Duk Karfin izzata Book 2 Page 51-52
💋 Duk Karfin Izzata 💋
💋The talent troupe writer's 💋
By
Star Lady
Page 51 and 52
A hankali hankali take bashi abincin abaki a mai ma kon ya ci abin cin sai ya tsare ta da ido yana kallon ta ya kasa ɗauke kan sa"yaya Prince lafiya kake kallo na haka"a hankali motsa lips nasa ya furta"kyakkyawa kyau nake kallo"ajiye spoon ɗin tayi ta shige kirjin sa tana faɗin"ai ban kai ka kyau ba"hannu yasa ya ɗago haɓarta suna fuskantar juna cikin shagwaɓa ya kwai kwayi yadda take magana yace"why kike ɓoye fuska?" "Saboda ina jin kunyar ka" "my Eshat anya ban baki ajiyar baby ba kuwa?"girgiza masa kai tayi kafin tace"aa babu baby""waya faɗa miki ba babyna a jikin ki?""babu wanda ya faɗa mini kawai na sani ne"shiru ya ɗan yi kafin yace"ya akayi kika sani?"ni dai nace maka na sani ne wallahi da gaske babu baby,yaya Prince dan Allah ni dai kaci abin cin kaji? kaga fa tun safe baka ci komai ba""kina son naci?"gyaɗa masa kai tayi alamar eh murmushi kaɗan ya ɗan saki kafin yasa hannu ya ɗauki spoon ya ɗebo abincin ya kai mata sai tin ɗan bakin ta,ba musu ta buɗe baki ya zuba mata abincin a bakin ta sanna ya haɗe bakin su waje guda ya zura harshen sa cikin bakin ta ya fara ansan abincin suna ci tare,cizan wasa ta masa a harshen sa tare da zame bakin ta daga nashi tana murmushi kafeta yayi da manya manyan idon sa na ɗan lokacin yana mai kara jin kaunar ta na ratsa duk wani jijiya da ɓargon jikin sa,ɗaukan spoon ɗin tayi ta fara ɗebo abincin tana tura masa abaki,ba shiri ya buɗe baki yake ansa tana zuba masa abaki zai haɗe bakin su waje guda ya tura mata rabi shi kuma yaci rabi almost 1h 30mins suka ɓata wajen cin abinci ya manta ma zai je kama wani ya shiga dunuyar soyayya.
Bayan sun gama cin abin cin ne ya dubeta yace"my Eshat ki zauna a nan karki bini waje munyi sallama daga nan ban yarda ko kofar ɗakin nan ki leka ba har sai na dawo"shagwaɓe murya tayi tace "yaya Prince idan zanje wajen su Ammi fa?""akoi kofa ta cikin kitchen ki bi wajen zai kai ki Part ɗin su Khalid daga nan kibi kofar kitchen nasu zai kai ki nasu Ammi amma ban yarda ki fito tsakar gida ba ki kulamin da kan ki kinji ko?zanyi kewar ki sosai na sani I love u my beautiful wife"yana kai karshen maganar ya mike cikin sauri ya nufi kofar fita yana faɗin"i need your prayer my lovely wife"zuba masa ido tayi kamar zatayi kuka zuciyar ta na mata zafin rabuwa da shi ji take kamar yana tafiya da numfashi ta kallon sa take sosai ba ko kyafta ido yana kokarin fita da murya kamar mai shirin kuka tace"my Habibi"chak ya tsaya na yan sakan ni kafin nan slowly ya juyo ji yake zuciyar sa kamar zata fashe ta fito waje,yana zin zafin tafiya da zai yi ba tare da ita ba yana tsoron tafiya da ita kar akawo musu hari wani abu ya same ta,yayi shiru yana tunani ta taho da gudu ta faɗa saman faffaɗar kirjin sa tare da sakin kuka mai ban tausayi,shi kanshi daurewa yake ji yake kamar zai yi kuka rabuwa da ita babban ciwo ne agare sa da kyar ya iya cewa"why are you crying my baby?"cikin kuka tace"my Habibi ni gaskiya sai dai muje tare idan ka tafi ka barni kafin ka dawo zan mutu" "are you sure zaki iya bina?zaki iya zama cikin sojoji?"cikin sauri ta gyaɗa masa kai tana faɗin"in dai kana wajen zan iya zama" "no Eshat idan ma mun tafi dake daga nan gidan mu na uk zan barki daga ke sai sojoji hankali na yafi yarda na barki tare da su Ammi ne that's why ban ce zan tafi dake ba idan na tafi dake zaki raba min hankali biyu ina yaki ina tunanin na barki a gida daga ke sai sojoji ni yanzu bana yarda da kowa tundaga kan Abdol na dai na yarda da kowa"kara kankame sa tayi tare da kara sankin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro"oh god"ya faɗa tare da ɗaukan ta cak suka nufi waje.
Yana fita sojojin sa suka yi saurin buÉ—e masa motar alokacin su Ammi duk sun koma cikin gida zama yayi cikin motar da ita a jikin sa,da sauri sojojin suka rufe motar suka tayar da gudun gaske suka fita gidan suna fita manya manyan motocin jibga jibgan sojoji ne suka shigo gidan dan bawa su Ammi tsaro sojoji ne manya manyan masu ji da lafiya da karfi a parking space na gidan su kayi parking na motocin su da gudu suka diro kasa daga saman motocin suka kewaye gidan gaba É—aya suka sai ta manya manyan bindigun dake hannun su kamar masu jiran wani motsi suyi harbi kallo É—aya zakayiwa face nasu ka san ba wasa a tattare da su.
BGS
Kai tsaye Airport motocin su bgs suka nufa har lokacin hiyana na masa kuka kasa kasa cikin muryan rarrashi yace"my baby wai kukan me kike ne?"cikin kuka tace"kukan daɗi nake gani ga mijina"kallon gefen ido ya mata kafin yace"kika tafi baki salami su Ammi bako ba ruwan Safras ato idan Ammi ta kiraki awaya kice mata ke dai kawai kin zaɓi ki bi mijin ki ne"turo baki tayi cikin shagwaɓa tace"wayo zaka min ka wanke kan ke ko?Allah cewa Ammi zanyi maganin barci ka zuba min cikin abinci ka sace ni ban sani ba"bai san lokacin da murmushi ya kubce masa ba wai ya sace ta girgiza kai kawai yayi Eshat na neman ta kure tunanin sa hannun sa ta kama tana kallon kyawawan fararen dogayen yatsun hannun sa"yaya Prince yatsun kan nan suna min kyau sosai"kawar da kansa yayi yana faɗin"au ɗazun dan a yaudare ni na tawo da ke yasa akace min habibi kenan ko?"hannu tasa ta fara cire masa botrin rigan sa tana faɗin"aa nima ban san na faɗa ba" "to ko kin sani ko baki sani ba ni karki sake cemin yaya Prince idan ba zaki gaya min suna mai daɗi ba kawai ki kirani Safras ɗina"hannu ta tura cikin singlet nasa bayan ta gama cire botrin rigar nasa a hankali ta fara shafa lallausan bakin gashin dake kwance a faffaɗar kirjin sa tana faɗin"to ka faɗa min sunan da zan rinƙa kiran ka kaji?"tayi maganar dai dai lokacin da ta kai hannun ta saman nipple nashi,da ɗan karfi yace"wash"waro ido waje tayi tare da zame hannun ta cikin sauri,lokacin guda idon sa suka sauya zuwa ja dama zaman da tayi a jikin san nan dannewa kawai yake sai gashi taje ta tsokano sa lunshe ido yayi tare da kama hannun ta ya mai da saman kirjin nashi ya jingina kai da jikin kujerar motar,a hankali ta sa yatsar ta tana kewaye masa saman ɗan bakin nonon nasa,da ɗan karfi ya cije lips nashi na kasa tare da runtse ido sosai lokacin guda fitar numfashi sa ta sauya ya fara numfashi da sauri sauri ganin halin da ya shiga yasa ta zame hannun ta cikin tsoro tana kokarin sauka daga jikin sa,da sauri ya kamota da kyar ya iya muɗe baki murya na sarkewa yace"ina zaki je?bayan ke kika nemi magana"turo baki tayi kasa kasa tace"kayi hakuri gashin wajen ne ya dade yana burgeni ina son wasa da shi"waro idon sa da suka sauya sukayi ja kamar wuta yayi karaf idon sa ya sauka kan baturen sojan dake tukasu yana kallon su ta cikin mirror motan yana kokarin yiwa sojan magana sojan yayi parking na motar a parking space na airport ɗin"out"abun da bgs yace da sojan kenan cikin sauri sojan ya buɗe kofar motar ya fice tare da mai da kofar ya rufe musu.
dawo da kallon sa kan ta bgs yayi sai faman ɓoye fuska take a kirjin sa"me ya kai hannun ki in da kika taɓan nan ko dai kina son baby ne?"da sauri tace"a'a"waskewa tayi da cewa"yaya Prince mun iso airport ɗin fa"mai mai ta sunan yayi"yaya Prince"da sauri ta shagwaɓe murya tace"sorry habibi muje to" "a haka kike so na fita kin san adadin dubbannin jamar dake waje suke jiran fitowar mune?"kallon sa tayi da kyau kafin tace"oh sorry bari na mai da maka botrin"ta kai karshen maganar tare da sanya hannu tana kokarin mai da masa da botirin hannun ta ya kama ya ɗaura a gaban sa yana faɗin"ga babban wutan da kika kunna ai ba botirin"a sukwane take kokarin cire hannun ta amma yaki sakin mata hannun ya danne sosai matso da bakin sa yayi sai tin kunnen ta kasa kasa ya fara magana"ina zaki je?ba zaki cire hannun ki ba har sai kin kashe wutar nan da kika kunna kawai ki fara aiki"juyowa tayi suka haɗa ido lokacin guda tsoron sa ya kamata ganin yadda idon sa suka sauya zuwa ja sosai"yaya Prince ni na yarda ka barni awajen su am...bata kai karshen maganar ba ya haɗe bakin su waje guda tare da tura hannun sa cikin rigar ta a hankali ya fara shafan tula tulan ta yana sauke ajiyar zuciya.
Sosai yayi kissed nata sannan ya sake ta yana kallon face nata"lafiya Eshat?na ga kamar ki na son yin magana"yayi maganar cikin dashewar murya kasa kasa tace"yaya Prince ni sai in ga kamar haryanzu jiki na kake so bani ba"shiru ya É—an yi kafin ya sanya hannu a hankali ya mai da botrin rigar sa da ta cire masa
bayan ya maida botrin sa gaba ɗaya yasa hannu a hankali yana kokarin buɗe motar cikin sauri tace"kayi hakuri yaya Prince karka ɓata rai"cool murmushi ya sake mata wadda bai taɓa yin irin ta ba kafin yace"me yasa zan ɓata rai na ji daɗi da kika faɗa min abun da ke ran ki kuma hakan ba zai sa nayi fushi ba dan ni Eshat nake so ba jikin Eshat ba so rashin taɓa jikin Eshat ba zai sa na sauyawa Eshat daga yadda bake ba so let's go"ya kai karshen maganar tare da buɗe kofar motar ya fito da sauri tabi bayan sa ɗaukan ta yayi chak kamar baby nan take yan jarida suka fara yi masa hoto ko ajikin sa masu mamaki suna yi masu tambayar kan su daman yayi Aure ne suma sunayi. Shiko ko ajikin sa takun sa kawai yake irin na jaruman maza ɗauke da Eshat nasa akafaɗar sa kamar yar baby.
Yana shiga girjin ya zauna saman lallausan kujera na musamman tare da ita a jikin sa,suna zama ba jimawa jirgin nasu ya É—aga kwanciya tayi saman faffaÉ—ar kirjin sa ta lafe lef hannu yasa yana shafa bayan ta a hankali hankali har barci ya É—auke su dukkan su biyu manne da juna.
FAHAD & AMRAT
"My amri wai me yasa kike gudu nane?"tsaye take a gaban mirror tana shafa mai yayin da shi kuma yake kwance saman gado"babu komai kawai tsoro nake ji"ta bashi amsa ba tare da ta juyo ta kalle sa ba,mikewa yayi zaune kafin yace"eyee dan na biki a hankali ko?oya zo nan"ba musu ta juyo ta nufo sa zuba mata ido yayi yana kallon ta cike da so da kauna har ta iso gaban sa"my amri da alama fa nayi ajiyar baby"waro ido waje tayi kafin tace"mutun shakara 14 yana iya aihuwa ne?"kai ya gyaÉ—a mata yana faÉ—in"sosai ma in mace ta fara period zata iya aihuwa"ya kai karshen maganar tare da jawota jikin sa suka kwanta a tare ya jawo musu bargo ya rufe su ya fara sarrafata san ransa yana zuba mata kalaman soyayya.
A ɓangaren lamrat ɗin yaya Yusuf ma ba laifi yanzu laulayin cikin nata ya ragu sosai sai fama da kasala da barci da take,tayi kiba sosai tayi haske abun ta hankalin ta kwance yaya Yusuf na bata kulawa sosai yana matikar ji da cikin nan nashi kamar ransa.
A ɓangaren itama Zahra ba laifi cikin nata ba laulayi sosai sai zaɓen abinci da take fama da shi ban da zaɓen abinci ba wani abu da cikin ke sata suna zuba love nasu da yaya Khalid ɗin ta son ransu basu da wata matsala.
Karfe 6 na yamma jirgin su ya sauka a STANSTED INTERNATIONAL AIRPORT LONDON UNITED KINGDOM cikin sauri ya saɓe ta a kafaɗar sa sai barci take zubawa cikin kwanciyar hankali ba tare da ɓata lokaci ba ya fito nan take yan jarida suka fara mamaki suna musu hoto masu tambayar kansu dama Brigadier yana da aure ne wasu tambayar kansu suke ko dai ya fara neman matan ban zane,shiko ko ajikin sa ya nufi wajen motocin da akajere awajen domin ɗaukan shi jibga jibgan sojoji masu ji da karfi da lafiya ne sukayi layi daga farkon bakin jirgin har wajen motocin tasu duk in da zai wuce sai sojoji sun sara masa ko kallon in da suke bai yi ba bare su sa ran zai ɗaga musu hannu ko makamancin haka dan idan da sabo sun saba da halin sa na ko in kula.
da gudu wani jibgegen soja fari tas daya maye gurbin Abdol ya buÉ—e masa mota ya shiga da ita a jikin sa da gudu jibga jibgan sojojin suka koma cikin motocin su suka tayar suka figi dankara dankaran motoncin da gudun gaske suka bar Airport É—in suka nufi gida
wayar sane ta fara kara tana neman agaji yana rungumi da Eshat ɗin sa yana jin wayar na kara har sai da ta kusa tsin kewa sanna ya ɗauka ganin sunan my dad my everything yasa yayi saurin picking call ɗin tare da manna wayar a kunnensa yana faɗin"hello Abba"daga ɗayan ɓangaren Abba yace"Safras ina humair?"kallon kyakkyawar face nata dake kwance saman faffaɗar kirjin sa yayi kafin yace"I'm so sorry my Abba"cikin sauri Abba ya ciro wayar daga kunnen sa dan ya tabbatar da bgs yake magana ba wani ba mamaki ne ya bayyana akan face na shi lokaci da ya tabbatar da bgs yake waya zancen zuci ya fara yi"yau Safras ne da cewa sorry kai ina ban yarda shi bane idan ma shine to gaskiya ina bukatar kallon face nashi dan na tabbatar da ba abun da ya shiga kan shi ni dai tun da na haifi Safras ban taɓa jin yace wa wani ɗan adam yayi hakuri ba Allah mai iko Allah mai canza bawa aduk lokacin da ya ga dama kai Alhadulillah Allah shine abun godiya"jin Abba yayi shiru yasa bgs yace"naso nazo na baka hakuri akan laifin dana maka a baya amma time ya tafi yanzu kuma na kara wani laifi kan laifi na tafi da Eshat I'm sorry ka tayani bawa Ammi hakuri"Abba ya kasa magana"eyee yau Safras ne tun baa ce yayi laifi ba ya ansa laifin sa ya bada hakuri Allah mai iko gaskiya ba zan taɓa manta wanna rana ba"danna recording na wayar sa Abba yayi kafin yace"gaskiya kayi laifi tafiya da ita da kayi kaga bata gama samun lafiya ba gashi kuma kama criminal zaka je yi zata rabama hankali waje biyu kana kokarin kama criminal sanna kana tunanin ta me yasa ma bazaka tura yaran ka su kama mutumin nan ba?ka kafe dole sai da kanka zakaje" "No Abba ina son kama shi da kai na saboda dalilai biyu na farko koma waye ne nasan ina da kusan ci da shi ya san abubuwa sosai akai na na biyu kuma mutun ne mai haddari na kasa da kasa ban son laifi na ya shafi wani soja ba inna tura yara sai in ga ba zasu iya min abun da nake so ba kuma zai iya fin karfin su dan yana da jama'a sosai ban son sanadina akashe soja ko ɗaya batun tafiya da Eshat kuma ina baku hakuri zan san yadda zan yi" "Allah Ubangijin ya kare min ku kuyi aiki lafiya ku dawo lafiya" "Amin ya Allah my Abba amma Abba why kake mamaki haka" "ni nace maka ina mamaki?"kallon face ɗin hiyana dake ɗan motsi yayi kafin yace"Abba ba iya aikin soja kaɗai na iya ba na iya karantar yanayin ɗan adam koda bamu tare innaji muryan sa ban san me ya baka mamaki ba amma acikin voice naka na fahimci kana jin mamakin"murmushi Abba yayi yana faɗin"sai kun dawo Allah ya tsare min ku"yana kai karshen maganar yayi sauri ya katse kiran mai da wayar gefe bgs yayi ya ajiye dai dai lokacin sojan dake tukasu ya danna hancin motar su cikin katafaren gidan su tun da aka wangale katafaren gate ɗin gidan nasu ya ke kallon Aryan dake tsaye a harabar gidan shi da Hisham mamaki ne ya kama shi"yaushe Aryan kuma ya dawo uk?"ya tambayi kansa yana cikin mamaki sai ganin Aryan yayi ya buɗe masa kofar mota cikin zolaya yace"barka da zuwa ango"harara ya watsawa Aryan kafin ya zuro kyawawan kafafun sa dake sanye cikin Booth kalan kayan sa waje yana kokarin fita motar hiyana ta farka tare da waro idon ta a kan kyakkyawar face nashi mikewa tayi daga jikin nasa tana mutsuke ido zuba mata ido yayi yana kallon ta shi kuwa Aryan wayar sa ya ɗauko ya fara yi musu video kasa kasa bgs yace"sannu da tashi sarkin barci"ɗan karkato da kai Aryan yayi yana faɗin"bgs ka rinƙa magana da ɗan karfi dan maganar ta fita a video"wani mugun kallo bgs ya wurga masa wadda yasa shi kawar da wayar ba shiri fitowa daga cikin motar hiyana tayi ta sunkuyar da kai kasa tana faɗin"ina wuni yaya Aryan" "lafiya lou sister ya gajiyar hanya?" "Lafiya lou yaya Aryan ina diyana?""tana cikin gida tare da Ilham matar Hisham"da sauri hiyana ta wuce cikin gidan,fitowa shima bgs yayi da karfi Aryan ya sara masa yana faɗin"sir munyi nasarar isa hotel ɗin a lokacin da ya dace kuma munyi nasarar kama yaran mutumin sai dai shi baya nan tun shekaran jiya sukace ya bar hotel ɗin mun tambaye su in da yake sunce suma basu sani ba baya taɓa faɗa wa kowa in da yake sai dai in shi yake son ganin su sai ya kirasu awaya yace su zo waje kaza zai basu aiki ɗaya daga cikin suma ce mana yayi baya tunanin wanda suke haɗuwa da shi shine asalin mai gidan nasu saboda muryan wanda suke waya da shi daban wanda kuma yake zuwa wajen su shima muryan sa daban hakan yasa suma suke tantama anya shine asalin wadda sukewa aiki kuwa" "yau wace rana Aryan yayi abun arziki"da mamaki bgs ke kallon sa"Aryan yaushe kazo kasar nan har kaje kayi wanna aikin" "lokacin da kaje cin amarcin ka mana sai in tsaya jiranka babban criminal irin wanna ya cubce mana" "yau dai kayi abun arziki"hararar wasa Aryan ya wurga masa kafin yace"sir zan iya tafiya?"wucewa bgs yayi ya nufi cikin gida yana faɗin"aa karka tafi ka kwana awajen"yayi maganar cikin tsokana bayan sa Aryan yabi yana faɗin"na shirya mana fita ni da kai da baby's namu dan mu kai su yawo fatan ba zaka ki zuwa ba"shiru bgs yayi bai tanka ba har suka shige cikin gida
dai dai zai shiga palo ba shiri yaja birki ya tsaya chak a bakin kofar palon ya kasa shiga sakamakon hiran da diyana da hiyana keyi a cikin palon kusa da shi Aryan yazo ya tsaya sukayi shiru suna sauraron diyana na yiwa hiyana lecture. Zaune saman sofa hiyana da diyanar suke suna fuskantar juna diyana ta tsantsara make up sosai a face nata tana sanye cikin wasu shegun riga da wando sun kamata sosai ta zuba lallausan bakin gashin tan nan har gadon baya tana tsotsar sweet mai tsinke wani pitinannen kanshin turare ne ke tashi a jikin ta kamar anyi ɓarin turare ta tasa hiyana a gaba tana bata kalan nata lecture zuba mata ido kawai hiyana tayi tana mamakin diyana ko waye ya koya mata dukka wanna abun oho katse mata tunani diyana tayi da cewa"Aunty hiyana ki dai na mamaki na in dai kika zauna da Aunty farida to fiye da haka zaki koya wlh,yanzu dai duk bama wanna ba dan girman Allah Aunty hiyana ki rinƙa yin make up sosai ki ajiye ustazancin nan ki fara kashe yaya Prince da wanka kananan matsastsun kaya ki rikita masa tunani ya zama komai yake ke yake tunani kingane ai?"kallon Aryan bgs yayi ya masa alama da ido irin wato"kai ma haka take rikita maka tunani kenan?"Aryan na son yin magana amma bai san su diyana suji dan yana son ji har karshen zancen nasu yana son jin amsan hiyana shidai bgs maman kin diyana kawai yake wai yar yarinyar nan hartasan rikitawa namiji tunani ita kuwa diyana cigaba da lecture ta tayi abun ta hankalin ta kwance take tsaro magana ɗaya bayan ɗaya"dan girman Allah Aunty hiyana karki sake sakawa yaya Prince atamfa ko dogon riga ko lace idan dai ba fita zakuyi ba kinji me aunty Farida tace mu zama karuwai a cikin gidan mazajen mu"tushe baki Aryan yayi saboda dariya data cubce masa shi kanshi bgs sai da yayi ɗan murmushi gefen fuska wai karuwai oh wanna yarinya"kin san me Aunty farida ta faɗa min? kowani namiji da kala abun da yafiso a tattare da mace amma mafi yawancin maza sunfi son breast na mace tom ki tsaya ki nitsu ki gane me yaya Prince yafi so a jikin sai kifi gyara masa wajen idan ba haka ba wlh Aunty farida tace Aure zai kara daga yau zan fara koya miki make up kuma wlh yaya Prince yana bala'i son mace mai make up dan akoi ranar da Aunty Zahra ta miki make up ina ganin sa yayi ta kallon ki sosai sanna kuma ko ban faɗa miki ba kin sani yaya Prince yana son kamshin turare ga turaruka mai daɗi da Aunty farida ta sa aka kawo mana daga Maiduguri daga ke har lamrat da Zahra ba wanda ya ɗiba amrat ce kawai ta ɗauka ita lamrat dan iskanci har wani cemin tayi turaren wari yake mata ita turaren jikin yaya Yusuf kawai take so ni zata gwadawa iya soyayya hmmm ta tambayi yaya Aryan ya bata labarin rikitashi da nake"girgiza kai kawai bgs yayi dan diyana ta fara wuce tunanin sa shi kuwa Aryan ya toshe baki saboda dariya diyana na neman kashe sa da dariya"Allah Aunty hiyana kamar yadda ake faɗe gaskiya ne wlh dukkan mu kin fimu kyau nesa ba kusa ba ke da bappa da Ammi da yaya Prince kike kama ni kuma da Ummi nake kama sanna wlh gaskiya ne kin fimu murya mai daɗi baki da yawan magana amma wlh idan kikayi magana ko macece a kusa dake sai taso ki sake magana dan ɗaɗin muryan ki ni kai na ina son sauraron voice naki to inaga namiji nasan kinfimu ilimin addini kin san abun da ya dace kiwa mijin ki to amma meyasa baki amfani da ilimin baki?me yasa baki yiwa yaya Prince abubuwan da Allah yace mace tama mijin ta?wlh da bakin shi ya faɗa min yana son ki tun lokacin da nake faɗa wa su Abba abubuwan da yake miki na mugunta yaya Aryan ya kawo min waya nayi magana da shi naki sai da muka koma ɗaki na ansa wayar nayi magana da shi shi da kan sa alokacin yace mi yana son ki kuma zai kula da ke na daina damuwa to kin gani ya kamata ke ma ki fara bashi kulawa ta musamman"dogon numfashi hiyana taja tare da sauke nauyayyar ajiyar zuciya kafin tace"nima inason sanya kanana kaya na masa kwalliya amma wlh kunya nake ji sosai ba zan iya ba"mikewa diyana tayi tana taku da kyar saboda ta kalmin da ta sa mai shegen tsinine sosai kusa da ita ta dawo ta zauna tare da tafa kafaɗar ta tana faɗin"Aunty hiyana ki daure ki ajiye kunya nasan kunya abune mai kyau a musulci amma ki daure ki ajiye kunya saboda bata da wata fa ida tsakanin mata da miji kuma wlh maza basu san mace mai kunya a ɗaki kinji na faɗa miki idan kika tsaya kunya nan zakiji yaya Prince ya tafi neman wadda bata jin kunya kinga yanzu yaya Aryan ya shirya mana fita tun ɗazun ya faɗa min karfe 8 na dare zamu fita zan miki kwalliya sosai kuma ni zan baki kayan da zaki sa amma kimin alkawari kowani kaya na baki zaki sa"hiyana na kokarin yin magana bgs ya shigo dan ya lura hiran sun nan ba mai karewa bane ko kallon in da suke bai yi ba ya wuce ya haura sama Aryan na shigowa diyana ta mike ta tafi da sauri ta faɗa saman faffaɗar kirjin tare da shagwaɓe murya tana faɗin"oyoyo yaya Aryan na"murmushi yayi tare da rungumeta yana faɗin"oyoyo my malama sarkin lecture sannu da kokari"miƙewa hiyana tayi cike da jin kunyan rungumar juna dasu diyana sukayi a gaban ta ta wuce ta haura sama.
tsayuwa tayi a palon su tana ganin yadda aka canza komai na palon kamar ba shiba an zuba sabbin furniture an sauya komai an kawata palon iya kawatuwa tasha mamakin tana tunanin Allah kaÉ—ai yasan dukiyar da aka narkawa palon nan a hankali ta taka ta nufi asalin bedroom nata
chak ta tsaya a bakin kofar tare da sa hannu ta murje idon ta dan ta tabbatar gaskiya idon ta ke gane mata ne ko ko karya an kwashe komai na ɗakin ta an zuba mata sabbi komai na ɗaki fari tas aka zuba mata an sauya mata gado an sanya mata katafare mai girman gaske sabanin na da da bai da girma sosai kallon manya manyan trolley da ke gere gefe guda tayi manya manyan trolley shake da kaya dozin 2 guda 24 kenan manyan ciki ma sun kasa rufuwa gaba ɗaya saboda cika da sukayi da kaya a hankali ta zura kafar ta ta shiga cikin ɗakin bakin katafaren gadon ta dake shin fiɗe da white bed sheet mai mugun laushi ta zauna tana bin ɗakin da kallon kara waro ido tayi lokacin da idon ta ya sauka kan makeken hoton ta dake manne a bango tana kwance saman faffaɗar kirjin bgs tana barci shi kuma yana kallon kyakkyawar face nata mikewa tayi cikin sauri ta karisa wajen tasa hannu ta shafa hoton dan ta tabbatar ba mafarki take ba tunani ta farayi"ko yaushe yaya Prince ya ɗauki hoton nan har ya kai aka wanke masa oho",juyawa tayi ta nufi dressing room nata tun a bakin kofa tayi mutuwar tsaye tana kallon yadda aka shirya dressing room ɗin shake da kaya da jakunkuna takalma agogo sarkan gold masu kyau da tsada sai ɗaukan ido suke ga manya manyan perfume masu kyau da tsada komai an shirya shi a gidan sa daban karisawa tayi ciki a hankali take taku kamar ɓarauniya kallon wajen jera kaya tayi mamaki ne ya kara kamata a ranta tace"kenan gaskiyan diyana yaya prince yana son kananan kaya sosai gashi su kaɗai ya sanya aka jera min anan gaskiya ya zama dole na rinƙa sa masa dan yayi farincikin kamar yadda nima yasani farinciki"tana cikin tunani idon ta ya sauka kan dangareriyar waya kirar I phone 14 pro tare da key motar Mercedes-Benz a kusa da wayar a saman drawer dake wajen hannun ta har rawa yake wajen ɗaukan wayar ta kunna harken screen ɗin a cike take da charji anyi setting na komai harda sim card a cikin ta shagala da kallon wayar kira ta shigo cikin wayar yar tsorata tayi dan batayi tunanin za'a kiraba kyakkyawar fiskar bgs ne ya bayya akan screen ɗin cool murmushi ta saki kafin ta ɗauki kiran tare da manna wayar a kunnen ta cikin nitsuwa tace"Assalamu alaikum" "idan kin yi sallar issha ki shirya Aryan ya shirya mana fita" "yaya Prince"sai kuma tayi shiru ta kasa magana"lafiya Eshat menene?" "dama am daman"kasa magana tayi sai in da in da take masa"ok i think maganar zatafi fito idan gani gaki kiyi sallar mangariba ki kawo min hot milk idan kin zo sai ki faɗa min maganar ko?"cool murmushi ta saki kafin tace"ina son ka sosai my Habibi" "my Eshat murmushi na miki kyau sosai idan ina ganin murmushi ki bana sanin lokacin da nima nake murmushi" "yanzu yaya Prince a ɗaki na ɗin ma sai da kasa camera?" "Ai ya zama dole na sa miki camera dan na rinƙa ganin duk abun da baby na ke yi"hannu ɗaya tasa ta rufe fuskar ta ta fito daga dressing room ɗin tana murmushi ta faɗa saman katafaren gadon ta cikin shagwaɓa tace"amma yaya Prince ai kai baka son yimin murmushin kuma murmushi kafa yafi na kowa kyau a duniyar nan" "lokacin sallah yayi idan kinzo zan miki murmushi sai kimin video ki ajiye kiyi ta kallo dan a shekara sau ɗaya nake murmushi"dariya tayi mai ɗan sauti kafin tace"nikam zaka rinƙa yimin sau goma a rana ai ko?" "Tashi kiyi sallah dan mangariba shot time yake da shi in kin kawomin hot milk ma karasa magana"yana kai karshen maganar ya katse kiran tare da ajiye wayar ya fito suka wuce masallacin su shida Aryan mikewa ita tayi ta nufi toilet kallo sosai ta tsaya tayiwa toilet ɗin dan shima an canza komai an sanya mata katon show glass an shake mata shi tab da shampoos da mayukan gyaran gashi masu matukar kyau da tsada ta shagala da kalle kalle da taɓe taɓe a toilet ɗin har su bgs suka dawo masallaci jin diran motocin su yasa tayi saurin cire kayata ta fara wanka sauri sauri ta ɗauro alwala ta fito ɗaure da kyakkyawar farin towel mai taushi a kirjin ta shiru ta tsaya a tsakiyar ɗakin tana tunanin inda zata samu hijabi da manyan kaya tasa tayi sallah gaba ɗaya kayan da bgs ya sa aka sanya mata a dressing room nata kananan kaya ne kuma ba hijabi aciki.
Juyawa tayi ta nufi wajen trolley da ke jere gefe guda dan ta duba ko zata dace ta samu manyan kaya
da kyar ta iya jawo trolley ɗaya babba na kasa ta kwantar ta buɗe ta tafara dubawa tayi saa domin gaba ɗaya akwatin cike yake da jallabiyoyi da hijabai dariya ne ya kubce mata lokacin dataga abun da aka rubuta a jikin akwatin"only for prayer""wato dai da gaske yaya Prince bai san manya kaya har da sawa arubuta min only for prayer to In Sha Allah saboda sallah kawai zan rinƙa sawa"ta kai karshen maganar tare da zaro leda ɗaya na jallabiya da hijabi ta maida sauran tayi tayi ta rufe akwatin ta kasa dan kayan sun cika sosai daman da kyar aka iya rufewa bai ma gama rufuwa gaba ɗaya ba ganin bazata iya rufewa bane yasa ta mike ta barsu awajen ta shin fuɗa dadduma ta sanya jallabiyar da hijabin ta tada sallah a nitse.
duk abun da take bgs yana kwance saman katafaren gadon sa yana kallon ta ta cikin system nashi daga shi sai shot da singlet asalin kyakkyawar surar jikin sa a bayyane.
Bayan ta idar da Sallah ta wuce dressing room nata ta zauna gaban mirror ta fara tsara kwalli ta shafa wannan ta goga wanna tayi mamaki ganin yadda tayi kyau sosai,taɓa tunanin ganin yadda su Zahra ke make up zata iya kwatatan tawa kuma har tayiwa kanta daga gani da ido kawai ba wandon jeans baki ta sanya mai stone masu shagen kwalli a jiki ta ɗauki bra tasa ta sanya t-shirt pink ta gyara gashin kanta sosai sanna ta feshe jikin ta da perfume masu bala'i kamshi da daɗi ta fito ta dawo bedroom ɗin tayi kyau sosai kamar ita tayi kanta kayan sun zauna a jikin ta sosai,sun bayyanar mata da duk wani albarkatu na jikin ta shape ɗin coca colar ta ya kara bayyana sosai,sakamakon yar kiban da ta kara hips nata sun kara cikowa kamar zasu fasa wandon ta ko ina ta haɗu sosai.
tana kokarin fita É—aki taji wayar ta na kiran sallar issha ala'amar lokacin sallah yayi dawowa tayi ta zura katon hijabin ta har kasa saman kayan ta shinfida darduma ta tada Sallah lokacin already su bgs sun wuce masallaci.
Tana idar da sallah ta fito jikin ta sanye da hijabin ta wuce kitchen na kasa,lokacin da su bgs suka dawo tana kitchen bai lura da ita ba ya wuce sama shima Aryan ya wuce part nashi yana faÉ—in"saura 10mins mu fita fa"cikin sauri ta haÉ—a masa hot milk É—in ta fito ta ta koma part nasu a palon su ta tsaya ta cire hijabin ta nufi bedroom nashi hannun ta rike da cup mai É—auke da hot milk É—in nashi.
Sallama ta masa da sanyayyar voice nata mai ratsa zuciyar mai sauraro shiru ba kowa a É—akin wucewa tayi ta ajiye masa cup É—in saman table tana bin É—akin da kallo shima an canza masa komai na É—akin komai na É—akin su iri É—aya har gadon su irin É—aya mamaki tayi lokacin da taga har bed sheet nasu iri É—aya saman gadon sa ta haye ta kwanta tare da É—auko wayar sa dake gefen gadon,ta kunna hasken screen É—in ta rubuta sunan Aunty farida wayar ta buÉ—e ta fara latse latsen a cikin wayar tana ta kasa gane komai na kan wayar duk in da ta shiga sai ta kasa fita ana haka ya fito sanye cikin wandon jeans blue da t-shirt fara tas mai laushi ya É—aure lallausan bakin gashin kan sa a baya,daddaÉ—ar kamshin perfume nashi ne ya daki hancin ta yasa ta É—ago kanta da sauri"subhanallah sarki ya tabbata ga Ubangiji da yayi wanna halittar"dukkan ninsu abun da suke faÉ—i aransu kenan kafe juna sukayi da ido sun kasa kau da kallon su daga kan juna tana yabon tsantsan kyan da Allah ya masa yayi da shima yake yaba nata tsantsan kyau É—in sun shagala da kallon juna ringing wayar sa ne ya dawo dasu duniyar kallon juna da suka shiga mika masa wayar tayi tana sunkuyar da kai dan ji tayi kunyar sa ya kamata ansan wayar yayi ya dawo kusa da ita ya zauna da sexy voice nashi ya fara magana a nitse
"my Eshat kin yi kyau over har ban san taya zan bayyana kyan da kikayi yau ba" "yaya Prince na kai rabin ka a kyau kuwa?kasan irin haɗuwa da kayi yau kuwa?"yana kokarin sake magana Aryan ya sake kira a karo na biyu"my Eshat Aryan ba zai barni na bayyana miki irin kyau da kikayi yau ba matso muyi hoto kafin mu fita" "yaya Prince daman kana hoto ne"girgiza mata kai yayi kafin yace"bana hoto sai dai a ɗauke ni ban sani ba kamar yanda yan jarida ke ɗauka na amma da kai na ban taɓa ba saboda ke yau zanyi"murmushi tayi ta faɗo jikin sa tana faɗin"waye ya dauke mu hoton dake ɗaki na wadda na kwanta a jikin ka ina barci?" "Cameran ɗakin nan ne ya dauka ina bincike a system naga video sai na yanki dai dai wajen"ya kai karshen maganar tare da ɗaukan su hotona masu kyau kala biyar sanna ya mike ya koma dressing room nashi,jim kaɗan ya fito hannun sa rike da jaket manya guda biyu bakake masu kyan gaske yasanya ɗaya ya sanya mata ɗaya a iya cinyar sa jaket ɗin ya tsaya masa ita kuwa har ya ɗan wuce guiwar ta hannun ta ya riko suka nufi palo dakin ta suka wuce da kansa ya ɗauko ɗan karamin hijabi baki ya sanya mata tare da takalma flat shoe baki,sanna ya riko hannun ta suka fita a cikin motar suka isko Aryan da diyana suna zaune a gidan gaba suna zuba love da alama Aryan da kan sa zai yi tuki wucewa bgs yayi ya nufi nashi motar da gudu rundunar jibga jibgan sojojin sa suka nufoshi hannu ya ɗaga musu ala'mar baya bukata mazaunin driver ya shiga yayin da ita kuma ta shiga ɗayan gefen"Eshat dawo ki zauna a nan"ya faɗa yana nuna mata kan cinyarsa waro ido tayi tana faɗin"to tayaya zaka tuka motar kenan?" "Kizo ki zauna zan fara koya maki motane dan na sai miki naki motar"shiru tayi bata sake magana ba ta buɗe kofar motar ta fito ta dawo ta gefen sa ta buɗe ta shigo ta zauna a kafar sa kwanto da kansa yayi saman kafaɗar ta ya manna mata kisa a lallausan wuyar ta dogon numfashi taja tare da saukewa a hankali ta kwantar da kanta a saman faffaɗar kirjin sa tada motar yayi a nitse ya fara tuki yayi gaba sannan Aryan ya rufa masa baya tuki suke a nitse cikin kankanin lokaci suka isa wani Katafaren shopping mall sukayi parking ko ina awajen gauraye yake da hasken lantar ki wadda ko allura ka yaddar kana iya ɗaukan kayan ka saboda haske. A hankali ya zame hannun sa daga kan steering motar ya dawo da shi saman marar ta lokacin da hannun sa ya sauka kan marar ta sai da taji numfashi ya ɗauke na wucin gadi kwanto da kansa yayi saman kafaɗar ta yana shakan kamshin shampoo data wanke kanta a hankali ya fito da harshen sa waje ya fara yi mata tafiyar tsutsa a wuya yayin da hannun sa ke kan marar ta yana shafawa a hankali hankali kasa jurewa tayi ta ɗan juyo kaɗan tare da zura hannun ta cikin rigar sa ta fara shafa lallausan bakin kwantatcen gashin kirjin sa zame hannun sa yayi daga kan marar ta cikin sauri dan tana neman rikitashi ya riko nata hannun data ke shafa kirjin sa da kyar ya iya buɗe baki da sexy voice yace"give me a hot kiss sai muje ko kin ga su Aryan sun wuce sun bar mu"matso da bakin ta tayi sai tin nashi ɗan bakin ta bashi zazzafar sumbata shafa kan ta yayi yana faɗin"Allah ya miki albarka my wife" "tare da kai my Habibi"buɗe kofar motar yayi ba tare da ya sake magana ba ya fito tare da ita a jikin sa.
Sai da ya rufe kofar motar sanna ya sauke ta ya riki hannun ta suka nufi wajen kayan kwalama da ciyeciye nan suka isko Aryan da diyana suna shan ruwan guzberi da stro ɗaya wuce su sukayi suka zauna a kugeran gefen su kasa kasa hiyana tace"yaya Prince ina son ice cream ɗin can akoi daɗi ranar da mukazo da yaya Khalid ya saya min in je in anso?"kallon wajen da take nunawa yayi ice cream ne kala kala a jikin signpost nasu sai wani bature dake tsaye a wajen yana mikawa duk wanda yazo yanuna wandda yake so sai ya ɗauko ya miƙa masa"you can't go"ya faɗa a takaice miƙewa tayi ta karisa wajen zuba mata ido yayi tana tafiya yaso yaje ya ɗauko mata ganin diyana ta mike ta nufi wajen yasa ya kyaleta taje da kanta itama tare da yar uwar ta,hannu tasa ta nunawa mutumin kalar ice cream da take so yayin da itama diyana ta nuna masa a tare ya ɗauko ya miƙa musu sun sa hannu zasu ansa ya janye baya kallon juna hiyana da diyana sukayi yayin da shima bgs abun ya bashi mamaki "shi kwata kwata tun da yake zuwa shopping wajen nan bai taɓa lura da wanna mai sai da ice cream ɗin ba amma tsabar kwaɗayi irin na mata su har sun san da wajen har da wani cewa ice cream ɗin da daɗi"yayi nisa cikin tunani yana kallon su yayi dan shi kuma mai sai da ice cream yake ta wasa da hankalin hiyana da diyana shi kuwa Aryan hankalin sa ma baya wajen su yana kan wayar sa da alama wani sako mai mahimmanci yake turawa.
a kule diyana tace"kai malam idan zaka bamu ka bamu idan kuma ba zaka bamu ba shike nan"duk da bai san me diyana tace ba ya fahimci ta ɗauki zafine akan wasa da hankalin da yake musu ita dai hiyana ta kasa magana sake miko musu ice cream ɗin yayi da sauri diyana tasa hannu zata ansa a tunanin ta tun da ta masa faɗa zai basu amma sai taga akasin haka domin kuwa da sukazo ansa sake janye wa baya yayi hiyana na kokarin yin masa magana sukaga ya waro ido waje kamar zasu faɗi kasa idon nasa da gudu ya fito daga in da yake tsaye ya duƙa kasa a gaban su ya miƙa musu ice cream ɗin mamaki ne ya kama su dukkan su biyu cikin sauri hiyana ta juya karaf idon ta ya sauka kan bgs dake tsaye a bayan su fuskar nan a ɗaure kamar an aiko masa da sakon mutuwa ganin sa yasa ta gane abun da ya tayar wa da mai sai da ice cream hankali murmushi ta ɗan saki tana mai kara gidewa Allah daya bata bgs a matsayin miji jarumin namiji wadda cikakkun maza ke zubewa akan guiwowin su idan sun ganshi hannu tasa ta ansan ice cream ɗin ita kam diyana dama tuni ta ansa nata tayi wucewar ta juyawa itama hiyana tayi bayan ta ansa ice cream ɗin tana kallon bgs alama ya mata da ido akan ta bar wajen ba musu ta wuce ta bar wajen a fusace yace da mai sai da ice cream ɗin"kneel down!!"ba musu baturen yayi kneel down dan yasan wanene bgs yana ganin sa a Tv yana ganin sa a jaridu da kafafen watsa labarai nadama tare da danasanin fara sai da ice cream arayuwar sa ya farayi yau ya taɓo abun da yafi karfin sa yau ya jajibowa kansa masifar da tafi karfin family su sai Allah ne kaɗai zai iya ceton sa yau kuka ya farayi tun bgs bai fara bashi horo ba
To masu karatu sai mun haÉ—u gobe idan mai ya kaimu
No comments