Duk Karfin Izzata Book 1 Paga 37
*Episode 3️⃣7️⃣*
........A fusache jabir ya juyo da niyar yayiwa wadda ya riƙe masa hannu rashin mutunchi, wani haɗaɗen guy idon sa yayi tozali dashi, ya haɗu iya haɗuwa sosai ga green eyes nashi sai kyalli yake saboda ya zaro su waje sosai akan wayar sa,ya riƙe hannun jabir da hannun sa ɗaya, ɗayan hannun nasa kuma yana rike da waya yana latsawa da alama
wani sakon yake turawa, sai dai kash duk wannan haduwar tashi fuskar nan tasa babu annuri ko kaɗan babu alamar dariya fuskar aɗaure take tam kamar hadiri,sauko da kallon sa jabir yayi izuwa kan surar jikin guy ɗin dogone sosai ga faffaɗar kirji, ɗamtsen hannun san nan kamar zasu fasa riga saboda chika dam dam da sukayi,ga wani lallausan bakin gashin mai kyau da sheki a kansa wadda ya tara ya ɗure a baya ya zuba jelar gashin nashi har tsakiyar baya, kallo ɗaya zaka masa kasan ya karɓi horar wan sojoji sosai.A hankali hiyana ta ɗago blue eyes nata ta sauke a kan guy ɗin,chikin tsoro da tashin hankali har lips nata na kerma, a hankali ta mutsa lips nata ta furta yaya prince kuma a school namu ko me ya kawosa? Bata gama rufe bakin ba, Bgs ya murɗe hannun jabir da karfi ta baya ji kake kas, kas, kashin ta balle, a guje hiyana ta juya ta bar wajen dan kar ya gama da jabir ya juyo ya haɗa da ita.
Wani gigitachen ihun azaba Jabir ya saki, bai gama ihun nasa ba Bgs ya sauke masa wani wawan nushi a gefen chiki nan take jabir ba ɗauke dif kamar an ɗauke wuta nepa alamar ya suma, sakin sa Bgs yayi ya zube kasa wanwar tsallake ta kansa yayi wuche ya nufi office ɗin Hm, da sauri rundunar jibga jibgan sojojin sa suka rufa masa baya.
gaba ɗaya jama'ar dake waje daga kan malamai har ɗalibai, kowa murna yake da bugun da Bgs ɗin yawa jabir.
Bgs
Yana kokarin shiga office na Hm shi kuma Hm na kokarin fitowa karo sukayi Hm yayi baya kamar zai faɗi, da kyar ya iya sai ta tsayuwar sa, Bgs kuwa yana tsaye kamar wani sadaukin yaki ko motsi bai yiba "sorry sir ban san kana shigowa bane chewar Hm
Bgs dai bai tankashi ba sai ma raɓawa yayi ta gefen sa ya wuche chikin office ɗin saman sofa ya zauna jibga jibgan sojojin 4 ne suka bishi chikin office ɗin hannun su ɗauke da manya manyan bindigu (gun) suka tsaya a kanshi suna bashi tsaro,sauran Sojojin kuma suka tsaya a bakin kofar shigowa
"Sir naji ka bugi wani awaje me ya haɗa ku? Hm ya tambaya yana ƙarisowa chikin office ɗin, dogon tsaki Bgs yaja kanfi yace "kawai naga zai bugi wata yarinya ne shiyasa na bugeshi dan na lura bai da hankali bai san me yake ba" "to wan to kuma wace yarin yace kuma wani yaro ne!? Hm ya tambaya yana kokarin zama a kujera "kai Ni ban sani ba domin duk kansu daga yaron har yatinyar ban ga fuskar ko ɗaya daga chikin suba, ni ba shine ya kawo niba, Abba ne ya aiko Ni, ya karisa maganar yana ya mutse fuska
tunani Hm ya shigayi "ko wani mai karan kwanne yau kuma ya haɗu da Bgs domin ina da tabbacin duk wan da Bgs ya buga to fa in bai mutu ba zai yi fama da doguwar jinya ko da ya tashi kuma ba lallai ya koma kamar da ba.
"Yallaboi Abba yace na karɓawa su Zahra transfer later, da sauri Hm ya ɗago ido yana kallan Bgs chikin rawar murya ya fara magana "lfy Abba yake son chan zawa su Zahra school? Mikewa tsaye Bgs yayi yana faɗin "Ni ma ban sani ba idan ka gama ka bawa Abdol later ya kawo min ina mota yana kai karshen maganar ya fice daga office ɗin.
Yana fita jibga jibgan sojojin sa masu ji da karfi da lfy kallo ɗaya zaka musu kasan sun samu training mai kyau suka rufa masa baya
Daga malamai har students din dukka kallon Bgs da tawagar sa suke kowan nan su tambayar kan sa yake wanene wan nan? Ko dai ɗan shugaban kasan American ne, dan wan nan bai yi gama da ɗan naija ba, awani ban garen kuma murna students keyi an musu maganin jabir yau dai kam an samu wadda ya tanka shi har ma ya sumar dashi, bangaren yan matan school ɗin kuwa kowanche mutuwa take akan Bgs da bai ma san sunayi ba, ko wacce fatan samun sa amatsayin miji take ba karamin rikitasu kyan shi yayi ba
Taku yake irin na manyan jarumai har suka kai in da sukayi parking motochin su da gudu wani matashin soja ya sha gaban sa ya buɗe masa kofar motar, shiga yayi ya zauna ya zuro kafafun sa waje ya sunkuyar da kai kasa yana latsa waya, da alama jiran Abdol suke
Aɓangaren hiyana kuwa
Da gudu ta nufi class ɗin su Zahra sai numfashi take sama sama, Zahra na ganin ta ta miƙe ta nufeta tana faɗin "hiyana lfy kike numfashi haka!? Me ya saki gudu kuma!? "Aunty Zahra yaya prince a school namu kuma ina da tabbachin ya bugi jabir" waro fararen manya manyan ido ta Zahra tayi ta dafe kirji chikin tsoro tace "mun shiga uku hiyana me kuma ya haɗa shi da jabir!? Allah yasa dai ma bai kashe shiba ya tsaya a iya bugu" "wlh Aunty Zahra ai jabir dinne ya rikemin hannu ni kuma na mare shi, shima ya ɗaga hannu zai rama kenan sai yaya prince ya rike hannun sa"
"Wayyo hiyana munshiga uku yanzu kina nufi a akan ki yaya prince ya bugi jabir!? Kuma ya ganki yasan dake jabir yake faɗan!? "Aa Aunty Zahra bai ganni ba domin lokachin da ya riƙe hannun jabir ɗin latsa wayar sa yake da alama wani sako yake turawa shiyasa ai na gudu dan karya ganni, yace nima zai hukun tani dama ni kam ya tsane Ni" ta karisa maganar kamar zatayi kuka rungumeta Zahra tayi tana faɗin "ki dena chewa ya tsaneki kin ji Allah yaya prince bai tsane ki ba kawai shi dai haka halinsa yake ne"
"Wai ma me ya fito dake daga Class naku ne? Har kika haɗu da jabir ɗin" "daman kai nane yake min chiwo nache bari nazo ki rakani office na Hm dan yasa amai dani gida ina tafiya a hanya ya tareni" "to shike nan yanzu muje wajen Hm ɗin sai amai dake gida koh?
"Kai Aunty Zahra ni wlh idan ki kaga na fita daga class nan to sai naji fitar motochin su yaya prince daga school nan kuma ma ai kan ya warke ya daina yimini chiwo" dariya Zahra tayi tare da raba jikin su tace "kai hiyana sarkin tsoro In Sha Allah ke che zaki zama matar yaya prince ɗin nan sai naga karshen tsoron" "dan Allah Aunty Zahra ki dai na yimini mugun fata kinji wlh ko da wasa naji an kira sunan shi ji nake zuchiya ta na bugawa da karfi" hannu ta Zahra ta riƙe suka koma wajen zaman ta suka zauna suna yar hiran su, yammatan class ɗin sai kallon su suke, kamar wasu tagwaye domin kamin nin Zahra sak yaya prince haka itama hiyana kamannin ta ɗaya da shi shiyasa suke kamar ta gwaye gashi yanayin jikin su ɗaya yan sirara sai dai hiyana ta ɗara Zahra tsawo kaɗan, Zahra kuma ta girmi hiyana da shekara 1.
Maiduguri
Kyau iya kyau diyana tayi kyau har ta gaji da kyau idan ka ganta zaka che yarinyar nan da madara take wanka saboda sabulan da Aunty farida ta haɗa mata ba karamin gyara ta yayi ba gata da iya ɗaukan wanka da make up ta chanza sosai ta kara haske fatar ta tayi luwai luwai ga wani sihirtachen kamshin dake tashi ajikin ta, yauma kamar kullun ta Chi kwalliya sosai kamar ka sa che ta gaje ka ajiyeta ka yita kallon ta kamar madubi dan kyau, sanye take chikin wata dan kareriyar lace Sky Blue da zanen fulawa baki a jiki, ɗinkin riga da sket ba ƙaramin zama kayan sukayi a jikin taba kamar daman a jikin nata akan ɗin kasu, ga wani haɗaɗiyar high heel baki da ta sanya
jama'a ya kuke ganin farin kafa da bakin takallama? sai ɗaukan ido kafar nata yake ga kunbar (farche) kafar ta nan yasha gyara fari tas dashi sai sheki yake ta sanya mayafi baki kalar takalmin ta ta zuba wasu ɗankara ɗankaran sarka da abun hannu na gold wadda Aunty farida ta bata, jakar ta ta ɗauka ta nufi waje
Taku take a hankali sai wani yauki da yanga take kamar bata son taka kasa ta fito harabar gidan, Aiman dake zaune chikin mota tun daga nesa ya zuba mata ido yana kallon yadda take taku chikin yanga da yauki har ta iso wajen motar ba tare da ya ankara ba, fitowa wajen Aunty farida tayi daga chikin nata motar tana faɗin "wan nan irin kwalliya haka my diyana dole namiki" murmushi kaɗan diyana tayi san nan tace "ngd Aunty farida"
Chiro wayar ta daga chikin jaka Aunty farida tayi tace "to my diyana gyara na ɗauke ki, gyara tsayuwa diyana tayi Aunty farida ta fara ɗaukan ta hoto har kala 10 ta ɗauke ta san nan tace "to ya isa haka shiga da wuri muje dan kar lokachi ya kure jirgi ya tashi ya bar yaya Aiman a nan"
"Aunty farida na shiga motar ki ne ko kuma naje na yaya Aiman? "Duk wan da kike so my diyana" "to bari na shiga na yaya Aiman, bata jira amsar Aunty farida ba ta buɗe gidan baya ta shiga kusa da shi ta zauna, wani nauyayyar ajiyar zuchiya ya sauke wadda sai da yasa diyana juyowa tace "yaya Aiman lfy murmushi kawai yayi mata dai dai lokacin driver's suka tada motochin, da gudu baba mai gadi ya wangale musu katafaren gate ɗin chikin ni tsuwa suka danna hanchin motochin waje
Sunyi nisa da tafiya yaya Aiman ya juyo da kallon sa kan diyana da kyau ya fara magana
"baby diyana in son ki bani hankalin ki magana mai muhimmanci nake son muyi" ɗago blue eyes nata tayi tana kallon sa chikin sanyin murya tace "to yaya Aiman in jin ka
"Ni ba zan ɓoye miki ba gaskiya ina son ki Auren ki kuma zanyi kuma na san kin san da hakan ko? Sun kunyar da kai kasa diyana tayi tana wasa da yan ya tsun ta "baby diyana ko baki so nane? Yayi maganar yana ɗan dukar da kansa kasa yana leken fuskar ta
"Ina son ka mana yaya Aiman kai fa yayana ne idan ban soka ba waye zan so? "Baby diyana ni fa ba irin wan nan soyayyan ba soyayya irin na Aure nake nufi ba na yaya da kanwa ba" "eh yaya Aiman soyayya irin na Aure'n ina son ka Nima.
Wani farinciki kine ya lullɓe sa ji yake kamar ya jawota ya rungume ta ajikin sa ko zai samu saukin a zuchiyarsa
A ɓangaren diyana kuwa, kuka take a zuchiyar ta tana faɗin "No yaya Aiman me yasa zaka min haka ni wlh yaya Aryan nake so ba kai ba, amma ba zan iya chewa bana son kaba kuma bazan iya chewa yaya Aryan nake So ba, Ni ban ma sani ba shin yaya Aryan yana sona ko dai kawai a matsayin kanwa ya ɗaukeni ni yanzu ya zanyi da rayuwata wayyo Hiyana ta kizo ki che cheni awan nan bala'i daman kin saba taimako na, ya Allah ka kawo min mafita
"Baby diyana tunanin me kuma ki ke yi? "Babu komai yaya Aiman " "ya zaki chemin babu komai bayan nayi magana har sau biyu baki jiba"
"Babu komai wlh kawai kewar su hiyana nake ne shiyasa" "to ki dai na damuwa kinji? naji Abba yace jibi Aunty farida ta mai daki gida ai" "Da gaske yaya Aiman" "eh mana shiyasa ma ai zan koma ban damu ba dan nasan jibi kema zaki dawo gidan badan zaki dawo ba ai da nima bazan koma ba, yayi maganar dai dai lokachin da driver's ke parking na motochin a Parking space na Airport.
Da sauri Aiman ya fito yana faɗin "my wife saura 5mnt jirgin mu ya ɗaga sai munyi waya, bai jira amsar taba ya wuche ya nufi motar Aunty farida dai dai lokacin itama ta fito daga chikin motar, sallama sukayi ya wuche ya nufi jirgi yana tafiya yana waigo diyana mamaki ne ya kamashi tunani ya shigayi "me yasa diyana bata fito daga chikin mota ta masa bye bye ba, ɗayan ɓangaren na zuchiyar sa yace "kila kunyar ka takeji ne Shiyasa kabari sai ka koma ka kirata awaya, sai kaji dalili, da wan nan tunanin ya shiga jirgin sai da Aunty farida taga tashin jirgin su san nan ta koma chikin mota
A ɓangaren diyana kuwa tun da Yaya Aiman ya fita daga chikin motar take kuka hawaye sharɓe sharɓe, gaba ɗaya hawayen ya wanke mata fuska,surutu ta rinkayi shi dai driver yana jinta amma ko ɗago ido bai yi ya kalleta ba dan yana tsoron kallon nata saboda Aunty farida ta musu gargaɗi akan duk wanda aka kama yana kallon diyana zai karɓi hukunchi mai tsanani daga wajen mijin ta, hakan yasa gaba ɗaya masu aikin gidan suna tsoron idon su ta sauka a kan ta koda kuwa ta bayan tane.
Key driver's ɗin sukawa motochin suka tayar suka nufi gida
KANO
kwanche yake saman katafaren gadon sa yana kallon sama yayi shiru kamar mai tunani hannun sa ya ɗago ya duba time a jikin dan ƙareriyar agogon gold dake manne a hannun sa, karfe 4:45pm mai da hannun nasa yayi gefe yana kwaɓe fuska karar wayar sa da ya jine alamar shigowar sako hakan ya sashi sa hannu yana lalubar wayar, chan daga ɗan gefensa ya jiyo wayar
Ɗauko wa yayi ya kawota dai dai sai tin fuskar sa,tare da kunna hasken screen ɗin ganin number da diyana ta kirashi shekaran jiyane ya bayyana akan screen ɗin hakan ya sa shi saurin meƙewa zaune tare da chire password ɗin wayar hannun sa har rawa yake wajen shiga massage
wow zafafan hotunan da Aunty farida ta ɗauki diyana ɗazun da zasu raka Aiman Airport ne aka turo masa sai dai an sanya wa hotunan backgrau an sanya wasu flower daga gefe gefe anyiwa hotunan kwalliya,ta yadda mutun ba zai gane a in da aka ɗauki hotunan ba zubur ya miƙe tsaye, tare da kurawa wayar ash eyes nashi ya kankame wayar sosai kamar wani yace zai kwache masa ita, daya bayan ɗaya yake kallon hotunan.
...nan take yaji jikin sa na rawa sai wani tsuma yake, ji yake kan sa ta masa nauyi gaskiya ina bukatar ganin matata a kusa dani dafe kan sa yayi ya koma ya zauna a gefen gadon a hankali ya fita daga wajen massage ɗin ya shiga contact ya fara kokarin kiran layin diyanar amma a kashe, wurgi yayi da wayar tasa saman sofa, da karfi ya fara magana
"Wai wanene ya ke min wasa da hankali haka ne!? Abba da alama awan nan karon kashe ni kake son yi da kan ka, oh my god!! Kwan chiya yayi a saman gadon rabin jikin sa na sama kafafun sa kuma na kasa, haka yayi ta surutu har barchi yayi awon gaba dashi.
Washe gari misalin karfe 5:5Am kamar dai kullun yauma lallaɓowa tayi ta fito daga part ɗin Ammi ta nufi ɗakin da yaya Ahmad ke kwanche, da sallama ɗauke a bakin ta ta shigo kakar kullun yana kwanche saman gadon sa yau dai idon sa a lumshe kamar mai barchi
Gefen gadon hiyana taje ta zauna a hankali tafaɗa karan to masa addu'oe tana tofa masa jin motsin mutun a kusa dashi ne yasa ya waro manya manyan fararen idon sa akan kyakkyawar fuskar sai shekin alwala fuskar nata yake
"Yaya Ahmad ya jikin naka, abun mamaki sai taga ya girgiza mata kai alamar yana samun sauki, mikewa tayi tsaye da sauri tace "yaya Ahmad yanzu kana iya motsa jikin ka!? Hannun sa yaɗaga mata alamar ta gani yana iya motsa wasu daga chikin gaɓoɓin sa, murmushi tayi wadda yasa dimple nata ya lotsa tace "Alhadulillah kasan me yaya Ahmad? saura kwana ɗaya na gama haɗa maka ruwan addu'a ka kuma nasan kana sha In Sha Allah zaka samu sauki, amma yanzu in kawo maka wani abu ne? Ɗaga mata kai yayi san nan yamata nuni da hannun sa alamar ruwa yake son sha, da sauri ta fice daga ɗakin ta koma part ɗin Ammi ta ɗauko masa ruwan faro mai sanyi daga fridge ta fito ta nufi ɗakin.
Tun daga nesa ta hango Bgs yana kokarin shiga ɗakin yaya Ahmad ɗin, ɓata fuska tayi alamar bata ji daɗi ba dan taso tabawa yaya Ahmad ruwan addu'ar nan ya sha zai tai maka masa, amma babu hali dan kuwa bata isa ta shiga ɗakin Bgs na chiki ba juyawa tayi jiki ba kwari ta koma part ɗin Ammi
Ƙarfe 7 dai dai suka gama shirin zuwa school suka zauna a palon sama suna jiran yaya Khalid, sai ƙarfe 7:10 yaya Khalid ya shigo palon Ammi da Sallama ɗauke a bakin sa har suna haɗa baki wajen amsa masa Sallamar zama yayi saman sofa yana kallon su ɗaya bayan ɗaya chikin sanyin murya ya fara magana
"Yau ba zuwa school domin Abba ya karɓa muku transfer later za'a Chanza muku makaranta Amma sai ranar Monday yanzu dai kuje ku chire uniform ɗin ku shirya muje muchi abinchi" to kawai su kache san nan suka wuche suka nufi ɗakin su, shi kuma ya miƙe ya fice daga palon ya nufi palon Abba dan zuwa yin breakfast
Karfe 8:20 gaba ɗaya family Abba sun haɗu a palo dan yin breakfast ban da Aryan da Bgs, abin chi suke chikin nitsuwa da kwanchiyar hankali ɗan gyarar murya Abba yayi ya dubi Fahad da hiyana ya fara magana "kai Fahad je ka kuramin babban yayan ku, ke kuma hiyana je ki kiramin yaya Aryan kusan tare suka miƙe suka nufi waje hiyana ta nufi part ɗin yaya Aryan Fahad kuma ya nufi part ɗin Bgs.
Da sallama Fahad ya shaga betroom nashi zaune ya same'sa saman sofa yana latse latse a laptop "yaya prince Abba na kiran ka" shiru Bgs yayi kamar bai ma san da shigowar mutun ɗakin ba aikin dake gaban sa kawai yake, zama kusa dashi Fahad yayi ya sake mai mai ta maganar "yaya prince Abba na kiran ka" nan ma shiru yayi kamar bai jiba Almost 10mnt Fahad na zaune yana jiran amsar Bgs har ya fidda rai da samun amsa yana kokarin miƙewa sai yaji Bgs yana faɗin "ae na Abban yake? nauyayyar ajiyar zuchiya Fahad ya sauke kafin yace "yana palon sa kuma ya che kayi sauri" shiru Bgs yayi bai sake magana ba, Fahad dai da yaga Bgs bai da niyar sake yin magana sai ya kama kan sa ya fice daga ɗakin dan in da sabo ya saba da rashin maganar Bgs
Abangaren hiyana kuwa da sallama ta shiga part ɗin yaya Aryan babu kowa a palon kasa haurawa tayi palon sama nan ma babu kowa, kofar betroom nashi ta nufa a hankali ta tura kofar tare da yin sallama ta shiga, tsaye yake gaban mirrow yana gyaran gashin kansa, sanye yake chikin wando jeans fari da bakar t-shirt chikin sanyin murya tace "yaya Aryan Abba na kiran ka" a sukwane Aryan ya juyo dan jin irin voice na diyana ganin hiyana che yasa yace "jeki ina zuwa, da sauri hiyana ta juya ta fice daga ɗakin tana yabon irin kirkin yaya Aryan a zuchiyar ta.
Shi kuma juyawa yayi ya chigaba da gyaran gashin sa yana tunanin diyanar sa
Kusan tare Bgs da Aryan suka shigo palon taku suke da kagan su kaga jaruman sojoji Bgs na gaba Aryan na bin sa abaya, zulaihat dake zaune kusa da Aunty amarya ta zuba musu ido tunani ta shigayi "ashe ma hoton sa da na kalla ban ga komai ba, asai a fili yafi kyau wow gaskiya guy ɗin nan ya hadu iya haɗuwa ba karya, har naji na kara son shi ga wannan faffadar kirjin nashi zai yi daɗin kwan chiya wlh kai gaskiya ayi sauri a ɗaura mana Aure in ba haka ba zan kai masa kai na, dan ba zan iya hakuri ba.
Tayi nisa chikin tunanin sai ji tayi Aunty amarya ta taɓa ta a ɗan firgiche ta ɗago ido tana kallon ta alama da ido Aunty amarya ta mata akan ta gaishe dasu Bgs, dawo da kallon ta kansu tayi chikin rawan kai ta yanga tace "hiii prince y kk tirkashi gaba ɗaya jamaa palon sai da suka ɗago suna kallon ta banda Aryan Bgs da kuma Fahad.
Murmushi Yusuf yayi a zuchiyar'sa yace "tab aiko ga wadda zata bi sahun yar sarki Zaria, Khalid kuwa dariya ma taba shi amma sai ya danne dan yasan idan yayi dariya tofa tabbas Bgs zai iya ɓaɓɓalla yarinyar nan, Haidar Umar mamaki ne ya kama su, ko su dasu kannen sa basu taɓa che masa wani hii ba bare ita da basu ma san daga in da ta fitoba kwashe kwashen Aunty Amarya ta kwaso ta, Abba kam tunani yake gai suwar mutunci ma akayi wa Safras yau she yake amsawa bare wani hii lallai su hii anji jiki
Shiru palon yayi kowa da abun da yake tunawa, hannu Zahra tasa ta ɗauki Cup ɗin ruwan dake kusa da Abba tana kokarin kawowa gaban ta kamar wadda aka bugewa hannu patal cup ɗin ya faɗi chikin plate ɗin abin chin zulaihat ruwan ya zube a chiki, chikin jin haushe da bachin rai abun da Bgs ya mata na rashin amsa hii ɗin ta da yayi ta miƙe ta zabgawa Zahra wani gigitachen mari, wani kara Zahra ta saki
Bata gama sauke hannu ba Haidar da Umar suka miƙe a tare suka wanke mata fuska da wasu gigitachen maruka a lokachi guda ta gefen dukka kuma tun ta tana kokarin sakin kara, Fahad ma ya miƙe ya mata ɗaya tamkar da dubu ta gefen kunne, wadda yasa gaba ɗaya taji duniya ya tsaya Chak kunnen ta ya dai ma ji na wunchin gadi, almost 5mnt tana tsaye tama kasa sakin ihun dan da alama bata chikin hayyachi sai da ta kara wani 5mnt san nan ta samu damar sakin wani razanannen ihu mai firgitarwa, Afusache chikin tsawa Aryan yace "get out a ruɗe ta kama hanya fita sai ihu take kamar wata mahaukaciya
Kuka Zahra take a hankali sai shessheƙa take ga shatin yatsun zulaihat kwanche akan kuma tun ta wajen yayi ja wur dashi gyaran murya Aryan yayi wadda yasa gaba ɗayan su ban da Bgs suka ɗago suna kallon sa,da hannu ya yiwa Zahra alama da tazo
Miƙewa tayi daga kujerar ta ta nufi waje sa, batare da yayi Magana ba ya mata nuni da hannun akan ta zauna kan chinyar sa, zama tayi yasa hannu ya goge mata hawayen kasa kasa yace "ya isa haka kuka kinji Auta? Gyaɗa masa kai kawai tayi alamar eh, spoon ya ɗauka ya fara ɗeban abinchi daga chikin plate na Khalid yana bata a baki.
Aunty amarya ji take kamar ta tashi ta shake Zahra dan haushi kwafa tayi a chikin ranta tana tunanin wani hukunchin ya kamata ta ɗauka akan yaran nan
Khalid kam yama kasa magana saboda bakin chikin marin sis love ɗin sa da akayi ajiye spoon na shi yayi yana kallon yadda Zahra ke chin abinchin da Aryan ke bata
Tunani Umar da Haidar suka shigayi daman yan uwan su suna son su haka dubi yadda yaya Aryan ke bawa Zahra abin chi a baki Alhadulillah Alhamdulliah
Duk wan nan abun da ake Bgs ko ɗago ido bai yiba bare kasa ran zai yi magana.
Haka zalika Fahad tun da ya mari zulaihat ya koma ya zauna ya chigaba da chin abin chinsa kawai
mikewa Ammi tayi ta fara magana "me yasa zaku mata irin wan nan maruka hakan eh!? "Ammi to me Auta ta mata da zata mare ta haka chewar Umar, shi dai Fahad kawar da kai gefe yayi dan bai ma son haɗa ido da Ammi dan bai da niyar bata amsa sai wani furzar da iska mai zafi yake daga bakin sa, dawo da kallon ta Ammi tayi kan Bgs dake zaune yana kallon wayar sa "kai yanzu kana ganin yaran nan suka mari yar mutane bazaka hana suba Koh? Shiru ya ɗan yi na yan second ni kafin ya buɗe ɗan karamin bakin yace "ai dai dai sukayi Ammi shiyasa"
"Dai dai sukayi ma zaka che ko? "Haba Aisha ya isa haka gaskiya ya faɗa miki ai dai dai sukayi mana da basu hukun tata bama to ni da kai na zan hukun tata Autan tawa guda za'a mara kuma a gaba na san nan batare da tayi laifin ko mai ba ai kam wane mutun, chewar Abba komawa Ammi tayi ta zauna tayi shiru tana tunani "nima har chikin raina naji wan nan mari da yarinyar nan tawa Zahra amma dai bai kamata su haɗu mata haka ba
Abba ne ya katse mata tunanin da take yace "to na tara ku a nan ne inason yin magana daku...✍️✍️
No comments