Dan Minister Complete Hausa Novel
馃DAN MINISTER* 馃拝馃拕
馃馃
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
*Bismillahir Rahamanir Rahim*
Dasunsn Allah meraha mejinkai
1-2
Wasu motocine masu numfashi da Rai da lfy masu bakin gilass guda bakwai suke gudu Akan titi kamar zasu tashi sama kowa kaucewa yake inyagansu musamman masu tafiya akasa gudun Kar abugesu abuge banza masu motama kaucewa suke bere masu babur da Keke ko jamian tsaro da suke Akan titi insunga wayannan motoci nazuwa Suma korar mutane sukeyi su tsaida kowace mota harse wayannan motocin sunshige ga wani mahaukacin kida dayake tashi acikin motar da tafi kowace mota acikin motocin guda bakwannan Kyau da haduwa kidan da yake tashi acikinta kamar agidan rawa haka kidan ketashi suna zuwa wani Dan kareran gida suka Danna Kan motarsu zuwa gidan dagudu masu gadi suka bude musu geat suka shiga ga jamian tsaro da bindigogi atsantsaye akofar gidan da cikin gidan dagudu wani Jami,in tsaro yazo yabude murfin motar da kidannan yake tashi wani matashin saurayine meji da kansa Dan kimanin shekara ashirin da biyar kyakkyawa ajin farko fari kamar balarabe kanshi yasha wani irin aski ga yaraba kalar gashin kannashi biyu Daya Baki Daya Jah wuyanshi dauke da wasu sarkoki awuyanshi ga hannunshi wasu manya manyan zobuna ga farcanshi na karshan hagu da dama yayi tsawo sosai gawani mahaukacin gajeran wando irin na zamaninnan da matasa sukesawa ajikinshi kafarsa dauke da wani bakin takalmi metsada gawani bakin gilass yasha a idanshi hannunshi dauke da wayoyi masu tsada fuskarnan tashi ahade Kai bazakace Yana dariyaba daga ganinshi kasan nera tazauna ajikinshi Dan gatane yanaji da kuruciya dakyau da kudi Daya motar matasane saanninshi suka fito amotar Suma du shigar tasu Babu ta arziki ma aikatan gidan se gaishesu sukeyi wasu sunzube akasa suna gaisheshi kamar wani sarki dokarsace du wani maaikaci na gidan in sunganshi su durkusa har kasa sugaisheshi Kuma karsu tashi seyabar wajan wannan dokarsace inba hakaba ranka yabaci kokuma abakin aikinka Banda sojojin da suke gadin gidan sune dokar Bata hau kansuba saboda bazasu yardaba subi irin wannan dokarba Kuma baya amsa gaisuwar kowa daga cikin maaikatan Kuma Dole inkaganshi ka gaisheshi duda baze amsaba Yana cikin tafiya zeshiga falan gidan yaikaro da wani maaikacin gidan bekula da tahowar wannan matashin saurayiba da zugar abokansa Babu zato Babu tsammani wannan maaikaci yaji saukar mari afuskarshi cikin tsawa da gadara matashinnan yafara yiwa maaikacinnan fada
yace Kai Kai waye mahaukacine dazaka hada hanya Dani sannan ka bugeni ko baka gani Kai waye da bazakabi dokataba dangidan waye Kai waye yatsayama kazami irinka talaka kawai har Ina hada jiki dakai zaka gogamin kazanta danhaka nasamuku doka in kunganni awaje ku durkusa har se nabar wajan wato Kaine metaurin Kai da bazakabiba to yau zanga waye yatsayama kaje ansallameka daga aiki ko harabar gidannan karka Kara dawowa inbahakaba Rai zebaci Kuma wata yazo karshe baka da albashi fice kabarmana gida Wawa kawai
Durkusawa maaikacin yayi Yana rokar wannan matashin yallabai Dan Allah katemakeni karufamin asiri karka koreni wlh bansan katahoba Dan Allah kayi hakuri daaikinnan dashi nadogara dashi mukecin abinci ni da inalina nasha wuya kannasamu aikinnan in kakoreni bansan yazanyiba zanshiga wani Hali Ni da iyalina
Kokulashi beyiba Daya dameshi kafa yasa ya Shure mutumin yasa jamian tsaransa sufita da mutumin yanaji Yana gani wannan maaikaci yarasa aikinshi
Cikin bacinrai yashige falan gidan Yana kwalawa mahaifiyarshi Kira mommy mommy
Atsorace tafito tana amsawa tace lfy nabil kaidawa
Yace nida wayannan mahaukatan maaikatan gidannanne wlh zandau mataki akansu gabadaya zankoresu nazuba wasu
Kafin mahaifiyarshi tayi mgn muryar mahaifinshi sukaji Yana mgn yace kamin dedai nabil du Wanda yabatama Rai Ni nabaka dama da doka kakoresu asa wasu kome kace Dana dashi zaai anfani Dan banasan bacin ranka du Kuma Wanda yabatama Rai ko waye shi se nadau mataki akanshi indai kudi naaiki amatsayinka na Dan MINISTER Kuma jinin masu kudi gaba dabaya kana da ikwan taka du Wanda kakeso akasarnan Nina tsaya maka mumuke da kasarnan mumuke da doka ahannunmu indai akankane wlh Zan iyayin abinda baazataba saboda irin kaunar da nake maka Dana Kai kadai Allah yabani dana namiji har yanzu bansamu waniba dolene naji dakai da duwani Abu da kakeso Kaine magajina ko bayan Raina ko da Raina dukiyata takace seyanda kayi da ita kayi abinda kakeso kataka du Wanda kakeso katemaki du Wanda kakeso ko nawa zaka kashe na tsayama nabil yanzu yakakeso ayi wayeshi Wanda yabatama rai acikin maaikatan gidannan yanzu adau mataki kanshi
Nabil yace daddy ai nadau mataki akansa har na koreshi daddyna danhaka nakesanka da irin gatan da kake nunamin da San da kakemin Nima inasanka daddy inakuma jidakai yanzu sonake ajawa du wani maaikaci nagidannan kunne daga Kan namiji zuwa mace Kai musu mgn Akan dokokina duka kasansu daddy Ni bani da lokacin da Zan tsaya da Yan aiki Dan Basu da matsayin da zantsaya dasu har nai musu mgn Dan baajina bane su nafisu da komai
MINISTER yace angama Dana nabil Dole abi abinda kace shi zaayi Bari yanzu yanzu a aiwatar da abinda kace
Nabil yace ok daddy yauwa daddy inasan kudifa najiya da kabani yakare Kuma banaso naje naciro a ATM bani da lokaci ga abokaina zanbasu kudi zasu Wala suyi bushasha inasan miliyan biyu Dan yau muna da bushasha Ni da abokaina
MINISTER yace ok nabil ai ba matsala kaje dakina kadauka ai kasan inda nake ajje kudi kaje kadauka ko nawa kakeso bakomai inkanasan kudi na fadama base kafadaminba nabaka izini kanazuwa kana dauka dagani se Kaine mukasan lambobin da ake anfani dasu na maajiyar kudina nagida ko Fatima mahaifiyarka batasaniba se kai nabil danhaka du sanda kakeso kaje kawai kacira kaji Dana
Yace ok daddy angama yashige yana fito Yana wata irin tafiya
Mahaifiyar nabil hajiya Fatima tace agaskiya alhaji baka kautawa bakayiwa yaranka adalci kaima bakawa kanka shima kansa nabil basanshi kakeba wlh cutarsa kake wana irin gatane wannan zaasa yaro amuguwar ahanyar da bazata doreba sedai takaishi ga halaka karfa kamanta da maganar Yan Karin mgn sukace kaso naka duniya takishi kaki naka duniya tasoshi Kuma ai bashi kadai bane danka Yana da Yan uwa Mata ko danshine namiji ayaranka kake nunamasa irin wannan mugun gatan katunafa Allah Amana yabamu akan yaranmu Kuma zetambayemu akansu sukuma sauran yaranka Mata nagidan miji Basu da hakki akankane Kuma angayama basajin haushin abinda kakewa nabil su baka musu da namiji haukane ko Dan shine auta Kuma namiji guda daya ayaranka dagashi baka Kuma haihuwaba kake nunamai irin wannan gatan kagafa abokansa ko darajar gaisuwa bamasamu insunzo gidannan haka zasu shigemu kamar zasu bangajemu kaga shigarsu dagasu har nabil Babu ta arziki kamar ba yayan musulmaiba Kuma Babu Wanda ya Isa yayi mgn akai kahau mutane dafada yanzu asati yarannan miliyan nawa yake kashewa shishi kadai ga daukan hakkin mutane bayin Allah da yakeyi musamman talakawa Kuma Babu Wanda ya Isa yayi mgn daga Yan uwa zuwa abokai har yanzu an ganeka in mutun nasan kudinka kuma kasoshi sedai yaso nabil dadu wani abinda yakeso kowa haushinka yakeji akan irin sangarta yarannan da kakeyi Amma Babu damar mgn kullin da bakincikin irin halin da nabil yake ciki nake kwana nake yini nimafa uwace Ina kaunar yarannan Amma ba irin wannan muguwar kaunarba Ni nake Masa kaunar da zatasa ya Gama da duniya lfy yahadu da Allah lfy nake Masa kaikuwa wuta kakeso ka kaishi besaniba gani Yake gata kake nuna Masa nikuma nice yake gani makiyiyarshi wlh kokadan banso kasamu wannan mukamin na MINISTER fetir ba bakuma bakinciki nake dshiba ko Daya tarbiyar Dana nake tinani sabo ko da Yaya tarbiyarsa takare saboda kudin da kake dashi da bushashar da kake Masa nakudi bare yanzu da kudinka ya nunku Akan da kwata kwata bahalinmu dayaba alhaji kafin tacigaba da mgn
MINISTER yace ya Isa ya Isa Fatima ko Dan Kinga namiki shuru Ni wlh bantaba ganin matar da take bakinciki da kishi akan dantaba seke haba Fatima kemafa inasanki meye najin haushi haka Dan Allah inbamu hadu munnunawa nabil kaunaba waye zenuna masa shikadaifa Allah yabamu namiji sauran yarana Mata da kike mgn akai ai Suma inasansu Kuma yanzu sunbar hannuna sunkoma karkashin mazajansu Kuma nabasu ilimi tarbiya nazaba musu mazaje nagari meyarage nai musu Kuma duka mazajansu nada dukiya Babu karamin maaikaci acikinsu Kuma ko nawa sukace min sunaso inabasu Kuma haka kawai wani lokacin inamusu kyautar kudi har yanzu kinki wayewa narasa meyasa ke da faffahna bakinku Daya kuntsani nabil ke uwace agareshi Amma bakyasanshi faffah kakane agareshi shima baya,sanshi abinnan nakonamin Rai wlh narasa yazanyi daku kullin faffah cikin kirana yake Yana min fada akan nabil abin har mamaki yake bani kodai wanine yaimuku asiri yarabaku da jininku Kinga illar rashin addu'a ko da ke da faffahna Kuna addu'a sosai wlh Dabaa muku asiriba Akan jininku Kuma inhar bazaki Fadi alheri ba Akan nabil to karki Kara mgn daga yau inbahakaba ranki zeyi mugun baci ke Zan iya hanaki saboda akarkashina kike faffah kuwa mahaifinane ban Isa naimai fadaba Akan nabil Nima akarkashinsa nake tinda shi yahaifeni ficewa yayi ranshi abace ko sallama bemataba
Tana tsaye takaici ya isheta nabil yazo yashigeta shi da abokansa suna wake wake ko kallo Bata ishesuba sukasa Kai suka fice wani hawayan bakincikine yafara zubo Mata
Tace Allah Allah yashiryeku Allah yashiryamin Kai nabil kagane hanyar gaskiya kagane Ni da mahaifinka waye mesanka da kaunarka Allah kasan halin da nake ciki kaimin mgnin abinda yadameni kaikace arokeka Kaine me maganin kowace matsala Allah kaganar da mijina uban yarana alhaji
Daki tashige takwanta saboda kanta da taji Yana ciwo
Iyace take kwallawa shatuwa Kira ke shatuwa bazaki fito kije kiyomin karaba daganan kikaimin nikan tuwanba kinsanfa nayi fishi da iyayanki akanki yanzu da kaina Zan nayin girkina tinda basa sanki basasan abinda nakeso fito Yar jikalleta takwarata Yar gatata maza fito kitafi
Shatuwace tafito daga daki tana turo Baki tana kunkuni tana dire dire gawata dammara Tasha ta kulle kugu sosai ga Tasha jambaki da jar hoda kwalliyar dai in angani anga ta Yan kauye da Babu wannan kwalliyar da kyanta zefi fitowa sosai gata farace tar kyakkyawa sosai Amma kwalliyar fuskarta taboye kyannata tace iya gani wlh kin iya damun mutane inakwance Ina hutawa kin dameni nafito togani seki kawo nikan natafi Kuma wlh du Wanda yaimin innafita Sena Rama kema kinsani
Iya tace kinmin dedai shatuwata mesunana jikalleta natsaya Miki duwanda ya tsokaneki kirama Nima Zan tare Miki kinji maza dauki kitafi gakudin nikannan karki Dade sosai
Daukan nikan tayi tafice tana ta tsalle tsalle tana Yan wake wakenta na kauye da Kara ahannunta in akuya tagani se ta zamgamata wannan Karan na hannunta ko kaza Yara kanana kuwa daga sunganta tataho da wanna dogwan Kara kaucewa suke ahanya kartaci zalinsu Allah yazubawa shatuwa tsokana da masifa ga tsiwar tsiya Babu Wanda taragawa babba ko yaro ko saanninta shayinta suke Haka kawai in tanajin tsokana take zuwa ta tsokano inkuma fada taga anayi intazo shigewa siyan fadan take yadawo kanta har tawaga take da ita ta kwawaye saanninta da Yara haka in tafito zasu dunga binta abaya ko Aiken yarinya uwarta tayi inhar yar tawagartace tofa indai tafito Kuma suka hadu da yarinya ahanya tofa Dole tabita tafasa zuwa aikan uwarta setacewa yarinya tatafi gida sannan zata tafi Dan mugun tsoranta sukeyi Yan tawagarta kowa yasansu acikin garin mazagai dake kauyan Kano kowa Kuma yasan shatuwa tsokana masifa takenta kenan tindaga kofar gari inkace kana neman gidan su shatuwa masifa shatuwa tsokana zaakaika har gidansu Dan tayi suna naban mamaki cikin garin mazagai iyayan Yara kuka suke da ita kullin suna cikin Kai kararta yarinya ko tana gida uwarta tasata aiki inhar shatuwa tazo har cikin gidansu yarinya tai sallama takwallawa yarinya Kira kome take ajjewa take tabita iyayan Yara daga sunga shatuwa akofar gidansu ko tashigo musu gida korarta sukeyi Amma abanza se yarinya tabita arana ana kaiwa iya kakar shatuwa Babu adadi sedai in Bata fitaba iya batasan bacin ran jikarta shatuwa Kuma bataso akawo Mata karar shatuwa zage mutun take itama iya inhar Akan shatuwane tofa kokai waye zaku Bata da ita in kanasanta tofa kaso shatuwa
Wata me awara shatuwa tagano dagudu tabita tace ke ladidiya wanakama wakika zaga Kika gudu jiya Daman yau nakeso nasa akamominke segaki nakamaki ajje nikan kwaryar nikan tayi tasa hannu tatunkude bokitin awarar Kan yarinyar tasa kafa Tai bal da bokitin yashiga kwata tarufe yarinyar da duka tace wannan hukuncinane kafin nasa su jummai suyimiki nasu hukuncin gobema kikara in angayamiki ana tsokanata nakyale
Kuka yarinyar taitayi Babu yanda zatayi saboda shatuwa tafita karfi Haka tatafi gida tana kuka tabar bokitin awarar da awarar awakai naci
Wajan Nika shatuwa takarasa tana zuwa itace takarshe akwai layi gabanta haka tashige layin taje tasa kwaryarta agaba tarike kugu tana ta jinjiga tana jiran taji memata mgn me nikan tsohone yace ke shatu meyasa bakyaji yanzu bakiga mutane agabankiba kikazo Kika shigesu kikasa naki agaba se da naje har gida naroki iya nace Kar akara turoki injina nikan tuwo shine yau kikazo ko kafin yarufe Baki
shatuwa tarufe wani yaro da duka tako Ina dakyar menikan yarabasu Dan azauna lfy daukan nikanta yayi yanika Mata yace jeki karki Kara dawomin inji wannan shine nafarko na karshe yarinya sekace annoba du inda kikaje se anyi fada dake baa kwashewa lfy dake Ni bani kudin nikana kitafi
Daukan nikan tayi tadora aka tana Waka tana tafiya wata kawarta tagano tace lami Ina Zaki
Lami tace aikena ummanmu tayi kantudo tace naimaza nadawo
Shatuwa tace Yasin Baki isaba sekin rakani har gida kafin kitafi naki Aiken
Lami tace wlh kema Baki isaba kijamin duka agida Daman ance saura naganki nabiki ga yayanmu yadawo angayamai abinda kike samu mukeyi yace karyakara ganina dake gashi mugune ya iya duka Kinga tafiyata naimaza nakai ance nakaiwa gwaggo rugwan da wuri da zafinshi karya huce
Shatuwa tace Kan ubancan kinma Isa Ni ince kirakani kice aa yau zanga yanda zakiyi kishige Bari kiga yanda zanyi da rogwan tinda bazaki rakaniba
rarumar lami tayi da dambe bayan ta ajje kwaryar kannata kafin lami tayi yunkurin kwatar kanta langar rugwanta tabare akasa wannan abin yabawa lami haushi sosai tarufe shatuwa daduka haka suka doku Dakar wani tsohu yarabasu yakorasu gida
Kafin shatuwa taje gida har ankaikaiwa iya karar shatuwa tafi uku shatuwa Bata koma gidaba sewajan magariba har iya tadau mayafi zata bita tashigo
Iya tace jikalleta kindawo anzo ankawomin kararki nazagesu nace wayace su tsokaneki dabasu tsokanekiba da Baki kulasuba ko shatuwata
Tawashe Baki tace eh iya sune suke ta tsokanata suna batamin Rai nakuma billahillazi du Wanda yaimin Sena mishi
Bandaki iya tashige Ashe baban shatuwa na labe jira yake yasamu damar yanda zekama shatuwa damkar shatuwa yayi yazare Mata Ido yace intai mgn iya taji Shi da itane shatuwa kome take tana Bala,in tsoran babanta Dan baya Mata tasauki baya goyan bayan irin abinda takeyi Babu yanda zeyine iya mahaifiyar shice koma Dole yai Mata biyaiya wani abinda iya takeyi har da tsufa shiyasa yake shuru bangaransu yajata sata adaki yaimata duka
yace meyasa arana ake kawo kararki Babu adadi ke wace irin yarinyace ko ance Miki rukwan Kaka haukane in iya tsufa na damunta kekumafa meyake da munki aljanu kome kullin burina kinutsu kizama yarinya tagari kiyi ilimi mezurfi Ni da mahaifiyar ki burinmu kenan Amma abin yagagara kinki ganewa haka kike zaune Babu Arabi Babu boko naso nakaiki makarantar kwana kibamabar garin gaba dabaya Amma iya Taki yarda daga na Mata mgnar setasa kuka wlh karna karaji ankawo kararki gidannan bakisan iya rashin mutuncin da take yiwa masu kawo kararki Dan tsufanta suke barinta dakuma darajar sanin manya Daba hakaba wlh datini anyi maganinku ke da iya ji da yau kinsan nawa nabiya mutane kudin barnar da kikeyiwa mutane hakuri kuwa har yawun bakina yabushe saboda ba da hakuri
Kuka shatuwa take jikinta na fari tace Dan Allah Abba kayi hakuri bazan kumaba nadena daga yau
Yace ke din kuwa fece kibani waje
Tana fita tatakarkara takurma wani ihu tace wayo Allah iya Abba yakaryani yayi raga raga Dani Dakyar zankai gobe
Ai iya Bata karasa metakeba abandaki Tai cilli ta buta tafito dagudu tana cewa kedawa kedawa
Tace abbane yai min duka Wai nafiya fitina Kuma Wai senayi karatun boko Kuma Wai takwana zekaini
Masifa iya tafara tace Yana Ina wato yarannan baze Dena shiga harkataba ko baze Dena dukankiba kenan Sena Masa Baki yabi duniya Wanda besan darajar Daba bokoko awuta wlh ba da niba Babu wani karatu da zakiyi nake koya Miki na Allo da na koya har da karatun mekwanciyar tsakar daki du Zan koyamiki tashi kije daki Bari naje wajan nasu nasamesu shi da munafukar uwar Taki da take zigashi Ni nataba ganin shashashar uwa irin suwaiba babarki kihaifi yarinya acikinki kina ziga babanta Yana dukanta ba lefinki bane bakinciki kikeyi Dan basunan mahaifiyarki akasaba sunana akasawa shatuwa Dole ki tsaneta yi kwanciyarki inazuwa Zan karbomiki abinda suka dafa kici sallarma inbaki samu kinyiba Gobe kyarama
SUWAYE IYAYAN SHATUWA DA KAKARTA IYA
Iyayan shatuwa haifanfun garin kanone cikin kauyen Kano mazagai sunan kauyen kenan anan mahaifin shatuwa umaru yaga mahaifiyar shatuwa mesuna suwaiba ya aura sunyi auran soyaiya da kwanciyar hankali Allah bebasu haihuwa dawuriba har sunfara finda Rai Allah yabawa suwaiba ciki sunyi murna bakadanba Allah yasauki suwaiba lfy tasamu yarinya mace ranar suna taci suna aisha tinda baban shatuwa ya auri suwaiba gida daya suke zaune da iya saboda baban umaru yarasu iyace tarege Dan Haka yace suzauna gida daya da iya ko suwaiba tana temakwanta da aiki saboda duka Yan uwanshi ba agarin suke da zamaba du suntafi inda suke aiki da matansu susu Tara iya tahaifa yanzu suwaiba yaranta shida tindaga Kan shatuwa Allah yakawo Mata haihuwa akai akai kafin tayaye tasamu wani cikin Aisha sunan iya itakuma da akasawa shatuwa sunanta tace ita bazata iya fadar sunan da su suwaiba suke fadawa shatuwaba ita nata zatana cemata daban shine tasa Mata shatuwa sukuma su suwaiba suke Kiran shatuwa da humaira wani lokacin Suma shatuwa suke cemata Dan iya tace batasan humara suna Kiran ta da shatuwa tinda aka haifi shatuwa duwata kulawarta takoma wajan iya ita taraineta Kuma ita ta yayeta bakaramin gata da sangarta shatuwa iya tayiba Dan tana nuna Mata so da gata ko dawasa Bata Bari adaki shatuwa haka shatuwa take zaune Babu Arabi Babu bako gashi yanzu shekarar shatuwa Sha hudu
Nabil ne awajan shakatawa Sha da abokansa shi Yana gefe cikin wata runfa azaune Kan wata kujera Kayan Shane kala kala agabansa yadora Daya Kan Daya yanajin waka Yana binsu da kallo abokan Kuma inbanda shaye shaye su da yanmatansu Babu abinda sukeyi
watace ita Daya tataso zata shige wani taje gurin nabil yaran yace Mata Iska nawahalar Dame Kayan Kara in dai nabil ne wlh sedai kimutu bazaki taba samun abinda kikesoba awajanshi dankuwa shi yanmata basa gabansa du wani shaye shaye da kikasan anayi Banda nabil danshi duka bayayi kawai shi Dan ya hulene shikadai du wani gurin shakatawa yanasan zuwa Kuma shikadai yakeso yayi rayuwarsa awajan bar shi dai dajin Kade Kade da wakoki da Kuma rashin mutunci in kashiga gonarsa mu har tinani muke nabil bashi da lfy kamar se annemar Masa magani Yana gani zamuyi yanda mukeso da yanmatanmu agabansa amma shi Babu shi ko akansa inmunyimai mgn seyace shi Yana da kankami bayasan kazanta ba ze iya taba kowace maceba ko yahada jiki da ita yafiso yayi rayuwarsa haka Dan Haka karki kuma Masa mgn Akan Wai kina sanshi indai nabil ne zemiki wulakancin da Bazaki taba zataba Ni Dame nabil yafini da kikaki Sona Ina tabinki kina min wulakanci yarinya kizo inda akesanki kibar wancan Mara lfyar da ko Mata nawa aka ajjemai baze iya sarrafasuba sedai yakallesu da Ido
Yarinyar tace mesuna finah indai Akan San nabil ne yanzu nafara Kuma semun kwanta gado Daya da nabil senayi yanda nagadama dashi kanaji kana gani kwalelanka banayi ko ana Dole
Tashige Tai tafiyarta wajan nabil
Saurayin dariya yasa yace Allah yaba da saa ai Bari bashegiya bace da ubanta yanmata
Finah nazuwa gun nabil tabaya tarungumoshi tana sauke numfashi tace Dan Allah nabil karkace komai karkaimin mgn sanka da shaawarka zasu kasheni kabarni naji dumin jikinka Dan Allah kazo muje dakin da nakama ko zafine karagemin kaji
Ranshine yai mugun baci afusace yasa hannu yai wurgi da ita tafadi gefe Daya tashi yayi yarufeta da duka yace ke har kin Isa kihada jiki Dani kazama irinki ninan da kike gani babu matar da zanhada jiki da ita kema yau da Kika tabani kinyi babban kunkure arayuwarki Dan Sena hukuntaki Konasa gusire Miki hannu Ni Nan da kike ganina Mata basa gabana bani da lokacinsu karki Kara zuwa ko tawajan inda nake awaje inkin ganni ninan da keke gani bana Zama guri Daya da Mata natsani Mata bare har su taba jikina banaso yanzu kinja senaje nayi wanka kin batamin jindadin da nakeyi awajannan inacikin farinciki kinkama kin batamin shi yaranshi ya kalla da Ido dagudu suka taho kuje ku hukuntata Senace kusaketa zaku saketa
Abokansane sukai tabashi hakuri suna rokarwa finah harya hakura yatashi yabar wajan Rai abace yatafi gida
WAYE NABIL DA IYAYAN SA
Mahaifin nabil alhaji sani haifenfan garin kanone zamane yakawoshi Abuja mahaifiyar nabil hajiya Fatima haifanfeyar yolace bafulatanace gaba dabaya aikine yakai alhaji sani Yola yaga hajiya Fatima soyaiya tashiga tsakaninsu manya suka shige gaba har sukai aure
alhaji sani mahaifinshi malam usiman da Yana cikin garin Kano da Zama saboda kasuwancin da yakeyi lokaci daya basansa mahaifi yace Masa yanaso yakoma kyauyan mazagai da Zama saboda gidansu na gado tin iyaye da kakanni gidan yake Kuma sunyiwa iyayansu alkawari bazasu sai da gidanba Dan Haka baban alhaji sani yakoma can dazama yazauna da danginsu awannan babban gidan tindasu sun tsufa sundauko gangara shine mekula da danginsu nacan lokacin su alhaji sani du sun girma Yama Gama makaranta yafara aiki besoba babansa yakoma wannan kauyen na mazagai dandai Babu yanda zeyine tindaga lokacin komai na baban alhaji sani yakoma mazagai Dan Haka akai akai su alhaji sani shi da iyalinsa suna zuwa siyara mazagai gai da kakan su nabil malam usiman
haihuwar Fatima matar alhaji sani bakwai biyu sun mutu saura biyar Kuma duka Mata take haifa ata karshen tasamu da namiji wato nabil shine nabakwai ayaransa danhaka yadauki San duniya yadorawa nabil bayasan lefinsa akasar waje nabil yai karatu Dr ne shi Amma saboda gatan da yake dshi yaki yafara aiki har asibiti nakanshi alhaji sani yace zebude Masa nabil yace bayaso shi bashi da lokacin duba mutane tinda Babu abinda yarasa narayuwa amma duda Haka seda yabude Masa katan asibiti agarin Abuja
yanyun nabil Mata akwai basira akwai hamida akwai Amina da mufida dukansu sunyi sure suna gidan mazajansu uku nakasar waje acan mazajansu suke aiki aminace agarin Abuja anan mijinta yake aiki
iyayan alhaji sani da Yan uwan babansa irin masu kudinnanne kusan dukansu masu kudine alhaji sani shima lokaci daya yabunkasa yazama mekudi Yana kasuwanci Yana aikin gwaunati har akabashi mukamin MINISTER shine yabar Kano yakoma Abuja da Zama Amma Yana da gida akano Kuma du lokacin da yagadama suna zuwa hutu shi da iyalinsa
mahaifin alhaji sani yatsani irin halaiyar Nabil basa shiri Shi da nabil kwatakwata kullin cikin yiwa nabil fada yake da nasiha da alhaji sani shima yanashan fada wajan malam usuman saboda lalata nabil da yayi da gata
hajiya Fatima itama batasan halaiyar Nabil kullin cikin yimasa nasiha take Yan uwanshi matama basasan irin abinda yakeyi saboda gababadaya alhaji sani yatsayawa nabil kome yagadama yayi har masu kula da lfyarshi yazuba Masa jamian tsaro Dan Kar wani Abu yasamu dansa Kano Abuja ansan nabil da irin rashin mutuncin da yakeyi musamman Akan titin mota ko inkataboshi zakaga rashin mutuncinsa ana tsoran nabil sosai musamman masu karamin karfi atsarinshi Kuma yatsani Mata baya shiri da su sekuma gashi mahaifiyarshi hajiya Fatima Bata goyan bayan abinda yakeyi Kuma batasan alhaji sani yake nuna Masa gata seyake gani itama basansa takeba duwani gidan holewa da otal nabil yasansu seya kwana awajan fatinsu Amma kome yake baya shaye shaye abokansa sunyi sunyi yakoya Amma yaki matanma anyi anyi yakoyi harka dasu yaki konawane abokansa sukeso zebasu suyi watsewarsu Amma bandashi yanMata nasanshi kamarme Amma shi basa gabanshi akasar wajema yanmatan turawa sunkawomai Hari Amma bashi da lokacinsu gashi da karfin shaawa Amma bashi da lokacin yanMata bare Kuma maganar aure ko ciwan mararshi yatashi sedai yanemi magani wani lokacin har kwantar dshi ake a asibiti in ciwan yatashi
alhaji sani nada katan gidan gona amazagai nabil nasan gidan gonar sosai intarayo Masa can make tafiya yayini Acan ko yakwana inyaga dama yaje wajan kakanshi malam usiman Wanda suke Kira da faffah wani lokacin Kuma har yaje mazagan yagama hutarwarshi agidan gonar beje wajan kakan nashiba sedai shi malam usuman din inyaji labarin zuwanshi yaje yasameshi acan yaimasa fadan da zemasa yataho gida du lokacin da nabil zeje mazagai baya shigar arziki wanna shigar ta nigogi ita yakeyi mutanan garin suyi takallanshi anacewa jikan malam usuman ne wasu Kuma suyi Allah wadai da shigar da yakeyi Kuma du Wanda yabi hanyarshi inyana cikin mota shi da yaransa buge mutun sukeyi Dan Haka har mutanan gari sunsani anaganin motucinsa zaahau kaucewa ko harabar gidan gonar baabi dosai se intakama dole
Rai abace nabil yashiga mota direbansa yajashi yaransa suka maramai baya dagudu motucin suka fita daga wajan shakatawar dokar nabilce inyana cikin mota baatafiya ahankali dagudu ake tafiya dashi gida yasa aka kaishi tinkan motar tagama tsayawa yabude murfin motar yafito yashige cikin gida kowa yakauce Masa sun durkusa bangaran mahaifiyarsa yashiga lokacin wata Yar aikin hajiya Fatima takwashe kololin da akaci abinci zatakai kicin taga nabil yashigo saboda tsoro gabadaya rudewa tayi tarasa yazatayi Kuma duka hannunta biyu kololinne
wani mahaukacin kallo nabil yawurga Mata yadaka Mata tsawa yakaraso gabanta yadauketa da Mari ya tunkudeta ita da kololin suka Fadi kasa seda kashin kafarta yaamsa wata Kara tasaki
yace kunyi mugun rainaniko Yan aikin gidannan gaba dabaya Sena canjaku Kuma gaki mace shine Zaki tsaya kina kallona har Kiki durkusawa ahanya kina kallona kina wani zaremin idoko Wai meyasa Mata kuke shiga harkata nikuma natsaneku bana sanku bana kaunarku du halinku Daya Baku da kamunkai kema da niyarki kihada jiki Dani da kinyi babban kunkure arayuwarki
Kukan Yar aikinne yasa hajiya Fatima fitowa dasauri Dan tasan kowaye zesa wani kuka agidan tace hm ai Daman nasan sekai Dan mankuli da yaji Kai nabil kaji tsoran Allah katinafa duniya ba matambata,bace karfa kamanta inba mutuwa akwai canjin rayuwa Babu Kyau wulakanta Dan Adam dufa Daya muke awajan Allah tinda shine yayomu kaguji ranar ladama dajin kunyar abinda ka aikatawa mutane karfa rudin duniya yarudeka kamanta da mutuwa da canjin rayuwa nabil wannan abunda kakeyi bahaline mekyauba kadena kaji tsoran Allah waima na tambayeka memata suka yimaka katsanesu haka Anya baka da shafar aljanu nabil kadaure kashiga isilamiya ko malam limanne me Jan sallar masallacin unguwarnan Yana koyamaka karatu ko kanabin wayanda yake koyarwa bayan sallar magariba da Isha kaima kakaru da abubuwa dadama Dan nasan rashin lilimin addinin musulinci ne yake damunka Dama Wanda yai rayu akasar w
turawa ta Ina yasan wani karatun addini bare yai aiki dshi gaba dabaya akidar turawa du kabi ka kwashe Harda Wanda batasuba
Wata dariya nabil yakwashe da ita yace Kai mommy wlh kinsani dariya da Raina amugun bace yake Amma wannan maganarki takarshe da kikayi tasani dariya Wai naje malam liman yakoyar Dani konabi wayanda yake koyarwa haba mommy Dan Allah yakikaji da kike fadar maganar Nan Ni wlh mommy narasa meyasa bakya sona daddy yafi Sona Kuma agaban Yan aiki kike kunyatani ke malama bace daga wajan inkingama kukan munafurcin tinda kingmajin fadan da mommy tagama yimin Kuma zamu hadu kema barin gidan zakiyi mommy kinsan meyasa natsani Mata Ina da dalili meyawa Amma bazaki ganeba mommy natafi dakin daddy acan Zan kwanta nahuta yau wata mahaukaciyace tabatamin Rai shigewa yayi besaurari me hajiya Fatima zata Kara cewaba
Girgiza Kai hajiya Fatima tayi tashige wajan da yar aikin take tabata hakuri
Masoyana barkanmu da sake haduwa asabon novel Dina somin tabine inkun bani kwarin gwiwa da sharhinku nacigaba inkuma Banga ruwan sharhiba natsaya da rubutawa inyamuku Dadi zanga kwarin gwiwar da zaku bani inkuma beyiba zanji shuru nikuma na ajje alkalamina
Bababu Wanda zanturawa ta PC karma abiyoni bana turawa ngd masoyana fatan alheri馃
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama* 鉂ゐ煈�
*'Yar kwalliya* 馃コ馃拑
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹
馃憼
馃拕馃拝 *DAN MINISTER* 馃拝馃拕
馃馃
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
Alhamdulillah Alah kulli halin
3-4
Nabil da yashiga dakin mahaifinshi kwanciya yayi yarufe Ido tinani yake akan nacin da Mata sukeyi akansa na suna Sansa afili yace bana sanku kukuma Kuna Sona meyasa kukemin haka bazanyi aureba bani da lokacinku rufe Ido yayi yafara bacci lokaci daya ciwan mararshi yatashi tin Yana daurewa yanaso yayi bacci har abin yagagara juyi kawai yake tayi lokaci daya yahada gumi duda sanyin esin da ke dakin
Ana Haka alhaji sani yashigo dakin Yana ganin halin da Dan nasa yake ciki lokaci daya yarude yakarasa wajanshi labil baka da lfyne meyake damunka
Saboda azabar ciwan da yakeji ko mgn yakasa hannu yasa Yana nunawa baban nashi mararsa
Dasauri alhaji sani yadau waya yakira Dr dake duba iyalinshi ya,fadamasa yai maza yazo dansa ba lfy cikin kankanin lokaci Dr yazo yafara dubashi yaimasa abinda yadace lokaci daya bacci menauyi yakwasheshi
Dr yace yallabai da matsalafa in har Baku dauki matakiba akan nabil Nan gaba kadan ze iya rasa kwayoyin haihuwarsa gabadaya saboda wannan temakwan da ake bashi zedena aiki Dan yanzu magani baya Masa aiki se allura itama nangaba kadan zata Dena aiki ajikinshi saboda Yana da karfin shaawa me zafi agaggauta yimasa aure Dan asamu mafita Kar abin ya illata lfyarshi Dan har aiki abin ze iya sawa aimasa nangaba
Numfashi alhaji sani yaja yace to Dr ngd insha allahu zaaimasa aidolema aimasa Dan kullin burina Naga gudan jinin nabil aduniya
Sallama sukayi da Dr yatafi
alhaji sani dakin matarsa hajiya Fatima yatafi
Yakarasa wajanta yazauna cikin damuwa yafara fada Mata abinda Dr yace akan dansu nabil
Hajiya Fatima tace anzo wajan alhaji aini tintini naso aiwa nabil aure ko zedena wasu abubuwan da yakeyi Amma nasan ban Isa nace wani Abu akan nabil ba kayarda danhaka nai shuru da bakina Kuma da matsala nabil yatsani Mata bayasan Mata tin abin baya da muna yanzu abin nashi yafara bani tsoro gani nake kamar nabil na da aljanu kyama sosai yake nunawa Mata Nima Dan uwarsace babu yanda zeyi Dani muke zaune inuwa Daya dshi Yan uwanshi matama dandai Babu yanda Suma zeyi dasu yake hurda dasu ko hanya bayaso yahada da mace bare Kuma ai maganar aure dazu dazunnan yaiwa Yar mutane duka har targade yaji Mata Dan taganshi yashigo tarude tarasa inda zatabi ya hukuntata Kuma wace macace zata iya Zama da nabil inba Wanda batasan ciwan kantaba irinshi kokuma ta aureshi Dan kudinshi Amma inhar mace me hankalice da tinani wlh bazata auri nabil ba komai kudinku Kai dshi
Alhaji sani yace kefa matsalata dke Kenan indai akan nabil ne alheri baya fita abakinki ai nafiki sanin raayin nabil Kuma da Babu wannan matsalar tashi da tataso da bazan Masa aureba har se ranar da yasoyi Dan kansa bare harnazo wajanki neman shawara Kuma yanzu zanbawa Dana shawara akai Kuma zedauka ko bayasan mace zan bashi shawara ya auri kowace macace inde zatamai maganin matsalarsa tashi yayi yafice cikin fishi
Hajiya Fatima tace Allah yaganar dku Kai da danka alhaji daga Kai harshi kunyi nisa zankira baffah na fadamasa halin da ake ciki nasan Kai bazaka fada masaba
Shatuwace takwashi zugarta sukayi dawa cikin gonakin mutane du gonar da sukaga tamusu Haka zatasa sushiga suyi musu barna sannan subar wajan du sanda tarayo Mata gonakin mutanene wajan wasanta ita da zugar kawayen ta gonar wani me mangwaro da goba suka shiga magwaran yanuna sosai sukai Masa barna sosai Kuma sukaki barin gonar suna tawasa aciki har me gonar yazo ya samesu yaga barnar da sukai Masa ransa yayi mugun baci sosai Kara dogo yadauka yahau dukan du Wanda yasamu Dakar suka,samu suka gudu du yasansu yagane fuskokinsu rainshi abace yatafi wajan megari yakaimai Karar abinda su shatuwa sukai Masa
Megari sawa yayi akakira iyayan yaran da su kansu su shatuwa har da iya seda tazo cewa tayi se tazo taga me zaayiwa jikarta
Gaba dayansu sunzo sun amsa Kiran megari Nan magari yasa me gona yafadi barnan da su shatuwa sukai Masa
Budar bakin iya tace to yanzu malam me kakeso aimaka wayace karka zagaye gonarka kai Mata kofa yanda Babu Wanda ze iya shiga lefinkane da kayi da yarannan bazasu shigarma gonaba har simaka barna yarannan kwatakwata nawa suke yaran da basugama hankaliba Dan abin kunya kakwaso jiki kakawo kararsu wajan megari yanzu Dan Allah bakaji kunyaba tsofai tsofai dakai
Megona yace ke tsohuwar banza kishiga hankalinki Daman Ina da labarinki inkinwa mutane sunbarki saboda tsufanki Ni inkinmin ba barinki zanyiba kwatakwata shekara nawa Kika bani da zanji tsoran yimiki mgn har naraga maki saboda girmanki ke ko tsoran Allah bakyaji zomuje kiga barnar da jikarki tasa akaimin agona Kuma wlh da nazone akan ajamusu kunne karsu kuma Amma wlh yamzu se anbiyani tinda Babu mutunci gobema kukara barin su suje gonar mutane suyi musu barna
Megari yace Wai ba afada kukeba kuke wannan abinba Karna karajin bakin wani anan iya gaskiya bakya kyautawa haba iya meyasa kike Haka tsufa haukane du abinda kikewa mutane in ankawo Miki Karar shatuwa nasani mutane nazuwa su fadamin ninake Basu hakuri saboda zaman mutuncin da kukayi da iyayanmu nake barinki Amma wlh Daba hakaba da matakin da zan dauka akanki ke da iyalinki da se kinyi mamaki sosai yanzu tinda kingoyi bayan jikarki shikenan zaayiwa mangwaransa da goba kudi ki biyashi ke da iyayan yaran da taja sukaje sukayi barnar Kuma du sanda suka Kuma harku iyayansu se mundau mataki akanku suma Kuma yaran bazamu barsu sutafi hakaba se nasa anmusu bulala yanda Nangaba bazasu kumaba
Kafin megari yagama yanke kudin da su iya zasu biya Sega wasu masu gonar Suma sunkawo karar su shatuwa Haka megari yahada yasa iyayan yaran da na shatuwa suka biya kudadan barnar da sukayiwa masu gonakin megari yasa dogarinsa yaiwa su shatuwa bulala sosai ihu shatuwa take kurmawa haka iya ma take kurma ihu daga anzubawa shatuwa bulala Haka iya zata takarkara tazuba nata ihun du sukabi suka cika wajan da ihu
shidai umaru mahaifin shatuwa takaici yahanashi mgn ga takaicin uban kudin da akasu suka biya gana shatuwa da na iya tinanin irin hukuncin da zeyiwa shatuwa in sun koma gida yakeyi
Nabil be farka daga bacciba se wajan magariba Yana tashi yafito bega kowaba bangaransu yashige yaje yai wanka yafito Yana zaune afalo alhaji sani yashigo shi da hajiya Fatima suka zauna kusa dshi
Alhaji sani yace nabil yajikin naka
Yace da sauki daddy
Nan alhaji sani yafadawa nabil abinda Dr yafada Akan cutarsa yaku Gaya Masa shawar da suka yanke nayi Masa sure
Dariya nabil yayi sosai sannan yahade Rai yafara mgn yace daddy kafasan matsalata da raayina natsanar du wata yarinya mace Ni Babu wani aure da zanyi wlh Dan Zan iya lahanta Yar mutane abanza wlh Dan ko gida daya Bata Isa mu zauna tareba Ni fa daddy bani da raayin aure bazan yiba mezanyi da mace nasan daddy wannan ba raayin kabane raayin mommy ne da wannan tsohon faffah Yama gangara kowa yahuta yaki mutun se shegen taurin Rai yaki mutuwa wlh du sanda tsohonnan yamutu Babu kukan da zanyi Kuma in har aka dauramin aurannan da kowace yarinyace sedai faffah yazauna da ita ko mommy ko Kai daddy Danni bani kuka aurawaba Bari kuga yauma Ni ba agidannan Zan kwanaba a otal Zan kwana muna da cashiya da bazaniba Amma saboda kun batamin Rai Dole nabar muku gidan Wai yau meyake faruwa da nine ake tabatamin Rai gobe America Zan tafi nahuta da nanjeria gabadaya Dan nasan wannan tsohun zeyi kirana naje Kuma bazaniba Nan da sati biyu ma muna da fatin da zamu agidan gonarka na mazagai
tashi yayi yaje yashirya yai ficewarsa ko sallama bewa iyayan nashiba yai ficewarsa yabarsu zaune afalo
Hajiya Fatima tace kunfi kusa alhamdulillah tinda har mahaifinka be bariba bare Kai kaga tafiyata ai bani da tacewa akan Dan gwal tashi tayi tabar alhaji sani Tai tafiyarta abinda zemata anfani
Alhaji sani kanshine yadau caji Yana ta tinanin yanda ze yiwa nabil aure saboda bayaso yarasashi afili yace nabil kayi hakuri banaso narasaka Dan Zan shiga wani Hali kilama Nima nabika Dan bazan jure rashin ganin,kaba nabil yanzu menene abinyi ita Fatima Ina zuwa wajanta zatahau gayamin bakar mgn tahau yiwa mutane waazi Zan ta rarrashinka nabil har seka yarda da mgnar aurannan
Yau nabil yadawo daga America satinsa biyu Acan shi da abokansa beso dawowaba saboda fatin da zasuyi na murnar ranar haihuwarsa a gidan gona na mazagai zaayi Dan Haka yadawo shi yace anan yake so yayi shagalin murnar ranar haihuwarsa saboda San gidan gonar da yakeyi kwansa biyu da dawowa aka hada shagalin
yau akeyin taran yagaiyaci manyamanyan abokansa du zasuzo bakaramin kudi akakashe awannan taran murnar haihuwar tasaba fadama Bata bakine du wannan abinba akeyi hajiya Fatima da malam usuman kakan nabil du Basu saniba taro yayi taro kowa yazo shikadai kawai ake jira motocinsane suka jero Akan layi sababbi dal alhaji sani ne ya canjamai su motocin masu dankaran kudi daga kasar waje aka kawosu shigarsama tawannan ranar daban take Haka motocinnan suka shigo garin mazagai dagudu suna badawa mutane kura kowa se kaucewa yake lokacin shatuwa da zugar kawayanta sunfito zasu Wasa sukazo zasu shige tagabansu motocin saura kadan su buge shatuwa akwai wani ruwa dake tare ahanya takai motocin sukabi tacikin ruwan gabadaya wannan ruwa yabatawa shatuwa jiki motar har tana gogarta shatuwa seda tafadi kasa ta kurje abin yayi mugun batawa shatuwa Rai motar da nabil yake ciki ita tafi ballatsawa shatuwa ruwa ko su tsaya suka shigesu warsu dagudu
Abin yamugun konawa shatuwa Rai tace Kan uba wayannan suwaye yau senaga ko suwaye musamman wannan motar da tafi kowacce Kyau aciki wlh bazan yardaba Sena Rama yau zasuga mezan musu
Kawayan nata sukace Kai jikan faffah usuman ne wlh karki yarda sekin Rama muje murakaki muma zamu tayaki
Dagudu sukabi motocin har motocin suka shiga gidan gonar ahankali su shatuwa suka faki idan mutane suka shiga gidan gonar Suma Babu Wanda yakula dasu
nabil aka budewa kofa yafito habawa Nan guri yadau shewa anamasa oyoyo su shatuwa Baki suka saki suna kallan ikwan Allah namiji suka gani da wata shiga Wanda Basu santaba harda su sarka yahade Rai sewani Shan kamshi yake
Me shatuwa zatayi inba dariyaba sauran kawayantama dariya suka fara nabil jiyayi kamar anamasa dariya juyawa yayi bega kowaba cigaba yayi da tafiya wajan da aka tanadar Masa Dan zama
Anfara gudanar da shagali du su shatuwa nagani wajan tayoyin motar da nabil yafito ciki shatuwa taje dakanta tanemi kusa ta fanfasa duka hudun bayan tagama Kai tsaye wajan nabil tadosa tabayanshi taje da ruwan kwata dauke ahannunta acikin wani gwangwani tabayanshi Tatsaya
tace Kai Dan daudu rabi aljani rabi namiji rabi Dan daudu juyo kaganni nicenan shatuwa masifa tsokana jikar iya ikwan Allah kowa yaci tuwo Dani Miya yasha
Nabil cikin mamaki dajin maganar shatuwa yajuyo ai shatuwa batayi watawataba tajuyemai ruwan kwatarnan akansan da jikinshi
Tace baamin ban ramaba da yau banrama abinda kaminba dako bacci bazan iyayiba saboda takaici gababa in kazo garinran in kaganni kakara watsamin ruwa ka bugeni nafadi su jinmai kuyi Masa Wakar danace zamuyi masa
Nan suka faramasa Waka dandaudu meshigar Mata rabi aljani rabi namiji Dan daudu matamaza meshgar mahaukata kowa yatabomu semun Rama katabo shatuwa jikar iya ikwan Allah
Dan mamaki da takaici wata Kara nabil yasa yaikansu dagudu zedaka kallone yakoma kansu kowa na mamakin meya hadasu Kuma yaakai yaran suka shigo wajan dakyar Nabil yakama shatuwa sukuma yaransa suka Kama kawayan shatuwa kida nabil yasa aka kashe
Nabil yace yau Wana irin hukunci zan muku yau me zan muku nahuce ni kuka batawa ranar haihuwata ke Yar kyauye mezubin mahaukata nikika yiwa haka da ruwan kwata Kika batawa jikina kusake Wakar da naji kunayi min
Shuru kawayan shatuwa sukayi suka kasa mgn saboda yanda nabil ya tsoratasu dukansu jikinsu rawa yake Dan sun tsorata dashi sosai
Shatuwa tace au Wai tsoransa kuke Amma kun bani kunya wannanne zebaku tsoro Toni Bari naimaka dandaudu meshigar Mata rabi aljani rabi namiji nandaudu matamaza kowa yatabamu se munrama
nice shatuwa
Kafin takarasa nabil yadauketa da wani mahaukacin Mari Dan bakin cikin abinda Tai Masa yarasa wana kalar hukunci zemata hannu yasa yashake Mata wuya menai muku meyasa Mata kuke Bina kintaba ganina a Ina Kika sanni sekin fadamin meyasa Mata du inda naje se sunbini se Kuma sun batamin Raina kifadamin Kona sumar da ke meyasa Kika batamin ranar haihuwata kinsan dogwan burin da nadauka Akan wannan ranar kinsan daga Ina nadawo Dan wannan ranar inajin kwatar da aka zubamin nasan wlh Babu meyimin haka se mace Ni bana shiga harkarku Mata Amma ku se kun shiga tawa meyasa kifadamin
Shatuwa takasa mgn Dan azaba se Ido da take zarewa Dan azaba sakinta yayi yakama hannunta na dama yamurde se da hannun yaikara ya tambatar yakarya hannun shatuwa sannan yasaki hannunta
wani mahaukacin Kara shatuwa tasaki Dan azaba tace mugu maye ze kasheni Daman matamaza dandaudu nada karfi haka kasheni zakayi da kakemin wannan tambayar Ni Ina nasani ni kasan mekamin dabaka tsokaneniba da bazan biyoka naramaba ka karyamin hannu wlh Nima Sena karya naka ko Nan gabane ta karasa mgnar tana mai da numfashi Dan azaba
Kuma Dan taurin Kai irin na shatuwa bakinta yaki mutuwa rashin kuya take tamasa shikuma Yana dada tinzira zuciyarshi na dada baci kowa Ido yazuba musu anrasa me Basu hakuri saboda tsoran nabil da bakar zuciyarshi Dan in ransa yabaci abin bakyau baa iya rarrashinsa
Nabil yakalli yaransa yace mekuke jira da wayannan mahaukatan kudakarmin su harse sun jigata kekuma bakinki yaki mutuwa ko to Bari kiga mezansa aimiki yanzu waiyau Ni nabil nine nataba mace haka da hannuna Amma yarinyarnan kin cuceni kingama Dani natsaneki kece mace tafarko da nafara tabawa da hannuna Kuma insha allahu kece takarshe Sena barmiki tarihi yau kamar yanda Kika barmin ya kalli yaransa kubarsu Haka ai sunyi sanyi ku je ku kwasomin buhunhuna acan dakin kukawomin kuga me zanmusu
Ana kawo buhunhunan yace kubude kufara samin wannan marakunyar da na karya ku kullemin ita kusata abutdin mota ku rufeta ita kadai sauranma du ku zirasu abuhu kusasu abut dasu zamu tafi ni nasan inda zamu kaisu
Andaga shatuwa kenan zaasata abuhu kakansa malam usuman yashigo gurin yaga danyan aikin da jikansa yasa yaransa sunayi cikin tashin hankali yadaka musu tsawa
Yace ku kisankai zakuyi nashiga uku nabil ze jamin mgn zaman garinnan zefi karfina adalilinka rainawa zaku kashe da banzoba mekuke Shirin aikatawa Haka nabil abin naka yakai Haka tinda labari yazomin kashigo garin katara mutane awajannan hankalina yaki kwanciya nace Bari nazo nagani wace tsiyar kake aikatawa Dan nasan halinka Dole sekayi abin fada me wayannan yaran sukai maka har wajan susu ashirin yanzu da ban zoba duka kashesu zakuyi ko Yaya nidai nasan indai akasa mutun abuhu baze shaki iska sosaiba nabil kafadamin mezakai da yarannan ko kafara satar mutane bamu saniba
Nabil yace shikenan hanaruwa gudu kazo komai yakuma baci faffah me yakawoka Nan Wana munafikinne yaje yafada ma meyasa daddy ya sai gidan gona anan yanzu Dan Allah faffah me yakawoka wajannan kokazo kunyatani acikin abokaina wlh faffah Ina raga maka Dan Kai Kaka nane Babu yanda zanyi dakai kasan me sukai min yau kasan wace ranace awajena Kai basanin mahimmanci ranar kayiba bazaka ganeba ko na fadama nifa kasan dokata na tsani Mata banasan Mata meyasa zasu zo su yimin haka Ni Babu abinda zanyi dasu Kano Zan kaisu nayardasu acan Nan yafadawa faffah abinda su shatuwa sukai Masa
Faffah yace nabil meyasa baka da hakuri meyasa kake wulakanta mutane du wannan halayan naka Babu meshi akaf iyalina sekai a Ina kasamo wannan mugun halin kayi kuskuran kula yarinyarnan bakasan itama wacece itaba yanda kake fitinanne itama haka take fitinanniya agarinnan da datayi maka Haka da baka kulataba kazo kafada min ko ka kaiwa iyayanta Kara ko megari Amma yanzu kaga abinda zuciya ta ebeka kayi ka karya musu yarinya kawayanta kasa anmusu mugun duka yanzu da ban zoba Ina zaka dasu kukama masu bin nashi manyan banza se abinda yace muku kuyi kukeyi saboda Kuna karkashinsa ana biyanku kudi acikinku kusan dukanku kun girmeshi Amma anrasa mebashi shawara tagari Dan Kuna tsoransa kace bansan ko yau wace ranace awajankaba nikuwa nasan ko waje ranace yau awajanka ba bikin murnar haihuwarka kakeba yau to nazo tayaka murna nakuma karama biki Daya akan Wanda kakeyi yau Zan karama wani farinciki yanda nasan bazaka taba mantawa da ranarba yanzu da ka karyata me kake nufi kana nufin ka karya banza baka isaba nabil baka karya banzaba kasan karya yarinyarnan me kahadawa kanka ranar auranka ka hadawa kanka wlh yanda ka karyata Kaine mijinta baka karya banzaba yau ka karyataka yau zaka aureta Zan daura maka aure da ita kaga taro biyu kenan Ni nakarama biki Daya Kar Wanda yatafi anan du kubiyomu zuwa gidan megari Dan halartar daurin auran nabil azamanku na abokansa muna gaiyatarku daurin auran nabil sani DAN MINISTER kuzo mutafi
Faffah kanlan mazan da yazo dasu yayi yace Kai kaje ka kiramin umaru baban shatuwa da Kuma iya kakarta suzo gidan megari cikin gaggawa ana nemansu Kai Kuma kaje kataho min da me gyaran karaya zuwa gidan megari
Yan uwan alhaji sani ne wayannan mutanan majiya karfi faffah sasu yayi suka daukarmai nabil cak suka samaishi amota akasa shatuwa itama amota da zugar kawayanta suka ja zuwa gidan megari du abokan nabil da sukazo fatin nashi suka bi bayansu zuwa gidan megari Dan ganewa idansu wannan auran mamakin da zaa daurawa nabil shi
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama*鉂ゐ煈�
*'YAR KWALLIYA*馃コ馃拑
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹
馃憼
馃拕馃拝 *DAN MINISTER* 馃拝馃拕
馃馃
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
5-6
Megari nazaune akofar gida akarkashi wata katuwar bishiya shi da jamaarsa segani sukayi motoci nata jeruwa suna tsayawa akofar gidan shi kallan ikwan Allah suka tsaya yi can Kuma sukaga faffah da yafito awata motar gakuma nabil ga shatuwa du anfito dsu amotar anrukosu zuwa gaban megari ana Haka Sega umaru da iya Suma sun iso wajan
Salati umaru baban shatuwa yafara yace wlh nasani shatuwa ce iya kinganiko abin naki shatuwa yaci gaba har da tsokano gari guda Daman ana cewa muzo ana kiranmu akofar gidan megari nasan shatuwa tayi halin wlh badaniba yau iya sedai koke inzaki iya baruwana wlh
Megari yace iya Isa umaru kajira muji meke faruwa ko mu Nan bamusan meyafaruba ganinsu kawai mukayi
Baffah yace du ku kwantar da hankalinku bawani abin tashin hankali bane sosai alheri ne yakawomu dukanmu Nan yanzu megari Ina neman alfarma dakai da liman da mahaifin shatuwa umaru da Kuma wayannan dattawan garin namu da suke wajannan inaso mudan koma gefe Dan da bayanin da nazo dshi zan muku alheri ne insha Allahu Allah yasa ku goyi bayana Amma Banda iya tadan jiramu tukunna in mungama tantaunawa itama akirata afada Mata aji raayinta
Megari yace to alhamdulillah du kutashi muje wayanda yace yanaso suji mgnar
Haka du suka tashi zuwa wani daki dake soran megari du suka samu waje suka zauna
Baffah ne yafara mgn yai sallama yabude da addu'a yace wani abune yau yafaru tsakanin jikana da shatuwa agidan gonar Dana sani Nan yabasu labarin abinda yafaru tindaga farko har karshe Kuma Ni na hango wani Abu alheri ne inhar kungoyi bayana Dan shima jikan nawa irin shatuwa ne ko ma nace yafi shatuwa da mugun Hali Dan tawani wajan halinsu yazo Daya tawani wajan kuma sun banbanta ta halaye Dan Haka hadin da nakeso ayi zezo dedai kowa acikin susu biyun zasu gyara junansu insha Allahu Dan na hango alheri alamarin Ni malam usuman mahaifi ga alhaji sani Kaka ga nabil Ina neman alfarma agabanku malam umaru mahaifin shatuwa yabawa jikana auran yarshi shatuwa adau rashi yau anan kofar gidan megari saboda abinda yafaru tsakaninsu Dan sukara hankali gaba ga tawagar munan nazo da ita ta Yan daurin aure Ina bawa malam umaru hakuri Akan abinda jikana yaiwa yarshi shatuwa insha Allahu ba ze kumaba Kuma Ni malam usuman namaka alkawari agaban su megari nabil da mu damgin nabil zamu rike shatuwa tsakani da Allah har karshan rayuwarta
Megari yace to fa wannan mgn batamu bace takace umaru Dan Kaine mahaifin shatuwa mu shawara ce tamu aciki Kai muke jira umaru muji raayinka akai
Malam umaru yace to gaskiya Ni wannan hadin auran baze yuwoba ban yarda dashiba Dan kowa yasanni agarinnan bawani kudi gareni ba se rufin asiri Kai Kuma baffah kowa yasanka Kai da ahalinka masu kudine barinma danka sani yafi kowa kudi azuriarka Kuma kowa yasan jikanka nibil da irin halinshi in yashigo garinnan itama Kuma shatuwa kowa yasanta da ita da iya da irin halinsu gankiya Ina gudun abinda zeje yadawo kunfi karfinmu ta ko Ina faffah shima Kuma nabil yafi karfin shatuwa ta ko Ina Dan da ba akasar Nan yai karatuba akasar waje yai karatu shatuwa fa da ko makarantar Allo batayiba bare ta boko wannan hadin baze yuwuba da matsala babba in akayishi kagafa faffah tashin farko haduwarsu me yafaru bare Kuma aka hadasu gida daya suyi zaman aure tare Kuma basan junansu sukeba Kuma nawa shatuwa take Bata wani girmaba Ina da dogwan buri akan shatuwa in Allah yabani iko Ina da burin shatuwa tayi karatu me zurfi sosai Kuma inaso in gyara ta ta Dena wannan halin nata Kuma yanzu ya zaayi da iya da ko tinanin rabuwa da shatuwa batayi ba Dan da kauna me karfi tsakaninta da shatuwa bazama ta taba Yarda da maganar aurannanba Dan bazata yarda arabata da shatuwa ba se dai kukira iya kuji nata ko zata yarda
Baffah yace karka damu umaru mudai yardarka kawai mukeso da sa albarkarka amatsayinka na uba awajan shatuwa iya kuma Ni da megari munsan yanda zamuyi mu rarrasheta ta yarda da auran Kai dai in tashigo kayi shuru karkasa Baki amaganar
Yace to shikenan Bari naje na kirata tashigo taji meyake faruwa
Umaru fita yayi yakira iya tashigo megari da baffah sukai Mata bayani nanfa Tai tsalle tadire tace batasan zanceba Babu me rabata da shatuwa bare har ai Mata aure da wani Dan gayu Kuma yanda ya karya Mata jika shima nabil se ta karyashi da kanta tace Ni iya fadan yadawo hannuna Ina yake Dan kwal uban yaro Naga shatuwa du tafadamin abinda yafaru da yaran kanku kirani ku fadamin Daman jira nake kufito na kwashe ubansa da Mari nazata dashi aNan ashema babushi yau Babu me rabani da jikanka usuman wlh banki mu doku Ni da Shiba Dan senayi zaman Yan bori Akan kafarsa shima har se na karyashi Zan tashi ai Naga yaran me kirar aljanu da yakoma kala biyu gaba Daya kamar ba Dan hausawaba Kuma kubude kunnanku kuji shatuwa dai bazan taba yarda da wannan auranba bazaaje akashemin jikata abanzaba afa garin masu kudinnan da naji ana fada shi uban yaran yake abawa dansa shatuwa suje su su sayarmin da ita sukara wani kudin Akan kudin da suke dshi
Megari rarrashin iya yayi da dadin Baki Amma fur Taki yarda
Baffah yace haba kekuwa aishatu Kaka wajan shatuwa ia bakisan yanda nake san shatuwa ba tana burgeni yarinya me kirki ga ladabi ga biyaiya na yaba da irintarbiyar da kika bawa shatuwa Dan Haka naso muhada iri da ke Baki iya tawashe Jin anyabi jikarta tin daganan suka hango alamun nasara ki temaka ki yarda da wannan hadin auran Dan Allah Kuma Kinga yau mukeso ashige da ita gidan mijinta dake Abuja Kuma Ni da kene yankai amarya da ango ke zakije kiga inda akakai jikarki da kanki acan zatayi jinya agidan mijinta zakina zuwa kina ganinta akai akai kema kina tayani ganin irin zaman da zasuyi Kuma in kin yarda da auran har kujerar aikin hajji Zan biya Mana Ni da ke muje mu rokarmusu zaman lfy Kinga har uban nabil da mahaifiyarsa du kikai musu kakar abinda da dansu yaiwa shatuwa Kinga se su jamasa kunne ko
dakyar baffah yasha Kan iya ta yarda da auran tate adaura Allah yabada zaman lfy kowa na wajan yayi murna umaru shima hamdalah yayi shatuwa zatabar gabansu yahuta da ba da hakuri da rigimar iya megari yafi kowa murna yahuta da sharia kullin
Megari yace alhamdulillah iya mungode sosai da wannan alfarmar da kikai Mana yanzu muje nasa ayi shinfida kowa ya zauna agudanar da daurin auran itakuma amarya shatuwa ashigo da ita ciki me gyaran karayar Naga ya iso tin dazu yashigo ya dorata kafin agama daura auran muntura Akira mahaifiyar shatuwa itama tasawa yarta albarka Kan atafi da ita
Nan aka shigo da shatuwa me Dori yadorata tana ihu tana komai iyama na ihu har aka Gama Dora karayar hannunta
Akofar gida Kuma Ana gudanar da daurin auran shatuwa da nabil baffah ne waliyin nabil malam umaru shine waliyin shatuwa baffah hannu yasa a aljihun nabil yaciro damin kudi ya irgi dubu dari biyu yamikawa megari yace ga sadakin shatuwa kowa ya sheda megari yasa hannu yakarba yasa albarka yanunawa kowa baffah yamayarwa da nabil sauran kudinsa
nabil yakoma hoto bakinshi yamutu yakasa mgn gani yake mafarki yakeyi wani iri yakeji zuciyarsa nayi be zataba be nufaba seji yayi anacewa Allah ya yarda aure ya dauru tsakani nabil sani da shatuwa umaru jikar iya ikwan Allah Akan sadaki nera dubu dari biyu lakadan ba ajalanba
kafin nabil yagama mamaki se jiyayi abokansa Yan tsokana sun dagashi sama suna tayashi murna suna ta Masa dariyar mugunta da tsokana
Megari ne yashiga yafasawa iya angama daura auran tafito ita da amarya zasu tafi Abuja haka mahaifiyar shatuwa tana hawaye taiwa yarta nasiha du da tasan bawani dauka zatayiba Haka aka fito da amarya shatuwa aka sata amota tare da iya akatafi
Baffah ya dada bawa kawayan shatuwa hakuri Akan abinda yafaru tsakaninsu da nabil yakuma musu alkawarin zuwa ganin gidan shatuwa in komai yanutsa hakama yabawa suwaiba mahaifiyar shatuwa hakuri tayi hakuri itama zata tagano inda yarta take in ankwana biyu Haka faffah yakama hannun nabil yasashi amota tare da tawagarsa ta Yan fati suka dunguma zuwa Abuja raka ango da amarya
Hajiya Fatima da alhaji sani sunacan basusan meyake faruwaba faffah ne yakira Amina yayar nabil yace Tai maza tataho gidansu tajirasu komai dare sunanan tahuwa zebata wata Amana yakira Hajiya Fatima itama yace Mata tashirya gashinan tare da Baki abinnan da takira tafada Masa komai yakankama Dan Haka tashirya gasunan sauran bayani se yazo ya tambayeta sani dansa nagari tace eh yace to du sujirashi gasunan
Sedare suka Isa Abuja zokiga zare Ido wajan iya da shatuwa sunga birni ko Ina da hasken wutar nepa kamar ba dareba ga dankara dankaran gidaje agarin anazuwa gidan su nabil Nan kallo yakoma sama iya dada zare Ido take saboda ganin dankareran gidan Dan baffah Haka aka bude musu gate motocinsu suka shige wajan fitowa amota ansha fama da iya cewa tayi bazata fitoba ayanke Mata Kai abinda yadada Bata tsoro ganin sojoji da bindigogi ahannunsu tadada tsurewa Dakar Amina tazo ta lanlabata tashiga
Baffah godiya yayiwa tawagar abokan nabil sannan kowa yashige gidansu sukayi sallama da ango mijin amarya shatuwa
Baffah Kama hannu nabil yayi zuwa cikin gidan da sallama ya shiga afalo yasamu hajiya Fatima da alhaji sani da su iya waje yasamu yazauna ya zaunar da nabil kusa dshi baffah yafara mgn yai sallama yace to sani da Fatima kubude kunnanku kuji me nazo dashi musamman Kai sani Dan nasan daga gunka matsalar take Nan yaimusu bayanin abinda yafaru tindaga zuwan nabil ma,agai har daura auransa da akayi da shatuwa wannan da kuke gani me karaya ahannu itace amaryar tashi Kuma itace Wanda ya karya din itakuma wannan tsohuwar itace iya kakar shatuwa tazo taga inda jikarta zata zauna yanzu amarya zata zauna a bangaran nabil cakin gidannan Kuma adakin nabil har se tawarke sannan acikin gidajanka kabasu Daya sutare acan Dan Haka ga amananan ankawo muku ta Yar mutane kuji tsoran Allah kukula da ita kamar yanda zaku kula da danku nabil
MINISTER yace baffah meyasa kahada wannan auran kafasan nabil wlh baze taba yarda da wannan Yar kauyanba Kuma nasan nabil basanta zeyiba Kuma baffah na sanka Baka tambayi nabil ko yana san ta ko baya san ta kawai ka yanke hukunci ne ka aura Masa ita wlh daga ganin yarinyarnan Bata da kunya Kuma bazasu zauna lfyba ko ta ilimin nasan nabil yafita da komai kagan tafa yarinya kamar aljana se zarzare Ido take tin da suka shigo ko ita kakar tata Naga se wani huhura hanci take tana wani zarzarewa mutane Ido wlh in har akabar nabil da yarinyarnan ancuceshi Kai nabil kana santa ko baka Santa kafada kowa yaji Dan Allah baffah inyace bayaso kabarshi yasaketa kowa yahuta Dan wannan aljanar yarinyar ba ajinsa bace
Nabil yace daddy bakinciki ya hanani mgn tin daga lokacin da yake hada auran nakasa cewa komai Dan ganin komai nake kamar amafarki Ni abinda yafi konamin Rai wai a cikin aljihuna baffah yaciri kudi yabiya sadakin wannan mahaukaciyar yarinyar wlh daddy nakuma tsanar mace arayuwata Mata sun yimin abinda bazan taba mantawaba natsani yarinyarnan ranar da nafara ganinta na tabata ta zamemin Bala,I ta zamemin alakakai arayuwa Wai yau mace akakawo gidanmu azaman matata inba Wanda ya haifi ubanaba waye zemin Haka na barshi ban dau matakiba aduniyarnan bazan taba san taba Kai bama itaba du wata mace wlh na tsanesu illa uwata da Yan uwana Mata sune kawai ban tsana Suma sun Zama Dolene awajena daddy yau baffah ya kunyatani Wai Ni nabil nine baffah yasa aka dinga daukana agaban yarana da abokaina da wayannan mahaukatan yaran cancak kamar wani yaro anasawa amota ana ta rikeni Wai Kar na gudu Ni baffah yaiwa auran Dole dabaka ta da hankalinkaba baffah saboda Ni har abada bazanyi aureba Dan ko anyimin bani aka daura waba mommy da daddy ka daurawa aurannan ko Kuma kanka ka daurawa tin amazagai nakeso nai kuka ko naji Dadi azuciyata Amma nakasa Daddy zuciyata zata fashe in har aka barni da mace azaman matata faffah Zan hutar da Kai Zan saketa yanzu Ni nabal sani Zan
Kafin yakarasa iya tace wlh karma kafara baka Isa kamayar min da jika bazawaraba inaji Ina gani da ban yarda da auranba Amma yanzu na yarda da auran shatuwa da Kai Kuma wannan ikirarin da kayi na ka tsani du wata mace wlh kajawa kanka Zama daram Kai da shatuwa Dan Haka ka karya min jika bass kamar kasamu rake to karike wlh baka karya banzaba se nasa shatuwa tarama Kuma ko ban sataba nasan shatuwa Yar halakce Ni tagado zata rama Kuma wlh da Wasa ka tabamin jika se narama Mata itama Kuma kafin natafi Sena Mata nasiha akanka du abinda Kai Mata tarama Kar ta barka kana kiramin jika mahaukaciya kaifa me kala biyu Dan Allah jibeka ko gashin kanka abin kallone jibi wani wando Rabin duwawu du awaje ana ganin wandanka naciki jibi wasu uban sarkoki awuyanka sunfi kala biyar jibi yatsun hannunka zobunan da suke hannunka dubi shigar taka babu ta arziki da ubanka yake Kiran jikata Yar Kauye me kirar aljanu Kai kumafa me kirar me za a kiraka me kirar aljani ifiritu Zan kiraka ko dandaudu ko me tabin hankali da ubanka yake cewa jikata ba ta da ilimi indai irin ilimin kane wlh gara ta zauna Haka da Wanda na koya Mata jikata ba jahila bace Dan Ni Nan nice na ke koya Mata karatu har me kwanciyar tsakar daki du na koya Mata kai Kuma na dawo wajanka sani kake kowa wlh inkai Wasa Zan tsinkeka da Mari Dan Naga baka da mutunci tinda nashigo Naga kana harararmu kaganni Nan wlh shegen karfine da Ni bankiba daga Kai har Dan nake mu daku Dan jina ne ke dakaukau saboda karfi Kuma Nima nayi alkawarin senayi zaman Yan bori Akan kafar danka tinda ya karya min jika Kuma wlh ko yasaki jikata Bata sakuba Zama daram Dan Bazata koma mazagai ana kiranta da bazawara da kuke kiramin jika Yar Kauye kowa asalinsa Kauye Dan kwal ubanka daga Ina ubanka yake in ba da ga kauyenba anzo birni anyi kudin Alla ya Isa anci burudi da shayi da abin Yan gayu an manta da kauye usuman kajawa danka da jikanka kunne wlh Basu sanni bane labarina sukeji Zan gwada musu halina in suka kaini bango
Kafin baffah yai mgn MINISTER yace lanlai tsohuwar Nan daga ganinta Bata da mutunci Ni kike gayawa wannan mgnar lanlai in baaraba aura nabil da wannan yarinyar ba wlh kashemi Dana zakuyi ke da jikarki yanda kike San jikarki Haka Nima nake san Dana nabil Ni Kuma azamana na mahaifin nabil bangoyi auran nabil da jikarkiba Dole ya saketa Kuma Nima zanwa Dana nasiha in jikarki tamasa rashin kunya yarama Kar ya barta nama San Dana nabil shima Dan halakne ze Rama kakuma balballata Ni nasaka kaji nabil wlh wuya kadai se tasa jikarki ta gudu ji wani suna Wai shatuwa ko dadin ji Babu Dan Allah baffah karka Hana nabil sakin yarinyarnan wlh ke tsohuwa karki Kara kiran Dana Dan kwal uba nagaya Miki
Kafin kowa yayi mgn shatuwa tatakarkara takurma wani uban ihu se da nabil ya toshe kunnansa tace nashiga uku Ni yanzu ma nagane me ake nufi tin amazagai ban ganeba se yanzu har fadan da babarmu taimin Wai nabi mijina Ni du ban ganeba Ashe Wai aure akaimin iya kina Ina aka auramin wannan dandaudun Mata matamazan aka auramin iya Kika Bari haka tafaru Daman shi abbah ba Sona yakeba neman Kai yake Dani su megari ma Haka du basa Sona Wai ma Kuna nufin anan garin Zan zauna billahillazi ba Zan iyaba tinda muka shigo garin Banga gonakiba Kuma Ni bazan iya rayuwa Babu dawa da gonaki Babu kawayena Kai dandaudu wayacema Ina sanka Allah yakiyaye na auri rabi mutun rabi aljani yanda baka Sona Nima bana sanka yanda ka tsaneni Nima na tsaneka Kuma nadau alwashi se narama abinda kami wlh bazan taba hakuraba bakasan shatuwa jikar iya ikwan Allah ba
Nabil yace nashiga uku kaina zefashe Dan Allah baffah kakawo karshan rigimar Nan Dan Allah badan niba kaji tausayi na baffah karabani da mahaukayar Nan wlh na tsaneta ko ganinta banaso nayi karka min Haka Dan Allah baffah Kai mgn kayi shuru tin dazu
nabil yaje yarike wa baffah kafa
Baffah yace nabil wlh wlh wlh kaji na rantse har sau uku aure ya dauru Babu me Rabashi se Allah tinda shine komai yake hannunsa Amma wani Dan Adam wlh be Isa yaraba auranka da shatuwa ba Babu shi Kuma baayishiba Kai da ubanka kubude kunnanku kuji Ni Ni usuman mahaifin sani Kaka awajanka nabil in har ka kuskure ko da Wasa kasaki shatuwa wlh wlh wlh Sena tsinewa ubanka sani yabi duniya ya lalace Kuma bani bashi har abada kuma nacireshi acikin yarana gabadaya in kanasan ubanka kabar mgnar raba aure ko mgnar saki in Kuma bakasan ubanka gafili ga medoki ka saketa kaga aiki da cikawa Kai da ubanka me daurema gindi naji kana gigin ambatan saki wlh daga yanzu mgnar tafita bakinka gaba daya Kai da shatuwa mutu karaba Kai zaka binneta ko ita ta binneka kace katsani du wata mace ko to ga macenan ku zauna gida daya tare in kaso Dan Allah kamutu tana warkewa zaku bar gidannan Kai yanda kakeji da rashin mutunci hakama shatuwa takeji dshi ga tanan ku kashe junanku daga ita har Kai da kuke cewa ba kwasan juna aure dai ya dauru Babu batun rabuwa kuje Kai da ita ku koyi San junanku Kai sani shawara ta rage taka kace bakasan wannan auran ko to kaiwa danka fada yazauna da matarsa lfy ko kabi San danka ya saketa Ni Kuma mahaifinka na tsine maka
Gaba daya Kan MINISTER ya daure wani uban gumine yake ta ketomai ajiki du sanyin esin da ke falan Amma yajike da gumi se gogewa yake jiyayi gaba daya ya tsani shatuwa arayuwarshi da kakarta iya yanzu ya zeyi tinda har baffah Yana Kiran ze tsine Masa Akan wannan aljanar yarinyar Baki narawa yafara mgn yace Dan Allah baffah bekai hakaba Amma Ni da zakabi tatawa da kasa nabil yasa
Iya CE tataso tazo gaban MINISTER tace au baka sadudaba ko bakayi sanyiba du da dokar da ubanka yasa maka ko tu Bari kaga tinda kaki jin mgnar ubanka Ni Bari na fara wankeka da Mari tukunna
hannu tadaga zata mareshi kafin hannunta ya Kai fuskar MINISTER nabil yayi kukan kura yataso cikin fishi yarike hannun iya jikinshi se tsuma yake Dan masifa da bacin Rai da yake cin ransa yace ke tsohuwa ki nutsu kishiga taitayinki kafin na koya Miki hankali uban nawa Zaki Mara haba zance kike wlh Ina gani ki mararmin ubana Ina wajen Ashe ban haifuba ko da Wasa Kar ki Kuma gigin daga hannu da sunan mararmin uba kema inaga ban karyakin bane Dan Haka kikaki yin sanyi har kike cewa Zaki ramawa jikarki Nima se kin karyani ko ta Bari kiji somin tabi hannunta ya matse da karfi iya tasaki Kara Dan azaba Kuma ki jawa jikarki kunne tashiga hankalinta da Ni takuma iya bakinta in bahaba Zan canja Mata kamanni ke ko kunya bakijiba ubana na MINISTER kidaga hannu Zaki mareshi kin san waye shi a kasarnan Kinkuwa San me mukamin MINISTER na man fetir yake nufi koni DAN MINISTER kin Isa kisa hannu ki mareni bare ubana dada matsa hannun iya yayi takuwa da wata karar me karfi
Haba wa cikin fishi shatuwa tataso tararumi wata kwalbar fulawa da ke gefen TV zata kwadawa nabil tana jefuwa cikin zafin nama MINISTER yataso yatare Dan karya samu nabil seji akai kau agoshin MINISTER lokaci daya jini yaballe Yana zuba agishin sa ran nabil dada baci yayi jiyayi zuciyarshi zata fashe Daya hannunsa yasa yadafe kirjinsa jiyayi jiri na ibansa lokaci daya idansa yakada yayi jajir besan lokacin da yasaki hannun iyaba shima yafara neman abinda ze kwadawa shatuwa da besamuba idanshi yarufe yayi kan iya yabi ze daka azaman shatuwa ihu iya tafara tana neman dauki Dan nabil yayi Bali,in Bata tsoro dagudu Tai bayan kujerar da baffah yake azaune
tana cewa nashiga uku yau Naga ikwan Allah usuman Daman Haka jikanka yake ka hadashi aure da jikata ko dai shima Yana shaye shayennan na zamani da matasa keyi wannan wanna kalar aurene Kai nifa sirikarkace jikata kake aure usuman zefa lahantani kanaji kana gani in wannan zakin yai wasan kura Dani wlh ragargazani zeyi
Tsawa baffah ya dakawa nabil ya tsashi tsaye yace Kai karka yonan ko dawasa bare har kakuma tabata kaikuma sani kadan kagani ku bacemin dagani afalannan Kai da danka zamuyi Zama na musamman Ni da Kai sani kekuma shatuwa bakiga me kikaiwa sirikinkiba ko Baki San uban mijinki bane
Shatuwa tace Ni bashi nai niyar samuba wannan dandaudun nai niyar jifa shikuma yatare Masa na fasa Masa goshi ban saniba tsautsayine se hakuri Kai Kuma wlh Sena zubar maka da jini tukunna zakasan nice shatuwa
MINISTER hannun nabil yakama suka bar falan Yana tafe Yana masifa
Du wanna ruwan masifar da akeyi hajiya Fatima da Amina na wajan sun kasa mgn se Ido da dariya da mamaki
Baffah yace Amina jeki Basu wajan kwana Kan gobe bangaran nabil Zaki kaisu kimusu du abinda yadace ko abinci Basu ciba du kibasu suci in kin Gama dsu kizo nabaki Amana ke da mahaifiyarki kinji Yar albarka
Tace to baffah suka fice zuwa bangaran nabil
Hajiya Fatima tace baffah yau naci dariya Naga ikwan Allah
Baffah yace rabu da su Ina sane nahada aurannan insha Allahu shine silar shuryuwar nibil da sani Dan Allah kiga abin kunyar da sani da iya suka yi gaban yarannan memakwan suyi musu nasiha suhada kansu su zauna lfy Sema dada Bata abin sukayi kowa nawa nashi muguwar huduba Akan zaman auransu sani idansa yarufe San dansa yake du mgnar da tafito daga bakinshi fada yake Haka iya San jikarta itama yarufe Mata Ido du abinda yafito daga bakinta fada take Fatima ke da Amina ga amananan nabaku na shatuwa ku temaka ku gyarata ku wayar da ita asata amakaranta in tawaye itace zata gyara nabil Kuma itace zata cusawa nabil Santa azuciyarshi da San Du wata ya mace azuciyarshi takuma nuna Masa darajar mace da mutuncinta awajanshi da kansa ze sauka daga Kan akidarsa ta kin Mata yakuma so shatuwa ammafa se anyi Dan karamin yaki sosai agidan nabil Kuma fa se kunyi hakuri da halayan shatuwa Dan yarinyar bataji Kuma Bata da tsoro ko kadan Dan Haka na hadata da nabil zata iya da shi rashin tsorantane yasa na hadata da shi Dan Naga nabil na da wata baiwa kusan kowa tsoransa yake tin da Kika kirani awaya Kika fadamin halin da nabil ke ciki nake ta tinanin matar da Zan zaba Masa Kuma Sega wannan abin yafaru tsakanin sa da shatuwa da Kuma kalaman da naji yanayi Kan mace yasa na hada wannan auran Allah yasa kin fahinceni Fatima
Hajiya Fatima tace nagane baffah Kuma naji dadin hadinnan Allah yabamu ikwan rike amanar Yar mutane yanzu inda matsalar take awajan alhaji take Dan shima yadace yaba da gudun mawa wajan hada Kan shatuwa da nabil Amna se gashi shima bayasan auran saboda dansa bayaso kasanshi du abinda nabil keso shi yakeso in da nabil yace Yana Santa shima alhaji ze sota yagoyi bayan auran Amma yanzu tashin farko kaga me yafaru da idanka Ni nataba ganin wannan Bala,in ranar da aka kawo amarya akwashi wannan ruwan masifar haka memakwan ayi farin ciki se abin yakoma bacin Rai Allah ya kyauta
Baffah yace rabu da shi se gone zamu hadu da sani yanzu zanje na kwanta gobe in Allah ya kaimu zamu karasa yanda zaayi Dan gobe in komai yalafa zamu koma Ni da iya
Kai 馃ぃ馃ぃ Yan DAN MINISTER fans ku da kuke tashirin zuwa biki kunga yanda aka kwashe ranar da aka Kai amarya shatuwa to Ina Kuma ga ranar da ake Shan biki Ashe zakusha raban fada tsakanin iya da MINISTFR da shatuwa da Nabil馃ぃ se kunzo
su hasana lawan
da su maman munur
da su shafa Umar
da Aisha ummu Minal
da hajiya Rashida
maman Abdulhakim
Yar mulki
maman Haifa
Amina isima il
maman baby
ummu hasim
maman kairat zariya
maman yaseer
momin twins daweesu novel grp ayishat daweesu novel grp
Asha biki lfy nidai Ina daga gefe馃ぃ
Ngd sosai Yan DAN MINISTER fans grp da irin ruwan shirhin da kikaimin tin daga ranar da nafara DAN MINISTER zuwa yanzu
da sauran grp grp da sunayansu na manta godiya nake Allah yabar zumunci da du wayanda na manta sunansu Dan Allah kuyi hakuri ngd sosai Allah yabar so da kauna
Bana turawa ta PC Dan Allah kuyi hakuri
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama* 鉂ゐ煈�
*'YAR KWALLIYA* 馃コ馃拑
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹
馃憼
馃拕馃拝 *DAN MINISTER* 馃拝馃拕
馃馃
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
7-8
Adaran aka Kira Dr yazo yaduba MINISTER yaimasa dinki nabil ma se da Dr ya dubashi har da su allura Dan ya samu bacci
Iya kwana tayi tana ta ruwan masifa Akan abinda nabil da babansa sukai musu hadub kuwa ta yanda shatuwa zata zauna da su tashata wajan iya gajiya shatuwa tayi da sauraran iya har bacci yakwasheta sannan itama iyan tasamu waje ta kwanta
Washegari da safe bayan anhada abin karyawa Amina tace mommy yazaayi wajan cin abincin safe kinsan dai inhar gabadaya za ahadu aci har da su daddy da su iya to wlh ba abinci zamuciba raban fada zamuci Dan Haka meye abinyi Ni wlh baffah nafijin tausayi shine me Shari,a jiya fa se da na Kai Masa maganin ciwan Kai yasha bayan yaci abinci Allah yabani tausayi to yanzunma in har aka hadasu waje Daya to tarihi zekuma maimaita kansa Dan Naga daga iya har daddy Babu me gudun abin kunya Akan aurannan Dan basa ganin mutuncin juna kowa nashi yakeso baa Kuma mgnar ango da amarya wayannan Kuma se Dua,i jiya dazan kwanta nasha dariya sosai Ni mantawa ma nayi da har awaya Zan daukeso du ranan da suka shirya na nuna musu abin kunyar da sukayi ranar auran shatuwa da Nabil Ni tin Ina mamaki har abin yakoma bani dariya yanzu mommy me kikece Amma Dan Allah abar baffah yagama huta gajiyar jiya in kin yarda kowa akai masa abin karyawarsa har inda yake jiya har wasu daga Yan iakin gidannan sunsan meyafaru jiya har kunyarsu nadinga ji su da abin kunya mu da Jin kunya Allah yakyauta
Hajiya Fatima tace eh Haka zaayi Amina kisa akaiwa iya da shatuwa nasu alhaji da nabil mu hadu muci tare baffah shima akaimai nashi gwara da mijinki yabarki Kika kwana da abin yamin yawa ai wannan Kuma Babu maganar muje mu kama waje ayi Dinner Dan abin kunya zasu barmana Kuma ba damuwarsu bace Da ni yanda na tsara abokan nabil da na shatuwa da mu kanmu iyaye du zamu hadu mu tayasu murna Amma yanzu fitinarsu bazata bariba ayi abin arzikiba daga iya da alhaji har amarya da angwan Dan Haka mun hakura ahadu ahidimar haihuwa in Allah yashryasu suka haihu mayi shagalin suna Allah yabasu zaman lfy
Amina ta amsa da ameeeen
Amina ce da kanta Tai sallama takaiwa su iya abin Kari tare da rakiyar Yar aikin gidan
Amina tace iya antashi lfy yagajiyar jiya ya kwanan kanwar tamu shatuwa Babu mgn ko du gajiyarce tana dariya ta karasa mgnar
Iya tace lfyklau yarnan ainaga ke da matar gidan Kuna da mutunci bakamar ebanbuncanba wannann hajiyar itace ta haifi rabi mutun rabi aljani kema Kuma yayar sace
Amina tace eh iya wannan itace mahaifiyar mu uwa Daya uba Daya muke da nabil
Iya tace Amma albasa batai halin ruwaba ammafa hajiya na hakuri da ubanku da wannan Dan kwal uban yaran
Dariya Amina tayi tace iya tamu Kuma kakarmu amarya awajan mijin shatuwa to iya ke da angwan naki haka zakuyi zaman auran ko dai kishi kike Dan jiya ya auro shatuwa ya Miki kishiya
Iya tace Allah yakiyaye ajikoki wannan yazama jikana yaran da tashin farko ya karyamin jika jiya Nima yakusa karyani Allah ne ya kwaceni yaro da shegen karfi se kace me kashin mindiriki
Me Amina zatayi inba dariyaba tace iya tamu Bari na barku ku ci abinci anjima zandawo muyi hira
Ficewa Amina tayi tana dariya tana mamakin rikicin tsufa irin na iya
Lokacin da Amina takoma taje tatarar har nabil da MINISTER sunfito sun fara karyawa
mommy tace mu har munfara mungaji da jiranki
Amina tace Hira muka tsaya yi da kawar nabil iya
Nabil da MINISTER wani kallo su kaiwa Amina Babu shiri taja bakinta Tai shuru
Kowa yayi shuru ana ta cin abinci Babu zato Babu tsammani se muryar iya akaji tashigo tana masifa hannunta dauke da kulolin da Amina takai musu na abin Kari tare da rakiyar shatuwa
Salati hajiya Fatima tafara tace shikenan Allah yai dare gari yawaye za afara Kuma ko karyawa ba mu gamaba bare ya tsirgamana iya ke dawa me yafaru yihakuri ki fadamin
Iya tace Ina suke ebanbunnan wajansu nazo nasan da sa hannunsu sune zasusa aimana wannan abincin azaman abincin safe ke dai nasan babu ruwanki kina da kirki ba kamar wayancan Marasa mutuncin ba yauwa Ashe gasucan takarasa gaban alhaji sani da nabil ta ajje musu kololin abincin agabansu ta karbi na hannu shatuwa shima ta ajje musu ga tsiyarku Nan kuhada kuyi taci ku hankalinku kwance sekai Loma Baki kuke tayi mukuma inmunso mumutu Ni da jikata Dan mugunta kunsan Koko da kosai da dumaman tuwo da yartsala da Masa mukafi sani da safe shine zakusa adafo Mana wannan abincin masu jankunnuwan nasara akawo Mana Dan yunwa takashemu takalli nabil Kai mekiran zakuna hararar me kake Mana tin da muka shigo dakai da wannan uban naka me katan ciki
Hajiya Fatima rokar alhaji sani da nabil take da Ido karsu kulata suyi shuru Amma Ina abanza
zuciya ta ebi nabil hannu yasa yakaiwa dining table duka se da wasu daga cikin glass cup din dake Kai suka fado kasa suka fashe idansa yarine yakoma Jah saboda bacinrai Daman Kuma da haushin su yakwana aransa shima Kuma tinanin in sun hadu irin hukuncin da ze dauka akansu yakeyi se Kuma Allah yakawo su taruwan sanyi
Yace ke tsohuwa wlh ya isheki haka cinfuskar da kike Mana Ni da ubana ya Isa Haka daga haduwarmu da ke zuwa jiya da yau kin kirani da kalar sunan banza yakai nawa ubanama Baki bariba Dan bala,i Kai se yanzu nagodewa Allah da nadage yarena na hausa be bar bakinaba du da zaman da nayi a America Kuma Allah yasa inasan yarena kome kafada min da yarena na hausa Zan gane Ashe da kin cuceni kamar nasan da wannan ranar narike yarena na hausa hannu binbiyu akasar da batamuba ga jikarki itama Babu kalar da sunan banzan da Bata kirani da shiba ita da kawayanta har da min Waka haduwata da ku akwana Daya tazamemin fitina wlh ke tsohuwa inhar kikai Wasa Kika Kuma kirana da wani sunan daba nawa wlh Sena gurza Miki Baki se na karasa cire wayannan jajayen hakwaran na gaban bakinki da suka rage Daman inajin haushin jikarki ta fasawa ubana goshi har da dinki Kuma se nadau fansa ko akanki ko Akan jikarki
Shatuwa Tai caraf ta anshe mgnar tace au Ashe Babu Dadi Ni da ka karyawa hannufa ai kome yafaru Kaine kaja ba waniba da baka Fara tsokana taba da du Haka Bata faruba gashi Ina ji Ina gani kabarni da jinya ai ko jiyan Ni ba shi nai niyar jefaba Kai nai niyar fasawa goshi yai maza yatarema Kuma wlh har yanzu ban hakuraba se narama Kuma ga tsiyar abincin kunnan Kuma Dole aje asamo Mana Wanda muka iya ci agarinmu
Nabil yace au har yanzu bakuyi sanyiba ko Dan ban gama nunamuku irin
Kalata bako
Plet da glasscup din Kan dining table din nabil yasa hannu yafara jifansu dshi suna tsalle suna kaucewa iya du tacika wajan da ihu da masifa shatuwa da taga abin bana Kare bane itama kome tasamu jifan nabil take dshi har abincin da yake gabansu ta dauka tana jifan nabil da shi lokaci Daya suka Bata ko Ina na wajan MINISTFR mutuwar zaune yayi yakasa motsi Yana kallan ikwan Allah Amina ita gefe ta koma tana kallansu anrasa me Basu hakuri hajiya Fatima tana boye abayan labulan wajan in taji anyi ihu se ta leko kanta daga taga ana niyar jifanta satai maza ta komar da kanta nabil kofin gaban MINISTER ya dauka da ruwan shayi ciki me zafi Yana tiriri garin ya watsawa shatuwa se awuyan iya wata mahaukaciyar Kara iya tasaki Dan azaba lokaci Daya du tabi ta gigice Dan zafi ai batasan lokacin da tashige karkashin dining table ta buyaba tana mai da numfashin wahala lokaci Daya wuyan iya yatashi abinka da tsufa ruwan shayin ya Kona Mata fata sosai ta gefan wuyanta
shatuwa ganin ruwan shayin da nabil ya watsawa iya da Kuma yanda iya take ta ihu yakuma konawa shatuwa Rai batasan lokacin da Tai tsanle ta finciko karfen labulan wajan gaba daya ta rikitosu sukayi kasa se ga hajiya Fatima abayan labule tana raba Ido tana ijiran ikwan Allah shatuwa Kan nabil tayi dagudu da karfen labulan ahannuta in takai Masa duka dshi se yai tsalle ya kauce Babu zato Babu tsammani garin shatuwa ta kwadawa nabil karfen se a gadan bayan MINISTER zafin karfenne yadawo da shi daga mutuwar zaunen da yayi tin dazu Dan azaba besan lokacin da shima yashige idan iya ta buyaba sun hadu susu biyu suna jinyar in da kowa aka illata shi Dan azaba bayansa rikewa yayi Dakar ma yakai kansa in da yabuya iya da MINISTFR Baki yamutu Babu me mgn
sunbar nabil da shatuwa na fafatawa fadan yakoma na manya nabil shima samu yayi yadauki karfen labulan daya yakan shatuwa da shi dagudu Yana kokarin kwada mata bakajin komai se karar karfe awajan Dan karfin Hali na shatuwa da hannu daya take wannan rigimar Kuma dudahaka shatuwa bakinta yaki mutuwa inbanda bakaken mgn Babu abin da yake fitowa daga bakinta tana gayawa nabil shikuma Yana dada tinzira ransa nadada baci gabadaya sunhada wani uban gumi Kai ace wani uban aikin wahala aka basu su keyi
Amina da taga suna niyar jiwa junansu ciwo kuma Babu Wanda yake da niyar hakura ya dena Dakar da dabara tasamu tafita wajan baffah ta gayomasa abinda ke faruwa da sanyin safiyar Nan da sauri baffah yabiyo bayan Amina tinkan yakaraso yakejin muryar shatuwa da Kuma karar karafuna natashi shikuma muskili Nabil baajin muryarsa akwai wata kofa tabaya Amina tacewa baffah sushiga tanan Dan asamu arike Daya daga ciki suna shiga Allah yabawa Amina sa,a tarike shatuwa tabaya shikuma baffah yasamu yarike nabil tabaya
Tsawa baffah yadaka musu ya wankawa nabil Mari yace kunutsu kushiga hankalinku meyake damunku haka ko kunsamu tabin hankaline bamu saniba daga jiya zuwa yau Kai nabil meyasa kake biyewa mace Kuma matarka Dan Allah jibi yanda dukanku kuke maida numfashi kamar wayanda sukayi aikin wahala Dan Allah kukalli barnar da kukayi awajannan gaba daya kun lalata komai nawajan har falo Baku bariba abincinma gabadaya kun zubar dshi saboda Bala,inku Ina sani da iya da fatima suke suka barku Kuna wannan danyan aikin
Hajiya Fatima ce tasamu tafito daga wajan buyar da tacanja tace baffah du munanan abinne yafi karfinmu in muka tsaya ciwo zasuji Mana abanza abarmu da jinya ai yanda suka haukace dinnan ran kowa yake abace acikinsu Babu me iya raba fadannan Daman se Kai baffah Suma masu daure musu gindin sunyi takansu sun kasa rabawa baremu Yan kallo baffah Ni banma San Ina suka buyaba tinda naji ihun iya dazu ban Kara jiba inaga sunsamu sunfice suna waje abin yafi karfinsu
Muyar iya sukaji ta karkashin daining table tana fitowa da rarrafe tace kun ganmu Nan Ni da Mara mutuncinnan muna jinyar jikinmu konani da ruwan zafi mekirar zakunannan rabi mutun rabi aljani yayi daban gudu na buyaba da salibeni zeyi kamar kaza aruwan zafi gabadaya ko ya aikani lahira Babu shiri mutun amurmurde kamar samudawan farko fuska amurtuke sekace me gadin gidan wuta idanshi Dan mugunta har wani Jah da Kore suke komawa Dan masifa usuman kahada shatuwa da Bala,i rashin sani yasa na yarda ankawo jikata inda zaa kasheta nashiga uku Ni Aisha anfasa aurena billahillazi usuman kadau mataki Dan bazan yarda inaji Ina gani acutarmin da jikaba Dan Allah kaga yanda gabadaya Rabin wuyana yasale da ruwan zafin da wancan damisan yawatso min ko tsufana beganiba Dan rashin imani har da cewa ze karasa ciremin hakwaran bakina nagaba da suka rege Kuma wlh ze iya fin hakama Dan Babu tausayi da digwan imani azuciyarshi zantafi da jikata in komai yalafa sunyi hankali shi da ubansa na dawo da ita wlh inaji Ina gani bazan bar jikata akashemin itaba
MINISTER ne yafito shima Yana rike baya yace Ni bance inaji Ina gani jikarki zata kashemin yaroba Nima ta gurguntani se ke baffah kagani da idanka tin da aka kawo fitinanniyar yarinyarnan take hakona jiya kaga me tai min yauma gashi ta barni da ciwan baya Dan Allah Dan annabi baffah ka temaka kacire dokar da kasa Mana Ni da nabil ya sauwake Mata sukama gabansu su koma in da suka fito har in da muke Dan masifa muna karyawa tsohuwar Nan tazo ta samemu tahau Mana masifa Wai su tuwo da Koko da kosai suka sani Dan kauyanci tin ajiya nabil yakuma fadamin bayasan yarinyarnan ko ganinta bayaso yayi ya tsaneta karfa murasa nabil baffah kadau mataki Dan Allah
Baffah yace du kanku kunemi waje ku zauna zamuyi mgn da ku kowa Zama yayi baffah yakalli nabil Kai nabil dakai Zan Fara Dan Kaine yanzu komai yake hannunka na shatuwa zaman nan dan kai da shatuwa akeyinshi yanzu Dan Allah azamanka na mijinta abinda ka kulata kukeyi yadace kaifa yanzu girma ya kamaka ko kana so ko baka so Dole kana hakuri Akan wani abin in matarka tamaka karfa kamanta ko Babu aure sama kake da ita ka girmeta bare Kuma yanzu da take akarkashin ikwanka Dan Allah ba girmanka bane karka Kara kulata ku Kara raba abin fada haka gaban mutane da safiyar Allah yanzu girmannan da kake da shi agaban yaranka da yan aikin gidannan yanzu du kazubar dshi a idansu dakai da ubanka dalilin wanna abin kunyar da kukayi jiya da yau kaga kuwa yanda maaikatan gidannan suka taru awaje suna sauraran abin kunyar da kukeyi Kuma saboda suna tsoro ko rabawa Babu Wanda yashigo yayi kabi zabin da nai maka nabil insha Allahu zakaga alheri komai daran dadewa kaji jikana nimafa ina sanka Ina kaunarka kamar yanda sani yake sanka San da nake makane yasa na zabama matar aure da kaina Dan Allah kana hakuri da ita karka Kuma kulata Kaine babba itama Zan Mata fada se mgnar iya kakar shatuwa cefa matarka itace Kuma ta raini matarka tin tana cikin tsumma har zuwa yanzu kaga kuwa dolene ka girmamata karka Kara kulata kome tai maka kaima kakace awajanka yanzu kaga ka kona Mata wuya saboda zafin Rai irin naka Dan Allah karage zafin Rai bashi da anfani arayuwa kaji nabil Allah yai maka albarka
Kekuma shatuwa nabil mijine awajanki dolene ki bashi girma Kuma kibishi sau da kafa aure yafi karfin Wasa Babu raini tsakanin miji da Mata daga yau se yau karna karajin wani abin yafaru na fada tsakaninku Dan Allah kuji tsoran Allah ku zauna lfy kiwa mijinki biyaiya aljannarki tana karkashin kafarsa se yadaga Zaki shiga karki Kara dagawa mijinki ko da muryane bare har takai ga niyar zaku illata juna da makami yanzu kema kin girma bakamar da bane da Baki da aure tinda kike kin taba ganin babarki suwaiba da umaru suna irin abinda kukeyi daga jiya zuwa yau ko Kai nabil tin da kake kataba ganin Fatima da sani suna fada to karna karaji kun yi ku zauna lfy ku Zama abin alfahari adangi da duniya gaba daya kodan yaran da zaku Haifa gaba inma mafarki like ki farka aure dai anriga an daura Babu rabuwa mutu karaba ke da shi inma zaku koyi San junanku to ku ku koya Dole muma wasu daga cikinmu dahaka muka so namu matan shatuwa dolene ki girmama iyayan nabil wannanfa da kike gani Kika fasawa Kai jiya yau Kuma Kika kwadamai karfe abaya uban mijinkinefa karki kuma gida dayafa zakuyi rayuwa kuke haka karna karajin bakin wani daga cikinku ku tashi ku tafi nagama daku Allah yaimuku albarka Allah yabaku zaman lfy yakade fitina Amina maida shatuwa dakinta
Kafin su tafi iya ta kalli nabil tace me mugun Hali kadaiji me Wanda ya haifi ubanka yace saura kaki ji Dan Allah jibi yanda yake ta huci kamar wani mayunwacin Zaki Tai maza ta toshe bakinta au yacefa in na Kara kiranshi da wani suna ze ciremin hakwaran gaba da suka rege na bakina Wai jiya wanama suna naji kakira ubanka dshi ko miss miss kome Kai Kuma naji kace Wai kana Dan miss miss ko me usuman Daman gwaunati mukamin da tabawa danka kenan mukamin Kiran maguna miss miss Kuma naji yakira fetir Daman du uban kudinnan da yatara da mukamin kiran miss miss ya tarasu Ashe magunama na da daraja akasar Nan ban saniba dakai na kirkine sani ai da inna komawa mazagai da nasa na tarama maguna dayawa in zan dawo ganin shatuwa na tahoma da su to baka da mutunci daga Kai har danka me shigar Mata
Me hajiya Fatima da Amina zasuyi inba dariyaba hajiya Fatima tace nabil tafi daki ka kwanta kaji ka huta rabu da iya Wasa take muku kema shatuwa jeki kwanta ki huta Kan akawo Miki abinda kike din
Bayan su nabil sun fita
Baffah yace iya na dawo gareki Dan Allah Dan annabi karki Kuma kula nabil kome yai Miki jikankine shi Kuma sirikinkine ki Dena kula sani kome yai Miki kizo ki fa da min shatuwa Kuma namiki alkawari nabil Babu abinda ze Mata ga Fatima za tana kula da shatuwa da Nabil yanzu anjima Ni da ke zamu koma mazagai Kayan dakin shatuwa anyafe du za ai Mata anan ki kwantar da hankalinki Kuma in an kwana biyu akai akai zamuna zuwa Ni da ke muna ganin yaran muga Kuma ya suke Zama kije dakin shatuwa ki shirya anji zamu tafi Allah ya kiyaye gaba
Iya tace habawa ai in ban ciba Babu wani bayani bana Kuma Jin ko wace mgn Ni fa afah bani abinda nafi wayo naci bazan iya cin Kayan da mugayannan suke ciba akawo min Koko da kosai ko tuwo ko Yar tsala da kunun tsamiya
Baffah yace karki da mu du NASA ai Miki kije zaa kawo Miki
Tace to yanzu naji zance shimafa wannan kaja Masa kunne Dan Naga har yanzu wani gani gani yake min Kuma Ni da naso mu Dan Kara kwanaki Dan wlh bazan iya rabuwa da shatuwa ba Kuma wlh Babu inda zani Ina nan Kuma ai nazata nice Zan Mata zaman daki
Tatashi ta fice tana sababi
Baffah yace sani kaban kunya wlh kabani mamaki sani da iliminka da hankalinka kake kula tsohuwar Nan Kuna Raba abin kunya gaban yaranku Kai sani bakaji kunyaba ko mukamin da kake dash na MINISTER baka dubi girmanshiba saboda San danka yarufema Ido ka daka ta tsohuwar nan kuka dinga Raba abin kunya gaban su nabil ita ai yadace Kai Mata uziri akwai tsufa na damunta da rashin ilimin Kai kumafa wlh kaiwa kanka fada kayi kokari ka hada Kan yarannan su zauna lfy Kar na karajin makamancin haka yasake faruwa
Yace to baffah kayi hakuri Amma gaskiya inajin tausayin nabil wlh
Baffah yace au du abinda nake fada be shigi kunnan kana ko
Katashi ka tafi kaima da mgnar da zamuyi da fatima
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama* 鉂ゐ煈� *'YAR KWALLIYA* 馃コ馃拑
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹馃憹馃憹
馃憼馃憼馃憼
馃憹馃憹
馃憼
馃拕馃拝 *DAN MINISTER* 馃拝馃拕
馃馃
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
9-10
MINISTER yace baffah kayi hakuri wlh tsohuwar ce bata da mutunci Dan Haka nake ajje komai agefe nake kulata yanzufa kaji me tace Wai MINISTER take Kira da Miss miss Wai mukamin Miss Miss aka bani Dan Allah Kar ta Kara kwanar Mana agida ta koma inda ta fito har jikar tata
Baffah yace Ni dai azamana na mahaifinka ka dena shiga harkar yarannan kayi kokarin hada kansu ba Wai kana hura wutaba Kana nuna bakaso tin daga jiya Allah yafara nuna maka ishara Akan auransu tashin farko anfasa maka goshi yau baya gaba in ka kuma shiga har karsu bakasan me ze faruba karabu da iya Kar ka daka ta halinta kaso shatuwa kamar yanda kake san nabil gaba bakasan wana alheri zata za me mukaba azuriarka gaba zakaji kunyar abinda ka aikata infa kaji nasihata in Kuma bakajiba to Allah yaba da sa,a tashi ka tafi
Bayan minister yafita
Baffah yace Fatima Allah yaimiki albarka Allah yabaki hakurin Kula da yarannan nasan daga ke har Amina Baku da matsala yanzu Dan Allah kiga me yarannan sukayi yau kowa acikinsu Yana Ji da danyan Kai ita rikwan Kaka uwa ba kwaba shikuma rikwan namiji uba bakwaba ga nabil da shegiyar zuciya da zafin Rai ga shatuwa da tsokana da taurin Kai shi ma Kuma nabil din akwai taurin Kai in Abu yafi karfinki atsakanunsu kina kirana ki sanar da Ni zan zo Dan sani ba ze musu fada na tsakani da Allah ba se yasa San zuciya aciki nashi ze so ita Kuma iya dole yau na jata mubar gidannan yakin badar din da akayima jiya da yau ya isa haka ai in har akabar iya agidannan bazamu iya gyara ko maiba yanzu kije kisa akai mata abinda takeso taci se mu tafi du abinda yashige Miki duhu Akan abinda na fada miki kiki rani kijin Allah yabamu sa,a Akan niyarmu ta alheri Kan yarannan
Tace ameeen baffah Ni yanzu damuwata yanda nabil da shatuwa zasu na kwana waje Daya wlh abinda kamar wuya Dan bakaga rigimar da mukayi dshi Akan su iya sun kwanar Masa adaki cewa yayi yabar bangaransa gaba Daya Kuma baya San komai na wajan shi sabo ze canja se da nacimai mutunci sannan yahakura Kuma kasan alhaji bayansa ze goya
Shawara baffah yai tabawa hajiya Fatima sannan yadada samun minister yadada jamasa kunne sosai Amina itama yafada Mata gudunmawar da yakeso tayi atsakanin nabil da shatuwa
Iya ankai ruwa Rana da ita sosai Kan ta yarda ta koma mazagai ta rabu da shatuwa bakara min kuka iya tashaba na rabuwa da jikarta har tausayi tabawa su baffah ana haka nabil yashigo falan yasamu iya tana kuka Baki yatabe yaja tsaki kawai se gani sukayi iya tatashi tsaye tabi ta bayan nabil babu zato babu sammani Dan Babu Wanda yakawo me zatayi tatakarkara ta dimawa nabil dundu a gadan baya se da yagantsare Dan abin yashige shi beyi zatoba se saukar hannunta yaji
Iya tace Dan kwal uba ai ga Wanda du yaja komai Nan yarabani da jikata muna zaman zaman mu Kuma Zan tafi saura ka Kuma karyamin ita Kuma har yanzu ban huceba se nayi zaman Yan bori akanka ko yaushene me zubin karfafa me shigar Mata dandudu kawai yau Kuma irin shigar da akayi kenan kuma ubanka nagani yaki ya hanaka Dan miss miss din uwa kawai takalli hajiya Fatima yarnan bakiya Saar Daba da mijiba du Basu da mutunci ke Kuma gaki saliha me kirki Amma auran Dole aikai Miki da uban Dan daudun Nan ko Dan Baku dace da junaba
wani irin juyowa nabil yayi cikin zafin nama da bacin Rai yadaga hannu ze damkota iya baffah yai maza yashiga tsakani
Yace haba nabil Kai ta hakuri kaji yau fa zata tafi shikenan Kuma in tatafi se Allah yasake hadaku Kar ka kulata yanzunma tsautsayine Bata saniba Tai maka
Baffah mgn yaiwa minister da Ido kar ya kula iya Dan yaga ranshi yabaci da abinda iya taiwa nabil
Nabil fita yayi daga gidan ko tafiyar baffah da iya be tsaya yagani ba cikin bacin Rai Yana ta huci zuciyarshi na Masa zafi ga baffah yahana shi yai maganin iya
Hamdalah hajiya Fatima tayi azuciyarta da nabil yafice gaba Daya daga gidan ahankali tace alhamdulillah gwara da ka tafi Dan Naga itama shatuwa kadan take jira Kai mgn ta kulaka ga alhaji shima ransa abace yake iya ta taba Dan gwal dinsa
Shatuwa Bata tashi yin kukaba se da taga da gaske zasu rabu da iya hankalinta yatashi Tai ta kuka rikicewa tayi se sun koma tare Dakar akasamu aka rabasu iyama kukan tafara Haka motar taja tafice daga gidan iya se waige take baffah yasha mitar iya Kan su je mazagai shidai ba da hakurine nashi har Allah yasauke su lfy
Nabil da yafita wajan da yake shakatawa yatafi yasamu abokansa acan suna ganinshi sukayo kanshi suna murnar ganinshi da murnar zasu hule tinda ga me kashe musu kudi yazo abokan nasa nasan suyi Masa maganar amaryarshi Amma kowa najin tsoro Kuma sunga yanayinsa Yana cikin bacinrai haka kowa ya hakura yaja bakinsa yai shuru
Da hannu yakira wani daga cikin abokan nasa yazo yabashi damin kudi yace gashinan kowa kabashi yai abinda yakeso in Basu isaba azo akarbi wasu
Yace to mutumina Dan Haka nake sanka kake burgeni baka halin karanta guri in bakai sunansa lami Ni da dashawarar da nakeso nabaka in zaka Dan bani lokaci yau Naga kamar kana cikin bacin Rai kaima kahau layi karabu da bacin Rai kadan Sha abinda muke Sha ko kadanne yau ka gwada lokaci Daya in kasha zakaji kafin yakarasa
Nabil ya daga Masa hannu cikin bacin Rai yace bani da raayin Shane tintini da inaso kaima kasan ko ana siyarwa nera nawa Ina da kudin siya Ni kwata kwata shaye shaye baya burgeni Kuma baya cikin tsarin rayuwata
Yace to ko finah ce yau Daya gatacan na kirama ita kuje ku huta da ita tinda kaga yarinyar na mutuwar sanka
Nabil yace tinkan nai maka rashin mutunci Kai maza ka bace daga wajannan Ni kake hadawa da mace ka kwasan wana Hali Mata suka jefani Kuma shine zaka zo kana bani wannan muguwar shaawar akan mace Kai maza kabace a idona
Jiki nabari yabar wajan
Finah na gefe du abinda yafaru tsakaninsu akunnanta da I danta ga taji labarin auran da yayi kishine ya rufeta afili tace in dai Ina raye nabil se kazama nawa se mun koma Abu Daya da Kai muzuba mu gani Ni da kai
Shatuwa ce kwance Kan makeken gadan nabil tana ta kuka idanta ya kunbura sosai sabo da kuka
Amina ce Tai sallama ta shiga tace kanwata har yanzu kukan kike tayi Baki hakuraba nanmafa gidane Babu abinda ze sameki kinji Kuma bawani dadewa zakiyiba za a Mai da ki wajan iya Kuma naji baffah na cewa da iya zata dawo Nan gidan gaba Daya da Zama saboda ke
Murna shatuwa ta fara tace dagaske kike
Kai Amina ta daga Mata
Nan Amina tasamu tafara janta dahira har tasaki jikinta Nan tasamu ta fara yi Mata tambaya Akan karatu
Shatuwa tace nifa Babu wata makaranta da nake zuwa iyace makarantata itace me koya min karatu Kuma iya tahana asani ako wace makaranta Dan bataso adakeni Nima Kuma banasan karatun Bari na biya Miki abinda iya ke koyar Dani kiji
Kema Kya karamin daga in da na tsaya
Biya Mata tafara ai ko nisa batayi da shirmen karatun taba Amina ta tsaidata tace ya Isa Haka shatuwa kinaso kema ki zama Yar birni Kuma Yar gayu kamar Yan matan garinnan ko da yake ban kaiki yawo Kinga yanmatan garinnan ba da sun birgeki sosai to kalarsu nake so ki Zama Zan sa akawo Miki me akoya Miki karatu daga na boko har na isilamiya Nima Kuma in nazo Zan na koya Miki Amma yanzu ki ajje karatun iya da ta koya Miki agefe har ki iya Wanda zaa na koya Miki kinji kanwata
Tace to ke ya zan na kiranki dashi
Tace anty Amina su nana yanzu abinda nakeso da ke wanka nake so muje na hada Miki ruwan da kaina kiyi muga kitsan kanki
Shatuwa na bude gashin kanta
Mamaki Amina ta fara yarinya me gashi Amma saboda rikwan iya ce ita kitsan kanta ya dankare ko tsagar kitsan baagani gawata uwar kasa akanta
Amina tinani tafara azuciyarta tafara mgn tace gaskiya da matsala yanzu Kai nasa ta budemin nagani to Kuma sauran wajanfa ga yarinya kyakkyawa Amma rashin kula yasa kyanta yabuya da zata yarda in na tsefe Mata Kai wlh dada kaina Zan Mata wanka yau dai Daya nayi Mata du abinda yadace na Kuma nuna Mata yanda zatana yi gaba yanzu yanda Zan Mata ta yardar ne matsalar
Zama Amina tasa shatuwa tayi ta tsefe Mata Kai tashiga bandaki tahada Mata ruwan wanka shima se da takirata tahada komai agabanta takuma nuna Mata du abinda yadace saboda gaba in zatayi tace yau komai Ni Zan Miki da kaina gashin kanki Zan Fara wanke Miki daga baya maje gidan gyaran gashi agyara Miki shi nifa yau ni zan miki wanka da kaina kinji
Shatuwa kitayi tadai yarda ta wanke Mata gashin Kanta lfy se da akazo wanka da gyaran jiki da du inda yadace aga Babu gashi da kazanta jikin mace shatuwa Taki yarda Dakar da rarrashi ta yarda Amina Tai Mata du abinda yadace ta Kuma nuna Mata kalar du wani Kayan da mace in tatashi wanka zata na anfani da shi da Kuma to du inda yadace aikuwa Amina bakaramin wankar shatuwa tayiba ta wanketa tas sannan ta barta Shatuwa se runrufe kirji ake abinma dariya yabawa Amina ganin ita kirjin tafi damuwa dshi
Suna fitowa shatuwa tasa hannu tarufe Ido tasa dariya tace wlh kunyarki nake ji anty Amina Kuma fa naji Dadi ako Ina na jikina sakayau nake jina ga wata iska me Dadi nashiga jikina nifa amazagai bana wani wanka sosai Kuma iya bata min fada Kuma fa Ni banasan kitso wlh
Amina tace ai Dole kice bakyasan kitso Daman ku Masu gashi bakwaso ataba muku Kai du wannan me saukine akwai inda Zan na kaiki ana wanke Miki gashi agyara Miki akai akai Kinga Babu mgnar yin kitso se haka in kina so wataran se ana miki Kuma mu anan wanka kullin akeyinsa safe da yamma da yammanma anfiso in Zaki kwanta kiyi inma sansamune Ni kullin sau uku nake so kinayi kinji kanwata zakifi Kyau da kanshi har maganar wanke Baki shima du yanda nakoya Miki da yanda nagaya Miki zakinayi kullin haka nake so kinayi Kinga yanzu kin Fara Zama Yar gayu Kuma Yar birni yanzu Kinga du yanda na koya Miki yanda Zaki shafa wayannan Haka zakiyi Banda kwalliya me yawa kinji kishirya inkin Gama kizo bangaran su mommy muyi Hira Kan natafi gida Kuma ko natafi akwai mommy zata nuna Miki du abinda Baki saniba Nima Kuma zanna zuwa wajanki akai akai muna gaisawa natafi Ina jiranki
Shatuwa Zama tayi tashafa du abinda Amina ta nuna Mata kamar abin arziki bayan tagama tadau jambaki da Hoda da jagira tazuba wata kwalliyar hauka itanan tafara Zama Yargayu kayan da Amina ta kawo Mata tace tasa su tasa wasu riga da siket ne na atamfa sunyi Mata Kyau sosai sun karbi jikinta abinda yabata kwalliyar fuskarta tsayawa tayi gaban mudubi tajuya takuma juyawa wani Dadi yakamata
tace Yasin du Wanda yaganni yau seya hargitse saboda mugun kyan da nayi
Amina tana shiga falan tasamu Hajiya Fatima azaune
Hajiya Fatima tace Amina ansamu ta hakuran ko har yanzu kukan take Allah yasa kinfara naki aikin
Amina tace eh ta hakura Kuma nafara aikina mommy ammafa akwai matsala sosai wlh yarinya kyakkawa Amma iya ta cuceta tabarta ba ilimi tana zaune cikin jahilci in kinji yanda mukayi da ita wlh se takaici yakamaki in yarinyarnan tagyaru wlh yarinya kyakkawa zaayi Kuma nabil seya rude Akan Santa se yasota sosai wlh Allah dai yabamu saa
Suna cikin hirarsu nabil yashigo ko sallama Babu bare gaisuwa yanemi waje ya zauna Yana kallan kofar shigowa yawani hade Rai kamar bega mutane awajanba
Hajiya Fatima tace Allah yakyauta Allah yashiryeka nabil Dan Allah yaushene zakayi hankali yaushene zaka Fara jin fadan da nake maka Akan sallama da gaisuwa yanzu kashigo Mana ko sallama Babu bare Musa ran gaisuwa Kuma me yakawoka wajena ko kamanta kana da Mata kamanta yamukayi da Kai jiyako tin wuri katashi katafi wajan matarka tinkan nakira baffah na gayamasa me kake niyar yi
Nabil yace haba mommy meyasa baka Sona yaushene Zaki Fara Sona kamar yanda sauran iyaye Mata suke San yaransu Dan Allah yaushene Zan samu kauna da kulawa awajanki yaushene mommy yanzu Dan Allah kin goyi bayana auran kandarar da akayimin na mara hankalin yarinyarnan da ita da kakarta Mara mutunci na tsaneta na tsaneta bazan kwana gu Daya da itaba
Hajiya Fatima tace nabil nikuwa nake sanka Kuma nake kaunarka Ni nake so kagama da duniya lfy nabil Babu uwar da zata haifi da a cikinta tace bata sanshi nabil kowace uwa burinta taga Dan da ta Haifa Yana hanya madaidaiciya hanyar da zata kaishi aljana Amma nabil kaki ganewa nabil kullin inamaka addu'ar shiriya Allah yashryeka Allah yaganar min dakai gaskiya kasan irin San da nake maka Kuma insha Allahu nasan Allah natare Dani Kuma ze cikamin burina ya amshi addu'a ta akanka har yanzu inasa ran zaka Zama yanda nake so na ganka insha Allahu nasan Kuma lokacin zakasan gaskiya nake fadamaka
Fitowa tayi zuwa bangaran Hajiya Fatima tana wata irin tafiya abin dariya ita adole tazama Yargayu du Dan aikin da yaganta na gidan tazo shigewa ta gabansa seyayi dariya aboye
wani daga cikin Yan aikin yace Allah kenan abinda kake wulakantawa arayuwa nabil Daman wataran se kunyi rayuwa tare Kai da kake wulakanta mutane musamman Mata gashi yanzu abin dariya kuga wanta ya aura azaman matarsa ai wannan tsohon arzikin yaburge Ni wlh
Dariya sauran sukayi Daya daga cikinsu yace ku dai yi ahankali Dan wlh kunsan Yana ciki bedade da shigowa ba Kuma kowa yaga yanda yake tafiya yasan ransa abace yake Babu ruwana
Hajiya Fatima na Kan yiwa nabil nasiha Sega shatuwa itama tashigo tana wata tafiya tana karkada idanu itama tashigo Babu sallama tanemi waje ta zauna irin zaman da nabil taga yayi yadora Daya Kan Daya itama shi tayi tana ta hura hanci ita ala Dole tahade Babu Wasa daga Hajiya Fatima har Amina kallan shatuwa suka koma yi
Hajiya Fatima tace ohh Ni Fatima du gautan jahne daga mijin har matar lanlai akwai aiki
Nabil Kare Mata kallo yayi besan lokacin da dariya ta kwasheshi yace tofa abin nayine Dan Kauye yashigo birni ba lfy se ya warke Dan Allah kiga wata kalar kwalliyar mahaukata Wai kenan gayu kikayi anan kenan gani kike Wai ke macace ko ahakan Allah yakyauta gaskiya baffah ka cuceni ka gama da Ni Wai arasa Wanda Zan aura azaman matar aure se wannan akuyanlen kuga wani kwalliya kamar anyiwi akuya kwalliya wlh bazan taba Sankiba kome Kika Zama aduniya na tsaneki bana san ganinki adalilinki da wannan tsohuwar na dada tsanar Mata aduniya
Tashi tsaye shatuwa tayi tadaka tsalle taje gaban nabil ta tsaya ta rike kugu tace Nima kamar yanda kake fada ka tsaneni Nima Haka na tsaneka ko ganinka bana san yi da idona kafara yiwa kanka dariya kafin kafara yiwa wani kaifa me shigar Kayan Mata dandaudu matamaza rabi mace rabi namiji adalilinka na rabu da iya me kaunata karabani da ita Ina ji Ina gani ta Ina Zan soka har naso Zama da Kai yasin baka isaba Kar Kuma ka kaini bango Dan wlh akwai abinda na dauko tin daga mazagai saboda Kai Dan na koyamaka hankali karka Bari nafara ma anfani dshi Dan yanda kabarni da jiyar hannunna kaima se na wahalar da Kai kaji jiki kamar yanda Nima naji wannan alkawari nane Ni bana yafiya Kuma bana manta ranar daukan fansa ga du Wanda ya tabani Dan Haka kabi ahankali kashiga hankalinka
Nabil tashi yayi yadauke shatuwa da wani gigitancan Mari me zafi yakuma dauketa da wani lokaci Daya tafara ganin duhu hannu yasa ze Kama hannunta me karaya dasauri hajiya Fatima Tai maza tarike Mai hannu se wani huci yake Dan bacin Rai
Yace mommy Dan Allah kibarni na karasa ragargaza hannun Naga me zatayi ita da kakarta kinafa ji mommy irin kalaman da take fadamin baa Mai damin da mgn baa Kuma yimin rashin kunya baa nunani da yatsa ban karyawa mutun hannuba Dan Haka kiki,yaye ko Dan gaba ki fita harkata har murabu Danni bazan iya Zama dakeba rikwan tsohuwa kazama kawai yau zanga yanda Zaki zo kice za mu kwana daki Daya wlh da yau sekinyi Dana sani arayuwarki
Shatuwa neman abin ramawa tafara yi da sauri Amina tazo takama hannuta tajata dakar suka bar falan Dan taurin Kai irin na shatuwa ko alamar hawaye Babu a idanta burinta kawai itama ta rama abinda yai mata jitayi takara tsanar nabil azuciyarta takuma dau alkawarin se ta dau fansa itama se tabashi wahala
Amina bangaran nabil tamai da shatuwa ta zaunar da ita itama Zama tayi kusa da ita tace haba shatuwa yakike,yin Haka bakiji fadan da baffah yai mikiba ko in har bakya,bin abinda baffah da mommy zasu fada miki Zan Dena kulaki Nima tinda nasan Nima bazakiji nawaba yanzu Dan Allah wace irin kwalliyace wannan afuskarki karki Kuma mu anan ba a irin wannan kwalliyar in kayi mahaukaciya za a dauki mace Zan koya Miki irin kwalliyar da Zaki nayi afuskarki Kar na karaji kin kula nabil Kuma kome zemiki Kar ki kulashi mijin,kine
Shatuwa tace to aini tin Ina yarinya baamin Abu ban ramaba in ban ramaba har bacci kasawa nake Kuma Iya tace karnabi fadan da baffah yai min Dan shima dandaudun baji zeyiba Kuma Ni iya itama tamin fada irin nata Kuma Ni Dole nabi fadan da iyata Tai min Kuma nata fadan yafi tinda cewa tayi du abinda yaimin narama Kar na raga mishi tace bashi da mutunci Kuma Ni gaskiya bazan iya kin bin mgnar iya ba kowadai acikinku zanji nashi in yamin Kuma Zan na aiki da kowanne kiyi hakuri Ina sanki karki Dena zuwa wajena Dan Allah
Shuru Amina tayi se da tagama tinani sannan tace naji shatuwa Allah yashiryeku se mgnar kirki kin iyako
Baki tawashe tace eh na iya sosai makuwa
Tace to zaayo Miki siyaiyar du abinda yadace na Kayan abinci in kin warke in Zaki koma saban gidanku ke da nabil se kifara girki yanzu anan mommy ce zatana sawa ana kawo Miki har kiwarke yanzu kije ki wanke fuskarnan Taki kiyi alwala kiyi sallah naji ankira Nima Bari naje nayi
Nabil dakin alhaji sani yashiga yaje yakwanta Dan shi abin ya zamemishi kamar Al,Ada in aka batamishi Rai dakin mahaifinshi yake zuwa ya kwanta ko yashiga yazauna har yahuce Zama yayi Kan kujerar da ke dakin se furzar da numfashi yake afili yace senayi maganinki yarinya yanda in kin ganni ko gaba zakina guduwa
Minister ne yashigo dakin Yana ganin nabil yasan ranshi abace yake dasauri yakarasa wajansa yace Kai dawa nabil badan tin abinda baffah yai maka bane kake fishi baka huceba nacema ai Zan rarrashi baffah yahakura ka saketa har mazagai zanje na rokeshi jira nake akwana biyu tukunna Nima kaina wlh basan yarinyar nakeba gakuma wannan maramuncin tsohuwar Nan tata ai Dole murabu da mugun iri nidai nafadama kaganawa yarinyar azaba karka taba raga Mata da kanta zataje tasamu baffah tace yasa ka saketa kome Tai maka karka barta kai Mata abinda yafi Wanda tai maka kaji ni nasaka
Nabil yace ai du abinda kace,min nayi du senayi daddy har dama Kari yanzu yanzu kaga me ta min mommy ce ta hanani hukuntata da se ta Raina kanta
Minister yace kamin dedai Dana Ni wlh narasa me hajiya Fatima take nufi da Kai kullin Bata goyan bayan abinda kake yi Ni ma kaina mijinta Bata goyan bayana yanzu abinda nake so da Kai ka kwanta ka huta kafin zuwa anjima in kanasan kudi ma ka iba in katashi
Minister wajan hajiya Fatima yaje ya sameta yace Fatima yanzu Dan Allah meyake da munki kekuma haka kike bakya kishin danki da mijinki kowama yatakasu badamuwarki bane Ina Yar sadakar da akabawa nabal dan kaniyarta nemanta nake me nabil yai Mata tabata Masa Rai ke Kuma da yake basan Dan naki kike ba shine Kika hanashi ya daketa ko kefa Naga alama kamar kina goyan bayan auran da baffah yaiwa nabil Anya kuwa basa hannunki aciki nifa nafara zarginki Dan ke basan nabil kike ba
Dariya hajiya Fatima tayi tace gaskiya girma yafadi Alhaji abin naka dada cigaba yake yanzu Kai bakaji kunyaba da kazo kana kunfar Baki akan yarannan gaskiya kaiwa kanka fada saboda gaba Kar aji kunya Ni wanka Zan shiga kaga tafiyata Dan kome Zan tsaya cemaka ba shiga kunnanka zeyiba bakaji na baffah ba bare Kuma nawa Kai da danka Allah yaganar da ku
Dare nayi lokacin kwanciya bacci yayi nabil yafito daga wajan minister yazo shigewa yaga shatuwa da Hajiya Fatima afalo suna Hira ko kwallan inda suke beyiba yashige yana Jin abinda zewa shatuwa in ta kuskura ta shigo bangaransa Yana shiga yakarewa ko Ina na wajan kwallo afili yace Allah ya temakeki yarinya Baku batamin waje naba yau da kinga rashin mutunci Ina jira yau Naga a Ina Zaki kwana dakinshi yashiga yaje yayi wanka yayi Shirin kwanciya bacci kwanciyarsa yayi hankali kwsnce
Bacci yafara ibanshi yaji ana buga kofa kamar zaa balla can Kuma yaji muryar shatuwa na mgn ka budemin kofa wlh ko na hanaka bacci wlh Babu inda zanje na kwanta se awannan dakin kafuto ka barmin dakina Ni karka samin kazanta adaki
Dataga baze fitoba fita tayi taje kicin ta dauko ludayin miyi tazo tahau yin kida da kofar dakin da nabil yake ciki akulle tacika ko Ina da karar kidan Amma can da taga bemataba tahau Waka dandudu matamaza meshigar Mata rabi aljani rabi mutun anji kunya me zamanman wando me wuya du sarka me fanti agashi me tafiyar Yan kaciya
Kidan da take be batawa nabil Rai sosaiba se Wannan Wakar da take Masa ai awani zabure yaduro daga Kan gado yahau neman abin da ze zaneta dashi dube dube yafara yagano belit dinshi yadauka yanufi kofar dakin yabude cikin bacinrai yayo kanta ze daketa itakuma Daman ta shiryawa hakan tasan yanzu ta tunzuroshi ransa yabaci Dan ta fahimta bayasan tana kiranshi da sunayan banza da Kuma wakar da takemai Dan taga ransa yabaci ranar da tasa kawayanta sukai Masa Waka tana ganin yabude kofar yayo kanta zefara zuba Mata ajiki Tai maza ta bude ledar dake hannunta ta Hura Masa kararar da Tai alkawari se tasamasa ajiki shi da minister in har shima be Dena yiwa iya rashin mutunci ba tindaga can takwaso shi agidan megari da zasu taho Abuja takwayi saa ta fesamai da yawa yashiga jikinshi sosai Kuma du dukan da ze Kai Mata baya samunta kaucewa take suna ta zagaya falan wajan nashi intaga ze cimmata ya sameta se Tai maza ta tura kujera wajan da yake shikuma seyai tsalle ya tsallake
Tace lokaci kadan nabaka zakayi sanyine yau zamuga ainahin rawar dandaudu me tafiyar Yan kaciya ai kowa yaci tuwo Dani Miya yasha yanda ka karyamin hannu nasha azaba wlh kaima se kasha tawa wahalar yau se kayi kwanan zaune yanzu muka Fara wasan muzuba mugani Waze gaji tsakanin Ni da Kai bawai bakasan mataba aikuwa zakaga aikin Mata ka kirani Yar Kauye to ga aikin Yar kauyenan kafara gani Dan yanzu nafara ban Fara komai ba Ina da salo kala kala kuma du se ka shasu gobema ka kara shiga gonata
Allah yabawa nabil sai,a yakama shatuwa yadaga hannu kenan ze zuba Mata belit din yaji lokaci Daya kamar anzuba Masa wani mahaukacin kaikayi ai besan lokacin da yasaki hannun shatuwa ba yatsaya Yana daurewa ai tin Yana daurewa besan sanda yafara tsalleba Yana Susa Yana tsalle Yana zagaye falan Yana Hawa Kan kujerun wajan ai besan lokacin da yacire rigar jikinshiba yafara ihu Yana Kiran daddy
Me shatuwa zatayi inba dariyaba har da kwanciya yanda taga yanayi yake dada Bata dariya Waka tahau yi masa asosa asosa asosa Babu ciwo cinnaka ya cijeshi asosa Masa asaso waiyo Allah asosa kaga yanda zaka nayi in kanaso kadena Jin kaikaiyin kaga yanda ake agarinmu du yanda nayi kayi
Ai dasauri ya yarda da abinda tace danshi Yama manta fadan da sukeyi Dan azabar kaikaiyin da yake ji rawa tafara tana juyi tana wakar asosa shikuma bawan Allah Dan azaba rawar yake yi da wakar bill hakki yanda taga yake rawar dariya take tayi Dan mugunta dogwan wandanma shima cireshi yayi yakoma dagashi se gajeran wando
Tace zuba dagudu katafi wajan su mommy ka nuna musu kafin kaje zaka Dena ji
aikuwa yace to Ina hanyar
tace kaganta Nan
Aikuwa yazuba da wani mahaukacin gudu yafice
Shatuwa takuma fashewa da dariya tace kadan kagani in dai nice yanzu kaga Ni se naje nai baccina hankali kwance Kai Kuma ka kwana azaune
Tashige daki Tai kwanciyarta tahau bacci cikin kwanciyar hankali
Litantafaina da na rubuta kamar haka
*HADARIN So*
*'YAR KWALLIYA*
*NAFI GANE ARO*
*HEDAYA IKIRARI*
*TALLAFEE*
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama* 鉂ゐ煈�
*'YAR KWALLIYA* 馃コ馃拑
👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝👝
👠👠👠
👝👝
👠
💄💅 *DAN MINISTER* 💅💄
🦚🦚
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
11-12
Yan aikin gidan du Wanda yaga nabil yataho dagudu bakaya ajikinshi Suma se su zuba da gudu kowa na neman wajan buya tindaga bakin kofa yake kwallah Kiran daddy mommy kufuto Zan mutu dagudu yakarasa shigowa minister najin Kiran da nabil yake musu yafito hankali atashe yanda yaga nabil shima abin yabashi tsoro ga jikin nabil du yatashi yayi kamar kurajene yafito Masa abinka da farin mutun
cikin tashin hankali minister yace me yasameka nashiga uku nabil karka tafi ka barni zanshiga mugun hali Nima za a iya rasani waye yaima wannan abin Haka Hajiya fito kiga me yasamu danmu kifito ki temakeni zanrasa farincikina
Hajiya Fatima itama cikin tashin hankali ta karaso wajan tace mekuma yafaru da,dandarannan me zangani haka nabil tsaya nagani
Dakyar tasamu yatsaya tagani lokaci daya tagane meye ajikin nabil ahankali tace wlh nasan kece shatuwa kece Zaki iya zubawa nabil karara ajiki Daman shine abinda kikayi dako tin daga mazagai Allah yashiryeku ku denawa junanku mugunta muje kafarayin wanka da ruwa mezafi tukunna Sena shafama magani kai Kuma alhaji kayi hakuri ka kwantar da hankalinka yanzu ze denajin abinda yake ji
Nabil bemasan iyayan nashi na mgnba shi takansa yake Yana rokar Hajiya Fatima da minister su Sosa Masa da Kar Hajiya Fatima tasa minister yakama hannun nabil aka kaishi bandaki aka hada Masa ruwan zafi yasamu yashiga yai wanka Yana fitowa Hajiya Fatima tasa ya shafe ko Ina na jikinshi da manja sannan yaji dadin jikin nashi kaikaiyin yadena besan sanda baccin wahala ya kwasheshiba ranar dai be kwana awajansaba se awajan su Hajiya Fatima yakwana adaki Daya daga cikin na Yan uwanshi Mata da aka ware musu kafin safiya zazzabi me zafi yarufeshi se da aka Kira Dr yazo ya dubashi hankalin minister Kuma in yayi dubu yatashi Dan,so Babu lfy ko abincin kirki yakasa ci Yana ta lfyar nabil dinsa
Shatuwa kuwa batasan ya nabil yakareba da ta sashi yafita baccinta Tasha har gari yawaye ita Tama manta da babinsa saboda burinta yacika tafara bashi wahala
Nabil da yatashi da safe tinanin abinda yafaru jiya tsakaninshi da shatuwa yafara afili yace tambas itace silar komai jiya aikuwa Zan yi maganinta Nima baffah baffah ka hadani da wahala tindaga ranar da na hadu da annobar yarinyarnan shikenan komai nawa yafara samun matsala kullin bana cikin farinciki saboda ita dolenema nabar garin gaba Daya
Hajiya Fatima ce tashigo tasamu nabil tace nabil katashi yajikin naka
Yace da sauki mommy
Tace to alhamdulillah nabil yau sonake nabaka shawara da Kuma Yar nasiha Zan maka nabil wacece mahaifiyarka
Yace mommy wace irin tambayace wannan kece mahaifiyata bani da wata bayan ke kece dai bakya Sona bansan meyasaba Kuma wlh abin na damuna sosai Naga ke da su anty Amina bakwa fada kina sansu sosai kodan Ni ba mace bace ko Danni namijine bansaniba mommy abokaina in naji suna hira atsakaninsu suna fadin abinda iyayansu Mata suke musu kuma suke nuna musu so da gata har mamaki nake mommy meyasa Ni du bana samu daga wajanki kecefa daya daga cikin wayanda sukasa na tsani mace aduniya bazan boye mikiba kecema mace ta farko da tasa min akidar kin du wata mace saboda kece Kika haifeni Amma baka nunamin so kamar yanda daddy yake nunamin ke kullin cikin yimin fada da hantara kikemin ko Abu daddy yai min na kudi ko na siyaiya se kinmai fada ko Ni kinmin Kuma Naga bakyawa Yan uwana Mata da Suma kekika haifesu Kuma in sone Ni yadace kifi so saboda da nine auta saboda naji ance anfisan auta Anfi Kuma nuna Masa so amma ni meyasa du bana samu daga wajanki se wajan daddy kullin daddy ne ke sani farinciki kekuma kece mesani bacin Rai Dan Haka nasawa kaina akidar kin du wata mace saboda uwar da tahaifenima ta nunamin tsana Bata sona to wace macace zata Soni Kuma du da tsanar da nayiwa du wata mace narasa meyasa ke nakasa tsanarki azuciyarta na gwada na gwada Amma nakasa tsanar taki suma Yan uwana Mata na gwada na tsanesu Amma Suma nakasa tsanar tasu du da Suma basona sukeba kullin cikin kina da tsanata suke mommy irin abinda kike min Suma shi suke min natashi Babu kauna tsakanina da uwata da Yan uwana Mata me yasa meyasa mommy wlh Ina sanki azamanki na mahaifiyata innaTina da Ni bakya Sona acikin yaran da Kika haifa kinsan irin kukan da nakeyi
Kasa karasa mgnar yayi yafashe da kuka kamar karamin yaro itama kukan tasa taje ta rungumeshi tana rarrashinsa har tasamu yafara shuru tinani ta fara azuciyarta tafara mgn tace gaskiya Nima Ina da lefi babba dolene nai kokarin gyara komai Dan na samu ka gyaru Allah sarki Ashe yanajin zafin abinda nake Masa nikuma Allah yagani Dan yagyaru neke Masa wasu abubuwan dolene najaka ajiki sosai nabil Dina har kagane Nima ina sanka alhamdulillah Allah nagode ma da kafara ansar addu'a ta Akan nabil saura alhaji sautin kukan sane ya dawo da ita daga tinanin da takeyi
Cikin karfin Hali tace ya Isa Haka Mana haba nabil Dina Ina kataba jin uwa ta haifi danta tace bataso se dai taki halinsa wlh nabil ni kuwace me sanka kasan yanda nake ji araina saboda rashin jituwar da take tsakanina da Kai Sam Babu jituwa da fahinta tsakanina da Kai kaki ka gane abinda kake yi ba Abu bane me Kyau wlh kullin mutane na kuka da Kai da rashin mutuncinka da iko da takama irin naka du ba Abu bane mekyau du bana so kake yinshi kuma ko na maka nasihah bajina kakeba kasan ya uwa takeji in taga danta nayin Abu mara kyau kasan ya nake ji in na saka ahanyar gyara kaki ji nabil meyasa kana Jin mgnar mahaifinka amma Ni Kuma baka Jin tawa mgnar ai yadace Kai Mana adalci Ni da mahaifinka in kaji tashi mgnar Nima kaji tawa Kuma ka zauna kayi tinani da mgnta da ta mahaifinka wancece zata saka ahanya ma daidaiciya daga yau ka zauna kana tinani in na fadama mgn Kai bani bama har su baffah du Wanda yaima nasiha kana Zama kana nazari akai kaji Kuma nabil du Wanda yaima nasiha wlh masoyin,kane ba makiyinkaba daga Ni har Yan uwanka Mata wlh du muna sanka muna kaunarka ka canja kagani daga yau kaga in bakaji dadin Zama da muba Kuma zaka gane mune masoyanka na ainahi shima alhaji bawai nace baya sankaba aa Amma San da yake maka yasa idansa yarufe baya gayama gaskiya kome kayi Wanda ba dedaiba se dai yagoyi bayanka baze taba yima fadaba Dan ka gyara Kuma har ga Allah ba gata yake nunamaba nabil kullalin burina Naga ka gyaru kazama kamilin mutun Wanda kowa Zena alfahari da Kai Kuma kowa Yana yabanka baka tabayin tinani kaga yanda kowa yake tsoranka Kuma abayan idanka kasan zagi da tsinuwar da kake Sha awajan mutane musamman talakawa ko ga Yan aikin gidannan baka yimusu adalci kana wulakantasu kana cimusu mutunci Dan kawai Allah yamaka arziki sukuma suna Zama karkashinku karfa ka manta du kanmu dayane Allahne ya yomu yanzu in har kana sona kamar yanda kace to kana jin mgnta Nima kamar yanda kake Jin ta mahaifinka kaji Allah yasa du kaji abinda nace daga yau in dai zaka na Jin mgnta mun koma kamar abokai zakaga gatan da Zan na nunama Kai Sema kafi samun gata Akan sauran abokanka yanzu nice abokiyar shawararka Dana Allah yai maka albarka ai du kajini ko
Yace eh mommy to kiyi hakuri daga yau na Dena du wani abinda ba kyaso in dai Nima Zaki Soni kamar yanda kowace uwa take San danta Ni kullin burina da tinanina Naga Nima kina nunamin gata da kulawa kamar sauran Yan uwana yanzu me kikeso na Dena kuma ki fadamin wlh Zan Dena
Hawayan farincikine yafara zuba a idanta hajiya Fatima kuka me karfi tasaki Dan murna
Dasauri yaje yahau goge Mata hawaye Yana rarrashinta shima Yana hawaye yace mommy kina dagamin hankali Dan Allah kiyi shuru wlh indai nine nadena
Tace nabil kasan kukan me nakeyi kukan farin ciki nake yau Allah yaamshi addu'ar da nakeyi akanka safe dare cikin dare kullin se na Hana idona bacci Ina rokwan Allah Akan yashirya,min Kai Kuma kullin ban finda Raiba nasan Allah me amsa addu'ar bayinsane musamman addu'ar uwa Akan danta yanzu Ni Akan tsakaninka da shatuwa nake so kudena fada sonake kadena kulata kome Tai maka karka daga Ido ka kalleta bare har Kai Mata mgn Kaine mijinta baasan megida da kula matarsa suna raba abin kunyaba kaga yanzu raini na neman shiga tsakaninka da ita Dan baka Kama girmanka
Kuma kabi nasihar da baffah yake maka se Kuma Kan Yan aikin gidannan Suma ka Dena musu abinda kake musu ka Dena takura musu
Yace to mommy du Zan Dena ko ban Dena dukaba Zan Dena wasu daga ciki in har Zakiji Dadi aranki ki dena min abinda kike min du Zan Dena Amma gaskiya nifa wannan yarinyar bana Santa kema kin sani yarinyar kina ganin abinda take min Bata da kunya Kuma Ni gaskiya bazan iya kwana da ita daki dayaba Dan lokacin da Zan karkaryata ma bazan saniba Kuma gashi kince na,Dena kulata in ta batamin Rai se dai in nakoma dakin da ke kusa da ita tinda da komai adakin shima Dan Ni bazan iya komawa dakin da ta kwana aciki ammafa du da nace yanzu in ta min lefi na Dena kulata ammafa du ranar da ta kaini bango nako gaji da abinda take min wlh se na bata mamaki itama kija Mata kunne tanena shiga har kata
Shuru Hajiya Fatima tayi azuciyarta tace alhamdulillah komai yakusa zuwa karshe insha allahu
Yace mommy yanaga kinyi shuru ko abinda nace be mikiba
Tace yamin Mana nabil bakomai kana kwana adaya dakin Allah yaimaka albarka Allah yadada shiryamin Kai itama shatuwa Zan sameta nai Mata fada sosai akanka Suma su Amina du za su Dena yima abinda suke maka maza tashi Kai wanka muje muci abinci tare
Dadine yakamashi yahau murna yace ngd mommy wlh yau kin sani farinciki Ashe dai kina Sona da gaske bandaki yashige yana ta fara,a yau mommy Bata Bata Mai raiba
Yau shatin shatuwa biyu agidan minister bakaramin hakuri nabil yakeyi da itaba ko Hajiya Fatima shedace gawata tsanarta minister da nabil suke dada nunawa Hajiya Fatima Jin dadinta yanzu nabil bayashiga harkar shatuwa tin ranar da tamai nasiha akanta shine bekara kulata sunyi fadaba yadan rage kadan daga cikin halayanshi ko Yan aikin gidan suma sunsan nabil yacanja Akan da har mamaki suke itadai Hajiya Fatima har yanzu tana kai kukanta awajan Allah akan Allah yadada shirya Mata shi yakuma dedaita tsakaninsu da shatuwa Dan in nabil yafara San shatuwa minister ze hakura da akidar da yasawa ransa Akan shatuwa Amina ma na iya yinta Kan shatuwa Babu lefi tadan rage wani abin Hajiya Fatima Kiran yaranta na kasar waje tayi taimusu nasiha Akan nabil su jashi ajiki sosai Dan yacire zargin da yakeyi akansu amina ma yanzu tadage wajan Jan nabil ajiki tana nuna kulawarta akansa tahaka itama take samu take bashi shawarwari cikin dabara Kuma alhamdulillah Yana dauka hakan yasa Hajiya Fatima cikin farinciki du wannan bidirin minister be saniba musamman ma kwanannan da aiyuka sukai,mai yawa nabil yanzu Yana Jin dadin yanda Yan uwasa Mata da mahaifiyarsa suke nunamasa so da kulawa basa Kuma numa suna kinshi saboda halayanshi
yaune baffah yazo da me gyaran karaya Dan yaga ya hannun shatuwa ko ta warke Kuma shima yaga irin zaman shatuwa da nabil me gyara yakunce daurin da ke hannun shatuwa alhamdulillah gyara ya gyaru dayake me dorin kwararrene
baffah yakebe da Hajiya Fatima da Amina Akan yaji Yaya zaman nabil da shatuwa da Kuma halayansu ko sun gyaru su Hajiya Fatima sun Masa bayani Akan nasarorin da aka samu baffah yaji Dadi sosai se dai sum masa bayani har yanzu shatuwa Bata Dena tsokanar nabil ba Dan Haka yakara jamata kunne ta dena yakuma ji Dadi da akasamu yanzu tanajin mgnar Amina shi Kuma nabil najin mgnar Hajiya Fatima
Baffah bayan ya sallami me gyaran karaya shi be tafiba se da yajira dansa minister yadawo wajan yamma sosai yadawo se dadandare suka samu Zama tare yace to sani nadawo Akan bakata na acikin gidajanka kazabi Daya kabawa nabil yatare da matarsa Kuma gobe gobe nakeso subar gidannan tinda matarsa ta warke su koma saban gidansu Dan su samu fahimtar juna sosai Kuma du wani Kayan dakin shatuwa Kaine nake so kadau nauyi gaba,daya saboda Kaine yanzu ubanta Kuma befi karfinkaba Dan Haka bazan bar garinnan ba se Naga sun tare Naga gidan da suke ciki
Gumine yafara ketuwa minister yace baffah Daman da gaske kake ba anan gidan zasu zaunaba yanzu in na basu wani gidan nasan me zatayiwa nabil na cutarwa ga wannan kakar tata Mara mutunci Kuma ai yarinyar tana da uba ai shine ze Mata kayan daki wlh Ni da nabil na Santa ko nawane Zan iya kashe Mata Amma gaskiya yanzu ubanta yai mata
Baffah yace Kai wato har yanzu baka sadudaba baka yarda da kandaraba shifa aure nufin Allah ne Dan Haka kabi ahankali ba aja da irin aurannan Dan bakasan me Allah yake nufiba akan nabil da shatuwa Dan Haka Kar na kara jin ka kushe Masa Mata da zaman auransu Kuma dolene kayi abinda nace ko ranka yabaci ba zanbar garinnanba se Naga komai yayi dedai yanda nake so
Haka minister ya yarda badan ransa yaso ba gari na wayewa minister yakai baffah gidan da yaginawa nabil tin kan yagama makaranta Daman ya ajje gidanne amatsayin Daya daga cikin manyan kyautintika da ze Masa ranar auransa gidane nagani na fada ankashe nera wajan ginashi haka minister yazubawa shatuwa da nabil dukiya ko Mai na zamani me tsada yazuba musu Amma Yana bakincikin ba matar da nabil ke so bace zatayi rayuwa agidan baffah yayi faranciki da yaga bajintar da minister yayi
su Amina ne Yan raka amarya gidanta aikuwa taci gyara Amina da Hajiya Fatima sunyi kokari Dan ko mahaifiyata se dai haka wajan gyarata Dan su sun san da mgnar tarewar Dan Haka tin kan lokacin yazo sukai Mata du abinda yadace na gyara
ango nabil be San da mgnar tarewaba se yau da aka,kai shatuwa baffah da Hajiya Fatima suka zaunar da shi suna Masa nasiha me ratsa zuciya akan zaman aure da kula da matarsa suka Kuma Gaya Masa yau zebar gidan yakoma saban gida yaso yaki yarda Amma da yatina da kukan farinciki da Hajiya Fatima tayi akansa na yafara Jin mgnarta se jikinshi yamutu Kuma gashi yanzu Yana Jin dadin Zama da ita da Yan uwansa Dan Haka yace to baffah da mommy du naji Kuma zanyi aiki da abinda kukace Amma baffah yarinyar na kaini bango sosai wlh darajar mommy takeci Kai Mata fada tadena Kar na fusata Dan bazatai kyauba in da ta daddy zanbi da tini tana gadan asibiti
Baffah yace karka damu du nasan komai Kuma na Mata fada bazata kumaba har Yan aiki du sani yazuba muku Allah yai,muku albarka tashi muje Ni zanma rakiya har gidanka daga Nan Ni zan shige garinmu in da nafi wayo kaga Kenan nine babban abokinka na rakoka saban gidanka
Dariya dukansu sukasa Hajiya Fatima da baffah sunji Dadi sosai da nabil be yimusu kardamaba Akan abinda suka fadamasa yabasu mamaki sosai haka baffah yarakashi har gida yahadasu yai musu nasiha sannan yashige mazagai
Minister besan nabil ya yarda da mgnar tarewarsu ba yasan nabil ba ze yardaba murna yai tayi yasan in nabil yaki yarda Dole baffah yahakura da mgnar Dan Haka ko mgnar bewa nabil ba yai ficewarsa wajan mitin se bayan dawowarshi yake tambayar Ina nabil Hajiya Fatima take gayamasa ai nabil yatare a saban gidanshi baffah nema yarakashi wajan matarsa ran minister yadada baci Dan bahaka yasoba mamaki yafara yaakai nabil Yayarda Kuma ko kiransa beyi yagaya masaba
Bayan tafiyar baffah kallan kallo suka tsaya yiwa juna shatuwa harararshi Tai tayi da murguda Baki shi abinma dariya yafara bashi kwafa yaja me karfi sannan yatashi yashige dakin da yake azaman nasa itama dakin da aka nuna Mata azaman nata tashige da kudiri kala kala aranta
Amina ta nemi malama mace me koyawa shatuwa karatu na boko da arabiya gidan Amina malamar take zuwa kullin Amina take sa ake kawo shatuwa gidanta ana koya Mata karatu da abubuwa da dama na rayuwa Amina tayimakin kokarin shatuwa na yanda ana koya Mata Abu take rikewa ban garan girkima Babu lefi tana Mai da Kai wajan koya
yanzu Babu lefi ta rage tsokanar nabil ba kamar Daba Amma har yanzu in tana jin tsokana tana tsokanoshi sedai shi yanzu yanayi ne kamar be gantaba rashin tsorone na shatuwa Amma yanda yanzu nabil yake hade Mata fuska Babu alamun Wasa ko faa,a a fuskarshi Dan karfin Hali irin na shatuwa Haka take tsokanarsa shikuma da kudirin da yayanke akanta na yin maganinta ko da sau dayane
Yau iya ce taje har gida tasamu baffah ta tubure masa Akan se ya kawota wajan shatuwa in bahakaba ta kaishi Kara wajan hukuma akan yakai jikarta garin Yan gayu gidan Miss Miss yasiyar da ita
Tace usuman tinda jikata tatafi Basu taba kawota ganin gidaba Kuma naba aminaina labarin kalar garin da danka da jikanka ke Zama da kalar gidan da suake ciki Dunn Basu labari shine suka fadamin danka na yankankai Kuma na yarda da maganar su Dan inba hakaba ta Ina ze Tara wannan uban kudin sun tambayeni aikin me yake Acan na gaya musu mukamin Kiran mage gwaunati tabashi ko acanma garin miss miss ake kiransa da shi Dan Haka yau wlh bazan yi hakuriba se munje tare da Kai na gano ta ashiryena nataho kaga har da kayana nataho Dan Haka daga Nan se gidan miss miss Dan tinda naji shuru nasan dandaudu da miss miss sun karasa min ita ta karasa mgnar da Kuka
Shi baffah dariya ma ta bashi yace iya ikwan Allah sarka me rikicin gangan kakar nabil da shatuwa sirika awajan alhaji sani me mukamin Miss Miss Nima na dan taba yakuma sa dariya to kiyi shuru ki Dena kuka Bari nasa wani daga cikin jikokinmu ya kaimu amotar,sa Amma aminannan naki sun iya Baki shawara me Kyau Ni Dan Allah kiyimin shuru tin da mun fito waje Kar ki taramin jamaar gari ga motanan shiga mutafi
Se da iya taga da gaske wajan shatuwa za a kaita sannan ta Dena kuka da ruwan masifa daga bayama baccine ya kwasheta amotar kafin sukai baccinta Tasha har da munshari baffah shi dai dariya yake ta mata seda suka Kai Abuja baffah ya tasheta
yace munzo tashi mu shiga
Baki ta washe tafito suka shiga gidan minister baffah yasa aka Fara kaisu
minister na zaune aharabar gidan Yana Shan iska Babu zata Babu tsammani yaga baffah da iya ko kadan be yi murna da zuwan iya ba Rai yahade yai kamar be gantaba baffah kadai ya gaisar
Aikuwa dawa Allah yahadata inba Shiba tace ai Dole ka dauke Kai kayi kamar baka ganniba ka hade Rai tinda kun siyarmin da jikata kun kara Akan kudin da kuke dashi Ina Dan kwal uban Dan naka me zamanman wando me gashi kala biyu muje ku kaini inda kuka sai da ta na karbo jikata in bahakaba na tara muku mutane wlh
Shadai baffah na gefe beyi mgnba
Ana Haka Hajiya Fatima tafito saboda Jin hayaniyar da taji taganin iyace da minister tace ashedai kunnena be jiyomin karyaba Daman nace iyace dasauri takarasa wajan tahau bawa iya hakuri tace haba iya Dan Allah kiyi hakuri be Kai hakaba Yan zudai shatuwa kike San gani ko
Iya tace indai suna da gaskiya anunamin ita Dan naji usuman nace min wai shatuwa Bata gidannan Ni ko saurararshi ma banyiba Dan nasan me ze fadamin an sai da shatuwa Dan Haka Ni ko cikin gidanku bazan shigaba se ankaini na karbo jikata in yaso shi Miss Miss din yasan yanda zeyi yamai da musu da kudinsu tinda bani naciba
Hajiya Fatima tace ikwan Allah Yanzu Dan Allah inba rigima irin takiba iya Wai shatuwa kike nufi alhaji da nabil sun sayar da ita se kace wata Yartsana Kinga muje ga direba can nasa ya kaiki gidan shatuwa ki ganta tananan lfy Ni Zan shigar Miki da Kayan
Baffah yace Ni nasha ciki Fatima se kun shigo in kingama raban rigimar iya kushigo tare ta huta
Ai baffah nashi iya tadada burkicewa dole hajiya Fatima tasa direba yakaita gidan shatuwa
Hajiya Fatima nashiga ciki bayan sun gaisa da baffah yake tambayarta ina it's
Tace ai Taki yarda mu shigo tare Dole se da nasa direba yakaita gidan nabil taga shatuwa
Baffah yace Fatima kinyi ganganci kin sanfa halin iya in nabil nagida se tayi abinda Dole se ya kulata danma ansamu yanzu yadan yi sanyi Dole yanzu mubi bayansu tinda bamu San me ze faruba
Hajiya Fatima hijabi tadauko tasa suka fito ita da baffah zuwa gidan nabil baffah kallan inda minister yake zaune yayi ze Masa mgn sun tafi gidan nabil se yaga Babu minister awajan zamansa
Baffah yace to shikuma sani Ina yaje Fatima ko dai yashiga ciki ne
Hajiya Fatima tace aa baya ciki Dan Banga shigarshi a
Hajiya Fatima direba takira take tambayarsa ko yaga minister
direban yace ai hajiya naji Yana cewa Musa direba yakaishi gidan yallabai nabil
Salati hajiya Fatima tafara tace shikenan baffah za akuma yakin badar alhaji yabi bayan iya kenan
Baffah yace Daman abinda nake gudu Kenan muyi maza mu karasa Kan ta kwabe
Hajiya Fatima tace ai nima se nakira Amina munhadu Acan Dan itace me iyawa da shatuwa yanzu
Kiran Amina hajiya Fatima tayi awaya tace Mata su hadu agidan nabil Amina tayi mamaki tinani tafara ko lfy
Direban na Kai iya gidan nabil tinda ga kofar shiga falansu tafara Jiyo muryar shatuwa tana ihu da kara nabil ne yamurde Mata kunne tana ta Kara Dan azaba yau takaishi bango Dole se da yakulata Miyar kubewa tayi tazubo akwano tataho falo da ita Dan tsokana nabil na zaune Kan kujera Yana kallo tazo ta juyemai miyar ajiki shikuma saboda bacin Rai ya kwace kwanan yai cilli da sauran miyar da tarage akwanan tazube awajan kofar shigowa Dan bacin Rai nabil yarasa wana hukunci ze Mata Yana rike da kunnanta yaki yasaki Daya hannun yasa ya dauketa da Mari har sau uku zafin Marin yadada gigita shatuwa takurma wani mahaukacin ihu
Tace waiyo iya ze kasheni kizo ki temakeni
Habawa iya najin Haka tace Ashe gara da nazo dawuri da ban zoba da ankashemin ke
dube dube tafara aharabar gidan wata doguwar sanda tagani ta dauka tashiga gidan da ita Allah yasa ta kula da miyar da ke zube akofar falan Amma Bata kula da sauran da ya ballatsu acikin falan du yabata waje dadama lokacin da tashigo lokacin shatuwa tasamu takwaci kanta daga wajan nabil tazuba dagudu shikuma nabil wayar T.V yacira yabita da ita ze zaneta zagaya falan suka hauyi dagudu ga shatuwa da shegen gudun tsiya kamar taci kafar kare
Ai iya itama Babu Bata lokaci tashigarwa shatuwa tabi bayan nabil da gudu abin dariya gudun nata saboda tsufa dakyar take gudu tana bin bayan nabil da sanda zata kwala Masa shikuma nabil bema San iya na binshiba Dan be kula da itaba daga shi har shatuwa Babu Wanda yakula da shigowar iya
Dedai Nan motar minister tashigo gidan nabil ihun shatuwa da iyi yajiyo ai ko motar bebari ta tsayaba yafito yashiga cikin falan cikin zafin nama Yana masifa shikenan sun hadu zasu kashemin Dana kwaya Daya da nake dshi namiji
ai kokarasa sauran mgnar da ke bakinshi beyiba yasa kafarsa cikin falan Kan miyar kubewar da su nabil suka zubar minister Babu zato Babu tsammani yaji anyi sama da shi andawo dshi kasa damm Dan azaba minister Kara yasaki yayi yayi yatashi tsaye yaje ya temaki nabil amma yakasa ashe yazamu gocewar kashin hannun shi na hagu ga Kuma yatsun kafarshi guda biyu da sukaji targade
Su nabil gudu suke suna ta zagaya falan iya na ta binsu abaya taga minister azaune ai bashiri tayi kansa
tace au Ashe kana gidan kana gani me zamanman wando ze kashemin jika bakayi mgn ba kaiwa danka mgn yabar min jikata Kar yakuma sata Kuka au baza kayi mgn ba ko to Bari nafara kwadamaka inkaji zafi kayi mgn
takarkarewa tayi tadaga sandar sama ta sakarwa minister ita abaya Kara me karfi minister yasaki Dan Safi
tace Kai Mai mgn yabarta ko na karama
minister mgnar ma yakasa dada daga sandar tayi takuma sakar Masa abaya
ai besan sanda yace nabil kabar Mata jikarta Dan Allah kayi hakuri zata karya min baya matarnan shegen karfin tsiyane da ita
Karar shatuwa du tacika falan shi nabil ma bejiba be kula da minister ba har yanzu bare iya dagudu sukayo wajan su iya alokacin Nabil yasamu yafara zubawa shatuwa bulalar ajiki saura kadan ayi tafiyar ruwa da iya nabil Ido yarufe yazubawa iya wannan wayar T.V itama ajiki lokaci guda iya tacika wajan da Kara Dan tsabar rudewa rasa inda zata shiga tayi Kai kanta wajansu takuma yi wajan guduwa yakuma dagawa yazubawa iya ajiki shi du ya dauka shatuwa yake zanewa saboda idanshi yarufe da zafi yakuma ruda iya tai hanyar waje dagudu tsutsayi Tai Kan cikin miyar kubewar Nan se jitayi anyi sama da ita tadawo kasa rimm wani marayan ihu tasaki ko mutsin kirki takasa tana kwance male,male cikin miyar kubewa garama minister shi yayi karfin Hali azaune yake Yana jinyar kanshi
Ana Haka motar su baffah da Amina tashigo gidan ihun da sukaji nafitowa daga cikin gidan gamasu aiki du awaje sunyi jugum,jugum suna,jin abinda ke faruwa aminace Tai saurin shiga ciki taci Karo da iya da minister ahanya
ihu tasaki tace su mommy kuzo kuga ikwan Allah yau abin nayine gasu iya da daddy anshemesu kushigo ahankali yau abin yayi zafi miyar danyan kubewace azube duka afalan
Cikin dabara suka samu suka shigo wajan dakar suka rabasu suka rabu Hajiya Fatima tarike hannun nabil Taki sakinshi Amina itakuma tarike shatuwa jansu sukayi suka zaunar da su Akan kujera Suma suka zauna
Kuka Hajiya Fatima tasa tace nabil kakaryamin alkawari ko yanzu kunga danyan aikin da kukayi ku kalli iya da alhaji du kun dokesu da bamuzoba kashe kanku zakuyi da Allah be kawomuba
Se lokacin nabil yaga minister da iya Hakuri Nabil yai tabawa Hajiya Fatima kukan da take Yana dada tadamai hankali Yana dada Jin tsanar shatuwa aransa
Shatuwa tace lah iya yaushe kikazo har da daddy
Baffah yace yimin sharu ta Ina zakusan sun zo kun shiga filin dambe Ni yanzu babu wata nasiha da Zan Kuma muku Dan ko karatune yaci ace kun dauka Dan Haka nagama yanke hukuncin abinda yadace Dan Haka yau nayarda iya muzo tare da ita taga jikarta Ashe daraban abinda ze faru Kenan
Yakalli su minister da har yanzu sun kasa motsi yanzu ai kunga abinda nake gudar muku gakunan da alama du kanku kunji ciwo ajiki kadan ma Kuka gani Kar kuyiwa kanku fada Kar kuyi kokari kuhada Kan yarannan se ku tashi mutafi gida
Iya tace wlh usuman karfin siyane da jikanka Ina ganinshi kamar kajin turawa bawani karfi zeyiba Ashe ba daganan takeba Kai me zamanman wando me ka dinga shaudamin ajiki wace irin bulala kayi anfani da ita ta fashe da Kuka
Amina dariya takewa iya
MINISTER Dakar aka kamashi yatashi tsaye akasashi amota iya Kuma aminace ta kamata tasata amota suka shige gida gaba Daya amota se ruwan masifa take tawa minister shikuma yaki kulata takansa yake
Nabil Daman yau da ciwan mararshi yatashi daurewa kawai yake har yakula shatuwa sukayi fada dare nayi yazo kwanciya ciwan Mara yatashi sosai kamar ze mutu Dakar yasamu yakira Dr dake dubashi awaya yagaya masa abinda ke damunshi
Dr yace gaskiya yallabai kayi hakuri wlh Babu abinda Zan iya yimaka na temako ayanzu Dan tintini namaka bayani Babu abinda zaa iya iyimaka kawarke inba aureba Kuma anmaka maganinka matarka ko tayi tafiya ne in banisa tayiba kasa ta dawo gida yaimai sallama yakashe wayar
Nabil juyi yai tayi yahada gumi sosai tinani yafara yanda ze je yasamu shatuwa da wata bukatarsa bayan shi yatsani Mata kamarsa ai inyayi haka girmanshi yafadi Zama ta dada rainashi da azaba ta dameshi bema,san sanda yasauko daga kangado yai hanyar dakin shatuwa Yana dafa bango Dakar yasamu yakai kanshi kofar dakin shatuwa hannu yasa yabude kofar dakin yakwayi sa,a dakin nata abude lokacin tafito daga wanka daga ita se tawul daure ajikinta
Ihu tasa tace me kazo yi dakina da wannan daran me yakawoka ko kayi mantuwane bananne dakinkaba ficemin daga daki ko natarama mutane ko kazo mukara wani bawa hammata iskarne
Shi ko Jin abinda take fadama beyiba gadan gadan yayo kanta yadagata sama cancak ya wullata Kan gado yahau kanta dukanshi kawai takeyi tana ihu tana cizanshi har da yakushi ko ajikinshi bema san tanayiba ta maganin matsalarsa yake gani yake in beyiba mutuwa zeyi Dan shi yasan me yakeji hanyarsa yafara nema Babu Bata lokaci yasamu yashige dakarfi
Wata mahaukaciyar Kara tasaki
Naguda daganan ango da Amarya asha soyaiyar Dole 😂
YAN DAN MINISTER fans
Sekunzo jinyar shatuwa
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama* ❤👸
*'YAR KWALLIYA* 🥳💃
👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝👝
👠👠👠
👝👝
👠
💄💅 *DAN MINISTER* 💅💄
🦚🦚
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
13-14
Nabil yawahalar da shatuwa sosai Dan gaba,daya baya hankalinsa saboda wata sabuwar duniya da yaji yashiga Wanda betaba shigaba se yau ita tana kukan azaba da Kiran iya da kawayanta Babu Wanda Bata kiraba har da su amina shikuma kukan dadin da be taba jiba yake surutaikuwa Babu Wanda beyiba har da yiwa baffah godiya shatuwa da wuya tayi wuya numfashinta daukewa yayi batasan sanda nabil ya bartaba bayan komai yanutsa rungume shatuwa yayi Yana ta Mai da numfashi jiyayi gabadaya ciwan da yakeji na Mara Babu kamar an dauke Masa wani Abu me dauyi ajikinshi wani baccine me nauyi yadaukeshi be farkaba se da gari yawaye sosai Ido yabude ahankali yaji mutun ajikinshi da sauri yaduba yaga shatuwa ce kallan inda yake yahau yi abinda yafaru jiyane tsakaninsa da shatuwa yadawo Masa kurawa shatuwa Ido yayi yaga ko motsi batayi ranarne yakare Mata kallo yaga yanda ainahin kalar fuskarta take yadade Yana kallanta irin rashin mutuncin da take Masa yatuno yakuma tuno abinda yashiga tsakaninsu adaran jiya wani tsaki yasaki yatashi afusace yasa kayansa yai hanyar waje har ze fita yatuno ko motsi bega tanayiba dawowa yayi yatabata yaga kamar Bata da Rai ruwa me sanyi yadauko ya kwara Mata takuwa saki wani marayar Kara tsaki yakuma Jah yai ficewarsa ko kallan halin da take ciki beyiba ko damuwa bare ya temaketa Yana dada Jin haushin kansa da yazubar da girmanshi kamarshi yaje ya aikata haka da shatuwa Kuma gashi shi yatsani Mata garin yayama shi yashiga dakin ta tinani yake tayi har yashiga dakinshi Yana shiga wanka yaje yayi bayan yagama shiryawa kasa Zama agida yayi yai ficewarshi gurin da yake shakatawa
Baffah se da yasa aka nemo me gyaran targade yagyarawa minister targadensa da gocewar kashin da yayi yafada yaji wajan gyara Dan gurin yayi tsami sosai
Iya tinda suka dawo takasa motsa jikinta barinma hannunta gabadaya jikinta ciwo yake Mata ga hannu yaki motsuwa itama se da akasa me gyara yaduba Mata hannunta yaga tasamu tsagewar Kashi ahannunta na dama aikuwa kafin agyara hannun ansha daru da ita Miss Miss kuwa takira sunansa ba adadi tana Masa ruwan masifa shi da nabil
Amina ce tazo da safe baffah ne yasa tazo da mgnar da zasuyi tasamu baffah abangaran da yake sauka yasa aka Kira Masa hajiya Fatima bayan sun gaigaisa
baffah yafara mgn yace to Kan mgnar mu na kiraku wannan shawarar da nayanke itace mafita insha allahu Kuma za a dace Amina tinda tafiyar Taki ke da mijin naki tazo zuwa kwas,din da zejeyi america kutafi tare da shatuwa tinda shi mijin naki yace tare zaku tafi Kuma sani na da gida acan america gidan nashi zaku sauka har mijin naki yagama kwas,din da zeyi na wata shida Dan Allah ki dada kokarin da kikeyi Akan Wanda kikeyi Akan shatuwa muma anan zamuyi iya namu kokarin Kan nabil har musamu abinda mukeso awajanshi Dan shiryuwarshi itace shiryuwar sani itama shatuwa hakane Dan Haka yanzu tinda kince yau da yamma zaku tashi zuwa America kije kisa shatuwa ta shirya ki hada,mata du abinda yadace ki tafi da ita gidanki lokaci nayi se dai ku tafi ko tanan karku biyo da ita Kuma karki Bari nabil yasan kece Kika tafi da shatuwa ko iya bazata San da tafiyar jikartaba Dan hakafa na yarda muka taho da iya dan Tai sallama da shatuwa Kinga karshe ga abinda yafaru itama bazata,san shatuwa tayi tafiyaba in bahakaba komai baci zeyi yanzu Fatima takira megadin gidan nabil ta tambayeshi ko nabil nanan yace bayanan yadade da fita Danhaka sekiyi sauri kije ki dauketa Kuma ko lokacin da wowarku yayi inhar dukansu Basu shiryu yanda mukesoba baza a dawo da shatuwa ba har se munga sun koma yanda mukeso
Amina tace to baffah Amma aganinka iya bazata damekaba Akan kafito Mata da jikarta kasan halintafa da rigima
Hajiya Fatima tace Nima tinanina kenan Kuma wannan matakin da kayanke Kan nabil da shatuwa baffah shine dedai Allah yabamu sa,a ni wlh daga iya har alhaji rigimar tasu dariya take bani garama nabil da shatuwa suna da dalilan abinda yafara hadasu fada tin farko Amma iya da alhaji Basu da wani dalili alhaji nabil yake tayawa fada iya Kuma shatuwa Kuma wlh Ina guje musu ranar da nabil da shatuwa zasu shirya zasuji kunya sosai mudai muna gefe kallone namu tasa dariya
Baffah yace rabu dasu gani sukayi zasu iya Ni abin takaicima sani ne mecewa indai Akan nabil ne ze ajje mukamin minister agefe in dokuwane shi da iya su doku Allah yaganar da su gaskiya; karku damu da iya danta umaru wato mahaifin shatuwa yasan komai Akan tafiyar Kuma yabamu goyan baya akai ita,kuma iya nasan yanda Zan shawo kanta har Allah yasa shatuwa ta dawo se Naga tafitarku Amina sannan zamu koma mazaigai Ni da iya Allah yakaiku lfy ku dawo lfy maza tashi kitafi Allah yai muku albarka
Amina gidan su nabil tasa direba ya kaita tana shiga taita sallama taji shuru ta dauka ko bacci sukeyi Kai tsaye dakin shatuwa tashiga ganin halin da shatuwa take ciki ko motsin kirki Bata iyawa tana kwance abin tausayi yadagawa Amina hankali tambayarta tafara me yasameta ko nabil ne ya daketa shatuwa Babu bakin mgn se kuka shima da kyar takeyi yaye bargwan jikin shatuwa da tarufu da shi tayi ganin yanda jini yabata inda take kwance yayi mugun tada Mata hankali Dakar ta rarrashi shatuwa tafada Mata abinda yafaru tsakaninta da nabil Amina taji Dadi sosai da haka tafaru tsakaninsu kafin shatuwa tabar kasar ita taiwa shatuwa wanka ta gaggasa Mata jikinta Taji tausayin shatuwa sosai ganin barnar da nabil yai Mata ita ta gyara ko Ina na dakin har zanin gadan se da ta wankeshi a injin wanki tayi du abinda yadace sannan takama shatuwa suka fito tasata amota da kayanta suka fice asibiti tatara Kai shatuwa aka dubata sannan suka shige gidan Amina yamma nayi wajan karfe shida jirginsu yatashi zuwa America baffah da Hajiya Fatima ne suka rakasu har sukaga tafiyarsu sannan suka dawo gida
Nabil tinda yaje wajan da yake hutawa tinanin shatuwa da abinda yashiga tsakaninsu yake ta dawo mishi ko Ido yarufe abinda yafaru yake gani ga fuskar shatuwa da take ta Masa yawo a idanshi kide kiden da ke tashi awajan da wakar du yau ji yayi basa Masa Dadi tinani yafara to da yafito yabarta awannan halin waye ze temaketa in tamutufa Kuma ko bakomai ai ta dalilinta yasamu lfy jiya Kuma yaji dadin da be taba jiba Daman mata na da wannan Ni,imar Haka me Dadi har da wannan ballagazar Mara mutuncin to yanzu waye ya temaketa ko tamutu fitowata daga gida jiyayi gabansa yafadi besan lokacin da yasaki wata karaba yafara mgn kamar zararre A,A,A Bata mutuba to Wai meyasa nake tinaninta Wai meyake faruwa da nine abokansa da sauran mutanen da ke wajan kallansa suke tayi suna mamakin me yasameshi yau haka Babu me bakin tambayarsa saboda kowa yasan halinshi wajan mota yanufa da sauri ze shiga dagudu yaransa suka rufamasa baya suka bude Masa motar Yana shiga sukaja suka fice dagudu zuwa gidansa
Motar ko Gama tsayawa batayiba yabude yafito da gudu,gudu sauri,sauri yashiga gidan jiyayi gabanshi yayanke yawani mugun faduwa dakin shatuwa yashiga dagudu yaga bataciki yaje da sauri yabude bandaki yaga bakowa aciki dakin yahau kalla yaga ko Ina tsaf angyara Babu alamun mutun yakwana acikinsa kangadan yakalla yaga agyare anma canja zanin gadan gabadaya fita yayi yahau duba ko Ina nagidan nanma be gantaba dagudu yatafi wajan masu gadi Yana tambayarsu da tsawa Ina matarsa
Jiki na Bari sukahu bashi amsa Suma Basu gantaba ko fitarta Basu ganiba
Yace Babu wata ko wani Wanda yashigo gidannan bayan fitata yatafi da ita
Sukace eh yallabai Babu kowa Kuma mu bamuje ko inaba muna wajannan da wasu sun shigo da mungani
Yace wlh inhar tabata kome yasameta kunsan Allah bazan barkuba Ni dakune to meye anfaninku agidan tinda baza kuyi abinda aka daukekuba korarku zanyi yau,yau dinnan bazaku dada kwanarmin agidaba dukanku se na kulleku kuje kuyi tinani ku fitomin da ita kannaje nadawo
Gida yatafi wajan su hajiya Fatima ko sallama beyiba yabanko dagudu Yana dube dube kamar me neman wani abin daga hajiya Fatima har baffah babu wanda yai Mai mgn yisukayi kamar Basu ganshiba dakunan gidan yahau dubawa be gantaba falo yadawo wajan su baffah yazauna yakwanta Kan goguwar kujera yarike kansa yarufe Ido kamar me bacci shi yasan meyake damunsa ga wani ciwankai da zazzabi me zafi na damunsa
Baffah ne yace nabil yau ko mgn Babu bare gaisuwa Ina matar taka
Nabil besan sanda yatashi zauneba Yana kallan baffah
Baffah yace ko dai baka da lfyne
Nabil yace lfyta kalau Daman batazo nanba
Hajiya Fatima tace wacece kake tambaya
Yace aa ba mgn nayiba
Komawa yayi yakwanta
Yace mommy a Ina tsohuwar Nan ta kwana
Kafin tabashi amsa sega iya tashigo
Iya naganin nabil tace me zamanman wando Ina shatuwa ko kakuma karyata ko baka,jina Kai min shuru
Ido nabil yabude suka hada Ido da iya batasan lokacin da taja bayaba
Tace nashiga uku Ni Aisha kuga idan mutun kamar gauta ko dai kakuma balballata Ina Nan bansaniba
Tashi yayi Yana hada hanya yai dakin da iya ta kwana nanma bega shatuwa ba dakin minister yatafi ya kwanta daga yarufe Ido se yaga shatuwa gashi San ganinta yake yarasa me yasa ga zazzabi yatakura Masa se rawar sanyi yake
Hajiya Fatima ce tashigo taga halin da yake ciki tace nabil baka da lfy bayannan Kuma da abinda ke damunka ka fadamin
Yace bakomai mommy kawai dai bani da lfyne
Tace to Alllah yabaka lfy Bari na kawoma magani tafice
Mgn nabil yahauyi shikadai kamar Mara hankali to Wai Ina taje ko an sacetane to ai babu Wanda yashigo gidana Kuma anty Amina tayi tafiya baza Kuma su tafi tareba tinda kwas mijinta zeje yi Kuma ai baffah da matsifanfiyar tsohuwar Nan baza su Bari atafi da itaba to yaushema Yar Kauye irin wannan zataje America ai ko jirgi Bata iya hawaba to waima meye nawa in tabata ba na hutaba da jarabar ta da ta wannan tsohuwar to Wai meyasa nake ta ganinta in narufe Ido ko Dan ta dalilinta naji saukin ciwan marata jiya Kai nabil manta kawai macacefa Kuma nafa tsaneta Wai meyasa naje nahada jikina da ita kazama Yar Kauye irinta tsaki yajah me karfi
Hajiya Fatima ce tadawo
Bashi magani tace Kai dawa naji kana ta mgn ko dai kun dada halinne Wai Ina shatuwa ana ta tambayarka kayiwa mutane shuru
Yace tana gida na barota
Mgni tabashi yasha bacine ya kwasheshi acikin baccin Yana ta mafarkin shatuwa da Kuma garar da yasha awajanta jiya kusan rabin baccin du mafarkinta yake
Iya da baffah sun koma mazagai Dakar aka lanlabata takoma da cewa tayi se taje tayiwa shatuwa sallama Kuma akwai nasihar da ta manta batai mataba
Shatuwa bakin America Tasha jinyar barnar da nabil yai Mata se da tawarke sosai Amina tasata amakaranta saboda shatuwa na da kokari Kuma Babu lefi tana ganewa turancine ake fama da ita in anyimata Bata gane wani abin in angaya,Mata da turanci se ta dawo gida take tambayar Amina me ake nufi da kalma kaza da turanci in Amina tabata amsa to tarike kenan karatu kuwa tana ganewa tamurje tadada fari sosai in ba ka santaba bazaka gane taba Amina tayi kokari sosai wajan dada wayar da ita yanzu shatuwa tazama Yar birni Kuma Yargayu acikin wata ukun da sukayi tsokanar da akasan shatuwa da ita yanzu du babu tazama saliha kamar ba itaba yanzu Abu dayane yake damun shatuwa da Amina ta kula dashi tana yawan tinani kome take lokaci daya zatai shuru ko mgn ake Mata bazata baka amsaba Amina tayi Mata tambayar duniyarnan meke damunta se tace Babu komai
Yau Amina nazaune adaki tana shayar da yarta shatuwa tashigo ta sameta tazauna kusa da ita Amina tace yadai kanwata Naga kamar da mgn abakinki
Shatuwa tace Daman tambayarki nazo nayi Dan Allah in mutun koyaushe na yawan se Tai shuru ta sunkuyar da kai
Amina tace cigaba Mana kanwata Ina jinki meye abin Jin kunya nifa Yar uwarkice
Shatuwa tace to anty in mutun nayawan tinanin mutun mekenan kamar Wanda kasani Kuma abokin fadanka Kai tayawan tinaninsa ko in kana bacci Kai ta mafarkinsa
Amina tace kafara damuwa dashi Kenan Kuma yanzu kana sanshi kekuwa kanwata meyasa kikemin wannan tambayar ko tinanin gida da su iya kikeyi
Ido tarufe tana dariya tace to anty bayan su mommy Kuna waya da su iya dah takuma,sa dariya
Amina dariya take ta dannewa Dan tagama ganota yitayi Bata gane me take nufiba tace karasa tambayarki du Zan Baki amsa
Kuna waya da Yaya nabil
Amina tace eh to muna waya da kowa Amma nabil gaskiya ba sosaiba iyama bama waya da ita
Shatuwa tace to in kunyi waya dashi Yana tambayarki yanake ko Ina nake ko bayayi
Tace aa gaskiya bayayi Kuma ai besan na taho da keba bemasan kina nanba
Hawayene yafara zuba daga idanta
.Amina tace menai Miki kanwata ko na Bata Miki Rai ban saniba
Tace aa abinne yabani haushi Ni fa anty kullin shi nake ta tinani ko bacci nake tinaninshi nakeyi yanzufa San ganinshi nake Amma shi be tabama tambayarki ko Ina nanba Daman anty besan kin taho daniba Kuma in yashiga wani halifa Kuma fa mijinane ai bebarniba muka taho Kuma kece memin waazi Akan hakkin miji kumafa kinsan iya wlh damunshi zatayi akaina in tazo Bata ganniba
Hamdalah Amina tafara tana murna tace to akwai dalilin da yasa muka taho dake se nangaba Zaki gane me ake nufi harshi nabil din Kuma mgnar fadan da kukefa yanzu nasan muna komawa zakuci gaba da abinda kuke Kuna rabawa kanku abin kunya agaban mutane ai basan junanku kukeba Kinga kuwa ai yanzu hankalinki kema akwance yake anraboki da abokin fadanka ko
Tace aa wlh ai Ni nadena fada Kuma ko me yaimin bazan Kuma kulashiba ai kinmin fada ga Kuma waazi inaji Akan Mata tabi mijinta sau da kafa in tayi zata shiga aljanna ai shima nasan yanzu yadena gakuma iya inasan naganta anty mu koma gida Dan Allah
Amina tace to kanwata karki damu munkusa komawa insha allahu komai yazo karshe ammafa naji Dadi ashedai anasan Dankanin nawa kanwata na San mijinta tanasan ganinshi
Dariya shatuwa tasa tazuba dagudu tafice daga dakin tanajin kunya
Amina Kiran hajiya Fatima tayi awaya tabata labarin yanda sukayi da shatuwa itama hajiya Fatima tabata labirin halin da nabil yake ciki dukansu sunyi farin ciki sosai
Nabil tin Yana boye batan shatuwa yanzu yakasa boyewa gashi yazu tinani yamasa yawa har Rama yafara yarage walwalar da yakeyi da ko fita yanzu bayayi sosai se dai yaje dakin shatuwa yakwanta in Kuma yagaji da kwanciyar yatafi wajan hajiya Fatima yau wajan hajiya Fatima yaje yasamu kuwa babansa minister nanan suna hira
Da sallama yashiga zuwa yayi yafada jikin minister yafashe da kuka me karfi yace daddy Kai da mommy ku temakeni tinaninta ze kasheni wlh Santa nake na Dena du abinda bakwaso in dai za a dawomin da ita mundena fada naje na roki baffah yace bemasan da batan shatuwa ba Kuma Allah yanzu inaga dasa hannunshi yasan inda take Ni har mommy ban yarda da itaba
Minister rudewa yayi yace alhamdulillah Allah na godemaka da kabawa nabil matar da yakeso ba wannan mahau
Kafin yakarasa nabil yarufe Masa Baki
Yace karka karasa daddy wlh bazan iya jure Jin ana zagintaba wlh Ni matata ba mahaukaciya bace da hankalinta nifa daddy ba wata matar auren da nasamo matata nake nufi Wanda baffah ya auramin Dan Allah gobe muje mazagai tare mubawa baffah hakuri ya dawomin da matata har in Kuma yaki mommy ma Taki to wlh se na Nemo gidan iya masifa na fada Mata anbatar Mata da jikarta Kuma bawasu bane su baffah ne ai nasan in taji masifarta,ma kadai ta Isa su dawo da ita Dan itama tanasan jikarta sosai
Minister Baki yasaki Yana kallan nabil bemasan sanda ya sauko daga Kan kujera yazauna akasaba Baki narawa yace nabil kakuwa San mekake fada kuwa ko dai da gaske kaima kabi layin Yan shaye,shaye abokanka inkuma ba hakaba to tsohuwar Nan da jikarta sun maka wani mugun abin sun kaika an haukatama zuciya akansu shikenan baffah zamu rasa nabil ai Dole naje har gida na ci mutuncin tsohuwa iya
Nabil yace wlh daddy karma kafara inhar kana sona to karka yiwa iya komai Dan ran shatuwa ze baci intaji Kuma zata dada guduna Nima Kuma yanzu inasan iya kome zatai min bazan kulataba Nima kakatace nidai abinda nakeso da Kai ka tayani Nemo shatuwa mukuma je mubawa iya hakuri mubawa baffah hakuri mukuma bazama neman matata adu inda take aduniyarnan
MINISTER wani gumine yake ta keto Masa duda sanyin esin da ke wajan zare Ido kawai minister yake tayi Yana kallan nabil
Me hajiya Fatima zatayi inba dariyaba har da rike ciki tasaki Buda tace Allah ngdma ranar muke jira yau gashi tazo Allah karabamu da abin kunya ko wana irine Naga yanda zaayi wajan zuwa gurin iya ba da hakuri da wajan baffah da alhaji yanzu Dan Allah bakaji kunyaba tin ba a je ko inaba ai ga abinda muke ta fadamaka Ni da baffah gashi kashiga fadansu yanzu zaka dawo kaji kunya gashi dai yaro yadawo yace yanasan matarsa saura iya ita Kuma zamuga yazatayi garama ita tsohuwace akwai shiruftun tsufa Kai kuwafa ai Babu wani tsufa da kayi Allah kadawo da shatuwa lfy muyi kallo muna daga gefe yanzufa tinda kana san danka seka Rakashi neman shatuwa da bawa iya da baffah hakuri du kuma se kamanta abin kunyar da kayi nasan yanda San nabil yarufema Ido ko cewa yayi kabawa shatuwa hakuri Bata zakayi ko to karma ku sakoni Dan bansan komaiba Akan batan shatuwa shine mijinta shi zefi kowa sanin inda matarsa take to mawai yaushe ta Bata ai kullin in yazo se na tambayeshi ya matarsa se yace lfy take har sako nake bashi yakai Mata du wayake kaiwa
Nabil zuwa gaban hajiya Fatima yayi yace mommy Haka mukayi da ke kinface kema kina Sona Dan Allah in kinsan inda matata take ki fadamin ko wani abinda na keyine bataso du ki fadamin wlh Zan Dena
shi dai minister har yanzo kallan nabil yake ko hajiya Fatima yakasa bawa amsa
Hajiya Fatima tace gaskiya abubuwa da dama bataso kakeyinsu Kuma ta fadamin Allah sarki har kuka take abin tausayi ko akansu ta guduma Allah masani Kuma ai badan Allah zaka denaba kaga Kenan in kaganta ta dawo zaka koma ruwa kaci gaba da halinka da bataso Kuma dada guduwa zatayi
Jiki na Bari yace wlh mommy nayiwa Allah alkawari Zan Dena danshi badan itaba tinda du kema kin fadamin Babu Kyau abinda nakeyi kecefa abokiyar shawararta kibani shawarar yazanyi na gyara ammafa wlh ko Ina iya take Sena Nemo gidanta na fada Mata halin da ake ciki dan itama ta Hura muku wuta kufito Mana da ita aini yau masifar iya ikwan Allah zata yimin Rana Kuma yanzu ita zanna gani inajin Dadi azaman shatuwa kafin aganta
MINISTER hannu binbiyu yasa yai tagumi Yana Jin ikwan Allah
Hajiya Fatima in takalli minister taga yanda yake ta raba Ido ga gumi na ta keto Masa dariyace take dada kamata Babu halin yi saboda nabil Kar yaga tana ta dariya yadau du maganganunta azaman Wasa ko yaudara zega Kuma tasan inda shatuwa take Dan Haka ta hade Rai ta nuna batasan komaiba
Tace Ni yanzu nabil azamana na mahaifinyar,ka Kuma me baka shawara Zan baka wasu shawarwari da zasu anfaneka Amma seni da Kai
Nabil yace mommy Ni yanzu nakeso muyu mgnar muje ko dakin,kine
Tace to tashi muje
Nabil yace daddy muna zuwa kaima da mgnar da zamuyi da Kai Kuma gobe kashirya mazagai zamu tare wajan iya da baffah
Hajiya Fatima da nabil daki suka shiga bayan sun zauna
Tace nabil shawarar da zan baka itace ka koma isilamiya cikin biyu ayi Daya ko anemo maka malami Yana koyamaka karatu agida ko kashiga ta malam liman da ke unguwarnan daga magariba ne da Isha akwai Kuma na bayan sallar Isha zuwa karfe goma nadare kazabi Daya kana zuwa karkayi girman Kai ko wata kunya Babu kunya wajan neman ilimi daga Ni har shatuwa bamasan halayanka da kakeyi nafarko maganar Yan aikin gidannan kacire musu dokar in sun ganka suna durkusawa har se kabar wajan kacire wannan dokar in sun ganka Kuna gaisawa cikin mutunci da girmamawa Amma Banda wannan durkusan har kasa Babu Kai Babu Kuma korar wani Dan aiki dake gidannan ko karkashinka Kuma wayanda ka Kora ada ko kabatawa Rai a Yan aiki du kabisu kabasu hakuri Wanda kaga yadace kayiwa alheri kayi Masa se maganar gudu da mota atiti babushi yanzu kudena Kai da yaranka kudena daukan hakkin talakawa Kai da su yanzu se girmamawa da Basu sadaka Kuma wannan kudin da kake rabawa abokanka suna aikata sabon Allah da kudin kadena ka koma rabawa talakawa maganar Jin kide kide du kadena ko karage ka koma Jin karatun Qur'an zuciyarka zatai sanyi zaka rage zafin zuciyar da kake dashi du in kashiga isilamiya zakaji waazi akai Kai abubuwa da dama insha Allahu du Zan na fadama ahankali kadaure kadena kazama me adalli da hakuri ga kowa kaji nabil kakoma mutunta Mata da darajasu kadena cewa ka tsanesu
Yace to mommy du naji Kuma zanyi isilamiyar ta malam liman zan shiga nafi karuwa da wasu abubuwan sosai
Tace yauwa nabil Allah yaimaka albarka
Nabil yaji mgnar hajiya Fatima yafara zuwa isilamiya hajiya Fatima da kanta taje har gidan malam liman Tai Mai bayani Akan nabil zefara zuwa isilamiyarsa ta maza magidanta da matasa Tai Mai bayani halin da nabil yake ciki Kuma Yana yawan temakawa da yawan yin waazi Akan zamantakewar Dan Adam ko malam liman yaji Dadi da Jin bayanin hajiya Fatima Akan nabil
ranar da taje ranar nabil yafara zuwa da magariba
hajiya Fatima taji Dadi sosai yanda taga nabil yafara canja halayansa ko Jin Waka yarage sawa yanzu ko abokansa basosai yake shiga harkarsuba har gida suke zuwa nemansa Amma Haka zasu hakura sukoma jiki bakwari gashi yanzu yarage yiwa abokan nasa bushaSha kamar da ko yajema baya Basu komai baya Kuma dadewa Yan aikin gidansu kuwa sunsamu yancin kansu Babu takura tsakaninsu da nabil Babu durkusawa har kasa ga kyauta da yake ta yawan yimusu kowa yaga canji Akan nabil mutanan garima sun sheda canjawar nabi almajirai in yafita Haka yake raba musu sadaka Dan Allah yadawo Masa da shatuwa lfy wayanda da ko almajirai bayasan ganinsu karatu kuwa alhamdulillah Yana fahimta sosai daga anbiya Masa zerike ga yawan waazi da malam liman yake tayi Kuma Yana shiga kunnan nabil sosai Kuma Yana anfani dashi motocinsu yanzu in sun taho ako Ina memakwan kade,Kaden da akeji da amotocin yanzu kuwa karatun Qur'an akeji natashi in adaki yake ko afalo abin da yake sawa Kenan karatun Qur'an ko gudu da motoci in Yana ciki yanzu andena yanzu kowa yaban nabil yake da samasa albarka ko sarkokin da yake sawa da irin shigar da yakeyi da su fentin kansa yanzu du yadena zarya kuwa amazagai Babu adadi wajan baffah Akan ya temaka ya dawo Masa da shatuwa ga ciwan mararshi yatashi sosai saboda yawan tinanin shatuwa da tinanin garar da yakwasa awajanta hajiya Fatima yanzu tafara tausayin nabil garama yayi sosai yakoma shuru shuru Babu wannan zafin ran da akasansa dashi
da nabil yaga baffah baze bashi amsaba Akan shatuwa Kuma baze dawo da itaba yayanke shawara ko baffah be saniba bare minister yaje ya Nemo gidan iya bakaramin rashin mutunci iya Tai masaba Amma be amsa mataba wajema yanema yazauna Babu korar da batai Masaba Akan yafice Mata daga gida nabil ko akansa yaki kulata Kuma yaki tafiya Dole ta sauko ta saurareshi aikuwa nabil Nagama fada Mata halin da akeciki Tai tsalle ta dire tace batasan zanceba tahau kuka wiwi Akan se annemo Mata shatuwa nabil da yaga haka yai ta tunzurata tana dada Hawa shima har da tayata kuka su baffah sun batar musu da shatuwa
Iya tace Ashe dandaudu me zamanman wando zaka canja kazama mekirki haka har kafara San shatuwa kaima Ashe dai kaima kyakkyawane haka kaboye kyan da Allah yai maka ka koma kamar matamaza nifa da kashigo ban ganekaba se da umaru yai min bayani yace Kaine tukunna na ganeka aiyanzu Kuma Ni da Kai Babu fada munshirya tinda kanasan shatuwata saura Miss Miss Shi,ai wannan uban naka bashi da mutunci baze Dena abinda yakeba Aishi basan shatuwa yakeba Kuma nasan be damuba da batan shatuwa kabarni dshi du zamu hadu Daman da tamu dashi yanzu dai katashi mutafi wajan usuman naji inda yakai Mana ita Kai Dan Miss Miss ka fadamin gaskiya ko dai ubanka Miss Miss yasai da shatuwa bamu saniba takuma fashewa da kuka Ni wlh da magunan yace na kawo Masa wlh Zan kawo Masa ba se yasai da shatuwa ba kumafa agabanka har alkawari naimai in yafara mutunci Zan tara Masa maguna na kawo Masa har gida takuma fashewa da wani kukan
Nabil du dadamuwar da yake ciki se da yafara dariyar maganar iya Yana mamakin karfin Hali irin nata agabansa tana zagemai uba
yanzu damuwa taiwa minister yawa saboda ganin halin da nabil keciki na damuwa gashi minister najin kunyar zuwa wajan baffah yabashi hakuri akan batan shatuwa haka Dole yacire kunya yaje har gida yasamu baffah yabashi hakuri Kuma ya rokeshi Akan Dan Allah in yasan inda shatuwa take ya dawowa da nabil ita
baffah dariya shima yafara Yana kallan minister
Baffah yace Kai sani ko dai mafarki kakeyi ko da yake ai ba kunyace da kaiba in dai Akan nabil ne komai ma zaka iya kaga abinda nake gayama Kenan yanzu gashi yadawo San matarsa Yana ta nemanta yashiga damuwa gashi kaima kadamu kazo kana tayashi neman matarsa Amma da idanka yarufe kadinga rashin mutunci da abin kunya yanzu kaima cewa zakayi ka goyi bayan auran shatuwa da nabil ko Dan baka da kunya kariga du kagama zubar da girmanka na uba a idan shatuwa yanzu ai kadada hankali kakuma dau darasi Akan abinda yafaru Nan gaba San nabil yakuma rufema Ido wlh Fatimace me San nabil bakaiba yanzufa ko shuryuwar nabil baka saniba Ni nasani baka da lokacin tarbiyarsa se ta munamai gata yanzu da ba Fatima mahaifiyarsa da kacuci nabil har karshan rayuwarsa tashi kabani waje se nayi shawara Akan mgnarka
Haka minister yadawo Abuja jiki Babu kwari
Iya ce da nabil sukazo har gida wajan baffah Kan mgnar shatuwa iya nazuwa tafashewa baffah da kuka tana ruwan masifa yafito Mata da shatuwa Dan Miss ne yazo yagaya Mata shatuwa tabata Kuma yasan komai har da hajiya Fatima nabil na gefe Yana Jin Dadi tinda iya tasa Baki fole afito Masa da matarsa
Baffah hararar nabil yahauyi yace to kaji Dadi ka fado Mata hankalinka se yakwanta Mara kunya Daman matar taka tana da Rana haka ban saniba ai da cewa kayi baka Santa ko kamanta na tinama to inkai yanzu kana santa itakuma in tace Bata Sanka Naga yanda zakayi Dole ai ka saketa
Kunne nabil yatoshe yace bazan iyaba wlh Babu saki Ni da ita Kuma jikina yabani itama yanzu tana sona Dan Allah ka dawomin da matata baffah wlh ba nabil din da kasani bane da
Baffah yace bani da lokacinka se kutashi mutafi Abuja wajan Fatima tinda yau in Allah Yayarda komai zezo karshe kabar mutane su huta da Kai da kakar taka Wai iya yaushe Kuma nabil yazama jikanki kuma kuka Dena fada
Tace ai yanzu mun shirya Kuma shinake gani azaman shatuwa tinda kun batarmin da shatuwa Kuma shi ne mijinta Ashe Dan Miss Miss na da kirki Haka ban saniba bakaga yanda yake yomin siyaiyaba har kudi yake bani su umaru ma hidima yake Tai musu Ashe yafi ubansa miss miss kirki tasa kuka
Shi nabil yanzu kome iya zatace akansa shi da ubansa baya Jin haushi dariyama take bashi
Baffah da su iya Abuja suka tafi sun Isa lfy minister nagida se ganin baffah da nabil da iya yagani nabil na rime da faggwan kayanta suka shigo
iya Kai tsaye wajan minister taje ta zauna kusa dashi tace to miss miss Allah yadawo Dani Ina shatuwa Ina matar taka Fatima itama Ina Mata kallan me kirki Ashe ka goga Mata mugun halinka ko se wani hararata kake kana zaremin Ido du baze tsorataniba ka fitomin da jikata kawai inma magunan kakeso NASA umaru yatara maka yakawo maka kafito da shatuwa kafin inmaka rashin mutunci
Hajiya Fatima tace yihakuri iya kijira zuwa anjima Zan rakaki inda shatuwa take kici abinci ki huta tukunna kirabu da alhaji Ni da kaina Zan kaiki
yau su Amina zasu dawo gida nanjeria mijinta yagama kwas dinsa har ma kwanaki suka Kara bayan wata shidan da sukayi zokuga murna wajan shatuwa ga kiba tayi ga Kyau takara tadada fari sosai ga turanci tanaji yanzu sosai ga yanzu in anganta bazaace tayi rayuwar kauyeba misalin karfe takwas na dare jirginsu ya iso nanjeria hajiya Fatima ce tatura direba ya dauko Amina da shatuwa Kai tsaye gidan minister aka shige dasu shikuma mijin Amina da yaranta gida suka shige se Amina Taraka shatuwa zata shige gidan nata mijin
Lokacin da suka dawo nabil be dawo daga isilamiyaba iyace da minister da baffah kadai agida shatuwa da taga iya har da kuka iyama kuka tafafa tana mamakin girman shatuwa da kyan da takara iya bakin masifa yamutu se murna ake tayi jikalle tadawo
Tace Allah sarki nabilu Yana Ina yazo yaga shatuwa ta dawo yaro Dan albarka ai ingaya Miki Dan miss miss yajansa yanzu du baya masifar Nan da yakeyi
Takalli Amina kema yannan yar Ina yabanki sallah Zaki kasa alwala Ashe kema kinbi halin Miss Miss har dake asace shatuwa
Kafin Amina Tai mgn Sega nabil yashigo dauke da sallama abakinshi cikin nutsuwa yake tafiya gawani kamshin turaransa da yacika wajan kansa akasa yashigo bema kula da suwaye afalanba shatuwa Ido takura Masa tashi tayi tsaye tana kallanshi Yana dago Kai sukai Ido hudu da juna
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama*❤👸
*'YAR KWALLIYA*🥳💃
👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠
👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠
👝👝👝👝
👠👠👠
👝👝
👠
💄💅 *DAN MINISTER* 💅💄
🦚🦚
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@ Real Husba'ahfama*
15-16
Ido suka hau mustsikawa suna dada kallan juna
nabil yace ko dai mafarki nakene ban saniba
Shatuwa itama wajan Amina takoma da sauri tace anty Yaya nabil ne wannan Naga Babu shigar da yakeyi ajikinshi ko sarkar Babu
Dariya dukansu suke musu Amina tace nabil ne shatuwa Kinga yacanja ko
Tace eh anty
Rada akunne Amina takewa shatuwa kardai kimanta da du abinda nagaya Miki kifaja ajinki kafin ki saki jiki dashi Amma Naga ke kanki rawa yake niyar ba da kanki kikeyi ke ko Ina se kin nuna wautarki ta ke rikwan kakace
Kafin shatuwa tayi mgn
Nabil yakaraso wajan shatuwa yasa hannu yatabata yaji dagaske itace ba mafarki yakeba hannu yabude almar tazo shatuwa Amina takalla taga Amina na harararta ai shatuwa Bata da mu da gargadin da Amina take mata da Ido na taja ajinta taje da sauri tafada jikinshi suka rungume juna suna dariya
Nabil yace Aisha ina Kika shiga nake ta nemanki meyasa Kika gujeni kinsan wuyar da nasha akanki kinsan halin da nake ciki saboda rashinki Ina kikaje du tsawan wannan lokacin nake ta nemanki waye yasaceki
Shatuwa tace ba anty Amina bace ta daukeni ta gudu Dani america baffah da mommy ne suka sata ta gudu Dani Wai Dan muna fada Ni da kai yanzuma se da taga nayi fishi da ita na dameta da kuka sannan tadawo Dani har cemata nayi yanzu mungirma mundena fada Ni da Kai Amma anty Amina Bata yardaba har da yimin fada tafashe da kuka
Amina hanu tadora aka tazamo daga Kan kujera ta zauna akasa tace shikenan angudu ba a tsiraba goyan Kaka Kenan akwai wauta daga temako se yazama lefi
Nabil ransa yabaci kallan su amina yafara Yana rungume da shatuwa Yana rarrashinta yace yanzu Ashe Daman du rokwan da nake Tai muku kunsan Inda matata take kukaki ku temakeni ku dawo min da ita se da itama ta dameku tukunna kuka dawo da ita anty Amina meyasa kikai Mana Haka kinsan halin da Dan uwanki yashiga akan hakan da kikayi baffah har da Kai mommy kema haka wlh daga yau Kar Wanda yakara dauke min Mata ba da saniba Allah bazan yardaba yishuru aishata gidanmu zamu tafi yanzu rabu dasu daga yau Kar wanda yakuma zuwa yace kizo kuje wani wajan ba da saninaba karki Kuma yarda kibi kowa kinji
Tace to Kuma ai kace katsani Mata baka sansu Kuma Nima kace baka Sona Ni bazan bika gidan kaba bayan baka Sona Kuma bakasan Mata Ni awajan mommy Zan zauna ko anty Amina ko nabi iya mutafi mazagai tare
Muryar nabil narawa yace haba Aisha kuskurene ko Ada da nake fada rashin sanine Amma yanzu nagane gaskiya wlh yanzu nasan darajar Mata Kuma Ina girmamasu ako Ina suke ta dalilinki nasan darajar Mata aduniya nasan Kuma wacece mace kema wlh Ina sanki Aisha Ina kaunarki bazan iya rayuwa in Babu keba kin Zama wani bangare na jikina karki min Haka Dan Allah ki temakeni kiyarda mu tafi gida yanzu karkisa su baffah suyi Mana dariya daddy da iya kusa Baki ku tayani bawa Aisha bawa
Shatuwa tace Babu ruwansu wannan tsakaninmune Suma ai shedane agabansu kasha fada baka San Mata ba sau dayaba ba sau biyuba
Kwacewa tayi daga jikinshi ta haura sama da gudu tana kuka aminace tabi bayanta da sauri nabil shima binsu zeyi
baffah ne ya hanashi binta yace nabil zauna muyi mgn da Kai Kar kadamu zamu tayaka Bata hakuri zata hakura katsaya yanzu muyi mgn dakai kasan shatuwa na da gaskiya ko tinda kowa yasan akidarka takin du wata mace arayuwarka Kuma daga Kai har ita kunsha fada a gabanmu kun tsani junanku Dan Haka muma muka rabaku muka dauke shatuwa ka Dena ganinta Kuma mu munzata temakwanka mukayi tinda bakasan Mata itama baka Santa Kuma nine jagoran aurama ita tinda itama tana tsoran dokarka takin mata kawai kasaketa mukoma da ita mazagai inda tafi wayo nasamu wani me Santa na auramai
Setin zuciyarshi nabil yadafe da hannu yanamai da numfashi Dakar yace Dan Allah baffah kabar wannan mgnar wlh ko amafarki bazan iya sakin Aisha ba bare da hankalina yanzu ko da tsautsayine da Kuma rashin sani Amma yanzu wlh nadena bazan kumaba Kar ka rabamu muna kaunar junanmu ko itama tana sona tana dai tsoran akidatane na kin Mata Kuma yanzu na Dena itama Kuma wlh Ina Santa in karabamu mutuwa zanyi rayuwata takare kunrasani kenan
kuka yafara kamar wani karamin yaro idanunshi na kakkafewa Yana neman sume musu
Ai minister besan sanda yaganshi gaban nabil yadagoshi Yana jinjigashi Yana Kiran sunanshi karka mutu nabil anbarma shatuwa indai itace farin cikinka shatuwa takace Babu me rabaku Nima Ina tayaka San matarka bazan Bari arabakuba ko da abinda na malkaka aduniya ze Kare Akan abarma shatuwa wlh du Zan bayar in kamutu Ni Kuma yazanyi baffah Dan Allah kayi hakuri kacire mgnar rabuwa tinda yagane gaskiya Nima Kuma nagane gaskiya na baka hakuri Dan Allah kayafe Mana daga Ni har nabil iya kisa Baki za a raba shatuwa da nabil kina kallo kinki cewa komai Fatima kiyiwa baffah mgn zamu rasa danmu shatuwa kizo kiga halin da mijinki yake ciki baffah ze rabaku kizo kice kema kina sanshi Dan Allah kiyi hakuri da du abinda yafaru abaya kiso mijinki
Iya sarkin kuka tace rabu dasu Miss Miss aidu jinshi nake Babu wani rabasu da za a yi ainima Ina da hakki akansu tinda jikokinane wlh bazan Yarda arabasuba Dan Miss Miss tashi kaji nabaka shatuwa har abada takace rabu da usuman ai kana da kirki yanzu Nima Ina sanka saura miss miss Naga shima yadan Fara mutunci tashi kayi hakuri anfasa rabaku Fatima mikomin ruwa mesanyi nabashi yasha ko giyarku ta yanbirni me sanyinnan tsiyayo akofi na duramasa abaki yasha wajan kunfa,kunfar Nan Zaki zubo zatafi rike Masa ciki
Hajiya Fatima tace to iya ikwan Allah ko Yaya se kinsa mutane dariya har da giyar Yan birni me kunfa Kuna shaaninku ke da alhaji kunyi amanku kun lashe kuku kadai su alhaji an saduda anga dangwal zemutu har da bawa shatuwa hakuri tatafi tana dariya
Ruwa me sanyi takawo hade da lemon da iya tace ruwan aka Fara shafamai afuska akabashi wani yasha Yana bude Ido wajan baffah yatashi yaje da rarrafe kamar wani yaro saboda jikinshi Babu kwari yakwanta Akan kafarsa yaishuru Yana Mai da numfashi saboda mgnar ma inyayi kirjinshi ciwo yake Daman Kuma bawata lfyce da Shiba du yawan tinanin shatuwa yasashi rashin lfy
Baffah kansa yahau shafawa da hannu yace Allah yaimaka albarka nabil yanzu na yarda kana san shatuwa Kuma zaka riketa Amana daga Kai har sani yanzu na yarda da ku alhamdulillah burinmu yacika na ganin kun shiryu ka kwantar da hankalinka Ni bazan rabaku da shatuwa ba tinda kana santa gatanan Amana nabaka ita ka riketa hannu binbiyu kabawa marada kunya kanunawa duniya mace Yar gatace awajanka Kuma Mata abin darajawane da girmamawa aduniya da idan kowa dadu wani da namiji kadau matarka kutafi gida Allah yabaku zaman lfy Allah yabaku zuria tagari je kakirata kutafi kayi hakuri da dauke maka Mata da mukayi baka saniba
Murna nabil yafara har da rungume baffah Yana ta godiya minister ma Babu kunya yake tayiwa baffah godiya Yana murna iya se washe Baki ake ana hawaye tana taunar goranta
Amina da tabi shatuwa daki duka takaiwa shatuwa abaya tana dariya tace Ashe kina da hankali kanwata aini nazata shirme zakimin Akan yanda natsara Miki Ashe kina sane adai tausayawa Dan uwana Dan Naga yagama macewa Akan sanki kema Kuma nasan kina san Dan kaninnawa ai da bakibi abinda natsara mikiba da munbata da ke
Shatuwa zatayi mgn Kenan nabil yaturo kofa yashigo kallan Amina yafara yace nifa wlh anty tsoranki nake yanzu tinda Kika sacemin Mata Kuma yanzu tsoran ganinku tare da aisha Zan dinga ji Dan Nagano yanzu kece malamarta itakuma dalibarki to malama ayi hakuri Zan tafi da matata gida tahuta tagaji sosai tanasan hutu duda kinmin lefi Dole nai Miki godiya Yar uwata ngd Allah yabiyaki anty Amina da gudun mawar da Kika bada baffah da mommy sun yimin bayani du abinda yafaru Kuma nagane
Amina nasiha takuma yimusu sosai meratsa jiki tace Ni zantafi kanwata se yaushe ko se naganki
Kai shatuwa ta daga Mata tasa hannu tarufe idanta tana dariya
Amina tace ai nasan amsar da zan samu Kenan awajanki kanwata zuwa gobe zansa akawo Miki kayanyakinki har abincin safe du zansa akawo muku asha soyaiya lfy Ni natafi wajan nawa mijin nabarshi shikadai agida tafice tana dariya
Amina nafita nabil yatako zuwa gaban shatuwa Ido yakura Mata Yana murmushi itakuma Kai ta sunkuyar kasa takasa had a Ido dashi wani kwarjini taga yayi Mata yacika Mata Ido
Yace Aishata babu mgn amaryar nabil jikokin iya ikwan Allah ko bakiyi murnar ganinaba har yanzu fishi kike Dani Baki huceba nasan namiki lefi ranar da zamu rabu Dan Allah kiyi hakuri ko temaka Miki banyiba
Kai tadago tana kallanshi fadawa tayi jikinshi tarungumeshi tafara mgn ahankali tace Ni Babu lefin da kai min ai hakkinkane mijina lefinka dayane zuwa biyu awajena kabini da mugunta ranar baka ragaminba katashi ka tsallakeni bakaji tausayinaba ko temakona bakayiba wannanne kadai yatsayemin araina Dan Haka na dada yarda baka Sona Kuma Dan katsani Mata kai min Haka Kuma bakaga wuyar da nashaba nadade Ina jinya saboda da Kai takara mgnar cikin shagwaba da kukan kissa
Dada birkita nabil tayi lokaci guda yaji yashiga wani Hali mararshi yaji tafara murda Masa saboda yanda take dada shinshige Masa jiki ga shagwabarta dada rudashi take jiyayi kafafunshi bazasu iya tsayawaba janta yayi zuwa Kan gadan dakin suka zube bakinta yakamo yahada da nashi sun Dade ahaka sannan yabarta suna Mai da numfashi Dakar yafusgo mgnar bakinshi yafara mgn
Aisha nidai bazan gaji da Baki hakuriba yanzu tinda Allah yadawo min dake lfy zakiga irin kaunar da Zan nuna Miki da gata da kulawa se kin manta kowa kin kuma yarda nabil masoyinkine na gaskiya kinji amaryata yasumbaci goshinta tashi mutafi gida kihuta kintafi kinbar mijinki da ciwanshi me wahalar dashi kin lasawa mijinki Zuma me Dadi kin dada jefashi agogin bege sefa kinyi hakuri da Ni aisha Dan mijinki jarimine ba rago bane
Ita Bata gane me yake nufiba tana kwance Akan girjinsa se shakar kamshin jikinsa take dagota yayi suka tashi tsaye kansa tahau kalla tana dariya tsalle tayi ta shafo gashin kansa taduba hannunta taga bakomai dariya tasa tace ai nazata bakin fenti kakoma shafawa gashin Kan naka Ashe ainahin gashin kankane yanzu Yaya nabil yabar shigar Mata yadena sa fenti akansa wlh naji Dadi yayana Kuma mijina naji dadin canjawarka kamafi kyau yanzu wlh kamar bakaiba kakoma balarabe mijina yadena shigar Mata da zame wando
Murmushi yayi shima yace ko Ni yanzu wlh shigar Bata burgeni Kuma naji Dadi da denawata yafaranta ran matata aikema kin canja sosai my baby gashi har wannan kwalliyar ta Yan mazagai kin Dena kin koma Yar birni muje gida bacci nakeji kema nasan agajiye kike ga mijinki na neman temakwanki
Hannunta yakama suka sauko kasa suka samu su iya nahira afalo lokacin Amina tashige gida shatuwa se wani sunne Kai take abayan nabil
iya tace au Dan miss miss Daman Kuna ciki tindazu ai munzata kun tafi Kai Dan miss miss ka kwacemin shatuwa kaga ko takaina batayi ta mijinta take
Dariya hajiya Fatima tayi tace ai iya sedai kiyi hakuri nabil yakwace Miki shatuwa mijinta zatabi shatuwa Kuma ta kwacewa alhaji nabil
Dariya minister yayi yace ai nayarda Ni shedane nabil yazama na shatuwa Kuma jikan iya
dariya kowa yasa nabil yace Dan Allah su baffah kuyiwa iya mgn tadena kirana da Dan miss miss daddy Kuma Wai miss miss take kiranshi nace Mata bahaka ake fadaba Taki yarda nace in Bata iya kiraba takirani da ainahin sunana nabil shima din da tatashi Kira se da tabata sunan Wai nabilu se kace wani tsoho kuma iya daga yau sunan matata Aisha kidena kiranta da wata Shatuwa nasoke wannan sunan daga yau
Iya tace ko sannu babana wlh baka isaba Shatuwa take Kuma Haka NASA Mata tin tana yarinya ban,yarda ana kiranta da aishaba kaima in nakiraka nabilu in kaki amsawa wlh Dan miss miss Zan kiraka dashi aikaine kakira kanka da sunan tin ranar da aka kawo Shatuwa gidannan Kuma naji mutane da yawa na kiranka da Dan miss miss shi Kuma ubanka Miss Miss ake kiranshi ko amazagai haka kowa yake cemasa ko bahakaba usuman
Baffah yai dariya yace hakane iya rabu dashi kowa yasanshi da Dan miss miss
Nabil hannun Shatuwa yakama yace zo mutafi Aisha baffah ma yakoma bin raayin iya su daddy se da safe mun tafi gida iya se goben in kinzo dada ganin gidanmu baffah Dan Allah karka tafi ban saniba
Ficewarsu sukayi zuwa gida Shatuwa se sunkuyar da Kai kasa ake ba bakin mgn
Iya tace a lanlai Shatuwa Dan Miss Miss ya fitsareki yakwace,minke da gaske ku ganifa ko akanta ba tadamu zata bishiba murnama Naga tanayi Kuma mun Dade bamu haduba ko tace aguna zata kwana tarufe Ido tabi mijinta ko kunya Babu ko sallama Babu se wani sunsunkuyar da Kai dake kasa kamar taiwa sarki karya zamu hadu gobene to Wai yaushema suka Fara San junansu Miss Miss ko kasani
Kunyace takama minister Dakyar yake mgn du kunyar hajiya Fatima da baffah yakeji yace Nima ban saniba iya loci Daya Naga sun kamu da San junansu musamman nabil kema shedace Kinga irin halin da yashiga da Babu Shatuwa se gashi Shatuwa itama tana San nabil nayi mamaki sosai da Haka yafaru iya Daman inaso nabaki hakuri Akan du abinda yafaru akan auran nabil da Shatuwa da rigingimun da mukayi abaya Dan Allah du amanta da komai yawuce yanzu mun Zama Daya mun koma Yan uwan juna Dan Allah kiyi hakuri Kuma tare zamu koma mazaigai naje har gida mu gaisa da mahaifin Shatuwa da mahaifiyarta nai musu godiya Kuma Suma yadace sozo suga gidan nibil da Shatuwa su samusu albarka baffah kaima bazan gaji da baka hakuriba Akan abinda yafaru abaya Mata tagari Fatima godiyata gareki se Ni dake nabiya Mana kujerar aikin hajji gada,dayanmu har da iyayan Shatuwa da kema iya har da su nabil du tare zamu tafi aikin hajjin bana shine tikwicina na auran nabil da Shatuwa
Godiya suke Kai Masa sosai iya har da kuka tace Allah sarki rayuwa daman akwai ranar da zanje maka Kuma ta dalilin Shatuwa da Dan miss miss nagode Allah yasaka da alheri Miss Miss ka gama,min komai arayuwata ta duniya wlh nahakura Akan abinda yafaru Nima kayi hakuri da abinda yafaru Ashe dai Miss Miss ana da kirki da mutunci ko kaifa ashedai Nima mukaminka na Kiran maguna agwaunati ze min Rana ban saniba gashi har maka kabiya Mana zamuje ai dole naci gaba da taramaka maguna wlh sunanan nasa anware wani kewaye agidan umaru Ina taramasu nasan wasuma yanzu Kan na koma gida sun haihu du se kataho da su in kaje in ka kaiwa gwaunati magunan tabiyaka kudinsu nabar maka Kai anfani da kudinka nakane Ni nabaka Ta fashewa da kuka
Hajiya Fatima da baffah me zasuyi in ba dariyaba shima minister dariya yake tayi
Hajiya Fatima tace iya me abin dariya aikuwa Dole Miss Miss in yaje yataho da magunan da Kika taramasa kije ki kwanta kihuta gobe se zuwa gidan su Shatuwa zaman daki ko kin fasa yimusu zaman daki
Baffah yace Kinga Fatima wlh karki zugota Kinga ta manta Kar azo tafiya tace Baza tatafiba kinsan rigimarta
Tashi kowa yayi zuwa bacci hajiya Fatima nashiga daki minister yabiyo bayanta yashigo dakin se jitayi anrungumota murmushi tayi tace miss miss abokin iya ikwan Allah sirikin Shatuwa uba awajan nabil
Yace hm aini Fatima yanzu bani da bakin mgn wlh kunyarki nakeji da ta baffah ga Shatuwa itama ko ya zata daukeni Fatima Allah yaimiki albarka ke Mata ta garice Kuma uwa tagari kinyi kokarin ganar Dani Akan abubuwa da dama Amma idona yarufe se yanzu Allah yaganar da Ni gaskiya wlh naji dadin yanda Naga nabil yacanja Kuma naji dadin yanda kowa ke yabansa mutane da dama na tarata su yimin godiya Akan abinda nabil yake musu na alheri Nima Naga canji ta yanda yanzu muke mgn dshi yanzu nabil har gaisheni yake har kasa Kuma yanzu Naga du yadena halayansa me kikeso nai Miki Dan na nuna Miki irin Jin dadin da nayi na kokarin doramu ahanya da kikayi kome kikeso ki fada zanmiki kishiya dai Babu ita Dan ke kadaice muradina bani da raayin Kara aure Kuma Ni yanzu mijin tacene ke Kan tacema du nine
Tace mijina Ni Kai nakeso da yarana kune abin Sona fatana Ni dai ka Dore abin haryar gaskiya daga Kai har yaranmu komai na jin dadin duniya ka wadatani dshi rokona Daya ka tayani gyara rayuwar nabil bisa hanya madaidaiciya da sauran Yan uwansa shine rokona agareka
Yace angama uwar gidana Kuma amaryata masoyiyata kome kikace shi zaayi
Dariya tasa tace alhaji Kenan munfa girma da wannan yanzu se saban jini su nabil da Shatuwa jikoki nawa yanzu muke dsu ai tsufa yakamamu
Yace bawani tsufa wlh se in kece Kika tsufa barima kigani
MINISTER yakoroni yahanani ganin komai 🤧🤧😜
Kafin su nabil su karasa gida se da suka ratsa yai Mata siyaiya me yawa yajido Mata Kaya kamar ba gobe daga naci har nasawa daganan gida suka shige motocinsu na tsayawa yaransa suka bude musu kofa suka fito agabansu beji kunyaba yarike Mata hannu dayaga bemasaba karata yayi da jikinsa yarungumeta da hannu daya kamar wani ze kwace Mai ita suka shige cikin gida
Me yaransa zasuyi inba dariyaba sukace oga mafa yabi hanya kuga Wanda kullin ikirarinsa yatsani du wata mace aduniya Amma yanzu shine me rawar jiki Akan mace bama yaso akallemai ita se wani haderai yake Yana wani kakkareta Dan Kar agane Masa Mata abinda yafi bamu dariya matar da aka dauramai ita dakyar akasha faman fada Akan auran Wai yanzu shine yadawo San matarsa itama kuga yanda take ta shinshige Masa sun dawo San junansu ai mu yanzu se godiyar Allah oganmu yadawo mutumin kirki munajin dadin aiki dashi
Daya daga cikinsu yace kunga mukwashi kayannan mushiga da su Kar oga yaji shuru mu batamasa Rai Kuma muma yafita namu hakkin yabamu kudi muyiwa namu matan siyaiya dadane ai oga baze bamuba
Su nabil nashiga falan gidansu daukan Shatuwa yayi kamar wata jaririyaba yai dakinshi da ita Akan gadan dakinsa ya kwantar da ita shima yabita yakwanta kurawa juna Ido sukai suna murmushi Shatuwa kasa daure kanlan da yake Mata tayi tasa hannunta duka biyun tarufe fuskarta dashi tana cigaba da murmushi
hannu nabil yasa yacire Mata hannayanta ya rungumeta yasumbaci lebenta yace karkimin Haka Aisha farin cikina Dan Allah kidena rufemin kyakkyawar fuskarnan Taki kinsan irin kewar da nayi Taki kuwa Aisha ban taba sanin Mata rahamaneba Kuma Ni,imane ku se ranar da nashiga kogin zumarki me tadi da ruda tinani tin daga ranar nagane darajar da kuke dashi awajanmu maza wanna ranar bazan taba mantawa da itaba takafa tarihi Bamba arayuwata Kuma wanna ranar tasani gyara abubuwa dadama arayuwata Kuma kikazo Kika gudu Kika barni kikabar mijinki da ciwanshi da yake damunshi kusan ko da yaushe Dan Allah karki Kara nesa da Ni Dan wlh bazan jureba kitashi muje muyi wanka nifa tare zamuyi kinji yakarasa maganar da shagwaba
Mgnar Amina tatina da take cemata sefa kinyi hakuri da mijinki Dan wlh shagwabanbene tin Yana yaro nasan Kuma yanzu tinda yayi nesa da daddy kece yanzu Wanda yafi kusanci da ke nasan ke ze dawo yiwa shagwaba memakwan ke kadai kina Masa shima yimiki zeyi shawarwarin da ta ringa Bata akanshi tatuna
Iska Taki anhura Mata a ido tadawo daga tinanin da takeyi tace nifa nayi wanka agidan mommy Kan na taho Dan agajiye muka dawo kasa daurewa nayi se da nayi wankana acan kaje kayi ai muna tare wataran nanan
Shuru yayi kome yatina seyai munshari yace to Bari Ni natashi naje nayi ni kadai tashi yayi yahau cire Kayan jikinshi Shatuwa naganin haka tatashi tafice zuwa dakinta da sauri
dariyama shi tama bashi yace yarinya Zama ki Dena Jin kunyata Danni tsarina da matata Babu Yar Jin kunya Dole Nagama ciremiki ita gabadaya Dan wlh cutarmu zatayi musamman Ni
Shatuwa nashiga daki tahau dariya tace Amma Yaya nabil dinnan bayajin kunya Ni mamaki yake tabani kamar bashine masifanfannanba me haderai Kuma Naga da Yana tare da yaransa hade Rai yayi yakoma yanda yake ada muna komowa daga Ni seshi se Kuma yasaki fuskarshi kamar bashiba
Tashi tayi tacanja Kaya tasa na bacci Tai du abinda yadace turaruka kuwa tayi barinsu ajikinta ba a mgn Dan Shatuwa baabociyar kamshice tanasan kamshi sosai ga Amina tinda suka je America Bata denawa Shatuwa gyare gyaren mu na mataba Dan gyaran da taiwa Shatuwa ko Babar Shatuwa se dai haka
tana gamawa kwanciyarta tayi Tai addu'a tatofe jikinta tahau baccinta tayi nisa abacci taji ana shafata ana Mata wasu salo ajiki tatsorata sosai Kara zata saki yai maza yahade bakinsu waje Daya sundade ahaka sannan yabarta
yace matsoraciya ninefa waye ze kwanta akusa da ke in baniba
tsorone yadada kamata yanda taji muryarshi tacanja jikinshi har rawa yake Yana dada hadata da jikinshi kamar za a kwacemai ita tsoro yakuma bata jikinta yahau rawa da tatuno da ranar da Tasha wuya awajansa yanda kadai yai Mata yanzu tasan baze raga mataba yau hawayene yacika Mata Ido tafara mgn da kyar muryarta narawa
tace bacci nakeji Dan Allah kabarni na kwanta nahuta kaje dakinka kaima ka kwanta ai Naga ko Ada da muke agidannan kowa dakin kwanansa da ban
Yace da kikace Aisha Amma Banda yanzu Dan wlh bazan iyaba Ni tsarina Babu raba wajan kwana da matata kitashi muje kisha ko wani abinne me ruwa in ma baza kici abinciba ga kazarkican Naga ko budewa ma bakiyiba bare kici kitashi banaso ki kwanta da yunwa
Cikin shagwabar da batasan tana dashi ba tace Ni banajin yunwa kasan me mommy tabani naci daga dawowata yau har farfesun kaza tabani naci Ni kadai tace Wai ko anty Amina Kar nabawa taci itama tamata nata se da safe kaje ka kwanta tajuyamai bayaya
Murmushi yayi azuciyarshi yace du wayanki Aisha bazan iya barinkiba yau karfin Hali kawai nake tin da naganki ciwan marata yake neman tashi
dakyar yasamu ya lanlabata sukayi nafila yai musu addu'a sosai ta zaman lfy da samun zuri,a tagari Madara me sanyi yabata Tasha dakyar sannan yajata sukaje suka kwanta daganan labari yacanja kala tsakanin nabil da Shatuwa aikuwa tafada Taji awajansa Dan gabadaya yafita hankalinshi Dan azaba jitayi Babu wani bambanci tsakanin ranar farko da tayau dan ta gurzu ahannnunshi tin tana daurewa se da tafara Mai Kuka da magiya sannan yaji tausayinta yabarta Amma ba Wai Dan yagaji da itaba jiyayima gabadaya tafi ranar farko haduwa
hawayene yake tazubo Masa shima a idansa ga wani farin ciki da natsuwa da yakeji azuciyarshi addu'a kuwa tashata awajansa awannan ranar tayarda nabil na Santa sosai Kuma yacanja yanzu yasan darajar mace Dan yanuna Mata gata sosai Wanda Bata taba kawo Haka daga wajansaba wankama shi yai Mata ajikinshi takwana mutsi kadan tayi seya tambayeta menene kome takeso har gari yawaye ranar ko masallaci bejeba agida sukayi sallar asuba tare suka dada komawa bacci
Basu tashiba se da karar wayar kiran Amina tatashesu tace taturo direba yakawo musu abin Kari yabuga kofar su yaji shuru Kuma masu gadi da yaransa sunce sunanan Babu inda sukaje har da tsokanarsa tace ko lfy Baku tashiba ko du gajiyar tafiyace da Shatuwa tayi jiya
wayar nabil yakwashe Yana dariya lokacin Shatuwa tatashi itama se kallan fuskarshi takeyi suna hada Ido dashi Tai maza tarufe idanta sumbatarta yayi yace amaryata takaina kintashi lfy yagajiyar tafiya Yana dariya me zansamu yanzu
Kukan shagwaba tahau yimasa tafada jikinshi tace bayan Kaine kagajiyar da Ni Ni Babu wani abu da zaka samu awajena fishi nake dakai se nakira anty Amina da mommy nakai kararka ka wahalar musu da Ni iya Kuma Naga yanzu kana neman kwacemin ita ko na fadamata bayanka zatabi
Dariya yafara Yana rarrashinta yace yihakuri aishata farin cikina fitilar rayuwata ai in kinyi fishi Dani zanshiga damuwa tuba nake kidince Ni imarki ta iya rudar da mutun yamanta da komai ke ta dabance nagodewa Allah da ban taba hada jiki da wata maceba se ke Kuma insha Allahu kece tafarko kece takarshe ngde Allah da yabani Mata irinki Allah yaiwa baffah albarka da su mommy bazan manta da ranar murnan haihuwata da naje mazagai muka hadu awannan ranar na rike ranar tana da mahimmanci awajena kingama siye rayuwata kinsamar min da Jin dadi da nutsuwar da bantaba jiba arayuwata rufe idanki matata kiga wani abu
Rufewa tayi mukullin mota me tsada yadanka Mata ahannu tare da wata gidan sarkar daham Dan kareriya
Ido tabude taga abinda yasa Mata ahannu kallanshi tatsaya yi tana mamaki takasa ma mgn
Yace kinfi karfin Haka awajena Aisha nadade da sayamiki wannan kyautar se mgnar Fara aikina a asibitin da daddy yaginamin zanfara aiki in mungama cin amarcinmu zan dinga duba bayin Allah Ina temakwansu shima du acikin kyautar da nai mikine da murnar dawowar matata gareni da Jin dadin farin cikin da Kika bani
Shatuwa rasa bakin mgn tayi rungume nabil tayi tana kukan farin ciki tana tamasa ruwan addu'a da gode Masa
Yace ya Isa Haka matar Nabil Bari naje nabudewa Dan Aiken da anty Amina ta turo yakawo Mana abin Kari munbarshi atsaye tin dazu
Soyaiya me tsafta da birgewa nabil da Shatuwa suke gudanarwa atsakaninsu inda suke burge kowa Kuma ake alfahari da su har yawan shakatawa suka tafi cin amarcinmu akasar waje inda suka kwashe wata Daya Acan sannan suka dawo gida suna dawowa ba dadewa nabil yafara aiki asaban asibitin shi da minister yabude Masa Yana aiki sosai Yana temakwan marasa shi mutane na alfahari da shi talakawa nayabansa sosai
Inda lokacin tafiya aikin hajji nayi minister yacika alkawarin da yayi nazuwa aikin hajji da yabiya musu iya ikwan Allah ansha kyauyanci da kokekoke a makka ko Ina za a tana katarin nabil da Shatuwa in iya na wata rigimar ko kauyanci dariya su minister suke Mata sunyi aikin hajji lfy sundawo gida lfy
Basu Dade da dawowaba shatuwa tasamu ciki nabil yayi murna sosai da su minister baffah na alfahari da auran nabil da Shatuwa nabil yasa anrusa gidan iyayan shatuwa anyi musu ginin zamani na masu kudi iya nata gidan daban nabil yagina Mata Yana temakwan Yan garinsu mazagai sosai yanda kowa nagarin mamaki yake yanda nabil yake musu barin kudi Yana temakwan su Kuma baya kyamarsu kawayan shatuwa du Suma anmusu Aure yanzu shatuwa tazama abin alfahari amazagai ko Ina hirarta akeyi ita da nabil ana samusu albarka
Shatuwa taci gaba da karatunta naboko Haka take zuwa da ciki ajikinta inda taci sa,a cikin bame laulayi bane
Finah tananan Akan bakarta na ko tahalin Kaka se nabil yazama mallakinta inda tadau aniyar binbiyar lamuranshi ako Ina yake har Allah yabata sa,a taje har asibitin da yake aiki tafaki idan mutane tashige cikin office dinsa lokacin yafita duba marasa lfy dube dube tafara anahaka wayar nabil Tai Kara yamanta betafi da itaba taga sunan da ke dauke afuskar wayar taga ansa farincikina tana gani tagane matar Nabil ce take kiranshi wani mahaukacin kishine yakamata tana dariyar mugunta tadau Kiran kafin shatuwa tayi mgn
finah tace ke Baki da hankaline da zaki kiramin saurayina awannan lokacin ke mahaukaciyar inace muna holewa Zaki takura mana waikema wacece dazaki dameshi munanan agidan da yagina min muna shakatawar mu kinganmu Nan akwancema yanzu muke bacci yadaukeshi yagama hutawa Dani kinganni akwance Akan fadanden kirjinshi Kai gaskiya my nibil ya iya soyaiya ga zumarshi medadi nabil nawane Ni kadai karki Kara kiranshi ko da Wasa kit takashe Kiran tana dariya yarinya du abinki nasan yau se kin barmin nabil Kuma Dole kice yasakeki
Nabil ne yabude kofar yashigo finah taji tsoro jikinta har rawa yake da ta ganshi fakar idansa tayi ta ajje wayar tahau kukan munafurci har da durkusawa kasa tana rokarshi yatemaka ko aurartane yayi dataga yaki kulata jikinshi tafada tarungumeshi kokarin rabata da jikinshi yafara amma ta cukikiyeshi Taki sakinshi tsawa yake daka mata Yana Mata masifa ko akanta shi tsoranshi Kar wani yashigo yagansu ahaka
Suna wannan halin Shatuwa tashigo arude da tsohon cikinta tana Nishi idanta yayi jajaur saboda kuka Allah ne yakawota lfy ko direba Bata jira yakawo taba dakanta ta tuko mota tazo ganin finah rungume jikin nabil shatuwa tadada yarda da abinda finah tagaya Mata awaya ita Kuma Dan makirci se tadada narkewa jikin nabil tana kukan kissa
shatuwa jitayi kanta na juya Mata silalewa tayi kasa ta sume lokaci guda jini yahau zuba ta kasanta ai nabil rudewa yayi besan sanda yai wurgi da finah ba yasaki wata Kara Yana Kiran sunan shatuwa se da nawaje sukaji da gudu mutane suka shigo Dan ganin meke faruwa aciki har da maaikatan asibitin temakwan gaggawa aka hau Bata aka fice da ita dakin haihuwa dagudu nabil nabiye da su du yarude Yama manta wana temako yadace yabata
yaransama shigowa sukayi dagudu suna ganin halin da ake ciki suka san finah tahada wani makircin tsakanin nabil da Shatuwa kamata sukayi suka Tisa keyarta zuwa waje Daya daga cikin yaransa yace muje mu tsareta har se hankalin oga yakwanta nasan zenemeta Dan akwai sa hannunta akan abinda yafaru
Yaran nabil ne suka Kira hajiya Fatima da Amina suka Gaya Masu shatuwa na nakuda Babu Bata lokaci suka taho zuwa asibitin dauke da Kayan da za a bukata na haihuwa Basu Dade da zuwaba shatuwa ta haihu tasamu Yan uku duka Mata nabil na kanta har tahaihu be yarda namiji ko Daya yakarbi haihuwar matarsaba zokuga murna wajan nabil shatuwa ta haifar Masa Yan uku duka Mata har da kukan murna zuwa yayi yarunggume shatuwa Yana kuka ita kuwa Ido ta rufe ko ganinshi batasan yi itama hawayenne ke fitowa daga idanta
Mejego lfy kalu ta sauka Babu wata matsala angyarata ankaita dakin hutu lokacine sukaga su hajiya Fatima nabil zuwa yayi dagudu yarunggume hajiya Fatima Yana dariya da kuka
Yace mommy Kinga ikwan Allah ko aishata farincikina ta haifarmin yan uku duka Mata asheni bansaniba Mata zan fara Haifa ayarana nafari na nunawa mata tsana cikin rashin sani Allah natuba kakafeni Allah ngd da kabani kyauta Yara Mata har uku
Amina itama Baki yaki rufuwa hajiya Fatima itama haka shatuwa taga gata kamar zasu Mai data ciki Kiran Yan uwa da abokan arziki nabil yahauyi Yana fada musu haihuwar minister da iya sunfi kowa murnar haihuwar minister gidanshi yasa akadawo da mejego da aka sallameta iya gabadaya tadawo gidan minister da Zama tana rainan Yan uku
Shatuwa Taki yiwa nabil mgn du mgnar duniyar da ze Mata bazata amsa maiba nabil yashiga damuwa sosai tin hajiya Fatima Bata gane meyake faruwaba har tagane sharesu tayi saboda mutane se bayan suna zatai musu mgn
Anyi Taran suna nagani nafada nabil da minister sunyi barin kudi asunan Yan uku ba a mgn
Yara sunci sunan hajiya Fatima da Amina da iya ana Kiran me sunan
Amina
ihisan
Me sunan hajiya Fatima ikiram
me sunan iya iman
akayan barka nabil har da lefe yahadowa shatuwa akwati goma shabiyu yace Daman yayi alkawari se ranar da tahaihu in ze hado Kayan barka ze hado da lefen shatuwa amaryar jego ataran suna har da Yan uwan nabil Mata nakasar waje du dunzo Suma sunyi rawar gani Amina yayar mejego da angwan jego ba a mgn Dan tayi bajinta ta kashe kudu sosai wajan hadu Kayan barka hajiya Fatima ma baa mgn baffah akayan barka har da shanu yahado dasu anyi shagalin suna lfy kowa yakoma gidansa lfy iyace tace Bazata komaba se shatuwa tayi arba,in
Nabil ne yasa shatuwa agaba Yana ta rukwanta Yana ta Bata hakuri Yana ranse Mata shi finah ba budurwarsa bace Amma shatuwa Taki yarda ko saurararshi takiyi
hajiya Fatima ce tashigo tace Daman Nima mgn nakeso nayi daku Wai meyake faruwa tsakaninku
Kuka shatuwa tafara Taki mgn nabil ne ya gayawa hajiya Fatima abinda yasani shatuwa tace wlh ba Haka bane mommy Basu labirin yanda sukayi da finah awaya ranar da zata haihu tayi
Ran nabil yabaci sosai yaranshi yakira yace sunemo Masa finah du inda take sukace ai Daman tin ranar da abin yafaru suna tsare da ita zuwa sukayi suka taho da ita har gaban hajiya Fatima da shatuwa da nabil
nabil da Ido yakalli Daya daga cikin yaransa yaciro bingiga yaseta Kan finah dashi Rai nabil yahade yakoma ainahin yanda yake ada yace kiyiwa matata da mahaifiyata abinda yafaru ranar da kikazo office Dina in bahakaba NASA aharbeki wlh
Nan finah jiki nafari tagaya musu gaskiya tace Dan Allah shatuwa da nabil suyi hakuri ita yanzu tadena sanshi Tama tuba gabadaya gida zata koma gaban iyayanta tayi aure Kar suyi Mata komai su barta tasan yanzu nabil yafi karfinta ko da bare yanzu San zuciyane yaja mata Haka
Hajiya Fatima ce tace da yaran nabil kubarta tatafi tinda tagane gaskiya Kuma tafadi gaskiyar abinda yake faruwa Allah yadada shiryata
Haka finah tafita jiki bakwari tana datasani Takoma garinsu
Hajiya Fatima fita tayi tabar nabil da Shatuwa kunyace takama shatuwa tataho tafada jikin nabil suka rungume juna suna dariya yace gaskiya kin wahalar Dani ko murna da godiya Baki barni nanuna mukiba na haifomin Yan uku da kikayi yanzu tinda kin huce se mgnar komawa gidako tinda kingama wanka iyama gobe tace zata koma
Bayan shekara goma shatuwa tagama karatu inda takaranci fannin lfy tazama cikakkiyar Dr tafara aiki a asibitin nabil tare suke zuwa aiki su dawo tare alokacin yaran shatuwa shida bayan haihuwar Yan uku ta haifi maza biyu Mata biyu
Girma yakama nabil da Shatuwa inda su iya baa mgn antsufa sosai da baffah
Rayuwa nabil da Shatuwa suke da iyalinsu cikin kwanciyar hankali da Jin Dadi
Alhamdulillah
Alhamdulillah
Alhamdulillah
Anan nakawo karshen Dan minister
Abinda yake dedai Allah yabamu ladansa Wanda mukayi kuskure Allah yayafe Mana Allah yasa muyi anfani da abinda ke cikin sakwan
Se Allah yasake hadamu awani saban novel Dina mesuna🤔😜 inda Rai da lfy Allah yahadamu da alheri
Godiya ta musamman ga masoyana a du inda suke Allah yabar kauna
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama*❤👸
*'YAR KWALLIYA*🥳💃
No comments