiko mana da Cefane wani Lokacin Direban gidan Anty Binta ko Badariya,a wannan gabar sai da yayi wata biyu da kwanaki sannan yazo ya ganmu shima din sallama suka zo yi Zasu tafi Umra shi da Zeey da iyayanta gabadaya har da ita Zeey din suka zo sallama kwana D'aya suka yi suka koma gidan Mama kuma suka Sauka sai da Safe suka zo min sallama,nayi masa korafin Haruna ya fara mganar rashin biyansa akan Lokaci sai ya fara masifan bazai iya ba gaskiya shi bashi da kudi kuma haka ya tafi bai bani ko sisi ba,Daganan na kuduri niyar bazan kara mai mganar ba Zan neman ma kaina mafita,Bani da wata mafita alokacin sai na maida lamurana wajen Ubangiji na rokensa yaga Halin da nike ciki da ni da ya'yana ya Gaggauta sama min mafitan da zan kula da kaina da ya'yana.

*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT Y'A SKWATO__SAKINA HASSAN 08066726866

INA MATA Y'AN KWALISA MASU SON GYARAN JIKI MACCE DA TASAN KANTA KULLUM CIKIN GYARA TAKE

INA MATA MASU FAMA DA RAMA KU KINSA KAYA BASU KAMA JIKIN KI 😫

INA MATAR DA ADDA JIKI BAKI DA HIP BAKIDA BAYA IN KINYI DRESS BAYANKI A SHAFE

INA WADDA KE FAMA DA ZUBEWA NONO KU KE BAKI JIN DADIN GANIN SU KAMAR SILIFAS

KINYI TA GYARAN BRST HAR KIN GAJI HJY TA GYARAN BRST WAHALA GARESHI DUK WADDA TACE MIKI GA MAGANIN BRST DA SHA ZAIYI TO KARYA TAFADA MIKI GYARAN BRST YANA SON JUREWA DA DAGEWA IN KIN FARA BA'A TSAYAWA INSHA ALLAH SAI KIGA SUN ZAMA NORMAL

MUNA DA INGANTATA ZUMA BRST DA MUNKA SARRAFA DA KAYAN ORGANIC HERBAL SU MACA DASU AGUAJE WADDA INDAI KIN RIKE TA INSHA ALLAH ZAKI GA SUN CIKO SUNYI KOSHI RUBA 2 KU 3 SUN ISA YAZAMA MIKI YADDA KK SO 4K

MUNA DA GARIN HIP DA BRST YAKE GYARA DA GYARAN JIKI DA KARIN NIIMA YAKE YI 4K

MUNA DA INGANTATA ZUMA TA HIP ITA MA MUN SARRAFA TA DA KNGAN TATUN KAYAN ORGANIC HERBAL DA KE FIDDA MIKI HIP 6K

MUNA DA ZUMA KIBA WADDA ZAKIYI FRESH DA BULBUL ITAMA RUBA 2 KU 3 ZATA YIMIKI YADDA KK SO 2K

MUNA DA GARIN GYARAN BRST DA KARIN NIIMA SHIMA GUDA 2 KU 3 ZAKI SHA 2K

GASKIYA DA AMANA ITACE NASARAR.MU

MUNA AIKA KAYA KU INA CIKIN YARDA DA AMINCI

MMN MUJAHID __SAKINA HASSAN MUNA SOKOTO DA KEBBI 08066726866

     *🅿️10*

*Wacece ZAINAB...?*

Cikakken sunanta shine Zainab Lawal bako asalin duka iyayanta uwa da uba Fulani ne gaba da baya,Mahaifiyarta Hajiya Halima bata yi karatun boko ba Saboda yar asalin rugar  Njob'oli ne fulani Jahar yola,Shi ma Dr.Lawal din, Mahaifinsa ya'yan maza suke da Mahaifiyar Hajiya Halima auran zumunci ne iyayansu suka kulla a tsskanin ya'yan nasu.
Shi Dr.Lawal a cikin garin Yola ya girma kuma nan aka haifesa saboda Mahaifinsa ya baro cikin Ruga saboda neman ilimi kuma ya samu Dalilin da yasa bai koma cikin ruga ba kenan sai dai Lokaci bayan Lokaci yana zuwa Dubasu,Sannan shima matarsa Daga Rugar aka aura masa shiyasa shima Alhaji Lawal aka ki bari ya bar gida.
Alhaji Lawal bako yayi karatun Boko har matakin Phd dinsa ya fara aiki da Hukumar Tattara haraji ta kasa reshen Jahar Yola,kuma achan ya fara zama bayan an aura masa Halima,Da farko yaso ya Bijirema auran ne,ganin kamarsa mai ilimi dan gayu a had'asa da yar Rugar da batasan komai ba Sai dai ya sauya shawara lokacin dayaje yaga Halima sai yaji zai iya auranta Saboda Tana da kyau Farace doguwar Bafullatana,ga gashi har gadon baya Hancinta har baka kyau kamar ita tayi kanta sai yaji alfahari ya karun masa Saboda Shi yana son abu mai kyau wanda zai zame masa abun Alfahari watarana.
Bayan auran su a yola suka fara zama,Ya na son Halima sosai,Saboda kyanta da sanyin Halinta,sannan Bafullata ne irin sa,Abu daya ne yayi mata cikas rashin ilimin Boko na addinin ma ba sosai take da shi ba Saboda ko acikin Rugar ba kmar yanzu da gwamnati ke basu tallafe tallafe domin inganta ilimi a rugga ba,
Yaso ya barta tayi karatu ammh Saboda Tsananin kishinsa yasa bai barta ba,kuma taso tayi karatun tunda ta dawo cikin gari da zama,ammh ya hanata saboda Yana da Tsananin kishi,bazai jure ganin ta a makaranta tana gwagwamarya cikin maza ba,Sai ya hanata ya nuna mata ilimi mace shine zaman gidan mijinta ta kula da ya'yanta dalilin haka yasa sai ta hakura iyayan su kuma Ilimin bai Dame su ba damuwa suka yi da karatun ba.
Dr.Lawal bako dan boko ne sosai Domin Rayuwar boko yake yi a gidansa shi ya tsara hakan tun farkon zaman auransa da Halima,Ya'yan su biyu ya tsara zasu haifa Saboda a cewarsa bazai zo ya haihu da yawa ba ya kasa Rike ya'yansa ba,Sai dai Kana naka Allah ya riga ya gama nasa Sai da Halima tayi haihuwa Uku suna yin wabi sannan ta Haifi zainab ta Tsaya Tsakaninta da kanwarta Zeenat suna kiranta Zuzu Shekara Biyar ne daga kanta kuma sai ta Haifi namiji sai dai ko arba'in din sa batayi ba ya koma ga Allah Daganan suka tsaida Haihuwa a cewar Alhaji Lawal bako Kada ta kara Haihuwa kyanta da Nagartatan su Lalace ita kuma bata da yadda zatayi bata iya masa gaddama rayuwarta da ita kanta sai abunda ya tsara mata.
Duka ya'yan nasa yadda yaso haka ya tarbiyarta dasu,Halima bata isa ta nuna wani iko kan ya'yanta ba tun suna kanana sai abunda Baban yace shi zasu aiwatar sannan baya shawara da ita gani yake bata san ne take yi ba Tunda bata da Ilimin Zaman duniya.
Zainab da kanwarta Zuzu sun taso cikin Sangarta da Sakewa da kuma Tsananin gata,ba kwaba ba kyara ba Gyara haka suka taso a gaban iyayansu koda sun yi wani abun mara kyau in uwar zata kwaba musu sai Uban ya hana sai ya rika nuna su kadai ne ya"yan su in basu ji dasu ba da waye zasu ji..?Dole ne su ji da su tunda basu da kamar su,In tace hakan bai kamata ba sai yace duk wanda kika ga bai sakar ma ya'yan sa Gata ba bai da shi ne sannan bai san Darajan ya'yan ba ne.
Daga karshe sai ta koma bangaran yaran sai ta Fahimci suma sun fi jin mganar Uban su fiye da ita tun suna yara sun Fahimci mahaifiyarsu kamar Hoto take sai Uban yayi shawara da su,ammh ita bai neme ta ba ko wani abu yace in suka ce Daddy mommy fa..?Sai yace su kyaleta kawai mommy bata san komai a wannan zamanin ba to har suka girma da wannan Tunanin aransu Daddyn su shine nasu uwar su kuma ta nan a matsayin Mahaifiyar su ammh bata da wani Say a gidan da Rayuwar su gabadaya.
Sun taso da Yare guda biyu a bakin su Turanci da Fullanci saboda Daga Uban har uwar basu yarda Yaren su ba In dai suna gida daga Fillaci sai Turanci suke yi Hausa kuma sai dai a waje ko a makaranta,Sannan in sukaje ziyara chan Rugga basa wani yare sai Fillanci sai yaren ya zauna Sosai a bakinsu..
Zainab da Zuzu kyakyawan yan mata ne na gani na fada kamar su, sukayi kan su Saboda kyau da zati to bangaran Uwa da uba duk kyawawa shiyasa suke jajir kamar a taba jini ya fito sannan sun tashi cikin gata da jin Dadi,Zainab ta gama junior secondary dinta suka koma Abuja da zama anan ta ida karatunta ta fada Universty of Abuja ta karanta Chemisty,Gatan duniya ba wanda basu samu ba komai suke nema kafin su yi mgana sun same shi Tun suna kanana komai yan aiki ke yi musu shiyasa su Rayuwar Hutu suka sani da jin Dadin.
Dr.Lawal bako Rauninsa Daya ne ya'yansa yana tsananin kaunar su,Zai iya batawa da duk wanda ya nemi ya tabasu sannan zai iya karta ma kowa rashin mutumci a kan wadanan ya"yan nasa,Yana nuna musu kauna a fili har tana wuce misali Hajiya Halima da suke kira Mommy ko tayi mai mgana sai yace me ta sani kan wannan zamanin tayi mai shuru kawai shiyasa ita nata ido ne sai dai tana addu'an Allah yasa kada su zame mai Raunin da zai zame masa Lalura watarana.
Ishaq kabir karofi ba Zainab ya fara sani ba,Dr.Lawal bako ya fara sani Lokacin da aka mai karin girma da sauyin wajen aiki ya koma Abuja shine ke rike da babban Ofishin su na Abuja,Haka kurum Ishaq yaji Dr.Lawal na Burgesa saboda he is Educated and Innocent,sannan jajirtattace ne kan aikinsa,Shi kuma Ishaq yana da Ladabi da Biyayya ga manyan sa shiyasa suka Saba da Dr.Lawal,Kuma karin ma abun yana ganinsa Farin namiji gaye kyakyawa mai ilimi da sanin ya kamata Dr.Lawal na son harka da mutane masu kyau da wad'anda suka san abunda suke yi,Dalilin Sabawar su yasa Ishaq bai iya kiran sunansa Sai dai yace Daddy kafin shekaru su ja su san komai na juna har gida Daddy kan gayyace sa gidaansa yaje yaci abinci anan yaga Zainab ya nuna yana sonta lokacin tana shekarar karshe a jami'a tana masters d'inta lokacin daya ganta yaji aransa mafarkin daya Dade yana yi ne Allah zai tabbatar masa bai nemi zainab  kai  Tsaye ba sai da ya fara Tuntubar Daddy shi kuma yace ya bashi lokaci ya kara Bincika Ishaq din kuma ya Samu komai yadda ya sanar da shi Cikin Lokaci ya amince batare da Shawara da Hajiya Halima ba Ya'yansa kawai yayi shawara da su,Daman kuma achan Rugga an saka ido kan rashin auran su zainab din,Shi daman baya so ya aurar da su in da zasu sha wahala ne ya fi son ya aurar da su inda yake da Mgana a wajen zai iya kula da ya'yansa ya kuma Tofa komai a lokacin da yaso a kan Rayuwar ya'yansa.
Zainab bata isa tace taki Ishaq ba ganin Farko da tayi mai taji ya shiga ranta suka fara soyayya sai dai da Farko taso ta Damu da taji yana da mata sai ya nuna mata kada ta Damu Fa'iza ba komai bace a rayuwarsa face Uwar ya'yansa ita ce First love dinsa da ta fadama Dr.Lawal Dariya yayi yaji Dadin da yarsa zata kasance Zara Cikin wata Hajiya Halima nata sai dai ido kawai har gwara ma Zuzu bata kai zainab rawan kai da Daukan duka Hallayar mahaifinsa nasu ba ita ta kan tsawarta mata taji,Ita ma tana nan tana karatu a Nile University of Abuja,zainab kuma tana gama karatu tayi Services a wani kamfani karafuna bayan ta gama kuma suka Riketa aiki a wajen,Batare da Ishaq din ya sani ba kuma Lokacin har an yi mgana ta iyaye lokaci kawai za'a sanya har zuwa Lokacin da akayi auran Ishaq bai fahimci bai da wani iko akan Zainab ba sai abunda Mahaifinta yace da shi ta ke amfani.
Shi ya gina auransa kan Soyayya da kyau nasaba kudi da nagartan ilimin zamani,ita kuma ta auresa ne Saboda kyansa da kudinsa sannan saboda Mahaifinta,shi kuma Dr.Lawal bako ya amince da auran ne saboda yana Tunanin Daga Ishaq har Zainab suna karkarshinsa ne zai iya yanke kowani irin Hukunci kan yarsa batare da ya D'aga ido yayi mgana ba.

Muje zuwa..!

****

*Katsina..*
Bayan wata daya.

Mutanen Umra sun dawo an kawo Tsarabobi kala kala nima Badariya ta kawo ma su Amir nasu,abakin ta nake jin Tsaraban ma aiko da shi sukayi ta Abuja suka sauka,Ya Ishaq din kuma bai zo ba,an kawo ma yaran Jallabiya Amir da Musty,Anum kuma Riga da wando,Ahmad kuma kaya riga da wando masu kyau da yarari,Sai Dabino da ruwan zamzam na amsa nayi godiya Daman ni ban saka aka ba ballata don ba'a bani ba na Damu Badariya ta fadamin har Hajiyar Dala an aika mata Da Tsaraba to daman ai ya kamata a aika mata ta chanchanta.

Damuwa ta daya ne yanzu yadda komai ya ke kara lalacewa,Ni ba na jin kaina sai ya'yana sune a gaba,Ko Haruna ni da kaina na shirya na shiga har gidansa Daman makota muke bamu da nisa,Na taba shiga sau biyu tun Fara kai su Amir makaranta,Sunan matarsa Sa'adatu,dayake bana harka da kowa sau daya ta taba shigomin gidan daganan bata kara ba Ishaq bayan Yan'uwana da Dangina har da Mutane ma ya rabani da su Ahalin kuma an ce Mutane Rahma ne.
Naje na same sa na bashi Hakuri akan rashin Biyan sa kudin sa wajen wata uku sai ya nuna min bakomai an zama D'aya tunda Hakkin makota ya hadamu matarsa Sa'adatu ta karbe ni Hannun Bibbiyu,Na isketa tana ta Saida Saide kayan miya da su maggi da gishiri kayan dai kulle kulle na gida na mata sai kuma zuwa ake yi ana siya sai abunda ya bani sha'awa naji Dama ni ce ban iya shuru ba har sai da nayi mata mgana nace dama nice ita ina son nima na Fara sana'ar cikin gida na mata, bata ji ba sai da na kara maimaita mata sannan taji ni Dariya tayi kafin tace"Haba Hajiya kamar ki ina ke ina wata sana'a..?kuna da Rufin asirin ku..Sana"a ai sai irin mu matan talakawa mu samu na Rufa ma kanmu asiri damu da mazajen mu"
Naji mamakin mganarta ni kuma sai nace mata"ai sana'a bata ga Talaka  bata ga mai kudi..Muna yin sana'a ne Domin dogaro da kanmu da kuma ya'yanmu sannan ita mace da neman na kanta a kasanta saboda kada gazawa ya zame mata nakasu watarana"
Sai ta jinjina kai kafin tace"Kuma hakane Hajiya"
Ina kallonta kai tsaye nace"Ba sunana Hajiya ba..Sunana Fa'iza ko ki kirani maman Amir"
Daganan tayi dariya muka cigaba da Hira sama sama,Ban jima ba na koma gida tundaga Lokacin araina na saka ma raina bazan zauna na mutu ni kad'ai acikin wannan gidan da bama ceto sai Allah ba nima zan rika fita na shiga jama'a domin su din Rahma ne.
Muna cikin Haka aka kore su Amir daga makaranta suna dawowa suka fadamin suna zuwa aka koresu kudin makaranta acikin makarantar suka zauna har sai da aka tashi Haruna yaje ya Daukosu hankalina ya tashi na rasa yadda zan yi na so na kira Ya Ishaq na fadamai sai kuma bani da kati ko na flashing kuma bani da ko asi a hannuna sai na koma na Rumgume hannunawana kawai na rasa mafita,kawai sai nace su dakata da zuwa makarantar sai an biya a baya duk Lalacewa yana biyan musu kudin makaranta akan Lokaci basai ta kai ga an koresu ba,ganin sun kwarari sati a agida ba bokon ba islamiyan sai dai nayi musu na Islamiyan agida,Sai suka fara Damuwa suna ta tambaya na Umma meyasa muka Daina zuwa makaranta..?Anum da Musty kenan Amir shi yafi su wayau da sanin me ake ciki,gabadaya na rasa mafita Kwana takwas da Faruwar haka Ranar da yammah sai ga Jamal yazo shima k'wallo suka zo yi anguwan ya shigo gidan ya iske su a bakin Anum yaji basa zuwa makaranta da ya ce meyasa yau basu je ba..?Shine daya tambayeni nace an koresu ne basu biyu kudin makaranta ba yana ta mamaki ya tambayeni ko na fadama Ya Ishaq sai nace mai A'a.
A gabana ya Daga waya ya Kirasa yana fadamai abunda ke faruwa duk da bana jin me yake fada nasan Fada yake yi kuma duk a kaina,Sai da suka gama mgana yace min Ya Ishaq yayi fada kan meyasa ban kirasa na fadamai ba..?
Har Jamal din na fadin"Anty Fa'iza kema da kin kirasa kin fadamai Halin da ake ciki.."
Kallonsa kawai nayi ban yi mgana me zan ce..?ko na fadamai ba ganewa zai yi ba shurun yafi alheri.
Labari har kunnen Mama da Anty Binta na kuma san nasha Zagi da cin mutumci washegari Jamal din yazo ya Dauke su ya kaisu makarantar ya biya komai,Sannan da yammah ya kawo min 20k a bama Haruna kafin ya Dawo na karba nayi godiya da Safe kuma da kaina na shiga na kai mai yana ta godiya nima inayi sai naga ai ni ce da Godiya domin ni yake yi ma alfarma.
Haka rayuwar ta cigaba da gangarawa masu jin dadi suna ji masu jin akasin haka ma sun cigaba da ji,Har azumi ya karato Ya Ishaq bai waiwayo mu ba abun na bani mamaki ace in shi ya manta damu su Mama ai basu manta yana da mata da ya'ya ba ammh sai naga suma basu damu ba kamar hakan ma yafi ye musu,Kayan abinci ko wani sako sai dai ta Hannun Mama ko Anty Binta batagwara,Ni bani da wata Daraja ko kima sai ta zaman ya'yansa kamar yadda yace din.
Tuni yara har sun saba tafiya makaranta ba biskit ba Lemo saboda babu Daga shinkafa sai taliya ake kawo min sai man girki da kayan maggi,duk abunda bazai zama Dole ba ba'a kawo mana shi,Nama ko mun manta rabon mu da shi,ni bana ma jin kaina yaran nake ji sun gaji da Rigima sun Hakura tunda babu sannan Tun suna Zencen Daada har suka hakura suka Dangana ni ce karfin gwiwan su shiyasa bana yarda na Sare ko Raunina ya bayyana agabansu
Ahaka muka fara azumin watan Ramadana,Har kuma muka fara shi muka sauke Ya ishaq bai zo ba,kuma bai taba nema na ba,Ni ma sai na kama kaina sai dai da watan nan mai albarka ban yi barci ba nayi addu'an Allah ya sama min mafita domin ya'yana domin goben su,Kayan sallar yara Sai ana gobe sallah Jamal ya kawo musu Amir da Musty shadda guda biyu sai yan kanti kowanne D'aya d'aya Ahmad ma shadda guda daya sai sauran yan kanti Anum kuma Atamfa da leshi dinkakku sai Doguwar riga guda daya,sai takalma su sai nawa kala daya jal na wata Bakar atamfa,ko araina ban ji zan sakaba sai dai in na zauna ba kaya ammh in dai suturan Ya ishaq ne na hakura da su har abada Tsoffin dai zan cigaba da sawa Tunda  bani da zabi ammh bayan ya jingine aure na dashi na cire ma raina kara Daura wani abu daya fito daga Hannunsa..
Ganin yadda ya kwarari wata Hudu bai zo ya ganmu ba nasan da gaske yake yi ya zabi Zainab a kaina sai ban ji komai ba sai dai naji Bakinciki har da ya'yan sa suma ya jingine su..?
Ban damu ba ni kawai Fafutaka nake yi har akayi azumi akaga gama bamu ci ko tsokar nama ba ballatana su Dankali da kwai sai tsurar abinci kawai nice nake Sarrafa nau'in abincin Tunda Allah yasa na iya sai Wahalan bata mana yawa sosai ba.
Naman Sa da naman kaza Jamal ya kawo min ranar idi da Safe na gyara na soya su Anum nata murna zasu ci Nama sai da nayi musu kwallah ina Tunanin tun yanzu kenan to nan gaba bansan wani Hali ni da ya'yana zamu shiga in dai na zauna ahaka ba,
Allah Sarki Goggo washegarin Sallah sai ga Hafsatu ta aiko da sakon Nama da Cincin da Cake,Naman soyayye da Danye,Sannan da sakon Hijabi Sabo da Anty mariya ta dinkamin da takalmi na karba na rumgume kayan ina kwallah Allah Sarki yan'uwana basu manta dani ba duk da ni ma ban manta da su ba yanayi ne yasa nayi nesa da su ba acikin son raina ba
Ta fadamin daga gidan Tamadina take jiya taje chan ta kwana ta kai mata kaya daga kano Anty Asiya ta aiko dashi sai naman sallah Daga Goggo sai na wajen Ya mariya naji dadin jin Tamadina tana lafiya,Naji takaici bani da abunda zan daga na bama mahaifiyata nima nema nake yi.
Zuwan Hafsah ne ya Debemin kewa Dani da yara Ranar sallah ta uku gidan Mama muka yini sai Dare Ya Ishaq ya sauka shi da Zainab,Anty Binta da Mama suka rasa ina zasu saka su saboda murna mun gaisa da ita sai mamakin ganin chanzawarta nake yi ta zama wata katuwa ta kara gogewa shima gogan ya Sauya kamar ba shi ba har da Tumbi ya sauke.
Darajan zainab yasa da ni da yara da Hafsah ya kwaso mu muka koma gida,Wannan karon ma Shashen sa ta sauka kuma ni na rika wahala da ita da shi,Dalilinta yasa yayo mana Cafane mai rai da lafiya Saboda sai abun take so ake ci acikin gidan,Da kuma zabinta ake amfani..
Hafsah ita kanta da take yarinya sai da ta ga abun bai dace ba ranar da zasu fita yace na shiga na gyara Bangaransa nasa,Suna fita ta kalleni kafin tace"Yanzu Anty Fa'iza bayan Girkin da kike musu har da gyaran inda suka kwana kamar wata yar aiki..?
Ban ce mata komai ba sai ma Dariya kawai da nayi to ai batayi karya ba kamar yar aiki nake agidan nan,Sati Daya suka yi mana suka koma inda suka fito,Hafsah dai ana jibi Tafiyarsu ta koma Karofi Saboda an koma makaranta..
Bayan tafiyar su muka koma Gidan Jiya kamar yadda muka Saba dai,Allah ya taimake ni Matar Ya Isa wajen Goggo ta haihu,yan biyu Dalilin dayasa Mama tace na shirya aje suna Dani,Murna kamar an biyamun aikin Hajji,Dukkamu muka tafi har da Anty Mahma da Halisa da yara,Nima tare da su Amir muka tafi chan na hadu da Ya Mariya,Yaya asiya dai bata samu zuwa ba,naji dadin zuwana karofi Allah yasa kuma Lokacin Tamadina tazo gida na kai mata su Amir ta gansu sai mamakin girman su take yi shi da Anum,Koda wani Lokaci in naga Tamadina sai na tuna da Dan'uwan  ta da akace sun hada Uba,Wanda tunda mahaifiyarsa da Danginsa suka tafi dashi ba"a kara jin Labarinsu ba sai ina Tunanin ko yana Raye..?ina fatan yana Raye domin shi kadai ne shakikin Mahaifiyarmu.
Hajiyar Dala tazo anan take kara Fadin Bikin Diyarta Suwaiba nan da wata Daya,ban saka raina ba Saboda nasan ba barina ma za'ayi naje ba.
Kwananmu biyu muka Dawo gida Mama kuma Yamai tatafi kanwarta Hure mijinta ya rasu ta tafi gaisuwa ta jima tafi Sati biyu Sai Badariya ta Dawo gidana tana kwana in gari ya waye tayi wanka ta shiga makaranta in kuma tana gida mu shiga kitchen tare tana ganin girki Saboda bata iya Sosai ba Tunda bata zaman gidan.
Ita kanta sai da tayi mgana ganin Daga Shinkafa sai Taliya kawai muke da shi tace ban gayama Ya ishaq cefane ya kare ba ne. ?Sai nace ban fada masa ba ashe da ta koma gida Mama ta dawo sai ta fada mata shikenan Cibi ya zama kari wai ina yawo ina fadin Ishaq ya barni da yunwa Mama musamman tazo gidan Har Store ta shiga taga shinkafa ta fara Masifa tana zagina wai wannan abincin dake gidan gidan uban wa zan kai da zan ce ba kayan abinci..?
Har tana fadin nama samu ne mata dadama suna neman irin Damata basu samu ba,Har jamin kunnen tayi kan wai ina albuzuranci da kayan abinci,bai isa ace sun kare ba ko dai ina Saidawa ko kuma ina kyauta dashi Ina mata rantsuwa da abunda zai kasheni ban taba Saida abinci ko nayi kyauta da shi ba,Tace bata yarda dani ba ni bakar Munafukace ni.
Haka tatafi ta barni ina kuka kamar raina zai fita abun ya koma har da kazafin Satan abinci wlh ban taba ba,Ba Halina ba ne sai dai nasan ko zan shekara ina Rantsuwa Mama bazata yarda dani ba.
Sai nayi kuka na ni kad'ai na Share hawayena na riga na yardan ma kaina Allah kadai ke da mafita sannan garesa nake neman mafitana,Acikin wannan tsukin Bikin Diyar Hajiyar Dala ya taso har ga Allah ban sa araina zan je ba sai ga Mama ta aiko Badariya akan na shirya dani za'a tafi kano yara kuna gidan Anty Binta zasu zauna tare da Halisa suna Exams bazata samu zuwa ba.
Ashe ashe da walakin goro a miya,Hajiyar Dala tace azo dani Saboda aikin abinci Shiyasa Mama ta ce na shirya ana gobe biki muka tafi dani da Mama da Anty Binta da Badariya,Su Amir kuma na bar su wajen Halinsa.
Chan muka iske Goggo da Anty Nasara Da Hafsatu Yaya mariya sai adaran da muka isa ta iso,Yaya Asiya kuma ace ciki gareta har ya fito sai korafin na Rame na lalace suke yi  sannan na kara baki na zama kamar tsohuwa ni dai bana cewa komai Saboda bani da tacewa,Tunda muka isa Hajiyar Dala ta Turani Dakin girki,Da Goggo tayi mgana sai Mama tace Saboda na iya ne,kuma don na rika nuna ma ma'aikatan girkin yadda komai zai tafi ni ban damu ba Saboda ai wahala aikina ne.
Ranar Daurin aure da Safe Bak'in Abuja suka Diro Ishaq da Zainab da kanwarta Zuzu wacce bata jin Hausa,ire iren kawayen Suwaibar Hajiyar Dala Hafsah dai da Badariya suna tare,Bamu hadu ba Saboda ina kitchen muna ta aikan abincin yan Daurin aure da ma'ikata,sai Dare na samu kaina ina Dakin da muka sauka nayi wanka kenan,na tada Sallar mangariba su Ya mariya suna Dakin ita da Anty Mahma da ta iso da Safe sai Hafsah,Sai ga Ya Ishaq ya shigo Dauke da Ahmad inaga Hannun Badariya ya karbesa.
Fuskarsa a gintse ganin Ya mariya Ita bata ma san yanayi ba Anty Mahma ce ke mai mgana ya fita ganin ina Sallah ba jimawa ya sake dawowa lokacin na Idar ina zaune ina azkar Tun zuwan su bai neme ni ba sai yanzu na zata ma Ahmad ke rigima ashe wai Girki zan yi amaryansa tace Faten dankalina kadai zata iya ci.,batare da nuna Damuwa ba na amsa masa ya fice Ya mariya ta hade rai ganin ina Ninke Hijabin da nayi salla a harzuke tace"Au ke ce ma baiwar Amaryan tasa kenan..?
Nayi shuru na kasa mgana Anty Mahma tace"Tunda umarnin mijinta ne ki barta taje tayi..Tashi kije Fa'iza"
Da Sauri na kama Hanya zan fice sai Naji Hafsah na fadin"Tab to ai ko achan gidan in yazo da ita..Itace komai nasu abincin su har da gyaran makwancin su"
Ya mariya ta gwalalo ido ni kuma sai na kasa fita na juya ina Harran Hafsah Saboda na jita ina kusa da ita Sanda ta fadi mganar..Anty mahma tace"Kin so ne Fa'iza gaskiya wannan karon ban goyi bayan ki ba..Har da gyaran inda kishiya ta kwanta da Mijina kayyasa.."
Ko da yake naga bakaramin so Ishaq ke mata ba..Ciki gareta naji Anty Binta na fadin shike wahalar da ita mama ai naji da wannan jikan nata Tun kafin ya Fito duniya.."
Ciki..!na nanata acikin raina kafin na girgiza kaina kawai na Fice Daga Dakin ina ji Ya mariya ta fara bala"i ban tsaya jinta ba Domin bazasu taba Sauya ma Tuwo suna ba har Abada yana nan a tuwonsa..
Adaran nan na tike nayi Faten Dankalin Turawa da Hanta,na kuma kai mata da kaina har Bedroom din Hajiyar Dala da ire iren mu bamu da Ikon shigansa.
Ita da kanwarta ne Zuzu,Na ganta duk tayi wani irin fari kamar zabiya tana kwance,Na gaisheta ta amsa tana Dagamin hannu ina ji suna mgana da kanwarta da wani yare shi dai ba Turanci ba kila bayanina take mata naga ta juyo tana min wani kallo ni dai na Fice ban kara kallon inda suke ba.
To bikin ma bai musu dadi ba washegari ya kwasheta suka koma Mama ke yawon fadin Laulayi ne ya sakata gaba mai wahalarwa yace ma ta bar zuwa bikin tace sai tazo Hajiyar Dala kanta ya kara fashewa ballatana da ta kawo kudi masu nauyi ta bata gummuwar Bikin ni duk sai Daga baya nake jin ma sun tafi ban ci Daraja ko arzikin ko sallama ya yi dani ba.
yaya Asiya bata mgana,yaya mariya ne bata iya shuru,Goggo kuma ke Tausanta to ba'a ma yi rabuwar arziki da Goggo karofi da Hajiyar Dala ba Ranar Litini suka koma karofi rayuka ba Dadi,Ba'a san me yahad'asu ba sun dai yi Hayaniya,Mu kuma sai ranar Talata muka koma katsina tsinke na abun Biki ba wanda ya bani ni kuma ban saka rai ba ammh su Mama sun yi guzarin Kayan fulawa da kalanda da jakunkunan rabo kaya dai niki niko ni ko Cincin kad'ai Ya Asiya ta bani na Riko ma su Amir.'

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866

Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta

Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake

Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba

Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳

Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take

Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi

Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce

Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866

IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀
 
       *🅿️11*

Ta gidan Anty Binta batagwarawa muka fara sauka saboda yara nan muka yi sallar mangariba da isha'i sannan nayi shirin tafiya ganin Mama bata da niyyar tafiya, ni kuma Saboda Dare sannan ga yara,Ganina cikin shirin tafiyasa yasa Mama tace na tsaya su Amir su ci abinci,kamar abun arziki na zauna suka ci abinci nima Halisa ta zubomin naci kad'an na kora da ruwa shuru shuru Mama taga na zauna ban tafi ba tagaji dai tamin mgana sai na fad'amata bani da kudi a hannuna ballatana mu yi na adaidaita zuwa gida.
Shikenan Mama ta fara fad'a ta inda take shiga bata nan take fita ba, ta kalleni tana fad'in"Ke kan Fa'iza ban ga amfanin ki ba..Tun da Ishaq ya aure ki bai Huta da wahalhalun ki ba..da an tabaki sai kice baki da ko asi ke ko irin Dubaran matan wannan zamanin baki iya ba? sai dai komai ki kwanta miji yayi miki tunda ya zama bawan ki"
Anty Binta na gefe ta karb'e da Fadi'n"Kuma Mama komai ne sai ka zauna miji ya baka..?,tsakani ga Allah yana ma kokari wlh,ammh duk da haka ba'a gani barin ma Yan'uwanta da Goggon Karofi,su yi ta korafi kuma in za'a duba tafi duka yan'uwanta jin Dadi ita Asiya ai malamin makaranta take aure ga abokiyar zama ita kuma Mariya d'an kasuwa ne mai karamin karfi ba wacce takai jin dad'in da Fa'iza take yi acikin su ammh kullum gani suke tana cikin Wahala'"
Mama ta ja tsaki kafin tace"To ai duk laifinta ne ita ke fad'a musu haka..Shiyasa nace miki Har ga Allah ban so hada zuru'a da Dangin Asiya da Sidi ba, domin nasan ba Dangin Alheri ba ne na tsiya ne kawai"
Ni dai ina zaune kaina a kasa na kanzil ban ce ba sai da suka gama cin zarafina sannan Mama ta zage jaka ta Dauko Dari biyar ta wurgomin tace sai na tashi na bar gabanta bata son ta kara ganina.
Jiki ba Karfi na mike nayi musu sallama yaran suna D'akin Halisa na Bisu na taho da su ko Tausayi na Mama bata ji ba ga goyon Ahmad ga Amir ga Anum ga Musty kuma na Tabbata Direban gidan zai kai Mama gida ni kuma Saboda k'iyayya bazata iya had'a Hanya dani ba.
Haka na fita ina Tare tare da su Allah ya taimake mu kafin mu isa Titi muka samu abun hawa zuwa gida.
Tunda daman dukkan mu a koshe muke sai shirin kwanciya kawai nayi musu,Tundaga Lokacin kuma Rayuwar mu ta cigaba da gudana yadda take tun farko ba chanji.
Ya Ishaq ko Labarin sa bana ji Wayar ma tawa ta Lalace inaga yara ne suka Y'ar  min ita a kasa ta bare biyu da na Had'a kuma nayi nayi ta kawo bata kawo ba sai na Hakura na tattara ta na ijiye ba mai nema na ni kuma ina gida Dagani sai ya'yana tun had'uwar mu da shi a kano sai da ya shafe wata biyu sannan yazo ya ganmu shima kwana d'aya yayi ya koma ko da daman ya Dawo komai na Cefanan mu ya kare daran ranar ma da yunwa yaran suka kwanta da Rana na samu nayi musu danwake da sauran garin Danwaken daya rage Shima jikinsa yayi sanyi daya ga ko kwaran abinci bamu dashi ya kira Mama yana mata mgana ga dukkan alamu komai na mu yanzu ya koma wuyar Mama ne.
Ya bani dubu biyar a hannu sannan ya Biya Haruna kudin watansa biyu ya tafi bayan ya fad'amin zai Dad'e bai zo ba zainab bata da lafiya Laulayi na Matsa mata shi ne ke kula da ita ban damu ba nayi mata fatan Allah yasa a rabu lafiya domin ni yanzu duniya baya gabana ballatana na Damu da abunda ke faruwa acikinsa ni dai kawai ya'yana sune nake ji sannan kuma zaman su nake yi,kuma Allah ne gata na garesa nake kai duka kukanaa..
Tun bayan da ya tafi ko gidan Mama da nake zuwa na Dauke kafata saboda sai in ina da kud'in zan je,kuma koma naje ba tarban arziki nake samu ba Shiyasa na kame kaina agefe Badariya ne ke d'an lekomu Lokaci bayan Lokaci sai Jamal in yazo gida Huta yakan zo Tunda suna yawan zuwa anguwan mu buga Kwallo.
Mama da Anty Binta kuwa Daman indai ka gansu to tabbas ba alheri ba ne ya kawo su.
Bangaran Karofi ma shuru ba wani Labari Hafsatun ma da kan lekoni kwana biyu ban jita ba tun rabuwar mu da ita a kano bana jin kowa nima bamai jina,Dani da yarana muka kulla kawance da juna in sun Dawo makaranta suna tare dani sai in barci yazo sun ma daina Damuwa da Zencem Daada Anum ce daman mai Rigima sai Mutsy to yanzu sun gaji sun Daina yawan damuna da Tambayansa sai nima hakan ya fiyemin saboda wani lokacin na kan rasa amsar da zan basu.
Ahmad na da shekara Biyu,na fara Tunanin ciresa a nono na yayesa ammh bani da komai da zan rika basa Tuni daman acikin Cefanan mu aka daina kawo mana kayan Tea,kuma ba ni da wani garin kuni ballatana na rika Damawa sai na kasa ciresa a nono Saboda kada ya wahala ni kaina bani da Lafiya duk na kara ramewa sannan ina Faman da yawan ciwon kai da jiri tsaye kawai nake ina tafe da Lalura ban sani ba.
Satin da muka shiga a Daddafe nayi sa saboda ciwon kan ya matsa min ga jiri  da zazzabi,sai dai ban kwanta ba Saboda yara,in suka fita makaranta sai na Dad'e ina kwance ina fama da kaina tun ina Daurewa har sai da ciwon ya kwantar dani Daran jumma'a,Cikin Dare na tashi na shiga Bayi na Dauro alwala kawai jiri ya kwasheni na koma na kwanta Tun daga Lokacin jikina ya rikice,sama sama nake jin komai kaina kamar zai Tsage gida biyu ga zazzabi na jin jikina,ina so na tashi ammh na kasa tashi ina jin su Amir suka shigo suna kirana "Umma.."Umma.."
Ammh na kasa amsawa Ahmad ma ya gama Budurina ajikina yana ta Dukana yana kiran sunana da gwarancinsa ammh na kasa tashi,ganin Halin da nake ciki yaran suna Tare dani barin ma Amir dake da wayau ya fahimci bani da lafiya su Anum nata damuna da surutu yace su daina Umma bata da lafiya Anum yar rigima sai ta saka kuka ganin haka Musty ya kama Amir ya Lallashe su.
Ina jin Amir na taba kafata yana fadin"Umma..Umma ana buga get"
Dakyar na iya bude baki nace"je ka bu d'e Amirr.."
Tare suka fita da Anum da Musty yana kai wa daman wajen sakatar tsakiya ne ya bud'e ashe Haruna ne yana ganin su basu shirya ba yace"Au yau ba zuwa makaranta ne Kabiru..?
Amir ya karkace kai kafin ma ya samu mgana da Sauri Anum tace"To ba Umman mu bata da lafiya ba ne"
Haruna yace"Subhanallah..Allah ya bata lafiya"
Aransa daman yayi tunanin haka Tunda bakwai da rabi bai taba fashi basu shirya ba,har zai wuce Anum ta saka kuka tana kiran Umman su,Haruna ya kalli Amir yana fadin"Jikin nata yayi zafi ne..?
Amir ya gyada mai kai yana fadin"eh bata iya tashi ma"
Cikin alhini yace"Bari nayi ma mai dak'i na mgana sai ta shigo ta duba ta..Allah ya bata lafiya"
Cikin Hanzari ko ya shiga gidansa ya samu matarsa Sa'adatu na sharan Tsakar gida tana ganin mijinta cikin mamaki tace"Ah baka tafi ba ne Megida..?
Cikin wani yanayi yace"Wlh ke dai bari naji shuru ne yaran basu fito ba na buga gidan sai ga su sun bude gwanin ban tausayi suna ta kukan wai Umman su ba lafiya"
Sa'adatu tayi salati kafin tace"Wayyo..Allah ya bata lafiya"
Ya amsa da Ameen kafin yace"Sako mayafin ki ki shiga gidan ki ga Halin data ke ciki"
Bata yi musu ba ta ijiye tsintsiyan Hannunta ta shiga D'aki ta sako Hijabi tace bari taje ta gani,a kofar gidan ma taga su Amir taja su zuwa cikin gidan Halin data ganni a ciki yasa Hankalinta ya tashi da Sauri ta fita ta koma gida ta fadama mijinta ga Halin da ake ciki.
Cikin wani yanayi yace"Jikin nata yayi zafi kenan..?.
Sa'adatu tace"Gaskiya ya kamata a tafi asibiti"
Ya jinjina kai yana fadin yana da lambar Ishaq bari ya kirasa sai dai yayi ta kira har sau uku bai daga ba sai kawai yace Sa'adatu ta shiga makotansu gidan wata Habiba ta mata mgana sai a kai yaran gidanta su kuma su tafi dani asibiti tunda ba'a samu Ishaq a waya ba.
Haka ko akayi ta shiga tayi mata mgana Habiba duk da bana Huld'a da ita bata ki ba tace zasu zauna a wajenta har mu dawo tare da Fatan sauki a gareni.
Sa'adatu ta sakamin Hijabi dakyar ta iya fito dani na shiga adaidaita sai general Hospital muna zuwa ganin Halin da nake ciki yasa suka karb'eni suka shiga dani bayan Dube Dube da gwaje gwaje suka bani gado bayan sun Dauramin Drip ana bukatar kudi mganguna,sannan Likitan ya fad'ama wad'anda suka kawo jini na ne ya yi sama sannan ga Zazzabi a jikina sosai.
Na galabaita da sai sun rikeni anan na kwana Biyu,Allah sarki ni ban san inda kaina yake ba ammh ina kwance ne Hankalina na wajen ya'yana sai da yammah na farka da su na Bude bakina Sa'adatu ce a wajena tun Safe girki kawai ta koma gida tayi,ita ke fadamin su Amir na gidan makociyarta Habiba cikin koshin Lafiya ta tambayeni ko ina da Lambar wanda za'a kira a sanar da su nace babu Saboda Lambar goggo kad'ai na Haddace kuma bana so a kirata a tada mata hankali.
Sai Dare Haruna ya biyo bayan ya Taso daga aikinsa ya Dubani ina ta musu godiya,ya kalleni kafin yace"Na yi ta kiran megidan ki bai Daga ba..Ko kina da lambar yan"uwan ki na nan sai ki bada na kira su na shaida musu"?
Kafin ma nayi mgana Sa'adatu ta bashi da amsa da nace babu.
Sai ya kara fadin"To ko gidan kakanin yaran nan zan je na shaida musu..?.
Sai na kasaa mai gaddama na D'aga mai kai kawai nan na kwana Sa'adatu ta kwana dani nayi nayi ta tafi gida tace bakomai su Amir kuma ta kira Habiban ta mata bayani tace bakomai zasu kwana a wajenta.
Washegari da Safe ta koma gida ta yi wanka ta yi abinci da Haruna yazo da Safe yace daganan gidan Mama zai je ya fadamata saboda yasan gida yana kai su Amir watarana in ya Dauko su daga makaranta.
Abun mamaki har Dare ba wanda yazo kuma daya dawo yace yaje ya sanu Maman da kanta ya fadamata,ammh kuma ba wanda ya lekoni sai Habibar ne tazo da yammah ita da su Amir suna ganina suka Nufeni suna kiran sunana na Rumgumesu ina jin Tausayin kaina,basu jima ba ta tafi da su ina ta mata godiya ganin su Amir sun yi tsaf dasu,tace bakomai ai d'a na kowa ne sai Dare sa'adatu ta dawo min da abinci da kayan da zan sauya na rasa da kalmar da zan gode musu su yi min gatan da su mama suka kasa yimin.
Sai da na kwana uku a asibiti sannan Sai ga Mama da anty binta sunzo dubani Lokacin ma naji sauki sosai basu iske sa'adatu ba ta koma gida ina gadon asibiti ma ban tsira wajen Mama ba, sai fad'a take min wai da gangan na kirkiri ciwo saboda ishaq ya dawo gabana ya Lalace to ban isa ba kaina na kasa ina kokarin maida hawayen dake cikin idona Anty Binta ne ta kalleni tana fadin"To meke damun ki..?
Wata mata dake jinyar na kusa da gadona Saboda general ward ne na mata tace"Haba baiwar Allah kya yi mata hankali baki ga bata da lafiya ba ne..?kun sameta ma yau da Sauki Sauki da kun ganta sanda aka kawota sai kun Tausaya mata Hawan jini yanzu ya zama ruwan Dare baga yara ba, ba ga manya ba"
Anty Binta da Mama suka kalli juna kafin Mama tace"Hawan jini..?
Anty Binta tace"Ba dole ta samu hawan jini ba ta sakama ranta bala'i ..Ishaq dai kike ma wannan kwanciyar shima mara lafiyan garesa achan tunda muna nan basai yazo ba"
Mama ta karb'e da cewa"Ai na gayamasa yayi zamansa kawai ya kula da Zainab"
Ina jinsu kaina na kasa ban ce musu komai ba suka gama cimin mutumci suka tafi ko tsinke basu zo min dashi ba,ba tambaya waya kawoni asibiti ina yarana..?ba abunda ya Dame su bayan tafiyar su haka na koma na kwanta ina ta kuka Matar dake kusa tace"Ki daina kuka kada ki kara ma kanki Lalura..Wad'anan dai ko suwaye basu da kirki kina gadon asibitin ma baki tsira ba..?
Ni dai na kasa mgana Likita yazo yayi zagaye da yazo wajena na tashi zaune idanuwana sun kumbura ya duba Fayel d'ina yana kallona kafin yace"Fa'iza Ishaq kin san abunda ke Damun ki..?
Na girgiza kai na alamun a'a cikin Sanin aikinsa yaja farar kujeran dake gefen gadon da nike kwance ya zauna yana fadin"Hawan jini..Jinin ki ne ya d'aga Sosai sannan kina da maleria"
Na dago ina kallonsa duk da naJi matar d'azu ta fad'a sai da nayi mamaki cikin yanayina nace"Hawan jini Likita..?
Sai ya d'agamin kai ya cigaba da fadin"Ki daina yawan Tunani in kina so ki Tsira da lafiyarki..Damuwa ita ta Haifar miki da matsalan da kike ciki..Sannan daga yau ki rika kwana cikin gidan Sauro saboda rigakafin Cizon Sauri Maleria na tada Hawan jini..Shima Hawan jinin yana Tada maleria in suka Had'e ma Mutun kuma bama son haka kiyi kokarin cin abinci sosai ki kuma kiyaye dokokin mu"
Na jinjina kaina kafin nace"Nagode likita..ina so ka sallame ni na koma gida"
Ya kalleni kai Tsaye kafin yace"Mijin ki ne zai dawo..?Domin wanda ya kawoki ya ce shi makocin ku ne mijinki kuma yana wajen aikinsa"
Cikin yanayin mganata nace"Ya'ya na..Likita na bar yarana ba su da kowa sai ni don Allah ka Sallameni"
Mirmishi yayi kafin ya mike yana Fadin"kada ki damu zuwa gobe da Safe zaki koma gida"
Na gyada mai kai daga haka ya wuce gado na gaba ni kuma na koma na kwanta ina Tunanin yadda rayuwata ta kare ace ina kwance bani da lafiya ammh ba wanda ya damu dani nasan da Goggo taji bazata zauna ba ni kuma bana son Damuwarta,Yau in da ace mutuwa nayi babu wanda zai san na mutu shi kawai ke sakani kuka.
Da yammah Sa'adatu tazo na tambayeta su Amir tace yau sun je makaranta,har acikin raina naji Dadi idona ya cika da Hawaye na kalleta ina Fadin"Nagode sosai..Allah ya saka da Alheri"
Ta amsa min da Amin a raina na Guduri niyyar in naji sauki na koma gida zan gyara mu'amalata da duka mokota na Domin na Lura sune Dangina dake kusa dani,Washegari da Safe aka bani sallama sai dai bamu tafi ba ba'a biya kudin gado da Sauran kashe kashe ba,Sai da Haruna ya koma gidan Mama ya fad'amata tace zata zo sai da muka kusa yini a asibiti sannan Anty Binta tazo tana ta wani yamutsan fuska ita ta biya duka kud'in da ake bukata sannan ta siya mgangunar da aka rubuta bata tsaya ba ta kara gaba Sa'adatu ta kamani ta Daukan mana Sauran kaya  muka yi sallama da yan daki muka fice.
Har cikin Dakina Sa'adatu ta kaini ta zaunar dani ina ta mata godiya matar nan bata tafi ba,Sai da ta share Dakunan ta gyara ta Dora girki Saboda yara ita ta Dinga fad'ama makotanmu bani da Lafiya duk da bana shiga ammh suna ta Shigowa Dubani har da Habiba ina ta mata godiya tace bakomai wlh..
Har yammah tana tare dani sai da su Amir suka dawo makaranta sannan ta koma gida bayan har wanka sai da ta tsaya nayi na sauya kaya naci abinci dakyar na sakata ta D'iba abincin da ta Dafa tatafi da shi su Amir sun yi murna da ganina motsi kad'an sai Amir yace"Sannu Umma Allah ya baki lafiya'
Sai na amsa mai da Ameen Amir su Anum kuma ba wayau suna ta wasan su sai dai sun yi murnan ganina Ahmad kuma saboda kwana Biyu bai sha Nono ba,sai ya manta da shi,Sai dai Habiba tace ya sha Rigima kunu take Damawa tana bashi,ya lafe a jikina yayi shuru Tausayin sa ya kamani na Rumgumesa ina jin kamar na fashe da kuka kwana biyu ne bana nan ammh ya'yana ma sai makota ne suka kula da su inaga in ba na tare da su gabad'aya Allah kad'ai yasan wani Hali zasu shiga shiyasa zan Daure zan kuma Jajirce saboda goben su
Washegari da muka Dawo gida ma Tun Safe sa'adatu ta shigo ita ta shirya yaran tayi musu kari dayake ita bata taba Haihuwa ba,bayan sun tafi makaranta tazo ta gyaran gidan,ta koma gida chan anjuma kuma tadawo tayi ma yara girki nasan ko bata fada ba aranta tana so ta tambayeni bani da Dangi ne..?
Ai rashin gatan yayi yawa sai dai bata ce min ba nima ban ce mata ba.
Kwana na Hudu da dawowa asibiti na ji sauki Nace sa'adatu ta daina zuwa tana min wahala na samu lafiya,Ranar har gidan Habiba sai da na shiga na kara yimata godiya sai dai duk wanda yaganni yasan na rame duk na kara Lalacewa.
Sati daya da faruwar abun Badariya tazo Dubani tana bani Hakurin bata sani ba sai abakin Halisa taji har asibiti na kwanta,ta yinin mu sai yammah da Halisa tazo dubani suka tafi tare,Ita ce ma suna mgana da Hafsah ta wayar Goggo ta fad'amata nayi ciwo har asibiti na kwanta ashe su Hafsah suna kano Yaya Asiya ce ta Haihu,suna kano shekaranjiya akayi suna Hafsa ke fad'ama Goggo tana ta Fadan ba wanda ya fadamata ballatana sauran yan'uwana kuma suna ta kiran wayata a kashe basu san ta Lalace ba..
Ranar laraba da Safe sai ga su A gidana Daga kanon suke Yaya Isan goggo yaje ya Dauko su a motarsa,Goggo ce sai Anty Nasara da Yaya mariya sai Hafsatu sai matar Isa Amina,sun zo sun ganni suna ta tafad'a gani na duk na fad'a na rame Goggo ta kalleni tana fadin"In wayarki ta lalace baki aron wata wayar makota ki kiramu Fa'iza"?
Kaina na kasa nace"Goggo ban da lambar kowa a kaina kuma layin yana gida"
Anty Nasara tace"to wa ya zauna dake..?
Kaina na kasa tace"Matar makocin mu haruna mai kai su Amir makaranta"
Su Goggo suka saka salati suka Dire,Yaya mariya tace"Daman wa kuke tunanin zai zauna da ita..?
Mama ko Binta..?azzalumai bakomai a zuciyar su sai mugunta ayi dai mu gani"
Goggo ta juya tana kallonta Lokaci daya tana fadin"Mariya..mariya ana rabaki da kiwon awaki kina fadin kyalla ta Haihu daga Saudatun har Binta ai ba sa'anki ko.?
Yaya mariya ta tura baki kafin tace"Ai gaskiya na fada goggo wlh wani Hisabin sai a lahira kalli yadda Fa"iza ta koma kamar wata yar aiki kalli gidanta kalli kujerun ta duk sun Fita Hayyacin su kuma wai wannan mai kudi take aure Allah dai ya waddan kudin miji in dai na irin mijin Fa'iza ne bashi da amfani ko ni da mijina karamin ma'aikaci ne wlh d'akina yafi na Fa'iza kyau sau dubu Saba'in wlh"
Anty Nasara na gefe ta kad'a baki tace"Ai ba gidan ne ya fita Hayyacinsa ba..ita kanta Fa'izan ku dubeta ku gani yadda duk ta fita kammaninta"
Fadin haka yasa duk suka sakamin ido suna karemin kallo Goggo tace"Duk kubar mganar nan mganar kayan daki zamu sauya mata in sha Allahu ai mune yan'uwanta Dolenta na kanmu Ishaq ba wajibinsa ba ne yayi ma Fa'iza komai ba"
Yaya mariya ta kad'a baki tace"ammh ai yana da shi..kuma bai gagaresa ba in da mutumci a wahalan da Fa"iza tayi da shi da danginsa ta chanchanci komai a wajensa"
Goggo tayi saurin tare mganar da kallona tana fadin"Fa'iza wannan ramar tayi yawa me ke damun ki ne..?
Sai nayi shuru na kasa mgana nasan in nace Hawan jini gareni na bude Sabon Shafi sai nayi kamar ban ji ba Sai da goggo ta kara mgana Sannan na ce mata Zazzabin cizon Sauro ne.
Goggo nata fad'an ko bana kunna mganin Sauro ne ni dai nayi shuru ban ce komai ba.
Hafsatu tayi girki Yaya mariya kuma ta ragemin wankin su Amir,daman sun taru Aminan isa kuma ta gyara Falon da Dakunan.
Bayan sun ci abinci sun yi sallar azahar na saka Hafsatu ta shiga da su gidan Sa'adatu suka yi mata godiya daganan nace suce ta kai su gidan Habiba itama suka mata godiya sukace bakomai ai yiwa kai ne.
Muna tare da su har La'asar akace Dan'uwa mai dadi naji Dadi sosai Yaya mariya ta nuna min Yaya asiya da D'anta a waya hoton da suka Dauka Ranar suna tasha kyau abunta sunan yaron Muhammad Auwal.
Sai bayan La'asar suka yi shirin Tafiya,Yaya Isa daman ya shiga cikin gari ne sai ga shi ya Dawo Hafsatu ta sakamai abinci da yake tana fashin Sallah tana falo Aminan Isa da Anty Nasara na Dakina suna sallah ni kuma ina Dakin su Amir ina sallah da ni da Yaya mariya Ahmad na goye a bayan Goggo Tun da ya fara rigima ta karbesa ta goyasa.
Ni dai na idar da sallah ina zaune ina azkar Sai naji mgana sama sama afalo Yaya mariya ta tashi ta fita,ba jimawa sai ga Hafsatu ta leko tace Goggo na kira na,Ina fitowa nagan su Tsaye sun yi cirko cirko gabana ya fad'i na zata ma wani abu ne,Goggo ta kalleni da Kwalin mganina a hannunta kafin tace"Ashe Fa'iza hawan jini gareki kikace mana wai zazzabin cizon sauro ne..?
Sai na kasa mgana na Dukar da kaina Yaya mariya ta yi kyafci kafin tace"ai bazata fad'a miki ba Goggo..Na rasa me Ishaq ya bama Fa'iza ya shanyeta bata kaunar Laifinsa daga shi har Danginsa"
Goggo ta kalleni ta kara kallo na kafin ta saka salati tana fadin"Na shige su ni Indo..Yanzu da ba domin Nasara taga mganin nan kuma tasan ko na menene ba da haka zata bar mu a matsayin Maleria ke damunta haba wannan ramar na Fa'iza ya yi wa ashe ashe Hawan jini gareta da kananun shekarunta"
Yaya Isa na gefe yayi karamin Tsaki kafin yace"Ba Dole ta kamu da Hawan jini ba Goggo..An aura mata wanda baisan Darajanta ba..Ina jin Labarin zaman Hakurin da yarinyar nan ke yi ku kuma su goggo kun kasa D'aukan mataki akan haka ai aure ba Bauta ba ne ibadan ubangiji ne ba na abokin Hallita ba..Ya maida matarsa kamar wata yar aiki ko baiwa yana chan Abuja ya tare sai yaga Dama yake zuwa Fisabillahi wannan adalci ne..?
Goggo tayi saurin tare shi da Fadin"Mijinta ne ya fi mu iko da ita..Sannan zaman aure ai zaman hakuri ne,Kuma ibada take yi Isa kada kace bamu Dauki mataki ba in ba so kake mu kashe mata aure ba"
Yaya mariya tayi karaf tace"Wlh Goggo da auran Fa'iza dai gwara zawarci"
Goggo ta aika mata da Dakuwa tana Fadin"Ya'yan nata fa ke zaki rike mata su in ta fice ta barsu da kananun shekaru..?
Yaya mariya ta tura baki kafin tace"Su zauna gidan Uban su mana Goggo"
Goggo tayi dariyan takaici kafin tace"Kayya mariya ai rikon ya'yan wani ba kowa zai iya ba sai wanda Allah ya bama wannan..Sannan kuma ya'ya sai uwar su mariya..Yanzu dai Allah ya kyauta..Tunda abun ya zama haka Mariya in ba Damuwa ki kara kwana ko zuwa gobe jibi in megidan naki zai bari lokacin ta kara watsakewa kinga Hafsatu suna da makaranta"
Yaya mariya tace"Bakomai da na kirasa bazai ce komai ba su Abba kuma suna gidan kakkaninsu daman."
Goggo ta kalleni tana fadin"Ga mariya nan zata zauna ta kara taimaka miki zuwa jibi ni kuma zan tafi da Ahmad tunda kin yayesa in kika ji Sauki kika warke sai na Dawo miki dashi"
Ban iya ma Goggo musu ba na tafi na Had'o kayan Ahmad na bata,Nasan tayi hakane saboda ta ragemin wahala sannan duk da ina jin Tsoron me zai biyo baya,ammh bazan iya ce ma Goggo A'a ba saboda ita kamar makwafin Tamadina ne a wajena duk da tana raye.
Ya Isa nata fad'a Goggo bata Biye masa ba Ta lallasheni tare da kara Jadaddamin nayi hakuri watarana sai Labari Goggo ta bani dubi biyar Ya Isa dubu uku kafin su tafi,Suka barni da Yaya mariya ta tasani tana ta min Fad'a wai na zauna na zama sakarya miji da Danginsa suna yadda suka ga Dama dani ni dai ban ce mata komai ba sanin Halinta.
Da yammah ko da su Amir suka Dawo basu ga Ahmad ba,na fad'a musu Goggo tazo ta tafi da shi suka fara Tsallen suma Yaya mariya ta tafi da su ta kyabe baki kafin tace"Wannan uban naku mai bakin hali ai bazai bari ku rabemu ba duk dai abun su bai isa ya sauya ma Tuwo suna ba"
Ban tab'a kawo ma raina Ya ishaq zai iya Dawowa ba sai ga shi washegari da yammah ya Diro dirowan bazata yayi mana Muna falo ni da yaya mariya,ita wayarta take latswa ni kuma ina kwance kan kujera mai zaman mutun uku duk da naji Sauki ammh jikina ba karfi su Amir na makaranta basu dawo ba.
Ko sallama ma bai yi ba sai da ya shigo Falon kuma da Yaya mariya ya fara cin karo suka yi ma juna kallo daya suka Dauke kai ni kuma jikina na rawa na tashi zaune ina gyara Wuyan rigana cikin rawan jiki da na zuciya nace"San..nnu..da zuwa.."
Wani irin kallon da ya bini da shi yasa Hantar Cikina ta kad'a na fara maimaita innalillahi acikin raina ko amsani bai yi ba kamar Hadari haka ya shige shashensa ya Banko kofa.
Na dago na kalli Yaya mariya sai tayi kamar bata ganni ba ta mike ta shige Dakina tayi kamar tana waya ni kuma jikina na rawa na shiga Kitchen bamu da ruwan gora na Daukomai purewater na saka a Filet da kofi gabana na fadi na nufi bangaransa Gabadaya ilahirin jikina ba inda baya raawa ina fatan kada Abunda nake tsoron Faruwarsa ya faru da na shiga Uku.

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866

Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta

Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake

Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba

Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳

Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take

Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi

Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce

Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866

IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀

      *🅿️12*

Ina shiga Bangaransa na iske sa tsaye a tsakiyar falon yana ta safa da marwa saboda bala'i hatta jakar da ya dawo da ita bai iya sauketa ba kamar yana jira na ina shigowa da sallamata yayi saurin zaburowa Sauran, sallaman tawa ma iya makoshina ta makale jikina ya Dauki karkarwa kamar wacce taga mutuwarta.
Hannunsa manuniya yasa ya na nuna ni cikin Matukar fushi yace"Me na gaya miki..?
Nace me na gaya miki Fa'iza akan wannan mara mutumcin yayar nan taki..?
Yafad'a Lokaci d'aya yana dagamin murya sai na tsaya na kasa gaba ballatana baya jikina na wani gif gif kamar wacce wani abu ke ja kafafuwana suka fara barazanar kayar dani sai nabi Raunin su suka rinjaye ni na koma na Durkushe saman kafafuwa na lokaci daya ina sauke sauke farantin Hannuna ina so nayi mgana na kasa tsoro nake ji kada Yaya mariya ta jimu tunda Jikin Shashen sa na jikin Dakina ne bazan so a ce yau mijina ya Tozartamin yar'uwa ba.
Ina wannan tunanin sai ji nayi ya sakar min gigitaciyar Tsawa Lokaci d'aya yana kara fadin"Nace me na fada miki Fa'iza..?
Hawaye suka gocemin na Tsoron abunda zai biyo baya,na yi baya da jikina ina karkarwa na had'a Hannayena cikin yanayin mgana ta da rawan baki nace"Don..Allah..Kayi hakuri ka yi shuru..Na kasa fad'a mata ne bazan iya ba..wlh bazan iya ba.."
Sai hawaye sharr suka gocemin wasu na korar wasu,Tsayawa ya yi yana min wani irin kallo na raini da kaskanci kafin yace"Au bazaki iya fada mata ba ko..?To ni bari naje na fada mata tunda gida na ne ba gidan wani ba"
Ya karishe fada a fusace yana sauke jakar da ya shigo da ita nan tsakar Dakin nasan zai aikata tunda ya furta Da sauri na mike na isa garesa na Durkusa ina kuka ina fadin"Don Allah..don Allah..!
Mgana ta ta kasa fitowa saboda kukan da yaci karfina Ganin yayi banza dani ya nufi hanyar ficewa yasa na kwashi gudu na isa ga kafarsa na kama na rike gam ina kuka kamar raina zai fita ina fadin"Kada ka tozartamin yar'uwa..Ka bari zata tafi..Zata tafi.."
Sai ya tsaya yana kallona kafin yace"Yaushe zata tafin..?
Cikin kuka nace"Gobe..Gobe zata tafi na rantse da Allah.."
Ko sake kallo na bai yi ba ya Fizge kafarsa sai da nayi baya na fad'i ya Fice da Sauri,ina ganin haka na mike sai da kaina ya sara jiri ya kwasheni ammh ban damu ba na marasa baya ba inda jikina baya rawa har da zuciyata ma gudu take yi da sauri a lokacin.
Sai dai me zuciyata ta tsaya waje d'aya lokacin da na fito na iske Yaya mariya Tsaye a tsakiyar falon daga dukkan alamu ta gama jin duka mganganun mu Saboda Ya Ishaq da karfi ya Dinga Tijaransa,Kasa karisawa nayi kawai sai na Tsaya ina raba ido jikina da zuciyata gabadaya yayi wani Dum kamar ya daina aiki na wani Lokaci.
Ya ishaq kuma yana ganin Yaya mariya bai yi wata wata ba ya gyara Tsayuwa yana fadin"Nasan yar'uwan ki bata gaya miki sako na ba ko..?
Yaya mariya ta kallesa cikin idon da bacin rai yasa s Launin su ya sauya kafin tace"Bata gayamin ba..Ammh Tunda kaga ai waka a bakin mai ita tafi dad'i"
Tafad'a Tana kokarin yaki da zafin zuciyar dake taso mata,Taji duka mganganun Ishaq ta dade tana jin Labarin Rashin mutumcinsa, bata taba katari da shi ba sai yau lalle ko zai sha mamakinta domin in ya yi mata kan kara wlh sai tayi masa na itace.
Cikin gadara yace"Na fad'a mata tun kwanaki da kada na kara ganin ki acikin gidana..Bazai yuyu ki rika shigomin gida bakya daraja ni ba..Kamar ni zaki rika gani kina D'auke kai kamar kin ga kashi..?ai ba gaba da ni kike ba ko Yayarku Asiya ba Sana'ata bace ballatana ke karamar alhaki kin raina uwata da yayata suna fada kina fada sannan ki rika shigomin gida kina raina min wayau bazai sabu ba..Kada na kara ganin kafarki acikin gidana Daga yau sai yau..In yar'uwanki zata yi zumunci dake in kun had'u awani waje ban hanaku zumunci ba ammh ba acikin gidana ba"
Ya karishe fad'a cikin nuna cin mutumci har yana nuna ta da Hannu,Yaya mariya tayi dariyan takaici kafin tace"Shikenan sakon naka..?
Ya daga mata kai Lokaci d'aya yana fadin"eh shikenan"
Yaya mariya ta gyara tsayuwa kafin tace"To ai ba saboda kai ko dangin ka nake zuwa wajen Fa'iza ba..Ku ai baku isa ba wlh Fa'iza yar'uwata ce baka isa ka raba jinin dake Tsakanina da ita ba gida kuma bazan fita ba sai dai kayi abunda zakayi"
Tafad'a cikin Jaddada mganarta cikin mamakinta yace"Haka kika fad'a..?
Ta daga kai kafin tace"Kwarai haka nace in kuma kana da yadda zakayi dani Bismillah.."
Kawai sai ta koma ta zauna kafa d'aya kan d'aya tana latsa wayarta cikin Fushi ya juyo yana kallona cikin Tsawa yace"Wlh ki Fad'ama yar'uwanki ta fice ta barmin gida tun kafin raina ya baci na hadata da jami'an tsaro.."
Na zaro ido cikin rawan murya ina fadin"Yan sanda.."!
Ko kulani bai yi ba ya shige bangaransa da Sauri ni kuma sai kawai na fashe da kuka da Sauri na karisa gaban Yaya mariya zan yi mgana kenan ta Dakatar dani da Sauri kafin tace"Kada ki ce Tak in na isa dake fa'iza in sha Allahu yau zan kawo karshen duk zalunci da yake miki acikin gidan nan"
Cikin kuka nace"Yaya mariya yan Sanda fa yace zai kira miki"
Tayi wani mirmishi kafin tace"in shi takamar shi iskanci na shanyesa na Dokesa ya Dade bai kira yan Sanda ba in yaso ya Dauko gabad'aya police din kasar nan gabadaya yau ko ni ko shi acikin gidan nan"
Tafad'a tana mai kara tabbatar min da mganarta nasan Halinta tana da kafiya da Taurin kai ban kara mgana ba ammh na tsorata sanin Halin Ya Ishaq na kasa zaune na kasa tsaye,Kawai sai gashi ya fito yana waya kalmar da naji ita ta Razani Cikin Fushi yake fadin"Yallabai gida na zasu zo akwai wata matsala ne..Ok sai sun kariso.."
Nasan zai aikata ba ni da Daraja a idanuwansa,ballatana Dangina su yi Daraja a wajensa zai iya aikata duk abunda yaga dama bai damu ba,kuma nasan bazai taba Saurarata ba sai kawai na zube gaban Yaya mariya na Hada Hannayena duka Biyu cikin kuka na fara fadin"Don Allah..Don Allah..Yaya mariya ki tafi bana so ya Tozartaki bana so aci mutuncin ki"
Yaya mariya ta dakamin Tsawa cikin fada tana fadin"Bazan fita ba ina nan inajiran duk abunda zai yi"
Shi kuma yace"Zaki gani sai kin raina kanki yau d'in nan"
Bana so wani abu ya faru shiyasa nake rokonta tatafi cikin wata murya tace min"Ni kike roko na bar miki gidan ki fa'iza saboda wannan azzalumin mijin naki..?
Lokacin da ta fadi haka baya falon ya koma bangaransa ganin bazata Fahimci ba yasa na tashi zan koma Shashen nasa sai gashi mun ci karo da juna,cikin sauri na rikesa ina Fadin"Don Allah kayi hakuri..Kada ka kira mata yan sanda"
Ba laifinta ba ne Goggo ne da suka zo Dubani jiya tace ta zauna na kara jin Sauki shine..Shine ma.."
Sai na kasa karisawa Cikin Tsawa yace"Shine me..?
Cikin In ina nace"Ta tafi da Ahmad tunda..Tunda na ya ye..s.."
Tas..! Kake jin karan marin da ya yarfamin sai d na yi gefe dafe da kuncina cikin Bacin rai ya nuna ni da Hannu yana fadin"Wacece ke da zaki yanke hukunci kan ya'yana ba tare da kin Sanar dani ba..?uban wa yace ki kai min yaro na wani waje? Ban miki kashedi kan hakan ba..?.
Nace ban miki kashedi kan haka ba Fa'iza..?shine kika aikata gaban kanki saboda kin raina ni ko..?
Yana mgana yana nunani da yatsa cikin bacin rai sai kawai na koma na durkushe ina kuka yaya mariya ta mike cikin Takaici da bakin ciki kafin tace"Ba dai Ubanmu kake zagi ba ko..?
Sannan daman ai dabba shi ke dukan matarsa wannan abun da kayi ya tabbatar min da cewa kai Dabba ne acikin mutane"
Ya Ishaq ransa ya baci ya taso mata itama ta taso da Sauri na shiga Tsakaninsu na rike Yaya mariya ina wani irin kuka kamar zan shide cikin Shakewar murya nace"Ki tafi..Ki tafi don Allah yaya mariya ki tafi.."
Yaya mariya ta kalleni kafin tace"Zan tafi..ammh ba ni kadai ba tare da ke Fa'iza yau zaki bar ma wannan azzalumin gidansa in kina da amfani in kuma baki da shi zai sani"
Sai na Rud'e na kasa mgana ta ja Hannuna keey kamar rakumi da alaqa zuwa Dakina ta fara Hadamin kayana tana yi tana fadin"Kin gama zaman aure in da ba'a san Darajan ki ba..da ikon Allah hakkin ki bazai barsa ba sai Allah ya saka miki"
Ni dai na kasa mgana sai uban kuka nake yi,Ta gama had'a min kaya cikin karamar akwatin Amir itama ta Hada nata kayan ta zura hijabi,Nima tace na Dauko Hijabi na saka ganin na kasa tashi yasa ta dauko min ta sakamin tajani,har zuwa Falo yana Tsaye hannayensa goye a bayansa yana Safa da marwa acikin Falon.
Yana ganin mu ya saki mirmishi kafin yace"Better..Ni bazan hanaki tafiya da yar'uwanki ba ni dai ban ce ta tafi ba in kuma tabiki wannan ra'ayinta ne sai dai ta sani in dai ta saka ta bar gidan nan to ta Rubuta ta barsa har abada"
Yaya mariya tace"To sai me..?ai daman ta bar sa har abada kenan wannan bakin gidan da bakomai cikinsa sai zalunci da mugunta da ikon Allah sai Hakkin Fa'iza ya Bibiyeka"
Ya ishaq yace"Sai dai hakkin kashe aure ya Bibiye ki dai..Sakarya wacce bata san inda ke mata ciwo ba..Na dai gama mganata ni dai in dai ta Fita to a bakin auranta sannan har Abada bazata Dawo ba"
Yaya mariya ta fincikeni tana fadin"Zaka gani yau kam zaman Fa'iza da kadaddaran auran ku ya kare"
Bai damu ba ya koma ya zauna ya Dora kafa d'aya kan d'aya ko ajikinsa,Yaya mariya ta rika jana har kofar Falo cikin Dashewar murya nace"Ban saka takalmi ba yaya mariya"
Cikin Fada tace"in mun je tasha na siya miki"
Na kara turjewa ina fadin"Yara na..Yaya mariya su Amir fa..?in na tafi wazai kula da su..?
Ta juyo tana min wani kallo kafin tace"Ko mutuwa zasu yi sai dai su mutu nan d'in ne gidan Ubansu ke kuma ai ba gidan naki uban ba ne wuce muje.."
Ta kara jana naki yarda na Bita na Turje ta juyo ta kara kallona afusace kafim tace"Fa'iza kada ki bari na saka miki Hannu"
Na kasa mgana sai kuka ya'yana nake Tunani in na tafi basu da wani Sauran gata bani da mafita sai zabin Dawowa na cigaba da zama acikin yanayin da nake saboda ya'yana.
Yaya mariya mamaki ya kara kamata lokacin da na kwace hannuna daga gareta na juya baya ina kuka nace"Ki yi hakuri..Kiyi hakuri..Ki tafi don Allah..BAzan iya tafiya na bar ya'ya na ba"
Kiyi hakuri"
Sai kawai na kwashi gudu zuwa Cikin D'akina ina kuka kamar raina zai fita kaina har wani bugawa yake yi Dif dif,Yaya mariya ta kasa motsi saboda abunda nayi Ya Ishaq kuma na zaune yana Dariya kasa kasa kafin ya mike yana kallon Yaya mariya cikin gadara yace"Fita ki bar min gida bakar munafuka..Kin dai ji kunya wlh kin kuma yi asara..Yar'uwan naki da kike Hakilo a kanta ta nuna miki baki da wata Daraja sama dani..Sai ki fice min Daga gida kada na kara ganin siraran kafafunki acikin gidana.."
Yafad'a yana nuna mata hannun alamun ta fice ta bar mai gida Takaici da bakinciki yasa Yaya mariya Zubar kwallah ta kalle shi ta kara kallonsa kafin tace"Naji kayi nasara a kaina zan tafi..kamar yadda ka bukata bazan kara zuwa gidan ka ba..Sannan mganar Fa'iza karyan ka ta sha karya ai jini yafi ruwa kauri sannan wata kusan tafi wata..Zan cigaba da zumumci da yar'uwata domin ba kai ka Had'amu ba..Mgana ta karshe shine akwai Allah kuma yana nan a madakata Duk abunda kake aikata ma Fa'iza na sharri da zalunci kai da Mahaifiyarka da yayarka,Da ikon Allah sai kunga sakkaya tun a duniya sai Allah ya jarabceka da iftila'in da sai ka rasa ina zaka saka kanka in sha Allahu sai Allah ya saukar da aya akan maza ire iren ka da basu darajan matan su sannan basa adalci  ya yin zamantakewar su,Kuma kada ka manta akwai Hakkin zumunci shima sai Allah ya tambaye ka, sannan hakkin Fa'iza bazai  barka kayi rayuwar da kake Buri ba Ishaq Kabir karofi."
Tana gama fad'in haka ta Sauke karamin akwatin na data Dauka,ta juya ta fice tana zubar da hawayen bakinciki da takaici duk da kalamanta sun Dakesa ammh bai damu ba ya Bita har get yana gayamata bakaken mganganu sannan ya Dawo Cikin gida ya Iskoni har dak'i yana gayamin duk mganar da ta fito bakinsa har yana fadim Tunda ya aureni bai Huta ba yake cikin Matsala ni ba matar kirki bace ni matar Tsiya ce.
Nayi kuka,kukan da ban taba yi ba,kukan yadda ya tozarta yar'uwata ni ban damu da kaina ba Daman ni bani da wata Daraja ammh Yaya mariya fa..?yar'uwata ce bata chanchanci cin zarafi da tozarci ba.
In da nagode ma Allah Yaran basu dawo daga makaranta ba,da suna gidan nan ban san wani amsa zan basu ba ina kwance ina kuka suka Shigo,Ganin su yasa nayi saurin share hawayena kaina ciwo yake yi duk yadda yaran suka so su fahimci wani abu ban basu dama ba da Amir ya dameni da Umma baki da lafiya ne..?naga fuskarki ta kumbura ne"
Sai nace masa wani abu ne ya fadamin a ido,Nasan inda Ya Ishaq ya mareni ne ya tasa sannan ga kuma kukan da na sha.
Tuni Ya Ishaq ya fice daga gidan na rarrafa na shiga kitchen na Dafa ma su Amir Jallop din taliya,kunyar kaina nake ji da abunda ya faru ace mijina shi ya tozarta yar'uwata da muka fito ciki d'aya uwa daya uba daya,Abun sai ya tsayamin a cikin raina ya kasa wucewa su kansu yaran su san yanayina ya sauya,suna mgana sai dai na bisu da ido kawai da wuri nayi musu shirin kwanciya Saboda ban jin Dadin jikina,Kamar kazar da kwai ya fashe ma aciki haka jikina ya koma,Kayana da Yaya mariya ta hada ni na kwaso su na maida su muhallinsu araina ina Tunanin Lokaci bai yi ba.lokacin da zan bar Rayuwar Ishaq bai yi ba akwai sauran Lokaci.

Ina D'akina zaune ina kuka ni kadai ina sharan hawaye na Ya Ishaq ya shigo Fuskarsa ba Fara'a,Ina ganinsa na Dago kawai ina kallonsa ina jiran naji dame kazo Saboda nasan wani Sabon Tozarci ne ilai cewa yayi gobe geben nan nasan yadda zan yi na karbo masa D'ansa kafin raina ya baci.
Jikina na rawa cikin rawan murya nace"Goggo ce ta karb'esa fa..?Sai naje nace ta dawo dashi..?
Cikin Tsawa yace"Ina ruwana da wata Goggo..Mama ce..?nace Mama ce..?
In ba munafunci kika so ba, meyasa baki aika ma Mama shi ta yayesa ba..?
To wa ma yace ki yayesa batare da kin Fad'amin ba..?
Kaina na kasa nace"Saboda bani da lafiya ne ina asibiti da kuma na Dawo sai yak'i karb'an Nono sai na yayesa kuma Goggo Saboda Tausayina yasa ta tafi dashi fa"
Karamim Tsaki yaja yana fadin"Kedai kika sani na riga na gaama mgana wlh in gobe da yammah tayi Ahmad bai Dawo gida ba sai na Wulakantaki Fa'iza"
Haka ya fice ya barni ina kuka,ina jin wani daci na tasomin a kasan raina ciwo nayi ba sannu ba Tausasawa ba Lallabawa sai tozarci da cin mutumci ya Allah ga baiwar ka Fa'iza ka bata mafita  D'aya daga cikin mafitan da ka ke bama Bayinka salihai.
Adaran nan barci sai dai barawo ya iya Sace ni da Safe kuma da zazzabi da ciwon kai na tashi su Amir na da Hadda Dakyar na iya musu shiri da abun karyawan su,To basu samu ma tafiya makarantar ba Haruna adaidatan sa ya samu matsala Babansu kuma ko motsinsa ban ji ba,Ballatana na saka ran zai kai su,Sai kawai nace su tube kaya su bari sai gobe sai fadi suke Daada bazai kai mu ba nayi musu shuru kawai ina ji Anum ta je tana ta Buga kofar Shashensa tana kiran sunansa Ammh har tagaji bai fito ba.
Sai daga baya da Amir yaja su suka fara wasa ita da Musty sai ta manta ammh da farko har ta fara kukan ta na rigima..
Ni ko kwata kwata hankalina baya jikina Tunani nake yadda Ahmad zai Dawo kafin yammah tayi nasan duk abunda yace zai aikata ammh na gwammace ni na tozarta da na iya cema Goggo ta Dawomin da Ahmad bazan iya ba Har abada bazan iya ba.
Ranar ko girkin rana ban yi ba gari na jika musu suka sha,Nima ba na wani jin Dadi sai da na sha Panadol cikin mganguna na hawan jini kuma yana da karfi sai Dare nake shan sa.
Bani da masaniyar Ya Ishaq na gidan ko baya gidan,Bayan la'asar ina Dakina na idar da sallah su Amir suna Haraban gida suna wasa dakyar na saka su suka dawo cikin gida suka yi sallah wasa na ransu suka koma suka cigaba da yi.
Tashin mgana na rika ji afalo lokaci d'aya da kiran sunana zubur na mike jin kiran sunana kuma Muryan Mama nake ji tana tsagamin kira da karfi kamar zata tsaga gidan.
Na fito da Sauri muka kusa cin karo da Anty Binta ina shirin gaisheta ta bangaje ni ta shige Mama na Tsaye tana Karkad'a jiki kamar wata mazari Cikin Daga murya tace"Shiga ki fito mata da kayanta jiya bata bi Yar'uwanta ba yau kuma zata bita Daga baya fito mata da kayanta yau in dai ba gidan Sidi da tamadina bane sai Fa"iza ta barmin gidan D'ana"
Hankalina ya tashi jikina ya fara rawa na karisa gaban Mama na zube ina gaisheta bata amsa ni ba ta fito da wayarta ta kira,naji dai tana fadin gasu sun kariso daganan ta kashe wayarta ta koma ta zauna tana kad'a kafa Anty Binta kuma ta rika kwasomin kayana ta na min watsi da su a tsakiyar falo na zama mutum mutum na kasa mgana har Ya Ishaq ya fito Daga bangaransa yana sanye da Jallabiya ko barayina bai kallah ba ya isa ga Mama suka gaisa.
Cikin ko in kula ya zauna gefenta yana fadin"Mama meke faruwa ne..?
Yafad'a yana bin kayan da Anty take watso kayana da kallo Cikin Daga murya Mama tace"Zaman fa'iza a gidan ya kare Daga yau..!
Cikin mamaki yace"Saboda me ne Mama..?
Mama ta mike tana nuna ni da yatsa tana fad'in"Har saboda wannan gayyar Tsiyar gayyar matsiyantan ne za'a zo har gida aci maka mutunci muma aci mana wace ce ita..?taimakon ta fa kayi ita har ta isa..?
Wlh sai ta bar min gidan D'a na damam Darajan mahaifin ku take ci dama ta kai iwar haka ammh Tunda daga ita har yan'uwanta matsiyata ne yau sai na muna musu nafi karfin su..Sakinta zakayi ta kara gaba nagaji da Fitina nagaji Tunda ka auri wannan yarinyar tsiya da Jafa'i basu bar Bibiyan rayuwarmu ba,meye amfanin Mata irin Fa'iza..?
Dangin Talauci Dangin kurame dangin tsiya da tsiyataku..?
Nace meye amfanin mace irin ta..?.
Ai tunda basu san an yi musu alfarma yau zasu sani"
Ta karishe fada tana kumfar baki Shuru yayi bai yi mgana ba, ni kuma kaina na kasa ina kuka,Mama ta cigaba da zagina ni da iyayena da yan'uwana tana aibatana Iyayena barin ma mahaifina da yake kwance a cikin kabarinsa naga bazan iya Jurewa ba na Dago kaina cikin kuka nace"Mama ni ki zageni ni ce nayi miki Laifi ammh me mahaifina yayi miki da kike aibatasa yana kwance acikin kabari..?
Sai mama ta saka salati ta Dire tana Fadin"Ishaq kana jinta ko..?
Sai nace ka sakete zaka saki wannan tsinanniyar bakar yarinyar nan kenan..?
Ya Ishaq ya kalleni alokacin nima ina kallonsa ne, ba kuma Saboda ya barni ba ne ina kallonsa ne domin nasan zai iya yanke duk hukunci da Mama tace ai bata san abunda ya faru ba jiya shi yaje ya fad'amata..
Cikin Karsashin muryan sa yace"Mama ni ba domin Sarkan da Mganar Baba ta sakani aciki ba da Tuni na Rabu da Fa'iza domin na Dad'e da sanin ita ba matar kwarai bace Matar Tsiya ce..Sai dai kalaman Baba su suke zaune da ita acikin gidan nan sannan su suka cece igiyan aure na dake tsakani da ita"
Mama tace"Kalamansa baza su yi wani Tasiri ba ai baya raye yanzu"
Kai ya girgiza mata kafin yace"A"a Mama ki yi mata kowani Hukunci ban da na saki..Ina tsoron kada bakin Baba ya kamani in na Saki Fa'iza"
Hawaye suka gocemin zuciyata naji tana wani irin Zafi shi ya D'aga murya yana fadin"Anty Binta bar watso kayan nan haka kiyi hakuri.."
Anty Binta ta fito tana faman Hararata a kaina ta Tsaya ta saka Hannu ta Dago habana ta kwasheni da mari mai kyau Mama tayi kyafci tana fadin"Kara mata tunda bata da mutumci"
Ta d'aga hannu da niyyar kara marina suka ji kukan su Anum acikin Falo sai ta Dakata,ta d'ago tana kallon su suna bakin kofa atsaye Amir na kuka ammh na hawaye,yana rumgume da Anum da Musty dake kuka share share ganinsu cikin wannan Halin sai naji Rauni ya kamani kawai sai na Bude murya na fashe da kuka
Mama da Anty Binta suka saki baki suna kallona Ya Ishaq kuma sai ya mike ya nufe su yana fadin"My Anum"
Ya saka hannu ya riko Anum dake jikin Amir ta ture hannunsa ta nufeni da gudu cikin kuka tana fadin"Umma..Umma"
Sauran ma sai suka mara mata baya na mike zaune na Bude hannayena na Tari ya'yana da silar su ne nake zaune cikin wannan kaskastaciyar rayuwar.
Rumgumesu nayi kam ina kuka da dukkan zuciyata Anum kuma Musty ma haka Amir ne ke faman gogemin Hawaye na shima kukan yake yi sai na Dago kaina nima na saka Hannuuwana ina share musu hawaye Bud'e bakin Amir sai cewa yayi"Umma ki daina kuka in na girma zan rama miki Dukan ki"
Sai wani kukan ya kwacemin na Rumgume sa ina fadin"Ka da ka zama mai Riko Amir..Ka zama mai yafiya saboda Allah ma gafurun Rahimun ne..Ba wanda ya Dakeni kuka kawai nake yi"
Zai yi mgana na girgizamai kawai ina Hawaye Ya ishaq sai jikinsa yayi sanyi Mama kuwa komawa tayi ta zauna tana Fadin"Yau naga makirci"
Anty Binta sai ta kasa mgana na mike na isa ga kayana na ina Tattarawa Amir da Anum suka tayani muka kwashe na Dauki Musty na Sabashi a baya na rike ma su Amir Hannu ban kara kallon barayin su Mama ba na koma D'akina ammh kuka na bai Tsaya ba.
Anum sai fadi take yi "Umma Daada ne ya Dake ki..?
Da Sauri nace"Ba wanda ya Dakeni Anum..ban da lafiya ne"
Amir da yayi shuru yace"Umma Anty Binta naga ta na dukan ki"
Da Sauri nace"A'a bata Dakeni ba..Hakuri take bani sanda kuka shigo"
Daga gani basu yarda ba Domin suna kallona suna kuma kallon junan su,Amir shi ya tayani na maida kayana cikin Wadrope Ranar tare na kwana da ya'yana acikin D'aki Daga ni har su bamu kara lekawa falo ba bansan Lokacin da su Mama suka tafi ba sannan abinci ma ban yi ba,nace zasu sha gari sukace basajin yunwa nima cikina duk ya toshe bana jin cin komai bakina kamar madaciya.
Washegari kuma Ban sani ba Ya Ishaq ya koma Abuja sai da naga an yini an kwana ban gansa ba nasan ya tafi kenan hadda kuma kwana Biyu su Amir basu samu zuwa ba sai Ranar Lititi suka tafi makaranta Lokacin an gyara adaidaitan Haruna.
Duk da bani da Tabbacin Yaya mariya ta fadama goggo abunda ya faru ammh duk sanda na Tuna abun sai naji ba Dadi,Satin Ahmad hudu A karofi Hafsatu ta Dawo min dashi nasha jinin jikina kila Yaya mariya ta sanar da su komai nayi nayi ta tsaya ta kwana tace Goggo tace kada ta zauna an had'ama Ahmad sha tara na arziki su goldemorn da su Madaran yara,kayan Tea har da Ferfesun kaza sai garin kuni da garin danwake Hafsatu sallah kawai tayi ta juya,ko awa daya batayi ba Daganan sai jikina ya karayin sanyi Ahmad yayi kiba sosai Tafiyarsa har ta fara nuna yana Gudunsa ko'ina sai naji Dadin haka acikin raina duk da bana jin kewarsa Domin na maido Anum wajena take kwana ammh shakuwar dake tsakanin Uwa da abunda ta Haifa Allah kad'ai yasanta.
Ko wata Biyu ba'a rufe da Faruwar lamarin da ya faru ba Zainab ta Haihu Namiji nima ba wanda ya Fad'amin Halisan Anty Mamah suka zo anguwanmu ita da Badariya Daga makaranta suka biyo,Shine naji suna Hirar kuma Badariyan ta tambayeni ko naji nace ban sani ba.
Nan take shaidamin shekaranjiya akayi Haihuwan Zainab ta samu Namiji C.S akayi mata Su mama kamar yanzu aka fara samin jika ta nan tana shirin gagarumin Taro sannan Anty Binta kuma tana ta shirya Mutanen da za'a tafi da su Abuja suna.
Ni dai ban ce komai ba,ammh a raina na ma Zainab fatan samun Lafiya da kuma raya abunda ta Haifa bana mata bakinciki Domin ni ban Dauketa a kishiya ba sai miji na sonka ne zai kara aure ka damu kanka, in ka san baka da wani Daraja babu abunda zai Dameka.

*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.

*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866

Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta

Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake

Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba

Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳

Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take

Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi

Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce

Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866

IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀

      
           *🅿️13*

Babu wanda ya damu dani ballatana su fad'amin haihuwar zainab d'in, ba domin naji a bakin badariya ba kila har sai in mun hadu na ganta da yaro a hannunta,Ya ishaq tunda ya koma ban kara jinsa ba,Su mama kuma da ni da babu a wajen su duk d'aya ne,
Baza su damu da naji komai,ta bangaran su ba Shi kan shi Uban gayyar ai bai Damu ba,Domin na tabbatar ma kaina da ni da banza duk d'aya muke a wajensa in ya saka kafa ya koma Abuja ina da yakinin baya tunawa dani ballatana ya neme ni ko a waya na Zargin hakan ne,saboda bai taba tambaya ta daidai da rana d'aya da cewa Fa'iza ina wayar ki ba..?
Ko na ji ina kiran wayarki a kashe me ya faru..?Bai taba min makamanciyar wannan tambayar ba sai na sakama raina bai taba kirana yaji bai sameni ba,Ballatana yasan wayata ta lalace.
Na riga na saka ma raina mata ire ire na ba su da wani muhimmanci,na amince ba ni da kyau sannan ba ni da wani gata ballatana nasaba,Ammh ni musulma ce sannan Allah ne ya Halliceni,a yadda yaso ya ganni,ban taba jin kunyar yadda Allah ya Hallice ba Saboda nasan bai fi son masu gatan a kaina ba nasan duka Bayi muke a wajensa kuma mun zo duniya ne domin bautar ubangiji.
Na kuna riga na sakama raina ba sai na samu soyayyar miji ba,sannan ba kima sai na zama wata aba mai Daraja ba ni dai ya kasan ce watarana  zan zama bango ga ya'yana shikenan Burina ya cika bani da wata Damuwa Ban matsa ma kaina sai su Mama sun so ni Dole ba domin akwai mutanen da ko Naman jikinka ka ke yankawa ka na basu suna Dafawa baza su taba sonka ba sai na sakama raina haka,Sannan nasan ba ni da abunda zasu kaunace ballatana na saka watarana komai zai zama Tarihi.
Ban san ma ba'ayi suna ba ashe an kara Sati d'aya kafin taron suna ana gobe sunan Badariya ta zo take fadamin Sakom Mama akan na shirya su Amir da kayansu na kwana Biyu zata tafi da su,Baban su yace a taho da su ban yi musu ba na tashi na Shirya musu kayan su masu kyau Amir da Musty da Anum Ahmad kuma ya cika Rigima daman su ukun Mama tace za'a tafi dasu sai da ta jira suka Dawo daga makaranta jin zasu Abuja wajen Daada Anum da Musty suka fara Tsalle Amir ne ya kalleni yana kwabe Fuska Lokaci daya yana fadin"Umma ni bana son zuwa a bar ni a gida"
Sai na kallesa Badariya Hankalinta yayi gaba kan wayarta sai bata ji sa ba na jawosa jikina ina Fadin"Haba Baban katsina wajen Daadan ku zaku je da Anty ku fa..?ba kwa so kaga Sabon kanin ku da Anty ta Haifa muku..?
Sai ya gyad'a min kai alamun yana so kumatunsa na shafa ina Fadin"To kada ka kara cewa bakason zuwa..Kai ma zaka je ka ga Sabon kanin ku ko Amir di na..?
Sai yayi dariyan su na yara kafin yace"Umma ke bazaki je ba..?
Kai na girgiza kafin nace"Zan zo ammh Daga baya kaji ko..?
Sai ya jinjina min kai,mganar da nayi mai yasa ya shiga cikin kannensa suna Murna sai da suka yi sallar mangariba suka ci Faten Ramar da nayi ina da Tsakin tun wanda Goggo ta kawomin ne yayi saura Gidan Sa'adatu na shiga na samu Rama dayake suna da Fili tayi shukeshuke har da su Zogale yanzu na fahimci mutane sune Rahma ina shiga makota na bayan kwana Biyu mu gaisa nima Sa'adatu da Habiba sukan lekoni Lokaci bayan Lokaci sai hakan yake min Dad'i ko da ba na ganin wani nawa a kusa dani Su din da nake gani sai suka Debemin kaso mai yawa na kewar da nayi shekaru yana Damuna.
Sai da su Amir suka tafi naji gidan yayi min shuru Kuka sosai Ahmad ya yi da yaga yan'uwan zasu tafi sai da na Shige da shi daki sannan suka samu Tafiya,Dakyar na samu yayi barci ballatana daman Ahmad akwai rigima irin goyon da nayi Anum ne itama akwai Rigima kuma har yanzu bata Daina ba tana tabawa wani Lokacin don ma ina had'a mata da Nasiha sai take rage rigiman wani Lokacin.
Sunan zai kama ranar jumma'a da Safe misalin karfe goma na Safe na gama wankin kayan yara kenan ina Daki ina shirya Ahmad da nayi mai wanka,kwata kwata ban ji sallama ba Saboda lalurata sai da naji Mganar ta kamar daga kofar Dakin da nake ciki,Ina juyowa muka hada ido Hudu da Yaya asiya Sabe da Jaririnta da karamar jakar matafiya a Hannunta.
Na saki baki fararan hakora na suka bayyana cikin yanayina da murnar da ta cikani nace"Yaya Asiya.."
Dariya tayi Lokaci daya tana karisa shigowa Dakin tana fadin"Na'am Yar Fa'i"Daman ta kan kirani da hakan in tana so ta zolaye ni..
Sai nayi Dariya,na bar Ahmad kan gado bayan na gama sakamai kaya na karbi jakar hannunta na sauke a gefe sannan na karbi Muhammad Auwal dake hannunta ita kuma ta Dauki Ahmad ta daga shi sama tana fadin"Kai Ahmadu naga ka kara girma ne daga ganinka Yaya Ishaq ka Dauko Tsawon kafa zaka yi"
Dukkanmu gefen gadon muka zauna na kamkame Muhammad Auwal da ya zama Lukuti da shi Dagani yana samun kulawa da kuma Nono mai kyau.
Cikin nuna farincikina na shiga gaisheta ta amsa itama cikin Fara'a kafin tace"Nace ni dai bari nazo na gani ko Fa'ina na lafiya ko bata san na Haihu ba ne? shuru baki ba wayarki sannan ina ta kiran ki a kashe kwata kwata bana samun ki kin gani Karofi zani nace bari na fara sauka naga Lafiyarki"
Tana fad'a tana karemin kallo Lokaci daya da nazarina sai na sunkuyar da kaina ina wasa da showel din dake jikin Muhammad Auwal,Naji kunya sosai shi yasa na kasa mgana na kuma san ko zan mutu Ya Ishaq bazai barni naje kano ba ko da ma nasan Haihuwarta ballatana ban sani ba sai zuwan da su Goggo suka yi,bayan sun baro kano alokacin.
Ganin na ki mgana yasa ta kyaleni ta Fahimci abun sai bata matsa min ba,Cikin Nazarin Dakin tace"Naji gidan shuru su Amir suna makaranta kenan..?
Kai tsaye nace mata"Suna chan wajen Babansu jiya mama ta aiko Badariya ta tafi da su baban su yace a taho da su"
Yaya Asiya tace"An yi haka jiya naje gida na iske su Hajiya nata shiri ni ban ma sani ba sai ajiyan ake cemin Amaryan Yaya Ishaq ne ta haihu aiki akayi mata gobe taron suna..har ma ake fadin Ishaq din ya yi ma mahaifin ita zainab din kara sunan babanta ya saka Lawal ammh zasu rika kiransa Farhan"
Kai tsaye nace"Allah ya raya sa"
Ta amsa da Ameen tana fadin"Ke ba'a je da ke ba kenan..?
Sai da na dago na kalleta sannan nace"eh bai ce a zo da ni ba"
Ta gyada kai tana fadin"Bakomai bayan an kwana biyu sai kije ki yi mata barka in kuma tazo shikenan"
Ban amsa mata ba na daga Auwal a Hannuna ina Fadin"Kai Yaya Asiya naga ya girma ne kun yi wata uku ne..?
Dariya tayi kafin tace"Watan sa biyu ne fa da kwanaki yana da girman jiki ne irin Goyon Husain ne zan yi"
Na mike ina Sab'asa a baya na kafin nace"Eh ai suna ma kama da Husain din"
Tace"haka kowa ke cewa"
Tsab na goyesa a bayana na Saka zani ya lafe Ahmad kuma daman da yaji Ruwan zafi sai barci kan gado Yaya Asiya ta kwantar da shi muka fito Falo muna Hira ni dai ina ta Fargaba kada ta sako mganar abunda ya faru Tsakanin Ya Ishaq da Yaya mariya sai naji batamin ba.
Ita tayi mana girki Shinkafa da wake da mai da yaji,Ita tazo min da yaji da kori a robobin su tunda Sana'arta kenan na Dauka ina shinshina kamshin Korin cikin jin dad'i nace"Yaya Asiya korin nan nada kamshi nima ina so na iya had'awa ko shi na fara saidawa in za'a siya"
Yaya Asiya tace"Indai za'a siya koyan sa ba shi da walaha Fa'iza..Sai na koya miki ke da ma na sanki da Sauri Dauke abu cikin Lokaci zaki gane komai sai ki rika zuwa kasuwa kina Siyo kayan  had'in kina hadawa da kanki kuma wlh akwai samu in dai kika Samu masu siya sosai"
Tun da naji ta ambaci kasuwa jikina yayi sanyi sanin ko sama da kasa zata Hade Ya ishaq bazai bar ni na rika fita kasuwa ba sai na share zencen ban kara mata mganar ba.
Sai bayan mun yi sallar azahar mun zauna muna cin abinci ta dago tana kallona kafin tace"in na kwana anan Gobe da Safe zan yi sammako na biya ta Dutsemah na gaida Tamadina na kwanan mata Daya daganan na karisa Karofi na sauke gajiya achan sati yace nayi kafin na koma"
Kai na jinjina kafin nace"Tamadina ta na lafiya..?
Kai tsaye tace min"Lafiya ke shuru Fa'iza muna saka ran haka kwanki da ina jego mun yi waya da Megidanta da Abokiyar zamanta sun tabbatar min tana lafiya,ban ce a bata ba ne kinsan ko tayi mgana awaya bazan gane komai shiyasa na bari sai nazo naje na ganta"
Na kasa mgana kunya nake ji ni da nake kusa ammh mahaifiyata na Raye sai ta shekara bata ganni ba Idanuwana suka ciko da kwallah Yaya Asiya ta gani ta kalleni sannan ta Girgizamin kai kafin tace"Kada ki dami Fa'iza nasan yanayin da kike ciki..Ki zauna ki yi ma aure Biyayya In sha Allahu zaki Rabauta ranar gobe kiyama a wajen Ubangiji..Sai dai duk Lokacin da kika samu dama ki rika zuwa kina Dubata bayan mu bata da kowa Fa'iza ita kadaice ta rage mana sauran gatan mu anan duniyan"
Jinjina mai kai nayi ban ce komai ba ina Tunanin to yaushe nake samun Daman. ?Ko karofi sai na jima ban je ba,in kuma naje sai mutuwa ko Biki suna ma ba na kowa ba sai wanda Mama ta amince min naje nake zuwa.
Zuwan Yaya Asiya ya D'ebemin kewa sosai,Sannan na Fahimci ko Rashin Lafiya na bata sani ba sannan ban ji  tamin mganar ba sai nima nayi mata shuru ban gayamata ba.
Da yammah na rakata makota na ta gaida su Sa'adatu da Habiba ina jin Dad'i Lokacin da na nuna ta nace yayata ce itace Babba ad'akin mu Sa'adatu ta kalleta tace"Ba kwa kama Maman Amir"
Dariya nayi ban yi mgana ba Yaya Asiya ce tace"Ai mu mun fi kama da Babanmu..Ita yanzu da ace kin taba ganin Mahaifiyarmu sai ki iya cewa yaya da kanwa ce saboda Tsabar kamar da suke da juna"
Haka ma Habiba tace itama kamar yadda ta fad'ama Sa'adatu haka ta fadamata,Da muka Dawo gida Yaya Asiya tace"Ko kefa Fa'i ki rika shiga Mutane don.Allah..Yafi ki yi ta zama agida ke kad'ai kamar mayya..Mutane Rahma ne sannan Makoci yafi dan'uwaka tunda sai wani abu ya sameka kafin wani naka yazo ya kawo maka Dauki makocinka yazo ya taimake ka"
Cike da gansuwa da mganarta nace"Hakane"
Domin ya faru akaran kaina kuma nagani,Tare muka kwana agado daya yaran mu na tsakiyar mu mun dad'e bamu yi barci ba Duk Mganar Yaya Asiya na Hakuri ne da kuma hakuri da yadda zamantakewar aure tazo min kafin mu kwanta sai da tace min"Fa'iza gaskiya ya kamata ki fara wata sana'ar ai zama haka bazai haifar miki da komai ba sai takaici Daman mun yi mgana da Mariya zamu tarfa miki jari tunda kina sha'awar Korin ko shi zaki jaraba ki gani ko za'a dace..?
Nayi shuru ban ce mata komai ba sai ta kyaleni sai da Safe bayan mun karya tayi shirin tafiya ta karamin mganar cikin yanayin mganata nace"Yaya Asiya bazai bar ni na rika zuwa kasuwa ba"
Tayi shuru kafin chan tace"Kuma da wannan don wannan..To shikenan  dai zamu tattauna muga wata sana'ar zaki fara wacce bazata kawo miki matsala da mijin ki ba"
Da haka muka rabu da ita har waje na rakata,ina ta mata godiya tazo min da caryfish da yawa,tace na rika miya da shi sannan da Bushasshan kifin da tazo da shi zata kaima Tamadina da su Goggo ta D'ibarmin na karba ina jin hawaye suna kawomin cikin Idanuwana kalli yadda yan'uwana suka zame min garkuwa ammh ahaka su Mama ke min kallo kaskastttaciya mara gata.
Na bata sakon gaisuwa wajen Tamadina tace min insha Allahu zata sanar da ita Sannan nace agaida su Goggo da kowa da kowa ammh na kasa cewa ta gaida min Yaya mariya ina Tsanaanin jin kunyarta sannan ina Tunanin ta Rufamin asiri bata bayyana ma kowa abunda ya faru ba.
Sai naji ta burgeni ta zama yar'uwa mai Rufa ma yar'uwata asiri.

****

Sai Ranar Litini da yammah Jamal ya Dawo min da su Amir,sun zo da kaya niki niki da jakunkuna mai Dauke da Hoton Zainab da Ya ishaq da kyakyawan D'an su kamar balarabe sannan kaladan ma ta Hoton yaron Dauke da sunan Lawal Ishaq kabir karofi(FARHAN)
yaci kayan alfarma kamar asace sa a gudu in ka gansa kamar d'an larabawa,Dole yayi kyau daga uwarsa har ubansa masu kyau ne masha Allah.
Sun taho da kayan fulawa da yawa da Soyayyan Naman kaza,Samosa,Meatpie,Sprilroll,Cake,Da sauran sai lemukan gwangwani jaka shake da kaya Sannan sun taho da Sabbin kaya yan kanti a bakin Amir naji yace Antyn su ta basu sabbin kaya.
Su Anum yan Abuja sai tsallen murna take tana ta bani Labarin abunda ya gudana achan Jamal na zaune kan kujera mai zaman mutum d'aya yana Latsa wayarsa shi haka yake bai cika Hayaniya ba cikin Daga murya ya Dago yana fadin"Anun shut up.."
Da Sauri tayi tsit har tana saka Hannunta a baki ta kama tasan Halinsa baya musu da wasa Musty ya kwace motar wasan da ke Hannun Anum,Domin har da tarkacen kayan wasa suka shigo da su.
Ta mika hannu itama ta kwace sai ya kwabe fuska zai saki kuka da Sauri ta dora Hannu saman bakinta tana fadin"Shiii up.."
Dagani Har Jamal sai da muka yi Dariya Amir kuma mai hankali kayan su da suka watsar a Tsakar Dakin yake tattara zuwa Dakinsu ina kaunar yaron har acikin raina Saboda akwai Boyayyen Dabi'un da ya Dauko nawa.
Jamal na je na kawo ma ruwa ya Dago yana fadin"matar yaya anya ruwan nan zai shiga kuwa..?
Ba waku ne..?
Nayi dariya daman nasan Halinsa kafin nace"Tuwon Masara nake yi miyar Kubewa D'anya zaka ci..?
Da Sauri ya mike yana fadin"Tuwo fa..Am ok."
Na wuce sai da Safe..My childreen Good Night'
Anum da Musty suka bisa da Bye bye uncle ni kuma ina yar Dariya nace ya gaida su mama yace zasu ji,nayi mamakin yadda nake yawan ganinsa a gida lokaci bayan Lokaci,sai washegari da ya shigo anguwan ya kara shigowa na tambayesa ashe yana garin.?sai yace min ya koma makaranta wlh yajin aiki aka shiga shiyasa ya Dawo shekaran jiya.

Nasha Labarai wajen yara musamman ma Anum Amir bai da surutu Musty kuma mganar ba wani kwari tayi ba rabi gwaranci ne,Anum sai fadamin take Umma jaririn Anty mai kyau ne muma yaushe zaki haifo mana Jariri mai kyau..?
Sai na kalleta nayi dariya naja kumatunta kafin nace"In sha Allahu zan haifo muku jariri mai kyau Anum"
Ta Dameni sai faman tambayana takr yaushe da nagaji nace mata watarana sai ta fara murna na kalleta ina jinjina yarinta yara dai basu da matsalan komai a duniya.
Nasan ko kayan da Anum suka Dawo dashi Darajan su Anum naci ba Domin haka ba nasan ko abunda ba'a so ba wanda zai kawomin
Naci kayan fulawan da suka zo da shi kazan dai su na saka ma fridge da safe ina saka musu cikin kwandon abimcinsu in zasu tafi makaranta da Lemuka daman kwanakin baya ruwa nake saka musu pure water da ya kare sai dai na d'ura musu na Famfo a Gorinan na su tunda bana da shi ban kuma da hanyar samu.
Ashe gayya ne guda akayi aka tafi Abuja Badariya taje ita da Halisa Anty Mahma da Anty Binta sai Hajiyar Dala da manyan ya'yanta guda Biyu,duk sai da Badariyan tazo ta ke fadamin.
Ranar da tazo gidana ta kwana Tunda basa zuwa makaranta suna yajin aiki kwananta ta uku mama ta matsa mata sai da ta koma gida ita kuma tana som zama saboda tana koyon girke girke a wajena Ammh Mama bata kaunar wani nata ya rabeni ballatana in tasan nata d'in yana so na ko Fad'an da take yi da Goggo saboda ni ne da ace Goggo bata kaunar mu kamar Yadda Hajiyar Dala ba ruwan ta damu da zaman Lafiya za su yi ammh Saboda ni ta yanke alaqa da Goggo sai wanda ya zama Dolen Dolen an had'a Dangi bata da yadda zatayi.
Ana haka ba Dad'ewa Yara suka yi Hutun makaranta suna gida sai na koma koyar da su na addnini a gida na Bokon kuma ban yi musu wasa ba nakan matsa musu su Dauko Littafansu Amir dake gaba dasu ya Rika Duba musu,nasan zafin rashin Ilimin boko tunda har da shi yasa na zama Bora agidan mijina tunda ko nasan zafin kaskasci bazan so wani daga cikin ya'yana ya Dan'dana abunda nayi shekaru ina Fuskarta ba.
Hutun yaran a gida ya taimakamin sosai na rage damuwa sannan walwalata ta Dawo har na fara maida jikina,sun gama cinye Hutun su suka koma makaranta a satin aka fara musu mganar kudin makaranta da Sabbin Littafai Anun kuma jakar makarantar ta mutu tana bukatar Chanji,sannan sabon Registration ne zata shiga primary 1 da suka fad'amin nace su bari in Uncle Jamal yazo su fad'amai Saboda ni bani da mafita.
Shi kuma kamar yasan ana jiransa sai ya Dauke kafa agidan ni dai fatana da addu'a ta kada su koresu daga makarantar karatun su ya tsaya,Ranar jumma'a sukace duk wanda bai biya ba kada ya zo ina jin haka sai na sakama kaina gwarin gwiwa na Fahimci an kawo gabar da ni ce uwar ya'yana kuma nice Ubansu Ranar Monday nace su shirya tare zamu je makarantar suna ta Murna,na yi wanka na saka kaya na mai kyau da Hijabi na shirya Ahmad na kulle gida nabi Haruna muka je makarantar ban taba zuwa ba Ya Ishaq ke zuwa ko Jamal in wani abu ya taso.
Yaran suka rakani har Office din mai makarantar Mace ce ina ta Fargaban ance da Turanci ake mgana ni kuma ban iya ba,Muna shiga Matar ta Dago fara kyakyawan gaske,na samu karfin gwiwa jin ta min mgana da Hausa ganina da su Amir yasa tace"Umman su ce ko..?
Na gyada mata kai ina mirmishi sai tace na zauna su kuma ta kada su aji suka tafi suna lekena.
Bayan mun gaisa cikin yanayin mganata nayi mata bayanin komai nace su yi hakuri babansu baya nan ne ammh in ya Dawo zai biya.
Sai tace bakomai tasan ba su da matsala da yaranmu nan tace zasu yi ma Anum Rigistration su bata Uniform din Primary section sai su had'a cikin Bill din kudin makaranta nace ba Damuwa muka rabu cikin mutumci a raina nace ashe ba ko'ina ne ake mgana da Turanci ba in ko Hakane nima zan iya shiga ko'ina da yarena na Hausa kuma nayi mgana a Fahimceni.
Haruna ya tafi bakin sana'arsa abun hawa na hau zuwa gida,Daman shi kudin da goggo ta bani da na wajen Yaya Isa na had'a na bashi na wata daya yanzu yana bin na wajen wata uku zuwa Hudu shuru Ya Ishaq bai basa kuma ko zuwansa na karshe bai tsaya ba ya tafi ma ban sani ba ballatana ma ya bani yace na basa ni fa na fara Tunanin tashi Tsaye kawai na nema ma kaina mafita na gama Fahimtar Sabon Iyalin da Ya Ishaq ya Had'a ya zabe su sama da ni da ya'yana ko da yake ai ni ya Dade da Zabar Zainab a kaina ya'yansa ne na Fara Gane ya fara mantawa da matsayin su a wajensu.
Sai a satin da naje makarantar ta su Jamal yazo gidan Anum sarkin karad'i ita ta fadamai an ce su biya kudin makaranta,To kwana biyu tsakani suka zo Da shedar an biya komai Anun an bata sabbin kayan makaranta da Text books,ranar kuma da Daddare shi Jamal din ya kawo musu littafan Rubutu da Sabbin Safuna da takalma ganin ba Jaka sai nake gayamai ta Anum ta lalace yace duka kudin da Ya Ishaq ya Turomai sun kare ammh zai yi ma mama mgana kamar nace ya bar shi ba sai yayi mata ba sai na kasa mai mgana.
Ni nasan za'a rina aiko da yaje yayi mata mgana fad'a ta kama yi tana fadin ina fakewa da ya'ya ina mai da D'anta bawa,ba domin Mama tasan ba'a sauya ma Tuwo suna ba da Tuni ta Hana Yaya Ishaq Dawainiyar ya'yansa to tasan dai ya'ya nasa ne sannan yana son su bazai iya kyalesu ba duk da Yaya Ishaq bashi da Kirki a wajena bazan yi mai karyan baya kula da Laluran ya'yansa ba wani Lokacin har da Muguntan Mama aciki gani take ina Fakewa da Guzuma ina Harbin karkasa.
Jakar da kuma taki bada kud'i a siyan ma Anum kenan Jamal yazo yana fadin da ya ke shi Santsi daya ne baya munafunci kaf abunda Mama ta fad'a ya fadamin sannan ya kara da cewa bai da kudi da ya siya ma Anum din Sabuwar jaka nace kada ya Damu ai na Gode da kokarinsa.
Dakyar na Lallashi Anum ta rika tafiya da Tsohuwar jakarta ni kaina naga duk ta mutu ta yayyage ammh ya na iya..?Tunda ba ni da wata mafitan sai dai ina jiran mafitan da na Roki Allah ya samar min kuma ina ji ajikina ya amsa duka addu'o'i na.

   Yau ta kama alhamis ne tun bayan tafiyar yara makaranta da suka maido wuta na fara guga sallar azahar kadai ya tadani sai rigiman Ahmad na shiga Kitchen na Damamai kuni na basa yasha sai ya fara harkan gabansa yana ta wasa da yar motan wasan yara na Mutsy da suka taho da shi Daga Abuja.
Hankalina ya tafi kan gugan da nake yi ban ji sallama ba,Kuma ko ma anyi in ba an matso kusa dani ba ne bana jin sallamr sai da naji an tabani na Juyo da Sauri har na Tsorata sai naga Tamadina da abokiyar zamanta Maman Isuhu suke kiranta.
Ai basan Lokacin da na watsar da gugan gabana ba na Daka Tsalle na Rumgume Tamadina ina murnar ganinta Cikin yanayin mganarta na Rikeni tana fadin"Faaa...Izzzaa..'
Sakin ta nayi na koma ina Dariya ina musu barka da zuwa,Ahmad ne motarsa ta makale jikin kujera sai ya fara kuka,Tamadina tayi Saurin zuwa ta Dauke sa,Ni kuma na kashe Soket din gugan da nake yi jikina na rawa Farinciki kamar ya sumar dani na nufi kitchen na Dauko musu ruwa na kawo musu ina gaishe su.
Sun sha ruwan Tamadina kuma wanda ta rage ta bama Ahmad kamar ya ganeta ya ko lafe a jikinta shi da ya ke da kiwuya.
Kafin ma na tambayesu daga Ina Mamar Isuhu ta ke shaidamin Matar yaron Uwargidan su ce ta haihu aiki akayi mata tana Asibitin katsina shine suka zo Dubata Tamadina tace su Biyo su yi sallah kafin su tafi.
Aiko naji Dadi,Dakina na kai su suka shiga bayi domin alwala ni kuma na fada Kitchen na fara kokarin sama musu abinci Jallop din Shinkafa na Dafa musu da bushasshan kifin da Yaya Asiya ta kawomin ina ta lallabawa Sauran sa kenan nayi takaicin rashin kudi ko Lemu ban da shi ballatana na siya musu kuma bani da kayan had'a Lemu ko daya ballatana na Had'a musu.
Har Daki na kai musu na iske sun Idar da Salla,Ahmad na kan jikim Tamadina yana ta wasan sa ta kalleni cikin mganarta tace"Suuuu...Saurrraaan...yarrran fa..?
Nace"Suna makaranta Tamadina sai yammah zasu dawo"
Ta gyada min kai Allah Sarki Uwa,uwa ce ko da akan bola take kwana,ita fa uwa ta gwammace tayi ma Abun da ta haifa ko da bazai rama mata wannan alherin ba.
Gyad'a Soyayyiya da Masara gashashiya ta kawo ma su Amir da gurjiya dafaffiya Maman Isuhu na Dariya tace abakin asibiti ta siya Masaran nan da gurjiya.
Ta turamin gabana tace na bama Yara sai hawaye suka kawomin cikin Idona na fara godiya Ahmad dai sai bare mai gurjiya take yi tana bashi yana Mamula da Hakoran sa guda Hudu Biyu a gaba biyu a kasa da suka fitomai.
Falo na koma har sai da suka gama cin abimcin,Sannan na koma naga suna shirin tafiya sai naji kamar kar su tafi ammh ba Dama Hijabi na Dauka muka fito ina Tunanin me nake da shi da zan basu..?
Na duba gabas da yammah ba ni da komai ballatana na basu haka muka tafi waje da su,ni nace su zo na kai su makota na da muke mutumci su gaisa.
Sa'adatu kadai muka samu Habiba bata nan taje gidan su daman yar katsina ce acikin gari.
Sa'adatu tana ganin Tamadina tace min"ga maman ku ko..?
Na gyada mata kai ta gaishe su cikin Ladabi daga jin yanayin mganar Tamadina basai ta nemi karin bayani ba tasan inda na gado Lalurata kenan.
Ita ta fitar dani kunya ta basu siga da yawa cikin wacce take saidawa bani da bakin da zan gode ma Sa'adatun tamin komai shiyasa mata mu daina kuskure domin mazajen mu sun hanamu huld'a da makotanmu sai mu Biye musu mu sani Annabi ma yayi Mgamar Hakkin makota sannan mutane Rahma ne duk yadda mutum yake shiga Jama'a yana da Bambamci da wanda ba ya shiga mutane sosai.
Har bakin Titi na rakasu suka samu Motar Dutsemah,Kunya naji da zasu tafi ban basu ko kudi ba Ahmad har da rigiman Tafiyar Tamadina nace Yaro yasan kakarsa.
Sai da suka wuce sannan na koma gida Ranar cikin Annushuwa na yini kamar an mun bushara da gidan Aljanmah sai dai ina ta kallon Tamadina ta kara ramewa nima tana ta kallona duk sanda na kalleta sai mun Had'a ido,Ina Kaunar Uwata a yadda take domin bani da makwafinta in kuma na rasata har Abada nayi maraici gaba da baya.
Haka kurum in na Tuna da kallon sai naji jikina yayi sanyi a raina nace kodai kallon karshe take yi mim..?
Tuna haka yasa sai da gabana ya amsa da Sauri nace a fili"A'a ba haka ba ne Insha Allahu ba yanzu zaki barmu ba Tamadina."
Da su Amir suka Dawo na basu tsaraban Tamadina suna ta murna sukace min waya siya musu ina Mirmishi nace"Kakar ku"
Sai Anum tace"Mama..?
Sai na kallesu nace'A'a mahaifiyata..Sunan ta Tamadina"
Anum tace"Umma bamu santa ba meyasa ba ma zuwa wajenta..?
Sai na kasa mgana nayi gefe da kaina araina ina auna yadda Ya Ishaq ya Rusamin rayuwata gabad'aya ace ya'yana ma basu san wacce ta Haifeni ba ?
sai kirjina ya karayin nauyi da Dubara na share hawayena na Lallab'e su da cewa zan kaisu su ganta Amir dai zai iya ganeta shima ba lalle ba.
A fili na furta"Na ga ta kaina ni Fa'iza wannan wata irin rayuwa nake yi haka..?

*FA'IZA NA GODIYA TACE KU YI HAKURI KOWANI TSANANI SAUKI NA WAJEN ALLAH TACE MADALLA DA KU MADALLAH DA MASOYAN JANAFTY*




*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866

Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta

Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake

Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba

Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳

Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take

Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi

Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce

Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866

IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀

          *🅿️14*

Tsakanin zuwan Tamadina da saukan su Ya ishaq da amaryan sa Zainab garin katsina kwana biyu ne,Ni bani da labarin suna tafe,Sai da yammah da suka iso gidan nagan su,Ashe wai Mama aka kawo ma Farhan ta gani shine suka zo gayya guda bayan kanwarta zuzu har da wata yarinya mai yi mata reno,sai Iyayanta Guda biyu,ban taba ganin inda iyaye ke rako ya'yansu ganin Dangin miji ba sai akan Amaryan Yaya ishaq na fara gani sai abun bai wani bani mamaki ba ya'yan yan boko ne da suka mallaki dukkan wani kawan duniya.
Shashen sa suka yada Zango dukkansu ni dai iyakata nayi D'awaniya da su kamar yadda na saba na abinci da shimfidar fuska wacce Hausawa sukace ta fi na tabarma.
Har shashen nasa na shiga suna ciki ita da kanwarta mai renon ne ke falo tana Fama da Farhan Yaya Ishaq kuma suna shigowa ya fice bansan ina zashi ba daga gani dai fitace mai muhimmanci.
Hannun mai renon sa na karb'esa ina kallon yaron yayi wani girma kamar dan wata biyar,Tsarki ya tabbata ga Allah nace acikin raina,Saboda ashe a Hoto ban ga komai na kyau da zatin yaron ba sai da na gansa a hannuna Jajir da shi kamar ka taba jininsa ya fito yafi kama da Yaya Ishaq sai dai Hancinsa irin na mamansa ne har da Idanuwan ma kuka yake ta yi yarinyar ta kasa lallashinsa na kalleta Lokaci daya ina fadin"me yasa ya ke kuka..?
Kamar zatayi kuka tace"Ni ma ban sani ba kuma ba yunwa yake ji ba yanzu na basa madaran sa"
Rikesa nayi a jikina ina kara Tattaba jikinsa naji zafi kad'an alamun yana Tare da zazzabi sai na kalleta lokaci daya ina fadin"Kamar da zazzabi a jikinsa bari nayi mai wanka sai a bashi mgani"
Kamar zatayi mgana sai kuma ta fasa ni kuma na fice da shi zuciya ta daya,Daman su Amir na makaranta basu dawo ba,kitchen na shiga na saka Ruwan zafi bayan na goyasa luf kuwa yayi shuru ruwan na zafi na juye a baho na shiga Dakina nayi mai wanka tas da ruwa masu dimi ina cikin yi mai wankan na fahimci Cibiyarsa ne ta dan kumbura ina da wani mgani da Goggo ta bani Tun Ahmad na karami da cibiyarsa ta fara kumbura ina fara shafamai ta koma ta daina ciwo kuma ta Daina kumburin,sai na Dauko daman ban cika banzarta da irin wadanan kayan ba tunda ina da yara na mulke mai Cibiyar da shi cikin kayan Ahmad da suka yi mai kad'an na saka mai riga da wando,na goyasa ram a bayana ba jimawa sai barci ya kwashe sa da shi a bayana na cigaba da Hidima ta Ahmad daman yayi barci ne yana tashi ya kafa rigiman sai na Sauke Farhan dake bayana na goyasa.
Ina Dariya shima na Sunkucesa na Saba a kafad'ana ina fadin"Haba babban mutum ka girma ka bar ma kaninka bambon mana"
Kuka ya fara min na fita da shi Falo na Zubomai abinci na zauna ina basa Shidda Saura sai ga yaran sun Dawo daga makaranta suna ganin goyo a baya suka fara tambayana Umma wa kika goya kamar ma Anum taji Labari.
Ina mirmishi nace"Sabon jaririn Anty ne"
Anum ta daka tsalle tana lekonsa ta bayana kafin tace"Umma waya zo da shi..?
Sai nace"Tare da Daadan ku suka zo da Antyn ku"
Anum ta fara tsalle tana oyoyo oyoyo Daada Musty na tayata Amir dai Dakin su ya shige ya Sauya kaya gudu ta kwaasa zuwa shashen baban nasu nace mata ya fita ta bari ta sauya kaya taci abinci in suka yi sallah sai ta shiga ta gaida Antyn nasu bata da yadda zatayi hakanan ta Hakura ni suka bari da kwashe takalma da jakunkunar su da suka watsar a tsakar Falon.
Anum dakina ta Shige Saboda na maidata da ita da kayanta tare dani,ina shigowa na iske ta watso kayanta kan gado da karfi nace"Anum ba na hanaki watso kaya ba..?
Cikin rigima tace"To umma ban ga wanda zan saka ba ne"
Riga da sikat na Dauko mata na bata ina Fadin"Duk na goge fa kayan nan ammh ji yadda kika wargazasu Anum"
Ganin ban ji dadi ba yasa tace"Kiyi hakuri Umma"
Kanta na shafa ina fadin"Bakomai yar Umma muje aci abinnci"
Musty kuma Amir ya cire mai kayan makarantar ya sakamai, na gida suka fito falo na zubo musu abinci Farar shinkafa da miya,Sa'adatu ta aiko min da Kayan Miya itama daga gidansu aka aiko mata dashi kamar babanta aikin gwari yake yi.
Dukkansu waje daya na Hada musu kamar yadda na saba sun fara ci,Anum da Musty suka fara rigima kamar kullum nace su bari suka ki sai na kalle su ina fadin"Anum zan mai da ke cin abinci ke kad'ai tunda bakya jin mgana"
Jin haka yasa Da sauri Amir yace"Umma ki yi hakuri Musty ke Tsokananrta ki barta mu rika ci tare"
Sai na gyada kai ina fadin"Musty kana son Bulala ne..?
Na fada ina nuna masa hannun alamun duka kafada ya makale dariya nayi kafin nace"To ka daina tsonakar Yaya Anum in baka son duka"
Da sauri ya gyada min kai Lokaci daya yana fadin"To umma"
Cikin Salom mganarsa ,cin abinci suka cigaba da yi a natse ni kuma Farhan dake baya na ne ya motsa sai na mike ina Jijjigasa Daidai da Bude kofar falo da Shigowar Yaya Ishaq bayansa Jamal ne da manyan Ledoji,Nasan har ga Allah bai kalleni ba,ballatana ma yasan wanda na Goya Sannu da zuwan ma da nayi mai ban ji ya amsa ba Jamal ne yake kokarin Sauke Lodijin hannunsa a falon da Sauri ya Juyo yana fadin"Jamal bani Lodojin Hannunka"
Yafada daidai da yaran zasu tashi suna kiran Daada da karfi nace su koma su gama cin abincin su duk da ban kallesa ba nasan sai alokacin ya bini da kallo ni kuma sai na Dauke kaina ba domin ina jin Haushin sa ba sai domin nasan ba ni da wata Daraja a wajensa shiyasa nima na koyi kama kaina.
Jin abunda nace ne yasa ya kalli yaran yana fadin"Ku gama cin abincin ok.?
Atare suka gyada mai kai Jamal ya mika masa ledojin hannunsa ya shige Bangaransa sai da ya shige na Dawo da kallona wajen Jamal wanda ya zauna saman kujera su Amir na gaishesa ya amsa yana fadin"My Childreen how far"
Amir ne ya amsa mai da We are fine Uncle"Dariya yayi yana fadin"Daddy na ya fi kowa gane karatu a makaranta ko Amir..?
Anum ta tura baki tana fadin"Nifa Uncle"
Kallonta yayi kafin yace"Mommy nama tana ganewa itama"
Jin haka yasa ta washe baki Musty kuma ya tayata,Sai alokacin ya Dago muka gaisa,cikin yanayin mganata nace"Ya su Mama..?Daga ina haka da yammah nan..?
Yana sauke ajiyar zuciya na gajiya yace"Wlh Dad din Anty Zainab muka kai Masauki  sannan muka je Restaurant  muka yi oder abinci muka Biya gidan Mama muka kai mata kinsan Mom din Anty Zainab din wajen Mama ta sauka"
Na jinjina kai ban yi mgana ba ya cigaba da fadin"Shine duk najini a gajiye me kuka dafa ne..?
Kai tsaye nace"Farar shinkafa da miya ne a zubo maka ne..?
Kai ya girgizamin kafin yace"Bari mu yi sallah naji an fara kira ma"
Ina shirin mgana Yaya Ishaq ya fito Daga bangaransa, da Sauri bayan sa Zainab ne da kanwarta,Wacce ke jan Hannun yarinyar da suka zo da ita baiwar Allah tana ta kuka.
Ganin su hankali tashe yasa Jamal ya mike cikin wani yanayi yana fadin"Me ke faruwa ne..?
Zainab ne cikin rawar murya tace"Farhan..Ba mu ga farhan ba"
Sai abun ya bani mamaki suna nufin basu ga Farhan goye a bayana ba..?
Kafin na iya mgana Zuzu ta mari yarinyar nan Lokaci d'aya tana Hankadeta cikin fada tace"Ina Farhan.?wa kika bama shi..?
Yarinyar sai ta kasa mgana sai kuka Ya Ishaq ya fara fadin"To ku ina kuka shige ku bar ta dashi..?
Zainab ta fara fadin"Muna ciki ni da zuzu muna mgana mu ka bar Farhan hannun Shema'u"
Ganin abun nasu ya koma kan yarinyar har Ya Ishaq ya fara fada ita kuma sai ta kasa mgana ta Dago tana kallona kafin nayi mgana da Sauri Anum tace"Jaririn Anty..?ga shi nan Umma ta goyasa"
Sai kallo ya koma kaina ni kuma sai na juya bayana suka ga Farhan goye a bayana,yana barcinsa cikin kwanciyar Hankali ina jin su suka Sauke ajiyar rai a tare Zainab tace"Thank god.."
Cikin yanayin mganata nace"Na shiga ne na iske yana ta kuka na karbesa ashe cibiyarsa ke ciwo shiyasa yake Rigima"
Kamar kiftawan ido nagansu a gabana,suna rige rigen kwancen goyen bayana ba Ya Ishaq ba,sannan ba Zainab ba kanwarta ba,zuzu ce ta kalleni tana fadin"So kike ya karye kafarsa..?ba'a fara goyasa ba"
Ni dai ban damu ba da Sauri na Sauko shi Tare suka karbesa ita da Zainab din Mamaki ya rufeni Lokacin da Ya Ishaq ya faramin fad'a meyasa ban yi mgana ba ina ji ana neman Farhan.
Na kallesa cikin yanayina Kafin nace"kayi hakuri na zata ka gansa a bayana"
Cikin Fusata yace"In da na gansa zaki ji muna neman sa..?
Kuma kada ki kara goyasa tunda bai saba ba,Ba irin yaran ki ba ne da kika Saba goyasu ba"
Kamar wata wawiya haka na bisa da kallon Zainab ta kara fadin"Honey kafarsa bata samu matsala ba ko..?
Tafada tana nuna masa suka Taru suna kallon kafarsa yaron suna Tattabasa kamar na shafamai mugun abu,Cibiyar Ta bude tana kallo Zuzu ta leka tana fadin"What is this..?
Wannan kayan fa..?
Tafad'a a wulakance,karbansa tayi Tun anan ta cire mai kayan da na sakamai,Ita da kanwarta suka koma ciki Shi kuma ya bisu,kamar wani bita zai zai,ni dai da kallo na bisu Jamal ne, ya koma zauna yana fadin Allah ya kyauta.
Yaran kuma duk sun yi wani iri,ganin abunda ya faru ni Dariya ma suka bani wai kafarsa zata samu matsala Saboda goye,Allah sarki rayuwa da goye na illa da tuni mu kan mu mun samu illah Tunda a baya kafin zamani ya zo da sauye sauye goyen aka sani ba wani gayu da feleke feleke irin na yan zamani masu nasaba da boko ya gama ratsasu ammh irin mu yan gargajiya ai goyen muka sani.
Daganan dakina na koma Dauke da Ahmad araina nace in na goya nawa ai ba mai cewa zan karya masa kafa,Amir da Musty tare da Babansu da Uncle suka tafi masallaci ni kuma muka yi namu ni da Anum.
Daganan ta tafi bangaran Baban nasu,Ta damu sai taje sai nace ta tafi,Su Amir kuma sai da suka yi Isha'i suka dawo suma ban kara ganin su ba Bangaran suka shige Jamal kadai ne afalo na zubo mai abinci yaci muna dan Taba Hira sama sama bai jima ba yayi min sallama ya tafi.
Daki na koma nayi wanka nayi ma Ahmad,na shiryasa nan da nan sai barci yau bai yi rigima ba sosai su Anum sai goma saura suka Dawo Daki  suna bani labarin sun ci nama da Ice Cream,Amir dai bana jin bakinsa sai bakin Anum da baya gajiya da mgana.
Washegari ba makarantar Boko sai Tahfeez tun safe nayi musu shiri suka wuce,Shinkafar jiya data rage na Dumama ma yara sukaci suka tafi,Sai Sauran Taliyan data rage na Dafa musu da miyar suka tafi da shi ni kaina Sauran Shinkafar naci bamu da dankali ba kwai ba komai na Kayan breakfast ballatana nayi  musu sai na kama kaina,ina gama abunda zan yi na koma daki bayan na tattara kayan yara da suka zubar afalo.
Dakin su na shiga nayi musu kaye kayen kayan da suka watsar sannan na koma nayi wanka na yi ma Ahmad daman na Dama mai kunninsa na dura masa yasha sai ya cigaba da Wasan sa,Ganin ban da wani abu da zan yi sai na dauko Qur'ani na fara karantawa ina cikin karatun ne naji Muryan Yaya Ishaq na kiran sunana sai da na kai karshen Ayan sannan na Tsaya Daga bakin kofa ya tsaya Ahmad na ganinsa ya fara tafiya wajensa yana Washe mai baki ya Dauke sa ya daga sama yana fadin"Ahmad ka zama kato yanzu"
Shi ko sai bangala Dariya yake yi.
Hijabin jikina na gyara sannan na kallesa ina fadin"Ina kwana.."
Ya amsa ba tare da ya kalleni ba ya cigaba da fadin"Ba abun karyawa ne..?
Kai tsaye nace"Babu komai na cefane shinkafar jiya ce da nadafa ta rage muka dumama muka ci ni da yara"
Shuru yayi bai kara mgana ba daganan ya fice Dauke da Ahmad ashe kasuwa ya tafi yayo mana Cefane duk da bamai yawa ba ne zai iya isa har bayan sun tafi muma yayi mana Saura.
Na rana kadai yace nayi Inaga a waje ya siya musu wanda zasu karya da shi,couscouss nayi musu da rana mai Hanta da kayan lambu,basu fito ba nima ban bisu ba sai bayan La'asar na shiga muka gaisa sama sama Farhan na Hannun kanwar ta kamkamesa sai ban zura kaina wajen karbansa ba,na fito na koma Daki Ahmad kamar ya sani yaki ko sauka yaje wajen zainab din data ke kiransa ya lafe ajikina.
Tunda suka zo suna bangaransa komai sai dai na shigar musu da shi ban damu ba domin nasan lada zan samu ciyar da su din da nake yi sannan Gidana suka zo akwai hakkin abinci su a wuyana.
Kwanansu uku da zuwa Ya Ishaq yace na shirya zamu je gidan Mama na gaida iyayan zainab,Da daddare mukaje dukkanmu har da yara da ita Zainab din sai da naga mahaifiyarta da mahaifinta naga inda suka Dauko Kyan Fuska Mahaifiyarsu Hajiya Halima mun gaisa cikin Sakin Fuska Mahaifin su Dr.Lawal ya amsa min a Wani karkace ya kalli yarsa yana fadin"My dota wannan ce abokiyar zaman taki..?
Ta dagamai kai tana fadin"Yes Daddy"
Ya kalleni ina Duke gabansa Ahmad na Hannuna kafin yace"Sannu"
Nayi shuru domin ban jisa ba Itace tace"Daddy ta na da problem din Hearing sai ka daga murya"
Ido ya ware kafin yace"is that serous.."?
Kai ta gyada mai sai naga ya daga glass din sa sama yana kare min kallo araina sai naji girmamsa ya zube ai shi Babba ne kuma namiji irin kallon kurillah dayake bina da shi bai Dace ba.
Su Amir kuwa da suka gaishesa ya amsa yana fadin"Bakaken ya'yan Ishaq kuna lafiya..?
Naji abunda yace sai naji ban ji dadi ba saboda su yara ne abu kad'an za'a fada su dauka wani abu ne Jikansa ya amsa yana ta mai wasa Anum nata son ya bata ta Dauka yace"No..No..baza ki iya ba kada ki kada shi..Kinga farin yaron da babu a gidan ko..?
Duka har su Mama suna falon Ammh ba wanda ya damu da mganarsa sai ma Dariya da Mama tayi tana fadin"Wlh kuwa Alhaji uwar ai sai dai in ta Haihu su dauko bakin Fatarta"
Hajiya Halima ce duk bataji dadin Mganganun ba sai ta juya tana yi ma Zainab mgana,ni dai ina zaune kamar wata yar aikin cikin su na kosa mu koma gida,aiko sai wajen goma muka koma gida,Da safe ina yi ma su Amir shirin makaranta Amir ya kalleni yana fadin"Umma menene baki..?
Gabana ya fadi na kallesa na kasa mgana ya kara cewa"Umma baki ba abu ba ne mai kyau..?
Da Sauri nace"Da baki da fari duk abu ne mai kyau Amir kaji ko..?
Ban kara basa damar mganar ba saboda bansan me zan ce mai a gaba ba,Bana so ya'yana su fuskanci abunda na Fuskanta tsawon shekaru
Ashe basu tsira ba Dole dai sai an goranta ma ya'yana kwanansu shida Zainab din tagayamin washegari zasu koma saboda ayyukansu sun zo sun gaishemu tunda naki zuwa nace mata zan zo in sha Allahu.
Zainab ba ruwanta macece Faram Faram ko ta na da wani abu aranta bata taba nuna min ba Kanwarta ne mai D'agawa da isa harta su Amir basa Rabanta,Har Anum da take da Son Jama'a basa zuwa kusa da ita ta cika Fad'a da isa da fadin rai.
Ni ban isa na hana su Amir shiga bangaran Mahaifin su ba,Suna son Daukan Kaninsu ni kums ban isa na Hanasu ba ai dan'uwansu ne ni bansan abunda ya faru ba da yammah bayan sun dawo daga makaranta Kayan su kadai suka cire ko abinci basu tsaya ba suka tafi chan wajen Farhan har da Amir da bai cika shiga ba in dai ba Tare da Babansu ba.
Ina kitchen ina Zuba musu abimci Amir ya shigo har da hawaye a gefen Idanuwansa na kallesa ina Fadin"Babana wa ya tabamin kai..?
Bai min mgana ba ya fita nima na Dauki abinci zuwa Falo na ijiye Saman Cafet din dake Falon na isa ga Amir daya zauna yayi Tagumi.
Na cire hannun Tagumi ina Fadin"Uhm..gayamin wa ya tabamin kai..?ko Anum ce ta tsokane ka..?
Cikin ido ya kalleni yace"Umma kin ce baki abu ne mai kyau..Ammh yar'uwan Anty tace min ni baki ne kada na Shafa ma Farhan baki na"
A rarrabe ya fadi mganar kuka yaci karfinsa Amir na da zuciya shiyasa bai cika Hayaniya ba.
Jawosa jikina nayi na Rumgume ina Fadin"Ya isa..Shiii..Ya isa"
Na dagosa na Share mai Hawaye ina Fadin"Kada ka damu da mganarta Da fari da baki duka Hallitan Ubangiji ne sannan Duka d'aya suke a wajensa.."
Zai kara mgana na girgiza kai ina Fadin"Ya isa zauna ka ci abinci"
Bai yi musu ba ya zauna sai dai sai ajiyar zuciya yake saukewa Raina sai naji ya baci taya zasu rika Gurbatamin Tunanin yarana Amir dan Shekaru tara da wani abu suna neman sakamai Tunanin banza.
Ina cikin Tunanin naji yace"Umma su Anum suna wajen Anty"
Kai na gyada mai ina fadin"Bari naje na taho da su"
Kai Tsaye bangaran nashi na shiga Zainab din bata falo sai kanwar nata,Sai yarinyar dake kula da farhan Tana rike da shi ita kuma Zuzu tana danna wayarta Anum da Musty suna ta wasan su ya'yan Anty ne su.
Ina shigowa kai tsaye ita na Nufa ina Fadin"Me kika fad'ama Amir..?
Da yanayin mganata ta Dago tana kallon kafin tace"Ni..?
Lokaci daya tana nuna kanta tana wani tabe baki ban damu ba nace"Baki Tunanin shi yaro ne..?in bazaki bari ya Daukesa ba,sai ki hanasa  ba wai ki gayamsa mganar da Hankalinsa bazai iya Dauka ba.."
Ta kuramin ido tana kallona ban damu ba na cigaba da fadin"Kada ki kara gayama yara na abunda zai Dame su bana so..Ke bakuwace ki gama bakuntarki ki tafi bana so ki shiga Tsarin Tarbiyan yara na"
Har na juya na juyo ina kallonta Lokaci da'ya ina Fadin"Sannan in baki sani ba ki sani da Bakin da Farin duka Hallitun Ubangiji ne sannan d'aya suke a wajensa Launin fata bazai taba zama wariya ga musulmin kwarai ba"
Daga haka na juya na kama Hannun Anum Da Musty muka fice ina kallo Har Zainab din ta fito daga cikin Dakin ta tsaya tana kallona ni kuma ko kallonta ma ban yi ba.
Haka kurum naji ni zan iya Daukan kowani cin zarafi ammh bazan aminta arika cin zarafin yarana ba a bata musu Tunanin su ba Shiyasa naja mata kunne tun da wuri.
Ni ban san ashe wannan mganar tajawo min bala'i ba sai da Daddare sai ga Mama da mahaifan Zainab din Har da Anty Binta sun zo gidan,Ya Ishaq da bai yini a gida ba shima ya Dawo Kirana kawai  yazo yayi da kansa Fuskar nan tasa a hade kamar Hadari Allah ya taimake ni yaran sun kwanta da wuri da a gabansu za"a cimin zarafi.
Ima fitowa tun da naga mama da Anty Binta na sadakar wannan taron nawa ne sai kanwar Zainab da ke jikin Mahaifinsu tana ta sharban kuka Fuskar kowa ba fara'a na samu gefe na zauna ina gaida su Mama ko amsani batayi ba ta fara dakamin Tsawa tana fadin"Rike gaisuwarki mara Mutumci me wannan yarinyar tayi miki kika zageta kika ci mata Mutumci..?
Sai da ta fad'a na Dago ina kallon Zuzu din har tana wani matse kwalla da majina sai alokacin na Fahimci komai ban ji nayi nadama ba cikin yanayin mganata nace"ni ban zageta ko naci mata mutumci ba..nayi mata fad'a ne"
Anty Binta tayi zaraf tana fadin"Fada..?Sannu uwarta yarki ce da zaki tasata kina mata fada ishasshiya.?
Hajiya Halima ce tace"a bi a sannu Hajiya"
Mama tace"Hajiya ai bata da mutumci ne..Daman bata so auran Ishaq da Zainab ba,kuma  tun tuni take neman daman cin mana mutumci bata samu ba sai yau"
Ni dai sai na kasa mgana Yaya Ishaq ya kalleni ya watsamin Harara yana Fadin"Daga kawai ta hana Amir Daukan Farhan Saboda bazai iya Daukansa ba sai ki bita har Daki ki zageta ki zagi iyayanta sannan har kina ikirarin cewa gidanki ne uban wa ya ce miki nan gidan ki ne..?
Ko da sunan ki na siya gidan ban sani ba..?
Kaina na kasa na kasa mgana ina jin wannan cin mutimcin Mama tayi kafyci tana fadin"Ahto tambaye ta dai"
Sai kawai na samu bakina da Fadin"Ku yi hakuri ba.."
Muryan Dr.Lawal ta katseni a Fusace yana fadin"Sorry for ur self..Akan ya'yana zan iya shari'a da koma waye..Daga tazo gidanki sai ki ci mata Mutumci..?ke ba domin Ishaq ba kin isa ki ga Zuzu a inda kike..?ai kalan zaren ba kalan yadin ba ne..Ba domin ina jin kunyar shi da iyayansa ba da sai kin gayama aya zakinta akan kukan da kika sa yata tayi kin san wacece ita..?ko ni bana sakata kuka Koda yaushe ina Tattalin Dariyan ya'yana ne ba Zuzu ba ko Zeey da kuka Hada miji kika kara yarda kallon Banza ma ya had'aku sai nayi maganinki sai na saka an batar dake da Dangin ki gabad'aya"
Yafad'a cikin Kaushin murya Hajiya Halima kunya ya kamata ta kasa mgana ta Dafe kai Zainab ce tace"Is ok Daddy. "
A fusace yace"No zeey kinsan ba na Had'a ku da komai a nan duniyan ko..?
Ko mommy ku ta sa ku kuka ina jin Dalili ballatana wata shara chan"
Hawaye suka wankemin Fuska ni ce shara..?ina jin Zainab din na fadin"I know Daddy..Forgive her bata sani ba ne zuzu plz ki bar kuka kada kanki ya fara ciwo..Gobe zamu koma Abuja is ok  kin ji..?
Kai ta d'aga mata ta koma ta lafe jikin Baban nasu yana share mata hawaye yana fadin"Am sorry Angel..am sorry"
Mama tayi kayci kafin tace"Ai daka Dauki matakin da kayi niyya Alhaji da sai tafi gane matsayinta"
Hajiya Halima tace"Hajiya komai ya wuce insha Allahu"
Ni ko ina zaune jikina ya gama mutuwa hawaye suna zubomin na saka gefen Hijabina na share Yaya Ishaq yace"Ki dago ki bata Hakuri tunda ita kika yi ma laifi"
Na kasa Dagowa sai ya dakamin Tsawa haka na Dago fuskata Shabe Shabe da Hawaye cikin yanayin mganata nace"Ki..yi..hakuri.."
Juyawa yayi yana fadin"Ta baki hakuri am sorry Zuzu.."
Kai ta gyada ta na kara kwanciya jikin Baban nata,Mama ta kalleni tana fadin"Sai ki tafi ki bamu waje mara mutumci"
Na tashi da Sauri na shige Daki na,na fada kan gado ina sakin kuka na bansan Lokacin da suka tafi ba sannan ni kaina bansan adadin Lokacin da na Dauka ina kuka ba kaina ya fara ciwo,ko sallar daren da na Saba a daddafe nayi saboda Jiri naji yana Dibana da Safe dakyar na iya tashi na shirya yara suka tafi makaranta kuma ahakan nayi musu abun karyawa na bar musu a kitchen na koma Dakina nasha panadol na kwanta ina jin kamar zazzabi zai kamani.
Ban san tafiyar su ba Domin Wanda ya ijiyeni bai min sallama ba Ballatana Dangin da sukace zasu batar dani,ni da Dangina Saboda an saka yar gata kuka,fitowa kawai nayi naga gidan wayam,sannan na Fahimci Daga ni sai halina acikin gida Zuwa yammah jikina ya Rikice jiri da Ciwon kai nasan jinina ne ya hau Allah gafurin Rahimun a ranar sai ga Hafsaatu ta zo Allah ya aiko ta Domin ta taimakeni ta iskeni kwance ba Lafiya ita ta taimakamin tayi ma yara Girki ta kula da su.
Ina da Sauran mganina na Hawan jini shi na sha bayan naci abinci,Gari na wayewa kamar waraka daga Allah sai naji Sauki,Naji dadin zuwan Hafsatu Goggo ta aiko ta ta dubami tazomin da su Kuka,kubewa,tsaki,garin kunu da wake,har da kudi in ji Goggo na karba araina ina roko ma Goggo Gida a gidan Aljannah Saboda yadda ta rike zumunci bata yada shi ba.
Kwana Biyu Hafsatu tamin ta koma saboda makaranta sannan tana kunshi yanzu sosai take samun masu zuwa nayi mata murna saboda sana'a itace mace a wannan zamanin da muke ciki.

*Littafin KANA NAKA book2and3,paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*

*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866

Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta

Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake

Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba

Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳

Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take

Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi

Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce

Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌

MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866

IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀

       *🅿️15*

Haka nan na cigaba da gungura rayuwata cikin dad'i da akasasin na cire damuwar komai a raina na riga nasan Yaya Ishaq ya zabi zainab daman a kaina sannan yanzu da abubuwa su kara kamari sai na Fahimci bayan ni ma ya zabi Sabon Iyalansa da Zainab ta fara tara mai fiye da ya'yansa sai na saka araina ni kadai suke da bayan ni ba su da kowa
Nasan zafin maraici nasan zafin rayuwa a gidan da ba gidan ku ba,bana fatan daya daga cikin ya'yana su fuskanci abunda na Fuskanta shiyasa duk kai da kawo na da Hakurina saboda su ne.
Ko da yaushe in na yi sallah ina D'aga hannuna sama nayi ma Allah kirari da sunanayensa matsarkaka sannan na yi masa magiya da naci domin ya sama min mafita kan rayuwar da nake ciki nasan bani na Tsara ma kaina ba Allah ya tsaramin kuma yaso ya ganni a haka to bazan yi masa butulci ba, sai dai zan rokesa ya sama min mafita. cikin irin kyakyawan mafitar da yake sama ma Salihai daga cikin bayinsa.
Sannan a koda yaushe addu'ata akan ya'yana shine Allah ya shiryamin su Allah ya jibanci lamarin su Allah ya sa su kaunaci junansu kada Allah ya Dora musu hassada da son kai Allah yasa su daukaka su haskaka acikin al'umma.
  Na cire Ishaq da abunda ya shafeshi acikin raina,Domin ina da tabbacin an kawo gabar daga ni har shi mun Fahimci wani irin zama muke gudanarwa ko da yake ni ai na Dad'e da sanin irin yanayin zamantakewa ta dashi shine a wajensa yake kallon duk abubuwan da yake yi min ahakan ma kamar yana min alfarma ne.
Tunda suka koma ban kara jinsa ba,Nima ban damu ba tunda ko ina da wayar baya nema na sai na maida kaina wajen kula da ya'yana,Ba na ganin kowa sai jamal shima sai in ya shigo anguwar tamu ne,Badariya kuma Mama ke hanata zuwa tunda basu koma makaranta ba sai na Dad'e ban ganta ba.
Ko cefanen mu ya kare sai dai nayi ta Dubaru na, saboda yara in ni nayi hakurin yunwa su baza su iya ba,akwai Ranar da sai mu yini bamu ci ba Daga karshe Garin kunun Ahmad nake dama musu su sha su kwanta,saboda bani da inda zan fita in nema koma naje tona ma kaina asiri zan yi sannan daga karshe ace karya nake yi,ana ganina a katon gida sannan an san mijina babban ma'aikaci ne ba kowa ba ne zai san yanayin da yawan mata suke Fuskanta acikin katon gida ba,da yawan mu ai kurace lullube da fatar akuya.
Ko sa'adatu da muke zumunci da ita sosai ban taba bud'e baki na fad'a mata matsalata ba sai dai yau da gobe bata bar komai ta fara Fahimtar gidan ne kawai da mijin ammh babu wani Sauran jin dadin da nake ciki da ni da ya'ya na har ta kai yara su ka daina zuwa da Abinci makaranta Saboda komai ya kare sai dai ruwa,Tsakin da Goggo ta aiko min dashi da garin Danwake duk ya kare a kitchen di'na ko kwaran Shinkafa bani da shi ban kuma san inda zan je na mema ba.
Mun yi sati cikin wannan yanayin Duka Dubaruna sun kare nima na kasa,Ranar wata laraba ko makaranta basu je ba,Basu ci abinci jiya da Daddare ba haka da Safe Anum da Musty suna kwance suna fama da ciwon ciki kuma nasan na yunwa ne Ahmad kuwa ya lafe ajikina sauran garin kunu ne na dama mai kadan ya sha shima ba domin ya ishesa ba,Amir kuma saboda ya na babba yasa bai nuna gazawarsa ba,Ammh shi kan shi yana jin yunwa ni kaina Dauriyan kawai nake yi ammh na fara Sarewa.
Muna zube afalo kamar kayan wanki kukan zucci nake yi na kasa na Sarari na Daga hannuwana sama nace"Ya Allah ga baiwar ka nan Fa'iza ka fini sanin Halin da nake ciki..Allah kayi gaggawan kawo min mafita d'aya daga cikin mafitar ka ya Allah"
Ban gama sauke Hannuwa na ba naji Sallama ina d'ago kaina naga Sa'adatu ashe Haruna ne yace ta shigo ta duba yau su Amir basu je makaranta ba Allah Sarki bawan Allah wajen wata biyar Yaya Ishaq bai biyasa kudinsa ba ammh bai taba gazawa daga kai su makaranta ba har mgana nayi mai ko zai bari ne yace min bakomai yiwa kai ne.
Ko ban fad'a mata ba ganin mu cikin wannan yanayin ya bata tsoro ta kalleni cikin Tausayawa tana fadin"Maman Amir Allah yasa dai lafiya na gan ku duk a kwance sannan Mallam yace yau su Amir basu je makaranta ba shiyasa yace na shigo na duba ko kuna lafiya?
Ina kokarin mikewa Ahmad ya lafeni na jingina da kujera ina fadin"Lafiya lau Sa'adatu yau din dai basu samu zuwa ba ne"
Shuru tayi kafin ta kalli su Anum lokaci d'aya tana fadin"Anum ko ba lafiya ne yau ban ji Surutun ki ba..?
Kawai sai yarinyar nan ta saka kuka cikin kukan take fadin"Yunwa muke ji tun jiya bamu ci abinci ba"
Musty ma sai ya fara kuka wai shima Yunwa Ahmad na jin su shima ya saka Rigima na saki baki kawai ina kallonsu na kasa mgana ta Dago tana kallo na kafin tace"Haba Maman Amir sai ki bar yara da yunwa in suka samu wata matsalar Dalilin haka fa..?
Sai na kasa mgana Hawaye suka cika kwarmin idona cikin wani yanayi nace"To ya zan yi Sa'adatu..?
Bani da wata mafita sai wacce ubangiji ya kawo min kawai"
Cikin mamaki tace"In shi babansu baya gari ba ga gidan iyayansa ba,bai kamata suna garin nan kuna zama cikin wannan halin ba ai yunwa bala'i ce musamman ma ga yaran nan"
Mirmishin takaici nayi mata ban kara mgana ba da Sauri ta mike ta fita ba jimawa sai ga shi ta Dawo da kuni da yawa abotiki da Soyayyan Dankalin Hausa ta Diremin tana fadin"In ke kin Daure ai su baza su iya daurewa ba saboda yara ne..Zaman taren kenan da ko Amir kika aikomin da nasan abunda zan yi"
Ni dai ban ce komai ba sai godiya nake yi mata nan da nan na tashi na shiga Kitchen na Dauko Kofuna na zo na Zuzzuba musu na saka ma kowa Dankalin,ita tafiya tayi ta barmu bayan ta kawo mana,Sai gashi mun ta  da shi duka Lalle gaskiyan almajiri da yace yunwa bata da Hankali na yarda sai da muka koshi na samu karfin jiki,Amir shi ya taimaka min ya gyara Dakin su ya kwashe kayan da suka zubar a kasa ni kuma na gyara Sauran d'akunan nayi ma Anum da Musty da Ahmad wanka Amir ma na cudamai baya sai bayan sun shirya naje nayi wanke wanke tun jiya ban samu yi ba nima kaina ba ni da karfin jiki.
Zuwa chan sai ga Sa'adatu da Shinkafa yar Hausa takai tiya Hud'u da Garin tuwo da Tsaki,Da kayan miya har da su maggi da mangyada,Na rasa da bakin da zan yi mata godiya na share kwallar data zubomin Lokaci daya ina fadin" Nagode..Nagode yadda kika ji kaina da ni da ya'yana ke ma Allah ya jikan ki"
Ta amsa min da Ameen Ameen ta jima muna hira sama sama da ita kafin ta tafi wannan kayan abinci su suka taimakemu suka fitar damu daga cikim Halin da muka so fadawa na rashin abinci Maman da ya bar ma sallahun komai namu bata Damu ba ko zamu mutu mun dad'e bamu mutu ba.
Abun da ke bani mamaki in ni bata kaunata ya'yan da har da D'anta aka bada gudummuwar fitowarsu duniya bazata tuna da su ba..?ammh bata Damu ina da yakinin ko rasa su sukayi sai nafi kowa asara ita d'anta yana da matar so sannan da yaron so bazata damu domin yunwa ta illatamu ba.
Ni kuma tundaga Lokacin nayi alkwarin ko zamu mutu bazan kara tambayanta wani abu daya Danganceni ni da ya'yana ba in suka Sauke Nauyin dake kansu ruwan su in basu sauke ba bazan matsa musu ba, duk wanda yayi nagari don kansa sannan Hakki ne ranar gobe kiyama sai Allah ya tambayesu domin ai ya'ya abun kiyo ne ga wanda aka bamawa,kuma za'a tambayi kowa yadda ya kiwata nashi.
Haka na dinga ririta kayan abincin nan Saboda in suka kare mu ne a ruwa bamu  kuma da wata mafita sai dai su kofofin ubangiji ba su da iyaka in ya kulle maka wata kofar kafin wani Lokaci sai ya sake bude maka wata Sabuwar kofar.
Dama bana ganin kowa kuma hakan bai dameni ba jamal ma ya jima bai leko ba ashe sun janye yajin aiki an koma makarantu,Nima ban sani ba ni ba Tibi ba Radio ba, ina nan dai Dim d'in sai abunda akazo aka fad'amin yaran ma tun suna damuwa da kallon har ya fita ransu na rika na cusa musu karatu acikin ransu shiyasa lokacin wasan su kad'an ne lokutan karatun su yafi yawa.
Badariya ce da tazo ita da abokiyar karatunta Raliya sun taba zuwa sau biyu da ita,ita take fadamin sun koma makaranta cikin Satin nan sannan  Jamal kuma Yamai sukaje shi da Mama sai shekaranjiya suka dawo jiya kuma ya koma makaranta,Sun iske na yi Tuwom masara miyar kubewa Bushasshiya Da yaji caryfish,sai tayi Dad'i sosai Badariya tace na zubo musu na kawo musu suka zauna akasan Cafet ita da kawarta ta suna ci suna Fira ni kuma ina gefen su Ahmad na jikina ya lafe.
Kawar Badariyan ne ta Dago tana kallo na kafin tace"Gaskiya Anty Fa'iza kin iya girki sosai kiji kamar ka tsinke Hannu"
Mirmishi nayi kawai ban yi mgana ba Badariya tace"ai in dai bangaran girki ne in kika zo wajen Anty Fa'iza ki yi Salute kawai Raly."
Raliya tace"Naga alama irin su ne watarana sai ki gansu da Babban Wajen cin abinci"
Badariya tace"Allah ya amsa bakin ki ai zata iya ta iya girke girken kala kala na zamani da na gargajiya"
Raliya tace"Nasani ai wanchan zuwan Danwake mukaci da salad haka na koma gida ina ma su Hajiyarmu Zencen suka yi tamin Dariya suna fadin Duk Santi ne"
Badariya ta kwashe da dariya kafin tace"basu karya ba santin ne"
Atare suka yi dariya kafin su cigaba da cin abincin su sai chan Raliyan tace"Badar wai ina matar bro din ki da Lokacin ina Kaduna kikace an yi bikin?ko ba anan gidan take zaune ba..?
Badariya tace"Tana Abuja tare da Yaya Ishaq ai yar chan ce ya aura har ta Haihu ma namiji Lawal suna kiransa Farhan"
Kai ta jinjina kafin tace Allah ya raya sai da suka gama cin abincin Badariya ta kwaahe komai ta kai kichen,tazo ta sharemin Falon ina ta barshi bata ji ni ba,Wayoyin su suka dauka suna ta Latsawa suna Hira jefi jefi ni kuma ganin Ahmad yayi barci na mike da niyyar naje na shimfidar da shi sai naji Raliya na fadin"Ke Badar na  manta ban fada miki ba, kinsan Hajiyar mu tana shiga kungiyoyin tallafa ma mata da marayu ko..?
Badariya ta daga mata kai batare da tayi mgana ba ita kuma sai ta cigaba da fadin"To akwai wata kungiyar Womens Charity Faundation kungiyace ta manyan mata da suke tallafama mata da marayu domin su Dogara da kansu suna koyar da Training din sana'o'i da Dadama sannan in sun gama,suna ware kamar Mutane ashirin Hazikan ciki su tallafa musu da jari kyauta"
Kasa kunnina nayi tun da naji mganar tallafama mata sai na koma na zauna inaji Badariya na fadin"Ni kuma meyasa duk kike fadamin wannan..?
Raliya tace"Banza baki cin Ribam zencen..duk shekara suna zaban State din mu na arewa su zo su koyar da sana'o'in da kuma bada tallafin wannan shekarar katsinan mu ne har anbuga Form din Hajiyarmu guda Goma aka kawo mata shine nace bari nayi miki mgana ko zaki yi sai mu cike mu yi tare Allah Foudation di'n suna koyar da abubuwa masu kyau matuka komai da kika sani ko banza muma zamu karu"
Badariya tace"Da karatun zamu ji ko da Koyan sana'a?
Raliya tayi dariya kafin tace"Haka Hajiya tace da nace ta bani Form guda Biyu ni dake sai tace mu ji da karatun ma tukunnah yadda muke da son jikin nan ba abunda zamu iya koya"
Badariya tace"Allah ya saka ma Hajiya da Alheri"
Suka yi dariya a tare ban shirya ba kawai naji bakina ya furta"Zan yi..Badariya zan yi dom Allah"
Gabadaya suka Dago suna kallona Badariya ta kalli Raliya itama ta kalleta suka kuma dawo da kallon su kaina cikin Sauri nace"In ba damuwa ni ina so zan yi"
Raliya tace"Da gaske Anty Fa'iza..?
Ciki  jin dadi kamar an ce ma an Daukeni nace"In sha Allahu.
Badariya tace"To ke kin ji Raly maza ki samo ma Matar bro di'na Form dim ta cike kuma ki fad'ama Hajiya"
Raliya tace"In sha Allahu kuwa ai tashi zaki yi muje gidan tare ki mata bayani mu karb'o tare kada tace shiririta na ne"
Da Sauri ko Badariya ta mike tana Fadin"Yauwa muje..Anty Fa"iza bari muje gidan su Raly din na yi mgana da Hajiya insha Allahu zaki samu"
Kai na gyada musu ina ma Raliya godiya tace"Bakomai Anty Fa"iza ni dai don Allah ki dauki bangaran girke girke yadda zaki kara zama top a harkan sai mu bud'e gidan abinci watarana"
Sai ta bani dariya ammh a raina na amsa da Ameen haka suka fita suia barni kamar an sakani a aljannah haka kurum nake jin farinciki acikin raina na fara Hango mafitar da na Dade ina rokon Allah akanta,sai dai jikina yayi sanyi ganin har kwana biyu Badariya bata dawo ba ballatana naji yadda suka yi,Sai da Satin ya shige wani ya shigo sannan tazo da Form din tana fadin ba kowa a gida ne shiyasa najita shuru cikin mamaki nace"Ina mama taje..?
Badariya tace"Abuja suka je ita da Anty Binta"
Na kalleta cikin wani yanayi kafin nace"Me ya faru..?
Badariya ta tabe baki kafin tace"Farhan ne ba lafiya mura yake ta fama dashi har ta na hanashi Numfashi sai da aka kwantar dashi a asibiti Ya Ishaq duk ya Rud'e ya Rudar da su Mama sai da sukaje suka gansa Hankalinsu ya kwanta"
Cikin jimami nace"Wayyo ya jikin nasa..?
Cikin basar da zencen tace"Yaji sauki sun koma gida ammh naji su mama na fadin baban zainab din yace zasu fita da shi kasar waje a kara Duba Lafiyarsa Nimonia ce ke damunsa"
Na nuna jimami na sosai ina ta addu'an Allah ya basa lafiya Badariya ta fito da Jakarta ta Dauko Farar Takarda Doguwa tana fadin"Kin ji Anty Fa'iza matso mu cike wannan Form"
Cikin Farinciki nace"ashe kin karbo min?
Badariya tace"Eh ai tun ranar mukaje nayi ma Hajiya bayani bata da matsala tana jin ma matar Yayana ce tace bakomai basai mun biya kudin Form d'in  ba tace ki cike a maida mata in sha Allahu zata sanar in Lokacin Traning din yayi ammh akwai pasport guda uku kina da shi..?
Na kalleta saboda ban gane me take nufi ba da Sauri tace"Hoto karami nake mgana wanda za'a lika acikin Form din sauran kuma za'a kai musu"
Ta fada tana nuna min inda za'a saka Hoton sai na gane nace mata bani da shi sai tace"Bakomai in mun gama zan Dauke ki Hoto a wayata in na fita sai na Biya shagon Hoto a Wanke min a maida shi karami yau nake so naje na kai ma Hajiyar, Mama ma karya nayi mata da zan yi subbmitting wani aiki a makaranta"
Kusa da ita na matsa ta sauka kasa saboda yadda zataji dadin Rubutu ta dago tana fadin"da Farko a jikin Form d'in sunanki ake tambaya"
Kai tsaye nace"Fa'iza Sidi karofi"
Ina kallo ta Rubuta sannan tace shekaru na gayamata sai kuma ina da aure..?ta saka eh ya'yana na wa..?
Ta saka,sannan yaushe Mahaifina ya rasu na ce ta saka shekaru goma sha da Rasuwarsa ta saka,sai ina da Mahaifiya..?
Nace ta saka eh,Sai ina da Sana'a ?in akwai wata sana'a nake yi acikin gida? nace ta saka Babu,Sannan matakin karatuna nace itama ta sani ko Takardan gama primary ai ban da ita Saboda ban gama ba sai Badariya ta saka matakin karatu na addini Saukakkiya a Qur'ani da Sauran Littafai.
Na kalleta cikin wani yanayi kafin nace"Kada su k'i daukata Badariya kila sun fi son masu takardan ko Sakandiri ne ko Hafsatu zan bar mawa..?
Badariya tace"Zasu Dauke ki in sha Allahu ai ba da Takarda zasu amfani ba, da Kwarewa ce ke kuma ai bana jin ki ta wannan bangaran"
Ni dai duk sai naji jikina yayi sanyi ta cigaba da karantomin ko'ina tana Fassaramim yadda zan gane tace ance in da wata matsala ta fanni hallita ko wani ciwo..?
Nace ta saka ina da matsalan ji,ta saka Hearing problem,Sai adireshin gida nace ta saka na gidan yayanta
Daga karshe sai jerin abubuwan da zasu koyar akwai girken girken zamani da na gargajiya nace ta cike min shi saboda na kara kwarewa, sai Gyaran jiki dilka da Halawa nace shima ta Cikemin,sai kuma koyan yadda ake had'a lemuka kala kala nace shima ta cikemin akwai koyar da Kunshi Fulawa,koyar da manshafawa da su sabulan wanka da na kamahi sai koyar da su yaji kori da kayan kamshin Girki sai koyar da Turaran kamshi na Itace da kwallacha
suma nace ta cikemin duk zan koya Badariya na Dariya tace"Anty Fa"iza duk ke kad'ai an ya zaki iya..?.
Ina da yakini acikin raina nace"In sha Allahu ai basu da wahalan dauk'a zan iya da amincewar Allah"
Ta amsa min da in Allah ya yarda sannan daga karshe akace in mutum nason a bashi tallafi yace eh ta sakamin eh sannan da kuma abunda zakayi da tallafin in an baka
Na kalli Badariya ina fadin"Kice ina son a bani tallafi nan saboda na kama sana'a daga cikin sana'o'in da suka koyar damu..Sannan saboda na rike kaina na kuma tallafama rayuwar ya'yana saboda inganta goben su watarana"
Haka kuma ta rubuta sai lambar waya nace ta saka min nata tunda ni bani da waya sai ko ta saka lambar wayarta.
Daga karshen karshen sai saka hannuna ta bani na jagwalgwala hakanan,Kafin ta tafi sai da ta D'auki Hotona  a wayarta bayan na saka Hijabi tace zataje a fito mata dashi a gyara muka yi sallama zuciyata ta cika da murna ammh ban daina saka Allah cikin lamarina ba adaran nayi salla sannan nayi addu'an  Allah yasa mafitan nan ta zame min mafitan alheri a rayuwata gabad'aya.
Ni dai ina ta addu'a ko da naji shuru ban damu ba daman nace in mafitan ta alheri ne Allah ya tabbatar min in kuma ba alheri aciki Allah ya kawo min wata mafitar ta alheri Ameen.
Kafin kayan abincin da Sa'adatu ta kawo mana ya kare ta kawo min Dankali hausa da yawa tace itama daga gida aka aiko mata dashi,Babansu ne ya noma na karb'a na saka albarka shi nakan soya ma yara da Safe su tafi makaranta,Wata rana ma har da rana ina soya mana muci mu sha ruwa,kuma dayake na koyama yarana cin komai duk abunda suka samu zasu ci basa zabar abinci shiyasa sai rayuwar tazo min da Sauki.
An yi wata da cike Form din da mukayi ni da Badariya tazo sau d'aya mukayi mgana tace Raliya tace an Tura Tarkadun namu chan kaduna inda Babbar Jibiyar kungiyar take da su zabi wad'anda zasu dauka za'a turo ma kowa ta sakon waya da lambar da ya saka Badariya ta tabbatar min da Hajiyar su Raliya tace ba matsala sai na saka raina asalama araina nace bakin Da Allah ya tsaga bazai taba hanasa abinci ba.
Ana haka kwatsam sai ga Ya Ishaq ya Dawo ranar wata asabar da azahar Lokacin bana gida na shiga wajen sa'adatu  muna hira to yara in sun tafi makaranta sai ni kadai kamar mayya na da zauna tunani ya kasheni sai nake shiga muna hira tana Debemin kewa rashin dangina akusa dani.
Get din a bude na barsa saboda ban yi nisa ba yagaji da Hon ya fita ya Bude ma kansa ya shigar da Motarsa sai da ya shiga gidan ya tabbatar da ba na gidan mamaki ya kamasa ya D'aga waya ya Kira Mama ko nazo Mama tace tafi wata biyu ban zo inda take ba.
Ransa ya baci nan da nan ya fara Tunanin haka nake fita ina barin masa gida a bude ina tafiyata gantalin da baisan yaushe na iya ba,Ni kuma ban san ya dawo ba sai biyu da rabi na Dawo gida domin yi ma yara girki,sannan nazo da Guzurin Dambun Dankalin da Sa'adatu ta zubamin mafarin zamana ma yau saboda na koya ne ina so nima watarana nayi lokacin da na shigo Haraban gidan naga Motarsa ban ji tsoro ko fargaba ba Allah na Tuba in da sabo ai yaci na saba da Tozarcin sa a gareni.
Kaina Tsaye na shiga cikin gida kamar daman yana jira na ne sai yau ya gwada kiran wayata a kashe duk tsawon Lokacin da ta lalace bai sani ba.
Yana ta Safa da marwa a falon ya kasa zama na shigo bayana goye da Ahmad Hannuna Dauke da kwanon Silba da Sa'adatu ta zubomin dambun aciki.
1do hudu muka had'a dashi Sanda na shigo yana bi na da wani kallo na raini kamar yadda ya saba ni kuwa sai na Dauke kaina ina fadin"Sannu da zuwa.."
Nafada ina nufar Hanyar Kitchen nasan yayi mamakin yadda nayi mai shiyasa ko taku uku ban yi ba yasha gabana cikin bacin rai yana fadin"Ni kika gani kika dauke kai kamar kin ga Dan'iska Fa"iza?
A gajiye na kallesa cikin yanayina nace"Nayi maka sannu da zuwa..ina so na shiga kitchen na sauke abun hanuna ne"
Kallo hannuna nawa ya shiga yi Lokaci daya yana fadin"Miye wannan kuma..?
Sai na Bude masa ina fadin"Dambun Dankalin Hausa ne na shiga ta koyamin ne saboda ina so nima nayi ma yara"
Yamutsa fuska yake yi kamar yaga kashi kafin yace"Wannan bakin abun ne zaki yi ma yarana su ci..?Shiyasa kika bar min gida a bude kika fita yawonki me na sha fada miki..?
Ban ce ban amince ki rika fita ko na  nan da chan ba indai ba gidan Mama ba..?shine kike so ki nuna min kin isa har kina shigowa kina ganina kika Dauke kai kamar kin ga sa'an ki ko..?
Na kallesa da Idanuwana da suka yi ciki ciki ban iya rashin kunya ba Saboda ba Halina ba ne ammh dai naji Tsoro nan nasa da nake ji a baya ya gushe araina na kasa ce mai komai kawai sai na rabasa na wuce kitchen na sauke kayan hannuna a zafafe ya biyo ni yana fadin"Fa'iza ina miki mgana kina wucewa yaushe kika raina ni haka ban sani ba..?
Ko tankasa ban yi na sauke kwanon Hannuna ya shigo Kitchen din yana Fadin"Daga gidan uban wa kike..?rokon abinci kika fara na salon zubar min.."
  Bai karisa mganarsa ba yayi shuru ganin Dankalin hausa zube a kitchen din sannan na bude karamar kular dake saman wajen wanda na soya ma su da Safe ne na rage ma Ahmad in ya tashi daga barci yaci,na dauko na barsa akitchen din yana Dube dube cike da mamaki..
Afalo na zauna akasa na kwanto Ahmad daga bayana da naji motsin tashin sa kamar walkiya sai ga shi a gabana yana fadin"Fa'iza wannan dankalin fa..?sannan naga store ba komai wannan watan mama bata aiko da kayan abincin ku ba ne..?
Ahmad na kallonsa ammh sai ya lafe ajikina ba irin zumudin daya saba yi mai a baya ni kuma ban kallesa ba nace"Wannan dankalin shi kad'ai garemu shima daga gidan haruna aka bani kyautarsa kayan abinci kuma ba'a kawo ba"
Daga haka na tsuke bakina daga alamu jikinsa yayi sanyi sai ya fara Fadan meyasa ban kirasa na gayamai ba cikin gajiya da korafinsa nace"A ina zan ganka ballatana na fad'a maka..?
Kai tsaye yace"Ina wayarki fa ?ko bata da amfani ne da bazaki kirani ba..?
Ina bama Ahmad Dankali nace"Bani da waya ta lalace tuntuni"
Sai kuma ya kasa mgana,Daganan ya shige bangaransa bansan ko ya kiran Maman ne me tace mai oho yadai fita sai chan kuma ga shi da Cefanen kayan abinci masu yawa wani Lokacin Ya Ishaq bai da matsala ta bangaran hakkin iyalansa da ya'yansa sai dai Mama itace tafi matssala ta wannan bangaran
Daga karshe yace na kwashe Dankalin nan na fitar mai dashi nace tab wlh bazan kwashe ba,Kafin yazo ai shine ya Rufamana asiri sai ya kasa mgana nasan yana ta mamakin yadda wannan karon nake iya maida masa mganarsa kai tsaye ni ko gani nayi tunda alfarma yake min nima sai na fara mai alfarma saboda ya'yan da suka hadamu tsakanina da shi ba Domin zumunci da baisan Darajansa ba.
Yaran ma da suka dawo ko da suka gansa ba su yi wani D'oki  kamar baya ba, shine daya lura da haka ya rika jansu ajiki washegari kuma yace bazasu je hadda ba ya daukesu suka tafi yawo ya siyo musu kayan kwalama da duk abunda suke so,Daganan ya sauke su gidan Mama sai Dare suka dawo ashe sallama yazo yi ma su mama zasu tafi india inda Mahaifin zainab ya dauki nauyin su Saboda aduba lafiyar Farhan sai a daran da suka dawo ya fadamin ban san Dalili ba sai naji ban damu ba nayi masa fatan isa lafiya da kuma samun abunda akaje nema.
Washegari Litini ya koma ban ma sani ba ashe ya biya Haruna kudadensa har da na wata biyu anan gaba yana ta basa Hakuri,Harunan ya ke shaidamin washegarin talata da na rako su Amir kofar gida araina sai naji sanyi,in zan fadi gaskiya Yaya Ishaq baya so na ammh kuma yana son ya'yansa kuma bai hadasu da komai ba, sai dai sabon iyalansa sun Dauke masa hankali har akan yara sannan da karin muguntar Mama acikin lamarin tunda ita ake barin ma komai.
Ina nan bansan abunda ke faruwa ba Ba mai nema na kuma nima bani da Hanyar neman kowa ashe Tamadina bata da lafiya ta fito daga bandaki ta zame ta fad'i shikenan jikinta yayi nauyi tun tana gida har an kaita asibitin general na bakin asibiti,Har Yaya Asiya dake kano ta sani tazo ammh ni da nake kusa ban sani ba Goggo ganin ba'a samu inda zan ji ba sai ta Kira Mama a waya tace ta fadamin Lokacin Hafsatu suna Jarabawa,bata samun zama shiyasa ma Goggon tace bari ta kira Maman,Tunda Har Yaya  mariya sai da tace tazo ta fad'amin tace ma Goggo sai dai tayi Hakuri bazata iya zuwa ba jin haka yasa Goggo bata matsa mata ba.
Ita kuma Mama da aka fad'amata washegari yamai ta tafi, diyar Kanwarta ta haihu,kuma abun bai Dameta ba shiyasa sai ta sha'afa.
Sai da jikin Tamadina ya kara rikicewa Goggo ta tada Ya Isa tace yazo ya fad'amin nazo in muna da Rabon ganawa da tamadina tana asibiti bata da lafiya.

*Littafin KANA NAKA book2,3.paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*


*Janafty*[6/23, 5:44 PM] +234 706 165 9686: *KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

*TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWAR ZAKI YI AMFANI DA ITA SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*..

          *🅿️16*

Na gigice tare da Dimaucewa lokacin da Yaya Isa yake shaidamin Tamadina bata da lafiya ta kwana uku a asibiti bayan tayi sati a gida ba yadda take.
Sai naji na rasa hankalina na wani lokaci, na koma nayi yaraf saman d'aya daga cikin tsofaffin kujerun falona kamar wata kayan wanki.
Hawaye nan da nan suka fara sintiri a saman fuskana kamar an bud'e famfo sai yau na kara tabbatar da cewa Mama bata kauna ta kuma har abada baza ta taba so na ba,Uwa ai ta wuce wasa ace a fad'amata rashin lafiya ammh ta gagara aiko ko Badariya ta shaidamin sai da aka gaji da jirana akaji shuru Goggo ta tado mutum tun daga karofi akazo aka fad'amin, kawai tuna hakan da nayi sai naji raunina ya karu na Fashe da kuka Yaya Isa ya zauna gefena yana fadin"Ki daina kuka Fa'iza jikin da sauki sosai.."
Na dago idanuwana sharkaf da kuka ina fadin"Wa ke zama da ita..?
Kai tsaye yace"Mariya ce..Asiya tazo ta kwana biyu ta koma to bata ma nan aka kai ta asibitin ammh naji Goggo tana fad'amin itama gobe tana Hanya"
Jin haka sai na kara saka kuka ina fadin"Allah ya tada kafad'un ki Tamadina Allah ya baki lafiya"
Ya amsa min da Ameen yana fadin"Ki tashi ki shirya sai na sauke ki a asibitin"
Da sauri na mike jikina yana faman bari har na shiga d'aki na Sunkunci Ahmad dake barci na goya na zura Hijabi sai kamar an tuna min na tuna da su Amir sai jikina yayi sanyi na fito ina Raba ido na neman mafita yanzu in na tafi ina su Amir zasu zauna..?
Ko gidan su Sa'adatu zan ce su zauna kafin na dawo..?Sai dai akwai D'awainiya acikin lamarin yara ba d'aya ba,ba kuma biyu ba har guda Hudu ganin yadda jikina ya kara Sanyi ne yasa yace min"Muje ko..?
Ya fada Lokaci daya yana mikewa sai yaga kuma ban biyosa ba sai ya juyo yana kallona kafin yayi mgana na taresa da fadin"Ya Isa yara na..Su Amir bansan inda zasu zauna ba, in suka dawo daga makaranta ba"
Kai tsaye yace"Su zauna gidan kakaninsu mana"
Sai kawai na koma na zauna ina sharan kwallah Lokaci d'aya ina fadin"Ya isa kaje kawai sai gobe da Sassafe zan taho in sha Allahu"
Shima kansa nasan mamaki yaji da mganata saboda yadda ya ke kallona sai na sake sadda kaina ina jan majina.
Ajiyar zuciya ya sauke kafin yace"Shikenan ki tabbata goben kin taho kin ji ko..?
Yafad'a cikin alamun Tausayawa acikin lamarinsa na gyad'a mai kai sai ya kara kallona yana fadin"Kina da kudin mota ne..?
Sai na kasa mgana shi kuma ganin haka sai ya cire dubu uku yan Dubu Sabbi ya bani yace nayi na mota na karb'a ina godiya na mike shi kuma ya wuce da sauri nace"Wani ma asibiti kace..?
Bai juyo ba yace"Asibitin general da ke bakin asibiti Dutsenmah"
Na gyada kaina ina fadin"Ka gaisheta ka fad'ama Goggo gobe da Safe ina tafe..Allah ya tashi kafad'an Tamadina"
Ya amsa da Ameen ya fice bayan ya kare ma falon kallo lokaci da'ya yana girgiza kansa.
Komawa nayi na zauna in da na tashi na Rushe da kukan,kukan bakinciki da takaiici ace Tamadina ta kwanta jinya tafi sati ban sani ba to ni a wani bingire zan saka rayuwata ne..?
Ahmad da yaji ina kuka shima ya fara Rigimansa na kwantosa na Rumgumesa na cigaba da kuka sai kawai ya rika bi na da kallo.
Haka na yini cikin wani yanayi motsi kad'an sai na daga hannuna sama ina fadin"Ya Allah ga baiwarka chan tamadina kafini sanin Halin da take ciki..Allah ka bata lafiya ka tashi kafadarta"
Ko abinci da na kan  yi ma yara da wuri ranar sai da suna gabda dawowa na dora musu farar taliya nace sa ci da mai da yaji,Domin bani da natsuwar yin wani abincin da zai bani wahala su kansu da suka Dawo sun ganni duk a sanyaye sannan fuskata da Idanuwana sun kumbura hatta Ahmad rigimamme yau bai yi min rigima ba kamar yasan bana cikin yanayi mai dadi.
Sun dawo suna murnan an basu resit a makaranta na shedar sun biya kudin makaranta har na Team biyu,Alfarma akayi musu saboda naje wajen sau biyu ina basu hakuri sai wannan lekowar tasa ne yaran suka mai mgana inaga yaje ya biya musu, ko kuma ya tura musu.
Ni dai da yake ba wannan ne a gabana ba ko duba Takardan ban yi ba,nace su adana cikin Littafansu.
Amir ne mai wayau cikin su shi ne ya tambayeni Umma baki da lafiya ne..?
Na kallesa cikin wani yanayi sai na kasa basa amsa,sai da daddare bayan mun idar da sallar Isha'i dukkanmu muna zaune sai na kallesu ina fad'in"Kowanne ku ya d'aga hannu ya ce Allah ka bama tamadina lafiya.."
Sai suka tsaya suna kallona Anum ce tace"Umma wace ce?
Da sauri nace"Ina wannan da ta taba kawo muku gyad'a da su masara har nace muku mamana ne kakarku.?
Suka gyad'amin gabad'ayan da sauri nace"To mahaifiyata ce, bata da lafiya ku yi mata addu'a in dai kuka yi sallah"
Fuskarsu ta nuna jimami Amir yace"Allah ya bata lafiya Umma"
Na amsa mai da Ameen atare muka daga hannu muka yi addu'a da Fatan Allah ya bama Tamadina lafiya.
Saboda tafiyata Dutsenma agobe da wuri nace su kwanta ko karatun Dare basu yi ba na kwana ina Tunanin inda zan kai su Amir su zauna kafin na Dawo na duba na hango ba su da inda yafi gidan Mama dole dai ko naki ko naso chan din zan ce Haruna ya kai su in suka dawo ban dawo ba.
Da asuba da na tashi ban koma ba ina gama shirya su na tafiya makaranta na Dafa musu abunda zasu tafi dashi makaranta,Tunda bani da komai sai nayi Tunanin na Dafa wani abu na tafin ma tamadina dashi,Shiyasa da kaina na saka Hijabi na raka su Amir kofar gida muka gaisa da Haruna na fad'amai zai kai su gidan Mama in suka Dawo da yammah ban dawo gida ba,Mahaifiyatace ba lafiya zan je na Dubata ya yi min Fatan Allah ya bata lafiya.
Na duka ina kallon yaran kafin nace"Zaku zauna gidan mama kafin na Dawo kun ji ko..?
Amir ne ya gyadamin kai Anum ce ta kwabe fuska tana fadin"Umma ki tafi dani"Na shafa kumatunta ina fadin"Zaku je Anum insha Allahu ku dai ku yi ta mata addu'an Allah ya bata lafiya"
Da haka na lallabasu suka tafi da Anum ta fara rigiman kayan sawan su ni kuma naga suna da kaya agidan mama bazasu rasa na sawa ba,Suna wucewa na shiga gidan Sa'adatu muka gaisa na gayamata abunda ke faruwa cikin tausayawa tace"Allah sarki wannan da kika kawo min ita muka gaisa ko..?
Na gyada mai kai cikin wani yanayi cikin jimami ta yi min fatan Allah ya Tada Kafad'a,na amsa mata Daman Nama nake so na siya sai tace min sai karfe tara mai naman bakin titi yake fitowa, sai na zauna muka cigaba da Hira sama sama Ahmad na bayana yana barci,Taran nayi muka yi sallama Daga gidanta na gangara bakin titi daga cikin Dubu ukun da Yaya Isa ya bani na siya Naman dubu Daya na koma gida na Dora jallop din Shinkafa,da nama daman ina da Cabeji sai nayi amfani da shi kad'an sai da nagama komai,na samu wata Tsohuwar cooler dina na zuba abincin aciki,sannan na je nayi wanka nayi ma Ahmad muka shirya tare,Atamfa ta na saka wacce Yaya Asiya ta dinkamana mu hudu,na Zura Dogon Tsohon Hijabina da yasha ruwa,kan duk ya kod'e da Takalmina duk yaji duniya ya d'aga tun wani Takalmi da Anty Nasara ta taba bani ne, yafi shekara hudu ina moransa don ma ban cika yawan fita ba,ai da yanzu bani da nasawa.
Rufe get din nayi da key din gidam,Na rike Dubu biyun da suka yi saura da abincin da na Dafa na shiga nayi ma Sa'adatu sallama sha daya da wani na isa gidan Mama,adaidaita na hau na sallame shi na shiga gidan ba kowa ina ta sallama Ashe Mama na falo tana faman kirga kudi sai dai ta ganni na shigo kamar daga sama hankalinta yayi sama bata ji sallamata ba.
Tana ganina kamar taga mutuwarta ta wani zabura sannan ta saka kudin hannunta kasan cafet din datake zaune,Tana wani zare ido tun kafin na kariso ta tareni da fadin"Lafiya ke kuma daga ina yarkace yarkace kamar yar gudun hijira..?
Gabanta na Duka ina gaisheta ta amsa a gaggauce tana kara fadin"Lafiya..?
Kaina na kasa nace"Dama..dama zan je Dutsemah duba jikin Tamadina ne"
Sai Mama ta gyara zama tana fadin"To ashe jikin har yanzu..?ni Goggon taku ta kira ni tace a fad'a miki na sha'afa tafiya ta kamani zuwa Yamai"
Ina jinta ban ce komai ba sai ta cigaba da fadin"Allah ya bata lafiya"
Na amsa da Ameen shuru dai taga ban tashi ba sai ta fara fad'a tana fadin"Wai ni kam sintirman me kika zo kika min a gabana..?
Da Sauri nace"Dama ina so su Amir zasu zo nan su zauna ne in na Dawo da wuri to..inkuma naga jikin nata yayi tsanani zan kwana shine..Shine nace bari nazo na fad'a miki tunda Babansu baya nan"
Har na gama Mgana Mama na bina da wani kallon banza sai da na Dire sannan ta karbe da fad'in"Daman ai tunda na ganki nasan banza bata kawo ki..so kike bayan na gama wahala dake na kuma dawo na ya'yanki..?to baki isa ba malama kije ki Dubata la'asar nayi ki kamo Hanya,Gida ba kowa Badariya ta shiga makaranta Jamal baya garin nima yanzu da kika ganni Hajiya Barira nake jira zamu fita ban san da wa kike so su zauna ba..Kuma Allah na gani bazan soke fitata saboda ke ba"Ta karishe fada tana tabe baki daman ai nasan za'a rina sai kawai na mike ina yi mata sallama ta bi kulan Hannuna da kallo kafin tace"Ke ke..Wannan abun fa ina zaki kai shi..?
Sai nayi mata kamar ban ji ba kuma na jita naki juyowa ina ji tana fadin"Aikin kenan shiyasa kayan abinci ba sa wata suke karewa ga inda ake kwashewa ana kaiwa ashe "
Daganan na jita sauran mganganun nata ban ji ba Domin na fice daga Falon Idanuwana na kawo ruwa naji Nadaaman zuwa ma.
Sai dai na fita Hakkinsu daga ita har Yaya Ishaq din.
Ni da naso naje tun da Wuri sai gashi sai azahar na isa Karofi chan na fara zuwa saboda ban san d'akin da suke ba,Ina ko zuwa na iske Yaya Isa zai kai su Goggo da matarsa da Anty Nasara Goggo na ganina tace"Ga ma Fa'izan nan ta iso..Sai mu rankaya muma asibitin zamu"
Sama sama muka gaisa na shiga Mota sai asibitin General na Bakin asibiti Tamadina na Female ward ne babban Dakin Yaya mariya muka iske a wajenta da Maman isuhu sai matan ya'yan su.
Muka  gaggaisa da tambayan mai jiki sukace da sauki na Ubangiji.
Na kara rud'ewa da naga Tamadina kwance bata motsi numfashinta na sama sama alamun dai tana jin jiki na karisa gaban gadon na tsaya ina kallonta sai kuka na dafa Hannunta da ba karin ruwa ina fadin"Allah ya baki lafiya ta madina"
Goggo ce ta fara bani Hakuri sai na bar gaban gado nayi baya sai yau muka had'u da Yaya mariya tun bayan Tozarcin da Yaya ishaq yayi mata, kaina na kasa cikin jin nauyinta na gaisheta da Tambayan ya mai jiki tace da Sauki sai na sauke kulan Hannuna a gabanta ina fadin"Ga abinci"
Bata kalleni ba tace"Allah ya ba da Lada"
Bamu dade da zuwa ba Nurses suka zo suka fitar damu waje,muka fito baranda d'akin inda mutane ke zama masu jinya da masu Dubiya muma Tabarma Yaya mariya ta shimfida mana muka zauna Yaya Isa ya wuce wajen aikinsa.
Haka na zauna jugun jugum,sai da Yaya mariya tamin mganar salla,Sannan na tuna ban yi salla ba, na mike tace zata rakani masallaci Ahmad ya tashi Lokacin sai Maman Isuhu ta karbesa tace muje mu yi sallan mu dawo su za su yi nasu anan Tunda ga ruwa.
Yaya mariya ta dauko kwanukan da sukayi amfani da shi zataje chan ta wanke sai nayi saurin karb'a muka tafi ,Sallar muka fara yi sannan na yi wanke wanken,muka Dawo muka iske Maman Isuhu na bama Ahmad abinci Goggo ta kalleni tana Fad'in"Yaron nan naki rigimamme ne kuna tafiya ya fara mana rigima"
Ina dariya nace"Goggo har yaye fa kin masa..?
Goggo tace"Nasha rigima dai,don ma yana ganin idon Hafsatu ne. ita ai ya saba ganinta a gidan su"
Sai alokacin na tuna da Hafsah da na tambayeta sai Yaya mariya tace min sai ta taso makaranta zata zo.
Muna zaune ana ta hira sama sama duk rabin hiran na ciwon tamadina ne Maman isuhu tana fadin yadda ciwon ya fara daga zamewarta shikenan abu kamar wasa bata ko iya tashi komai sai an yi mata, suna mganar ni kuma ina faman share kwallah
Goggo tace"Abun ba dadi..Allah dai ya bata lafiya.."aka amsa da Ameen Goggo ke tambayana ashe Mama bata sanar dani ba..?nace bata gayamin ba Goggo ta jinjina kai kafin tace"Allah ya shirya Saudatu"
Yaya mariya na gefe tace"Itama karamar waya ya kamata a nema mata Goggo ace sai arika yin abubuwa mutum bai sani ba, yana chan shi kadai kamar wani mara gata da galihu"
Goggo tace"Haka Isa yace.bari dai komai ya daidaita bazai gagara ba"
Ana cikin tattaunawar ne sai ga Yaya Asiya ta diro ita da mijinta Dauke da kayan Dubiya katan din maltina da Ruwan gora,Ya duba jikin Tamadina bai jima ba ya bama Goggo dubu goma sannan yayi mana sallama ya tafi yana min tsiya da na gaishesa ya rike baki yana fadin"Wa nake gani kamar Fa'iza Asiya?
Tana dariya tace"Itace mana"
Sai kawai yace"Ke kan Fa'iza bakya zuwa ziyaran kano yaushe rabo na da ganinki..?
Goggo tace"Ai in dai Fa'iza ne haka take gidan kowa bata zuwa"
Bai tsawaita zencen ba ya karbi Ahmad yayi masa wasa yana tambayana Sauran yan'uwansa nace suna makaranta Dubu d'aya ya sama Ahmad a hannu kafin ya tafi Ya Asiya ta tafi rakasa.
Ni dai sai duba yanayin Rana nake yi Saboda la'asar nake son na tafi sai na kalli Yaya Asiya da ta dawo daga Rakiyar ina fadin"Don Allah karfe nawa..?
Yaya Asiya ta duba agogon wayarta kafin tace"Uku da rabi"
Sai na jinjina kai ba wanda dai yace wani abu sai da aka kira sallah mukaje mukayi sallah su Goggo kuma anan sukayi nasu sanda muka dawo an fara barin yan dubiya suna shiga D'akin.dukkanmu muka shige muna kara Duba jikin Tamadina ta nan a yadda take sai dai Numfashi,Bata ma sanin wanda ke kanta Yaya Asiya ta kalli Goggo tana fadin"Anya goggo bazamu sauya ma Tamadina asibiti ba..?
Ko dazu da naje raka babansu Usaini sai da yayi min zencen"
Goggo tace"To nima Isa ya cemin haka ammh ku bari an juma in megidan nasu ya zo sai muji ra'ayin shi"
Mganar Goggo yasa ba wanda ya kara mgana ni sai na zauna wajen kanta na sunkuya na rika karanta mata Fatiha da Suratul yasin sai Arrahaman goman Farko da ayatul kursiyu ina Tofamata a kanta zuwa kirjinta na dauki Wani Lokaci sannan na mike na rike Hannunta ina fadin"Allah ya baki lafiya Tamadina.."
Gabad'aya suka amsa min da Ameen sannan na sauke hannunta na gyara mata kanta saman filo na koma baya ina sharan kwallah Maman Isuhu na fadin"Sai hakuri..Allah zai bata lafiya"
Yaya Asiya da Yaya mariya suka hada baki wajen fadin"In sha Allahu"
Ahmad dake hannun Goggo na karba na goya Yaya mariya na ganin haka ta kalleni cikin wani yanayi kafin tace"Ba dai tafiya zaki yi ba Fa'iza..?
Sai na kasa bata amsa kaina na kasa nace"Tafiya zan yi sai gobe zan dawo tare da yaran gabadaya in sha Allahu"
Yaya mariya tace"Haka zaki tafi ki bar Mahaifiyarki cikin wannan Halin..?
In kafin Goben baki Dawo kin Tarar da ita da rai ba fa..?
Sai naji hankalina ya tashi Yaya Asiya ta daka ma Yaya mariya tsawa tana fadin"Haba Mariya wannan mganar bai kamata acikin wannan yanayin ba"
Goggo tace"To ban da abun mariya in ta zauna ai ba sauki zata saka mata ba..Ki barta tafi Dakinta ta kula da ya'yanta tunda gobe tace zata dawo..'
Yaya mariya sai ta juyar dakai ta fice Daga Dakin Tana fadin"Ai shikenan ta tafi..In ta rasu zata fi kowa kuka na sani Saboda itace kad'ai ta zabi miji da Danginsa fiye damu Ahalinta"
Sai kawai na Fashe da kuka Yaya Asiya ta kamani tana fadin"Daina kuka Fa'i haba Fa'i kamar baki san Halin mariya ba share hawayen ki,Ki tafi goben in Allah ya kaimu sai ki Dawo"
Na kalleta hawaye jage jage ina fadin"Ammh Tamadina bazata mutu ba ko..?zan zo na ganta ko..?
Har suna had'a baki da Goggo da Maman Isuhu wajen fadin Insha Allah sai na share hawayena nayi musu sallama goggo tace ina da kudin mota nace mata eh,har zan tafi Goggo tace na dawo na Dauki kulata tunda an juye abincin na koma na Dauka sannan na fice ina kara waiwayan ta madina.
A baranda naga Yaya mariya nayi mata sallama tayi banza dani bata amsa ba sai kawai na girgiza kai na wuce a bakin asibitin na Hadu da Hafsatu da kawayenta,muka gaisa tace har zan tafi nace mata eh sai gobe zan dawo mukayi sallama suka shige ni kuma na hau adaidaita zuwa inda zan hau motar katsina shida saura na yammah na isa gida ina sauka daga adaidaita Haruna na karisowa da su Amir sai da na sallami mai adaidaitan sannan na isa wajen su yaran suka sauko suka zo suka Rumgumeni nima na rikesu muka karisa wajen Haruna bayan mun gaisa yace min daga gidan Mama suke gidan ba kowa shine ya Dawo da su in ban dawo ba su zauna wajen Sa'adatu zai koma tunda bai tashi aiki ba..nayi mai godiya na tara ya'yana na bude gida muka shiga,Allah yasa  akwai sauran shinkafar da na Dafama Tamadina shi na basu suka fara ci kafin nayi musu girki..
Anum tace min"Umma kakanki ta warke..?
Sai ta bani Dariya na rikota jikina ina fadin"Ba kakata bace kakarku ce Anum ni mahaifiyata ce Mamana kum, kamar yadda kuke da Umma nima ina da Mama"
Sai tayi dariyan su na yara batayi mgana sai nice nace"Ta ji sauki gobe zan kai ku gaisheta kuna son zuwa.?
Suka amsa mim atare,nan dai nace musu gobe da su zan tafi Anum sarkin yawo tana ta murna ita da Musty Amir kuma daman bai da Hayaniya.
Taliya na yi mana mai miyar Jajjage mukaci da daddare kafin mu kwanta kamar yadda na sakama raina ban yi musu shirin makaranta ba Saboda na saka araina tare dasu zan tafi in ta kama na kwana ne bani da matsala.
Kafin takwas na safe duk mun shirya na Dibar musu kaya kala daya dukkansu Ahmad kuma Biyu a wata jaka da Babansu ya siya ma Amir mai girma kuma tana da Hannu aciki na Dura kayan,Buga get din haruna shi ya fitar dani na gayamasa bazasu samu zuwa makaranta ba Dutsemah zamu je tare yayi fatan samun sauki ga Tamadina ya wuce wajen sana'arsa.
Karfe tare muka fito na rufe gidan muka shiga nayi ma Sa'adatu sallama ta karbi address din asibitin tace zata yi ma Habiba mgana zasu zo in sha Allahu nace Allah ya yarda.
Ina da kudi dubu da wani abu a Hannuna zasu ishemu na Dawowa kuma bazasu gagaremu ba,Ni na zauna na dauki Anum da Musty a jikina Amir kuma nace ya zauna a inji saboda Saukin kud'in mota,goma da wani abu tama na a bakin asibiti ina Rike da Hannun Anum musty kuma Amir ne ya rikesa tunda d'ayan Hannuna na Riko Jaka muna tafe ruk'i ruk'i har Dakin da aka kwantar da Tamadina sai dai gabana yayi tsalle waje d'aya sanda naga ba itace bace akan gado sai ma wata mata da nagani.
Na rud'e dakyar na iya gaida gadon na kusa da Inda Tamadina ta kwanta. sannan na tambayesu mai gadon nan,Mara lafiyan na kwance bata mgana, masu jinyata ne guda biyu suka kalli juna in ban manta ba, jiya ma na gansu tare muka yi sallar La'asar da D'aya daga cikin su kamar daga sama mai kibar ciki tace"Ya ku ke da ita..?
Duk da sun ga kamannina da Tamadina cikin rawan baki nace"Ni yarta ce jiya ma ai nazo"
Kamar saukan aradu haka naji mganar"Ayya ai ta rasu yau da asuba kila ma an"
Bata karisa ba ta kusa da ita ta Rufe mata baki sai na kwalalo ido ina fadin"Eheee.."
Kamar ban ji ba sai naji lalurata tayi girma kunnuwana sun toshe bana jin komai Sama sama naji ana fadin"To ko ban gayamata ba,zata sani gwara taji tun yanzu"
Sai wata murya tana fadi'n"Ba haka ake fadin mutuwa ba sai ki barta in ta karisa gidan sai taji"
Ni dai bazan iya cewa ga yadda na iya fitowa daga asibitin nan ba, na dai tsinci kaina a bakin asibiti ina Shatatan Hawaye na manta da su Amir dake tare dani,Sai da naji muryan Amir yana fadin"Umma umma.."
Sannan na dawo hayyacina na juya ina kallon sun yi tsuru tsuru sai na Share hawayena na sunkunci musty na Saba ina rike da jakar kayanmu muryata shake nace"Amir rike ma Anum Hannu"
Gaba nayi ban tsaya bi ta kansu ba yau,ina dai jefa kafane kalaman Yaya mariya na dawomin da cewa in tamadina ta mutu sai nafi kowa kuka,Saboda Halin da nake ciki Tun daga Bakin asibiti har anguwan su Tamadina anguwan mallan yusuf Dutsemah a kasa muka je shi Anum ta gaji da kiran Umma ban ko amsa ta ba, nagaji bata kanta nake yi ba shi kanshi Amir din ya jigata ni kuma nafi su wahala ga Goyo da Musty ga Jaka ko da muka iso futu fitu kamar wad'anda suka fito daga Cirani kofar gidan cike da maza masu karban gaisuwa ni bana wani gani sosai ban iya gane  kowa ba ina gaba su Amir na bin bayana har Cikin gidan da Mata suke cike Damkam ni dai so nake na isa Dakin Tamadina na tabbatar da ta rasu ne ko wasa ne..?
Ban san me matan da na wuce a tsakar gidan suke fad'i ba sai da na Dangana da Dakin Tamadina naga Mutane zazzaune suna ta kuka Goggo na fara Hangowa tana ganina ta Dago tana fadin"Ga fa'izan ta iso ma ba ma sai Isan yaje Dauko ta ba"
Jakar Hannuna na Sauke tare da Musty na karisa gaban Goggo na Duka ina fadin"Goggo kada kice min da gaske ne abunda aka fadamin a asibiti wai Tamadina ta rasu..?
Ina mgana sai hawaye sharr Goggo ta rike kafadata tana fadin"Sai hakuri Fa'iza duk wani mai rai mamaci..Tamadina ta amsa kiran Mahallincinta yau da asuba basu jima da dawowa daga makabartan ba"
Ni dai naji ni na sulale jikin Goggo na fashe da wani kuka,Kukan da yasa Dakin ya rikice Ahmad dake baya na ya fara kuka jin na Dannesa haka ma Musty da Anum Amir ne kawai bai saka kuka ba Goggo ta jani ta sunce goyon ta Dauki Ahmad,Ya Asiya kuma ta mike tana sharan kwallah tana Fadin"Hafsatu riko Amir ga shi chan"
Dukkansu kukan suke yi ammh na zucci ta mike ta rikosa suka zo suka zauna sai ya kalleta yana fadin"Anty Hafsatu Maman Umman ce ta mutu.?
Sai ta gyada mai kai Lokaci d'aya ta Rumgumesa tana kuka.
Bansan adadin Lokacin da na Dauka ina kuka ba, nan da nan wani malolin abu yazo ya taremin makoshi ya kasa wucewa hakuri kawai su Goggo ke bamu Daga baya sai kuka na ya Dauke sai dai Tafarfasan zucci kawai.
Har washegari ban iya saka komai abakina ba Hafsatu ce ke ta Dawaniya da su Anum,Ahmad kuma yana Hannun Goggo har ta da su Yaya mariya sai da na dawo ina basu tausayi suka koma suna Lallashina naci wani abu Dakyar adaran na sha Farau Farau sai dai ko minti goma bai yi ba acikina na amayar da shi na koma ina Numfarfarshi
Bakina baya da wani Dand'ano ballatana na iya cin wani abu,sai Ranar Biyu da rasuwa na samu nasha Fura ya zauna acikina Mutane Dabam dabam sun zo gaisuwa Dangin mazajen su Yaya mariya da mazajen kansu,suna nan da su ake zaman gaisuwa hatta da yan makarantar su Hafsatu sun mata kara na zuwa da kuma kololin abincin su,Hatta da sauran dangin mu ta bangaran uwa suna nan tare damu,ammh ni ba Mijina ba Ahalinsa sai ranar uku sai ga Mama da Anty Binta sun zo da rana suna ta wani jin kai,ko awa d'aya basu yi ba sukace zasu tafi,Muna zaune adakin Tamadina dukkanmu,ni ina gefe kaina a jikin bango ina bin kowa da kallo Carbi ne a hannuna inaja Hijabin Yaya Asiya ne ajikina da shi nake kwana nake tashi wanka kuma tun da nazo ko sau daya ban yi ba.
Mama ta isa kusa dani tana fadin"Ai ya kamata ki koma gida hakanan saboda karatun yara sannan ki bar gida ba kowa kada a haura ayi sata."
Bata bani mamaki da kalamaanta ba, sai na kalleta da Jajayen idanuwana kafin nace"Aka rasa rai ma aka Hakura ballatana abun duniya..?
Na tsareta da idanuwana cikin wani yanayin da na tabbata bata ganina aciki ba.sai ta mike tana fadin"Rai ai da'ya ne, shi kuma asara ai suna da yawa"
Ban ce mata komai ba Anty Binta kuma ko ya Hakuri bata iya ce min ba nima ko ban gaisheta ba,sai dai naji tana Tambayan ina yaran..?
Naji Yaya Asiya na gaya musu Hafsatu ta shiga makota dasu tayi musu wanka,Da zasu tafi Mama bataji kunya ba tace Ishaq na yi mana gaisuwa Dayake basa kasar shi da Zainab.
sun je india a Duba Farhan Saboda Haushi Goggo ce kad'ai tayi fatan su dawo lafiya ni kuwa Idanuwana na Rufe naji wani Tiriri na fitowa daga  
k'asan raina,kaina ciwo yake yi har na bala'i ga jiri,nasan bani da lafiya. ammh halin da nake ciki ban ki nima ace na Mutum ba,da dai irin rayuwar da nike ciki wacce bata da wani amfani.

*Littafin KANA NAKA book2,3.paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*


*Janafty*
[6/24, 12:54 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

*Ina gaida Matar Abba,Maryam jumare.*
*Madalla da ke Hauwa'u(Real smasher)Fa'iza ta ce na gaishe ki*
*Fa'iza na gaida mai sunan k'anwarta Hafsah Hafnan,(Sahibatu) tace sannu da Himma.*
*Fa'iza ta ce na isar da sakon gaisuwarta ga uwar Dakin Gudayo da Yabi,tace madallah da kawar kirki irin ki Surayya Dahiru gwaram.*

*Ishaq na gaida Ahalin Masoyansa gabad'aya,yace na Fada muku. ya ji duk zagin sa da kuke yi groups groups,Har da masu sauya masa suna wai Isiya,Yace kwa yi ku gama shi da Fa'iza mutu ka raba takalmin kaza.*

*JANAFTY NA GAIDA MASOYANTA
MASU AIKO MIN DA SAKO GA FA'IZA DUK NA ISAR DA SAKON KU,TAJI KUMA TACE TA D'AUKA IN SHA ALLAHU ZATA MIKE TA TAIMAKI KANTA*

        *🅿️17*

Ranar da akayi addu'ar bakwai da Daddare,aka taramu saboda washegari zamu watse. kowacce zata koma gidan mijinta,Cikin taron har da Megidan Tamadina da abokan zamanta. sai manyan ya'yan gidan maza,sai mu sai Goggo da Baba Ati kamar kaka take wajen Tamadina ita kad'ai ta rage acikin dangin mahaifinsu da na mahaifiya tunda daman auran zumunci ne tsakanin iyayan nasu..
Bayan bude taro da addu'a da yi ma Mamaciyar addu'a sai d'an nasiha garemu na hakuri da rayuwa,duk yadda tazo ma bawa sai kuma aka gangarowa mgana kan abunda ta bari na magada.mu kenan to da yake bata bar wani abu ba,sai yan kayanta da gado da Sauran tarkace nan take kuma mukace mun yafe a raba ma bakuta,suka shiga saka mana albarka Megidan su ya ce Tamadina tun iya zaman da yayi da ita, bata taba sab'a mai da gangan ba,saboda haka ya yafe mata duniya da Lahira,haka Sauran abokan zamanta suke ta fad'in alherinta suna fadi'n bata yi musu komai ba mace mai kirki da son zaman  lafiya,Daga karshe Yaya mariya ta muskuta tana kallo Goggo Lokaci d'aya tana fadin"Goggo ya mganar bashi.shin ko sun san ana binta a bashi Saboda a biya a sauke mata nauyi..?
Maman isuhu ta kad'a baki tun kafin Goggo tace wani abu tace'"Allah ya jikan Tamadina ba mace bace mai cin bashi ba,ga yara nan duk sai su tsallakemu su kawo mata ajiyan kudadensu,wlh yadda suka bata haka suke karb'an su ko chanzasu batayi.bata taba cin bashi ba,macece mai godiyar Allah da Wadatar zucci"
Gabad'ayan mu dad'in wannan yabon mukaji,har sai da hakan ya nuna a saman fuskar mu,an tashi taron cike godiya da fatan Allah ya jikan Tamadina bayan Goggo ta sanar da Mutan gidan gobe zamu koma gidajenmu suka nuna alhininsu.
Bayan mutan gidan sun fice suka bar mu, mu kadai Ni ina gefe nayi tagumi bana mgana Amir ne kadai bai yi barci ba yana jikin Hafsatu,Yaya mariya ce da Yaya Asiya ke ta zencen su da Goggo da Baba Ati acikin Hiran ne Yaya Asiya tace"Baba Ati wai har yanzu ba'a samu labarin inda Dan'uwan Tamadina yake ba..?
Baba Ati ta sauke Numfashi kafin tace"Ke dai bari Asiya wlh ba'a samu ba.Kwanaki har chan karayen naje da muka kai yar gidan mallam Akilu aure chan. aka tabbatar min sun tashi sun koma cikin garin kano hannun wani Dan'uwan ita Zuwairan"
Yaya mariya tace"kuma babu lambar waya Baba Ati..?
Ta jinjina kai kafin tace"Gaskiya babu..Ai tun lokacin zamanta a korafi batayi dogon Huld'a da kowa ba Zaman nasu ma da mahaifiyar Tamadina kakar ku kenan ba dadi gaskiya har da shi Mallam din saboda bata so auran ba,mahaifinta ya had'a abun akwai wanda take so shiyasa sanda aka kawota batayi huld'a da kowa ba,ko Haihuwar Usman din Rabo ne kawai da ya rantse yasa aka samar dashi.
Sai kuma mallam din yazo ya rasu.to bayan ta fita Takaba,Danginta suka zo tafiya da ita.sai ta nuna zata tafi dashi to rayuwar nan ba wanda ya damu da rikon D'an da ba nasa ba, saboda ganin Nauyi ne in ma ta barsa anan d'in shiyasa ba Gaddama akace zata iya tafiya da shi Har ga Allah na zata zata rika kawosa ko don yar'uwansa da suka Had'a uba sai kuma gashi Tunda ta saka kafa ta bar Karofi yau shekaru sama da Arba'in da Doriya bata Dawo ba.sannan shima Usman din bai nemi Dangim mahaifinsa ba har yau din nan kuwa"
Ba kuma wanda yasan inda suke ahalin yanzu"
Gabad'ayan mu muka sauke Numfashi Yaya Asiya tace"To Allah yasa yana raye"
Yaya mariya tace"In sha Allahu ma yana Raye kuma in dai da rai da rabo watarana zamu had'u da shi"
Muka amsa gabadayan mu da Allah yasa Goggo ta gyara zama tana fadin"Duk inda yake in dai jinin ku ne zai nemeku jini ai ba karya ba ne".
Muka jinjina mata kai alamun gamsuwa ni ko araina sai na samu kaina da addu'an Allah yasa yana raye domin shi kad'ai ne shakikin Tamadina anan duniya mu kuma kawun mu Namiji kwara d'aya tak da yau zamu bugi kirji muce muna da shi acikin raina ina addu'an in dai yana raye Allah ya bayyana sa da gaggawa.
Washegari da shirin tafiya muka tashi. kowa kagani da Kuzarinsa ban da ni,kwata kwata kamar an zaremin lakkan jikina,Goggo sai fad'a take min wai na kwazzabi kaina bana cin abinci Yaya mariya na wajen tace"Kuma zama da yunwa bazai taba Sauya komai ba..Tamadina ta rasu sai dai mu yi fatan Allah yasa tana kyakyawan karshe"
Sai hawaye ya kecemin suka shiga tsere bisa kumatuna, bayan mutuwar da ta dake ni,yayi sanadiyar tasomin da ciwona da daman kamar jira yake na shiga hali makamancin sa,Mun had'a duka kayanmu na yara Hafsatu ta wanke musu ta had'a musu ta musu wanka,ta shiryasu haka ma su Yaya mariya sai kuma sabon kuka ya tashi muka zauna mu hud'u muka ci kukan mu muka koshi,muka share Hawayen mu. Goggo tagaji da bamu baki ta Hakura ta koma gefe ta zuba mana ido bayan ta kira Yaya Isa tace yazo ya Dauketa ita da Hafsatu da mariya da Baba Ati, Yaya Asiya kano zata wuce nima kuma gidana zan koma.
Da azahar sai ga Hajiyar Dala,mun dauka ma bazata zo ba ne ahalin taji Rasuwar. tunda Goggo da kanta ta kira wayar ta,ta fad'a mata,Tazo tayi mana gaisuwa ta bama Yaya Asiya dubu goma Sadaka batayi awa d'aya ba,Ta ce zata tafi, nan take zencen zata karisa katsina Tare da Direba take jin Haka yasa Goggo ta kalleni tana fadin"Fa'iza tunda kun gama shiri,sai ki bi goggon taki tunda katsinar zata shiga"
Da Sauri tace"Aa ba gidan Saudatu zani fa gidan Wani abokin Major ne. mahaifiyarsa ta rasu zan biya nayi musu gaisuwa suma na wuce"
Ina jin haka nima murya a sanyaye nace"Ki bari kawai Goggo zan tafi da kaina"
Sai goggo ta jinjina kai kafin tace"Shikenan"
Daga haka tayi mana Sallama tatafi Goggo ce ta rakata har Dakunan matan gidan tayi musu gaisuwa, kafin Tafiyarta sai da ta dawo sannan Yaya Asiya ta bata kudin da Hajiyar Dala ta bata Goggo ta karb'a tana fadin"Kudin ku ne ai Asiya ba ni aka bawa ba"
Yaya Asiya tace"Goggo mu bama bukata ayi sadaka Allah ya kai Haske kabarin mahaifiyarmu"
Goggo ta amsa da Ameen itama fita tayi da kudin Dakin Maman isuhu ta shiga ta bata kudin Dakyar ta karba, Goggo tace kun yi wahala damu wajen kwana takwas ku karba ku kara Allah ya Rufa asiri .sannan ta karb'a tana sharan kwallah da kara fadin Allah ya jikan Tamadina.
Yaya Isa ya kira yace gashi nan zuwa,Shinkafa suka dafa mutam gidan suka zubo mana yaran aka zuba mawa suna ci ni dai bakina yayi nauyin  bana jin Dad'in komai kaina wani Dum dum kawai yake yi duniyar ma ba daidai nake jinta ba.
Kwatsam sai gasu Sa'adatu da Habiba sun zo min gaisuwa nayi mamakin zuwan su sai da aka gama gaisawa sannan na kalle su ina fadin"A ina kukaji rasuwar sannan waya kwatanta muku gidan nan..?
Sa'adatu tace"Ai tun da naga an kwana biyu baki dawo ba nace ba Lafiya Megidan ma nata jimamin abun.  yace haka kurum bazaki je ki zauna ba ko don makaranta yara da muka ga an yi kwana biyu sai yace bari yaje gidan kakaninsu su Amir yaji ko Lafiya. to chan yaji abunda ya faru wajen kanwar Baban su Amir ce domin ina ganinta tana zuwa itace ta fad'amai mahaifiyarki ta rasu sai ya Nemi ta kwantatamai gidan nan sai ta mai kwantance mun d'an sha wuya kafin mu gane,sai dai kinsan gidan mutuwa baya boyuwa balle da naga ba'a gane ba sai na rika kwantance da cewa Bebiya bata mgana sai ko gashi an kawo mu"
Na jinjina kaina,kwallah na Taruwa acikin idona makota na ne da ban had'a komai da su ba,Ammh sun nemi inda nake sun zo min gaisuwa Su mama kuwa tun ranar uku basu dawo ba,bana saka ma Yaya Ishaq a lissafi bai Dauke ni da Daraja ba,ballataana ya Dauki dangina da iyayena abun Daraja Har afili na nuna musu jin Dadi'na na nuna su ga sauran yan'uwana da Goggo suka dinga saka albarka har da gurasa Habiba tazo da shi ita kuma Sa'adatu sai ta Dafo Dambun Shinkafa da yaji Zogale Goggo ta karba ta kai ma Mutun gidan suna fad'in Allah ya bada Lada
A nan suka yi sallar La'asar sannan suka yi shirin tafiya sai nace su jirani mu wuce tare Lokacin Yaya Isa ya iso ya tafi masallaci ne,na mike na shiga uwar Dakin Tamadina na Dauko jakar kayan mu da Hijabina.da Yaya Asiya ta wankemim Goggo ta matsamin nayi wanka da Safe na fito falo na ce Hafsatu tazo ta sakamin Ahmad a bayana na goyasa ta sakamin shi har na saka zani na goyasa irin na D'ago kaina sai Duhu ya mamaye ganina na fara Laluban bangon gabana na rasa sai nayi luu ta baya zan fad'i sai  naji an tareni ana salati kuma hannuwana ne da yawa suka rikeni,Sama sama nake jinsu jiri ya rikeni da kaina da ya dauki wani irin azaban ciwo,Kamani sukayi na zauna Yaya mariya ta kwanto goyon Bayana Goggo fad'i take"Daman ni nasan yarinyar nan bata da lafiya, shigen zurfin cikinta yasa taki mgana"
Asiya kira min Isa yayi maza yazo in asibiti zai kaita ya kaita kada ta yi ma kanta Lahani bamu sani ba"
Ina nan zaune Dafe da kaina ina jin Sannu sannu na tashi Daga bangarori Dadama, chan jimawa na zame na kwanta naji shigowar Yaya Isa da Bayanin da Goggo take yi masa,sai yace a kamo ni muje asibiti a dubani.
Yaya mariya ta kamani muka fita mutan gidan na tambayan lafiya tace jiri ne ya kwasheni Maman isuhu tace"Daman daga ganinta bata cika lafiya ba itama"
Ni dai ina jinsu har muka fice muka shiga mota wani asibitin kud'i acikin gari ya kaimu shi ya shiga ya fita muka ga likita akan Lokaci gwajin Farko sai ga jini na ya yi sama Dari Biyu da Doriya sai ucler likitan nata fada ina so na kashe kaina da na fadi zan iya kamuwa da Ciwon barin jiki, ko jini ya haye yayi sama na mutu mgunguna ya bani bayan yayi min alluran jijiya ta ucler sannan yace na rika cin abinci sosai saboda kiyaye lafiyata.
Muna hanyar Dawowa Yaya Isa sai fad'a yake yi,Yaya mariya bata mgana sai dai kawai ta sauke numfashi tace"Uhm" abun yafi karfin ta wannan karon ko da muka koma makotana sun tafi sun so su jira dawowarmu Goggo tace su tafi Saboda Dare sannan sun bar iyalansu agida to sanadin haka komawa Katsina bata yuyu ba da Goggo ta kawo mganar Yaya isa ya maidani sai yace"Haba Goggo kalli Halin da take ciki fa..?,jininta yafi dari biyu a yadda take nan ko kanta bazata iya mora ba ballatana ga yara tare da ita,kawai mu wuce da ita gida in taji sauki sai ta koma"
Sai Goggo ta kasa musamai saboda taga Halin da nake ciki,Ni a motar Yaya isa muka tafi ni da Goggo da Baba Ati da yara su Yaya mariya da yaya Asiya da itama tafiya kano tasha ruwa suka hau ta haya mun yi sallama da mutanen gida muka rabu suna Hawaye muma muna yi.
Sai dare muka isa karofi ni dai abinci suka matsamin naci, nasha mgani na kwanta barci. Salolli na ma sai da asuba na rama su na ji saukin Jirin sai dai ciwon kan ne,Washegari Yaya Asiya ta koma kano Yaya mariya daman muna isowa ta wuce gidanta
Wasa wasa jikina ya ki dad'i har sai da na kara Sati a karofi Goggo na kula da ni,tare da su Amir kamar kada na koma inda na fito sai dai ba Dama ranar da nake da kwana bakwai a karofi Goggo ta saka Yaya isa ya maidani da Yammah bayan taga naji sauki,Tare da sha tara na arziki komai ta had'amin su garin kunu,garin Danwake,Wake,Tsaki,rama bushasshiya da Zogale sai Taliya yar Hausa da yara suke so sai ta saka aka Murzamin ta samin a kwali saboda kada ta karye hatta kayan maggi sai ta siyamin,da kayan miya mai yawa sannan ta saka Yaya isa ya kaini har gida ni da yara ina ta masa godiya shima da ya saukeni ya bani dubi biyar yace na rike sannan ya Jadaddamin naa kula da lafiyata na amsa mai da in sha Allahu.
Gyaran gidan na fara ko'ina duk yayi kura,Amir na tayani da kwashe kaya su Anum kuma sai dai su kara batawa,Adaran Taliya yar murji na Dafa mana na manja mai ruwa ruwa muka ci tare a faranti daya muma Santi muna gamawa bayan mun yi sallah na saka suka kwaso littafan makarantansu nace su duba tunda gobe zasu koma makaranta.
Wasahegari Laraba da wuri na shiryasu na kuma fita da su da kaina,Haruna da Sa'adatu da na leka gidan suka karamin gaisuwa da tambayan ya karfin jikina..?nace naji sauki sai hamdalar ubangiji.
Makota na dake kusa dani wad'anda ban taba ma shiga gidajen su ba sun shigo sun min gaisuwa daga suce Sa'adatu ta fad'a musu ko Habiba naji Dadi Sosai domin ba karamin masoyin ka ba ne zakayi rashin uwa yazo yace maka Allah ya kara hakuri kuma bazaka manta da wannan mutumin ba, wanda kuma bai ce maka Allah ya kara Hakuri ba,shima girman abunda ya aikata yana nan acikin ranka bazaka taba mantawa dashi ba.
Na dawo da kwana Biyu Anty Mamah tazo min gaisuwa tace ta zo sau biyu bana nan,nace mata eh nayi rashin lafiya ne tayi min gaisuwa ta kuma bani Hakurin sun yi tafiya ne chan dangin megidanta Kumo dake jahar Gombe ta jima muna ta Hira sai la'asar tatafi bayan nayi mana Danwake da manja da yaji taci ta koshi,sannan mukayi sallama washegari kuma daga makaranta Sai ga Badariya tazo min gaisuwa itama da ban hakura Mama bata nan bikin D'iyar Hajiya Barira k'awarta tatafi wajen satin ta daya Abuja aka kai Amarya, dagachan ta biya gidan su Zainab ta kwana biyu.
Sai kawai na samu kaina da cema Badariya"Sun dawo ne..?ya mai jiki..?
Badariya tace"Basu dawo ba suna chan jikin Farhan da sauki sun dai Tsaya Hutawar su kawai"
A fili nace"Allah ya dawo da su lafiya"
Daganan ban kara tofawa ba,Bata jima ba ta tafi tace saboda Mama yanzu in taga ta Dad'e sai ta fara fada, nace gaskiya kam ya kamata ta tafin kada dare yayi mata.
Mutuwar Tamadina ta Dakeni matuka,sai dai na zauna nayi Tagumi ina sharan kwallah in Amir yaga nayi Tagumi sai ya cire tagumin yana fadin"Umma ki daina tagumi ummanki zata dawo"
Sai ya bani dariya na jawosa jikina ina fadin"Aa bazata dawo ba Amir..Ai kasan mutuwa ko.?kuma a makaranta an fad'a muku duk wanda ya mutu ai baya Dawowa a rami za'a ha'ka a binnesa shikenan bazamu kara ganinsa ba"
Cikin yanayin mganar sa yace"Ita Umman ki a rami aka sakata..?
Sai na gyad'a mai kai Lokaci d'aya ina fadin"Eh mana..kowa zai mutu muma watarana zamu mutu a hak'a rami a binne mu baza'a sake ganinmu.Mu yi ma wadan'da suka rigamu mutuwa addu'a muma in mun mutu sai mu samu masu yi mana addu'a"
Ya gyad'a min kai kafin yace"To Umma zan rika yi ma umman ki addu'a"
Daman kuma ina yawan fad'a musu in sukayi sallan su rika cewa Allah ya gafartama iyayanmu da magabatanmu da yan'uwanmu,kuma suna yi,Har su Anum haka na koya musu nima in dai na yi sallah sai na Roki Allah ya jikan dukkan yan'uwa musulmai da suka rigamu gidan gaskiya mu kuma Allah yasa in tamu tazo mu samu cikawa dakyau da imani.
An yi addu'ar Arba'in Tamadina,Ni ban je ba Hakama Yaya Asiya su Goggo ne da Yaya mariya suka koma sai dai daga gida nayi mata addu'a da Sadakan Allah yakai haske kabarinta na Rokar mata salama da amimci a wajen Ubangiji a kabarinta,Ni tunda Tamadina ta rasu komai ya fita kaina naji bakowani wani abu ne zai rika batamin rai ba,Na riga nasan na rasa dukkan wani bangare na jin Dadi, Dariyata kadai ya'yana ke gan. sune kad'ai yasa har yau nake tsaye kan kafafuwana,Saboda hakane yasa na Dage da shan mgunguna saboda in nazo na kasa ko nayi Rauni ya'yana baza su iya d'aukan maraici tun suna da kananun shekaru ba. shiyasa karfina da Kuzarina duk Ta dalilinsu ne shiyasa ita uwa ya'yanta kan zama gwarin gwiwanta sau da dama.
Kwata kwata nama manta da mganar Form din da na cike na koyan sana'o'i da bada tallafi,na mikama Allah duka al'amarina,sai kwatsam Badariya tazomin da labarin an Turo mata sako Daga Kungiyar Women charity Foundation kan zasu tantancemu ranar asabar karfe goma na Safe a wata makarantar yan mata Dake cikin gari sai na rud'e na fara rawan jiki ina fadin"Bada..riya..To ni ya zan yi..?bansan ko'ina ba fa..?
Sai tayi Dariya tace"Sha kurum ki zan yi ma Mama karyan makaranta sai nazo na rakaki"
Sai da ta fad'i haka sai hankalina ya kwanta, tun daga ranar ko dayaushe addu'ata d'ayane in da alheri acikin wannan mafitan. Allah ya tabbatar min in ba alheri Allah ya musanya min da mafi alheri.
Sai naji zuciyata ta natsu da al'amarin,Ranar jumma'a Dakyar na iya barci Saboda Zullumin abunda zai faru gobe,Da sassaafe na shirya yara suka wuce Tahfeez nima ban zauna ba na shirya tara da wani abu Badariya tazo na goya Ahmad na saka Dogon hijiba na mai ruwan kasa duk yasha ruwa na rufe gida muka tafi,Ita ta biya kudin adaidaita gaskiya akwai tafiya ba kad'an ba tsakanin gidana da Makarantar mun isa goma saura Haraban makarantar cike da manyan motoci daga gani abun na manyan mata ne.
A wani babban hall na makaranta ake taruwa kai tsaye muka nufi chan mun shiga mun tarar da mata da yawa duk sunzo,muka samu waje muka zauna ina ta raba ido sai da goman tayi sannan Manya mata masu nasaba da ilimi da zati suka rika shigowa suka tsaya a gabanmu, ina ji Badariya namin Rad'a mai bakin mayafi mai jikan nan Hajiyar su Raliya ce na jinjina kaina daga gani kudi da isa sun zauna ajikinsu
A she mu Talatin suka Dauka,Bayan sun kira sunayen kowa da kowa muka mike gabad'ayamu akwai yan rakiya ire iren Badariya,Wata Hajiya ce mai glass take kiran sunaayenmu,na kasa Raunanun kunnuwa a ina jin sunana na mike bayan Badariya ta rike hannuna muka mike tare sannan ta koma ta zauna, ashe Wani kati zasu raba na na shedar Training d'in da zamu yi sannan da wasu bayanan da suka danganci abunda za'a koyar damu.
D'aya bayan d'aya aka rika kiranmu ana bamu wani karamin kati mai dan Fad'i.sannan akwai hoton kowacce ajikin katin har akazo kaina,na mike na kwanto ma Badariya Ahmad dake bayana na fita ina raba ido har gaban Babban ajin na mika hannu na karb'a ta kara kallona sama da kasa har na juya sai ta kirani da fadin sunana"Fa'iza Sidi karofi'
Sai na juyo da Sauri saboda ina gabda ita naji ta fad'i sunana yasa Hajiyar su Raliya ta D'ago tana kallona sai na rankwafa na gaisheta da girmamawa sai ta amsa itama cikin sakewa Lokaci daya tana fadin"Kece matar Brother din Badar..?
Sai na gyad'a mata kai cikin yanayi mganata nace"Eh hajiya tare..tare ma muke da ita"
Sai na juya ina nuna mata Badariya ashe har tataso dauke da Ahmad tazo wajen mu,Ta duka ta gaida Hajiyar Raliya ta amsa tana tambayanta Mama tace tana lafiya sai ta kara kallona tana fadin"Ashe tare kuka zo..?
Badariya tace"Na rakota ne Hajiya"
Kai ta jinjina tana kara kallona nasan har da mamakin ganin yanayina sai matar nan mai glass ta duko tana mata mgana naga tana nuna mata Takardan hannunta sai ta amsa tana Dubawa kafin tace"Fa'iza abu hud'u zaki koya..?kuma a ka'ida biyu ne kina ganin zaki iya..?
Da Sauri nace"Eh zan iya Hajiya.."
Sai dayan Matar tace"Hajiya kinsan dokace Biyu ne ai hudu yayi mata yawa da wanne zataji..?
Sai naga ta duka daidai kunnenta tana yi mata mgana sannan ta jinjina kai,Itama kuma Hajiyar Raliya sai tace muje mu zauna.
Komawa mukayi muka zauna ina ta Raba ido,naga mata kala kala ire irena masu fama da rayuwa da zamantakewar aure,ni dai akasan raina ina jin yakinin zan koyi duka abunda za'a koyamin Saboda shi kad'ai nake ganin gatana a wannan duniyan.
Bayan an gama bawa kowacce Katin ta, sannan suka fara mana bayanin yadda abubuwa zasu kasance zamu fara koyan abubuwan da zasu koyamana nan da sati d'aya zasu raba abun gida Biyu Mrning da Aftternoom,Da Safe za'a koyar da abubuwa Biyar da yammah ma biyar daman goma ne,Da Safe za'a koyar da girke girke da Had'a lemuka,Da yammah akwai koyan yadda ake hada halawa da dilka,Da yadda ake yinta,Da had'a Turaren wuta na Icce da Humra da su Kwallaca,sai na fara nazarin ya abubuwa na zasu kasance..?kenan sai dai na rika zuwa safe da yammah kenan..?
Sannan sun yi mana bayanin awa Bibbiyu ne da Safe tara zuwa sha Daya da Yammah D'aya na rana zuwa uku na yammah,sannan sun bamu shawaran mu natsu zamu iya duka abunda za'a koyar damu tunda na wata uku ne tsawon sati goma sha Biyu ina jin duk abunda suke fad'i Saboda da karfi suke mgana kamar su san da masu Laluran rashin karfi ji irina.
Sun tabbatar mana da cewa acikin mu za'a dibi mutane goma masu hazaka da aka ga sun chanchanta ranar da zamu gama za'a basu Jarin su a Hannunsu,sannan sun horemu da mu maida hankali komai daki Daki zasu koyamana duk abunda bamu gane ba mu yi tambaya. kada mu zama masu duhun kai,Sannan daga karshe sun ce zamu rika zuwa da Littafi da biro mu rika rubuta sunayen abubuwan da za'a koyamana saboda in mun koma gida mu yi bita,Sannan zamu rika rubuta sunanmu kullum inda muka zo da Turanci wato Attendence.
Sannan ko da wani lokaci zamu rik'a zuwa da wannan katin shine shaidar an tantance mu sai mun nunasa za'a barmu mu shiga, zuciyata na cika da Farinciki har na fara tunanin ma na iya duka abunda nasaka raina zan koya,ajikin katina  an saka Abunda nake son koya kamar yadda Badariya ta Rubuta, shi zai nuna inda ya kamata na tsaya sai Sha biyu  na rana aka tashi sun tabbatar mana da cewa kwararun ma'aikata ne zasu jagoranci wannan tafiya tamu mun yi godiya sosai sukace mu yi ma shugabar wannan kungiyar addu'a da fatan nasara Rayuwa, ni ko araina nace duk Sallah sai na sakata nace Allah ya yi mata gatan Duniya da lahira kamar yadda itama tayi mana gata a duniya.
Daga nan muka rabu da Badariya ta taremin adaidaita na Dawo gida zuciya ta cike da Farinciki,Sai dai na Fara Tunanin inda Zan rika kai Ahmad Saboda sun ce ban da yara saboda ba wajen da yara zasu zo ba ne,akwai abubuwan da bai kamata yara su shakesa ba yayin had'asa.
Sa'adatu ta fadomin rai nako shiga na gayamata ta tayani murna ta kuma tabbatar min na rika barin mata Ahmad zata kular min da shi sai naji Sauki na Dauki damaran maida Hankalina kan damar da Allah ya aramin,Naji dadi tun Sha daya zan dawo gida nayi ma yara girki ko na kimtsa gida da la'asar kuma in na Dawo sai naji da girkin su kafin su dawo makaranta.
Har wankin yaran sai da na kwashe na wanke na goge tare da nawa tunda zan fara fita ba lalle na rika samun Lokaci ba,Ranar Alhamis saura kwana biyu a fara koyar damu Yaya Ishaq ya dawo da Safe na sallami yara sun tafi makaranta kenan ina zaune afalo ina bama Ahmad kuninsa ya shigo ban ko ji sallamansa ba ina chan ina Lissafin duniya.
Sai da ya kariso cikin falon ya kara yin sallama sannan na jisa,na d'ago na kallesa,kamar ba shi ba ya kara Kiba har da karin Saje da gemu ga Tumbi alamun yana samun hutu da jin Dadi.
Kamar bakina na ciwo nayi mai sannu da zuwa bayan na kauda kaina.
Ahmad kuma sai ya fara dagamai hannu yana gaurancinsa.
Bakinsa na gogemai da Kyallen dake gefena shi kuma sai ya Duka ya Dagasa sama bayan ya sauke jakar Hannunsa, mikewa nayi ina kakkabe jikina zan wuce dakina araina ina fadin ka dawo adaidai kuwa.
Sai dai ban karisa ba ya D'aga murya kirani na juyo cikin mganarsa yace"Kin yi min sannu da zuwa baki dauki kayana kin kai min ciki ba.kuma zaki wuce ni kamar kin ga wani banza Fa'iza..?
Sai ban damu da kalamansa ba na koma na Dauki Jakar ya mike ina gaba yana baya ya bude shashen nasa. muka shiga a tsakiyar falon na Dire masa jakarsa na juya naji ajikina ya Juyo yana kallona ammh ban tsaya ba,Sai dai kuma har na fice bai yi mgana ba,dakina na koma na shiga kakkabewa ina gyarawa da na gama na koma Dakin yaran ina tattara kayansu da suka zubar ni kad'ai a araina ina auna abunda zan fad'a ma Yaya Ishaq akan fitar da zan rikayi araina naji wannan karon bazan iya Laushin da na saba yi mai ba.
Ina da Dakin yara naji yana ta kiran sunana da karfi na fito na iskesa zaune afalo Ahmad na jikinsa yayi barci a bakin kofa na tsaya ina jiran cewarsa sai ya kalleni cikin mamaki yana fadin"Kika tsaya min a nan kuma..?
Sai na kariso tsakiyar falon na Tsaya sai da yaga dama sannan yace"Ba wani abu ne agidan..?
Sai kai tsaye nace"Kamar na me..?
Da mamaki ya D'ago yana kallona cikin Hargaginsa yace"Ban sani ba..Wannan wani irin tambaya ne? tunda kikaji nace wani abu ina mgana kan abin ci ne"
Ni kaina bansan meyasa yanzu shakkanan da tsoron Yaya Ishaq suka Fita daga raina ba ,cikin Yanayina nace"Oh gaskiya bakomai sai ruwa Danwake nayi ma yara suka tafi makaranta dashi"
Wani kallon mamaki yake bi na da shi, mamakina ya hanasa mgana ni ko na shiga kitchen na Zubo masa Ruwan Famfom da ya bar mu muna sha,Na kawo mai a karamin jug da kofin Roba duk yaji jiki shi gareni saboda aciki zan basa araina kuma nace bazan Dafa maka komai ba domin bansan da zuwan ka ba.
Gabansa na duka na Sauke ruwan na kuma tsiyayamai na mikamasa sai yaki karba ya bini da kallo kafin yace"wannan ruwan fa..?
Ba na gora ba pure water ne..?
Kai tsaye nace"Babu muma wannan muke sha tun ba yau ba"
Sai jikinsa yayi sanyi cikin wani yanayi yace"Acikin Cefane babu ruwa ne yanzu..?
Nace "Babu.." daganan na sauke Kofin hannuna ganin yaki karb'a ina shirin tashi naji yace"Ashe Kuma Babarku ta rasu..?muna chan Mama ke fadamim..?
Kallon da nayi masa zan iya rantsuwa da Allah ban taba masa makwancinsa ba,da muka kusa shekara goma da Aure,Idanuwana na tsaida a kansa bako kyaftawa cikin wani irin amo nace"au ashe ne ma..?baka tabbatar ba kenan..?
Sai yayi saurin cewa"Kinga ba na son korafi Allah ya jikanta da rahma"
Da karfi na amsa da ameen Ameen Saboda addu'a yayi a gaban idonsa na Dauke Ahmad na shige da shi na Shimfidar na koma na zauna a gefensa ina auna waye yaya ishaq a wajena a tsawon wad'anan shekarun da muka dauka tare..?abu daya ya taba bani da zan kallah naji dad'i shine ya maidani Uwa ya bani ya'ya bayan wannan sai Tarin Tozarci cin mutumci kaskanci da Sauke Daraja da na Fuskanta a zama na dashi.
Ishaq shine sanadiyar da aure ya gama fita daga raina kwata kwata.

*Littafin KANA NAKA book2,3.paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*

*Janafty*
[6/24, 6:53 PM] +234 808 711 8630: *KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

*Gaisuwar Fatan alheri ga iyayen Janafty*

*Anty Habiba Abubakar Imam ikra*
*Anty Summayyah Abdulkadir(Takori)*
*Hajiya Hadiza Mahe muhammad(Mama)*
*Hajiya Halima Dalha Shehu(Umma)*
*Hajiya Hauwa Maman unwas(Mommah)*
*Na gaishe ku,Madallah da iyaye kamar ku,Allah yasa a gama da duniya lafiya Ameen*

         *🅿️18*

Na dauki tsawon lokaci aciki kafin na fito,domin nima sama sama barcin ne ya fara fizgata.ko da na fito falo baya nan, da na leka haraban gidan ba motarsa. sai hakan ya bani tabbacin fitarsa kenan ya tafi gidan Mama. domin ba inda yake zuwa da wuce wajenta,ko Anty Binta sun fi mgana ta waya ko su hadu gidan Maman.
Ban damu ba na cigaba da Harkokina, na riga na saka ma kaina yak'inin Tunda har ya zab'i iyalan zainab sama da nawa iyalan nima zan zab'i ra'ayina da ya'yana sama da shi mu ma Ture mganar aure a tsakanin mu sai dai a duba zumuncin da Allah ya riga ya had'a ,kuma shi sada zumunci Umarnin Ubangijine kuma shi Umarnin Ubangiji sab'a masa babban Laifi ne.
Haka kurum naji ina sha'awar shan Faten Rama ina da sauran tsaki tun wanda na dawo dashi daga Karofi shi na Tankad'e na wanke na d'ora sannan na Jika bushasshiyar Rama nayi amfani Dashi bani da nama ko kifi sai nayi amfani da wake na watsa musu aciki,sai Faten yayi dad'i yana tashin kamshin kayan miya da Daddawa da su Citta,na juye a kula ni saboda bazan iya jiran yaran ba, sai da na Dib'i nawa muka sha ni da Ahmad sannan na sake yi mai wanka nima nayi muka sauya kaya shidda Saura yaran suka Dawo daga makaranta suka cire Kayan makaranta, suka sauya na gida sannan na zubo musu faten a faranti suka na suna santi,bayan sun gama Anum ta fara min labarin makaranta Musty kuma sai wasan zagayen falon yake yi Amir kuma kan kujera ya hau yana Duba Littafansa.
Anum wasa da kaina take yi,kalaba ne daman har ya kusa warware kansa ma, domin ni nayi ma kaina.Ahmad kuma na daka Tsalle saman jikina Amir yace"Umma ki dubamin aikin nan ban gane ba..?
Ya fad'a yana mikomin littafin rubutun sa  na karb'a nayi gefe da kaina Ahmad nata mika hannu da Sauri Amir yace"Umma karki basa zai ya ga min"
Cikin yanayi na nace"Bazan basa ba.Arabiya ne zan koya maka kabari ayi sallah mu natsa tukunna"
Ya amsa min da Toh ya karb'i Littafinsa Kiran sallar mangariba ya tadamu mukaje mukayi alwala mukayi jam'i gabad'ayanmu afalo bayan mun idar na d'aga hannuwana Ina addu'a Sai suma suka d'aga sai da na shafa sannan suka shafa na kalle su ina Fadin"me kuka rokar mana acikin addu'an..?
Amir ne yace"Umma a makaranta an ce mu rika ma iyayan mu addu'a"
Kai na jinjina masa ina fadin"Yauwa to ina so in dai kuka yi sallah ku rika rokar ma Umma Sa'a da nasara a abunda zata yi kun ji ko..?
Da Sauri Anum tace"Umma me zaki yi..?
Kanta na shafa ina fadin"Ba'a fada ma yara sai abun ya tabbata ke dai ki rika yi ma Umma addu'a ai zaki yi ko..?
Da Sauri ta d'agamin kai sai na Shafa kumatun ta ina saka musu albarkar acikin raina Musty da Anum har sun fara wasa na dakatar da su nace su karanta azkar din su,shiyasa suka natsu,Kiran sallar isha'i ya tadamu muka yi sallar tare sannan muka zauna mukayi addu'o'i Anum da karfi ta rika fadin"Allah ka bama Umma sa'a Allah ya bata gida da mota"
Sai ta bani Dariya Amir ya kwab'e ta da Fadi'n"Aljannah ake cewa"
Da sauri tace"Eh Allah ka ba ma Umma Aljannah "
Ba zato kawai Musty yace"Allah ka sa Umma ya hau jigi"
Gabad'ayanmu muka kwashe mai da Dariya idona ya ciko da kwallah na kama Musty na rumgume ina fadin"Ameen Ameen Allah yasa amsa bakin ku ya'yan albarka kuma Allah ya baku duk abunda kuke so duniya da lahira"
Anum ce ke gyara ma Musty sunan Jirgin da bai iya fada ba sai nanata mai take yi yana fadin Jigi sai suka sanyani Nishadi ina ta Dariya Tuni na manta da duk wani bakincikin dake Damuna. zuciyata ta dawo fara tas kamar farar takardan da ba'a taba yi  mata wani Dameji ba.
Falo na tattara su muka koma na hana wasan nace mza a dauko Littafan makaranta a duba sukaje suka Dauko na shiga Tsakiyar su,su kuma sun Zagaye Ahmad ne ya fara kiriniya zai yaga musu littafai sai na Daukesa na goya a baya na ammh duk da haka sai uban zillo yake yi shi sai ya sauka naki ko sauke sa.
Na Amir guda biyu ne Arabiya da na English na Arabiyan na koya masa,Sai na Anum littafin koyon bakake ne da aka saka su,siya itama na nuna mata yadda zata yi na Musty kuma na turanci ne sai Littafin da na saka ya Rubuta Huruful Hija'iya na Damki hannunsa ina koya mai rubutawa da Fadin su a baki, muna rubutawa muna fad'in su d'aya bayan da'ya sauran na turancin da ban iya ba nace Amir ya taimaka musu tunda shi yana primary 3 ne zai je hud'u Anum na 2, Musty kuma 1,Ahmad ne ya rage shima in da ina da kud'i saka shi zan yi, bakinsa ya bude achan kamar yadda Babansu yayi ma Anum da Musty.
Sai da suka gama duka aikin makarantan nasaka suka kwashe Littafan suka maida jaka suka maida su dakin su,sannan na zubo mana Faten nan a katon faranti muka Had'u muna ta sha Ahmad na kan jikina ina basa a baki Musty ma yasa ka rigima sai na rika basa Anum na ganin haka ta kwabe fuska zatayi kuka tace"Ni fa Umma"
Sai itama na riga bata a baki Amir ne kad'ai ke shan abunsa da kansa muna cikin haka sai ga Yaya ishaq ya shigo da Leda sai dai yaran suka juya suka gansa kwatsam ni nama manta ko alama ban ce musu Daada ya dawo ba.
Haka suka tsallakeni suka nufesa Har da Ahmad,Amir ne kawai ya tsaya a tsaye sauran kuma jikinsa suka fad'a ya tarbesu yana fadin"Oyoyo ya'yan Daada"Anum sarkin Karad'i ta ce"Daada yaushe ka dawo..?mun daina ganinka ko da yaushe muna tambayan Umma sai tace baka nan".
Ina jinsu sai ya kasa bata amsa sai da ya kai ga zaune sannan ya Dauketa ita da Musty da Ahmad ya Dora zaman jikinsa Amir ya zauna agefensa yana fadin"Umman ku bata gaya muku nayi tafiya ba ne..?Kanin ku bai da lafiya jaririn Antynku muka kai Asibiti"
Da Sauri Anum tace"Jaririn Anty mai kyau"?
Sai ya gyad'a mata  kai,sai suka nuna tausayawar su Ledar hannunsa ya warware ya fito musu da Minti da Biskit wajen rabasu musu ne yaga Hannun Anum duk maiko ya shinshina sai yaji warin Daddawa da Sauri ya Dago kansa yana kallona ni kuma shan Fate na, na cigaba da yi kallo basu isheni ba.
Sai ya kalli Anum yana fadin"Me ye a Hannun ki Mamana..?
Da Sauri ta ce"Daada Fatee ne Umma tayi mana dad'i"
Sai ya k'ara kallona ya kuma kalli Farantin gabana cikin yamutsa Fuaka yace"Fa'iza meye wannan..?
Naji sa ammh sai nayi kamar ban jiba. sai da ya kara Daga murya yana fadin"Nace meye wannan kika bama ya'yana Fa'iza..?
Na dago kaina ido cikin ido nace"Fate ne"
Saboda naga abun na sa kuma ya fara zama renin wayau faten ne bai sani ba..?
Ya maimaita sunan fate a ransa da Fili kafin yace"Me kenan..?ina mikewa nace"Abinci ne shima.."
Su Anum na kallah ina fadin"Kun koshi ne..?dukkan su suka d'agamin kai sai na nufi kitchen da shi nasan ya bini da kallo ammh ban ko waigo ba sai da na shiga na sauke abun hannuna na wanke hannuna na fito ina Fadin"kuje ku wanke hannuwan ku"
Kamar suna jirana suka sauka da gudu zuwa Daki har da Ahmad shi kuma sai ya kalleni yana fadin"Ina miki mgana kina basar dani Fa'iza?
A kaikace nace"na baka amsarka nace maka abinci ne"
Sai ya kasa mgana sai chan yace"Baku da abinci ne a gidan sai kin basu wannan abun sun ci hannunsu sai wari yake yi"
Sai ma ya bani Dariya na murmusa na gyara zama na akasan cafet din Falon ban yi mgana ba da kansa ya mike ya shiga kitchen din yaga bakomai Sai Dubaruna irin na mace mai ya'ya Shinkafa kad'ai ta rage mana itama ko Tiya bata kai ba,ba domin Goggo ta taimakeni ba da Tuni asirina ya Dad'e da Tonuwa a idon duniya domin tun da na dawo daga Rasuwar Tamadina k'waran abincin ban gani ba.tun Cefanen da yayi mana kafin ya tafi shima bamai yawa ba ne,ina jin ba shi da kudi a tare da shi ne lokacin.
Ina ganinsa ya fito cikin wani yanayi ya kuma daga waya ya kira Mama naji yana mgana ammh Dayake ban maida Hankalina akansa ba ban ji me yake fad'i ba.tunanina na chan inda mafita ta take, da Tunanin yadda komai zai faru jibi,Har na kosa ma jibin yayi mu fara kamar na matso da jibin gobe haka nakeji zumud'i kawai nake ji akasan raina kamar nama iya komai  haka nake ji.
Sunana naji yana kira da karfi sannan na Dago ina kallonsa cikin Mganarsa yace"Wani banzar Dabi'a kika samu ina mgana kina ji na,kina yi min banza..?
Kai tsaye nace"Kayi hakuri abun ka ga mara karjin ji sai hakuri"
Sai ya kasa mgana,Bata rai yayi yana Hararata kafin yace"Na rasa wata irin mace ce ke Fa'iza..?
Yanzu kayan abincin ku ya kare bazaki iya kiran Mama ki fad'a mata ba..?jamal baya gida yana makaranta ita nake turo ma kudin cefanan ku duk wata da kudin bukatun yara, ammh yanzu da nayi mata mgana tace bata zauna ba sannan bata san cefanen ya kare ba"
Kallonsa kawai nayi na kasa mgana shi kuma sai ya cigaba da fad'a yana fadin"Badar na zuwa gidan nan fa ko ita bazaki aika wajen maman ba..?Ko ke bazaki shirya ki je ki gayamata ba..?
Sai kawai nace"Kayi hakuri.."
Saboda na datse mganar ganin yaran sun fito kowanne da Biskit da minti a Hannunsu,Shima jin abunda nace ne yasa sai ya kasa cigaba da tijararsa,Daganan sai hankalinsa ya koma kan yaran yana ta tambayan su abunda suke so suna  fad'amai da labarin makaranta ni ko araina ina kara jinjina kaifin ikon Mama akan komai shi kayan abincin sai naje na Fad'amata ya kare kenan zata fidda kudin da ya turo mata ta siyan mana kenan..?kamar tana yi mana alfarma a raina daman na Guduri niyar ko zamu mutu da yunwa na gwammace duk mu mace da naje wajen Mama nace mata bamu da abinci.
Tara nayi na tattara yaran suka je suka yi shirin barci suka kwanta Anum ma da Ahmad na kwantar da su akan gadona,Na fito falo zan d'an gyarasa tunda yaran duk sun zubar da Ledojin Biskit din a tsakar falon na iske sa Lafe kan kujera yana waya a hankali yake yi shiyasa ban jisa ba sai na shiga abunda ya fito dani bayan na gama zan koma Daki sai ya kwalamin kira na Dakata na juyo ina kallonsa a kishingid'e yake sai ya Dago yana fadin"Naga zaki shige ciki ni me zan ci..?
Sai nayi shuru ban ce komai ba ya kara maimaita mganarsa ya karishe da fadin"ina jin yunwa kuma ban tsaya gidan mama naci abinci ba'
Cikin yanayin mgana tace"Sai Faten in zaka sha..?
Yadda yayi da fuska ne sai da naji kamar nayi dariya sai dai na kanne cikin kaushinsa yace"ki sama min wani abu"
Ko bakomai yaci darajan Zumunci da ya'yan da suka had'amu sai na juya zuwa Kitchen ina fadin"Sai dai shinkafa ita kad'ai garemu"
Ina jinsa ya mike yana fadin"Dafamin ki yi min source din miya tunda naga akwai kayan miya dare yayi ba na son na sake fita ne"
A daran nan ma dafamai Shinkafa araina ina kallon gas d'ina ina godema Wutar nepa ba domin anguwar da muke ana barin wuta ba, da tuni na raina kaina Gas ne mai shidda,wanda ke amfani da
Gas da Electric,basan shekara nawa na kwashe ina amfani da shi da wuta ba, tun Auran Ya Ishaq da Tarewansa a Abuja komai ya sauya,a baya yana mana Refliing ko ya aiko Jamal ya yi mana, ammh daga baya komai ya sauya sai da nayi da mai wuta,shi kuma baya da saurin girki,tunda bani da wata mafita hakanan nake hakuri da shi,Daman gas din Yaya Ishaq ya siya san da zamu dawo gidan.
Har goma da wani abu sannan na gama na had'a komai na kai masa shashensa a falo na sauke mai komai yana ciki ko bari ya fito ban yi ba na koma Dakina nayi shirin kwanciya,na kwanta sai barci ban farka ba sai asuba,bayan na idar da sallah nayi ma yara shirin tafiya makaranta saboda yau Jumm'a ne basa dad'ewa sai basu je da Kwandon abinci ba sai ruwa da na Dura musu suna shirin fita su yi ma Haruna mgana sai ga shi ya fito yace zai kaisu suna ta tsallen murna.
Shi ya kwashe shi suka fita ya kai su sai wajen goma ya shigo gidan,da amajirai guda biyu suna ta shigowa da kaya,kayan abinci ne ya siyo masu yawa har da Biskit din yara da Lemun su da ruwa har da kayan Tea wanda har yaran sun manta da shi sun saba da kunu har da su kwai kayan miya da kayan lambu,Dankalin Turawa da yawa haka ya siyo ina zaune ina karishe ma yaran guga afalo sannu da zuwa kawai nayi mai na juya na cigaba da aikin gabana har ya sallami yaran ya shige shashensa ya sake fitowa kayan na nan zube afalo ban kauda su ba cikin fad'a da bacin rai yace"Wai fa'iza wani salon iskanci kuma kika samo..?
Na dago ina kallonsa ya cigaba da Fadin"nine kike nufin zan kwashe wad'anan kayan ko me kike nufi..?
Ban ce komai ba na kashe soket din Abun gugan, na wuce na fara Daukan kayan ina shiga dasu ni ko na daina rawan jikin kan abunda bazai D'ore ba
Sai da na kwashe duka na shirya komai a muhallinsa ina shirin na koma na cigaba da aikin gabana yace"ki sama min abunda zan ci"
Kamar nace zainab bata aiko maka dashi ba ne..?
Sai na fasa rashin kunya ba Halina ba ne sai na Tashi na shiga kitchen dafamai mai Dankalin Turawa nayi,sai nayi mai miyar kabeji da taji albasa sai na Dafa mai ruwan tea na Dafa mai kwai guda biyu kuma duka na Tattaramai ko abakina domin na koshi Faten jiya na dumama nasha abuna yaran, kuma Farar shinkafa na Dafamusu da Mai da yaji sukaci kafin su tafi makaranta.
Yana zaune afalon na kawo mai ya kalli Filet da jug din da na sanya mai Ruwan zafin kai tsaye yace"Gabad'aya komai naki ya tsufa Fa'iza..Ji kwanukan cin abinci sun fita Hayyacin su mtswww.."
Ya saki tsaki daga karshe ina jinsa ban ce masa komai ba na koma na cigaba da aikin gabana,sai da na gama na kashe komai na kwashe zan koma Daki naji ya daga murya yana fadin"Ki shirya in yara suka dawo makaranta zamu je gidan Mama a gabanta sai ki fad'amata in ni nayi miki iyaka da zuwa gaisheta"
Sai abun ya bani mamaki.matar nan Kwata kwata bata kaunar ganin kwanciyar Hankalina, burinta ta samo hanyar da za'a tozartani, to da ikon Allah kanta zai koma ni dai ina Daraja ta ko ban auri Yaya Ishaq ba. kamar uwa take gareni, tunda ta rikeni bata barni na yi rayuwa a titi ba sannan duk tsananin wuya da Dadi ta killaceni acikin gida rayuwata bata shiga tsaka mai wuya kamar na sauran matan da rashin gata da mafita yasa suka fada harkan banza ba,ballatana ina auran Abunda ta Haifa har abada bazan ki Darajata ba.
D'aya saura na rana yaran suka Dawo shi yaje ya Dauko su da kansa masallaci jumma'a ya tafi da mazan har da Ahmad ni da Anum mukayi tamu a gida,Shinkafa da miya Da salat nayi mana ni da Anum muka fara cin namu kafin su dawo suna Dawowa na zubo mai yaci tare da yaran,Suna ta Murnan tunda na saka musu sabbin kaya nace gidan mama zamu je.
Wajen uku saura na rana muka isa gidan Mama,Mun iske gidan cike Anty Binta,da su Halisa da Anty mahma da ya'yanta kamar ana biki yaran muna zuwa suka had'u da abokan wasa suka tafi suna ta wasan su.
Afalon kowacce tayi shigar alfarma har ta da Mama ko da taga jiya taga yau da na gaishesu dakyar suka amsa min gwara ma Anty mahma Halisa daman ita ta gaisheni har tana min gaisuwa,Ni da Badariya ne muke mgana kasa kasa kan gobe Badariya tace"Kin fad'a ma Yaya ishaq dai ko..?
Na girgizamata kai kafin nace"Ban fada masa ba ammh zan shaida masa yau in mun koma gida"
Badariya ta zaro ido kafin tace"in ya hana ki fa ?nasan Halin Yaya Ishaq barin ma in ya fad'ama Mama wlh bazaata bari ba"
Kai tsaye nace"Wannan karon bazai iya hana ni din ba"
Cikin mamaki take kallona bata samu zarafin mgana mukaji muryan Mama asama tana Sababi sai da na Saurara naji dani take tana cema Yaya Ishaq gatanan ka tambayeta yaushe rabon da kafarta tako gidan nan da sunan gaisheni.?
Anty Binta ta karbe da cewa"Ballatana ni banza abanza mama"
Shi kuma sai ya d'ago daga Danna wayarsa yana kallona Lokaci daya yana fadin"Shiyasa na kawo ta gata gani ta fad'a in ni nayi mata iyaka da gidan nan? Gata nan ni da kaina na yarje mata zuwa Gidajen ku duk sati ta gaisheku ita zaku Tuhuma me ke hanata zuwa"
Mama ta tabe baki tana fadin"Rashin mutumci ne ba wani abu ba.ko yaran nan bata kawo su, nace to in kai ne ma kake so ka raba su da nan gidan basu da inda yafi gidan nan a wajen su ta bangaran ta da take takama wa take dashi ?uwar tasu da ta rage itama Allah ya karbi a binsa sai naga karyan tsiya "
Idunuwana suka ciko da kwallah na kasa mgana zagi da cin mutumci ba wanda Mama batamin ba Anty Binta na tayata sai da Anty Mahma tace"Haba Mama ki barta hakanan mana ba ta baki hakuri ba"
Sai Mama tayi shuru tana Numfarfashi ni dai kaina na kasa ina bata Hakuri Saboda Yaya Ishaq yace na duka na basu hakuri in ba haka ba sai ya sabamin ban ki ba na Duka gwiwa Bibbiyu na basu hakuri dakyar suka Hakura.
Daganan suka yi kamar bana falon suka cigaba da Hiran su sai Badariya tajani Dakinta tana bani Hakuri na kalleta cikin wani yanayi kafin nace"Bakomai duk wanda yayi ma Aure bauta bazai taba tabewa ba..Sannan sakamakon sa na wajen Ubangiji"
Daga haka muka saki mganar mu kama wacce nake ganin zata Fisheni Badariya sai jinjina yadda zan rika zuwa sau biyu arana take yi.nace mata kada ta Damu zan iya ai nace Allah adakin ta nayi la'asar sannan Mama ta aiko wai nazo nayi musu abincin dare haka na kwabe Hijabi na shiga kitchen da Badariya ta shgo zata tayani Mama na ganin haka sai ta kirkiri aikenta sai bayan mangariba ta dawo Lokacin na gama Tuwon shinkafar har na kulle a leda Miya ce bata karisa ba.
Har ta Anty Binta sai da taci tayi guzuri Anty mahma dai da wuri ta koma gidanta mu kuma sai wajen goman Dare tuwon nan ko bakina ban ci ba,su Amir dai sun ci da Babansu duk na Takura na kosa na koma gida.
Kusan Lokaci d'aya muka fito da Anty Binta itama zasu wuce afalon Mama ta kalleni tana fadin"Wai ni kam fa'iza ina kayan ki da Ishaq yake miki ne..?bana ganin ki da su sai tsumma kike sawa"
Gabada'ya suka kalleni harda shi da Mama,Bai dai yi mgana ba sai Mama ce ta tabe baki kafin tace"Daman da Tsumman ta dace.aiko don yan'uwanta su zagesa zata rika mugun shigga alhalin daidai misali yana fita Hakkinta"
Har muka isa gida mganar Mama tamin Tsaye arai bayan wannan kayan Da Anty binta ta bani ko Hijabi Ya Ishaq bai kara dinkamin ba.ammh Mama ta iya bud'e baki ta fadi yana Fita Hakkina, Lalle gaakiyan masu iya mgana da sukace wata shari'ar sai Lahira.
Sai da duk nayi ma yaran shirin barcin daman ko da muka dawo su Anum duk sun fara barci,sannan na Dauki wannan Katin I.d card kenan na nufi bangaran Yaya Ishaq acikin raina ina jin cewa wannan karon bazan iya bin Umarninsa ko ya amince ko bai amince ba wannan karon ba gudu ba kuma ja da baya insha Allahu.
Na shiga na iske baya falo yana cikin Bedroom dinsa ba domin ni nake bukata ba,ba yadda zai sa na bisa ciki Tuni na kiyayewa kusantar inda yaya Ishaq yake saboda Dalilai masu karfi.
Bedroom din na shiga da sallama baya Dakin sai nayi mamakin to yana ina..?
Har na juya zan fita naji karan Bude kofa kii..Sai na juyo muka hada ido shima kallon da yayi min nasan na mamakin ganina ne.
Yana sanye da kayan barci riga da wando, masu taushi Farare na barci,Ya kariso tsakiyar dakin yana fadin"Lafiya..?
Har yana wani gimtse ransa kila yayi tunanin wani abu nazo nema sai yaga na mikamai abun hannuna ya karb'a yana zama gefen gado lokaci daya yana fadin"Wannan kuma na menene.?
Sai dai yayi mamakin ganin Hotona da sunana da dukkan bayanan abubuwana ajikin katin sai ya kara Dagowa yana kallona cikin mamaki ya kara fadin"Fa'iza duk wannan abun na menene..?
Sai na duka a gabansa na gyara zama na Dakyau kafin nace"Kune yan boko ka karanta Dakyau zaka fahimta"
Ya sake karantawa ya Dago cikin mamaki yana fadin"Naga Katin shaida ne na Training din da za'ayi na koyon sana'o'i daga karkashin kungiyar Women charity Foundation."
Shine nace ban gane ba naga hoton ki da sunanki shaidar katin naki ne"
Mirmishi nayi Cikin karfin gwiwa na fara mai bayani da yadda kawar  Badariya da ita kanta suka samo min form din na cike,da kiran mu da akayi wanchan satin mukaje da bayanin komai na karishe mganata da fadin"Gobe zamu fara koyan abubuwa kuma na tsawon sati goma sha Biyu ne,Sannan sau biyu za'a je a rana ni kuma abubuwan da nake so na koya da Safe ake koyar da biyu da yammah biyu kenan kaga a rana sau biyu zan rika zuwa kenan safe da rana"
Har na gama bayanina yana kallona cikin mamakina daya nuna har a saman fuskarsa,Cikin kaushinsa yace"Duk a yaushe kika fara yanke ma kanki hukunci yin wani abu batare da sanina ba Fa'iza?
Nima kai tsaye nace masa"A ranar da ka zabi wata matar sama dani.Nima aranar na zab'i yanke ma kaina da Rayuwata komai batare da na saka ka aciki ba"
Maganata ta girgiza sa ya tsaya kawai yana kallona,ban damu ba sai ma naji kamar gwarin gwiwan. da na shigo da ita ta ninka wacce na samu yanzu tsoro ko fargaba sun fice daga raina kwata kwata.
Hanuna na saka na karbi katina daidai Lokacin da yace"Ni ki ke gayama wannan mganar Fa"iza..?Rashin kunya zaki yi min.?
Kai na girgiza kafin nace"Ko d'aya kada ma ka dauka ahakan Yaya Ishaq ai ko ba aure tsakaninmu kai yaya na ne,kuma babu rashin kunya har Abada tsakani na  dakai.kawai akwai lokacin da in mgana tazo a muhallinta gwara a fad'eta kawai da a barta tayi ta zama a inda ba Muhallinta ba"
Sai ya kasa mgana sai kallona yake yi cikin mamaki nasan aransa mamakin ya akayi na samun bakin yi masa mgana yake yi ni ko araina nace daga yau bakunan fa'iza sun bud'e kenan Har Abada.
Cikin Ajiyar numfashi yace"Naji yanzu meyasa kika fad'amin..?
Na gyara zama na nace"Saboda ya dace ka sani ko ba komai ina gadin gidan ka.
da kuma kula da ya'yanka in fita ta kamani naa jera sati ba ma wata ba, yana da kyau ka sani d'in shiyasa nake shaida maka"
Kai tsayae yace"In kuma nace baza ki fita ko'ina ba na isa ko ban isa ba..?
Ya fada yana kallona cikin ido nima sai na Dago ina kallonsa bansan Lokacin da bakina ya furta"a wannar gabar Isar ka bata isa ba Yaya Ishaq.."
Sai ya zabura yana kallona cikin bacin rai ya nuna da hannu yana fadi"Ni kike cema isa ta bata isa ba Fa'iza"?
Sai ya mike yana Huci Lokaci d'aya yana fadin"Lalle kin fara rai na ni kin manta waye ni a wajen ki kenam? Gantalin da kika farayi na shiga makota yasa kika koyi rashin kunya da rashin Tarbiya ko..?
Sai nima na mike kai tsaye nace"Na fada maka kada kawo mganar rashin kunya a wannan muhallin saboda kai kanka kasan ba Halina ba ne yanzu ta kamane kasan wasu abubuwa.."
Cikin Hargagi ya katse ni bayan ya tasomin yana fad'in"To nace bazaki yi ba in kuma zaki nuna ban isan ba ne bismillah Fa'iza wlh sai na nuna miki Oder side of me da baki taba gani ba"
Ban bari ya sauke mganarsa ba nace"A matsayin ka na waye kake fad'in bazan yi ba..?
Yadda nayi mganar ta basa mamaki sai ya tsaya yana kallona Lokaci d'aya yana nuna kansa cikin mamaki yace"Ni ki ke fad'ama wannan mganar..?
Kai tsaye nace"Eh tambayar ka nayi a matsayinka na waye..?
Mirmishin gefen baki yayi kafin yace"Ina da matsayin yaya gareki sannan kada ki manta ni mijinki ne"
Nima mirmishin takaicin nayi kafin nace"Mijin jingina..?ko yayan da baisan Hakkin kanwarsa a kansa ba..?
Nace mijin Jingina Yaya Ishaq ka ke kira Miji..?
Mgana takara  girgizasa ban bari ya fita daga Girgizan ba na Dora da Fadin"a shari'an ce kai ba mijina ba ne yanzu.Saboda ka zabi wata matar sama dani,ka jingine aure na shekaru biyu kenan,ni matsayina kawai ina kula da ya'yan ka ne sannan in amtsayin Yaya kake mgana baka da wannan Hurumin saboda sai yaya ya zama nagarttace nagartansa zai yi yab'o har ta yab'anyan, da k'anwa bazata iya zarta da wani abu batare da yardan sa ba,Duka baka cike kowani Gurbi ba shiyasa nace isar taka bata isa wannan karon a wajena ba"
Baya ya juyamin ya kasa juyowa ya kalleni, ban damu ba sai nayi kokarin Dauke Hawayen da suka kawo idanuwana na cigaba da fadin"Tun Lokacin da ka zabi iyalan Zainab sama da ni da ya'yana.isar ka ta zama bata isa akaina ba, sannan tun alokacin na Zab'i ya'yana sama da kai,kuma tun  lokacin da ka zabi Dangin zainab Sama da Dangina nima na zabi Dangina sama da naka dangin, ban ce Dole sai ka amince ba ina fad'a maka ne Dole zan fita na nema ma kaina mafita Kuma Dolenka, ka kare mganar hakan daga bakin kowa in kana gudun fallasar Jinginannen auran mu zuwa kunnuwan da bazaka so hakan ba"
Shuru yayi ya kasa juyowa ni kuma da nagama mgana sai kawai na kama Hanyar fita cikin Shakewar murya yace"ya'yana fa wazai kula da su.?
Na juyo muna kallon juna ido cikin ido kafin nace"Nima ai ya'yana ne..Ni nake kula da su Lokacin da ka zab'i zainab da ahalinta sama da su.ai a yanzu ba'a wulakance ka gansu ba, nayi alkawarin zan kula da su domin nan duniya nice gatan su nima sune karfin gwiwata da dalilan da yasa nake zaune cikin kaskantataciyar rayuwa"
Ina gama fadin haka na bude kofa na fice har nakai dakina hawaye ne ke kwaranyomin sai na zauna agefen gado na rumgume abun hannuna a saman kirjina,na fashe da kuka,a hankali a hankali kuma ina samun salama da Sauki acikin zuciya ta.
Sama na kallah nace a fili"Allah kana ji kuma ka na gani.
Ya Allah ka sama min Mafita, mafita mai amfani a rayuwata da ya'yana. ka hananin jin kunyar duniya ka bani dukkan karfi da juriyan daukan duka Jarabawowinka."

*TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWAR ZAKI YI AMFANI DA ITA SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*..

*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

*Fatan alheri,ga mutane masu kirki da karamci.*

*Aisha muhammad alto(Sisinah)Sannu barka da arziki kin yi kokari da kika Haifa min D'a,Allah ya raya mana Baby boy.*
*Fatan alheri zuwa ga Khadija Salisu yusuf(Ummina)*
*Halima yusuf gwarzo(Besty) ina miki fatan alheri*
*Nana Halima(Masoyiya)ina gaishe ki Fa'iza tace na fada miki,tana kaunarki kamar yadda kike kaunarta.*
*Ina gaida Uwar biyu Mrbb,Allah ya raba lafiya*
*Sannu gwana uwar Dakin gwanaye,Feedhom nace Allah ya sa afi haka.*
*An gaida Uwar Muwaddata da Anum Ramlat Abdurrahaman Manga,Maidambu,ina godiya Allah ya saka da alheri*
*Ina miki Fatan alheri Uwar Farha Fatima miss flower(Rabin raina).*
*Sannu Amina minajo na,Fa'iza na gaida Masoyiyar asali.*
*Sannu Anty maryam,Fa'iza tace nayi miki godiya,da shawarwarki ta fara sanin cewa itama Yar Adam ce.*


*Madallah da mutane masu karamcin irin ku,Nagode sosai Allah ya bar zumunci,ya kuma had'amu a aljannah*

           *🅿️19*

Saboda Zumud'i ko fargaba zan ce, sai wajen uku saura na dare na iya samun, barci kuma cikin ikon Allah Kasala da nauyin jiki sun kasa barina na tashi na dauro alwala.
nayi salollin Nafila sai dai ina daga kwancen ban daina Hailala da ambaton Allah akan dukkan lamurana ba.
Washegari kamar yadda na saba tashi da wuri haka na tashi, na shirya yara na sama musu abun kari. sukaci sakamakon sun saba tafiya ba abinci,yau din ma haka suka tafi sai dai kamar yadda na sabar musu sai sunci sun koshi suke tafiya yadda kafin yunwa ta jigatasu, lokacin sun dawo gida sai na ba ma kowannen su Goran ruwan faro guda d'aya sun tafi da shi koda bukatar shan ruwan ya taso musu.
Suna tafiya nima ban zauna ba, na fara shiri falo kawai na gyara Dakin yara kuma nace sai na dawo nayi wankana na shirya kaina shima Ahmad na shiryasa bayan na Dama mai kokon sa. na duramai a wani karamin jug,Sauri sauri nake yin komai kada farkon fari kuma nayi latti na samu Tsoffin littafan su Amir da suka gama amfani da shi na Dauka da pencil saboda rubutu duk da ban iya Turanci ba, kuma ban iya Hausa ba, ai na iya rubutu da ajami kuma ina iya karantawa shiyasa ban damu ba.
na tabbatar ma kaina duk abunda na Rubuta zan iya ganesa.
Na hada da katin  shaidana na goya Ahmad a baya na daukan mai wasu kayan. ko da ya bata na jikinsa na fito Falo Tara saura,naci karo da Yaya Ishaq a falon yana waya kallo d'aya nayi mai ban kara ba,shi kuma ganin kamar tafiya zan yi yasa ya katse wayar Hannunsa,ta gabansa na gifta cikin yanayin mganata nace"Ina kwana.."
Ina fad'in haka na kama hanya zan fice sai ya mike jiya ya kwana yana mamakina sai da yaga abunda nayi yau sannan ya amince da gaske nake yi,sai ya saka baki ya kirani da karfi na Dakata na juyo ina kallonsa kai tsaye yace"Ina kike shirin zuwa..?
Ni kuma sai naga kamar yana batamin Lokaci sai na juya ina fadin"In da na fad'a maka jiya..Ina Sauri ne kada na makara"
Na fada ina jimke dubu d'ayan da na Dauko cikin kayana sun sha ajiya tun Kudin da Yaya Isa ya bani ne Lokacin da ya maidoni gida, Dubu buya kad'ai na Taba ukun suna na nan ina Boye da su, sai da hakan ta faru na Daga hannu nagodema Allah domin zasu yi min amfani.
Kawai sai naga ya sha gabana a matukar fusace cikin d'aga murya yace"Ni kike nuna ma ban isa dake ba Fa'iza..?
Baya naja ina fadin"Ban ce baka isa ba.Sai dai na nuna maka isar taka ce wannan karon, bazata isa a wajena ba ka bani hanya na wuce ina bata Lokacina"
Sai ya tare hanyar ni kuma sai na kasa wucewa cikin Daka tsawa yace"Ki koma nace ba inda zaki je"
Sai nayi wani kayattacen mirmishi takaici na Fahimci in na zauna haka Ishaq zai cigaba da Nakasa rayuwata kamar yadda ya saba to wannan karon ya makaro domin d'an zaki ya riga ya girma.
Sai kawai na kallesa ido cikin ido kafin nace"Sai dai kayi hakuri wannan karon bazan ji mganarka ba.Na fada maka tun Ranar da ka zabi Zainab da Ahalinta sama da ni..Nima Daga wannan ranar na zab'i Rayuwata da ya'yana sama da kai"
Mganganuna sun dake sa sai ya kasa motsi har na raba ta gefensa na wuce abuna,Kafin na fita sai da nayi addu'an fita gida,sannan na karisa gidan Sa'adatu muka gaisa na kwanto mata Ahmad Allah yasa yayi barci ta karbe sa tare da kuninsa tamin Fatan Alheri daganan na fita na samu Adaidaita sai cikin gari.
Makarantar ta yan mata ne zallah suna barayin su sannan mu kuma inda zamu zauna wani babban aji ne, ko da nazo mata sun fara taruwa sai dai ma'aikatan basu riga sun kariso ba,na gaisa da matan dake kusa dani muka zauna jiran su tara da wani abu suka iso,,Rukuni rukuni suka jeramu a layi mun nuna katin shaidarmu sannan suka sanyamu a rukunin da zamu fara koyan abunda ya kawomu.
Ni rukunin girke girken aka sanya ni shi zasu fara koyar damu sai sun gama sai ayi barayin Had'a lemuka da rana ne Rukunin Koyar da Turaren wuta da Had'a Dilka..
Sai na Fahimci da Safe duk abun ci ne zasu koyar damu shiyasa sai suka raba abun,Ni dai ban tsaya kalle kalle ba na saka ido sosai,ina Fahimtar komai masu koya mana Rukunin Farko,Su biyu ne dukkan su mata ne, Daga ganinsu sun san kan aikin su Sanye da Fararen riga da Hula na masu kirkin da muke gani a Kwatin Talabijin.
Ranar farko wainar kwai suka koya mana da miyar gyada mai allayahu,sosai na karu na kuma rubuta sunayen abubuwan da suke fad'amana bamu gane ba,Suna yi suna yi mana bayani yadda zamu fahimta sannan in baka gane ba sai kayi Tambaya komai da komai na girken girken su, sun zo da shi suka kafa karamin Dakin girki a babban D'akin da muke ciki, nayi tambaya in da naga ban gane ba.kuma sun kara yi min bayani suna da Sauki kai matuka da iya mu'amala.
Daman kuma Koyar damu ne aikin su, har kuma mh iya sun kuma tabbatar mana da cewa zamu iya girke girke masu kyau da inganci.bayan an gama dukkanmu muka D'andana mu biyar ne a rukunin Girke girken,muna ta santi saboda yayi dadi sannan da alkawarin in muka koma gida zamu gwada mu gani.
Sai rukuni na biyu Had'a lemuka,Zobo suka fara koya mana Had'ashi,Duk da na iya zobo sai naga nawa shirme ne ashe ga inda ake zobo nan,Ranar anan Rukunin ya kare shima sun bamu mun sha dad'i,Daga karshe sukace in da bamu gane ba mu yi mgana ni dai akwai karambani daman duk abunda ban ji ba sai da na tambaya suka kara gayamin,Ranar farko kawai da fara zuwana naji araina zan iya komai insha Allahu na dawo gida da Farinciki na iske Ishaq baya gidan ban Damu ba daman na fita da key da na ga ya Kulle gidan sai na bude bayan na Biya na Dauko Ahmad.
Ko girki ban yi ba Dakunan kawai na gyara na share, Lokaci yayi na makara ma a rukunin Rana sai d'aya da Rabi na isa har an fara an raba mutane kowa da Rukuninsa sai da na nuna Katina sannan aka kaini Rukuni na,Abu na farko da suka fara koya mana yadda zamu had'a Turaran kamshi na Icce ne ranar shi mukayi har aka tashi,shima in da bamu gane ba suna bamu ikon Tambaya in da kuma zaka manta sai ka Rubuta na dawo gida karfe hudu da Rabi na yammah na biya gidan Sa'adatu na kara dauko Ahmad sallah kawai nayi na shiga kitchen Saboda yan makaranta suna hanyar Dawowa.
Duk da na gaji ammh ban damu in dai aikin wahala ne na saba shi kuma ya zame min jiki,sai da nayi wanka sannan naji dadin jikina Yara suka dawo makaranta da yammah suna ta Tambayan Daadan su nace ya fita bansani ba,ko saboda abun da ya faru ne sai da yaran suka gaji da jiran sa, suka kwanta sannan ya Dawo ina Falo ina Tattara kayan da suka zubar daya shigo nayi mai sannu da zuwa bai amsani ba sannan bai kalleni ba. ya shige bangaransa a raina nace ko nace a banza.
Washegari ma ya rigani fita,Nima ko Lokaci nayi na yi tafiyata kamar jiya,Sai dai na Fahimce zan rika shan wahala in dai ina jeka ka dawo sai na yanke shawaran in mukayi sati uku, zan fara zama achan sai mun gama Rukunin rana sannan zan dawo gida gabadaya kud'ina kada su kare wajen adaidaita na rasa mafita.
Yaya Ishaq kuma tun daga wannan sa'insan tsakanin mu mgana bata kara Hadamu ba, ni dai ina fita Hakkinsa in mun had'u ina gaishesa shine baya amsani duka duka kwana Hud'u yayi ya koma ko sallama bai yi min ba. ganewar ma da nayi bai kwana agidan ba nasan duk tsanaani in dai yana gari to zai kwana agidansa.nima ko na tattarasa na watsar domin da gaske nake yi na zabi Rayuwata da Rayuwar ya'yana sama da tashi Rayuwar.
Na cigaba da zuwa wajen koyon sana'o'i na hankalina kwance kusan indai akace wannan abun shi kad'ai ne Hope din ka da Fatan ka to gabad'aya Tunanin ka da Rayuwarka zaka Dorasa akansa ne,ya kuke gani in hakan ta faru da mace irina da daman jiran mafita take yi..?to kamar misalin nice Domin na maida gabad'aya Hankalina da natsuwata kan abunda nake koya,Shiyasa duk nafi kowa ganewa a Duka Rukunina tun bamu Rufe wata ba Ma'aikatan suke yaba hazakata da Kokarina,Gashi abubuwa Hudu nake koya ammh kwakwalwata tana Daukan abubuwa dadama. sannan ina gane duk abunda aka koya mana.
Muna rufe wata d'aya da Farawa na koma ina zuwa sau d'aya in na tafi sai Hudu nake dawawo saboda in aka tashi Rukunin Safe sai na zauna sai Rukunin yammah Tunda ma'aikatan suna nan suma ka'ida sai Hudu na yammah suma suke tashi, duk abunda muke yi suna daukan komai sannan suna Rubutawa saboda suna turama kungiyar Bayanan komai.
Yau da gobe zara bata bar komai ba kudin hannuna suka kare sai na koma takawa da kafata yara na fita makaranta nake fita da nisa sosai kafin na kai na jigata ammh hakan nake Daurewa na sama kaina yakinin ba wanda ya isa ko ya samu yana kwance, sai da ya fita ya wahala,Muna Hutu Ranar jumma'a duk sati sau Shidda kenan to ranar ne nake samun na gyara gida, har yi ma yara wanki da Sauran aikace aikace ni kaina nasan na Rame saboda wahala.
Badariya sai da muka raba rabin watanninmu sannan tazo gida ranar wata jumma'a muka hadu a bakinta nake jin Anty Binta tazo sau biyu bana gida ta je ta fad'ama Mama sai Fada take,Tana fadamin Maman ta kira Yaya Ishaq din tamai mgana ba'a san me ya fada mata ba,basu kara mganar ba,Badariya tace ita dai tayi gum da bakinta bata tofa ba, tana ji Mama na fad'an na fara gantalin bin gidajen makota.nayi dariya nace gwara da kika yi shuru baki ce musu komai ba.
Araina naji mamaki ban Dauka Yaya Ishaq zai yi Laushi ba ni dai abunda na sani bazan zauna Damar da na Dade ina jiranta ta Kubcemin ba,Bandamu domin ba ta su nake ba ta kaina nake da ni da ya'yana. Badariya taji dadin yadda na fadamata muna koyan abubuwa da Dadama,sannan wahalata ta ragu saboda Sa'adatu ta Daukemin Laluran Ahmad sai abun yazomin da Sauki,Ban gayama kowa ba So nake ko yan Karofi na basu mamaki Fata na da Dakiyata azabeni cikin mutanen goman da za'a basu tallafi saboda zai yi min matukar amfani.
Yadda Yaya Ishaq ya tattarani da ni da ya'yana gefe d'aya.haka nima na tatrarasa na watsar Sai dai ya'yansa ban isa na cire musu tunaninsu akan sa ba,ko bakomai mahaifin su ne,ya zama Dolen su ni kuma ko da yake mijina ai ba Dole na ba ne,Na riga na jigata da tafiyar kasan da nake yi ammh ban ji ko sau d'aya na gaza ba nayi fashi sau Biyu shima Ahmad ne yayi ta zazzabi ba Halin na fita na bar shi kuma zuwa da yara an hana, shiyasa na zauna na Kula da shi har yaji sauki muna gabda cinye wattani ukun mu,Badariya ta dawo wajena da kwana ashe Mama da Anty Binta Abuja sukaje sulhu Zainab ta samu ciki sai suka yi sa'insa da Ishaq akan Farhan bai yi kwari ba, zata zubar da cikin shi kuma ya hana ita kuma sai ta Ture mganarsa ta yi mgana da mahaifinta yace ta zubar, tako je aka markadesa shine rigima ta kai su ga Har Ishaq din ya mari zainab din ai ko Badariya tace Mahaifinta ya Kira Mama yana fadin Ishaq ya gama marin auransa kuma sai yayi mganinsa sai ya yi kararsa a kotu,Ai ba jaka ya aura masa ba.shine Mama ta rud'e ta yi ma Anty Binta mgana ta rakata suka tafi Abuja su sulhunta mganar.
A raina sai nace tun yanzu..? Auran barikin fa kenan,ai na Dauka ko me zainab tayi Yaya Ishaq zai yi hakuri da ita,tunda ita yar so ne kuma ita ya zaba ban dai nuna komai ba nayi fatan Allah ya Daidaita su Saboda ni bazan yi Dariya don haka ta faru ba Namiji ai duk inda yake yana amsa sunan sa na Namiji ne.
Wajen kwananta hud'u a gida na sannan su Mama suka dawo, sai ta koma gida Saboda harkan gabana nake yi yasa ban damu da na Bibiya ya suka kare ba,Nidai bana fatan tun yanzu auran su ya samu matsala ina Fatan su tara kyakyawan zuru'an da Yaya Ishaq yake mafarki da fata ko zai daina kallona a matsayin wacce ta zama Sillar shiga tsakaninsa da mafarkinsa da Burinsa.
Mun cigaba da zuwa muna koyan abubuwan da ake koya mana har ga shi yau da gobe bata bar komai ba zamu kammalah,Watanni uku kamar kwana uku ne a wajen Ubangijinmu,Ranar jumma'a muna Hutu asabar zamu gama gabad'aya ranar Lahadi kuma za'a sallame mu da Takardan shaidar abunda muka koya, a kuma wajen za'a bama wad'anda suka chanchanta tallafi.
Ranar jumma'an ina gida tunda bama zuwa ranar Sai ga Badariya da Raliya sun zo min da labari mai dadi bayan mun gaisa na kawo musu ruwa su Amir suna haraban gida suna waasa.
Raliya ta kalleni tana fadin"Anty Fa'iza ina tayaki Murna kin yi abu mai kyau, Hajiyar mu tana ta fad'amin a duk report din da ake kawo musu a duka Rukunin da kike Dauka kin zama zakara sosai ma'aikatan suke yabawa da kokarin ki"
Sai naji dadi na godema Allah acikin Raina Badariya na gefenta tace"Ai Anty Fa'iza ba daga nan ba Raly ni daman nasan zata iya"
Raliya tace"Haka na fad'a ma Hajiya..Nidai mun zo cin sauyin Sabon girki ne Anty Fa'iza me zamu samu..?
Na mike ina Dariya nace"Daman jiya alalan mai kifi da kwai aka koya mana yau daman ina da niyar gwadawa"
Ihu suka saka gabadayan su Badariya tace"a hada mana har da lemu mai Dadi don Allah"
Sai nace to a raina ammh ina Tunanin ina zan samu kudin kifi da kwai, tunda ina da wake kamar Badariya ta sani taja Raliya suka fita ba jimawa sai ga shi sun dawo da cefane har da kankana da kankara sukace Lemun kankana suke so nan da nan ko na shiga Kirchen na fara aiki suka shigo suna Tayani da hira da d'an taimakon da bazai gagara ba.
Nikan Waken Amir na aika ya kai mana makota muke da gidan nikan, kusa da gidan Habiba ne daman in dai aike ne ko nika kusa haka to Amir nakan aika Tunda ba nisa sosai,cikin awa uku muka gama alalan kwai da kifi na kuma had'a musu lemun kankana nan sukayi sallar mangariba suka zauna suka ci suna santi Raliya tace"Anty Fa'iza in da saura a samin a leda sai na kai ma Hajiyarmu alalan nan taci taji itama"
mirmishi kawai nayi daman na Mudu daya da rabi nayi na Dibar mata da yawa tace kowa sai yaci a gidansu ta karishe da Fadin"Zan miki tallah Anty Fa'iza dole mu bude Fa'iza Kitchen"
Badariya tace"Sosai ai Oder zamu fara yi wannan girki ai ko Hotel ko Restaurant albarka"
Haka suka yi ta zuzuta girkin da zasu tafi mukayi sallama suka tabbatar min da jibi zasu zo tunda taron a babban Hall din makarantar su ta Umaru musa yar'aduwa za'ayi.
Washegari da mukaje gwaji dukkanmu mukayi,Ma'aikatan duka gefe suka koma suka bar mana abunda zasu yi ranar, Kunun gyad'a muka yi bangaran abun sha kuma ni na zama zakaran rukunin mu sai bangaran girki kuma yam ball muka yi ma'ana Fanken doya,shima ni na zama zakara na Rana ma rukunin hada Kolaccha  ma ni na Jagoranci Rukunin mu,haka bangaran had'a Dilka da Halawa anan wajen muka mulkama kafafun mu da Hannuwan mu,wasu har da Fuska ni dai ban saka ba,Sannan mun had'a Turaren Humra na ruwa mai kamshi shima muka goga a jikin mu saboda muji yanayin kamshin,Ranar sai Yammah na dawo gida su Amir gidan Sa'adatu suka zauna sai da  na dawo.
Ranar Lahadi kuma na fada ma su Amir su yi min addu'a yau zan gama abun da nace musu ina yi suka yi ta cewa Umma Allah ya baki sa'a na amsa da Ameen.
Saboda taron gamawa ne Tare da Ahmad naje bansan makarantar ba, mai adaidaitan ya kaini hall din ba Boyayye ba ne ina zuwa na tambayi inda ake taro wasu yanmata suka nuna min, da wuri naje wasu duk basu zo ba ammh naga wasu daga cikin mu.
Karfe sha d'aya aka fara taron manyan mata masu alaqa da kungiyar duk sun zo ciki har da Hajiyar su Raliya na ganta ba su gayyato yan jarida ba Saboda basa son duniya ta sani su don Allah suka yi,Sai mu kawai da muka samu Horan sai kuma yan'uwan wasu daga ciki da ma'aikatan da aka Dauka suka koyar damu sai yan kallo.
Su Badariya sun zo su da gayyar kawayen su sai dai hannu suka Dagamin, tunda su suna baya mu kuma gaba akace mu jeri mu Talatin din da muka samu Horan.
Bayan jawaban godiya da kuma Fatan alheri ga wannan kungiyar aka gayyaci wata Hajiya Zubadai  itace kamar ma'ajin kungiyar reshen Jahar katsina ta fito tayi jawabi akan manufar kungiyar da kuma manufar taron da suka shirya garemu na mata talatin da suka koyar da su sana"o'i goma.
daganan aka bata sunayen mu ta rika kiran mu d'aya bayan d'aya muna karban Takardan shedar abunda muka koya ni ce ta goma acikin wad'anda ta kira Fa'iza sidi karofi. Dayake tana amfani da amsa kuwwa abun mgana, najita na fita Ahmad na goye a bayana ta bani Takardata sai da nayi Hawaye,Ina gani wata ta kusa da ita nayi mata rad'a a kunne ta kalle tace"Fa'iza sidi karofi ko..?
Na jinjina mata kai sai ta bani Hannu muka gaisa cikin kayattacen mirmishinta tace"Weldone Fa"iza"
Duk da ban ji me tace ba nasan yabo ne sai na jinjina mata kai sannan na koma na zauna,ina Duba Takardan Hannuna da Turanci ne sunana kad'ai na iya ganewa aciki,ammh nasan ko a hakan na tsaya na cinma wata gagarumar nasara a rayuwata ba Nakasashe sai Mai nakasar zuciya, sannan akace babu maraya sai Raggo. in ka tashi ka nema bayan ka bama Allah zabi to shi kuma Allah zai saka maka da kyakyawan sakamako.
An cigaba da kiran mu har zuwa ta karshe sannan wata Hajiya laila daga kaduna itace mai rike da mikamin P.R.O na kungiyar ta fito zata bada shedar girmamawa ga wad'anda suka zama zakaru a rukuninsu,Allahu Akbar ban taba zata ba, Ba zato ba Tsammani naji sunana Fa'iza sidi karofi na fita aka bani wani d'an kwalba mai ban sha'awa da sunana ajiki sannan matar ta tsaidani tayi jawabi da turanci sannan tayi da Hausa tana mgana akan cewa ina da Hearing problem, sannan ban yi boko ba.ammh na iya zama ta farko a fanni masu kokari a dukkan abunda na Koya, sannan ta sake bani wani abu nazare a wuya na ta makalamin na Girmamawar na koyi abu hudu masu wahala a acikin wattani Uku,Sai tafi raf raf ta bani Hannu muka gaisa har tana yi ma Ahmad dake bayana wasa ko da na koma na zauna sai na daga hannuwana sama ina fadin"Allah na gode maka..Alhamdullahi ya Allah dukkan wata ni'ima daga gareka ne"
Matan dake kusa dani suna ta min murna ina amsawa bakina har kunni na juya ina hangen su Badariya ta D'agomin hannu na Daga mata kyautan da takardan da aka bani, ita kuma sai ta Dagamin babban yatsanta alamun jinjina.
Bayan ni an kira mata uku suma an basu lambar girmamawa ta zama zakaru a rukuninsu,Daganan an wakilta uku daga cikin mu suka fita suyi jawabin godiya ni dai nace bazan iya ba Saboda ban taba fita gaban jama'a nayi mgana ba ko karban kyatuttukan ma Dakyar na iya fita kamar zan fadi haka na rika ji.
Ma'aikatan da suka koyar damu suna sun yi jawabin godiya ga wannan kungiyar sannan sun gode mana Bisa yadda muka basu had'in kai har muka koyi abunda ake so mu koya har kwalliya ta biya kudin sabulu.
Daganan sai suka koma gefe suna mganganu bayan minti goma aka sanar da kungiya ta ware zakaru guda goma da kungiya zata bama tallafi,Sauran kuma da ba'a basu ba,ba domin ba su kai ba ne a'a haka tsarin kungiya take suma nan gaba zasu iya samu.
Gabana sai ya fara fadi na riga nayi yakinin ko ba'a bani ba bazan bari abunda na koya ya tafi a banza ba sai ga shi nice ta Biyu Fa'iza sidi karofi Hawaye sharr suka zubomin na kasa sharesu bakina har kunne na fita. Kudin a Farar takarda ne an nade sannan ga sunan kungiyar ajiki Hajiyar su Raliya ta bani na Duka har kasa zan karba sai kawai na Daidaici gabas duk da goyon Ahmad dake bayana ban damu ba nayi Sudujul Shukur sai Hall din ya Dau Tafi da kabbara ina dagowa ina hawaye Shabe shabe na saka hannuwa bibbiyu na karb'a sai ta bani abun mgana tace nayi godiya,muryata ta shake ga kuka sannan ga yanayina cikin mganata nace"Alhandulillah ya Allah Godiyar ta sace.Domin abu mai kyau ko akasasin sa daga gare sa ne,Ina godiya ga wannan kungiyar na gode..Madallah da mutanen kirki, madallah da mutanen kwarai masu karamci.
Nagode Allah ya jibanci lamuran ku, kamar yadda kuka jibanci namu Allah ya suturtaku kamar yadda kuka suturtamu Allah ya albarkaci dukiyar ku da ya'yan ku da iyalan ku gabadaya, Allah yasa wannan aikin taimakon naku ya zama mizanin ku a gidan Aljannah..Nagode Nagode, na yaba ubangiji ya gani sannan yafini yabawa"
Ina ma wannan kungiya fatan alheri Nagode"
Duk da mganar bata fita sosai ammh sun fahimta sai tafi su kuma suna ta amsawa da Ameen,ina tahowa muka had'e da Badariya muka Rungume juna Fadi take"Congratulation Anty Fa'iza"
Ahmad da yaji matsa sai kuka na Sauke shi ta Dauke sa ta dagasa Sama tana fadin"Kai yau ranar farin cikin Umman ka ne ba kuka"
An ta kiran sauran ana basu suna addu'a mata da yawa muna cikin wata Rayuwa masu kuka in an basu suna da yawa,asauran da ba'a basu ba suma ance kungiya zata san abunda zatayi musu daga karshe sun horemu da mu tashi Tsaye mu mori abunda muka koya, acikin Gidajen mu da kadan kad'an watarana sai mu zarce Tunanin mai Tunanin sun Hore mu kada mu zama ballagazun mata mu zama mata wad'anda zasu iya shiga ko'ina saboda kansu da ya'yansu. maraici ba komai ba ne in dai mace ta mike ta nema to zata samu da yardan Allah,Sannan sun horemu da mu gyara kanmu mu zama masu tsafta da kwalliya da ado saboda kada mu zama Borori a gidan mazajen mu, ni dai ban bi ta kan wannan mganar ba saboda da mata masu kyau da nasaba ake yi ba irin mu da muka ke da nakasu a komaii ba, abu daya na sani wannan wajen da nazo ya kara Budemin ido akan rayuwa na Fahimci harkan nema ba bambamci mai kyau ko mara kyau in ka iya kawai ka Huta.
sai biyu na rana aka tashi Taron Haka Badariya da Raliya suka rikamin Gayya gayyan kawayen su muna gaisawa,Badariya ko bata gajiya da Fadin matar yaya na ne fa Sai naji wani abu ya soki raina ko yayan nata bai taba nunani haka acikin mutane kamar ta ba, shiyasa nake kaunar Badariya kwatankwancin yadda take kaunata.
Nayi sallama da matan da muka saba dasu yayin koyan abubuwan da muka koya,Ban samu ganin Hajiyar su Raliya ba suna cikin mutane sai nace Badariya ta bari ta rakani har gida nayi mata godiya.
Ranar saboda farinciki ina komawa gida na tasa kudin nan a gabana ko Bude su ban yi ba ina ta ma Allah kirari da Hamdala,Yara suna Dawowa makaranta na rika daga su sama ina Juyi afalo fad'i nake yi"Umma tayi nasara ya'yan Umma..nayi nasara"
Sai suma suka rika murna suna tsalle Har da Amir ma kamasu na Rumgume hawaye suka gocemin komai na zama a duniya ya'ya ne karfina da ba domin su da ban san kuma ya zan yi ba.
Na shiga gidan sa'adatu washegari nayi mata godiya kwana uku tsskani Badariya tazo mukaje gidan su Raliya chan kusa da anguwan su Anty mahma ce nayi mata godiya tana yaba'min har tace Raliya ta kawo mata alala yayi dadi suna bada girke girken Suna ko Birthday, ko biki in sha Allahu Zata saka arika nema na nace nagode sannan tace nayi shawara da mijina ko yan'uwa na samu wani abun sana'a na siya da kudin hannuna wanda zai taimake ni kada na kashe su a banza nace mata in sha Allahu,muka yi mata sallama ta bani sabulai da Turare kamshi da kudi tace na siya ma Ahmad sweet muka fito ina ta yaba kirkin matar a hanya nace Badariya in ta na da kudi a waya ta kira mun Goggo tace tana da shi,ta ko daga waya ta kirata bayan ta Dauka ta ma zata Hafsat take nema sai tace mata tana bayi
Bayan sun gaisa,Sai Badariya tace Fa'iza ke son mgana da ita.
Yadda Goggo ta jini cikin farinciki yasa ina cewa ina son ganinta tace"Zan zo in sha Allahu gobe daman kamar kin san cikin satin nan nace zan leko na dubaki,najiki cikin farinciki fa:i daga gani wani babban albishir ne ko Ishaq ne ya biya miki Umra".?
Bansan Lokacin da na kyalkyace da Dariya ba,Itama nasan zolayata take yi.muka rabu akan sai tazo, daganan Badariya ta nufi gida nima na Dawo gida.
Kwana Biyu tsakani sai ga Goggo Ya Isa ya kawota da Safe bayan mun gaisa na basu ruwa na Dauko kudin da Kyautar da aka bani da Takardan shedan abunda muka koya, na sauke gabanta lokaci d'aya na kora mata jawabin komai bakina har kunne Goggo ta Dauki kudin ta farke ta Fiddo su sabbin yan Dubu Dubu ta nuna ma Isa tana fadin"Isa kaga Bud'i daga Allah ko..?.
Yaya isa ya karba ya gani duka kayan ya jinjina kai kafin yace"Lalle Fa'iza na tayaki murna dakyau"
Goggo tace"Duka kyauta Fa"iza..?
Na gyada kai ina Mirmishi Goggo tace"Masha Allah..Allah ya saka musu da alheri Allah ya biya su kudin nan sunzo a daidai daman mun yi mgana da Sauran yan'uwanki nace su had'a miki kudi wanda zaki rike ki fara wata sana'ar zama haka bazai yuyu ba,sai kuma muka ga abun alheri ai shikenan ma fad'uwa tazo daidai da zama kenan"
Goggo tace na ijiye kud'in zata koma in na chan sun hadu zata sake dawowa,na tambayi Goggo dame zan fara na sana'a?
Da sauri Yaya Isa yace"Ki fara da sai da zobo da Kunun aya, da ruwa tunda kin koya kuma kin iya sauran sana'o'in ko daga baya sai ki fara bazai gagara ba"
Nima na yarda da shawaran sa haka ma Goggo sun tafi da niyar goggo zata kawo min kudin in su hada na bangaran su.
sai na had'a dashi Tare da Yaya Isa zasu kara dawowa.sai ayi shawaran Fridge din da za'a siya mai kyau, wanda zan fara sana'ar dashi.

*TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWAR ZAKI YI AMFANI DA ITA SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*..









*Janafty**KANA NAKA..!*

*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*

*Madallah da gidajen Sada zumuntar dake cike da mutane masu karamci,Naji dad'i sosai ina ganin sharhin ku Janafty tace Son so.*

*JANAF NOVELLA.*
*SURRAYYA DEE FANS.*
*KANA NAKA COMMENTS SECTION.*
*SABO DA KAZA COMMENTS SECTION.*
*TAKORITES.*
*JANAFTY'S.*
*JANAFTY GIVEAWAY ROOM.*
*ZAUREN KHADIJA CANDY.*
*KITTY NOVELS.*
*BENEFICIAL WRITERS.*
*FEEDHOM NOVELLA.*
*MY WATTPADIAN PIPU,FA'IZA TACE SANNUKU DA KOKARI.*

*Kuna da yawa baki ma bazai kirga adadin ku ba,ammh Fa'iza taji kuma ta gani,tace na fada muku ana kyawun tare.*
*Tagode kwarai Allah ya bar zumunci da kauna*

          *🅿️20*

Ranar da Goggo suka zo suna tafiya,da yammah sai ga Yaya Ishaq ya dawo,wanda rabon sa da garin tun zuwan da yayi muka yi sa'in sa kan Fita, gashi har mun gama.kimanin wata uku kenan baya nan, ammh a haka har yana da kwanjin son ya zaunar dani a gida, sannan yana da bakin fad'in mgana kan ya'yan sa. ya'yan da in ya saka kafa ya tafi mantawa yake yi da su, ba domin Allah da Dubaran mu na mata ba,da Tuni wata mganan ake yi ba wannan ba.
A she tare da zainab suka zo ban sani ba,Sai bayan ya fita ya dawo da Daddare yaran suka nufesa suna murnan ganinsa ni bai min mgana ba ko a d'azun da ya shigo na gaishe shi bai amsani ba sai dai ya kalleni ya kauda kansa, sai dawowar da ya sake yi ne bayan ya raba ma yara tsaraban Sweet din da yazo musu da shi, ya fito yana fad'amin na shirya yanzu ni da yara zamu gidan Mama na gaida Zainab tayi rashin lafiya an yi mata aiki an cire mata tsakuwar ciki, da kamar zan ce bazani ba. sai kuma na fasa ban yi mgana ba yaran suna ta murna ni kuma sai na Had'e rai na ko Kyallin Fara'a ta bai gani ba.
bayan sallar isha'i yazo ya kwashemu sai gidan Mama.
Naga abun mamaki Mama haka take rawan jiki akan Zainab da Farhan kamar zata kwanta mata,afalon Mama muka sameta an kara mata filo ta ma fa warke,ammh Mama ji da ita take yi shiyasa taki bari ta sauka a gidan saboda acewarta na fara halin gantali bazan kula da ita ba sosai gata ba ta da lafiya mun zo ba Dadewa sai ga Anty Binta ta iso itama dai kamar Maman kamar zasu maida Zainab ciki
ni dai Farhan na dauka ina mamakin girmansa har ya fara Tafiya fari da shi Dumur mur kamar yaron Turawa ko da yake meye maraban sa da Turawan..?sai bangalamin Dariya yake su Anum suna mai wasa yaana kara sakin Dariyan su na yara.
Mun gaisa da Zainab nayi mata sannu ta amsa min ina d'an nesa da ita ne bayan mun gaisa sai na sauya wajen zama ina rike da Farhan a hannuna Anum tazo ta rikemun hannu tana fadin"Umma Anty tace kizo"
Sai na Dago ina kallon Zainab sai ta yafito ni da Hannu da zan tashi sai Farhan ya sauka kasa yabi Anum da ta mai chakulkuli ta gudu ,gefenta na samu na zauna ashe Mama da Anty Binta suna kallon mu bansani ba.
Gaisuwa take so tayi min bayan ta muskuta daga zaunen da take ta kalleni tana fadin"Kwanaki Honey yake fadamin maman ki ta rasu ko..?
Sai na jinjina mata kai cikin Tausayawa tace"Ayya sory for d lost..Allah yajikanta da gafara"
Da karfin gwiwa na amsa mata da Ameen,ita ta cigaba da ja na da Hira ni sai dai nayi yaken Dariya sai korafin take yi ban taba zuwa Abuja ba, ammh ita tazo ta sauka wajena yafi a kirga ina Dariya nace"Megidan ne bai taba min tayin zuwa ba"
Cikin mamaki tace"Kai.!Ni kuma Honey ce min yayi kece baki son zuwa fa"
ban yi mamakin mganarta ba,sai nayi Saurin cewa"Na bari sai kin haifa ma su Anum kani tukunna, Farhan ya girma yana bukatar kani ko k'anwa"
Sai ta zabura Lokaci d'aya tana Fadin"Aa bazan iya ba maman Amir ai ko ke naga kokarin ki da'yan ma is ok"
Ni dai ina ta Dariyan mganarta a raina nasan zasu kwashi yan kallo da Yaya ishaq shi da mafarkin sa kenan auran mace mai kyau da samun ya'yan Turawa,ga shi ya samu sai kuma ya fara ganin mike ai bazata sabu ba,Anty Binta da Mama kamar su mutu da bakinciki ba so su Zainab din ta sakarmin ba sun so yadda suke min wulakanci itama ta wulakantani sai Allah ya fisu.
Ammh duk da haka basu kyaleni ba, su dai in basu tozartani ba basa jin Dad'i a gaban Ishaq din da Jamal da yace cikin satin nan ya dawo Badariya ce kad'ai  bata nan tana gidan Anty mahma,Allah yasa yaran suna chan suna wasa hankalin su baya kanmu Mama ta kalleni cikin yanayin kaskancinta gareni tace"Ke kuma wani gantalin kike zuwa kwanaki Binta tayi ta zuwa bakya nan..?
Sai na maida kaina kasa na kasa mgana Domin nayi alkwarin bazan ce mata komai ba..
Anty Binta ne tace"Ai bazata fada miki ba ta fara zama gagararriya.Shi kan Shi Ishaq din ta fara fin karfinsa,da na kirasa na fad'amai ga halin da ake ciki bude bakinsa sai cewa yayi na kyaleta tayi duk abunda taga dama"
Mama tace"Uhm nima ai haka ya fadamin sai na kawo ido na saka musu daga shi har ita.Ni damuwata d'aya in ta fice ta bar masa gida ba kowa a shiga a sace wani abu ai shi ke da asara ba ita ba"
Kaina na kasa ban dago ba araina nace ina abun sata a wannan gidan..?shi kan shi yasan bai ije komai ba kamar yadda ban yi mgana ba shima kala bai ce ba sai faman dannan waya yake yi ita kuma Zainab waya aka kirata daga gidan bata tashi daga Falon ba ammh ta sauya yare zuwa Fillanci..
Nan Mama tayi nata cin mutumcin Anty Binta na tayata daga karshe Mama tace"Ai tunda Uwar su ta rasu naga tana wani tashen iskanci, mutuwa ai d'ayace kuma duk abun ki dai baki isa ki dawo da ita ba.Ni Allah na tuba mq cewa nayi gwara da ta rasu ta Huta rayuwa ko'ina ba inda tayi kyau"
Subhanallah na fada a fili na Dago ina kallon Mama bata damu ba tacigaba da Fadin"Shiyasa yana kirana yace suna tafe nace ya sauke Zainab anan yadda bata jin dad'in nan ga shi Fa'iza kuma ta saka Mugunta a ranta ai sai ta bar Yar mutane ta shiga wani Hali mu shiga uku"
Anty Binta tace"gwara da kika yi haka Mama"ni dai ban ko kara Dago kaina ba,zaman duk ya isheni ga shi Badariya bata nan zainab kuma tana gama waya ta tashi ta shiga ciki zata kwanta Yaya ishaq ya bita har sai da na gaji da jiransa sannan ya fito yaran har sun fara barci,Mama Tuni ta Dauke Farhan ta shiga da shi Ciki Musty da Ahmad ne suka yi barci nan saman Cafet ammh Mama bata damu da su ba,Anty Binta ta rigamu tafiya mu bayan mun fito Mama ta kira Yaya Ishaq ya koma ciki fiye da minti goma sannan ya fito muka tafi har muka isa gida ci kanki bai ce min ba nima haka, Domin naga yana wani shan kamshi ne da cin mgani a raina nace Indai ta fa'iza ne kayi a banza domin ban ma san ka nayi ba.
A satin yara suka yi Hutu daman sun gama jarabawa,karshen Team,Na lura wannan karon zasu dade tunda bayan zainab ta kwashe Kwana hudu gidan Mama sai ya maidota gida nan shashen shi inda ta fara sauka,su Anum nata murnan Farhan ya Dawo gidansu da kuma suka Dawo sai naga baya cewa nayi abinci da su, sai dai ya Rika fita yana siyo musu nima sai na kama kaina.Daman ba abincin gareni ba Shinkafa kad'ai ta ragemana itama Saboda wanchan cefanen ya siyo ta da yawa ne,Yadda bai nema ba nima ban Tusa kaina ba,Sai dai ina na shiga kullum da Safe mu gaisa da Zainab wani Lokacin ita takan fito falo mu gaisa har mu taba hira tana da Sakin jiki komai ta gani sai tace Maman Amir kaza maman Amir kaza.
Shi megidan nakan gaishe sa, sai dai ba kullum yake amsawa ba sai yaga Dama ni ko ban damu ba saboda ban ga abun da nayi mai masa da zai nemi kara Rataye ni a sama ba,Farhan kuma ya zama d'an wajena nike dawaniya da shi har kwana yana yi a wajena,nasan Ko Yaya ishaq din yayi mgana ita Zainab  zatace ya kyalesa a wajena Saboda ta taba cemin wai bana gajiya da goya yara da Dawaniyar su..?
Ni kuma sai nayi Dariya nace mata ina son yara, kuma Dawaniyar su bai taba bani wahala ba. cikin mamakina tace zata kawo min Farhan nan da zarar ta yayesa bata son wahala ga aiki bata zama Allah yasa ma tana da mai renon sa ,ko ta kaisa gidansu a bakinta nake jin dukkansu sun samu Hutu ne shiyasa zasu fi sati kafin su koma.
Ranar da suke da kwana takwas da zuwa sai ga Goggo da Yaya isa,ya sake kawota na rika ina zan saka da Goggo da tazomin da su garin kunu garin Tsaki da garin masara,yaji kayan kamshi wake mangyad'a da su manja,sai garin Danwake da Taliya yar Muji ina ta Murna sai dai ashe zan ninka Murnata Dubu Dari.Goggo ta kawo min tace Dubu Hamsin ya'yan Dakinta suka hada'min Dubu Hamsin yan'uwana Yaya Asiya da Yaya Mariya har da Hafsatu ta saka Dubu Biyar kunsan na fada muku tana kunshi kuma Sosai take da mutane.
Kuka ya gocemin na karb'i kudin ina Fadin"Duk ni kad'ai Goggo.?
Goggo tace"Duk Fa'iza ita kad'ai yar gatan  Mutanen karofi sun ce ki kara jari.Allah ya sanya ma wannan sana'ar da zaki fara albarka"
Na amsa da Ameen ina zuba musu Godiya ni muna Dakina ne ni da Goggo shi kuma Yaya isa yana falo shi da su Amir.
Sai da muka fito domin muji shawaran Yaya Isa kan abunda za'a siya,Goggo ta lura da Farhan ta tambayeni waye nagayamata sai ta rike baki tana fadin"Ikon Allah girman dan mutum ba wuya.."
Ta daukesa Dayake ba shi da kiwuya sai Dariya yake mata Goggo na shirin mgana sai ga Yaya Ishaq ya shigo falon da farko yayi mamakin ganin su Goggo, Daga baya sai ya basar ya kariso suka gaisa da Isa. ya kuma gaida Goggo sannan ya shige shashensa Goggo ta kalleni tana Fadin"Har amaryan nasa na gidan kenan..?
Nace"Eh tana ciki ko zamu je ku gaisa ne.goggo itama aiki akayi mata aka cire tsakuwar ciki fa"
Goggo bata damu da cewa bai taba kai mata Zainab ba,tace min sai mu shiga ta Dubata kafin mu wuce yanzu dai mu fara abunda ya kawomu.
Su Anum na fattaka zuwa Waje Farhan ya sauka a hannun Goggo ya Bisu duka kudin na zube ma Yaya Isa bayan nayi mai godiya sannan nace"Yaya isa ni dai a siyamin babban Fridge saboda zan fara gwada zobon da kunin ayan nagani"
Yaya isa yace"Hakan shine Daidai ne Nayi mgana da wani abokina suna kawo su masu kyau daga Parthercourt, kayan suna jirgin ruwa sun kusa isowa yanzu abunda za'ayi zan tura masa kudin fridge din da katon sitafileza,Tunda kuna samun wuta basai kin had'a da injin ba. Sauran kudin kuma sai ki rike a Hannunki saboda siyan abubuwan hadin da zaki fara sana'ar da shi ko ya kuka gani..?
Goggo ta jinjina kai kafin yace"Hakan ma yayi.Allah yasa zata fara cikin nasara"
Muka amsa mata da Ameen nan take ya kira abokin nasa sukayi mgana yace a turamai dubu Dari da Hamsin dubu hansim sai na rike a Hannuna,Muna cikin mganar sai ga Yaya Ishaq ya fito ya sake fita ko sannu bai ce mana ba, muma ba wanda ya kara bi ta kansa, kamar yadda bai taba tambayata ba nima ban taba Tunanin na fadamai komai a kan abunda na je na koya ba
Da gaske nake yi na zab'i Rayuwata da rayuwar ya'yana sama da nashi muradin.
Bayan Yaya isa ya cire kudin sai ya bani Dubu Hamsin a hannuna,sannan suka yi shirin tafiya har Goggo ta manta na tuna mata na rakata har Shashen Yaya ishaq,Zainab din na ciki ni na leka nayi mata mgana ta fito tana mika nace mata Goggon mu ce tazo Daga chan karofi, bayan sun gaisa Goggo ta mata sannu da jiki ta amsa tana kallonta Lokaci d'aya tana kallona kafin tace"Ammh suna kama da Momyn kano sosai Maman Amir"
Sai nayi Dariya kafin nace"Eh kanwartace fa Goggon"
Sai ta rike baki tana fadin Honey bai taba min mganarta ba.Dagani har Goggo yake mukayi mun kasa bata amsa,Tana tambayana yadda muke nace mata da goggo da Momnyn kano da Mahaifin su Yaya ishaq da mahaifin mu Uban su d'aya,Ta jinjina kai cikin karin mamaki daga gani bata san wani abun ba sai abunda aka nemi ta sani kawai ta sani
bamu jima ba Goggo ta mata sallama muka fito ta Daura After dress saman kayanta ta fito anan ne ma Yaya isa ya taba ganinta suka gaisa nace mata Babban yaron Goggo ne ta jinjina kai tana fadin"Suna yana yi da Honey"
Sai da ta fad'a na kara kallon Yaya isa naga suna da'n dibar kama kamar yadda ta fada d'in.
Mun rabu da su Goggo kan sai an kawo Fridge din Yaya isa zai kawo min Goggo tace na aika makotan mu na kusa nace zan fara saida Zobo da kunun aya da ruwa, saboda na samu masu siya aiko ban zauna ba su Goggo na tafiya na zari Hijabi nace ma zainab zan fita yaran kuma sukace sai sun bini Amir ne kad'ai ya zauna a gida haka na tasa har da Farhan gidan Sa'adatu na fara shiga na isketa tana yin shasshaka,kusan yara da Rigima su Anum suka saka Rigiman sai sun ci ina zare musu ido tayi dariya kafin tace"Kaji maman Amir kina zare ma yara ido ku zauna a gama sai kuci"
Dariya kawai nayi ta mana shimfidar Tabarma a tsakar gida Farhan ta Dauka tana fadin"Basu koma ba kenan..?.Sai na Daga mata kai, Saboda ranar ta shigo taga zainab din sun gaisa sai a ranar tasan ma ina da Abokiyar zama,domin ko a hira ban Fad'a mata ba.
Tana aikinta muna Taba hira cikin Hiran nan ne nake gayamata sana'ar da zan fara tayi murna cikin Murnan ne take fadin"Aiko zan aika miki kusa damu ana siya fa a baya, chan gidan akwai matar da ta zauna tayi sana'ar kuma wlh tana samun ciniki da kuma suka bar anguwan sai ba wanda ya kama gashi muna samun Wuta sosai za'a siya in sha Allahu"
A fili na furta Allah yasa daga shiga na gayamata sai ga shi na shantake ba yara ba nima sai da ta zubo mana Shasshakan muka ci da manja da yaji. sannan na Tarkata su muka koma gida Yaya Ishaq da Zainab na Falo suna cin gashashiyar kaza, yaran suka nufesu ni kuma nayi dakina Zainab ce kad'ai tamin mgana Gogan kuwa ko kai bai ma Dago ba.ni ko a jikina nasan yana mamakina ya Dauka irin da ne da zan rika binsa jikina na bari yana min wulakanci,Sai dai yanzu shi kanshi yasan takun ya sauya.
Sati biyu suka yi a katsina suka koma Abuja,har na fara sabo da Zainab sannan ga Farhan, da zasu tafi Yara har da kuka shima yaro ai yafi son inda yara yan'uwansa suke. shima Rigiman ya saka Uban ya lallashesa Dakyar,Anum kuka Musty kuka suma sai sunje sai Zainab tace na had'a musu kayan su ta tafi da su kamar zan ce a'a sai kuma naga bani da wannan Hurumin balle da naga Uban gayyar bai ce komai ba., sai na shiga Daki na Hada musu kayansu a jaka,ba masu yawa ba saboda bana so su rasa din Tahfiz din su,Allah ya taimakeni Ahmad na barci da shima za'a sha Rigima da shi.
Ji na yayi ina fad'a ma Zainab kada su Anum su jima saboda hadda Karaf ko sai a kunnensa cikin Kaushinsa ya kalleni kafin yace"Kada ki kara nuna min iko akan ya'yana Fa'iza, ki kiyaye ni Wlh"
Har yana nuna min hannu a raina nace shi kuma wannan me akayi masa..?sai nayi kamar ban jisa ba. Saboda Zainab da ya'yana yasa nayi musu Rakiya daganan gidan Mama suka biya suka musu sallama sai gida ya zama Dagani sai Amir sai Ahmad.
Sun tafi ko sati ba su yi ba Yaya Isa ya kawomin Dankareren Fridge dina da Starplayzer,murna ta kamani sai da nayi kwallah na Shafa na taba nayi addu'an da Fatan nasara da Yaya isa zai tafi nace yace ma Goggo Hafsatu tazo ina nemanta haka ko akayi washegari sai gata ita nasaka ta zauna ta Rubutamin duka abunda zan bukata, ina so mu shiga kasuwa na siyo kayayyakin mahad'in sana'ar  mai yawa yadda zai jima bai kare ba.
Kamar Badariya tasan ina nemanta sai gata tana ganin Fridge din tace"Allahu akbar Anty Fa'iza wannan abun arzikin haka.?
Ni dai sai Dariya nake yi,Farinciki ya kasa boyuwa a saman fuska ta,  albarka tayi ta sakawa itama, sai bayan ta zauna nayi mata bayanin kudin da aka had'anin Daga Korafi taji dadi tace"Allah yasa a mizani"Zuwanta yasa sai ita da Hafsatu suka dinga tsara yadda komai zai fara sun yi mganar goruna, nace ina da wasu da na tara Badariya tace duk da haka za'a karo Saboda abun fa so suke ya habaka kuma ya shahara.
Hafsatu tace"Kuma nan gaba kad'an har da Sticker zata buga a saka sunanta ajiki"
Badariya tace"in sha Allahu muna fatan ya zagaya nageria gabad'aya wannan kunin ayan da zobon namu ai ba irin nasu ba ne"
Dariya nake ta yi musu naga sun fi ni zagewa,Ranar bamu je kasuwan ba sai Washegari Badariya ta dawo muka tafi mu uku dayake nasan abubuwan hadawar shiyasa sai siyayyan bata Dauki Lokaci ba kudi basu fi dubu Goma ba suka Rage bayan mun Dawo gida mun siyo sabbin Goruna,na wajena wanda na Tara Hafsatu ta wankemin su tas a daran na Dafa ganyen zobon da Safe kuma na Had'a shi ni da Hafsat muka dura su a gorinaa muka saka su acikin Fridge dayake ba waje a kitchen falo na ijiyesa, kunin aya kuma nace sai naga yadda wannan ya fara karbuwa Ruwa daman Tun jiya Hafsatu ta saka aka siya aka Dura aciki.
Bayan yayi sanyi na Dauka na aika ma Sa'adatu da Habiba guda uku uku, Dayake Hamsin hamsin nayi saboda Farkon Farawa ne,Shi lamarin Ubangiji daman haka yake ballatana ga wanda yasan Allah ke yi sannan ya maida lamarinsa a wajen sa, cikin Sati uku da fara sana'ata sanu a anguwanrmu,balle su Sa'adatu sun ta min tallah,Da D'aya d'aya Biyu  biyu aka fara zuwa siya sai gashi an gane ni, da ina yin na mudu da rabi na zobo sai na Dawo na Tiya har da rabi,Ni kad'ai nake abuna Hafsatu ta koma gida Karofi Satin su Anum hud'u babansu ya Dawo da su kwana D'aya yayi ya koma kuma yaga komai tunda yana gidan masu siye siye suke shiga suna fita yadda bai min mgana ba nima ban damu da yasan komai ba,To ina ruwan kaska da kifi..?
ni alokacin ma Sabgan gabana ta isheni.
Ko wata biyu ban rufe da farayin zobo ba na fara had:awa da kunin aya, Ruwa kuwa Mota ke saukemin Haruna yayi min Hanyar motar ruwa take kawomin har Kofar gida tana Saukemin.Saboda Hidiman yara sun koma makaranta yasa sa'adatu takan shigo ta tayani Wani Lokacin kuma Badariya na lekoni,Itama ta bangaranta ba abunda zan ce mata sai godiya tunda taje da shi makaranta kawayenta suka sha suka fara santi, Tundaga b'atagwara suke zuwa siyan zobo na da kunin Aya na, Har kuma Lokacin Mama ko Anty Binta basu san  halin da ake ciki ba.
Ban rufe wata shidda da fara wannan sana'ar ba,na sanu sosai a rana na kanyin zobo fin ma Tiya hud'u kuma ya kare,Sannan na chaba Lokacin azumi nayi ciniki,sai na Dafa zobo sau biyu arana kunin aya kuwa na Tiya Biyar shidda duk yana karewa Musamman daga gidansu Raliya Direban  su ke zuwa ya siya fin na Dubu uku in ji Hajiya balle da yake sanyi ga Dad'i ga gard'i sannan cikin Tsafta ba kazanta.
Na aika da shi har Karofi Goggo da su Yaya mariya sun sha sun kuma saka albarka,Yaya Asiya ce kadai bata sha ba tayi nisa,na yarda da mutane da suke fadin in kana da abun yi na sana'a damuwa ma bata da wani muhalli a wajenka,to hakan ne ya faru dani ne, ni mantawa ma nake yi da ina da wata matsala tunda nasan dadin Goma Biyar shikenan Rayuwata ta sauya Daga duhu zuwa haske cikin Lokaci kalilan Allah ya Daukakani,Sannan nayi amfani da Damar haka na tallata ma mutane na ina had'a Turaren wuta humra da na Kamshin Daki, da kwallacha sannan ina yin Dikar Amare da Halawa.
Duk da Ribar zobo da kunin aya na siya kayan amfanin wannan bangaran,Aiki na farko da na fara na Hajiyar su Raliya ce diyar kanwarta zatayi aure ta bani kwangilan had'a Turaren wuta na Rushi da na Humra,Sannan ni nayi ma Amarya Gyaran jiki,kuma ta bani kwangilar abinci,Kafin na rufe shekara na yi suna ta wannan bangaran Domin ina yin Girki a gida in dai bai wuce Takeway ashirin ba ko Hamsin,in ya wuce haka sai dai naje gidan masu sha'anin sai dai bana kwana wasu ni nake siyan komai na girki sai dai su bani kudin a Dungule in kuma yana da yawa sai dai na amshi kudin sallama.
Taimakona D'aya da Hafsatu ta gama jarabawarta ta Dawo wajena ta na taimakamin,Su Mama sun ji na fara sana'ar kunin aya da zobo, to azaton su Sana'ar bata D'ore ba shiyasa basu damu ba.shi kuma Yaya Ishaq yana ganin komai ammh kamar an Daure masa baki bai taba min mgana ba, nimana zama Busy women ban da Lokacinsa balle na tsaya masa bayani.
Sai dai na gayamai sana'ata ta jama'a ne,sannan ina zuwa kasuwa kuma in fita ta kamani ta bangaran kwangilan girki zan fita,sai yace min ai na zab'i Rayuwata sama da aure nayi duk abunda naga Dama babu ruwansa dani,tunda yace haka na fita Sabgan sa,to ni zai gayama aure..?
Auran da a D'ofane ya ke..?
Daganan ban kara bi ta kansa ba harkan Gabana nake yi,Ya'yana kuwa ba na yarda na shiga Lokacin su ko ya yane ina basu Lokaci na domin sune dukkan karfin gwiwata.

*******

*BAYAN SHEKARU BIYU..*

Katsina.
*Layout*
8:12pm.

Zaune nake saman sabon gadona da ban jima da sauyasa ba,ina ta had'a kayana da kwanakin nan nq maida Hankalina wajen hadasu waje daya. Duk wani abu daya Danganceni in dai nawa ne,wanda kuma bai da alaqa da ni,na bar shi,ina cikin zakulo kayan Wardrope dina na chan kasa kasa da na jima ban saka su ba, naci karo da ledan kayan da Anty Binta ta taba bani na Fadar kishiya auran Zainab.
Wanda Yaya ishaq ya yi min kusan shekaru Biyar da wani abu ko Kallon su ban karayi ba,Bayan su ma akwai wasu na sallah da Mama ta tab'a aikomin sau d'aya,suma din banta Amfani dasu ba,na rika ware su agefe nawa wanda na d'inka da gumina da wanda yan'uwana suka Dinkamin ina ware su a gefe daya.
Kamar wani abu ya shiga kaina sai na Dakata na koma nayi Tagumi da Hannuuwana Bibbiyu.shin hukuncin da nake shirin Dauka bazai shafi rayuwata da na ya'ya na nan gaba ba..?
Sai wata zuciyar tace"Ko ban zabi hakan ba.Hakan ya dace domin babu amfani cigaba da zaman".
Da haka na kara samun yakinin cigaba da aikin gabana,Ban ji shigowarta ba sai ji nayi an fad'omin a saman kaina har sai da na Tsorata Ina Dagowa naga Anum sai na bata rai ina Fadin"Bansan sangarta ke har gobe baki girma Anum..?
Baki ta tura kafin tace"Umma yaya yace ki zo lokacin karatu ya kusa"
Agogon dake dakina na Daga na kallah, karfe takwas da rabi ya wuce da sauri na Dafe kaina kafin nace"Ban san lokaci ya tafi ba,muje kada Mallam Amir yamin Bulala"
Dariya Anun ta farayi lokaci d'aya tana fadin"Umma sai Yaya ya dake ki..?
Ina Dariya nace"Sosai malami na ne fa, in na makara zai min Bulala"
Itako abun ya bata dariya ina rike da Hannunta har tsakiyar falona,Wanda ya sauya yanayi a baya kujerun duk sun mutu da Cafet d'in ammh yanzu na Sauya sabbin kujeru da Italian Cafet sannan na sauya ma falon da Dakunan Sabon Fenti na siya ma yaran Sabon Tibi,Ko a yanzu ma Mbc3 ke aiki shi kad'ai ,Ahmad ne ke saka rigiman sai an kunna masa.
Kanwata Hafsatu na kalla dake kan kujera ta kishigid'a da katon katakon ta na yanka salatif, Anum nace ta yanka ta yi mawa da Daddare nagaji da ganinta da Farar kafa,Musty na zaune a kasa inda Karamin allo yake kafe a Tsakiyar falon,Amir na kallah dake tsaye yana faman rubutu da Alli.
Hafsatu ta Dago tana fadin"Umma ta makara yau"
Ina yar Dariya cikin yanayina nace"laifin ki ne.da baki ankar dani akan Lokaci ba"
Zama nayi a kasa kusa da Musty,ina leka abunda yake rubutawa a littafinsa cikin dariya yace"Umma zane nake yi"
Fuska na gyara kafin nace"Sarkin zane fa to me ake zanawa yaron Umma?
Da Sauri Anum ta leka sai ya Boye yana bata rai,ta na kokarin kwacewa ganin sun fara kokawa sai na Raba fadan ina fadin"Anun koma ki zauna yaron Umma nuna min abunda ka ke zanawa.?
Sai da ya boye kada Anum ta gani Gida yake zanawa mai kyau daman Tunda Musty ya fara wayau bai da aiki sai zane zane ni kuma in dai nayi sallah sai na rokar masa Allah yasa zane zanen ya zama Hanyar cin abincinsa..
Karb'a nayi na Dubawa lokaci d'aya ina fadin"Kai kai..Wannan gida ya had'u chanchad'i"
Cikin nishadi yace"Umma irin wannan gidan zan gina miki,in na girma nayi kudi"
Na kalli gidan sannan na kara kallon Musty wanda yake cikin shekaru na takwas har da wani abu,Kansa na Shafa ina fadin"Allah ya ida nufi yaron Umma,ka cigaba da dagewa da karatu watarana buri zai cika in sha Allahu"
Anum na tura baki tace"Umma ni fa nace zan gina miki gida"
Ina jin haka sai nayi dariya nace"To shikenan ke sai ki siyamin mota"
Da sauri tace"Aa Umma sai dai Jirgi"
Ina jinjina kai nace"Lalle waya ga Umma ajirgi babban mgana"
Dariya na saka suma suna tayani Amir daya gama Rubutunsa ya tsaya kikan bayan ya goya hannuwansa a kirji kamar wani babba,da muryansa da ta fara tashi daga na yara zuwa na manya ya fara fadin"Umma kin makara kuma kin zo kin ta sa ya'yanki kuna ta surutu"
Da Sauri na kama bakina ina fadin"To Mallam ayi mana afuwa kai kowa ya kama bakinsa"
Da Sauri suka ko kama Hafsatu na gefe tayi Dariya tana fadin"Umma da ya'yanta"
Juyowa nayi ina nuna mata Amir ji nayi yace"Umma.."
Da Sauri nace"Anty Hafsat ce ba ruwana"
Kai ya girgiza kafin ya juya yana kallon Ahmad sannan ya kara juyowa yana fadin"Umma kalli d'anki bai da aiki sai kallo"
Ahmad muka kallah da ya bada hankalinsa kan abunda yan aljanu suke yi a tibi ko jin mu ma ba yayi Dariya ta na Danne ina fadin"Ayi masa afuwa Mallan yaya"
Sai ya juya da yar sandansa yana fadin "Zamu maimaita karatun mu na jiya Umma ki karanta min"
Sai na gyara zama kalmomin Turanci ne da ma'anar su.
Na fara karantawa daga Number 1,kamar haka.
Mother _Uwa
kenan da Hausa.
Na biyu kuma Son_Yaro da Hausa.
Na uku kuma Brother_Yaya.
Husband_Miji.
Wife_Mata.
Sister_yar'uwa.
Uncle_Kawu.
Grandmother_kaka.
Mother inlow_Uwar miji.
Sister in low_Kanwar miji
Friend_aboki.

Tsab na karanta duka kuma na fassara Amir ya kalleni kafin yace"Please clapp for  Umma"
Sai tafi Raf raf har da Hafsatu cikin masu tafawa cikin jin Dadi nace"Mallam na dauke wad'anan sai na gaba kuma"
Sai ya jinjina kai ya goge wannan ya sake Rubutu wasu.
Sannan ya shiga karantawa yana Fassarawa.

Beautifull_mai kyau
Handsome_kyakyawa.
Marrige_aure.
Divorse_Saki.
T.Shrt_Riga.
Trolley_akwati.
Money_kudi.

Bayan ya gama karantawa sannan yace mu amsa bayan shi,da ni da su Anum muka bud'e murya muna amsawa bayan mun gama yab''i daya bayan daya yana mana bayani kowacce kalma da ma'anarta da Hausa kuma sosai na natsu ina ganewa lokaci da'ya ina kallon Amir daya girma shekarunsa yanzu sha Biyu a duniya ya gama primary zai shiga Jss1 ne,Anum kuma tana shekaru na goma ne Musty takwas Ahmad kuma shidda,Sosai na ke karuwa da ilmin ya'yana Tuni nasan kalmomin turanci irin su come,Sit Down,standdup,zagi ma nasani da Turanci,Nima fa yanzu ba wani karamin kalman da za'a fadeta da Turanci wacce bana ji.
sannan ina kan koyan sanin kalmomin Turanci masu saukin Fad'a da masu ma wahalan,Amir ke koya mana ni da yara Kokari garesa sosai kokarinsa har ya girmi shekarunsa. ina jin su ya tada Aum tana karantawa ni kuma nayi Tagumi ina kallon ya'yana sannan ina auna Shekarun da suka gabata.yadda na sha gwagwamarya da kuma yadda Daukakan Allah ta sameni Lokaci daya.
Ina nan a fa'iza ta yar gargajiyata saboda ko zan sauya a komai Tunanin ado ko kwalliya basu dace ga mata munana irina masu nakasun hallita har yanzu bai bace daga tunanina ba,Sai dai ni Fa'iza na samu cigaba ta Fanni Rayuwata gabad'aya yanzu haka bazan ce kaf katsina ba ammh rabinta da kewayanta sun san wacece *SAFMA* Ko Fa'iza sidi karofi mai Turaran kamshi da dilkan amare Safma sunayen ya'ya na ne da ni kaina nake amfani da shi, a Kunin aya na da zobo sai kuma Ina saka Sticker ajikin Turaren wuta ko kwallachaa,Sannan ina amfani da shi wajen girken girken da nake yi na Birthday ko na suna ko wani biki wanda in nayi shi a gida,acikin Shekaru biyun da suka gabata ban san irin godiyar da zan yi ma Allah bisa tarin Ni'imarsa ba, da a baya Naira Biyar ma  sha'awa take bani ammh ban da yanzu da na rike manya manyan kudade basan adadin su ba, 
Yanzu haka na bude acct inda nake tara kudad:e na,Sannan na mallaki wayar hannu Badariya da Hafsa sun yi matukar kokarin wajen koyamin yadda zan yi amfani da ita, sun kuma Bude min shafuka a instergram da Sauran su da sunan SAFMA,domin inganta sana'a ta suma ba'a bar su a baya ba wajen tayani tallata sana'ta.
Ni kaina bazan iya kirga mutanen da nake hulda dasu ba yanzu,Sannan bansan adadin costumer na ba, abu da'ya na sani in yau nayi ma wata aiki gobe sai ta kawomin uku daga bayanta saboda na Tsaida gaskiya sannan na rike Allah.
Nasan bani da kyau sannan bani da gata,ammh kuma ina da baiwa duk wanda na hadu da shi mu'amalan aiki ta had'amu shikenan mun zama D'aya Baban katsina ya Dad'e yana cemin ina da baiwa ban sani ba sai yanzu in na Duba kaina ayanzu da ban jiran ayin komai da ni da ya'yana, sai na Tuna Tamadina naso tana raye na jiyar da ita dadin Duniya?sai dai ban manta da ita ba ina yawan mata Sadaka da fatan Allah ya jikanta da Rahma.
Matar da ta fara zame min uwa ita da ya'yanta a garin katsina itace Hajiyar su Raliya da ya'yanta ita ta zamemin makwafin Mama a garin nan ta Daukeni kamar yarta duk wani Cigaba ta bangaranta na fara samu ya'yanta da yan'uwanta a Dangi suka D'aukeni nima sai na Daukesu a Dangina ballatana da ta Fahimci halin zamantakewar da nike ciki sai ta zama tsanin dukkan wani Cigabana.
A yanzu haka kaf danginta da zuru'arta ni nake had'a ma ya'yansu turare da gyaran jiki in za su yi aure,Sannan ni nake yi musu kwangilar girken girken sha'aninsu suna zuwa wajena kai Tsaye nima ina zuwa wajen su kaina Tsaye sun daukeni dagani har ya'yana ahalinsu susan yan'uwana da Goggo suna zumumci da su Hajiyar su Raliya mace ce mai mutumci da Sanin Darajan Dan adam, kuma ko da nake da abun hannuna a yanzu ni da ya'yana alherinta bai taba yankewa a gareni ba.
Haka ma Badariya itama bazan manta da ita ba, Ita ta fitar da Zobo na da kunin aya na a jami'ar su ta Umaru musa yar'aduwa aka sanni na zama Dila ana sara, ni yanzu kusan in ba na gida gida da suka saba siya makota ba, na daina saida zobo da kunun aya rabe rabe sai dai a sara kamar D'ari ko sama da haka.
ballatana yanzu da Hafsa itama take aji daya a jami'ar itama tana zuwa dashi kuma ya kare,Har ta Yaya mariya duk sati tana zuwa ta karb'a Saboda ta fara yi da kanta sukace sun fi son dan'danon nawa sai kawai ta koma tana sara a wajena.
Ta ko'ina budi ya budemin na Roki Allah mafita kuma ya bani sannan na rokesa albarka acikin lamarin shima ya sakamin,Yanzu har ma'aikata na Dauka su uku suna taimakamin wajen hada zobon da kunin aya sai Sa'adatu da ita nake biyanta duk wata Saboda tana taimakamin kuma bazan manta da alherinta ba.
Sannan kuma Dawowar Hafsatu wajena sai itama na jawo mata Mutane Saboda Ina gyaran amare ita kuma tana kunshi sai gidanmu ya zama wajen shige da Ficen mata manyan masu abun hannuwan su,
Ni da ya'yana mun daina jiran wani ya yi mana ko ya bamu,na daina jiran kowa,ko Kudin makarantar su na biya musu ya kai su biyu,mganan kayan abinci da Cefane mantawa nake ma ina da Miji,na riga na saka ma raina ni kad'ai ce sannan ni ce uwa da uban ya'yana.Iyakata duk abunda naga zai yanke min na shiga kasuwa na siyo.
Ishaq ya dad'e da sanin Fa'iza yanzu bata jiran wani ko wata ballatana ta wulakanta.
Snnan ni na saka Ahmad a makaranta, naga ya wuce misali a gida ban jira kowa ba na kaisa da kaina,nayi masa registration,sannan Sauran bukatun yarana ma ba na jiran sa,ko Maman da ya saba wakiltawa ta kawo musu in taga dama.
Ya'ya na suma suna kece raini cikin Sutura mai kyau,da Tsada ashe rashin samun jin dad'i ne yasa fatar su ta Dishe da suka samu sauyin rayuwa da mayuka da sabulai masu kyau da Tsada sai ga shi sun yi tas da su, hatta  ni bakin nan nawa ya rage nayi shar dani na kara kiba kamar ba ni ba.
Don ma ban maida hankali wajen gyara ba,da kila da yanzu fa'iza ta sauya sauyawa ta sosai.
Yaya Asiya da tazo kwanakin baya ta taga yadda rayuwata ta dawomim fad'i ta ke yi "Allah mai girma.Shi yasa akace kowa yayi hakuri zai dafa dutse har ya sha romonsa,ga shi Fa'i ta dafa tana shan Romon sa"
Sai dai nayi dariya domin suma daidai misali ina taimakon su tunda ina da shi,Bangaran Yaya ishaq kuma zan iya shaidar sa ta banganran, bai taba nuna bakinciki ko hassada kan samuna ba,Kamar yadda bai tabamin mganar ta yaya komai ya fara Fa'iza..?nima ban taba gayamai ba kuma bai Damu da ya sanin ba.
Nima ba ni da wannan lokacin,sai dai shi kanshi yasan Fa'izar da ya sani a baya yanzu ba ita bace wannan Fa'izar ta samu ingantattacen Rayuwa,da sauyin da na tabbata ko a mafarki bai taba tunanin ni Fa'iza zan samu ba,sai dai shi Allah ba ruwan shi da wannan in ya tashi,Daukakarsa ba nasaba ko chanchanta yake dubawa ba,Bayi duka D'aya muke a wajensa.
Da gaske dukkanmu mun zab'i Rayuwar da muka ga zata Dace damu shi ya zabi zainab da iyalanta, nima na zabi ya'yana da sana'ata sai yayi wata uku bai zo katsina ba,ko yazo kwana d'aya biyu ya koma,ni ko baya gabana da zuwansa da rashinsa duk d'ayane a wajena,yadda baya shiga Sabgata haka nima ba na shiga tasa kowa tasa tafissheshi.
Suma yaran suna girma suna kara Fahimtar Babansu yafi son zama wajen Antyn su fiye da zama a inda Umman su take sun rage zumud'in zuwansa.
Zainab ta kara haihuwa an samu Fadil ita ta matsamin ta kuma matsa ma Mijinta naje har Abuja karo na Farko sunan fadil kuma nayi mata abun arziki kamar yadda take yi ma ya'yana Anty Binta kamar ta kasheni haka takeji sai dai ba dama Saboda Dan zaki ya riga ya girma, duk da basu daina cin zarafina  ita da Mama ba,ammh sun rage suna shakkar min wani abun ganin yarana sun girma sannan nima na wuce Tunaninsu yanzu Fa'izar yanzu ba Fa'izar da suka saba tozartawa a baya ba ne.
A sunan Fadil di'n zainab da mahaifiyarta sun sakarmim komai ni nayi gabacin girke girken da akayi kuma ba'a ji kunya ba, abokan aikin Zainab suka zo suna ta santi,Dani da yara dukkanmu mukaje mun fi Sati a Abuja,kuma Uban gayyar na Abujan lokacin, ammh yadda ban gabansa nima haka na nuna masa tuni na daina masa ma karan,Sai mu had'u in ban ga dama ba, sannu bana ce masa,shi kuma mamaki da girman kai yasa ya ke nuna kamar bai ganni ba.
kwana Goma muka kwashe  a garin Abuja Sannan muka Dawo katsina, har kums gobe Zainab bata tab'a min wani abu na Tozarci ba,sai kanwarta ita kuma ance bata kasar ta tafi kasar waje karatu.
Mama ta samu labarin Daukakata Daga sama ne, bata yarda ba sai da tazo ta ganin ma idonta komai ta koma gida tana fada,ta kira Yaya ishaq ta tirkesa kan ya barni ina tara mata agida sannan ina yawon zuwa gidaje da sunan yin girki, tunda aikin abinci sana'a ce da zai bar ni ina gantali da sunan girki.
Badariya ke fad'amin a gaban Anty Binta yace bazai iya hanani abunda nake so ba,kamar yadda shima ban taba hanasa abunda yake so ba. daganan sai ya kashe bakin su,Nasan sun yi min abubuwa da Dadama ammh ban rike su a raina ba, Mama har gaban abada matsayin uwa take gareni ina yi mata alheri sai dai bata tab'a karba ba har Atamfofi na taba siyan musu dukkan su Har Hajiyar Dala Mama ta Dawo min dashi tace a Fad'amin ban yi arzikin da zan siya mata zani ta Daura ba.tun kafin Ubana Sidi yasan kudi ta sani bazan Rud'eta da abun duniya ba.
Bana damuwa da mganganunta,Anty Binta dai ta amshe tana fadin nima haka na rika tatsan kaninta abun nasu ma kamar sun haukace Koda yaushe Goggo ke nuna min Ribar Hakuri tabbas kuma nima naga Ribar wannan hakurin da nayi shiyasa nake nuna musu komai ba komai ba ne.
To ni ina naga lokacin biye musu ma..?
Ina da abun yi lokaci na sana'ata ne da ya'ya na,ko D'an nasu da suke takama da shi Fa'iza ta daina ara masa lokacinta yanzu ballatana su.

****

Kiran sunana da Amir yake yi ne ya Dawo dani Daga tunanin da na shiga Firgitgit na sauke Tagumina ina fadin"Uhm me kuke fad'i..?
Amir yace"Umma wannan dogon Tunanin fa..?
Gyara zama nayi ina fadin"Ina tunanin watarana zakayi aure ka kawomin suruka nima"
Sai ya bata rai su Anum suka saka Dariya ya daka musu tsawa Hafsah tace"A"a kyalesu su dara Mallam"
Sai ya yi fushi ya wurgar da Sandar Hannunsa ya wuce fuu ya shige Dakinsu,Na bisa da Dariya Saboda shi yasha fadi'n bazai yi aure ba sai yayi kudi ya kaini Saudiya.
Su Anum na bari suna rubutu kan karamin allon na koma kusa da Hafsah ina fadin"Hafsah inaga fa hostel zaki koma ki fara bincikawa tun yanzu"
Sai ta dakata da abunda take yi ta kalleni tana fadin"Meyasa..?
Mikewa nayi ina fadin"Ba yanzu zaki san dalili ba.Ki dafa ma yaran nan indomie ki  hada da kwai,kuci ni cikina ya cika"
Da Toh ta amsamin tabi ni da kallo tana mamakin meyasa nake wasu abubuwan kwana Biyu haka fa Sa'adatu tace na gayamata zan bar mata sana'ar zobo da Kunin aya nan da Lokaci kad'an,kuma naki cewa komai, bayan haka Ni kaina nasan Hafsat ta fara zargin wani abu ni kuma bazan bari ta fahimci komai ba ko Goggo bata san abunda na Kudura a cikin Raina ba, har gobe ina jin bakinciki da Yayata mariya bata kara takowa inda nake ba sai dai mu had'u a karofi ko in naje gidanta tunda yanzu na samu sake Fita free,to ina ma jiran sa kenan..?
Shi da sai ya yi wata uku bai zo ba,nima ko nake gaban kaina.
ammh indai gidana ne Ya mariya ta daina zuwa tun sanda mai shi ya yi mata iyaka da shi.
Cikin Sati d'aya na gama Had'a kayana waje daya,Ranar ma cewa nayi basai anyi zobon yammah ba, na safe daga daya kare a barsa haka,Da Daddaran nace ma Hafsat gobe zan tafi karofi tare da ita su Anum kuma Gidan Mama zan kai su,mamaki ya sa ta kasa mgana nima ban kara ce mata komai ba Domin ta shiga D'akina taga kayana a had'e waje daya kamar wacce zata tashi,ko zata yi Hijira.
Ni ko da na koma D'aki sai na shiga Tunane tunane na tuna sanda na saka Ahmad a makaranta har barazana Ishaq ya yi min in ina nuna mai iko kan ya'yansa sai ya rabani da su ya kai ma Mama su,niko a lokacin sai nace mai kada yayi gaggawa ya bari Lokacin da zasu koma karkashin kulawan maman ai ya kusa,
sannan na fad'amai suma ya'ya na ne, sannan komai nayi musu ban fadi ba ni uwace garesu kuma in yana ganin don yace na kula dasu ai baya biyana, balle yace aikin kudi nake yi masa.daga Lokacin bai kara tada mganar ba.
Na kwana sallah da neman zabin Allah duk da zuciyata naso ta karye Saboda in na kallesu bansan yaya zasu ji in yau suka wayi gari bana tare dasu ba sai dai ko bana so lokaci yayi da zan hakura da rayuwa tare da Ishaq kabir karofi.
Allah mai aiko da kaddara a lokacin da yaso washegari da safe su Anum na shirin tafiya makaranta ni kuma ina dakina ina faman jan casbaha ina hawaye,Kirjina yana ta zafi Saboda yanayin da nake ciki naji Hayaniya afalo da Mganganu sama sama,da Sauri na fito da Hijabina sai naga Jamal hankalinsa tashe yara duk sun yi cirko cirko a falo.
Hankali tashe na karisa ina fadin"Lafiya Jamal me ya faru ne..?
Cikin wani irin yanayi yace"Wlh Yaya Ishaq ne EFCC suka kama shi Daga  Wajen aikin su na Abuja. tun jiya yana Hannunsu,Zainab ta kira Mama ta na kuka take fad'amata"
Sai naji na Rude yara ma suka fara tambayan me ya samu daada.
Cikin Tashin Hankali nace"Me yayi..?su waye EFCC..?
Cikin tashin hankali yace"Wata hukuma ce ta federal goverment da ke kula da sace sacen kudad'en gwammatin kasa,To abun dai kamar shiryawa akayi ance wasu miliyoyin kudi ne suka yi batan Dabo a ma'aikan su Yaya ishaq da aka tsannanta Bincike sai aka gano da saka Hannanunsa kudaden suka fita, shine hukumar tazo ta kamasa ance ko ganinsa basu bari an yi ba har yanzu.."
Sai na sulale na zauna kan kujera ina salati Amir ne yabi bayana da Salatin su Anum kuma kuka suka saka suna Kiran sunan Daada cikin kad'uwa nace"Hafsah cire mu su kayan makaranta mu..mu tafi gidan Mama"
Jamal Ahmad ya Dauka yana Lallashi ni kuma sai na koma D'akina na kalli kayana da suke had'e waje d'aya sannan na Maida su gefe a Fili na Furta"Ashe har yanzu Lokaci bai yi ba..?
Shin sai wani Lokaci ne ya Dace na Fara wata Sabuwar rayuwar..?

*Karshen littafi na D'aya*

*Nan na kawo karshen Littafi na D'aya na KANA NAKA,akwai sauran gwagwamarya,ga dai Ishaq a hannun EFCC,ko ya zata kaya..?*
*Ya matsayin aikin sa?Ina kudurin Fa'iza..?Zata tafi ne ko zata sauya ra'ayi..?ya makomar auran Zainab da Ishaq..?tunda da yuyuwar Abuja zata gagareshi shiga wannan karon?ya Mama zata yi..?Ishaq shine duka karfinta,Wani irin Daukaka ce take Bibiyan Fa'iza..?*
*Duka tarin amsoshin ku suna cikin Littafi na biyu da na uku,akan farashi mai sauki regular N500,sai kuma tsarin VIP1000,wannan karon bana son tsarin kati,a turo ta POS, akan wannan acct no din 0552179550 Jamila Umar gt bank,Zamu tafi Hutun sallah,sai bayan sallah in muna Raye zamu dora daga littafi na biyu,ammh in dan kun cika adadin ku na Mutane 250 da suka siya,ni nasan ina da masoya Fa'iza ma nada masoya ku yi Dafifi wajen rakata har border domin jin Abunda zai cigaba da gudana a rayuwarta da Ishaq,Janafty tace ta gode Allah ya hadamu a aljannah Ammen*





*Janafty*

No comments