Duk Karfin Izzata Book 1 Paga 35
*Episode 3️⃣5️⃣*
.........da sauri ta miƙe ta nufesa tana faɗin "yaya Aryan kai... Bata kai karshen maganar ba ta ɗakata kuma chikin sauri ta dakata daga nufarsa da take, jiki ba kwari ta juya ta koma wajen books nata ta zauna ta dukar da kai ta chigaba da abun da take.
A hankali chikin nitsuwa ya fara magana "me yasa kuma kika juya kika fasa karasowa" batare da ta ɗago ta kallesa ba tache "saboda kai ba yaya Aryan ɗin bane, da mamaki Aiman ke kallon ta, chikin mamaki yace "ya akayi kika iya gane chewa ni ba Aryan bane? bayan ko iyayen da suka haife mu in dai ba tare suka ganmu ba, basa iya banbanta mu, sau dayawa Abba na kirana da sunan Aryan haka zalika ya kira Aryan da sunana muna kama sosai bamu da wata bambancin"
Cikin sauri batare da ta ɗago ba tace "wlh kuna da banbanci sosai ma kuwa,
Karisa shigowa yayi cikin palon ya zauna saman sofa mai zaman mutun 2 yana faɗin "to menene bambanci namu?, Har lokachin diyana taba ɗagoba tana duke da kanta tana ta rubutu a chikin book nata, shikuwa Aiman ya kafeta da Ash eyes nashi sosai yake kare mata kallo
Kanta na kan takar dar da take rubutu tafara magana "yaya Aryan ya fika dogon hanchi, hanchin sa siririne sosai, san nan yafi ka manya manyan ido kuma shi idon shi yayi kalar ash sosai, sannan yana da ɗigon baki a ta gefen sagen sa, bakin sa yayi red sosai, kuma yafi ka dogayen yatsun kafa, gashin kansa yafi naka tsantsi da kuma baki, kuma... Bata karisa maganar Aima yace "ke ya isheni haka, a yaushe kika kare mana kallo har haka kuma shi Aryan ya fini komai ke nan? Ni babu abun da na fishi?"
Still dai bata ɗago kanta ba tace "aa yaya Aiman, akoi abubuwan da kafishi mana sosaima, gyara zama Aiman yayi kafin yace "ok ina jinki faɗamin ni kuma dame dame na fishi"
"Kafishi katon hanchi mana domin shi yaya Aryan hanchin sa, siririne kuma dogo sosai kai kuma naka dogone amma kuma kato, san nan ka fishi katon kafa, shi kafarsa karamine kai kuma naka kato, ka fishi katon kai, ka fishi jiki, kuma muryan yaya Aryan, ɗan siririne kai kuma naka iri na wanchan yaya Umar ɗin ne kato kuma .... "Ke dalla kiyi mani shiru idan muryana katone ya akayi dana yi sallama kika kasa gane ba Aryan bane? Ya akayi lokachin da kika ɗago kika ga fuskata baki gane ba Aryan bane? sai da kika zo kusa dani
"Ai saboda ina sunkuye da kai na kasane ne shiyasa naga kamar yaya Aryan ne, wlh da ina a tsaye ne na ganka bazan che yaya Aryan bane, saboda kuna da banbanci sosai kuma ai don na daɗe banji muryan yaya Aryan bane shiyasa naji kamar shine"
"Ok to ya isa ina Aunty farida" "Aunty farida bata nan taje shopping" "waya miki kwalliyar nan" ya tambaya yana kare mata kallo from head to toe, sai lokachin diyana ta ɗago kai chikin zumuɗi tace "ni nayi yaya Aiman, nayi kyau ne? "Murmushi yayi kafin yache sosai ma my sister, ai daman ke kyakkyawa che, da sauri diyana ta miƙe ta dawo kusa da shi ta zauna tafara magana
"Yaya Aiman kasan me, batare da tajira amsar sa ba ta chigaba da magana "yan school namu kowa chewa yake wai ina kama da laraba ina da kyau sosai" "eh mana sister ai gaskiya suka faɗa miki kinma fi larabawa kyau ai" murnushi tayi sosai wadda yasa har dimple nata ya lotsa, shi kuwa Aiman ya zuba mata ido kawai yana kallonta daga samma har kasa
"Yaya Aiman ina yaya Aryan yake? ya akayi kazo kai ka ɗai? "Abba ne yace nazo Aunty farida nason ganina, san nan kuma yaya Aryan yana gida" "to yaya Aiman ka kiramin shi awaya inason yin Magana dashi" "ok kawai Yaya Aiman yace san nan ya fito da wayarsa daga aljihun wandon jeans dake jikinsa, ya kunna hasken screen ɗin wayar, ya shiga contact yana neman layin yaya Aryan.
Da sallama Aunty Farida ta shigo palon hannunta riƙe da manya manyan ledoji shopping, da sauri Aiman ya ajiye wayar sa ya miƙe ya nufi Aunty farida ya ansa mata ledojin yana faɗin "Wellcome Aunty babba" "Aiman ka iso kenan? "Eh yanzu na shigo,
Zama sukayi saman kujera ɗaya mai daman mutun 3, nan suka fara gaisawa
"Yaya Aiman kazo ka kiramin yaya Aryan ɗin mana" chewar diyana, waro ido waje Aunty farida tayi chike da mamaki tache "ke wani yaya Aryan ɗin kuma wato yanzu diyana duk maganar da namiki bata shiga kunnen ki ba koh?
Turo baki diyana tayi chikin shagwaɓa tace "kiyi hakuri Aunty farida na mantane shiyasa, amma ba zan sake ba" subhanallah ido kawai Aiman ke binta dashi yama kasa magana kawai kallon ɗan karamin bakin nan nata yake baya majin me take faɗe shidai bakin kawai yake kallo.
"To tashi ki kwashe books nakin nan ki mai da ɗaki kizo mu shiga kichin yau da kaina zan yiwa yaya Aiman girki kizo kema ki tayani, da sauri ta miƙe chike da zumuɗin zata shiga kitchin yau.
tattare books nata tayi ta maida chikin jaka ta ɗauki jakar ra nufi stair ɗin.
KANO
wani zazzaɓi mai zafin gaske ne ya rufeshi, sai rawan sanyi yake, ga ash eyes nashin nan sun chanza sunyi jaa sosai gaba ɗaya jijiyoyin kansa sun tashi, zaune yaƙe saman sofa ya dafe kansa da hannu ɗaya, yayi shiru kamar mai tunani.
Almost 10mnt yana wan nan yanayin, a hankali yasa hannun ya ɗauko wayarsa dake gefe guda, kunna hasken wayar yayi ya chire password ɗin san nan ya shiga contact, layin Aunty farida yayi dealing ya fara kira, ringing ɗaya Aunty farida tayi picking tare da faɗin "hello Aryan"
Da kyar ya iya buɗe baki, baka jin voice nashi ma sosai ya fara magana "Aunty farida y kk" , subhanallah! Aryan baka da lfy ne? Yana ji voice naka haka? Tayi maganar a ruɗe "Aunty Farida Abba da Ammi suna neman kasheni da kansu" "A uzubillahi!! haba Aryan me suka maka haka? har zakache suna neman kasheka"
"Aunty farida sun ɓoyemin matata wlh ina sonta ina san ganin ta, ina chikin damuwa Abba yaki faɗamin in da take Ammi kuma bata isa ta faɗamin ba saboda dole tabi umarnin Abba, pls Aunty farida kisa Abba ya dawomin da ita in dai ba so kuke ku kashe niba, kin san yadda nakeji a chiki zuchiyata kuwa? Ya karisa maganar chikin rau'nanniyar murya
Wani irin farin cikin Aunty farida taji, jitake kamar ta zuba ruwa a kasa tasha dan daɗi yau Aryan da bakinsa yake faɗin zai iya mutuwa a kan mace, lallai diyana kin chiri tuta waiii, jin Aunty farida tayi shirune yasa yace "Aunty babba ko kema kina bin bayan Abba ne? Da sauri tace "a'a Aryan yanzu kasan ya zamuyi kaje ka sanar da Abba kana sonta kuma Auren ta zakayi nan ba da dadewa ba, nasan kana faɗa masa haka zai dawo maka da ita"
Dogon numfashi yaja tare da sauke ajiyar zuchiya kafin yace "No Aunty farida ni bazan faɗawa kowa ina sonta ba kema na faɗa mikine dan keche sirrin mu kuma pls kada ki faɗawa kowa, har sai ɗan uwana ya samu matar da yakeso shima sai a haɗa Auren nu lokachi guda.
"Aryan idan fa baka faɗawa Abba chewa Son ta kake ba wlh zai iya bawa wani bare Aure'n ta"
Chika tsawa Aryan yace "No Aunty farida hakan ma ba zai yiwuba ni dai kawai yanzu kiwa Abba magana ya dawo da ita san nan kuma karki faɗa masa nache ina Son ta" to shikenan Aryan, ɗazun nan ma Aiman ya shigo" "ok to Aunty Babba kinga kwakwalwa Aiman na gab da samun matsala saboda rashin lfy Ahmad shiyasa ma muka zaɓi mu turashi wajen ki wata kila idan baya ganin Ahmad ɗin, zai iya mantawa da wasu abubuwan, pls Aunty farida bama sai na faɗa miki ba karki barshi ya rinƙa zama shi ka ɗai bare ya samu daman yin tunani gida ki mantar da shi komai, ki lallaɓa ki samo masa mata a cikin family mijin ki, ki haɗasu dan a haɗa Auren mu gaba ɗaya zanso hakan"
"Eh hakan zai yi daɗi kam zan yi iya bakin kokarina, Khalid da Yusuf su already suna da natan su, saura Shi ogan naku da Aiman da Fahad, sai wayan chan marasa jin haidar da Umar, Allah ya tashi kafadun Ahmad shima yabi sahun ku" "amin kawai Aryan yace daga nan sukayi sallama, ya kashe wayar ya ajiye a gefe guda san nan ya miƙe da kyar ya nufi toilet.
Aɓangaren Aunty farida kuwa tana gama waya da Aryan tafara Neman layin Abba, kira ɗaya Abba ya ɗaga chikin zumuɗi "tace Assalamu alaikum Abba na albishir" da faraa Abba yace "goro my daughter"
"Abba yau Aryan da kansa ya furtamin yana Son diyana kuma wlh duk hiran da mukayi nayi recordined" "wow my daughter gaskiya nafi kowa murna da hakan dole namiki kyauta mai girman gaske saboda tun bayan Aihuwar ku baa taɓa bani lbr mai dadin wan nan ba" "to Abba yanzu ya kamata diyana ta dawo gida dan wlh Aryan na chikin damuwa sosai bakaji yadda naji voice nashi ba kamar bai da lfy "
"Za'a dawo da ita my daughter amma ba this week ba sai next, dan ina son in masa surprise ne. "To shike nan Abba na sai munyi waya" tana gama faɗin hakan Abba ya katse kiran, sai faman murmushi yake
Washe gari tun asuba Hiyana ta lallaɓo ta fito daga part ɗin Ammi ta nufi ɗakin yaya Ahmad, kamar dai kullum yauma haka ta same'sa, gefensa kaɗan ta zauna tafara karanto masa addu'a kamar yadda ta saba, tanayi tana hawaye sosai almost 10mnt ta ɗauka tana masa addu'a bayan ta gama ne ta ɗago kai tana kallonsa yayin da shima ita yake kallo chikin sanyin murya tace
"Yaya Ahmad kanajin sauki kuwa? Murmushi yayi tare da lunshe idon sa ya sake buɗe wa, alamar Eh ba karamin daɗi tajiba ganin yadda ya chanza yanzu har hasken sa ya fara dawowa ya fara dawowa dai dai kamar da, tayi nisa chikin tunani, kamar daga sama taji tsayuwar mutun a kanta a ruɗe ta ɗago blue eyes nata taga dai babu kowa yan waige waige tafara yi still dai bata ga kowa a ɗakin ba, miƙewa tayi chikin tsoro tana faɗin "yaya Ahmad sai gobe kuma idan nazo... Bata karisa rufe bakiba wani iska mai karfin gaske ya hanƙaɗata ta faɗi ka buge da jikin gadon, da karfi ta furta innalillahi wa inna ilaihir rajiun hasbunalluhu wani mal wakil, nan take is kan ya tsaya chak wani karfi taji yazo mata ta miƙe da sauri har tana haɗawa da gudu ta nufi waje.
Tana fita tayi karo da Bgs shi kuma yana shigowa, baya baya tayi ta faɗi kasa chikin tsawa "yace ke me kikeyi a nan!? "Muryan na rawata tace "kayi hakuri yaya prince daman nazo duba jikin yaya Ahmad ne" ɗago hannun sa yayi yana kallon ɗankareriyar agogon gold dake manne a hannun sa, karfe 5:10Am dawo da kallonsa kanta yayi duk da chewa wajen akoi ɗan duhu baya ganinta sosai hakan bai hanashi fahimtar chewa tabbas wan nan ɗaya daga chikin yaran da Ammi ta ɗauko daga Yola bane dan yasan Zahra dai bazata zo nan wajen at this time ba, batare da ya sake magana ba ya tsallake ta ya wuche ya shege ɗakin da yaya Ahmad ɗin ke kwanche
Ita kuwa jiki ba kwari ta mike ta nufi part ɗin, Ammi
Yana shiga ɗakin ya ɗaga ido yana kallon sama a hankali ya fara magana "ya kamata na samu time na duba Camera nan fa ko kuma nasa ko Fahad ne ya duba min, dan ya kama nasan suwaye da waye ke shigowa ɗakin nan, kuma meke kawosu zan yi kokari naga na binchiki Cameran gaskiya, dan ni ban yarda da kowaba.
Sauko da ido sa yayi kan Ahmad dake kwanche, a hankali ya taka zuwa wajen gadon kasa kasa yace "Allah ya baka lfy my bro, bari muje masallaci sai mun dawo yana kai karshen maganar ya juya da sauri ya fice daga ɗakin.
To kwanche tashi babu wuya awajen Allah yau dai diyana na da 2 week's a Maiduguri wajen Aunty farida dan ta
Yauma kamar kullun sanye take chikin doguwar riga abaya pink colour ta tsantsara make up ɗin ta kamar ka sache ta dan kyau, ta goge tayi kyau sosai takara haske da chika fatar jikin tannan kuwa kamar kitaɓa jini ya fito, sai ɗaukan ido take kamar madubi, taku take a hankali ta sauko daga stair case ɗin ta shigo chikin palon a tsakiyar palon ta tsaya kamar mai tunani, da ɗan karfi tace "yes yauwa na tuna jiya ai yaya Aiman ya sayamin sim card ya kamata na kira yaya Aryan tun da na san number sa, da sauri ta juya ta koma ɗakin ta
Ɗauko wayar ta tayi ta fito palo ta zauna saman sofa mai zaman mutun 3 kunna hasken screen ɗin wayar tayi, sauri sauri ta shiga contact ɗin ta babu number kowa awajen daga na yaya Aiman sai na Aunty farida, shiru ta ɗanyi na yan second ni da sauri kuma tafara rubuta number sa tana gamawa ta danna call wayar tayi ringing har ta katse bai ɗagaba, sake kira tayi nanma bai ɗaga ba sai a garo na uku ya ɗaga chikin faɗa ya fara magana
"Wai wanene ke neman ta kuramin ne? Chike da zumuɗi tace "yaya Aryan ni ne fa" zubur ya miƙe tsaye muryan sa har rawa yake yace "ke ina ki ke ina Abba ya kai..... Bai karisa maganar ba yaji an katse kirar, da sauri ya chiro wayar daga kunnen sa yabi kiran Amma ina layin akashe sau uku yana gwadawa amma a kashe wani irin raɗaɗi yaji zuchiyar sa na masa na dama ya farayi yana faɗin " dama ban ji voice nata ba da yafi min yanzu zata sake jefani chikin tashin hankali, wurgi yayi da wayar gefe guda ya dafe saitin zuchiyarsa a hankali ya koma ya zauna a gefen gadon.
Aɓan garen diyana kuwa wani wawan mari Aunty farida ta sakar mata bayan ta ansa wayar tata ta kashe chikin tsawa tafar magana "ke bakyaji ko? eh wato ni ban isa in sa ki abu ko in hana kiba koh? Sokike Allah ya isan Abba ya kamani ko? Chikin kuka diyana tafara magana "kiyi hakuri Aunty farida na kasa mantawa da yaya Aryan ne shiyasa amma namiki alkawarin bazan sake ba" nan take Aunty farida taji jikinta yayi sanyi kuma tayi na damar marin'ta da tayi Allah sarki So kenan
Zama tayi gefenta ta rungumo ta tafara magana "ya isa my diyana kinji kiyi shiru, ni banche ki manta da yaya Aryan ba ki chigaba da tunanin sa In Sha Allah next week ma zamuje gida sai kiga yaya Aryan ɗin naki kinji ki share hawayen ki ya isa haka" chike da zumuɗi da farinchiki diyana ta goge hawayen ta tana faɗin "amma Aunty farida idan mukaje gida a chan zaki barni ko? "Eh mana my diyana ai daman mai dake zanyi" dariya diyana tayi kamar ba ita bache mai kuka yanzun nan, a wan nan yanayin Aiman ya shigo ya same'su
Saman sofa mai zaman mutun 1 ya zauna yana faɗin "to baby diyana me kuma ya faru naga sai murna kike? "Yaya Aiman zan koma gida mana shiyasa nake murna, miƙewa Aunty farida tayi ta ɗauki wayar diyana ta wuche ta haye sama ta barsu awajen,
"Baby diyana yau kinyi kyau sosai, sun kuyar da kai diyana tayi saɓanin da, idan an che mata tayi kyau sai tafara dariya, tana farin ciki.
"Yaya Aiman nagode kuma kai ma ai kayi kyau sosai" "to taso kizo na mana hoto kinji my baby chikin nitsuwa ta miƙe ta karisa wajen da yake zaune saman hannun kujerar da yake zaune ta zauna, chiro wayar sa yayi ya rinƙa ɗaukan su pic masu kyau sai murnushi suke su dukka, bayan ya gamane ta miƙe ta koma kujerar ta ta zauna suka chigaba da hirar su
KANO
Sis Love yana ga kin rame ne kwana biyun nan Zahra dake zaune kusa dashi ta ɗago kai zatayi magana kenan dai dai lokachin Bgs ya shigo palon da sallama ɗauke a ɗan karamin bakin nan nashi, fuskar nan tashi kamar wani hadari a ɗaure take tam, sanye yake chikin wando jeans baki da t-shirt blue ba ƙaramin kyau kayan suka masa ba, asalin halittar jikin sa ya bayyana faffadar kirjin san nan a tsaye take tam, ɗamtsen hannun san nan kamar zasu fasa rigar saboda chika
nan take Zahra ta miƙe jiki na rawa tace "sannu da shigowa yaya prince ina wuni, shiru ya ɗanyi yana kallon Khalid dake zaune ko kallon in da Bgs ɗin yake bayyi ba dan baya son su haɗa ido chikin tsawa yace "ke wuche ki bamu waje, ai tun bai kai karshen maganar ba Zahra ta nufi hanyar ɗakin su da gudu har tana tuntunɓe
"Me kake yi a nan Khalid? Sai lokachin Khalid ya ɗago kirjin sa na dukan uku uku dan shi kanshi yana fargaban ansar da zai bawa Bgs amma kuma ya zama dole ya sanar dashi dan shi gaskiya ya gaji yana son Zahra sosai.
"Hira nazo yi wajen matata ta" tirkashi waro green eyes nashi yayi waje sosai yana kallon Khalid, yayin da shima Khalid yake kallon sa "wai Khalid kaji abun da bakin ka ya furta kuwa? "Kwarai kuwa Bgs naji mana barima na mai mai ta maka hira nazoyi wajen matata kuma kanwata farinchiki na burin raina abun alfahari muradin rai na kai in ta kai che maka itache duniyata komai nawa, mutuwan tsaye Bgs yayi yama kasa chewa Khalid komai, ganin haka yasa Khalid ya miƙe ya fice daga palon ya barshi tsaye awajen.
Yana fita tun bai yi nisa ba yace "alhamdulliah alhamdulliah alhamdulliah, yau dai na gama da duk wata matsala ta, kai Bgs kai dai wlh ina maka adduar Allah ya ɗora maka soyayya wadda bata sonka inga ta tsiya yana magana yana sauke nauyayyar ajiyar zuchiya da haka ya nufi ɗakin sa ya haye gado ya kwanta
To masu karatu sai mun hadu Ranar Monday idan mai dukka ya kaimu..✍️✍️✍️
Book 1 fa yana gab da karewa sauran page 3 ko 4
No comments